HARAMTACCEN AURE COMPLETE

 HARAMTACCEN AURE COMPLETE 

Kwance take a tsakiyar gado, tasha lullub’i da shiga ta alfarma, k’amshi ne yake tashi ta ko ina a jikinta, an mata irin lullu’bin da ake ma Amare danginta sai shirye-shiryen tafiya suke.

A cikin mayafin nata, wayar tace ri’ke a hannunta tana kan chatn sai murmushi take cikin farin ciki abinta.

Ibraheem ne Yace “Amarya kinsha ‘kamshi.

    Sai da tayi fari da ido sannan ta fara typin

  Majeeda “Haba dear banson haka fa ko ina amsa sunana Amarya ai sai randa na ganni a gidanka”

     Yace “hakane fa tawan, shiyasa ba wani kishi nake da wannan auren naki ba”

    Majeeda “Ay ‘kara ka kwantar da hankalinka kam, don wannan auren nawa dashi da babu duk ɗaya”

    Yace “kedai ki kulamin da abinda nake matu’kar so, karki bari ya ‘kwacemin a darennan plz”

  

A zuciyarta kamar ya soka mata wu’ka takeji, anma a zahiri sai tace “menene zan kula maka da?” cikin zolaya tayi maganar hakan ya sanya har sai da tayi dariya a zahiri.

Duk ‘yan ɗakin saida suka jita hakan ya sanya wata Abokiyar wasanta tace “ikon Allah! Ni majeeda na tab’a ganin amarya irinki, ranar aurenki anma baki damu ba ko kukannan bazakiyi ba?” wata tace “kema kin faɗa, nima tun d’azu nake gulmarta a zuciyatah, ban ta’ba ganin Amaryar da batayi kuka ba ranar aurenta koda babu hawaye”

“Haba Aunty zaynabu, aure ai abin farin ciki ne ga masoya, ko wanda kika ga suna kukan don rabuwa da iyayensu ne”

Cikin lullub’in nata sai data gatsina sannan tace a ranta “Allah ya tsareni da zama Masoyiya da majeed, wlhy ko kad’an aurennan bai dameni ba tunda ba sonshi nake ba”.

Saida kowa ya gama mata bankwana ya tafi, sannan ta yaye mahafin da aka mata lullu’bi dashi daman duk yaa dameta, hafsatul kiram ta zato ido tana kallonta “wai majeeda badai da gaske bakiyi kukan amarcin ba?” tace “ke banson iskanci uwar meye a cikin kukan amarcin? Aishi wlhy bai isa inyi kuka saboda aurenshi ba tunda ya yarda aka aura mishi ni”.

Tace “Allah ya huci zuciyarki”  majeeda tace “Ameen” tana gyara kwanciya “sai yaushe zaki tafi?” hafsa tace “Yanzu fa don naga ma shirin korata kike” yanayin da tayi maganar ya bama majeeda daria tace “wace ni da korar Hafsatul kiram? Idan ma anan zaki kwana wlhy muyi kwanciyarmu anan”

Hafsat ta ri’ke baki “kinga rufamin asiri, Ya umar har ya iso sai waya yakemin” majeeda tace “yayi masoyan asali” ta rataya jikkarta tace “Tohm Asubah ta gari majeedar majeed” harara takai mata, don ta tsani a haɗa sunanta dana majeed, ko bankwanarta ma bata amsa ba.

Ta duba online har ibraheem ya sauka, ta kashe wayan kawai ta murgina ta kwanta idonta cike da barci ga gajia.

Sai da barci mai daɗi ya fara ɗibanta, kamar daga sama taji an jefo mata wani abu samanta, a firgice ta farka haɗe da tashi zaune tana shirin kurma ihu tayi ido huɗu dashi.

Cikin masifa ta sauko daga kan gadon “Miye haka majeed zaka wani jefo min Abu ina cikin barci na?” galala yake mata kallo sannan Yace “ke kin d’auka barci ne ya kawo ki gidannan?” sannan ya girgiza kai yana ta’be baki “tohh kima ajiye wallahi tunda kika yarda kika aureni, kazar amarci ce aka bani in kawo miki don nasan da kwa’danta kika kwanta”.

“Allah ya kiyayemin, ba ro’karka nayi ba don haka ka kwasheta ka ficemin daga ɗaki, kuma wallahi ka sani kaine kayi kuskuren aurena”

       “ke kin isa in shigo da ita kuma in fita da ita? A cikin garar ne aka haɗo miki da ɗaƙinnan da zakice in fice miki daga ɗaki?

     “oho dai, kaima kasan nafi ‘karfin ɗakinnan ai da duk wani abu daka mallaka”

Bai tanka mata ba ya juya zai fita, ta ‘kwala mishi kira “kazo ka ficemin da ledar nan nace” bai ko juyo ba wani haushin ya ‘kara zo mata iya wuya, daman abinda tafi tsana kenan a halayyar Abdul majeed koda suna gida, jin kai da miskilanci

A k’yamace ta saka hannu ta ɗan ɗauki ledar kamar wacce ta ri’ke abin k’yama, ta wuceshi ta riga shi fita ta tillar da laidar.

A zafafe ya juyo cikin jin haushi yana kallonta, itama kallonshi take ko ɗar babu a fuskarta tana maida numfashi.

Baiyi wata-wata ba ya nufi inda take ya ɗaga hannu ya kai mata wani wawan mari, cikin zafin nama ta kauce har tanajin hucinshi.

Ta ɗago fuskarta tana kallonshi cikin mamaki da takaici “Yanzu Yaya majeed nice zaka ɗaga hannunka ka mara? Wlhy da kayi kuskuren da zaka daɗe kana dana saninshi” Yace “kuskuren me zanyi?” yana matsowa inda take “ke kin isa inyi dana sani don na mareki? Sai in dakeki na daki banza?” tace “mu daki juna dai, don na rantse banyi kama da macen da zata tsaya namiji ya dake ta ba” kafin ta rufe baki kau ya kai mata mari har saida ta du’ke, ta kai hannu tana taɓa kuncinta da take tunanin ko yaa zurma ciki.

Sosai taji marin da’kyar ta iya daurewa ta ɗago, bata tsaya wani tunani ba itama ta ɗaukeshi da zazzafan mari, shima yayi tangal tangal zai faɗi, sannan ya ɗago kallonta kawai yake yama rasa da bakin da zai mata magana.

Itama tsayawa tayi tana kallonshi sai huci take cikin shirin duk yanda ta kama, har lokacin dafe take da gefen fuskarta yana mata raɗaɗin zafi, baice mata komi ba kamar yanda ta zata, sai dai ya fara dube-dube can ya hango incense burning ɗinta, ya janyoshi ya fuzge wayarshi ya nufo ta gadan-gadan.

Batasan sanda ta runtuma waje da gudu ba, tana waige-waige can cikin sa’a itama ta hango wayar chargern ‘yan kawo Amarya ta ciro ta tsaya tana jiran isowarshi, kamar wani zaki ya tafo ya ɗaga wayar wuta itama ta ɗaga ya murɗe hannunta sannan ya tsula mata, ta ri’ke wurin ta fara murzawa.

Ya ɗaga ya ‘kara zuba mata wata a tsakiyar baya, taji zafinta sosae ta saki ihu, baba haule mai aikinda aka kawo musu ta jiyo da gudu ta fito inda suke tana sallallami.

Ganin majeed ya juya wurin baba haule ya saka majeeda ɗaga tata wayar ta zabga mishi, ya juya yana kallonta idonshi jajir da ɓacin rai baba haule tace “miye haka majeeda shi ga bari ke bazaki bari ba?” tace “ai wallahi baba haule bazai shani a banza ba biyu fa yaimun”.

Tace “yau naga abinda ya girmi kakannina ni haulatu tunda nake, wlhy ko a labari ban taɓajin amarya da angon dake faɗa ba ranar aurensu”

Yace “Allah ya sauwa’kemun da amarya da wannan baba haule kima daina faɗa”

      “haba yarannan, aurennan fa an riga da an ɗaura, ku sanya ma zuciyoyinku ruwan sanyi mana”

       Majeeda tace “Ai wallahi badai a aurena da majeed ba, ai nasha faɗa bani sonshi ya nace sai da aka aura mishi”

    Ya taso mata cikin faɗa “toh uban waye yace yana sonki? Ke kinsan na wuce da aurenki wallahi” tace “oho dai kuma saina rama ɗayan bulala na don komai zakai dai-dai nake dakai,” tana kaiwa nan ba shiri ta tsula mishi bulala.

Ko gezau baiyi ba, saima ya sha’kota fuskarshi tattare da ɓacin rai tana ta kiciniyar k’wacewa anma ya ri’kota gam, ta fara kai mishi bugu yana kaucewa yana ‘ko’karin ri’ke hannuwanta.

Wata sabuwar rigimar ce ta ‘kara kaurewa, da baba haule taga bazata iya rabawa ba ta fita da gudu tana ‘kwala ma mai gadinsu kira.

Shima hayaniyarsu taa hanashi barci ya taso da sauri yabi bayan baba haule suka shiga gidan shima mamaki fal cikin zuciyarshi, da’kyar suka ‘kwace majeeda a hannun majeed, baba haule ta shige ɗaki da ita har lokacin bakinsu baiyi shiru ba suna aika ma juna ba’kaken maganganu.

Shima ta lallab’ashi ya tafi ɗakinshi, sai huci yake irinna sadaukan mazannan.

Kowanne da ɓacin rai tare dajin haushin ɗan uwanshi ya kwanta, don barci yana ɓarawo ne kawai ya sacesu, anma kowanne zuciyarshi kamar zata fasa ‘kirji ta fito

Washe gari tunda safe baba haule tana gama haɗa musu break fast ko tsayawa karyawa batayi ba ta fita ta tari napep sai gidansu Abdul majeed.

Har lokacin ‘yan biki basu gama tafiya ba anata hada-hadar haɗa musu break, baba haule ta raɓa ta gaishe su sannan ta wuce ɗakin Umman Majeed.

Tana falon d’akinta tana waya cike da kwanciyar hankali da alama mai wayan tana tayata murnar bikinne, sai data gama wayar cikin fara’a suka gaisa da baba laure.

Umma tace “Anma dai baba haule lafiya da sassafennan” kanta a ‘kasa tace “Rashinta ne ya tado dani tunda sassafennan, don jiya bamu yi barci da kwanciyar hankali ba” Umma ta ‘kara sassauta murya cikin tashin hankali tace “meya faru baba haule?” gyara zama tayi ta faɗa mata duk abinda ya faru.

Ran Umma ya ɓaci sosai ta fara faɗa “lallai yarannan anyi mararsa mutunci, mu zasu bama kunya? Ana tunanin in anyi auren zasu daina faɗa anma suyi biris da maganarmu! Bari inje in samu Alhaji in faɗa mishi”

Baba haule tace “tohh shikenan hajia ni daman gani nake tun wuri gara a raba auren nasu tunda basu so, kar wata rana a wayi gari sun kashe kawunansu ma”

    Umma tace “su kashe kansu mana, ya fiye mana dai da ace su ba ‘kananan yara ba sun sanyamu karya Alk’awari” baba haule tace “tohh Allah dai ya kyauta”.

Koda Umma ta jema Abba da maganar shima faɗa ya dingayi, ya ciro wayarshi ya kira ‘kanenshi mahaifin majeeda ya sanar mishi, shima faɗa ya dinga yi suka ce su haɗu gidan, bazasu yarda yara su maidasu k’ananan mutane ba harsu tada Alk’awarin mahaifinsu.

Majeeda ta fito daga wanka, tana shafa mai ta jiyo k’arar motoci, da sauri ta zura doguwar riga ta fito daga bangarenta jin kamar maganar mahaifanta.

Hangosu tayi kuwa kowannensu fuskarshi babu walwala, gabanta ya faɗi tabbas akwai matsala, a sanyaye ta fito daga ɗakinta kamar marar gaskia, ta samu wuri ta rakuɓe tana gaishesu.

Umma kawai ta amsa mata, sai ga majeed ya fito da shirin fita, shima saida gabanshi ya faɗi ganinsu su duka a falon, a sanyaye kamar ita shima ya koma gefe ya zauna ‘kasa, shi baima samu kowa ya amsa mishi gaisuwan ba.

Shiru ɗakin yayi na ‘yan mintuna sannan Abba Yace “sannunku kunji, sannunku da abinda kuka aikata” duk suka k’ara sunnar da kawunansu kamar mararsa gaskiya.

Abba Yace “Tohh wlhy ku buɗe kunnuwanku kuji, ku baki isa ku maidamu k’ananan yara ba, mune nan mu muka haifeku, Alk’awari muka ɗaukar ma mahaifinmu kuma akanku bazamu karyashi ba wallahi”

   Daddyn majeeda Yace “in banda shirme da shiririta irin nasu ai idan ana shiga kabari a fito tohh za’a aurennan a kwance”

      Abba Yace “bawai kunga daman muna ɗaga muku k’afa ba, tohh wallahi kuka kuskura kuka raba aurennan sai dai ku nemi wasu iyayen badai mu ba” duk suka ɗago a tare suna kallon Abba.

      Daddy Yace “wallahi nima ba a gidana ba, kuma zan tsine miki ne duk ranar da kika k’ara faɗa da mijinki”

Umma tace “ita kaɗaice mai laifin? Baza’a ɗaurama ɗiyata laifi ba a barshi ga k’wareta, nima kau ina shirin tsine mishi duk ranar daya k’ara dukanta”

Gaba ɗaya komi ya kwance musu, sauraren iyayensu kawai suke har suka gama faɗansu suka tafi babu mai wani kuzarin magana duk sun kasa motsawa daga inda suke, har iyayen nasu suka tafi.

Sunfi rabin awa babu wanda ya motsa daga inda yake, babu wanda ya cema kowa wani abu, duk wani kuzarin dake jikinsu ya saki.

A hankali majeed Yace “miye mafita? Nifa tsakanina da Allah bazan iya zama dake a matsayin mata ba” tace “nima haka wallahi, kuma indai zamu zauna a inuwa ɗaya sai munyi faɗa” yace “hakane ya zama dole musan abunyi” tace “tohh me zamuyi?”

Yace “mu rabu kawai kowa yayi sabgarshi, tunda kowa ɓangarenshi daban” ta zaro ido “idan fa suka gano?” yace “tohh waye zai faɗa musu? Kinga saima in samar miki admission kici gaba da makarantarki” tace “hakane tohh sakeni”

Ba wani tunani ko damuwa a fuskarshi Yace “na sakeki saki ɗaya” itama ba da wani abu a ranta ba tace “saki ɗaya ai ana komawa” kafin ta rufe “baki yace “na sakeki saki biyu” tace “ai wallahi saki biyunma ana komawa, ka cikashe kawai” Yace “na sakeki saki uku.

Nikam mamaki ne ya kamani da wannan ɗanyen hukunci da suka yanke a tsakaninsu, anya kuwa zaman nasu zai yiwu a haka?

Kafinnan waye Abdul majeed? Wacece majeeda? Menene tarihin auren nasu? Idan kuka biyoni a sannu zan warware muku

WANI LOKACI KAFIN AURANSU…

Alhaji Sani da Alhaji salisu, y’an uwane dake matu’kar son junansu da son zumunci, kaka Abdul hameed shine mahaifinsu mahaifiyarsu khadija taa rasu da daɗewa, shi kaɗai ya rage musu shiyasa suke matu’kar ji dashi.

Alhaji sani wanda suke kira da Abba, kuma mijin Umma, yana da yara biyu, Abdul majeed wanda aka saka ma sunan kaka, da kuma ‘kanwarshi zahra.

Sai Alhaji saleesu shima Yara biyu ne dashi duk mata, Aunty zainabu wacce ta girme musu su duka, da Autah khadeeja (majeeda) itama sunan kakarta ne da shiyasa ake ce mata majeeda.

Tun haihuwar majeed, kaka yake matu’kar ji dashi saboda sunanshi da aka saka mishi ga yaron shiru-shiru da saurin shiga rai, babu ruwanshi da hayaniya sai dai baison raini, kusan kullum suna gidan kaka shida Aunty zainabu da ta girme mishi da shekara 3.

Aunty zainabu nada Shekara 10, majeed nada shekara 7, k’anwarshi fatima zahra tana da 2years, aka haifi majeeda, iyayensu sunyi matu’kar murna sosae, bama kamar da tun bayan haihuwar zainabu basu k’ara samun haihuwa ba sai akan majeeda.

Ranar sunah aka saka ma jaririya suna khadija, anma za’ana kiranta da majeeda, kaka yaji daɗi sosai kasancewar sunan matarshi ne aka saka mata, tun a ranar ya k’udurta wani abu a ranshi, tsakanin takwaranshi majeed, ta takwarar matarshi majeeda.

****

Aunty zainab ce ta fito da shirin fita, taci kwalliya da goyon majeeda a bayanta, ta samu momie zaune ɗakinta tana kallo.

Tace “momie zamu tafi” momie tace “tohm a dawo lafiya, a gaida kaka Alhaji” zainab tace “zaiji momie” sannan ta fito har driver ya fito da mota, ta shiga sannan ta kwance goyon majeeda ta rungumeta ya tada mota sai gidan kaka.

Tana shiga da sallamarta, Abdul majeed dake zaune kusa da kaka ya amsa mata yana “oyoyo Aunty zainab” kaka daya cika baki da dambun naman da ƴaƴanshi suka kawo mishi Yace “Allah yasa da matata kikazo mun zainabu” tace “ni baka ma son ganina kenan sai wannan tsohuwar matar taka?” kaka Yace “Ai kinsan dolene naji da deeje, kedai kwantota ki mik’omin itanan mu gaisa” ta mik’a mishi ita majeed duk ya haɗe rai.

Tana hannun kaka sai mutsilniya take irinna jarirai tana ture majeed ta k’afarta, haushi ya kamashi ya rik’o k’afafunnata ya ri’ke, kaka ya lura dashi tun haihuwar majeeda ba wani son ganinta yake kusa dashi ba .

       “majeedar zaka ɗauka ne?” saurin girgiza kai yayi.

   Kaka Yace “haba takwarah na, ina lura dakai fa tun haihuwar ɗiyarnan ba son zuwa kusa da ita kake ba”

 Majeed ya k’ara ɓata rai Yace “Ay nifa babu ruwana da ita kaka, tun haihuwarta ka daina ji dani da taazo sai dai kayita ɗaukanta, ko gidansu mukaje da ummana sai tayita ɗaukanta”

  Kaka Yace “kai bakaso ana ɗaukar matar taka ne?” da sauri yace “ni ba matata bace, bani sonta” shiru kaka yayi bai k’ara cewa komi ba.

Kiran sallahn da akayi ne ya saka zainab ta fita ɗauro Alwala, kaka ya mi’ka ma majeed ita yace “ri’keta tohm inyi sallah” kamar bazai amsheta ba, sai da kakanma ya kwantar mishi da ita sannan ya fita alwala.

Kaka na tsakar yin alwala, zainab na shirin shiga ɗakin suka jiyo majeeda ta k’wala wani uban kuka, da gudu zainab ta k’arasa shiga ɗakin ta iske bakin majeed dai-dai k’afarta ya gartsa mata ciwo da sauri ya ɗago.

Ta tsaya tana kallonshi “meka mata majeed?” ya fara kame-kame “wallahi Aunty zainab babu abinda na mata, ita keta kukanta tana halbina da k’afafunta” tace “tohh ka ɗauketa ka rarrasheta mana” badon yaso ba, ya ɗaga ta sama duk da ba wani k’warewa yayi da ɗaukan ba, aykam saitin bakinshi ta dalalo mishi tumbuɗi.

Baisan sanda ya saketa ba saida ta kusan faɗowa zainab ta ri’kota ya fita da gudu yana kakarin amai, sai da suka nutsu suka dinga mishi daria.

Haka rayuwar majeeda da majeed take tun suna k’anana, tun lokacin data fara tafiya data samo abun ɓarna saita nufeshi ta k’wala mishi, shima haka indai daga shi sai ita ne ya dinga mintsininta kenan, kwata-kwata basu zama wuri ɗaya.

Haka rayuwah taci gaba da tafiya, babu jituwa sam tsakanin majeed da majeeda, tana da shekara 6 ko wucewa zatayi sai majeed ya saka mata ‘kafa taa faɗi, gata da masifa ita ma ta ɗago suyi tayi dak’yar iyayensu suke rabasu.

Cikin haka kaka ya kwanta ciwon ajali, ya tara ‘ya’yan nashi duka ya fara musu wasiyya sannan yace “na sanku da zumunci, da kuma son zumunci, ku k’ara rik’e junanku ko bayan raina, a duk lokacin da naga khadija da Abdul majeed sai wani abu ya zomin a raina, ji nake kamar nine da mahaifiyarku, naso ina da rai inga ranar aurensu, anma kumin al’kawari ko bayan rai na zakuyi musu aure”

Alhaji Sani Yace “Insha Allahu kaka bazaka mutu bama sai kaga auren nasu”

    Kaka Yace “inaa Sani, kai dai kawai ku rik’e alk’awari, don ciwonnan nawa jikina yana bani bana tashi bane, ko bayan raina ban yafe ma duk wanda ya saɓa wannan alk’awarin ba a cikinku, majeeda itace matar majeed” tare suka haɗa baki “Insha Allah baba”

Maganar daya faɗa k’arshe kenan, sai dai yayi kalmatus shahada, rai yayi halinsa.

    Sunji mutuwar mahaifinsu sosai, sunyi kuka, tare da k’ara jaddada maganarshi ta k’arshe suna k’ara ɗaukarta da muhimmanci.

Sai dai wani Abu, majeeda da majeed suna girma suna k’ara rashin jituwa a tsakaninsu, tun suna ɗaukar abun nasu yarinta ce, har sunkai lokacin da majeeda ta gama secondry school, majeed ma ya gama makarantarshi har ya fara aiki, Aunty zainab kuma anyi mata aure da shekara ɗaya.

Yau gidansu majeed ta shirya ta tafi, zahra nata yi mata tsegumin bata son zumunci sai dai ita tazo, yau dai ta shirya driver ya tafi kaita.

Tayi sallama falon ta shiga, babu kowa, saita wuce ɗakin umma ta gaisheta sannan ta fito ta nufi ɗakin da zahra take.

Hangota tayi ta k’urama t.v kallo da alama a tsorace take, lallab’awa tayi har inda take ko sanin taa shigo ma batayi ba, sannan ta k’wala k’ara saitin kunnanta.

Aikam ta mik’e a firgece daman duk a tsorace take, ko tsayawa kallon majeeda batayi ba ta zunduma waje a guje tama rasa inda zata nufa, itama majeeda tabi bayanta da gudu tana mata dariya sai so take ta rik’ota, anma ina tama k’i tsayawa wuri ɗaya sai dai taji tayi karo da mutum.

Da sauri taja da baya zuciyarta cike da fargaba ta ɗago idonta taga ko waye, suka haɗa ido da majeed yana mata wani irin mugun kallo.

Ganin shine itama taja tsoki kawai ta nufi wurin zahra da tayi tsuru-tsuru tana kallon majeed, tace “muje matsoraciya, kinsan bazaki iya ba kika saka film ɗin horror ke kaɗai a ɗaki kina kalla”

Tace “Tohh yana iya tunda ina son kallo? Film ɗinne yayi kyau” har lokacin zahra satar kallon majeed take daya kasa motsawa daga inda yake har lokacin.

Ya daka musu wata uwar tsawa “baku da ido ne da zaku bugi mutum da wasan banzanku na k’ananan yara kuma bazaku bashi hak’uri ba?” zahra tace “kayi hak’uri yaya” tana zungurar majeeda itama ta bashi hak’uri.

Majeeda tace “hak’urin me kike bashi? Shine fa ya shigo ta hanyarmu” ta murguɗa baki sannan ta juya taci gaba da tafiyarta.

Yace “lallai ma yarinyar nan, yauma rashin kunyar zakimun?” waiwayen ɗakin ta kamayi sannan ta ɗago idonta itama ta watsa mishi wani irin kallo sannan tace “babu yarinya anan”

         “idan nazo na murɗe wannan shegen masifaffen bakin naki kyamun bayani”

Tace “zan zauna ne kamar sakara ka murɗemin baki? Kaima kasan ba tsoranka nake ba wallahi”.

Nan fa faɗa ya kaure, majeed ya kasa wucewa ɗakinshi saboda yanda majeeda ke gasa mishi maganganun, ranshi yayi matuk’ar ɓaci shiyasa yarinyar ko ganinta bai sonyi, masifaffiya ce kuma tayi matuk’ar rainashi.

A zafafe ya nufeta da niyyar kai mata mazga, dai-dai lokacin umma ta fito jin hayaniya, majeeda na tsaye inda take ko gezau ba tayi ba

Umma tace “Aaaaah, majeed mezan gani haka? Abin naku ya wuce faɗa a baki har duka zaka kai mata?” cikin jin zafi yace “Umma zan tsaya k’aramar yarinya kamar wannan ina faɗa tana faɗa ne? Ai wallahi sai ta gane ni ba sa’anta bane”.

Tace “ai sai dai in baka faɗa ba wallahi, donni bazan tsaya kana nunamin iko ba”

  Umma tace “tohh kuci gaba kunji ko? Tunda a gabana ma bazaku bari ba, kana babba anma bazaka daina shiga harkar k’annan ka ba, zo ka wuce ɗakinka” tana nuna ma majeed hanyar ɗakinshi.

Ya wuce yana aika ma majeeda da harara, itama harararshi take harya wuce ɓangarenshi, sannan taja hannun zahra suka wuce ɗakinta.

    Sai dare Driver yazo ɗaukanta, Zahra ta rakota har wurin motar. Zata shiga kenan idonta ya hango mata Majeed babu nisa da inda take, shida wata yarinya da alama zance suke, aikam dariya ta fara harda rik’e ciki. Zahra ta fara dudduba jikinta tasan halin Majeeda da dariyan mugunta tace “wai meya baki dariya haka?” ta buɗa baki zata yi magana ta k’ara kwashewa da dariya. Zahra tace “wai miye haka?” ta soma k’ulewa, shima Majeed yana jiyota hankalinshi duk ya dawo kanta sai aika mata da harara yake ta cikin duhun, dak’yar tana rik’e cikinta tace “Abin da ya bani mamaki na gani, wai mace da zuwa wurin namiji zance”.

    Zahra ta sassauta murya tace “don Allah ki daina mana, kin san dai halin Yayanmu yanzu ya taso kuyi tayi, itama budurwarnan tashi ce da shegiyar k’wak’wa”.

   Tun kafin ta gama magana Majeeda tace “barni in faɗa wallahi, an daiji kunya mace  da zuwa zance wurin namiji, ko meye ma abun so anan?”

    Cikin faɗa ya taso inda take kamar zai shige mata, zahra harta ɓalla da gudu cikin gida, itama shigewarta tayi cikin mota da sauri kafin ya ida isowa tace ma Driver ya tada su tafi. Sannan ta lek’o da kanta da k’arfi tace “kayi kai kaɗai, da wannan marar aikinyin da take biyoka har gida, wlhy k’arama tun wuri ki canja masoyi wannan ba abinso bane” sannan suka wuce nan suka barshi yana cizon yatsa data gama gaggaya mishi maganganu kuma bai mata komi ba.

    Har dare idan ta tuna ita kaɗai sai ta dinga daria, koda suna chatn da Ibraheem sai da Yace mata “wai ya na ganki yau kina cikin farin ciki?” Tace “Ay kullum ma cikin farin ciki nake da annashuwa indai ina tare dakai”

Yace “Hakane Masoyiyatah, anma da alama farin cikin naki na yau yaafi na kullum” tace “hakane fa, wlhy wani abune ya bani daria, anma dai bazaka tambayeni ko miye ba?”

      “ko ban tambayeki ba nasan zaki faɗamin ba?😉

    “hakane Masoyi, anma ka share kawai”

    “na share Masoyiyah, bani labari”

     “ba labari sai dai na zuciyatah”

     “shi nafiso masoyiyah, bani labarin soyayyatah a cikin zuciyarki”

    Anan suka bar maganar, suka ci gaba da firarsu kawai, anma idanta tuna abinda taima Majeed sai ta dinga dariya ita kaɗai, kafin shima ya tashi ramawa.

***

   Sun gama fira da Ibraheem yayan k’awarta kuma saurayinta, fito ta rakashi har gaban mota suna fira kamar karsu rabu.

   Daddy ne ya shigo ya kallesu Majeeda sai k’yalk’yala daria take, tana ganin haka tayi saurin shanye dariyarta ta dai-daita nutsuwarta, ibraheem ya fita har inda daddy yake ya duk’a ya gaisheshi, sama-sama ya amsa sannan ya wuce cikin gida.

    A sanyaye Ibraheem ya koma wurin motarshi ya shiga, ta rik’e k’ofar motar duk taa marairaice fuska ganin canjawar yanayinshi.

    Sai ga motar Majeed taa shigo gidan, ta ɗaga kai kawai sannan ta maida hankalinta wurin Ibraheem.

    Zuwa yayi har inda suke sannan yayi parking motar ya fito, zai wuce Ibraheem ya mik’a mishi hannu suka gaisa sannan yayi gaba yana cewa…

   “yau naaga nacin zance, saurayi na zaune saman seat ɗin mota don tsabar baiji da mace zai barta tsaye tana shan gajia” ya wucewarshi kawai.

   Tasan da ita yake, kawai dai bata son ta tanka mishi a gaban Ibraheem ne ya sakata sharewa, ba daɗewa ta sallami Ibraheem sannan ta shige gidan, ɗakinta kawai ta wuce donma karsu k’ara haɗuwa, bata sanma sanda yabar gidan ba.

   Da safe taje gaishe da Daddynta, harta taso zata tafi ya tsaida ita, ta koma ta zauna kanta a k’asa gabanta naa faɗuwa.

   “ɗazu wanne yaro ne yazo gidannan?” sai da ta ɗanyi shiru sannan tace “Yayan k’awata ne Daddy”

    “Yayan k’awarki kuma meya kawoshi gidannan?” shiru ta k’arayi har saida ya k’ara maimaita tambayarshi sannan tace “ba komi fa Daddy”.

   Yace “ina fatan hakanne, domin kuwa naa riga dana miki miji” da sauri ta ɗago da fuskarta “miji kuma Daddy?”

    “k’warai ma kuwa, idan ma bakisan ko wanene ba yanzu zaki sani, domin kuwa tun kina k’aramarki mukayi ma Mahaifinmu Alk’awarin haɗaku aure da Majeed”

   Wani irin zabura tayi “Majeed dai Abba? Ni wallahi bazan aureshi ba, na rantse bani sonshi” yace “tohh naji baki sonshi, tashi ficemin daganan, maganar aure tsakaninku dai babu fashi” nan ta k’ara fasa wani kukan, ta tashi ta nufi ɗakinta har tana tuntuɓe a hanya faɗi take ita wallahi bazata taɓa aure Majeed ba.Batayi wani barcin kirki ba saboda yanda ta k’agara gari ya waye, ga uban kukan da tasha da safe duk idanunta sun kunbura. Gari na gama haske ta shirya wurin 11 tace ma Momie taa tafi gidan Aunty Zainab, da yake tasan matsalanta da damuwanta kuma bata da wani abokin shawara kamar Aunty Zainab ɗin shiyasa momie bata hanata taje ta kwantar mata da hankali ba.

   Napep ta tara ya kaita gidan Aunty Zainab, tana sauka daga napep ɗin yana fitowa da motarshi daga gidan, ta juyar da kanta gefe kamar bata ganshi ba, yayo kanta da mota kuwa har ya kusan take mata k’afa sannan ya fito daga motar.

     Yana nunata da ɗan yatsa yace “ina fatan kinsan abinda ke faruwa, kuma baki amince musu ba” sai data gatsina sannan tace “kaima kasani ai bazan taɓa amince da auran ka ba”

        “Yaa miki kyau, don wallahi aka aura min ke gutsun-gutsun ina iya miki in jefar dake, don ko kaɗan baki cikin kalar matan da nake so”

       Tsoki kawai taja ta juya ta tafi don batason tsayawa magana dashi ma, wata tsanar shi ce ke k’ara zo mata ta shige gidan Aunty Zainab kawai.

Tun daga ranar kullum cikin damuwa suke, babu wanda bai kwanta rashin lafiya a cikinsu ba, k’iyayya sosai suke nuna ma junansu, anma iyayensu sukai watsi dasu sai dai hidimar biki kawai suke.

     Duk yanda suka so a fasa auren sai da aka ɗaura shi su duka babu mai so, a tunaninsu iyayen idan akayi auren daga baya zasu warware ne suci gaba da son junansu, basu sanda babban kuskure ne suka tafka ba (inji rash kardam).

A gurguje dai

Mu koma labari….

Ci gaban labari

    A hankali majeed Yace “miye mafita? Nifa tsakanina da Allah bazan iya zama dake a matsayin mata ba” tace “nima haka wallahi, kuma indai zamu zauna a inuwa ɗaya sai munyi faɗa” yace “hakane ya zama dole musan abunyi” tace “tohh me zamuyi?”

    Yace “mu rabu kawai kowa yayi sabgarshi, tunda kowa ɓangarenshi daban” ta zaro ido “idan fa suka gano?” yace “tohh waye zai faɗa musu? Kinga saima in samar miki admission kici gaba da makarantarki” tace “hakane tohh sakeni”

    Ba wani tunani ko damuwa a fuskarshi Yace “na sakeki saki ɗaya” itama ba da wani abu a ranta ba tace “saki ɗaya ai ana komawa” kafin ta rufe “baki yace “na sakeki saki biyu” tace “ai wallahi saki biyunma ana komawa, ka cikashe kawai” Yace “na sakeki saki uku.

    Wani ihun daɗi ta saki saboda tsananin farin ciki, ta tashi tana tsallen murna, harta tafi ta dawo.

       “Anma babu ruwan kowa da harkar kowa? Babu aurenka a kaina, babu faɗa a tsakaninmu, ko nuna iko da shisshigi” yaja tsoki yana juyar da fuska

      “ke duk wannan ya dama, salon kuma shegen surutunki ya kai ki faɗa ma wani”

     “Anma haka zamu zauna ba tare da kowa ya sani ba?

       “nafa gaji da ganinki wurinnan malama, babu abinda ke tsakanina dake, ki ɓacemun da gani”

Kamar ta maida mishi da bak’a, ta tuna idan tayi hakan faɗa ne zasu ci gaba, ta taɓe baki kawai ta shige ɗakinta, cikin ɗokin ta kira ibraheem ta faɗa mar.

     Kiranshi ta dinga yi anma tak’i shiga har ranta ya soma ɓaci don yanda ta k’agara ta faɗa mishi tasan sai yaa fita murna, cikin haka sai ga kiran hafsatul kiram babbar Aminiyarta kenan.

  “Ran Amarya ya daɗe tare dana angonta”

   “wacece Amarya? Yanzu duk k’wak’warki dai bazaki kirani da wannan sunan ba” inji majeeda.

     Bayan hafsatul kiram tayi dariya tace “Tohh ina angon naki? Na kasa hak’ura ne na kira ki, duk da nasan kunanan tare yana jinya” ta faɗa cikin tsokana don tasan zata k’ular da majeeda.

    “banson iskanci fa hafsa, ina auren yake da har zai samu zuwa kusa dani ma?”

   “saman kanki mana, da aka ɗaura miki jiya”.

     “tohh wallahi na saukeshi yanzunnan, karma ki ɓatan rai ina cikin farin ciki?”

     “kamarya majeeda?” ta faɗa da mamaki”

Da yake majeeda ta yarda da hafsatul kiram sosai, kuma tasan duk rintsi bazata taɓa faɗama wani sirrinta ba, kuma tana cikin son ta faɗa ma wani, nan take ta kwashe komai ta faɗa mata.

   Shiru tayi kamar wacce tayi suman zaune sai da majeeda tace “ko kin kashe wayar ne?”

   “kin kashemin bakin magana dai? Yanzu auren naku kuka kashe a washe garin amarcinki? Kuma zaku zauna a gida ɗaya? Haba majeeda kamar dai…..”

      “kinga rik’e mamakinki da duk maganganunki, da kuma sirrina, kinsan don na yarda dake ne na faɗa miki ko? Babu wani abin dana sanin insha Allah”

   “Allah ya yarda, anma duk kin sakemin jiki”

   “tohh a warware lafiya, ki gaishe da Ya umar” bata jira me zata ce ba ta kashe wayar.

  Layin ibraheem taci gaba da neman, sai sintiri take a tsakar ɗakinta, can taji taa fara ringing, ta samu kujera ta zauna tana jiran ya ɗaga anma har ta katse shiru.

    Sai da ta mishi kira biyu ana ukun ne ya ɗaga da alama barci ya tashi.

   “na kwanta barci da tunaninki, banyi mafarkin komai ba bayanki, gashi na farka da zazzak’ar muryarki, plz in fara jin sautin lallausan murmushin masoyiyah ta” sai da ta mishi murmushin sabo da yanda kalamanshi suka mata daɗi tace, “ba murmushi na kaɗai zaka farka dashi ba, harda Albishir ɗin da zaiyi maka daɗi sosai”

  “faɗamin da sauri masoyiyah, tunda kafin ki faɗa ga tukuicinki” ya sakar mata daddaɗan kiss a kunne

Ta rufe ido ta buɗe cikin nishaɗi, “Yaimin daɗi sosae masoyi, karfa ka sakani mantawa da albishir ɗin”

     “sai in k’ara miki wanda zai saka ki tuna”

  “banma manta bafa, anma duk da haka naa biyoka bashi, yanzu miye yayi mana katanga da zama mallakin juna?”

     “Auren ki da majeed mana” inji ibraheem

    “tohh k’ara kwantar da hankalinka, don indai aurena ne yanzu…..”

Maganar ta mak’ale mata saboda ganinshi tsaye a k’ofar falonta, yana wurgo mata wani mugun kallo

  Shirun da Ibraheem yaji tayi ya saka ya dinga “hello, masoyiyah, kina jina?”

      “ina jinka masoyi zan kiraka yanzu,” sannan ta katse kiran tana k’ok’arin dai dai ta nutsuwarta.

   Ta kalli majeed tana mayar mishi da irin kallon da yake mata “Meya shigo dakai ɓangarena? Ka mantane sharaɗinmu na babu wanda zai shiga harkar wani? Kuma bazaka zo inda nake ba”

     “ke har kina da bakin magana? Baki manta da sharaɗinmu ba meyasa kike k’ok’arin faɗa mishi sirrinmu?”

         “ni ban faɗa mishi ba ko kaaji naa faɗa?”

   “kina shirin faɗa dai, wannan ba k’aramar magana bace da idan kin faɗa ma wani yaɗuwarta bazai kawo matsala ba, har yaushe kike tare da Ibraheem da kika yarda dashi har zaki faɗa mishi wannan sirrin namu? Ke kin kasa rik’e sirrinki ta yaya kike tunanin wani zai rik’e miki? Wallahi karki kuskura ki faɗa ma wani wannan maganar”

   Jikinta yaa riga da yaayi sanyi, taama kasa maida mishi, ya juya ya bar ɗakin, taja tsoki “daman gulmace da sa ido ya shigo dakai kenan” ta harari k’ofan tana murguɗa baki kamar yana ganinta, sannan ta tashi ta shige ɗakinta.

   Yinin ranar bak’i ta dingayi masu zuwa ganin gidan Amarya, kowah yazo sai ya zagaya gidan ana lellek’a ɗakunanta, ba k’aramin haɗuwa da tsaruwa gidan yayi ba, ga dukiyar da iyayenta suka zuba mata a ciki.

  Ba ita ta zauna ba sai 9 na dare bak’inta suka gama tafiya, duk taa gaji ga yunwa bata samu taa girka komai ba, baba haule dai taa koma gida,

     Kwanciyah tayi ta jawo wayarta miss calls ɗin Ibraheem ne babu iyaka, itama ta kirashi bai ɗaga ba, ga yunwar dake yatsina mata y’an hanji, mik’ewa tayi kawai ta nufi kitchen ta ɗaura girki, da yake an haɗa mata komi.

   Fried cous-cous ta dafa dai-dai cikinta, sai k’amshi ne ke tashi, tananan tsaye harya gama dahuwa ta sauke ta jawo plate zata zuba kenan ta juyo wayarta na ringing a ɗaki, ta ajiye da sauri ta tafi ta ɗauka wayar.

   Ibraheem ne, ta zauna gefen gado sannan da ɗaga kiran.

     “Da fatan ma’abociyar kyakkyawan murmushin nan tana cikin nishaɗi”

   “sosai tunda ina tare da muryan masoyinah”

     “kawai ɗazun ina cikin ɗokin jin albishir daga gareki, saiki yankemin waya, halan angonki ne ya kiraki?”

      “shiya shigo dai, anma ai bai isa don ina waya dakai in katse saboda shi ba”

   “Hmm, kin manta da mijinki ne? Kina kulawa dai don baniso muna shiga hak’k’ik aure da yawa” sai can ya tuna kuma.

       “Yauwah aurenki yanzu ma… me kike cewa?” sai da ta ɗan daburce duk taa rasa me zata ce sannan tace “yanzu ne yake k’ara damuna masoyi, anya bazamu gudu muyi aurenmu?”

    “Aure akan aure kenan? Nifa banda matsala da iyayena Masoyiyah jiran fitowarki kawai nake, basai mun gudu ba kinji tawan”

     “tohh” kawai tace mishi a zuciyarta tunani take anya bazata faɗa mishi ba? Kuma sai taji tsoran kashedin da Majeed yayi mata haka kawai ta fasa faɗa mishi.

Majeed yana ɗaki shima babu inda yaje, sallah ce kawai take fiddashi, sai juyi yake akan gadonshi saboda yunwar da yakeji tunda rana, daya juya sai yayi tsaki “Yanzu mutum ya tafi restaurant yana haɗuwa da idon sani akama yi mishi surutun ya fara fita cin abinci”

    Gani yayi zaman bazai mishi ba, ya tafi kitchen ya duba ko zai samu abinci.

    Cikin sa’a kuwa ya hango tukunya saman cooker gas, ita ya fara buɗawa, abinci ya gani kuwa da zafinshi k’amshi sai tashi yake, ya jawo plate ɗin daya gani a wurin ya juyeshi tass sannan ya fito falo ya zauna ya fara ci.

Sai da ta gama wayanta da ibraheem daman yunwa duk taa addabeta, ta fito ta wuce shi a falo ta nufi kitchen ko kallon inda yake batai ba, shima ko sanin taa wuce baiyi ba.

Ta duba inda ta ajiye plate babu, kodai bata ɗauko ba? Ta janyo wani plate ɗin dai ta taho zuba abinci, tana buɗa tukunya wayam babu komi, fiddo idanu tayi waje cikin mamaki ta ɗauka tukunyar tana girgizawa kodai bata gani dai dai bane, anma wayam babu komai.

   Toh waye zai shigo har gidanta ya kwashe mata girki? Kodai aljanu ne, can ta tuna fa ay ba ita kaɗai bane a cikin gidan, toh shi kuma mezai dameshi da girkinta? Tunani dai ta dinga yi taga bazai mata ba, ta fito daga kitchen ɗin can ta hango shi ya saka plate a gaba yana kwasar girki.

  Cikin jin haushi tace, “Anma dai in ba’a kawoni da ɗaki a gara ba an kawo ni da cous-cous ko?”

    Baiko ɗago ya kalleta ba Yace “Anma a gidana kike zaune, indai zaki zaunamin a ɗaki, dole ne kimin girki, bayan wannan babu wani abu” ba tace mishi komi ba ta koma kitchen ɗin don yanzu batason magana tayi nisa tsakaninsu yanzu zasu fara faɗa.

Bayan wata biyu…

   Majeeda ce sanye cikin doguwar rigar material, ta ɗaure kanta da ɗan kwalin, ta jawo Abayarta har k’asa ta saka, sannan ta ɗaura nik’ab a fuskarta, ta janyo hand bag ɗinta sannan ta fito waje. Driver nanan yana jiranta, ta buɗe sit ɗin baya ta zauna yaja motan sai ALQALAM UNIVERSITY dake cikin garin katsina.

   Kullum shigarta kenan tunda ta fara shiga makarantar, kamar wata matar aure shiya saka har yanzu batayi koda k’awa babu ruwanta da kowah.

      Sai marece sosae ta koma gidan, bata lura da motanshi ba ta saka kanta cikin falon, maganganu ta fara jiyowa.

     “haba Aisha, ba nace karki zomin gida ba? Karki manta fa akwai banbanci tsakanin gidanmu da gidana”.

   “akwai banbanci, anma kasan ko inane zan iya zuwa don in ganka, tunda kai ba son zuwa gidanmu kake ba”

     “naji, anma kincemin inzo banzo ba? Ki k’ara hak’uri mana lokaci kaɗan ya rage a fara maganar aurenmu”

    “kullum haka kake cewa, ni dai tunda nazo ka bari ko gaisawa muyi”

Wani abu ne ya tsaya ma majeeda har wuya, kamar ta kama majeeda ta shak’e takeji, a ciki-ciki tayi sallama ta shiga ɗakin duk suka juyo suna kallonta, ta k’urama majeed ido kawai, taa daɗe bata ganshi ba, don tunda ya fara zuwa aiki ya daina zaman gida, girki ma idan taayi a kitchen take bar mishi.

   taa rigashi ɗauke idanunta, ba tare da tace komi ba ta shige ɗakinta.

      Ibraheem ya faɗo mata a rai, yanzu yaa daina kiranta, ko kiranshi tayi sai yaga daman ɗagawa, koya ɗaukama bazasu wani daɗe ba zai kashe wayan, shiyasa itama ta daina damunshi, yanzu hankalinta akan karatun kawai ta maidashi.

   Cikin ɗakinta haushin Aisha ne kawai ya cika mata ciki, daganan tana jiyo maganganunsu tak’i tashi ta tafi duk da maganar da majeed ke mata, tashi tayi ta tafi falon bayan ta cire hijabin jikinta, ta gyara ɗaurin kwallabin sannan ta fito.

    Shiru suka k’arayi suna kallonta, ita kam kamar ma batasan dasu ba, ta k’arasa gaban kallo ta kunna, ta rik’o remote ɗin ta zauna kallo.

      K’asa-k’asa Aisha taci gaba da mishi magana duk hankalinshi na kan majeeda, ta k’ure k’arar ma yanda bazasu ji ba, duk a takure yake anma Aisha taa kasa ganewa, kawai ya juya zai tafi ɗakinshi itama ta mik’e zata bishi.

Majeeda ce tasha gabanta,

       “kinfa fara wuce iyaka malama, don tsabar rashin kunya ki biyo mijina har gidana, kinga ban tanka ba shine zaki bishi har ɗaki, ubanme zaki yo a ciki?”

   “Akan mijin da bai damu dake ba baya sonki kike tada jijiyoyin wuya? Abinda ranki ya baki shi zamu yo”

    “k’arya kike wallahi ki shigo har gidana kina faɗamin magana, banza mai k’wak’war namiji har gidanshi, ai naga mugun son da yake miki ne ya saka sai dai ke ki biyoshi”

    “laaah, ni kike faɗa ma magana? Kana jinta fa majeed”

       

Duk suka maida kallonsu ga majeed ɗin, “Da bakizo gidanta ba taa faɗa miki? Kinga muje in maida ke gida”

       Majeeda tsayawa tayi tana kallonsu har suka fice, lallaima yaa fifita wannan banzar a kaina kenan, har saida ta jiyo ta mata gwalo, haushi kamar ta fasa ihu.

    Lallai don yaga yanzu babu aurenshi a kaina ne harda shigomin da wata a gida, wallahi bazan yarda ba nima sai na rama.

   Bai wani daɗe ba ya dawo, anan ya wuce ta inda ya barta, ya wuceta inda take tsaye yana tafiya da kakkausar murya cikin gargaɗi yace, “babu ruwanki da kowacece zatazo wurina, babu ruwan wani da harkar wani” ya wuceta sannan ya k’arasa maganar.

   Kwana biyu tayi tana tunanin yanda zata rama abunda Majeed ya mata anma taa gaza samun mafita, gashi kullum sai ya raba dare kafin ya shigo gidan, tunda safe kuma yake fita, ita yaa maida ita er gadin gida duk da baiyi mata shamaki da fita ba.

   Yauma da marece sosai ta dawo daga lecture, suna hanya drivern ta ya ɗaukota, da yake hanyar gidansu majeed ne, hakanan taji tanaso taje gaishe dasu, ta cema drivern ya biya da ita.

    Ya ajjeta ta fito har zata tafi kuma ta dawo “malam balah zaka iya tafiya, zan ɗan daɗe ne” yace, “tohh hajia” sannan ta shiga gidan da sallamarta. 

     Zahra taci karo da ita, aikam ta buga uban tsalle da gudu ta taho rungumeta “Oyoyo Matar Yayanmu”

     “Aifa sis kamar a bakinki aka raɗa wannan suna, ina umma?”

    “tana ciki ki shiga bari inzo”

     “tohm naa bari”.

Ta yaye labulen ɗakin Umma ta shiga haɗe da sallama, ta ɗago tana amsawa tana ganin Majeeda ce ta k’ara faɗaɗa fara’arta tana mata sannu da zuwa, sai yanzu ne ma wata kunya ta k’ara nannaɗeta, ta duk’a har k’asa tana gaida Umma ta amsa mata.

      “Ina majeed ɗin ko ba tare kuke ba?”

    “Daga makaranta ne yace Driver ya kawoni, anma zaizo ɗaukana Umma”

     “Tohh Allah kawoshi lafiya, kuna dai zaune lafiya ko?”

     “Alhmdlh Umma”

  “ki faɗamin gaskia dai naaga duk kin rame” wai taa rame fa, tace a ranta, tana tuna randa taje gida momie cewa ta dinga yi taayi k’iba taayi haske, alamar dai tana mata zargin ciki ne da ita, da yake momie ce sai ta ce mata “momie ni kece uwah ta farko da akama ɗiyarta auren dole kuma tazo ganin gida a ce mata tayi k’iba” momie tace “watau ma auren dole aka miki ko? Kina nufin har yanzu baku zaman lafiya da mijin naki?” tace ma momie, “ba haka nake nufi ba momie”.

      Umma ce ta katse mata tunani “Yadai kikai shiru Majeeda? Indai da matsala ki faɗamun in tsawata mishi”

     “ba wani matsala Umma, kawai kwana biyu banji daɗi bane” ta k’ak’alo k’arya.

   “tohh Allah ya k’ara lafiya kundai je asibiti ko?”

   “Ai naaji sauk’i Umma”

     Zahra ce ta shigo ta janye ta suka koma can ɗakinta da fira, itama tsokanarta take kodai sun samu rabo,

    “nikam sis kamar Abinda kowa ke jira kenan, duka yaushe aka gama hidimar bikin ko hutawa bamu yi ba?”

       “Abinda kowa ke jira mana kenan, in hutawa ne kam ai kinyi, anma burinsu Abba kenan kullum ganin en jikokinsu”  sai da gabanta ya faɗi, tayi shiru tama rasa abin cewa, tohh ta inama zata samu cikin tunda ba auren garesu ba?.

   Haka ta yini cikin gidan duk tayi sukuku kuma, har bayan isha’i taa rasa yanda zata tafi kuma gashi tace ma Umma Majeed ne zaizo su tafi, yanke shawarah tayi kawai ta kira malam balah, shi ɗinma ta dinga kiranshi anma wayanshi a kashe.

Wurin 9 Umma ta lek’o ɗakin Zahra, “wai ina majeed ya tsayane?”

        “Umma inajin dai wani abunne ya rik’eshi, anma zan tafi kawai kar dare yayi sosai”

    “A’ah ya zaki tafi ke kaɗai? Ki mishi waya dai yayi sauri yazo ku tafi” ita kam ko number wayarshi ma bata da, yama za’ayi yazo ɗaukanta.

   Har 10 tayi ta rasa dabarar da zatayi tabar gidan Umma, su duka suna zaune a falo, gabanta sai faɗuwa yake, tun farko ma meya sakata yin k’arya.

      Sa’a tayi wayarta ta fara ringing, tayi saurin maida wayan silent sannan tayi kamar taa ɗauka sannan ta ɗan matsa daga inda su Umma suke ta fara magana yanda zasuji.

     “hi, lafiya lau ya aiki?” ta ɗanyi shiru sannan tace, “A’ah ya za’ai na tafi kace na jiraka?”

     “Ayyah! Tohh a dawo lafia, sai ka dawo gidan” tun kafin ta zauna Zahra tace “Halan ina ya tsaya?”

      “wai kinji fa gaisuwar wani baban ɗan wurin aikinsu sukaje Mashi, anma suna hanya kuma motan a cike take, yace inje a napep” Umma tace, “Ayyah!Allah yaji k’an musulmi, sai kiyi sauri dare na k’arayi, tace “tohh shknan Umma”

Zahra ce ta rakata har bakin titi, sun daɗe suna tsaida abin hawa duk da mutane a ciki gashi batason hawan mashin, dak’yar suka samu wani mai napep ta shiga sukayi bankwana da zahra.

    Har ya tada zai tafi Yace “hajia ina za’a kaiki?” tace, “G.R.A”

     “kiyi hak’uri hajia bazanje can yanzu ba ina ɗan sauri ne” babu yanda ta iya ta fito daga motan gashi dare ya fara nisa 10:3., ta juya ko burbuɗin Zahra babu, ga unguwar babu mutane.

  Tsayuwar ta fara gajia da ita ta ciro wayarta tana dubawa, ba don tana da abunyi da ita ba, sai don kawai ta rasa abinyi gashi har lokacin ba wani motan da zata hau.

       Wata haɗaɗɗiyar mota ce ja, mai shegen kyau ta wuce inda take, sai kuma akayi reverse da motar aka dawo saitin da take, kaudar da kanta tayi sannan ta matsa gefe. Kusan mintina biyar mai motan bai fito ba kuma shi bai tafi ba ita kamar ma batasan da wani mota a wurinba.

    Buɗe motan yayi ya fito da takunshi na k’asaita, “Masha Allah” na faɗa saboda irin kyaun dana hango a tattare dashi, harna kusan jefar da wayata kasancewar darene ina tunanin ko Aljani ne, dai dai inda Majeeda take ya tsaya.

    “Da alama kina jiran Abin hawa, gashi kuma dare ya fara nisa zai miki wahalan samu” kajimin mutum ko ina ruwanshi dani

   “hakane zan samu insha Allah”

      “Zai miki wahalan samu fa, kiyi shawara da zuciyarki idan harta amince miki zan kaiki har inda kikeso, babu daɗi kamilalliyar mace kamarki ta tsaya a titi a cikin darennan”

    Maganarshi fa hakane, idanma ya tafi ya zata samu wanda zai kaita gida? Kuma da alamar natsuwa a tattare dashi ta san bazai cutar da ita ba, gaba tayi wurin motar kawai ba tace komi ba, ya buɗe mata yaci gaba da karanto addu’ah a ranta.

    Har k’ofar gidanta ya kaita “ajjeni nanma yayi” yayi parking ta fito tana mishi godia, murmushi kawai yayi yaja motanshi, dai dai lokacin majeed shima ya sako motanshi kuma yaga lokacinda ta fita daga motan.

     Kamar wanda ake hankaɗawa ya shiga gidan tana dai-dai shiga ɗakinta yasha gabanta,

    “daga gidan ubanwa kike?” na ɗauka “gidan ubanka zatace”😄 tunda gidansu taje,anma sai tace “gaishe dasu Umma mana, kana da matsala da fitata ne?”

     “k’arya kike tun ɗazu Umma tacemun kin taho, wane ɗan iskane ya maidoki?”

   “kash!” ta dafe kanta da hannu ɗaya “kaga nama mnta ban tambaya sunanshi ba, ragemin hanya yayi, babu ruwan wani da harkar wani” shiru yayi yana kallonta yama rasa bakin magana, tohh meyasa ma ya tanka mata? Shi ina ruwanshi kowa ma zata kula.

   Ta juya ta barshi anan zata shige ɗakinta, k’afarta ta zamo bata ankara ba ta taho zata faɗo da sauri ya tare ta ta faɗa a k’irjinshi ta tallabeta da hannuwanshi, kallonshi take cikin fargaba saboda yanda ta kusa faɗuwa, sai maida numfashi take, shima kallonta yake cikin ido, wani irin yanayi da bai taɓaji ba ya ziyarceshi wannan kallon da suke ma juna.

   K’ara matseta yayi a k’irjinshi, tsawon lokaci suna a haka kafinta lumshe kyawawan idanunta ta buɗe, idonshi dai-dai laɓɓanta ta buɗesu a hankali tace “da zafi” yanda ya mata rik’on, sakinta yayi yana dai-daita kanshi, sannan ya juya ya tafi yana waiwayenta, itama kasa motsawa tayi daga inda take ta k’ura mishi ido cikin wani yanayi harya shige ɗakinshi.

      Jiki a sanyaye ta shige ɗakinta, ta kasa mantawa da yanayin data motsa fuskar majeed ce ke mata yawo a sanda take a k’irjinshi.

    Haka Majeed ma ya kwanta barci da tunanin abinda ya faru, daya rufe idonshi yanayin yake dawo mishi, koda ya buɗe kuwa bazai daina ganinshi da majeeda rungume ba, juyi kawai ya dingayi a lallausar katifarshi yana jiran lokacin da barci zai ɗaukeshi.

Hmm niko nace kome hakan ke nufi??

    Da Asuba, ciwon mara ne ya farkar da ita, tun cikin barci ta fara juye-juye harta farka, ta dafe cikinta ko motsi batason yi, tanason ta ɗauko maganinta anma ta kasa tashi saboda yanda ya matsa mata.

      Dak’yar ta samu ta mik’e ta jawo jikkarta ta fara laluben maganin sai dai kwalinshi babu ko ɗaya, kamar ta fasa kuka ga wani irin azababben ciwo, haka tana duk’ewa ta samu ta haɗa ruwan zafi a toilet taje tayi wanka anma duk da haka kamar ana k’ara tunzuro ciwon cikin gashi ita kaɗai a ɗaki.

     Dak’yar ta iya k’arfin halin kwaso kuɗi a jikkarta ta fito mai gadi ya siyo mata, da yake a ɗan duk’e take tafiya rik’e da cikinta ga azabar ciwo, bata lura dashi yana shigowa falon ba ita kuma zata fita harta kusan kai mishi karo, da sauri ta dawo da baya, kanta a k’asa tabi gefenshi zata wuce, shima gefen da zata wuce yabi suka kusan haɗewa a tare, kuma kowannw ya koma ɗayan gefen, da suka kasa wucewa dai ya saka hannuwanshi biyu saman kafaɗarta, sannan ya juyar da ita ya wuce.

    Wani irin murɗawa cikinta yayi anan ta duk’e-duk’e rik’e da cikinta, ta daɗe a haka kafinta iya mik’ewa tana ɗagowa suka haɗa ido da majeed, duk ta daburce tace, “yadai?” yaɗan saki fuskarshi “ba komi”, sannan ta juya ta wuce a wahalce.

     Bata iske mai gadi ba, da alama bai gidan gashi duk taa gama jigata, haka ta lallaɓa ta koma ɗakinta, tana faɗawa gado ta saki kukanta marar sauti ga ciwon sai k’aruwa yake, ta dinga murgina saman gado harta sauko k’asa.

    “Ga maganin” taji ya ambata, ta ɗaga fuskarta tana kallonshi rik’e da laida a hannu, ya ajje robar faro da cup a kusa da ita, ta mik’a hannu ta ansa maganin, irin wanda takesha ne da pad guda biyu, ta ɓallo guda ɗaya ya mik’a mata cup ɗin ruwa ta haɗiye dak’yar sannan tace “na gode” ta koma ta sulale k’asa tana jiran ciwon ya lafa, a haka barci ya kwasheta duk taa k’udundune wuri ɗaya.

    Tausayi ta bashi ganin yanda tayi kwanciyar duk taa takura, lokaci ɗaya har taayi ramar dole, sai lokacin ya tuna ko break fast batayi ba ya bata magani, da sauri ya tafi kitchen ya ɗauko flask da kayan tea ya ajje mata.

     Tananan kwance inda ya barta tana barci, anma da alama batajin daɗin barcin ciwon cikin ma bai gama sakinta ba sai rumtse ido take tana rik’e ciki.

        Bazai juri ganinta a k’asa ba, ya saka hannu ya tallabota, kamar yaa ɗauka jaririya, ya dire ta saman gado, tun lokacin da yaa ɗaukota ta farka, anma ta kasa buɗa idonta wani irin kunyarshi maa takeji.

   Megasa Yaya majeed zaina taɓani koya manta yanzu babu aure tsakaninmu? tunaninta ya katse saboda yanda mararta ta k’ara juyewa, tai wani irin k’ara batasan lokacin data k’ank’ame hannunshi da hannu ɗaya ba, ɗayan hannunta na rik’e a cikinta har lokacin da yake yana tsugune saitinta.

   Wani irin tausayi take bashi ganin yanda takeyi, fuskarshi kamar zai tayata kukan, ya kalli hannunta dake sak’ale a nashi, zara-zaran yatsunta masu kyau sosai da taima ado da jan lalle, baisan sanda yaci gaba da murzasu a hankali ba yana kallon kyakkyawar fuskarta, sai runtse ido take, ga ciwon ciki, ga wani irin yanayin da takeji hannunta rik’e a hannun majeed.

   Kallonta yaci gaba dayi, sai yanzu ne yake k’are mata kallo, ya saka hannu ya yaye mata yalwataccen gashin kanta mai sulɓi daya rufe mata fuska, fara ce tas, irin farinnan mai kyau, gashin girarta gazar-gazar mai kyau kamar an zana mata shi, gata da manyan idanu masu kyau da ɗaukar hankali, girar idonta bak’a wulik koda a rufe suke idanunta k’ara kyau suke, da dogon hancin ta wanda ya dace da kyakkyawar fuskarta, idanunshi ne suka sauka a kan ɗan ‘karamin bakinta (pink lips), ya tuna yanda take motsashi idan tana mishi masifa, sai yaji ta burgeshi ma idan suna faɗa kyau yake mata.

   Yanzunma motsashi ta dingashi kamar zata tashi, dimples ɗinta na lotsawa, a hankali yakai ɗayan hannunshi zai shafi gefen fuskarta, kamar ance ta buɗa ido, ya sauka cikin nashi da sauri ya mayar da hannun

Sauri tayi ta tashi zaune, ciwon cikin ma taa daina ji.
   “ki tashi kiyi break fast”
  “Yaya majeeed me kakeyi har yanzu ba nasha maganin ba?”
    “eeh anma ai bakici komai ba, donma kin samu an nuna miki kulawa?”
     “naji anma dai ka fita zansha”
  “indai kinason in fita sai kinsha koda tea ne, ko so kike a fara cewa ban kula dake?”
   “wama zaisan banda lafiyan? Nidai nagode hakanan”
    “Yanzu wani yasan ciwon ciki kike me zasuyi tunani?” yaja tsoki, itama shiru tayi bata k’ara cewa komi ba.
Bai hak’ura ba saida ya haɗa mata tea, sannan ya fita “Gobe in Umma ta k’ara tambayanki kice ban kaiki asibiti ba ko ban kula da cin abincinki” yanayin yanda yayi maganarne ya sakata murmushi, ko umma ce ta mishi magana?
   Bai k’ara shigowa ɗakin ba, da rana yunwa ta isheta, gashi duk jikinta babu k’arfin da zata ɗaura girki, kuma tea yaa isheta hakanan, hakanan dai ta fito da nufin shiga kitchen ɗin ko zata samu abinda zataci.
    A tsakiyar falon suka haɗu da plate a hannunshi shak’e da yankakkun fruit, ta ɗan kauda kanta zata wuce.
       “ban ɗauka zakici abinci ba shiyasa na taho miki da fruit kawai” ta juya zata tafi
   “shima na k’oshi fa” ta koma zata tafi, “tohh me kikeso a anso miki?” “ba komi fa” taci gaba da tafiyarta, rik’o hannunta yayi, tana niyyar k’wacewa suka jiyo sallamar Aunty zainab tana shigowa ɗakin da sauri ya saketa.
      Kamar ta koma a ranta tace nifa shiyasa banson zuwa gidan yara, majeed yace, “sannu da zuwa Aunty” ta amsa tana niyyar zama
   “Aunty kizo shigo daga ciki mana,” ta matsa daga wurin Majeed suka wuce ɗakinta tare da Aunty zainabu” bayan sun zauna ne Aunty zainabu dai ta gaji da kallonta ganin dai k’arfin hali kawai take.
    “Anma dai baki lafiya ko?”
“eeh anma naa warke”
     “me akace yana damunki?”
   “A’ah bamuje asibiti ba, ina dai jin….”
    “kinajin me Majeeda? Zaki zauna da laulayi ne bazakuje asibiti ba kamar dai wacce batayi karatu ba?” maganar Aunty ma dariya ta bama majeeda,
   “Aunty ciki kuma? Nikam kowah ma ya samin ido dole ne daga mace tayi aure sai haihuwa? Nidai ulcer tace ta ɗan tashi”
   “ba dole bane anma don me ake auren? Karma ki fara sanyama ranki wannan, ni ba gashi ina jiran haihuwar ba Anma har yau Allah bai nufa ba”
       “ni Aunty kima daina maganar nan”
   “saboda me?” ta tsareta da kallon tuhuma, ta kasa magana, sai ga majeed yayi sallama ya shigo.
   Suna gaisawa da majeed, Majeeda ta mik’e, “Aunty me za’a girka miki?” “kinga basai naci komi ba daman a hanya nake, garin damuna k’ara in sauri in wuce” cikin wasa majeeda tace “Aunty ko ruwa dai aka fara ai a gida kike, kuma dai yaune zuwanki na farko”, “ina laifi ma da kika ganni?” majeed yace “ba laifi Aunty anma mudai yini mukeso” daria tayi sukaci gaba da fira harda majeed, sai da ya fita sannan ta jawo ledar magungunan mata masu kyau ta mik’a mata tana mata bayaninsu.
    Saurarenta kawai take, ita dai ba buk’atarsu gareta ba, babu amfanin da zasu mata sai dai tayita ajiya kar tak’i amsa Aunty tayi tunanin wani Abun.
   Aunty Zainabu bata daɗe ba ta tafi, Majeed ma lokacin ya bar gidan.
   5:00…
      Taji dai yunwar tak’i saurara mata, tun safe fa tea kawai tasha, daurewa tayi ta shiga kitchen ta fasa k’wai dai dai cikinta ta soya, sannan ta zauna falo ta cinyeshi tas tasha ruwa, sannan ta fara jin kanta.
    Sai dai me, kamar abinda ciwon cikin ke jira kenan, tun kafin ta tashi daga wurin mararta ta fara wani azababben ciwo, dak’yar ta iya kai kanta ɗaki.
   
   Ana gama sallahr isha’i ya shigo gidan, kai tsaye ɗakinta ya nufa har lokacin tana kwance da ciwon ciki.
    Yaje inda take “Sannu ya jikin?” kai kawai ta ɗaga mishi “don Allah ka haɗamin ruwa mai zafi a toilet” da sauri ya mik’e ya tafi haɗa mata ko 5mnt ba’ai ba yace “gashi can” dak’yar ta mik’e tana tafiya, ya bita a baya yanaso ya rik’ota don gani yake kaman zata faɗi, sai da takai k’ofar har ta shiga taga bai koma ba cikin gatse tace “ko zaka taimaka min da wankan?” da sauri ya koma yabar wurin bayan ta rufe k’ofar.
    Sai da ya tabbatar tasha magani, ya tsaya har barci ya ɗauketa sannan ya bar ɗakin nata.
   Kwana biyun da tayi tana ciwon ciki duk shine yake kula da ita, wani lokacin sai dai ta tsaya tanata mishi kallon mamaki wai yaya majeed ne haka yake mata hidima,
    Cikin kwana biyunnan ba k’aramin shak’uwa sukai ba, ko fita yayi yanzu yaa daina daɗewa zai dawo gidan koda bazasuyi magana ba, itama duk inda yaje a k’agare take ya dawo.
    Ta gama kwanakin da take tayi wanka, yanzu taa samu sauk’i, anma duk da haka yana shiga ɗakinta yayi tsaye kawai bazaice komi ba, ko su haɗu falo kallo anma babu wani magana tsakaninsu.
     Yau tun kusan da rana hadari ke haɗuwa yana washewa, shima ya hanata fita taje makaranta, anma har dare ba’ayi ruwa ba.
10pm.
    Aka fara iska mai k’arfi, tana kwance ɗakinta bayan majeed ya lek’o ya fita, tayi shirin barcinta da er qaramar riga iya cibi mai hannu bra, sai sket ɗan qarami ko cinyoyinta bai gama rufewa ba, anma saita rufa cikin bargo fuskarta da hannuwanta ne kawai a waje, ta saka charge tana chatn.
    Tunda aka fara iskan tayi kasak’e tama kasa chatn ɗin, abinka da jaharmu ta katsina😉 ana fara iskannan ba daɗewa aka ɗauke nepa, da sauri ta maida kanta cikin bargo tana jiran a tada Gen, wani irin tsoron da bata taɓa ji ba ya kamata, har aka fara ruwa a duk’unk’une take duk taa tsorata, ba shiri ta jawo zaninta dake gefe ta ɗaura sannan ta zura hijabinta, ta yaye bargonta a hannu da sauri ta nufi ɗakin Majeed tana haskawa da fitilan wayanta sai sauri take tana waige-waige, tana zuwa ta faɗa kawai sannan tayi sallama.
   Yayi ɗai-ɗai saman gadonshi dagashi sai Vest da gajeren wando, ya ɗago yana kallonta duk tayi tsuru-tsuru da jingin kaya a hannunta, gajiya tayi da kalan kallon da yake mata tace, “an ɗauke wuta kuma naga ba’a tada Gen ba, nidai tsoro nakeji ni kaɗai gashi ana ruwa”
    “Ɗakin naki ne kike tsoron kwana?” ta ɗaga mishi kai.
     “tohh shknan ki kwanta anan bara in koma falo” ta ware manyan idanunta cikin ɗan hasken fitilan tana kallonshi.
    “Inyi zamana a ɗakina mana, Ai wallahi falonma sai dai mu tafi tare” ta fara warware bargonta ta shimfiɗa gefen gadon da yake daga k’asa, ta buɗa wardrobe dinshi ta jawo wani bargon ta kwanta sannan ta rufa dashi duk yana kallonta.
   Led lamp ɗinshi ya jawo zai kashe, “Don Allah yaya Majeed karka kashe hasken tsoro nakeji,” ya maida ya ajiye sannan ya jawo bargonshi shima ya rufa duk sukayi shiru.
    Can aka fara wata irin tsawa, ta wani k’ank’ame gadon cikin tsorata tana karanto addu’ar da akeyi in ana tsawa (subhanallazi yusabbihul ra’adi, bihamdihi walmala’kati min khifatihi) tana maida numfashi da sauri da sauri.
   “kinga nifa bazaki hanamun barci ba da wannan tsoran naki, sai wani k’ara kike…” tun kafin ya rufe baki aka k’ara wata tsawar, batasan lokacin da tayi wurgi da bargon da take ciki ba ta haye saman gadon daman tuni taa cire hijabin jikinta, wurin hawan gadon zanin ya cire ta faɗa jikin Majeed ta ruk’unk’umeshi, yasa hannu zai cireta daga cikin shi ta k’ara rik’eshi tana jan numfashin tsoro, saitin kunnanshi take jan numfashin, gaba ɗaya taa gama rikita shi.
    Tananan a jikinshi har aka gama ruwan saura yayyafi, anma duk da haka bata sakeshi, kallon k’irjinta yake yanda zuciyarta ke harbawa, komai nata a bayyane, ga wani irin k’amshi dake tashi ko ina a jikinta, ya fara kai hancinshi yana shinshinar wuyanta, ya saka hannunshi dai-dai cibinta yana shafa cikin, duk da ta shiga yanayi bai hanata rik’e hannun nashi ba, ko tsawa saurararta baiyi ba ya fara kissing ɗinta ta ko ina, yana sarrafa jikinta yanda yaga dama duk ya rikece.
   Ita ɗinma ta fara manta a wacce duniyar take, tuni yaa  rabata da duk wasu kaya dake jikinta, bata tashi tsorata ba saida taji yana niyyar shigarta, ta fara tureshi anma yak’i sakinta, harda ɗan kukanta “Yaya majeed ka daina, babu kyau fa”, ya ɗago da jajayen idanunshi cikin sark’ak’k’iyar murya, “Plz majeeda kar muyi haka”, cikin wata irin murya dake k’ara rikitashi “Nidai a’ah yaa maj….” ya hanata k’arasawa, ya haɗa bakinshi da nata, cikin kalan nashi salon mai rikitarwa.
   Duk wani ihu da take tana tuttureshi harda cizo da yakushi bai tsaya saurara mata ba, baimasan tanayi ba har saida ya fara jinshi dai dai sannan hankalinshi ya dawo jikinshi, kwantawa yayi gefenta yana maida numfashi kamar wanda yasha gudu.
    Kasa koda motsi tayi, har lokacin hawaye take, maido nepa da akayi ne ya sakashi mik’ewa ya haɗa mata ruwa mai zafi a toilet, yazo inda take ya saka hannu zai ɗauketa ta buge hannu, yaja baya, “kinga karki k’arama kanki wahala idan kin shiga ruwan zafi zaki rage jin ciwon” dak’yar ya lallaɓata ya kaita toilet ɗin, sai harararshi take, shikam dariya yake abinshi saboda wani irin farin ciki da yakeji.
     Cikin kwamin wankan ya direta, taga yak’i ya fita, “me kuma kakemin anan” ya shafi gemunshi “wankan da kika tambayeni kozan taimaka in tayaki, shine zan miki”,
    “Haba Yaya majeed, plz nidai ya isa haka, ka ficemin plz”, “tohm saikin fito, ga wani ruwan nan a bocket wanda zaki wankan tsarki” “naji” kawai tace da taga alaman in batayi magana ba bazai fice ba, sannan ta maida kanta tana jin wani yanayi daban.
    
   40mnts later
Ta fito tana tafiya dak’yar, har ya gyara shimfiɗar ya canja zanin gado, ta kwanta gefen gadon sannan ta juya mishi baya, mirginowa yayi inda take ya kwantar da kanshi saman kafaɗarta ta tureshi muryarta da alaman kuka take tace, “wai me kakeyi haka Yaya Majeed? Kasanfa abinda kakeyi haramun ne” ya ɗan rage fara’arshi, bayan ya kamo hannuta yana wasa dashi “me nayi da ba dai-dai ba? Ɗazun da kika k’udundune a jikina na hanaki ne?” ya kai mata cizo a yatsanta daya saka a baki ta saki k’ara, da sauri takai mishi bugu a k’irji, “bafa wasa ake ba Yaya Majeed” sai kuma ta fashe da kuka sosai.
    “Ka cuceni yaya majeed, shikenan ka rabani da abinda nake tak’ama da, yanzu wanne namiji ne zai aureni a haka bayan kai kamin saki uku? Zina fa kenan muka aikata, da wanda bai sona kuma”
   “Bayan NI DAKE, wa yasan zina muka aikata? Kin manta duk duniya tana mana kallon miji da mata ne? NI DAKE ne kawai mukasan babu aure a tsakaninmu”
    “Zamuci gaba da zama a haka ne? Kasan dai duk daɗewa dolene zanje na auri wani” hannunta dake rik’e a nashi ya ɗaura a bakinshi,
   “ki daina faɗar haka plz, karki rabu dani Majeeda, sai yanzu na gane sosai ina buk’atarki a rayuwatah, wannan sirrine tsakanin NI DAKE, kinsan dai idan har iyayenmu suka san halin da muke ciki tsinuwa ne kawai, kuma dole su rabamu” ya marairaice fuska, “banson na rasaki a rayuwatah”
     Tunda ya fara magana take kallonshi kamar wani zararre, anya Yaya majeed yana cikin hankalinshi? Baki a buɗe tace “HARAMTACCEN ZAMA zamuyi kenan?”
    “kada ki zurfafa tunaninki mana, ki manta kawai da yanzu babu aure a tsakaninmu, ki kalleni a matsayin mijinki, tunda babu wanda yasan sirrinmu, muma mu manta abinda ya faru”, hafsatul kiram ce ta faɗo mata a rai, ita kaɗaice tasan sirrinta da majeed, tohh anma yanzu ai basu k’asar sun tafi moscow ita da umar ɗinta, kuma ta yarda da ita bazata taɓa faɗama wani sirrinta ba.
     “nidai bazan iya HARAMTACCEN ZAMAn nan ba, kowa yaci gaba da harkarshi kawai tunda daman ba sona kake ba, kawai sha’awanah kake”
    “Waye ya faɗa miki bana sonki?” yayi saurin katseta.
   “bai kamata wannan maganar ta fito daga bakinki ba, ni kaina bansan sanda na fara sonki ba Majeeda, anma ki yarda dani ina sonki, tun lokacin dana kasa ɗauke idanuna daga kallon kyakkyawar fuskarki a wancan ranar, na tsinci kaina da matsananci tausayinki a lokacin da kika fara rashin lafiya, har nakejin daman ciwon ya dawo a jikina, wannan ba so bane? Duk inda zanje koda na fita daga gida tunanina yana a kanki ta yanda bazan iya ɗaukar lokaci ba sai nazo na ganki, a hakan ba sonki nake ba?, da meyasa bana sha’awar jikinki sai yanzu? Idan har banisonki bazan taɓa sha’awarki ba, bansan yaushene ba ko kuma tayaya na fara sonki, anma na rantse da wanda raina yake a hannunsa ina sonki fiye da yanda nake son kaina,”
    “kafin yanzu ina buk’atar, abinci, ruwa da iska ne kawai don in rayu, anma yanzu rayuwatah tana matuk’ar buk’atarki majeeda”
   Share hawayenta tayi cikin farin ciki ta kwantar da kwanta a k’irjinshi, “nima ina sonka sosai yaya majeed” ya saka hannu yana shafa gashin kanta shima cikin jin daɗi yace, “Kin yarda zamuci gaba da zaman aurenmu?” ta ɗaga mishi kai.
   Tasha barci sosai har 10 ta wuce sannan ta tashi, a hankali ta buɗe idonta tana kallon gefen da yake, bainan sai dai ta hango takardar daya mata rubutu a jiki “Good morning” ta ɗanyi murmushi sannan ta dire k’afafunta k’asa ta sauko ta fito falon tana tafiya a hankali, anan ma bainan ta wuce ɗakinta kawai.
    Shiryawa tayi cikin wata haɗaɗɗiyar doguwar riga mai shegen kyau, da kaɗan ta wuce mata gwiwa, itama ɗan k’aramin hannu ne da ita, saboda yanda takejin jikinta bazata iya ɗaukar kaya mai nauyi ba, gashin kanta ma data tubke ji take duk ya mata nauyi, ta warwareshi kawai ta ɗan kwantoshi daga gaba, ga wani k’amshi da yake tashi ko ina a jikinta.
    Da fara’arta ta fito cikin nishaɗi, har lokacin bai falo, ta wuce dinning table kawai hango kululon da ita a jere daman yunwa takeji.
     Tana tsaye ta fara buɗa kulan farko farfesun kaza ne, na biyun kuma soyayyan dankali ne, tana cikin buɗewa taji an rungumotah ta baya, sannan ya sak’ala hannuwanshi cikin nata “kin tashi lafiya?”
  “lafiya lau sannu da gajia” ya sakar mata kiss a wuya, ta nok’e tana daria sannan yace “gajiarme”, “kasha girki mana”
   “ba wani gajia tunda masoyiyatah na girka mawa” daria tayi sannan ta juyar da kanta ta kwantar a kafaɗarshi, “kema ya taki gajiyar?”
    “gajiyar me?” ta tambayeshi yana daria sai so yake ta ɗago da fuskanta “kinaso in faɗa?” ta k’ara shigar da kanta a jikinshi tana daria “A’ah, nima ba wani gajia tunda masoyinah na faranta mawa” dariya suka yi dukansu, tace, “nifa Yaya Majeed na qagara naji girkinnan” a shagwaɓe tayi maganan, “yanzu kuwa,” yaja mata kujera ta zauna, sannan ya zauna kusa da ita.
    A plate ɗaya ya zuzzuba musu, ta ɗauko fork zata fara ci ya rik’e hannun, “daga yau wannan aiki nane” ta buɗa idanu tana daria, wata sabuwar soyayyar majeed na k’ara shigarta, ji tayi tafi kowacce mace farin ciki da samun Abokin zama wanda yake bata kulawarshi,
    Haka yaci gaba da bata a baki har saida ta k’oshi, sannan ya langaɓe kai cikin wani salo “Saura ni”, itama langaɓar dakai tayi “nifa bakacemun zanyi aiki ba” shikenan tunda bazaki bani ba, ni bama zanci ba ya tashi kamar zai tafi.
   Dariya sosai ya bata tace “toh shikenan daman nasan ka k’oshi tun a kitchen” ya dawo da sauri ya zauna, “bazaki lallaɓani bama ko?” ta jawo fork ɗin, “anma sau ɗaya zan baka”, ya marairaice “Yana iya tohh? Na yarda” ta ɗebo abincin ta nufi bakinshi dashi, saida ta kusan saka mishi ya buɗe bakinshi, sannan ta juyar da cokalin ta cinye tana daria “laah! Aikam bazan yarda zaki biyani ne” ya jawota yana k’ok’arin saka bakinshi a nata sai k’yalk’yatar daria suke.
    Haka ya gama cin Abincin a shiririce, sunayi suna nishaɗinsu irinnan na ma’auratan gaskennan,
   Ranar da yake friday ne bai fita office ba, wurinta ma babu maganar zuwa ckul, soyayarsu suka dinga sha kamarsu cinye juna, sai tarairaya majeeda takesha a wurin majeed, ko motsi zatayi tare suke motsawa😉 yananan lik’e da ita, kunsan irin farkon soyayyarnan.
   Komai batayi ba ranar, girkin rana ma shine ya musu sai dai ya zaunar da ita falo ya kunna mata kallo, ta narkar da fuska  a shagwaɓe tace “nidai banson kallonnan, k’ara muje can kitchen a tare ko bazanyi komai ba ina kallonka”
   Ya kamo hannunta yana shafawa a fuskarshi “banso ki shigo kimin dariyan ban iya ba, kiyi kallonki, indai ninema bazan iya minti 2 bana ganin fuskarki ba, zan na fitowa” ta k’ara marairaicewa “nidai…” ya ɗaura hannunta a leɓenshi, “plz kiyi kallonki” ta ɗaya mishi kafaɗa sannan ya juya ya tafi girki.
    Bai minti biyu zai fito ya sumbaceta cikin soyayya, sannan ya koma a haka harya gama girkin.
     Da dare ne dai saiya fita ya musu take away, wannan rana ku biyu sun zame musu na farin ciki sosai.
   Da dare suna zaune suna kallo a falo ta fara rufe ido alaman barci, sannan ta tashi daga jikinshi tana mik’a, “nidai saida safe” ya ɗago yana kallonta “barci?” ta ɗaga kai, “tohh bara in kashe kallon in taho” rausayar dakai sannan ta juya ta tafi ɗakinta, sai da tayi shirin barci sannan ta kwanta sai gashi ya shigo shima da shirin barcinshi.
   “Anan zaka kwana?”
  “ehh mana, in rama miki kwananki” murmushi kawai tayi har yahau gadon ya kwanta.
    “nida na kwana a k’asa?” a hankali tayi maganar, ya jita anma sai yace, “me kikace?” Majeeda tace “bance komi ba”
    Ya jawota jikinshi sannan yace, “anan dai kika kwana” sukai daria su duka, sannan ta juya mishi baya duk da amanne take a jikinshi.
    Sun daɗe a haka, su basui magana ba, kuma ba barci suke ba, ya saka hannu ya kashe fitilan.
   Tsawon lokaci sannan yayi magana a hankali “Meya hanaki barci” tayi shiru kamar mai barcin gaske batace komi ba, ya fara mata tafiyar tsutsa a wuyanta ta nok’e tana daria, “kice wani abu mana” inji majeed
    “me zance?”
 “wani abu mai daɗi”
    “plx ka barni nayi barci”
  “plx nima ki faɗamun yanda zanyi barci mai daɗi”
   Ta nisa tana jan numfashi sannan tace, “Ina sonka Yaya Majeed, tabbas aurenah dakai bai cikin zaɓina, sai dai banson sanda soyayayarka ta cikamun zuciyah ba, kai namijine da kowacce mace zatai Alfaharin samu, fatana ko da yaushe in kasance tare dakai har k’arshen numfashina, ina sonka yaya Majeed, soyayyar da bata da iyaka, bazan daina sonka ba har Abada”
   Ya k’ara rungumota jikinshi cikin jin daɗi farin ciki fal a zuciyarshi.
     “nima ina sonki sosae Majeeda, ki kasance a tare dani, zan maye miki duk wani damuwarki da farin ciki, bazaki taɓa dana sanin kasancewa dani ba, ina sonki da yawa majeeda, don Allah karki barni” ya jawo hannunta bayan ya zare zoben hannunshi, ya saka mata, ta damk’e lallausan hannunta cikin nashi “zan kasance tare dakai har gaba da Abada yaya Majeed”
    “Na shirya miki wani albishir gobe, anma bazan faɗa miki”
   “plz mana yaya majeed”
 “idanna faɗa miki bazai miki wani daɗi ba, kin gani da idonki” tace “tohh shknan” anma badon taso, duk tunaninta ta kasa gane ko Albishir ɗin menene, gashi ba ranar birthday ɗinta bane, ta hak’ura dai a haka barci ya ɗaukesu
  8:35am
    Ta fara farkawa, kallon bayanshi take bayan ta buɗe ido, ta murgina inda yaketa dubashi bai tashi ba, ta kwantar da kanta kawai a bayanshi tana jin soyayyarshi na k’ara shigarta.
        Gani tayi kawai ya buɗe idanu sannan ya murgina ta koma k’asa, ya tallabo fuskarta yana kallon kyakkyawar fuskarta, itama kallonshi take suna ma suna murmushi, ta ɗan ɗago da fuskarta takai mishi kiss a goshi, ya lumshe ido ya buɗe cikin nishaɗi,
     “kawai bana gajiya da kallonki” ta juyar da idanunta cikin jin daɗin abinda ya faɗa, sannan cikin narkar da murya tayi magana,
   “tohh ka faɗamin magana” kiss ɗinta ya mayar mata sannan yace, “inasonki da yawa Majeeda”
    “Nima ina sonka sosai”
  Tare suka shiga kitchen, a shiririce suka haɗa break fast suna shan soyayyarsu, shi baiso tayi aiki, itama tafi so ita tayi, sai dai sukayi a tare kowah dai baison ɗan uwanshi ya wahala.
    Tare suka zauna suka ciyar da junansu, sannan suka koma barci sai kusan azahar suka farka.
   3:00pm
  Suka fito da shirunsu, tana sanye da wani haɗaɗɗen material skye blue, ɗinkin riga da sket yayi matuk’ar amsarta, tayi kyau sosae da farin mayafi, sark’ar wuyanta ma fara, ba wani makeup tayi ba, anma kyau kam tasha shi.
    Shima sanye yake da wani haɗaɗɗen yadi shima skye blue, ɗinkin yasha aiki mai kyau, ba k’aramin haɗuwa yayi ba, tabbas ba qaramin dacewa sukayi da juna ba.
    Saida suka tsaya suka sha hotuna masu kyau, sannan suka jera suka fito tana kwance a jikinshi,
    “wai ina zamuje?”
  “wurare da yawa, yaune farkon fitarmu, har sai kince kin gaji” ta k’ara kwantar da kanta jikinshi.
    “baka fiddo motan ba Yaya majeed yanzu sai naje can?” duk’awa yayi ya ɗaukota, suna tafiya yana kallon fuskanta cike da soyayya.
   “kanaji dani da yawa”
      “Kin cancanci fiye da hakan” sai da ya buɗe ya sakata, sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver, ya fitar da mota suka tafi.
   Wurin siyar da motoci yayi parking, suka fito a tare tana duba wurin “kamar wurin saida motoci”
     “lallai kifin rijiyace ke, motah zaki tayani zaɓe”
     “wow! Anma dai kowace irice ka ɗauka red colour, ina sonta sosai”
   “Akwai su da yawa, kedai muje ki zaɓamin”
     “zan jiraka a mota plx”
  “kin gaji?” yana ɗaga mata gira.
    Ta ɗaga kai tana dariya, ya buɗe mata ta shiga motan sannan ya wuce wurin, ya ɗan ɗauka lokaci sannan ya dawo, yaja motan suka tafi.
  
     A yana driving ma suna rik’e da hannun juna.
   “Yaya majeed wai me zakayi da mota, bayan wanda kake da?”
     Ya ɗan juyo yana kallon fuskarta, suka sakarma juna murmushi.
    “banso wani ya k’ara ɗaukomin kene daga makaranta, plz karki k’ara shiga motan kowa, ga motanki nan idanma bananan”
   Ta k’ank’ame hannunshi cikin tsananin farin ciki.
   “dagaske motahta ce yaya majeed?”
    ya ɗaga mata kai yana murmushi.
    Wani ihu ta saki, sannan ta faɗa jikinshi, dole yayi parking a hanya.
    “Nagode sosai yaya…” ya ɗaura hannunshi a saman leɓenta.
    “babu godia a tsakaninmu, kinmin Abinda bazan iya biyanki da komai ba Majeeda, ina sonki da yawa, babu abinda bazan iya miki ba” ta ɗago fuskarta suna kallon juna,
    “nifa ban ɗauka wani babban abu na maka ba Yaya majeed, anma nima ka sakani farin cikin da bansan yanda zan bayyana maka shi ba, kullum soyayyarka k’aruwa take a cikin zuciyatah”
   “Kinason jin ta yanda zan gane kinyi farin cikin sosae?” ta ɗaga mishi kai cikin zumuɗi.
   Ya matsa dai-dai kunnanta ya mata raɗa, ta ɗago suna kallon juna ya kanne mata ido.
    “Rannan da zafi fa”
  “wannan bazakiji ba, indai ba baki shirya faranta min ba”
    “A’ah fa na yarda, anma sai gobe” ya ɗaga kafaɗa, “na yarda”.
    “Kina jin yunwa?” ta ɗaga mishi kai.
   Ya juyar da motan suka nufi restaurant.
   Suna cin Abinci suna firarsu, sai dariya duke, kallonsu kawai zakayi ka gane masoya ne dake matuk’ar son juna,
    Alama ya mata da idanu data juya taga wasu tsofaffi mata da miji A bayansu, suma soyayyarsu sukesha kamar ba tsofi ba ko a nigeria, da jikanyarsu y’ar yarinya mai kyau, A hankali yace mata,
    “na k’agara mu zama kamar tsofinnan”
       “nima sun burgeni sosae”
  Sun gama suna fitowa suka haɗu da Aisha a hanya, tun kafin su ganta ta tsaya tana kallonsu, hannunsu mak’ale da juna, suna tafiyarsu gwanin sha’awah zuciyarta sai bugawa.
   Majeeda taa rigashi ganinta, itama saida k’irjinta ya fara bugawa wani irin kishinta takeji, ta fara k’ok’arin zare hannunta daga nashi, ya rik’eta tsam don shima yaga Aishan, har sukazo suka wuce inda take tsaye kamar bai ganta ba, ta juya taci gaba da kallonsu har suka shiga mota.
    Batace mishi komi ba, anma duk jikinta yayi sanyi, shikam baima nuna mata alaman komi ba yaci gaba da janta da fira har saida yaga hankalinta ya kwanta.
   “plz Yaya Majeed muje gidansu momie da gidansu Umma”
     “Marece yaa farayi sai dai gobe” ta marairaice fuska.
    “kaifa kace saina gaji”
  “nifa naso mu koma gida, anma ki zaɓa ɗaya dai”
     “nidai tohh muje gidan Umma na daɗe banga zahra ba”
      “Gidan momie zamuje nan kika daɗe bakije ba”
     “Duk yanda kace mijin gidanah” ya harareta da wasa
   “mijin gidanki ma ba mijinki ba?” tayi daria sosai,
    “hakane mijina, kuma MASOYINA NA HAR ABADA (mrs Umar)”
     “gsky naji sunannan yaimin daɗi”
Text ya shigo a wayarshi, tana hannunta tana game, shi kuma yana driving.
    “Dubamun text ɗin waye?”
Tayi minimizing sannan ta shiga duba text ɗin, sai da kanta ya sara ganin mai turowan, anma tadai dake.
    “karantamun mana” da ɗan washe fuskarta ta fara karanta mishi,
    “Wai honiee yaushene zaka daina wahalar da zuciyatah ne? Yanzu don kana tare da wannan banzar matar da bama son ta kake ba zaka shareni” ta k’yalk’yale da daria bayan ta gama karantawa,
    “ke kuma miye na daria, sai akace miki ki karanta duka, Aisha ce ko?”
     “harma akwai wata bayanta kenan? Nifa aka mawa ba kaika ba, da gaske dariyar ta bani”
    “nidai naji haushi, ba tun yau ba nasan kina sane da bata gabana”
   “yanzunma ban tambaya bafa”
     “tohh nayi shiru matar gidana” sukai dariya lokacin sunzo k’ofar gidansu, aka buɗe mishi gate suka shiga.
    Tare suka jera suka shiga falon momie na sallama da bak’uwa, ganinsu da tayi tare tama kasa ɓoye farin cikinta, tayi saurin sallamar bak’uwar ta taho sai k’ara washe baki take,
     “tare kuke tafe?” Majeed ya shafa gefen gemunshi ya silalo daga saman kujerar kanshi a k’asa yana gaisheta, Majeeda ta koma inda take ta kwantar da kanta jikinta,
    “Momienah inata kewarki”
  “ba gashi yanzu kinzo kin ganni ba?”
    “ba irin haka ba momie, gidannan ma dukanshi ina kewarshi”
     “Rabani da shagwaɓarnan taki, kunyi sa’a ma daddynku yana gida”
   Ta tashi tana murna,
 “Anma naji daɗi sosae momie bara naje in gaisheshi”
      “Tohh ɗiyar daddynta” yanayin momie kawai zaka kalla ka gane tsantsar farin cikin da take ciki.
    Majeeda da Majeed tare suka jera suka shiga falon Abba, shima yaji daɗin ganinsu sosae a tare, ya dinga sanya musu Albarka.
 
    Sannan gabanta ya shiga faɗuwa, tama kasa haɗa ido da Abba, duk a tsorace take gani take kamar zai iya gano abinda suke ciki, duk jinta take wata daban,
   Ta gaya musu kyautar motar da Majeed ya mata, suka dunga mishi godia sosae,
   Majeed ya lura da sukukun da Majeeda tayi, duk hankalinshi na kanta, basu daɗe ba suka tafi.
Suna shiga mota kamar ya mata magana kuma ya fasa, sai da suka shiga gida ya bita har cikin ɗakinta, ko a lokacin jikinta a sanyaye yake.
   Ya tsuguna inda take ya ɗaura hannunshi a saman gwiwoyinta, ta zuba mishi ido tana k’ok’arin kauda damuwarta.
    “kina tsoran za’a iya gano HARAMTACCEN ZAMAn da muke ko?” ta ɗaga mishi kai,
   “toh waya sani bayanmu dazai iya faɗa musu har su gane? Wannan tsoran naki ne da shakku kawai matsala na, plz ki daina kinji” tayi murmushi saboda yanayin daya k’arasa maganar,
     “na daina masoyi, kawai gabana ne yake ta faɗuwa”
    “ki manta komai a ranki mana, banason abinda zai rabani dake”
    “nima hakan”
Bayan wani lokaci…
SO DA SHAK’UWAne (Amrah A msh) kullum ke k’aruwa a tsakaninsu, wani kulawan sai tsakanin Majeed da Majeeda, komai a tare sukeyi, tarairayarta yake sosae kamar k’wai ɗaya a cikin miya, baya shakkar nuna mata soyayyah a gaban kowa, soyayya suke irin babu irinta a duniya,
     Majeed ne ya fito da shirin fita, yasha kyau cikin farar shadda, yana tsaye yana saka agogo itama ta fito da mayafinta,
    “tohh saina dawo masoyiyah, mezan zo miki dashi?”  ta mak’ale kafaɗa kamar wata k’aramar yarinya,
   “nifa da gske bazaka barni ni kaɗai ba”
   “haba tawan, ya za’ai naje wurin ɗaurin aure dake?”
    “tohh ka fasa zuwa mana”
   “Ɗaurin Auren Abbakar ɗin?” ya faɗa yana zaro ido,
    “inkin yarda dai na kaima Aunty zainabu Ajiyanki” ta ɗan saki fuskarta,
    “Anma bazaka daɗe ba?”
  “da an ɗaura aure zan dawo”
    “tohh shkenan muje”
   Suka fito tare, a hanya suna tafiya tana tsaidashi, komai ta gani tanaso ya sai mata, kwaɗayi dai kala-kala shi kuma ya dinga biye mata,
     A k’ofar gidan Aunty zainab ya ajeta, ta sauka sannan ta lek’o tagar da yake,
    “saika dawo,” ta mishi kiss a gefen kumatu
    “tohh babe, saina dawo” ya ɗaga mata hannu yana fara’a, saida ta shiga gidan sannan ya tafi,
   Tana shiga Aunty ta taso da fara’arta tana mata oyoyo, ta zube saman kujera, Aunty ta kalleta da mamaki,
    “Halan a gajiye kike?”
  “A’ah aunty, yunwah dai”
 Aunty ta zauna kusa da ita,
     “ya gidan naku?”
   “lafiya lau Aunty” sannan ta gaisheta, duk ba yanda Aunty ta saba ganinta ba,
   Ta jawo ledanta ta fiddo Apple ta faraci, sai dafe kanta take,
    “Aunty nace inajin yunwa, ko saina nema abincin?”
   “Tohh ay naga daga gidanki kike, kuma baki sanar dani zaki zo ba”
   “ni ban tsaya na k’oshi ba, ganin zan fito”
    “tohh ay yanzu zan ɗaura na dare” ta mik’e tana dafe da kanta,
    “nidai bazan jira ba Aunty, bara na dafa ko cous-cous ne”
    “sai dai indomie”
  “tohh yana iya” ta nufi kitchen ɗin, indomie ɗinma saida ta rumurmutsi wata taci hakanan kafin ta dafa, ko dahuwa bata k’arasa ba ta juyeta ta fito,
    Aunty nanan inda ta barta, ta fito tana tafiya tana rik’e kanta, ga wani irin tashin zuciyah da takeji idanta shak’i k’anshin indomie ɗin, ta daure dai ta zauna, Aunty tace,
   “wai lafiyanki?”
  “wlhy Aunty ciwon kai nake fama dashi kwanannan, da jiri” taje zata zauna, jiri ya kwasheta ta kusan faɗuwa da sauri Aunty ta taso zata rik’eta, ta daure ta ajje indomie ɗin,
    “Wai yadai majeeda” sai dai kawai gani tayi majeeda ta sulale a wurin,
   Aiko duk ta rikice, ta shiga kiran layin mai gidanta muhd anma yak’i shiga, ta kira layin majeed, taa kusan katsewa ya ɗauka,
    “kayi sauri kazo yanzu majeeda ba lafiya, kayi sauri plz” bata jira me zaice ba ta katse,
  
   Shima jin muryarta a rikice, duk hankalinshi ya tashi, bai tsaya sallama ta kowa ba ya shiga motanshi ya nufi gidan Aunty, tafiyar mintuna kaɗan ya kaishi gidan,
    Ganin halin da Majeeda take ya sakashi k’ara ruɗewa,  baisan sanda ya saka hannu ya ɗauketa ba, Aunty ta biyosu a baya suka wuce Asiti sai kwarara gudu yake, ikon Allah ne kawai ya kaisu,
    Aunty na zaune bayan an shiga da Majeeda, Majeed kam sai zagaye wurin yake yaje ya dawo, har Aunty zainabu ta gaji tace mishi,
    “wai bazaka zauna ba Majeed?”
     “Aunty yazan zauna bayan ita tana can tana shan wahala”
    “tohh ci gaba da zagayen ku raba wahalan”
  Nurse ce ta fito,
     “likita yace zaku iya shiga” tun kafin Aunty zainabu ta mik’e ya rigata shiga ɗakin, Abokinsa Mukhtar ne ya hango, ana ce mishi Dr. Shaheed, ya taho da fara’arshi yana bashi hannu,
    “ka ce mana Amaryar da aka hanamu rakiyar ango don karmu ganota ne aka kawomin har inda nake”
   Majeed yayi daria sosae  “kasan dai yanda abun yake, anma ay har gida naso muzo da ita”
   “har yanzu na biyo bashi kenan?”
   “yanzu dai Aboki ya jikin nata?”
  Dr. Shaheed, Ya washe baki tare da k’ara mik’a mishi hannu,
    “ina tayaka murna”
  “banson iskanci fa, matata na kwance asibiti kace kana tayani murna, meke damunta plz?”
    “Koma menene ai aikinka ne mutuminah”
   “ni kuma? Kaifa ɗan iskane rashin lafiyar matar tawa ma saika jamun rai?” Dr. Shaheed sai dariya yake mishi ganin ya damu sosai yace,
    “Amaryarmu tana ɗauke da juna biyune, na tsawon sati shida”
Ya fiddo duka idanunshi cikin tashin hankali ne koko mamaki? K’ila kuma duk tsantsar farin ciki ne,
    “ciki shaheed?”
 “k’warai kuwa Aboki, idanta farka zaku iya tafiya, anma bayan ka bani goron Albishir ɗina” ya faɗa cikin zolaya,
  Aunty Zainabu dake tsaye a k’ofan tace, “Ai wannan babbar Albishir ne Dr, ni da kaina zan kawo maka”
    “Tohh Aunty godia nake,”
Duk majeed yayi sukuku har Dr. Shaheed ya fita, Aunty ta wuceshi taje inda Majeeda take kwance, idanuwanta a buɗe ta farka, anma hawayene kawai ke zuba a idanunta,
   “Miye haka Majeeda? Keda zanga murna da farin ciki a fuskarki, miye na kuka kuma?
   Shiru tayi ta kasa koda k’ifta idanunta ne, sai dai hawayenda takeyi kawai, Aunty Zainabu tayi maganar harta gaji,
      “Aunty Zainabu ina ganin fa murna ce taima Majeeda yawa, wannan kyautah ce Allah ya bamu da ba kowa yake bama ba”
    “hakane, ayni namayi tunanin ko ciwonne”
    “A’ah da akwai matsala daya faɗamun”
    “hakane fa” ta zunguri Majeeda,
  “Tashi mu tafi tohh, tun yau kin fara tunanin ciwon nak’uda” saida Majeed yayi dariyar dole,
    A hanya ta dinga kiransu momie tana musu Albishir, Abdul-Majeed yana driving ya juyo,
   “wai ya kike faɗa musu tun yanzu Aunty?”
   “tohh sai yaushe zan faɗa musu? Kaga kuwa yanda suke murna” shiru bai ce mata komi ba, har gidanta suka ajjeta, tana k’ara nanata musu shawarar likita yanda za’ana kula da Majeeda,
    Saida ta fita sannan Majeeda ta samu damar fashewa da kuka, baiyi k’ok’arin lallashinta ba har suka isa gidansu, tun kafin ya gama parking ta fito daga motan har tana shirin faɗuwa, ta ruga ta shige ɗakinta, sulalewa k’asa tayi ta ɗaura kanta saman gefen gadon tana kuka,
   Ya daɗe a tsaye jikinshi a sanyaye, sannan ya matsa inda take, ya mik’a hannu zai jawota ta buge hannu, ya k’ara mik’a hannu ta tureshi tana ci gaba da kukanta, cikin sanyin jiki ya zauna gefen gadon, sai kuma ta maida kanta samanshi sannan taci gaba da kukan,
   Hannunshi yasa yaci gaba da shafar gashin kanta,
   “Ya isa hakanan tohh, meye na kuka” ta k’ara k’arfin kukan nata,
   “Miye na kuka? Idan banyi kuka ba dariya zanyi saboda ina murna da wannan abun dake jikina?”
    “kenan baki murna saboda ɗana yana a jikinki?” tayi tsit tana share hawaye,
   “Anma bata wannan hanyar ba Yaya majeed”
   “saita wacce hanya? Kenan kuwa har abada bazamu ga ɗanmu ba, kina nufin har yanzu baki kallona a matsayin mijinki?” ta shiga girgiza kai,
   “abunda ya kamata muyi murna da farin ciki ne, ki daina kallon cikin dake jikinki a matsayin wanda muka samu a HARAMTACCEN ZAMA, ki kalleshi a yanda kowa ke kallonshi, kema kina sonshi ko?”  ta daga mishi kai,
   “nima inason duk wani abu dazai fito a jikinki, ina sonki sosae Majeeda”
    Ta tashi taɗan rage tsawonta, ta kwantar da kanta jikinshi tana wasu hawayen, ya ɗago da fuskarta
   “bazan taɓa bari kiyi kuka ba Majeeda indai ina tare dake” ta juya bayan hannunta tana murmushi zata share hawayenta, ya rik’e hannun,
     “na miki alk’awarin share hawayenki, a duk halin da kika tsinci kanki, na farin ciki kona damuwa, ina tare dake”
    Ya saka harshe yana share mata hawayen, sai kukan natama ya koma na farin ciki, ya haɗa bakinshi da nata yana kissing ɗinta, har saida yaga hankalinta ya kwanta, sannan ya saketa,
   Tun daga ranar Majeed ya k’ara ninninka kulawan da yake bama Majeeda, tana ɗauke da cikin ne kawai anma komai yi mata yake, su Umma ma kullum cikin aiko mata ciye-ciye suke, ba’a ɗaukar lokaci zatazo ganinta,
  Cikin nada wata bakwai momie tace zata maida ita gida, ya marairaicema Aunty Zainabu,
   “Aunty Zainabu yanzu mena gaza wurin yima majeeda? Ynzu kun tafi da ita wata nawa kenan bazan ganta ba? Plx Aunty don Allah ku barmun matata”
    “Aiken momie ne fa ya zance mata knan? Haihuwar farko ce yama za’ay ka iya kula da majeeda”
  “Tohh Aunty idan na samo mata mai aiki fa?”
     “har k’ara hakan, anma dai ka barta ta koma gida gsky” duk ya rasa yanda zaiyi da Aunty Zainabu kamar ya fasa mata kuka, ya kalli majeeda,
   “kinason kije gida ki barni anan?” kallon Aunty Zainabu tayi sannan ta maida kallonta ga Majeed,
     “Idan kace A’ah bazan je ba”  Aunty Zainabu ta kalli Majeed tana ɗaukar jikkarta,
   “Nasan ma A’ahn zakace, ni naa daina zuwa gidanku inga rashin kunyarnan”
     “Hak’uri za’ai Aunty”
  “oho, ku kuka sani dai”
   Majeeda ta fara k’ok’arin tashi saboda yanda cikin yayi girma,  “Aunty bara in rakaki
 “yi zamanki, Allah dai ya raba lafiya” su duka amsa da “Ameen”,
   Ya dawo kusa da ita bayan Aunty ta tafi,
     “Ban kyautah ba ko Majeeda?”
    “A’ah itama Aunty ai taga kana kula dani sosai”
   “Bazan iya jurar rashinki ba koda na kwana ɗaya ne”
   “nida babynmu ma bamuso muyi nisa dakai”
     “Yauwah tawan” ya kwantotah jikinshi, ya fara shafar cikinta,
    “babyna nason hutu, muje ku kwanta” ya fara k’ok’arin ɗaukarta, ta rik’o hannunshi,
   “nifa na gaji da kwanciyarnan, yanzunnan fa ka taso ni zuwan Aunty”
     “Tohh ay nafison kina kwanciya ku huta”
   “nidai hakanan, likita ma yace ina motsa jiki ai”
  “tohh naji kuɗan zauna”
   Ta kamo hannunshi ta rik’e cikin sanyin murya tace “Yauma bazaka kaini wankin kan ba?” ya k’ara damk’e hannunta cikin nashi,
    “ki gane mana, nifa banso ku wahala ne”
   “nidai gsky yayi datti sosae”
  “tohh zan wanke miki, shknan?” ta rik’e bakinta tana daria,
      “ina ka taɓajin namiji da wanke kai?”
    “A gidan Majeed da Majeeda” ya bata amsa yana murmushi,
   “meye a ciki? Nima fa ina wanke nawa”
   “hakane tohh muje toilet ɗin”
   “toh ina zuwa” ya tafi da sauri ya kai mata doguwar kujera a toilet ɗin, ya haɗa ruwa mai ɗumi sannan ya taho ɗaukarta,
  
   Harta k’ok’arta ta mik’e, tana tafiya dak’yar,
    “Yanzu sai dai kin tashi kin bama babynmu wahala?” ya taho zai kamata,
     “nidai ka barni plz, nan da toilet ɗin”
   “naji taho in rik’e ki tohm” dak’yar ya barta ta tafi ita kaɗai, ya gyara mata kujera ta zauna,”
    Hannunshi ya ciko da shampoo ya lafta mata, sannan ya fara gogawa a hankali kamar wanda baison taɓa kan, ta saka hannuwanta duka biyun a kumatu tana kallon ikon Allah ta mirrow,
   Kusan 15mnts kumfa bai gama haɗewa ko ina ba, ta saka hannu ta shafi kan,
    “Yaya majeed a haka yaushe zai wanku?”
    “zai wanku mna, bazan dai miki yanda zakiji zafi ba”
   “wankin kai ma har zafi ne dashi? Nidai bara inyi da kaina,
    “in barki kisha wahala kenan, indai kin gaji a bari sai gobe” haka tana ji tana gani ya dinga lallaɓawa a hankali yana wanke mata, daya murza sau ɗaya sai ya kwaraya ruwa, dak’yar ta mishi dubara tana wankewa yana zuba mata ruwa,
 
   Babu inda bai jik’e ba a jikinsu kafin ya gama wanke mata kan, sai da duk suka sake wanka sannan suka fito,
    Akazo wurin drying, da hand dryer yake busar mata da kan yana sharcewa, haka ya dinga soka comb ɗin yana zarewa, ba don ya shartu ba ya tattara mata abinta ya k’ulle,
   Yau taa rigashi farkawa, a hankali ta janye hannunshi daga jikinta, ta kara mishi pillow, sannan ta taho a hankali zata sauka daga saman gadon, sai dai taji ya kwanto jikinta ta baya, yana shak’ar qamshin gashinta, ta sauke ajiyar zuciya tana dariya,
    “yau na makara ko? Har kina shirinmin wayau”
   “A’ah da sauran lokaci fa, ni ɗinma na fasa fita, kai kwanciyarka”
   “nak’i wayon naki, kingama tashi na” idonshi cike da barci ya sauka daga gadon, daman basu daɗe da komawa ba bayan sunyi sallah, ba don tanaso ba ta koma ta kwanta,
   Kamar kullum saida ya tabbatar ta cika cikinta, sannan shima yaci, ya gyara mata kwanciya bayan ya aje mata duk abinda zata buk’ata sannan ya fita office,
    Duk bayan mintuna kaɗan zai kirata yaji ya take, kafin lokacin tashi yayi zuwanshi uku yaga koda abunda take buk’ata, ko kaɗan baison ta nema abu ta rasa,
    Da marece ya taimaka mata ta shirya tsaf, shima da shirinshi ya rik’o hannunta suka fito,
     “Yaya Majeed baka faɗamun inda zamuje bafa”
    “kedai kizo muje”
 “plz ka faɗamin Yayanah”
     “babynmu zamu k’arasa ma sayayya” saida ta tsayar da tafiyarta tana mishi kallon mamaki,
   “Yanzu siyayyar baby har akwai abinda ya rage mana?”
    “Shine zamuje mu gano ai, idan an kawo wanda bamu siya ba” mamaki daya mata yawa ma kasa cewa komi tayi,
    Sun kwaso siyayya sosae na baby da nata itama, ɗinkuna harta fara gajiya da yinsu, kayan babynma babu abinda basu siya ba anma duk saida ya k’aro, da ɗan gadonshi mai shegen kyau, shima kala biyu kenan suka siya, duk wani abun da zasu buk’ata sun siya sun aje tun kafin watan haihuwar yayi,
    Watan haihuwarta ya kama, momie da kanta ta sake mishi maganar komawar Majeeda gida, anma ya rufe ido ya bata ha’kuri kawai, haka Umma ma taso ta koma wurinta anma ya hana, sai dai ta tura mata Zahra tana taimaka mata, sunajin daɗin canjawarsu,
****
Tun cikin dare ta fara jin cikinta na juyawa, ana zungurinta, haka ta daure tayi sallahn Asubah tana ta k’arfin halin kar Majeed ya gane batajin daɗi, duk da Zahra nanan saida ya tabbatar ta cika cikinta, da duk wani abunda ya saba mata, sannan ya fita office,
     Haka ta takure wuri ɗaya tanajin ciwon na k’aruwa, ko Zahra ta shigo sai dai ta daure kawai tana murmushin yak’e, harta gama duk abinda take ta dawo ta zauna tayata fira,
    Sai haɗa zufa take ciwo na cinta ita kaɗai, tun tana iya maida ma Zahra harta kasa, ta fara k’ara tana rik’e cikinta,
      Zahra duk ta ruɗe ta kira layin Majeed, yana dai dai kiran Majeedar sai gashi ta kirashi, yayi saurin ɗauka tun kafin tayi magana ya rigata,
   “Zahra Abun yaazo ne?”
 “eeh Yaya kayi sauri kazo tana wahala sosae”
   “ganinan yanzu” tun kafin su gama waya ya fito daga office ɗinshi, cikin hanzari ya shige motarshi ya nufi gidan,
   Kafin suje Asibitin Umma ta rigasu, kusan tare sukaje da Aunty Zainabu, haka aka shigar da Majeeda, idanunshi duk sunyi jajir saboda tausayinta, kamar ya tayata kukannan yakeji,
    Ya kasa zama, ya kasa tsayuwa, yana jiyo kukanta har cikin ranshi, duk yanda Umma taso ya Zauna ya nutsu ya kasa, saima ya matsa nesa dasu yaci gaba da safa da marwanshi,
    Tasha wahala sosai har kusan la’asar bata sauka ba, har ana niyar ai mata aiki, cikin ikon Allah sai ga kai ya fara fitowa, dak’yar bayan tasha wahala, ta silalo k’aton jaririnta namiji,
     Kyakkyawan gaske dana kasa tantance da wanda yake kama a cikinsu, dogon hancinshi da gashin girarshi duk na Majeed ne, sai ɗan k’aramin bakinshi da fararen idanuwanshi na Majeeda, gashin kanshi mai sulbi ya kwanta, kamar na babanshi,
   Bayan ankai Majeeda inda zata huta akace su shiga, tunda Majeed ya ɗaukeshi sau ɗaya ya gani ya maida ma su Umma, ya koma wurin matarshi don duk damuwarshi tana a kanta
  Awa shidda tayi aka sallameta, Asibitin cike da family ɗinsu, haka suka cika motoci suka nufi gidan Majeeda da Majeed,
      Anan ma saida Umma taso ta tafi da ita gidanta tayi wankan Arba’in, anma Majeed yak’i amincewa, shida kanshi ma yayi driving don kar Umma tace dole sai an kaita can,
  Murna sosae su Abba sukai da jaririnnan kasancewarshi jikansu na farko, duk da a yanzuma aunty Zainabu na ɗauke da juna biyu,
   Kyautar tsantsararren gida Abba ya musu, zasu koma bayan suna,
      Kullum gidan cike da Mutane kamar a ranar ne suna, su Majeeda ba zama sai hidima da jama’a kullum Majeed cikin k’orafi yake bata bashi lokaci,
   Zahra takai mishi abinci yace ta turo mishi da Majeeda, fitowarta wanka kenan, saida ta ɓata lokaci wurin shiryawa, nanma dak’yar k’awayenta suka barta ta tafi, jaririn na kukata ɗaukeshi kawai suka tafi ɗakin babanshi,
    Tana shiga ya maida k’ofar ya kulle, da dubara ta ajje babyn, tun kafin tayi magana ya haɗa bakinshi da nata, sun daɗe a haka tun suna a tsaye har suka zauna gefen gado, kukan babyn ya saka suka tsagaita, ya zauna yana kallonsu ta saka mishi abincinshi a baki,
   “ko kewata bakiyi ko?”
  “Fiye da kaima Yaya Majeed”
     “ban yarda ba, tun haihuwar yaronnan kika daina kula dani, baki damu da cina ba, baki damu da kizo kiga yanda na tashi ba, idan bana kiraki a waya ba bazaki kirani ba”
   “ka yarda dani Yaya Majeed komai nake kana cikin Raina, ni kaina na k’agara a gama hidimarnan” ya mik’a hannu ya ansheshi bayan yaa gama sha,
    “Na kaasa koyon barci ba tare dake ba”
      “nima haka dear, yanzu ai na kwana biyu ne kawai”
   “Yayimin yawa fa,”
  “kaaci abinci?” kai ya girgiza mata, da sauri ta tafi ta zubo mishi, ta zauna ta bashi saida ta tabbatar ya k’oshi sannan ta k’yaleshi, taa daɗe har saida aka mata waya tayi bak’i sannan ta koma ɓangarenta,
   Tana ganinsu ta saki fara’a,
   “laah! Asiyah kardai ku cemun kune sai yau”
    “donma kin ganmu kenan, mu da ba’a faɗa nawa ba?”
   Fatima tace “ke kike maganarmu, yanda suke da hafsatul kiram ma ko ita bata faɗa mata ba” sai da gabanta ya faɗi da suka ambaci hafsatul kiram, na’urorin jikinta ne suka dakata da aiki na wani lokaci suna magana ma anma ko saurarensu ba tayi,
   Sai da Asiya ta taɓota, sannan ta dawo daga tunaninta duk ta rikice, ta fara murmushin yak’e,
   “Wa? hafsatul kiram? Kema kinsan bata k’asarne, kuma na rasa numberta tunda ta canja sim”
     “itama haka tace sanda na faɗa mata haihuwarki, halan tunda ta tafi bakuyi waya ba?” kai Majeeda ta ɗaga ma Fatima, sai kuma ta zaro ido da taji abinda tace,
    “kika faɗa mata na haihu, ya akai kika faɗa mata?” duk suka tsaya suna kallonta ganin yanda duk ta rikice lokaci ɗaya, Aunty Zainabu dake tattara wankin baby ta kalleta shek’ek’e,
    “miye don An faɗa mata?” ta k’ara washe hak’oran yak’e,
   “Ba komi Aunty kawai dai naso in bata mamaki ne”
   Fatima tace “kinga barama na mata waya ta fara miki k’orafin rashin kiranta tun yanzu” Majeeda sai k’ok’arin dai daita nutsuwarta take, ita tsakaninta da Allah ko tunawa da hafsat bata sonyi, tana cikin tunani Fatima ta mik’o mata wayar,
    “Aminiyatah!!” inji hafsat,
  “Na’am, Amaryar Umar shikenan an manta da mutane babu wani zumunci”
     “Haba! Ni zance miki haka, har ki sake aure bazaki sanarmin ba?”
  “Wai Aure? Ni ɗin?”
  “tohh daa wa?”
    “kinga besty zan kiraki, kinsan hidimar jama’a, yaushe zaki dawo?”
    “nan kusa, amma bazan faɗa miki ba nima, ki gaishemin da baby” a sanyaye tace “zaiji” sannan ta saki ajiyar zuciyah bayan ta kashe wayar,
   Basaina faɗa muku ba, kunsan nutsuwa taa k’are ma Majeeda a wannan rana, haka ta yini da tunani sosae, duk taa shiga damuwa,
Ranar suna yaro yaci suna Abdallah, ba k’aramin shagali akai ba a wannan rana, gida yaa cika da mutane, Anyi abinciccika kala-kala, nama ko ko shi kaɗai kakeso sai kaci ka k’oshi, ga gassasun kaji da soyayyun ma,
    Kayan barka ma Majeeda ta samesu harta rasa wurin ajjewa, banda kudaɗen data samu, gida cike da jama’a babu masaka tsinke, muryarta harta soma shak’ewa saboda hidima da jama’a,
    Tana cikin canja kaya text ɗin Majeed ya shigo mata,
    “Hey babe, i cant stop thinking about uh koma me nake ke nake gani, ina kewarki plz bzan ganki ba?” sai da ta ɗanyi murmushi sannan ta maida mishi,
    “miss uh more dear, hidimar jama’a sai a hankali, zaima zama abun magana idan nace zanzo”
   “plz babe, kwalliyan kawai zan gani” sai da ta ɗauka lokaci sannan ta maida mishi amsa, saboda yanda mutane keta shigowa,
   “ka duba pics a whatsapp yanzu”
   “nidai ban yarda ba, ga frnds ɗina ma zaku gaisa, sunata so su ganki”
    “Wlhy babu damar barin ɗakinnan fa, muyi waya dasu mana?”
    “Shikenan bazaki zo ba”
   “M srry nawan”
   “owk ki samamin lokaci da dare plz”
    Bata mishi reply ba wata frnd ɗinta ta anshe wayar, suka ci gaba da fira, haka a gajiye ta k’are hidimar, bata samu zuwa ba sai dai suka sha waya da dare,
   Washe gari su Aunty Zainabu suka dawo gyara mata gida saboda yanda aka ɓata ko ina, tare da wasu mutanenta da Zahra suka shiga gyaran,
       Tana can cikin bedroom ɗinta ta fara jiyo magana kamar ta hafsatul kiram sama-sama, gabanta ne yayi mummunan faɗuwa, ta tashi a hankali take tafiya zata lek’a taga kowacece, sukai kociɓus da ita tana shirin shiga bedroom ɗin,
    Sai da taja ta baya kamar wacce taga Abun tsoro,
     “Amaryar jego”
   “ke kuma haka ake dawowa babu labari?”
    “daman ayna faɗa miki mamaki zan baki” ta k’arasa inda Abdallah yake kwance ta ɗaukeshi,
     “Masha Allah, wannan kyakkyawan babe”
    Ita dai Majeeda binta kawai take da murmushin yak’e ko zama ma taa kasa yi, hafsat ɗinma ganinta take kamar wata mutum daban,
    “Ki zauna mana, kinsan ina da tarin tambayoyi sosae a baki na” duk taa ruɗe take magana,
   “tambayoyi kuma? Ay kya bari dai kisha ko lemu ne”
   “Haba gidanki nazo fa, kamar dai wata bak’uwa”
   “saiki zama bak’uwar mana tunda zuwanki na farko ne, kedai bara na kawo miki”
     “nidai ki barshi ki zauna” bata saurareta ba ta nufi hanyar fita, tana mata magana anma saida ta fita,
   Zahra ta rok’a Alfarma, ta kai mata drinks ɗin, sannan ta samu wuri inda su Aunty Zainabu suke ta Zauna, don ganin hafsatul kiram take kamar wata surukarta,
   Saida ta aiko kiranta ba don taso ba ta tashi ta tafi,
   “kin ganmu nan aiki muke ta fama dashi”
   “Shine kuma zaki barni ni kaɗai zuru”
     “kizo mu tafi falon mana kamar wata bak’uwa” ta mike zata tafi, hafsatul kiram ta kamo hannunta ta zaunar da ita, kanta ta dafe daya fara sara mata,
    “Daga ganin yanda kike kauce-kaucennan ya tabbatarmun da baki da gaskia, plz majeeda karki tabbatarmun da zargin da nake miki na HARAMTACCEN ZAMA kuke da Majeed”
    “kinga wannan ba lokacin da zamuyi maganar nan bane,”
    “sai yaushe zamu yita? Ko kina nufin wani auren kikai kika fito sannan kuka maida aurenku?”
    “keni babu wani auren da nayi, daman can wasa nake miki babu wani raba auren da mukai da Majeed” ta faɗa kanta a k’asa,
     “da gaske kike?” hafsat ta tambayeta tanason haɗa ido da ita,
    “da gaske mana”
  “k’arya kike Majeeda, akwai yanayin da mutum zaiyi wasa da kuma yanayin da mutum zaiyi magana a gane gaske ne, yanda kukai aure da Majeed babu abinda bazaku iya yi ba”
   Kuka ta fashe dashi, don kalmomin da zata kare kanta sun k’are mata, Hafsatul kiram ce kawai tasan matsalarta, kuma itace rufin asirinta, tasan zata bata shawara mai kyau,
   “ina sonshi hafsa, ina matuk’ar sonshi, bansan ta yanda akai na fara sonshi ba, anma bazan iya rayuwah babushi ba, ke kaɗai kikasan sirrinmu, shiyasa muka yanke shawaran muci gaba da rayuwanmu a haka, koda mun faɗa a gida tsinuwa ne kawai, Bama zanso abinda zai rabani dashi ba” hafsatul kiram hannunta har kyarma yake,
   “kina nufin bayan ya miki saki Ukun kuke zaune a tare?”
   “eeh don Allah ki taimaki rayuwatah karki faɗa ma kowa, wlhy bazan iya rayuwa babushi ba” duk ta rikice mata, tana kuka tana rok’arta, sai rirrik’eta take,
     “plz hafsa kicemun bazaki faɗa ma kowa ba”
     “Abunda naketa faɗa miki kenan Majeeda, anma ko sauraratah bakiyi ba, Yanzu idan kuka mutu a haka me zakuce da Allah? A haka zaku zauna kuna tara yara? Wata k’ila ni kaɗai nasan sirrinku a yanzu, kuna tunanin harku mutu Allah bazai to na asirinki ba? Duk son da kuke yima junanku bai kamata kuyi irin wannan zaman ba, kiyi tunani wannan ba soyayyah bace da zaku kai kanku da halaka, in banda abunki…..”
     “Plz hakanan nidai, naji shawaranki, nidai kicemun bazaki faɗa ma kowa ba”
    “Abinda ya dameki kenan? Naji bazan faɗa ba Majeeda, sirrinki da yafi wannan ma ni mai rik’e miki ce, wannan Alk’awari ne tsakaninmu”
    Cikin farin ciki Majeeda ta rungumeta tana murna,
    “Na gode sosae Aminiyatah”
     “babu godia tsakaninmu”
 Sannan ta ɗago fuskarta tana ci gaba da murmushi,
   Cak, fara’ar fuskarta ta ɗauke kamar wacce aka faɗa ma sak’on mutuwa, jikinta yahau rawa, hango Aunty Zainabu da tayi tsaye a k’ofa ta tsura musu ido,Wani wahalallen miyau ne ta haɗe da k’yar, tayi tsuru-tsuru da ita kamar wadda aka dasa, buɗe baki tayi zatai magana ta kasa ta bar bakin buɗe tana kallon Aunty Zainabu,
   Jikinta bai tashi kyarma ba saida Aunty Zainabu ta doso inda suke, tana tafiya tana kallonsu fuskarta babu annuri, bata ankara ba sai dai taji ta fara jik’ewa da zufa ta ko ina,
   “Aunty wallahi zan miki bayani, don Allah ki dakata, abinda kikaji ba haka bane”
   Bata tankata ba harta k’araso inda take,  tuni taa gama sandarewa, sai dai taga ta duk’a inda take, ta ɗaga filo ta zaro wayarta, sannan ta juya tabar ɗakin, ba tare data tanka musu ba
   Wata munafukar ajiyar zuciyah ta saki sannan ta juyo inda hafsatul kiram take itama duk taa haɗa zufa, tama fita ruɗewa, (wanda suka karanta littafin hafsatul kiram sun santa da saurin ruɗewa, abu kaɗan ke sakata kuka), tuni hawaye suka wanke mata fuska, harta so ba Majeeda dariya,
     “Akwai matsala fa” inji Majeeda,
   “Matsalan me kina ga batace komi ba, da alama bataji mu ba”
   “Zanyi fatan hakan hafsat, anma nifa hankalina bai kwanta ba da irin kallon da take mana” duk sukai shiru kowa ya rasa abun cewa,
  Sun daɗe a haka babu wanda ya iya cewa komi, k’arar shigowar text ne ya katsesu a wayar Majeeda, duk saida suka firgita, sannan ta daure ta duba, kamar wata marar lafiya,
     “I don’t say it enough, but wanted to let you know that I love you.”
   “luv uh too i swear, ina ka shige?”
    “cikin zuciyarki…lol ina hanya hope kowa dai ya gama tafiya, ina kewar matata da yawa”
   Ta sauke ajiyar zuciyah, addu’ah ta shiga yi Allah ya kawoshi gidan da wuri, tare da Addu’an Allah yasa Aunty Zainabu bataji su ba.
   Firarma kasawa sukai ita da hafsat, da gudu ta tafi toilet ta zazzagar da fitsarin data kusan saki shigowar Aunty, tana dawowa ta zari jikkarta,
   “Tohh Aminiyah, nidai zan tafi”
   ta tashi da sauri tana gyara ɗaurin zane, “ina kuma zaki tafi ki barni cikin wannan bala’i?”
    “Haba, ki kwantar da hankalinki mana komai zai dai-daita insha Allah, zamuyi waya Ya Umar yana waje”
   “kema fa hankalinki tashe yake taya zan kwantar da nawa?” dafa kafaɗarta hafsat tayi, suka fito tana kwantar mata da hankali,
   Sai dai me? Falonta wayam babu furnitures nata, komai an kwashe kamar sabon gini, duk suka saki baki suna kallo har Aunty Zainabu tazo ta bangajesu ta wuce bedroom ɗin nata tana sauri,
    Kayan sawarta ta dinga kwashesa tana juye mata a akwatunanta, hafsat na ganin haka ta mata sallama ta tafi, bata samu maa ta amsa mata ba,
    Tafiya tayi da sauri inda Aunty take ta rik’e mata hannu,
    “Aunty ina za’a kaimin kayan kike kwasarsu?”
Bata tankata ba taci gaba da kwashewa, sai da ta gama kwashe komai, ko k’yalle bata bari ba ta jasu tayi waje dasu, Majeeda ta k’ara shan gabanta,
    “Aunty don Allah ki faɗamun ina zaki kaimun kaya?” k’ara shareta tayi taci gaba da jan kayan,
   Duk ta ruɗe kuka kawai take kamar wacce ake zare ma rai, ta kwanta nan k’asa kamar k’aramar yarinya tana gunjin kuka,
     “Don Allah ki rufamun Asiri Aunty yanda naki ya rufu, ki taimakeni karku rabani da Yaya Majeed, shine rayuwatah, don Allah Aunty ki tausayamun” idan Aunty Zainabu ta tankata ku da kuke karatunnan kun tanka, haka taci gaba da kuka har muryarta ta soma sik’ewa,
  Tana ji tana gani suka kwashe komai na ɓangarenta,  harta Abdallah goyeshi tayi a bayanta, ta wurga mata mayafi,
    “ki tashi mu tafi nace”
 Da tafiyar gwiwa ta gangaro inda Aunty take ta rik’e k’afafunta,
   “ki kasheni ma kawai Aunty, zaifimun sauk’i da rayuwa babushi, don Allah karki Rabani da Yaya Majeed Aunty, ina sonshi” ta k’ara fashewa da kuka hannuwanta rik’e da k’afafun Aunty Zainabu,
   Ji tayi Aunty ta k’yalk’yale da daria,
   “lallai Majeeda bansan sanda soyayya ta rufe miki ido ba haka, ranar da za’a kawoki kin cika ma mutane kunne, ‘don Allah karku kaini, bazan iya rayuwa dashi ba,’ yau kuma kece da cewa bazaki iya rayuwah babushi ba, Sabon gidan da Dadd ya baku zaku koma, ko wani kike ba ajiyar kuɗin da za’a sake miki wasu kayan?”
   Wata doguwar ajiyar zuciyah ta saki tana jan numfashi, ta ɗago kanta tana kallon Aunty cikin shakkun maganar data faɗa, murmushi taga tana mata,
   “Aunty dgsk sabon gidan zaki kaini?”
   “da gaske mana, idan ba can ba ina zan kaiki?” shiru tayi sannan hankalinta ya fara kwanciya,
    “da tunanin me kikeyi?”
 “ba komi Aunty, mu tafi” tana maida mata murmushinta, suka fito suka tafi, sai jan Aunty take da labari don ta tabbatar ba haushinta takeji ba, ita kuma taci gaba da biye mata,
   Bata ankara ba ta gansu hanyar gidansu Majeed, ta ɗago fuskarta cikin wani hargitsin tana kallon Aunty, tun kafin ta mata magana ta rigata,
    “Zamu biya ki musu ban kwana ne” sannan ta saki ranta, hankalinta kwance suka shiga gidan, kai tsaye ɗakin Abba suka wuce
   Kowah ya haɗu a ɗakin kamar ana wani taro, Daddynta da Momie, Umman Majeed da Abbanshi, harda Zahra ma, Majeed ta hango shima zaune, anma bata ga alaman damuwa a fuskarshi ba don shima ba’a mishi maganar ba, kuma bai taɓa kawowa a ranshi zasu san da maganar ba,
   Ganin haka itama bata damu da ganinsu ba, don bataga alamar Aunty taji maganar da tayi ba, suka samu wuri saman carpet ita da Aunty suka zauna, suna satar kallo ita da Majeed,
   Abban Majeed ne ya fara magana “bamu zauna nan don ku mana k’arya ba, ko mu saurari wani shirme naku, kun riga da kun gama kaimu k’arshe, ku faɗa mana tsakaninku da Allah wanne irin zama kuke tsakaninku”
  Ba wani shakku a ran Majeed yace “irin zaman da kukeso muyi Abba, mun daina faɗa, ina bata duk wani hakk’inta na aure, ka tambayeta kaji” tun kafin a tambayeta ta amshe
   “sosae ma kuwa Abba, yana kulawa dani, muna zaman mu lafiya”
Daddy ya jefa musu da tambayar da duk saida ta kusan katse musu en hanji,
   “Bayan kun raba auren naku kenan?” duk suka fara muzurai irinna mararsa gaskiya, dak’yar Majeed ya iya k’arfin hali,
     “Raba Aure kuma daddy kamar wasu mararsa hankali, mema zaija mana raba aure?”
   “Wa kake tambaya cikinmu?” inji Abba,
    “daman ina hankalin yake? Ban taɓa tunanin zaku iya aikata hakan ba, kun munafunce mu, kuma kun cuci kanku…” Majeed da har yanzu baisan yanda akai ba, yayi saurin cewa
   “Abba mufa ba abinda muka aikata, idan ma wani ne yakeso ya haɗamu daku wallahi sharri ne”
    “waye zai muku sharrin cikinmu? Koda yake, daman kun daɗe da maidamu shashashai tunda har kuke tunanin bazamu gano zaman da kuke ba” Abba ya mik’a hannu ya ansa wayar Aunty Zainabu data ɗauka kusa dasu, ta kunno recordn ɗin maganar Majeeda da hafsa yanda kowa zaiji,
   Majeeda kamar ta zunduma da gudu, tama kasa zama kamar wacce zafi ya kama, hawaye ne kawai ke kwararo mata ta ko ina, tunda take bata taɓa shiga tashin hankali haka a rayuwarta ba, tama kasa ɗaga kai ta kalli kowa, Majeed ma tunda ya ɗukar da kanshi bai k’ara ɗagowa ba, zufa kam rigarshi harta jik’e,
   Ɗakin yayi shiru, sai sautin kukan Majeeda dake fita a hankali,
   “Shima wannan ɗin sharri ne?” Abba ya tambayesu,
  “Anma na rantse Abba babu abinda ya shiga tsakanina dashi…”
  Wani irin k’wallo Daddy yayi da ita,
    “shi cikin Abdallahn a ruwa kikasha cikinshi? Ko har yawon iskanci kike fita?” tai saurin rik’e bakinta, tana dafe inda daddy ya sa mata k’afa saboda zafin da yake mata, idanunshi sunyi jajir da ɓacin rai,
   Sai lokacin takai kallonta ga Momie, ta duk’arda fuskarta tana share hawaye da alama kuka take, wannan wane irin tashin hankali ne yau take gani?
   Abban Majeed ma cikin rawar murya da alama dauriya yace,
   “kun cucemu, kun karya duk yarda da mukai daku, Alk’awari ne mukai ma mahaifinmu, Anma a sanadiyyarku mun kasa cikawa, Allah ya gani munyi iyakar k’ok’arinmu, anma kun nuna mana baku isa ba, HARAMTACCEN ZAMA?, bansan a ina kuka samo wannan tarbiyyar ba, kuma kunyi kaɗan kuce mune muka baku ita, me kukeso jama’a suce a kanmu? Mun muku auren dolene kuka maida kanku haka? Wlhy k’arya kuke duniya ta zagemu a kanku, bazamu taɓa yafe muku….”
   Umma tace “duk meya kawo hakan Alhaji? Yanzu kuma inka musu baki ya kakeso su zama?”
    “harna yaushe kuma? ZAMAN DADIRO fa, wallahi zaifimin daɗi ace mutuwa sukai da inga wannan rana” duk k’arfin halin da Abba yake  da kuka ya k’arasa maganar,
   Can ciki Majeed shima Yace “Ayi hak’uri Abba, kuskure….” wani irin Mazga da Abba yakai  mishi a baki har saida yayi jini, cikin tashin hankali ya buɗe bakin sai gashi har hak’ori ya fita,
   Hakan baisa Abba ya saurara mishi ba, saima ya tashi ya rufeshi da duka ta ko ina, daddy na rik’eshi anma kamar yana k’ara mishi k’arfi, shiko Majeed ko motsawa baiyi ba, yana zaune yanda yake Abba na jibgarshi, dak’yar daddy ya k’waceshi ya matsa sai huci yake,
    “ka k’yaleni in kasheshi in huta da wannan bak’in cikin nashi, ai duk laifinshine, shine babba kuma sakaran banza, inama amfanin haihuwarshi?”
   “A’ah Yaya, idan har akwai laifinshi tohh nata yafi yawa”
      “laifinta data buɗa baki ta sakeshi? Idan har ya daraja maganarmu bai saketa ba zata saki kanta ne? Ko zata ma kanta ciki ne? Shine lalataccen ɗan iskan da yayi sanadin komi, ita tana da raunanniyar zuciya, da kalamai en kaɗan zai iya galaba a kanta” yana gama faɗi ya shige bedroom ɗinshi,  Umma ta tashi ta bishi,
  Haka su Daddy suma suka fita, Aunty Zainabu taja Hannun Majeeda suka tafi anan kowa ya watse akabar Majeed kamar wani zararre,
   Saida Zahra ta dawo ta mishi magana sannan ya mik’e ya tafi yana tangaɗi ko kallon gabanshi baiyi harya shige ɗakinshi
    Har sukaje gida Majeeda kuka take, babu wanda yayi k’ok’arin rarrashinta, kamar ranta zai fita haka take wannan kuka,
      Suna zuwa Aunty ta rakata tsohon ɗakinta, kayanta komi sunanan, ta kwance mata goyon Abdallah ta ajjeshi sannan ta juya ta barta nan,
  Jawoshi tayi ta ɗaura saman jinyarta ta tsura mishi ido, kowanne hali babanshi yake ciki? Shikenan fa kamar k’iftawar ido komai ya gama faruwa, rungumeshi tayi a jikinta taci gaban da kuka,
Bayan kwana biyu,
Majeeda babuci, babusha, saita kama dole, tayi wata uwar rama tayi bak’i sosae, kullum cikin kuka take, daga Momie har daddy babu wanda ya kula da halin da take ciki, Abdallah kanshi yayi ramar dole saboda bai samun isasshen abinci, sai dai da madara ake kaɗa mishi,
   Kullum cikin kiran layin Majeed take bai shiga, babbar damuwarta kenan da batasan halin da yake ciki ba, rayuwar gaba ɗaya taa burkice mata da babu Majeed a tare da ita,
    Sai a kwana na Uku ne Momie ta fara gajia da halin da take ciki, tunda ta shiga ɗakin bata fito ba, abinci yanda aka kai mata haka za’a ɗaukeshi, ruwa kawai take ɗura ma cikinta,
Tana kwance ta saka waya a gabanta tana kuka, bayan ta gama kiran layin Majeed,
   Momie tace “tashi Zaune” babu gardama ta mik’e zaune tana share hawaye, momie ta jawo kwanon Abinci ta ajje mata gabanta,
   “banson gardama, ki maza ki cinye abincinnan idan baso kike muci gaba da sanya miki ido ba” kuka ta fashe dashi sosai ta faɗa jikin momie,
    “Don Allah momie kuyi hak’uri”
   “naji tashi kici abinci nace” ta tallabota, sai da ta tabbatar taci mai yawa sannan ta k’yaleta bayan tasha ruwa, da kanta ta fita da kwanonin sannan ta dawo zauna tana fuskantar Majeeda,
    “Damuwar me kike?” tayi shiru ta kasa ɗago kanta, momie ta zare wayarta dake sak’ale a hannunta,
   “bamu isa mu rabaki dashi ba Majeeda? Yanzu kiran menene kike mishi?” shiru ba amsa,
   “ke ba k’aramar yarinya ba da basai an zauna ana miki faɗa ba, yanzu duk bayan wannan neman wata alak’a kike a tsakaninku? Ki zauna kiyi tunani kanki ne kike cuta, kece mace, daga inda ya samu wata macen zai manta dake, kekau kina nan kullum kina cutar zuciyarki da tunaninshi, kiyi tunani idan har yana sonki me yasa ya sakeki? Da yake kanki rashin hankali ya k’are kika zauna kikaci gaba da zama dashi, kullum kuna cikin saɓon ubangiji, kuna tara ma kanku zunubai, me zakuce da ɗanku idan ya girma ya gano ta hanyar da kuka sameshi? Ki godema Allah da abun ya tsaya a haka, damarkice da zaki zauna kita rok’ar yafiyar ubangiji, ki manta da Majeed da rayuwar da kukayi a baya,”
   “Momie wallahi na kasa ne, kullum ina k’ok’arin mantawa dashi, don Allah ki tayani da Addu’ah”
   “ki k’ara dagewa kam, don babu wani sauran zama a tsakaninku, babu inda kika taɓajin anyi saki Uku an koma, kema kina tashi kina addu’ah Allah ya yafe miki, ya kuma yaye miki sonshi, namiji ne da ba’asha mishi alwashi, duk yanda yakai da sonki wata rana shida kanshi zai goranta miki,……” nasiha dai sosae Momie ta shiga yi mata, gaba ɗata jikinta yayi sanyi, har momie ta barta tana zubar da hawaye,
   “Taya zan fara koyama kaina rayuwa babu Majeed?”
Majeed,
Shima tun daga ranar duk wani farin ciki ya k’aurace mishi, yana raye anma yafi kama da matacce, ko kukan ya kasa yi, idan ya fara kallon wuri ɗaya sai ya daɗe a haka, ko magana baiyi, tunsu Umma na ganin abun wasa harya fara damunsu, ada Zahra ce kawai ke kula dashi,
   Umma har sanyashi gaba take taita kukan kodai ya haukacene, gashinan dai har asibiti anje babu wani ci gaba, ko abinci aka ɗura sai anbi da ruwa zai haɗe,
  
Wata rana Zahra taje take bamasu Momie labarin halin da yake ciki, sai a sannanne majeeda na laɓe ta jiyo, taci kukanta harta gode ma Allah,
   Abdallah ne ta goya ta tafi dashi su Umma nata jajenshi, daga can ɗaki ya dinga jiyo kukanshi, takenan duk abubuwan da suka faru suka dunga dawo mishi, baisan sanda ya k’walla k’ara ba, sai a sannanne yayita kuka,
   Wani lokacinshi kanshi kukan yana maganin damuwa, sukaita murna jin ya dawo hankalinshi,
Aisha tana yawan zuwa ganinshi, duk da ba wata fira ke shiga tsakaninsu ba, anma tana k’ok’arin debe mishi kewa
A gurguje plz
Bayan shekara ɗaya
Abubuwa da yawa sun faru cikin, ɓangaren Majeeda ta gama makarantarta, hankalinta kwance ta fara mantawa da Majeed duk da abu mai wahala ne ta iya cire tunaninshi a ranta, anma tana k’ok’arin hakan,
      Abdallah yayi wayau, yana ɗan jagwalgwala magana, babu inda bai zuwa yawo koda gudu ne, kakanninshi kowanne ɓangare ji suke dashi, duk da ba’a yayeshi ba anma kusan kullum a gidansu Umma yake yini, ba k’aramin tausayin yaron sukeji ba, Aunty zainabu ma ta haifi ɗanta namiji, Abdul k’adir,
***
Anata shirye-shiryen bikin Majeed da Aisha, anyi hidima sosae duk da angon ba wani nutsuwa gareshi ba, mahaifinta ne ma ya matsa akayi saboda yanda ta guji auren kowa ita dai sai Majeed kullum tana gidansu, duk yanda Majeeda taso ta danne zuciyarta ta halarci bikin kasawa tayi, sai dai ta kulle kanta a ɗaki tayi ta kuka,
   An ɗaura aure, can kaduna state aka kai mishi amaryar don yanaso yayi nesa da gida,
   Dare yayi Amarya na can bedroom ansha lulluɓi ana jiran ango, kamar daren farkonshi da Majeeda shi kaɗai ya shigo da ledar kaji da drinks a hannu, ya tura k’ofar ɗakin zai shiga,
    Daren farkonshi da Majeeda ya faɗo mishi, yanda suka dinga faɗa kamar sun cinye junansu, baisan sanda ya saki laidar ba ya dawo da baya, kujera ya samu a falo ya zauna yana sharar hawaye, ba kaɗan ba yake kewar Majeeda,
     Shiru-shiru Aisha ba ango,  tun tana tunanin yana hanya ya kusan zuwa harta daina ta fara tunanin abinda ya tsaidashi,
   Har k’arfe ɗaya babu Ango, hankalinta fa ya tashi ta fara tunanin ko ina ya shige, shawarar kiranshi a wayane tazo mata, ta ɗauko wayarta ta kirashi, can falo ta dinga jiyo ringing ɗin wayar anma ba’a ɗauka ba, haka ta dinga kira tana katsewa, ta fara tsorata, cikin sadaukarwa ta lallaɓa ta fito falon,
Can ta hangoshi saman kujera yayi tagumi da alama tunani yake, ta daurema zuciyarta ta k’arasa inda yake, sai da ta ɗan taɓoshi sannan yasan da zuwanta,
      “Majeeda ko?” ta tambayeshi tana kallonshi da raunanniyar murya,
    “bazan miki k’arya ba Aisha, naa kasa mantawa da Majeeda, wlhy komai nake ita nake tunawa” cikin sigar lallashi tace,
    “ba abune mai sauk’i haka ba hniee, anma insha Allah nayi maka alk’awarin maye maka gurbinta, zan zame maka mace ta gari, zan maka dun abinda zai faranta maka in guji wanda zai ɓata maka, zan nuna maka soyayya fiye da wacce kake tsammani, ina sonka da yawa hniee”
   “ngde Aisha, kiyi hak’uri kinji, insha Allah zanyi k’ok’arin daina tunaninta”
    “ba komai fa hniee, taso muje ka kwanta, tunanin ya isa haka,” haka taci gaba da lallashinshi da kalamai masu daɗi har sai da ta tabbatar hankalinshi ya kwanta,
   A daren ranar Majeeda tayi kukanda bata taɓayi ba tunda tazo duniya, yanzu ne ta k’ara tabbatar ma kanta da taa rasa Majeed, daman Momie ta faɗa mata namiji ba’asha mishi alwashi, shknan har yayi aurenshi,
   Ga wani ciwon kai daya matsa mata ko barcin ta kasa, ita kaɗai a ɗaki Abdallah na wurin momie yayi barci tace a barshi tunda ba tashi yake ba, sai faman shafa confo take a kai,
    Abubuwa sun mata yawa kamar ita kaɗai damuwa ta k’are mawa, ga faɗan Abba kullum maganarshi ta fiddo miji tayi aure, kamar tana zaune a saman kansu,
   Tohh ita wama zata aura? Ita da ba fita take ba ballantana wani yace yana sonta, inma fitar dole ta kama mata da dogon hijabinta da nik’ab take tafiya, ta saɓa Abdallah a kafaɗa kamar matar aure, dole aji shakkar mata magana,
   Yanzu haka sauran sati ɗaya lokacin da daddy ya bata ya cika, koya aura mata duk wanda yaga dama, ta riga ta hak’ura da koma wanene, tunda ta rasa Majeed bata da wani sauran zaɓi,
   Kwana Uku da bikin Majeed har lokacin bata da wani natsuwa a tare da ita, zata fito dai ta taya Momie en aikace-aikacen da suka kamata, sai Momie tana janta da fira duk don taga hankalinta ya kwanta, anma data koma ɗaki sai wata sabuwar damuwar kuma,
   Yauma kamar kullum ta gama duk abinda take, ta shiga da Abdallah toilet ta sake mishi wanka, tun kafin ta shiryashi yaketa son ya fita, tana saka mishi kaya kam yabar ɗakin,
   Ta ɗauka ɗakin Momie ya tafi, ta shareshi tayi kwanciyarta har barci ya fara ɗaukarta ta jiyo muryar Momie tana tambayarta “Ina Abdallah” da ta ɗauka cikin barci ne, sai kuma ta tashi firgigit,
   “Momie ba wurinku yaje ba?”
   “A’ah tunda ya biyoki rabona dashi” ba shiri Majeeda ta sauko daga kan gadon,
   “ni wannan hegen yawon na Abdallah, yanzu haka yana can yana ɓarna”
   “Aikam k’ara ki nemoshi, don yau yaimun ɓarna kujera zanyi dashi”  tana dariya ta zira hijabinta,
   “Momie ana zauna mai gida?”
  “ni bani miji da wannan maɓarnacin, na barma Umma dai” dariya kawai tayi ta wuce, kullum cikin bata dariya suke, Momie da Abdallah,
Gidan ta shiga zagayewa, lunguna da sak’o da duk inda take tunanin Abdallah babushi, duk faɗin gidan babu inda bata duba ba, harta fito tsakar gida, inda ake ajje motoci ma taa dudduba babu shi, ta k’arasa tana tambayar mai gadi ko yaa ganshi,
   “wallahi hajia da yake na zagaya bayan gida ban lura ba koya fice, kuma saina manta da gidan a buɗe, duk an duba gidan bainan?” bata tsaya bashi amsa ba ta saka k’afa zata fice, kuma saita tuna bata da nik’ab ɗin, da gudu-gudu, sauri-sauri ta koma ciki sannan ta ɗauko ta dawo,
   Momie cikin tashin hankali take tambayarta,
   “Momie ban ganshi ba bari in duba cikin unguwa”
Abinka da unguwarda babu mutane, yaransu ma basu cika fita ba, sai en tsararun mutanen data gani take tambaya, anma kowa amsar ɗaya ce bai ganshi ba, tsananin tashin hankali harta fara hawaye ta cikin nik’abinta,
  Harta yanke shawarar komawa gida ta fasa, tasha kwanar layin bayansu, tana shiga ta hangoshi hannun wani handsome zaune saman bayan mota yana mishi wasa, sai dariya yake abinshi,
   Saida ta saukar da ajiyar zuciya, sannan ta k’arasa inda suke,
   “Ina wuni” ta gaishe dashi, cikin rashin fahimta yake dudduba kusa dashi, sannan ya dawo da kallonshi gareta ya tsura mata ido cikin nik’abin data rufe fuska dashi, yana son garin fuskar mamallakiyar zazzak’ar muryarnan, shikau Abdallah sai wasanshi yake a jikinshi,
    “Yaron dake hannunka nawa ne, ya fito daga gida” majeeda ta faɗa cikin k’osawa da kallon da yake mata,
  “ta yaya zan gane ba satarshi zaki ba, kina cikin wannan bak’in Abun”
   “na maka kama da mai sata ne? K’ila dai kaike shirin hakan” ta mik’a hannu zata ɗaukoshi aiko ya k’ara mak’alk’ale mutumin,
   “Abdallah” ta k’wala mishi kira cikin ɓacin rai,
  “Ayam” ya amsa da gwarancinshi,
   “Zo muje gida Momie na kira”
  “um-um, uncle” ya faɗa yana k’ara rik’e mutumin, takai hannu zata ɗaukeshi da tsiya, ya rirrik’eshi gashi bataso ta haɗa jiki dashi,
   “Don Allah ka bani yarona in tafi”
   “kingama tsoranki yake, alamar bai sanki ba, ki buɗe fuskarki idan da gaske kin sanshi” ganin tana k’ara ɓata ma kanta lokaci ya sanyata ɗaga nik’ab din, tsaida komi yayi ya tsaya yana kallonta, duk yanda yake hasaso kyawunta a zuciyarshi ta wuce nan,
   Abdallah na haɗa ido da ita ya k’ara lafewa jikin mutumin yana daria,
   “Auntieee, wannan ne”
 “wannan ne me? Kazo muje nace” ta jawoshi ya koma da baya yana dariya,
   “Don Allah malam ni Matar aure ce ka bani yarona in tafi”
   “Ni naa tambayeki ne? Ai gashinan saiku tafi, nima da kika ganninan mijin aure ne, kawai yaronne bani da, kuma ina matuk’ar son yara da saurin shak’uwa dasu”
   “nima duk ban tambayeka wannan ba” sai lokacin yayi dariya sosae harya fara bata haushi,
   “wai matar aure, don kuna kama dashi shine zai zama ɗanki? Matar aure ma kama ne da ita”
   “tunda kaa gane ina kama dashi, kasan ba satar shi zanba kenan? Ka saukeminshi in ɗauka” ya sauko daga samar motar ya saukeshi anma yaqi sauka,
   “gashinan masu ɗa”
Yaro fa yak’i sauka, sai daria yake yana rik’eshi,
   “ban juwa, didan”
  Duk yanda taso anma yak’i yarda da ita
    “hajia ki rok’eni kawai in kai miki yaronki gida” bata saurareshi ba taci gaba da lallashin Abdallah yazo su tafi, anma yak’i yama maida ita kamar k’awar wasanshi,
   “Abdallah bazaka je gida ba?”, ya tambayeshi, shikau harda saurin ɗaga kai,
   “Meyasa?” yayi shiru da yake maganarshi ba k’wari tayi ba,
   “mu tafi can muyi wasan ko”
  “eeh janje didan”
     “Yauwah tohh mu tafi yaron kirki” ya ɗaurashi a kafaɗa sukai gaba don yaga hanyar da Majeeda ta biyo,
   “Auntie mu tafi ko? Nima zan wuce gidane yanzu, ko an barmun shi?” batace mishi komi ba dai tabi bayanshi, suka tafi, sai da sukaje dai-dai gidan tace “tohh sauke minshi anan” ana saukeshi kau yayi cikin gidan da gudu,
   “na gode” tace mishi kawai, sannan tabi bayan Abdallah, yayi tsaye a k’ofar yana kallonta harta shige,
   Mai gadin ya taso rufe k’ofa ya ganshi nan tsaye, ya fasa rufewar bayan ya lek’o da kanshi,
    “Barka dai yallaɓai”
  “Yauwah baba, sannu da aiki” ya juya zai bar wurin,
   “Aiki da godia, wurin Alhaji kazo ne?”
  “A’ah yaron Matar gidan dai na maido”
   “matar gidan kuma? Ɗiyar Alhaji dai” harya fara tafiya ya dawo jin haka, baba mai gadi harda gyara tsayuwa zai fara tsegumi,
   “Shifa yaron?”
  “ɗanta ne, anma yanzu shekara ɗaya kenan da en watanni basu tare da mijin”
  Gaskiya mai gadinnan akwai surutu, mutumin ya faɗa a ranshi,
   “Allah sarki, nagode sosai baba” ya zaro dubu biyu ya mik’a mishi, ya amsa yana washe baki, don akwaishi da son kuɗi
   “ni keda godia yaro,” sai kuma ya kasa tafiya, yayi shiru yana so yayi ma baba magana,
  “numberta zan baka?” da sauri ya ɗaga kai,
  “yauwah baba za’a samu ko”
  “eeh yaro, anma ka k’aro dubu biyar”, yana kallon tudun Aljihunshi, ikon Allah wannan wanne irin mai gadi ne? Gashi dai tsoho sai tsurku da son gulma, ga shegen son kuɗi,
   Ya kwaso duk kuɗin Aljihunshu dubu uku,
  “gashi baba, daman su kaɗai suka rage”
  “tohh shknan yaro nima rabi zan baka tunda rabi ka bada” baza’ayi haka ba baba ina zuwa,
   Ya koma inda ya aje motarshi, ya jawota k’ofar gidan, ya dawo ya mik’a mishi dubu biyar cas sannan yace yana zuwa, ya shiga ɗakin da yake ya ɗauko wayar bala driver daya bari chaji ya kawo mishi,
   “Gashinan Alhaji duba, ko hajia Majeeda, ko Majeeda, ko er gatan Alhaji duk yanda kaga an rubuta”
   “Sunanta majeeda kenan” ya faɗa yana murmushi, “suna mai daɗi, kuma ya dace da ita,
  Ya maida mishi wayar yana godia bayan ya ɗauka number,
   Abdallah da gudu ya shige gidan, Majeeda na mishi magana bai tsaya ba saida yaje inda momie take ya faɗa jikinta yana daria, sannan taja ta tsaya tana kallonshi,
  “Abdallah ina ka tafine muna ta nemanka?”
   “wuyin uncle” ya fara lallaben Aljihunshi ya ciro chocolates yana bata,
   “shine ya baka wannan” ya ɗaga mata kai,
   “ka daina fita yawo kaji” nanma ɗaga kan yayi, sannan ya sauko kuma ya tafi wurin Majeeda ta ɗaukeshi, suka tafi ɗaki,
   Faɗa sosae ta mishi harya fara kuka, ta rungumeshi don batason ɓacin ranshi, ta share hawayen daya zubo mata,
   “ka daina rashin ji kaaji yaro nah”
   “baran kala fita ba”
  “yauwah nima naa daina maka faɗa” taci gaba da lallashinshi har yayi barci,
  Da dare harta kwanta, taji wayarta na ringing, ta jawo da duba bata gane number ba ta maida ta aje, mai kiran dai ya nace da kira gashi barci takeson yi, ta ɗauka kawai batayi magana ba,
   Ɗayan bangarenma shirun akayi, harta gaji da saurare ta kashe ta maida ta ajje, aka sake kira ta kashe wayar ma gaba ɗaya,
Da safe tana kunna wayarta kiranshi ne ya fara shigowa, ba tare data duba bama ta ɗauka,
   “Assalamu Alaiki” ya faɗa da daddaɗar muryarshi cikin nutsuwa,
   “Wa’alaikas salam,” ta amsa mishi,
   “Hajja Majeeda ina fatan kin tashi lafiya” mamaki ne ya kamata sosae yanda har yasan sunanta,
   “Yi hak’uri don Allah ban gane mai magana ba”
   “wanda kike tsammanin kiranshi ne, ko kuma nace wanda kike tunani a halin yanzu”
   “Banfa gane mai magana ba”
  “kina neman k’arin bayani dai, anma daɗewarmu a jiya, bai kamata ki sauri mantawa dani haka ba, kamar yanda nima na kasa daina ganin kyakkyawar fuskarki”
     “Shine kuma akace dole sai nayi tunaninka? Don Allah malam na faɗa maka fa ni matar aurece” ta faɗa da alama ya fara ɓata mata rai
   “Ajiyan fa kamar naa yarda, kafin in gano gaskia, don Allah majeeda mu duka ba k’ananun yara bane, ki bani dama in faɗa miki abinda ke tafe dani” shiru ta mishi, hakan ya bashi damar ci gaba da magana,
   “Sunana Shaheed, anma family namu sunfi kirana da sarki”
   “sarki?” ta maimaita, ba tare da taa sani bama,
  Yayi er dariya “da ina yaro kuka ne dani, shine mama na ta samun sarkin kuka”
   Dariya ya bata, ta rik’a abinta ciki-ciki tana saurarenshi,
   “ina rik’e da kamfanin mahaifina ne a halin yanzu, bana aikin gomnati, naayi karatun gaba da secondry har zuwa master’s, sannan kuma kamar yanda na faɗa miki ina da Mata shekararmu biyar kenan da aure, Allah bai bamu haihuwa ba, ban taɓa tunanin auren MATA BIYU ba, sai jiya da na ganki, kallo ɗaya kika kwanta min a rai, Allah ya jarabceni da soyayyarki, don Allah Majeeda ki bani dama, ki shigo rayuwarmu nida iyalina, ina matuk’ar k’aunarki,
   Shiru tayi kamar mai nazari, hakanan taji hawaye nason zubo mata,
   “Don Allah kice wani abu Majeed, kice kin yarda, a shirye nake dana miye miki gurbin tsohon mijinki, na zame ma Abdallah tamkar mahaifinshi, ki amince dani, ni masoyinki ne na gaskia”
    Kasa rik’e kukanta tayi, ta kashe wayar kawai ta jefar da ita, taci gaba da kukanta da ita kanta bata san dalilinshi ba, sai da tayi mai isarta, sannan ta shiga toilet ta wanke fuskarta, ta fita daga ɗakin tana jinshi yana sake kira ko kallon wayar batayi ba,
   Kamar mai tsoron wayar ta kasa komawa ɗakin duk da taa gama abinda take, ta nemi wuri a falo ta fara kallon dole har marece yayi, sannan ta koma ɗakin,
   Miss calls ɗinshi 99, ta kashe ta gaba ɗaya ta tura ta jikka ta ajje, wani irin nauyinshi takeji, don yaa wuce saurayi tunda harda Mata, zai kai irin 35 haka, wani irin yanayi takeji a kanshi, anma ta rasa ta yanda zata fassara yanayin, bata ɗauka bayan Majeed ba akwai namijin dazai iya tsaya mata a rai haka, ita tayaya ma zata fara soyayya,
       Kwananta biyu bata kunna wayar ba, sai ana uku, gobe kenan lokacin da Daddy ya bata zai cika, tana gyara ma Abdallah kayanshi ya shigo da gudu,
    “Auntie, Momie na kiya” ya koma da gudu yana faɗa mata, tana tambayarshi ‘ina Momien’ ko tsayawa baiyi ba,
  Tana zuwa momie ta faɗa mata bak’one tayi, ta koma ta sako mayafi sannan ta fita,
     Can ta hangoshi da Abdallah saman cinya sai surutu yake zuba mishi, hannunshi choculate har babu hannun rik’ewa, yana hango ta ya kasa daina kallonta, har tana harɗewa ta samu dai ta k’arasa, taja kujera ta zauna, sannan ta ɗan zamo ta gaidashi,
    Ya amsa yana ta fara’a, har lokacin idonshi na kanta,
   “ke kuma kalan naki salon horan kenan Majeeda?” ta k’ara k’asa da kanta tana wasa da yatsunta,
  “Anan ɗinma babu amsa? Yau kwana nawa kin kashe waya da sai dai ki jini asibiti, kasa daure wa nayi yau nazo da k’afafuna sauraren Amsa”
   “hhm” tace da alama duk ta takura da zaman, haka amsarta ta kasance, sai kuma “eeh” da “A’ah” shi kaɗai yake zuba surutunshi harya lura da yanayinta,
    “Da alama yau baki cikin yanayin kodai sai a waya zaki bani amsar” da sauri tace, “toh shiknan” sai da ya murmusa, “in kuma naji a kashe gobe ki k’ara ganina” murmushi kawai tayi, ta mik’e ta tafi,
   “ba bankwana?” ta kasa juyowa,
   “Allah ya kiyaye hanya”
       “Ameen” ya faɗa yana sauke Abdallah, bayan ya cika mashi aljihu da kuɗi,
   Ya juya zai shiga motarshi saiga Daddy ya shigo, ya tsaya harya fito sannan yaje ya gaisheshi har k’asa cikin ladabi, ya tashi zai tafi ya tsayar dashi,
A gurguje,,,,,,,,,
    Daddy yace “sai dai ban ganeka bane” cikin ladabi yace,
   “Sunana Shaheed ibraheem imamu Abba, nazo wurin Majeeda”
    “tohhhh, Alhaji ibraheem dai wanda na sani?”
    “eeh Abba”
 “tohh masha Allah, idan ka koma gida saika turo iyayen naka, nan da wani ɗan lokaci sai a….”
    Don tsabar jin daɗi ma baisan sanda ya katse Daddy ba,  “Da gaske Abba” wani irin kallo ya mishi na rashin ganewa sannan ya gane bai kyauta ba, daya saka k’ok’onto a maganar, yaci gaba da washe baki ba kunya Shaheed kema Daddy godia,
   Washe gari lokacin daya ɗibarma Majeeda ya cika, tunda safe data shigo gaisheshi ya tsayar da ita,
    “kina sane da yau ne lokacin dana ɗibar miki ya cika”
    “eeh Abba, bani da wani zaɓi, Insha Allah zanyi biyayya ga duk mijin daka zaɓamun”
    “Tohh tashi kije, Allah ya miki Albarka, daga yau ki fara shirye-shiryen bikinki nan da wani ɗan lokaci” wani irin faɗuwar gaba taji,
    “Ameen Daddy” ta mik’e jiki ba k’wari tabar ɗakin, tohh anma meyasa bata faɗa ma Daddy Shaheed ne zaɓinta ba? Kuma dai gani take kamar yaa fasa don tun bayan tafiyarshi, bai nemeta a waya ba, koba wannan ma yanzu tafiso Daddy ya sake mata wani zaɓin da kanshi, don ta samu ta mishi biyayyar data kasa a baya,
•••   •••   •••
   An kusa bikin Zahra, sai aka saka lokaci ɗaya, Duka bangarorin sai shirye-shiryen biki suke, su Majeed anzo biki, shi yanzu hankalinshi kwance, soyayya da kulawa babu wanda bai samu a wurin Aisha, tuni ya manta da komai ya rungumo matarshi don ba k’aramin so take mishi ba,
   Majeeda ma tunda hidimar bikin ta kama, ta kwantar da hankalinta, bama kamar da taasan Shaheed ne zata aura, ta kasa yarda ne, anma wani ɓangare na zuciyarta faɗa mata yake ta fara kamuwa da soyayyar Shaheed,
     Ansha shagalin biki, garin Mashi aka kawo mana Zahra😉, Majeeda kuma Aka ajeta Katsina Layout, taci kuka sosai, kamar shine aurenta na farko,
    Da dare ya kirasu ita da uwargida domin musu nasihar zaman lafiya, tana zaune kafin uwar gidan ta fito taa tsura ma wani hotanta dashi ido, sunyi kyau sosae tana tsaye ya rungumota daga baya suna dariya, kyakkyawahce anma bata da haske sosae da ɗan k’aramin jikinta mai kyau,
    Jin tafiyarta ne yasa Majeeda ta daina kallon hotan ta maida kanta k’ansa, ta zauna kujera mai kallon wacce suke sai k’amshi take zubawa, da yake Maryam akwai tsafta,
     Sai da ta ɗago ta kalleta ne, kamar ba itace a hotonnan ba, tayi wata uwar k’iba sosae, irin hajiyoyinnan, cif ta cika kujera mai zaman mutum ɗaya, babbar mace mai halin dattako, bai ɗauki wani lokaci yana musu bayani ba, ya sallamesu kowa ta koma ɗakinta,
    Zaman su da Maryam sosai takejin daɗinshi, tana janta a jiki, har dangin shaheed take janta kasancewarta mace mai zumunci, da fahimta, ɓangaren Shaheed ma bata da wata matsala, yana bata kulawa sosai yakeji da iyalanshi, bata da wata damuwa yanzu,
    Sai dai kewar Abdallah da yanzu yake hannun Umma, kowa yaso a bar mishi shi, sai daga k’arshe suka hak’ura aka barma Umma,
    Watansu Uku da aure Allah ya albarkaceta da juna biyu, ba k’aramin farin ciki Shaheed da Maryam sukayi ba, kusan ma Maryam duk ta fisu Murna, tun daga lokacin ta ɗaukema Majeeda duk wata hidimar gida, ita take kula da ita, sai abinda takeso za’a girka, Maryam mace ta gari ce sosae, kusan tare suke rainon cikin,
   Har mamakin Maryam take, mace mai kawaici da k’ok’arin danne kishi, irinsu kaɗanne a duniyar nan, ko godiya take mata sai dai tace
    “banson haka fa Majeeda, ni ban taɓa kallonki a matsayin kishiya ba sai dai er uwa, abinda muka daɗe muna Addu’ar nema ne da Shaheed, Allah bai bamu ba, kuma yaa nufeki da samu, ina tayashi son duk abunda yakeso, wallahi ji nake duk ɗayane”
     “Gaskiyarki Auntyna, ina yima kowacce mace Addu’ar samun kishiya ta gari kamarki” Maryam tayi daria,
    “da kuma macce ta gari kamar ki ba” sukai dariya gaba ɗaya, kamar ba kishiyoyi ba,
   Cikin Majeeda nada wata hudu, k’awar Maryam tazo ta iskesu suna fira da Majeeda, sai dariya suke bazaka taɓa cewa kishiyoyi bane, ko gaisuwar Majeeda dak’yar ta amsa taja Maryam suka shige ɗakinta, tun kafinsu zauna tayi k’asa da Murya,
    “Me nake faɗa miki Maryam? Ke har yanzu kin kasa gane inda ke miki ciwo”
   “ko kuma kece kika kasa fahimtata Asiya, nifa babu abunda yarinyarnan ta tsaremun”
    “Aikam baki shirya ganin aibun kishiya ba, wallahi karki ga yanzu da cikinnan yana miki kawaici, tana ajje ɗa a cikin gidannan keda babu duk ɗaya, a hakan ma ya aka k’are? Wallahi duk yanda kikeson Shaheed tana haihuwa zata rabaki dashi”
  Anzo wurin, don babu abinda Maryam tafi tsana a rayuwarta kamar ace zata rasa Shaheed, “Tohh anma Asiya, nima fa inason inga yaro a cikin gidannan, shekara nawa bamu samu ba?
   “Zaki ga yaro a cikin gidannan, anma kina da iko dashi? Wata da tazo cikin ɗan lokaci zata rabaki da gidanki, idan kuma so kike sai lokaci yayi ki bani labari tohh in saka miki ido”
    “inaaa zan zauna? Nidai yanzu ya za’ayi?”
   “kuɗi kaɗan zaki bada, yanzu daganan wurin wani malamin zaure zanje a lalata abinda ke cikinta, daganan kema in anso miki maganin haihuwan”
   “da gaske nima zan samu haihuwan?”
  “indai kinyi yanda akace, kuma saikin yarda da malamin sannan zaki ga aiki”,
   “gaskia wannan ba k’aramin Albishir bane, anma don Allah kar ayma Majeeda wani mugun abu” tsoki Asiyah taja,
   “hajia idan kinason aiki, ki tashi ki ɗauko yanzu in dawo miki da magani, da zafi-zafi ake dukan k’arfe”
   “inaso mana, yanzu kuwa”
Ta tashi ta lalubo mata kuɗi ta bata, har bakin gate ta raka ta sannan ta dawo,
   Ranar Majeeda keda Shaheed, Anma Maryam ita tayi komai kamar yanda ta saba, babu wani canji a tare da ita, bayan sunyi dinner yaja matarshi suka wuce ɗaki,
    Ta fito daga wanka tana ɗaure da towel, ta isa gaban mirrow ta zauna zata fara shafe-shafe, suka haɗa ido ta cikin madubin yana kwance ya k’ura mata ido, suka sakar ma juna murmushi,
   “banson kallo fa”
   “laifine don mutum ya kalla matarshi? kawai tunani nake”
   “tunanin me kuma?”
  “Da wanne irin farin ciki zan kasance a ciki? Idan ya kasance dake na fara rayuwa”
  “hhm zaka fara ko”
  “wallahi da gaske nake Majeeda, ban taɓa farin ciki ba kamar ranar dana fara ganinki, kowanne dak’ik’a ɗaya da nayi tare dake, ina alfahri dasu, ji nake kamar donke kaɗai akayi zuciyatah, kece farin cikina”
    “nima ina farin ciki dakai sosae, inajin daɗin kasancewa dakai, ina sonka fiye da kowacce halitta dake doron k’asa” ita kanta batasan sanda maganar ta fito mata ba, anma tasan tabbas k’aryane ta faɗa,bata da kamar Majeed a zuciyarta,
  Cikin farin ciki ya tashi ya tare ta zata saka kaya,
    “da gaske kike kina sona fiye da kowa” cikin son subar maganar tace “da gaske mana, har kana k’ok’onton soyayyar da nake maka?”
   “A’ah wlhy, kina nufin har daddyn Abdallah kenan?”
    “wake Maganar daddyn Abdallah kuma yanzu?”
   “nidai inason sani plz, nasan kinso Majeed sosae Majeeda, kina nufin son da kikemun yanzu yafi nashi?”
   Rasa yanda zatayi tayi, duk ya tsareta da tambaya, gashi batason ɓata mishi rai,
     “Soyayyar Majeed daban take a zuciyatah, ban taɓa tunanin zan iya koda kallon wani namiji a matsayin namiji ba bayanshi, anma a yanzu da nake tare dakai, banama tunawa dashi, nikam soyayyar da kake nunamin ma ta isa, ban buk’atar sanin tsakanin Ni da Aunty Maryam wakafi so, wannan sirrin zuciyarka ne”
   “ke ta dabance Majeeda, kalamanki suna matuk’ar tasiri a zuciyatah, kece wannan sirrin na zuciyatah, kinason sanin wa nafi so?…..”
Girgiza mishi kai tayi, ba magana, ya jawota ya haɗa da jikinshi, ya fara aika mata da sak’onni cikin wani irin yanayi, m sai da aka turo k’ofa sannan sukai sauri suka saki juna,
   Maryam ce saida ta shigo tsakiyar ɗakin sannan ta fahimci halin da suke ciki, sai da ranta ya sosu, anma ta kanne kawai,
   “kuyi hak’uri na shigo muku kawai, bansan oga na ciki ba”
   “haba, Aunty keda ɗakinki kuma”
   “uhm, maganinki na kawo miki, nasanki da wasa dasha”
  Ta mik’a mata ruwa a cup da maganin, ko kaɗan bata kula da yanayin canjawar ruwanba, sai da ta kwankwaɗeshi tass, sannan ta mik’a mata cup ɗin,
    “nagode sosae Aunty”
  Ta ɓata rai “banson haka fa, sai da safenku” ta fita ta rufo musu k’ofa
Ta juyo wurin Majeed tana mishi murmushi,
    “Auntynah tana ji dani sosai”
     “gaskia ne, nayi sa’a sosai da samun mata na gari”
   “Muma munyi sa’a da samun miji na gari, da kowacce mace zatayi alfahrin samu”
  Ya jawota bayan ta gama saka rigar barcinta,
   “hajia nifa na gaji da wannan jan lokacin” ya kashe musu fitila, saboda yau cikin tsananin buk’atarta yake,
   Tun lokacin daya fara da shasshafa jikinta ta fara jin wani yanayi a jikinta, can cikinta takejin kamar wani abu na motsi anma ba sosae ba yana ɗan tsira, bata ɗauka wani abune daban ba, anma ciwon har tsakiyar kanta take ji, kasa taɓuka komi tayi, wani irin azaba ta dingaji bayan ya tashi ya shiga wanka, kamar tafiyar tsutsotsi haka ta dinga ji a cikinta duk yaa yamutse kamar ana cin kayan cikinta, ga wani irin zafi kamar ana dahuwa a ciki,
   A haka ya dawo ya iske majeeda,
     “wankan fa dear?” shaheed ya tambayeta,
  Dak’yar ta iya buɗa baki tana cije leɓe,
      “zan tashi inyi” baima lura da yanayin da take ciki ba, yaja bargo ya kwanta,
  Haka ta dinga juye-juye, hannuwanta biyu ta dinga sawa tana matse cikin ko zataji sassauci, kamar ruɓaɓɓen abu haka takejin cikin, ta sauko qasa komai ta samu ɗaura ma cikin take ta dinga juye-juye, da taji dai abun bamai k’arewa bane, ko nak’udar Abdallah bataji azaba haka ba, a kwance ta dinga jan jiki har inda Shaheed yake, ta dinga tashinshi, baimasan tanayi ba barcinshi yayi nisa,
    Hawaye ta dinga zubarwa masu zafi, ko ina jikinta ciwo yake kamar ba nata ba, ko hannunta bata son motsawa maganar ma ciwon buɗa baki takeji, haka ta dinga daurewa tana kiranshi, ta saka hannu tana bubbugashi, wani masifaffen ciwon nema idan jikinta ya haɗu da nashi,
   Jinta tayi taa jik’e kamar wacce tayi fitsari, a ruɗe ta saka hannu ta shafa k’asanta, jinine ta gani a malale, ba k’aramin ruɗewa tayi ba, ta fara wani irin kuka,
   “Na shiga Uku, ya Allah ka taimakeni kar in rasa wannan farin cikin na shaheed, don Allah ka tashi shaheed, karmu  rasa abunnan da muke matuk’ar so, ka tashi shaheed karka rasa mu” haka ta dinga kuka, tana sambatun da azabarma bata bari tasan tana yi ba,
    Maryam na jiyota daga inda take laɓe, ta koma ɗaki cikin farin ciki bama kamar da taji Shaheed baisan tanayi ba, anma kuma a yanda take jin tana magana dak’yar tausayinta take ji sosae, da kuma tausayin shaheed idan ya rasa wannan cikin na Majeeda daya k’wallafa rai a kanshi,
    Sai da ta galabaita sosae, harta suma a wuri sannan shaheed ya farka, da sauri ya buɗe idanunshi ganin halin da Majeeda take ciki kwance a gabanshi bata ko motsi, cikin tashin hankali ya shiga girgizata anma ko motsi ba tayi, ga jini malale a jikinta daya qara tayar mishi da hankali,
    Fridge ya ɗauko robar ruwa ya dawo inda take ya fara kwara mata, ta saki wata doguwar ajiyar zuciyar, idanunta sun k’ank’ance saboda azaba ta shiga hawaye,
    “Cikina Shaheed, mutuwa zanyi, mutuwa zamuyi nida babynmu”
   “bazaki mutu ba Majeeda, rayuwatah tana buk’atarki, don Allah kicemun babu abinda ya samu babynmu” girgiza kan zafin ciwo kawai take, tana hawaye, duk ya fita hayyacinshi,
   Ganin yanda take dafe da cikinta, da alama tana cikin azabar ciwo, ya ɗauko robar ruwan ya shiga tofa mata addu’ah, wadda RAZ suka kawo a littafin dodon jatau, da kuma ayatul kursiyyu, suratul ikhlas, falaq da nas, kowanne sau Uku, ya dawo fuskarta ya bata tasha, sannan ya kwantar da ita, ya shafe mata fuskarta da cikin, da hannuwanta da k’afafuwanta, ta kwantar da kanta kawai jikinshi, tayi shiru tanajin ciwon na lafawa kaɗan-kaɗan,
   A haka barci ya ɗauketa jikinshi, ya gyara mata kwanciyar, bai koma barci ba, sai dai ya ɗauko Al-Qur’ani yana karanta mata har aka kira sallah, kallon tausayi kawai yake mata, kamar ya cire ciwon ya maida a jikinshi, rok’on Allah ya shiga yi daya kare mishi abunda ke cikinta, yasa babu abinda ya sameshi,
   Sai da aka kira sallahr asubah ya lallaɓa ya sauketa daga jikinshi, yana tashi itama ta buɗe ido, da k’arfinta ta yunqura zata tashi, ya dawo zai rik’ota
     “ina zakije?”
   “wanka zanyi”
       “tohh kwanta bara in haɗa miki ruwan”
   “Zan iya fa”
  “kedai ki kwanta nace”
     “tohm ranka shi daɗe”
  Ta koma ta kwanta ba don tanajin daɗin kwanciyar ba, don ko ina jikinta a ɓace yake, sai dai jinin ya daina zuba,
    Shiya taimaka mata ya mata wankan, dak’yar ya barta ta gyara wurin duk da tace mishi ta warke, sannan ta koma ta kwanta bayan tayi sallah jinta take kamar bata taɓa ciwo ba,
   “tashi fa zakiyi mu tafi asibiti”
   “Ba buk’atar wani asibiti fa, na warke”
 
 “kinason min wasa da baby ko? Da lafiyanki ma, jini kika zubar fa, na damu da sanin matsayin da babynmu yake ciki plz ki tashi mana” sai kuma yayi shiru muryarshi ta canja damuwa ne fal a ciki,
   “Duk laifinane Majeeda, da nasan zaku cutu jiya duk buk’atar da nake da wlhy dana hak’ura, baki kyautamun ba da baki faɗamun ba tun wuri”
   “Nima fa ban sani ba, anma fa tun kafinnan ne nakejin ciwon, karka zargi kanka shaheed, bara in shirya ɗin”
    “tohm” ya faɗa kawai yayi zurfi cikin tunani, duk damuwah ce a ranshi,
   Tare suka fito bayan sun shirya, karo sukaci da Maryam da kayan abinci a hannunta, ta tare su da murmushi,
    “Yanzu nake shirin kawo muku break fast ashe harkun fito, bara in kai muku dinning” ta juya tana ci gaba da magana, wani irin farin ciki take ciki,
    “inanan ina aiki, anma hankalina na wurinki, ya jikin naki?” sai da Majeeda tayi shiru cikin mamaki sannan ta bata amsa,
    “Yayi sauk’i auntie, Kin tashi lafiya?”
  “lafiya lau Majeeda,” sannan ta juya wurin shaheed ta duk’a har k’asa cikin ladabi ta gaisheshi, ya amsa mata kamar shi yayi ciwon ba Majeeda ba, duk ya shiga damuwa,
    Abincinma kaɗan yaci, ya tashi bayan yacema Majeeda ta sameshi a waje, harya juya zai tafi kuma ya dawo da kallonshi kan Maryam, cikin wani yanayin da har saida ta tsorata,
    “Ya akai kikasan Majeeda bata lafiya?” kame-kame ta shiga yi, tama rasa amsar da zata bashi, Majeeda ce tayi murmushi,
    “Ba daɗewa fa ka faɗa mata zamuje asibiti” da sauri Maryam ta ɗago tana yak’e,
   “eeh mana, kaine ka faɗa”
   Har lokacin kallonta yake, don yasan kishi babu abinda bai saka mata, kuma bai manta da maganin data kawo mata ba, don ranar ne kawai ta taɓa bata magani da kanta, shi yamayi tunanin k’wayar maganinne tunda a hannu tazo dashi,
   “tunda muka fito bamui maganar asibiti ba,”
    “Miye haka Shaheed?” majeeda ta tambayeshi, hannu ya ɗaga mata yana kallon Maryam, can dubara tazo mata,
    “Wai Yau nice kake tsarewa da tambaya saboda na nuna kulawa a kan matarka? Jiya kukan data dinga yi tana wayyo cikina waye baiji ba? Ban taɓa tunanin hakan daga gareka ba Shaheed” sauke ajiyar zuciyah yayi sai kuma baiji daɗi ba,
     “Kinsan na yarda dake da yawa Maryam, kiyi hak’uri, na fara tsorone kada ko kishi ya saka kin fara canja halaye, ina tsoran halin Matan yanzu”
   “Duk k’ok’arin da nake akan matarka anma abunda zakamun kenan don yanzu ka samu ɗa? Ni kake zargi Shaheed? Ni….?” ta kasa magana ma saboda kuka,
    “ba haka bane Maryam kiyi hak’uri don Allah” tashi tayi ta ruga da gudu ɗakinta, dak’yar take gudunma saboda kib’a, yabi bayanta, Majeeda ta samu wuri ta zauna duk taa damu itama,
    Sun daɗe yana rarrashinta kafin su fito, tana dariya kamar ba itace ta gama kuka ba,
   “Tohh Majeeda a dawo lafiya”
   “Ameen Auntie, ban gajia kullum da gode miki, inama kowacce mace addu’ar samun kishiya kamarki, kici gaba da hak’uri damu plz”
    “ba komi Majeeda, anma zai addu’arnan taki….,ba kowacce mace keson kishiya ba”
  “indai irinki ce Auntie kowah ma zai so” murmushi Maryam tayi ita kaɗai tasan fassaranshi,
    “Tohh shknan saikun dawo, Allah ya baki lafiya”
   “Ameen”
  Sannan ta koma ciki, su kuma suka tafi asibiti,
    Tsadajjen Asibiti sukaje, ba ɓata lokaci sukaga likita, aka mata scanning da duk sauran abubuwa, likita ya tabbatar musu da babu wani abun daya samu cikinta, anma tana k’ara samun hutu sosae, (bed rest) saboda jinin data zubar, sunyi farin ciki sosae, ba kamar Shaheed saida yayi sujjadar godiya ga ubangiji, lallai Addu’ah bata faɗuwa k’asa banza,
    Sun fito tare suna tafiya taji yaro ya rirrik’e mata k’afafuwa,
    “Mamanah” muryar Abdallah taji da mamakinta, ta  juya shiɗin dai ne, ta ɗagoshi dak’yar zata ɗauka, Shaheed ya ansheshi,
   “Yanzunnan fa likita yace ki daina ɗaukar Abu mai nauyi”
     “Uncle”Abdallah ya faɗa, Shaheed ya harareshi da wasa,
   “bana hana Uncle ɗinnan ba” Abdallah yayi dariya,
   “Na daina Daddyna” Majeeda dai kallonshi kawai take baki buɗe,
     “kai dawa kukazo Asibiti?”
  “Nida Umma ne, ni kuma na fito” Majeeda ta kamo kunnenshi zata murɗe,
   “Yanzu yawonnan bazaka daina ba Abdallah?”
   “in zaki mishi faɗa kuma sai kinji mar ciwo? Zo muje kaji Abdallah Umma na can na nemanka” ya juya sukai gaba ta bishi a baya, duk nisan da yayi kau tsaf ya gane inda ya baro Umma, suka shiga batasan ma bainan ba,
   Suka gaisa da Umma, ashe Aisha ce batajin daɗi,
    “Umma Ashe Aisha bata lafiya kuma banji ba”
     “jikinne nata kullum ba daɗi Majeeda, Shiyasa ma bama faɗa”
   “Allah sarki, meke damunta”
  “har yau dai basu faɗa mana ba, anma jikin nata da sauk’i ma” 
     “Allah ya k’aro sauk’i Umma” ta k’ara kallonta, barcinta takesha, ita har manta kamanninta ma take, rabon data ganta tun tana gidan Majeed, hannunta ta duba,
    “Aikam na baro jikkata inda na zauna” Shaheed da keta shan surutu wurin Abdallah yace “bara in ɗauko miki tohh”
    “A’ah yi zamanka bara inje” ta fice da sauri tana tunano inda take ganin ta barota, cikin sa’a ta ganta, tana ɗauka ta juya zata tafi, ta jiyo maganarshi a kunnanta, bazata taɓa mantawa da muryarba, bazata taɓa manta yanayin da takeji idanta saurari muryar ba, shiru tayi ta kasa motsawa daga inda take, ko kallanshi ma batayi ba, wani irin yanayi da bazata iya fassarawa ba ta shiga, ganin haka ya canja akalar zancen,
      “ke haryau baki iya gaisuwa bane?” murmushi tayi jin ya tuno da lokacin da suke faɗa, kafin aurensu kenan,
   “Ayni banga Abinda zan gaisar ba anan”
       “lallaima yarinyar nan, yauma rashin kunyar zakimun?”
   “babu yarinya anan” ta bashi amsa,
   “idan nazo na murɗe wannan masifaffen bakin naki kinmu bayani”
   “Zan zauna ne ka murɗemun baki? Kaima kasan ba tsoranka….” sai kuma tayi shiru tana k’ok’arin maida hawayenta, su duka suka yi daria,
     “Gaskiya da munyi yarinta”  ta faɗa tana juyowa, shima dariyar yake, sai kuma yayi shiru, shima da damuwa a fuskarshi
    “lokacin da muka fara gane gaskiya kuma k’addara tayi halinta” sai yanzu ta ɗago suka haɗa ido, tun bayan rabuwarsu bata k’ara ganinshi ba, shekara kusan Uku, yayi fari ya k’ara kyau sosae, sai dai rama da yayi da alaman bai cikin kwanciyar hankali,
   “Yaya Majeed dukka rame” ita kanta batasan sanda ta faɗa ba,
   “kekam Matatah na kwance Asibiti, kullum ciwo, idan ban rame ba ya za’a gane nine mijin?” ya faɗa da zolaya, sosae ya bata daria,
    “Allah ya bata lafiya”
  “Ameen, kwana da yawa, faɗamun ya rayuwanki?”
 “ba daɗi, tun bayan rabuwar mu, Munyi aure da shaheed, matsalan dangin miji, ga kishiya kullum saita zaneni, miji babu ruwanshi dani, babu ci babu sha, babu wanda zan faɗama matsalana, kaifa?” yaɗan murmusa, irin yanda yake idan taa gama burgeshi,
   “Munyi aure da Aisha, Masifa harta linka taki, safe daban rana daban, ba ruwanta damun girki, kullum tayi ficewarta bata tambayata, ta rainani batajin magana ta kuma…” yayi shiru yana tunani, suka k’arayin daria a tare,
   “ina cikin farin ciki yaya Majeed, bani da matsala da kowah”
   “nima haka Majeeda, Aisha macece ta gari, banda damuwa yanzu saita ciwonta kawai, sai muna tunanin taji sauk’i kuma abun ya dawo”
    “Insha Allahu zata samu lafia”
    “Ameen fa”
   “Yanzu dai mu manta da rayuwarmu ta baya, ko babu komai mu en uwanah ne, kina kallona a matsayin yayanki, komai ya wuce”
   “komai yaa wuce fa,” ta faɗa tana share hawayenta cikin dubara, “bara inje yanzu zamu tafi”
     Ta juya ta tafi, shima bai iya ce mata komi ba, soyayyar gaskiya kenan, kowannensu k’ok’arin ɓoye damuwarshi yake da murmushi, anma a zuciyoyinsu sunajin ciwo sosae,
  Tana zuwa sallama sukayi da Umma, bayan ta k’ara duba Aisha, sosae ta bata tausayi,
Lokacinda Maryam ta fahimci cikin Majeeda nanan bai fita ba, ba k’aramin kad’uwa tayi ba, ba shiri ta nemo Asiyah har ita suka koma wurin Malam, sai dai sunyi rashin sa’a ya tabbatar musu babu makawa sai an haife cikin, sai dai daga baya zaisan yanda yayi da yaron harma ita Majeedar tabar gidan,
   Bayan wata biyar Majeeda ta haifo santaleliyar yarinyarta Mace, ko ban fad’a ba kunsan ba k’aramin farin ciki iyalannan sukayi ba, har Maryam taji dad’in zuwan yarinyar, tun haihuwarta ita take hidima da ita, wani irin soyayyarta take ji,
    Ranar suna yarinya taci suna Maryam, shawarar Majeeda kenan, ta dage sai anyima Maryam takwara, ansha shagali sosae, tun ranar haihuwarta har washe garin suna, babu wanda bai shaida da haihuwar Maryam ba, harta da Aisha matar Majeed kullum tana gidan, don yanzu sun zama kamar en uwah,
   Kullum Maryam k’arama tana wurin Maryam, tsakaninta da Mamanta sai in tana rigimar yunwa, Shaheed ma acan ya tare b’angarenta wurin d’iyarshi, ita dai Majeeda ta zama er kallo,
    Tun tana da shekara guda suka yayeta, sai dai madara, ganin haka Maryam ta koma wurin Malam, da maganarsu ta baya kar Majeeda ta samu wuri tayita haifa ma Shaheed yara, ita kuma ta zama hoto, shima  abu ya bada da zata zuba mishi a abinsha, tace “shi yafi komai sauk’i malam” sannan tayi godia ta tafi,
    Majeeda na kwance, Shaheed ya shigo d’akin da Marece ne, tayi mamaki sosae don da wuya ya shigo idan ba dare ne ba,
    “Sannu da dawowa” baice komai ba yaci gaba da k’are ma d’akin kallo, duk da daman yanzu yaa daina kulata, sannan ya zura hannu Aljihu ya ciro takarda, ta kalleshi da mamaki,
   “takardar miye?” cikin yanayin da bai tab’a mata magana ba yace “in faɗa miki da baki mana, idan ni yaronki ne, Ansa ki duba” jikinta ba k’wari ta mik’a hannu ta amsa ta buɗa, Saki Uku ne reras, tana ganin haka ta kulle takardar idanunta cike da hawaye, ita kuma k’addarar da Allah ya ɗaura mata kenan,
      “Mena maka shaheed?”
   “kawai na gaji da zama dake, babu laifin da kikamun, ki tattara kawai ki tafi, sannan kuma karma ki sakaran tafiya da Maryam, tuntuni na barma Maryam ita” wani irin takaicine ya taso ma zuciyarta, wani irin kallon tsana take mishi,
     “Sai yanzu ne na fahimceka, lallai yau na yarda ka cika namiji, watau aurena kayi in haifa maka ɗiya ka cimun mutunci? Lallai idan ance maza DUK HAKA SUKE (littafina mai zuwa), bazanyi gardama ba, saika zauna dasu halayensu da baka taɓa tunani ba zasuna bayyana, ka  rusa duk wata yardar dana maka Shaheed, kaci amanatah, bazan taɓa yafe ma cutar dani da kayi ba, kuma Maryam nina haifeta babu inda zan tafi in barta”
    “Da ita kikazo? Zaifi miki ma daki manta da ita, don keda ita har abada, kuma kici gaba da zama har in dawo in sameki” ya fita fuuu yabar ɗakin, anan ta zube k’asa tasha kuka sosae kamar ranta zai fita, da kanta kuma ta rarrashi zuciyarta tayi shiru, jikkarta kawai ta ɗauka tabar gidan,
     Mai napep ya ajeta k’ofar gidansu, ta fito dak’yar take haɗa hanya ta shiga gida,
   Momie da Umma ne a ɗakin tazo gidan, Abdallah ma ya koma gidan babanshi a can ya sakashi makaranta, dak’yar har tana ganin jiri ta faɗa falon, wurin zama a kujera harta kusa faɗuwa, ta jinginar da kanta kawai tana dafe kanta dake mata ciwo sosae, duk suka taso sukayo inda take,
    Kasa basu amsoshin tambayoyinsu tayi, sai dai ta mik’a musu takardar dake hannunta, duk tare suka saki salati, sunyi matuk’ar tausaya mata, Umma kamar karta bar gidan don tausayin Majeeda, babu wanda zaiga halin da take ciki bai tausaya mata ba,
A gurguje dai….
Bayan shekara Uku…
Majeeda ta kwantar da hankalinta, Yanzu ta zama lecturer a makarantar Umyu katsina, tsakaninta da Majeed sai dai mutunci kawai na en uwah, gida ma ganin halin da take ciki ya saka ko maganar aure basu mata, kullum dai suka mata Addu’ar zaɓi mafi Alkhairi,
    Aisha ne da Majeed kwance ya juya mata baya, ba barci yake ba, anma kuma yayi shiru kamar mai barcin,
    “Kayi shiru hniee inata magana ni kaɗai, kuma nasan ba barci kake ba” shirun ya k’ara mata,
    “kana jina fa” baice komi ba, ta kamo k’afarshi ta fara mishi susar k’adangaruwa,ba shiri ya fara dariya, ya kamota ya rungume, tureshi tayi suka fuskanci juna,
    “Wai hniee Meyasa kullum nake maka maganar dawo da Majeeda kake shareni? Wlhy na faɗa maka banda Matsala da hakan, kuma kunason junanku, ga Abdallah kullum k’ara girma yake, zaiso ya ganshi a tsakiyar iyayenshi”
   “ke ba mahaifiyarshi bace?”
   “Duk da haka nidai ka dawo da ita don Allah”
    Fuskarta ya jawo ya haɗa da tashi suna shak’ar numfashin juna “Hakan kikeso” ta ɗaga mishi kai,
    “Zanyi komai saboda farin cikinki, Anma nidai ki dainamun maganar zanyi tunani akan hakan”
   “naji anma baza’a ɗauka lokaci ba?” ya gyaɗa mata kai, duk wannan maganar da take k’arfin hali ne kawai, yana rungume da ita, ɗagotan da zaiyi yaga jinine ke fita ta hancinta, ta tafi luuu ta faɗa gefe, cikin tashin hankali ya rink’a jijjigata, ciwon nata nayau yafi na kullum ɗaga mishi rai, doguwar riga kawai ya ɗaura mata saman kayan barcin jikinta, ya ɗauketa a ruɗe ya saka mota, dak’yar ya iya driving zuwa asibiti,
      Har gari ya waye bata dawo hayyacinta ba, likitoci na iyakar k’ok’arinsu a kanta, en uwanta cike a asibitin, wata nurse ta lek’o tace “Waye Majeed?” da sauri ya matsa inda take yana cewa shine, yabi bayanta suka shiga Maryam na kwance ta farka, idanunya tsaye kanshi tana murmushi, ta mik’a mishi hannunta ya rik’e yana hawaye, ta ɗan ɓata rai da wasa,
    “Miye na kuka kuma hniee? Ka kwantar da hankalinka kaci gaba damun addu’a kamar yanda ka saba, wlhy koda mutuwa nayi ina cikin farin ciki sosae, burinah ya cika, na rayu na wani lokaci kuma zan mutu a matsayin matarka, kada ka manta da maganar da mukayi jiya da dare, kada ka manta dani Majeed” k’ara rirrik’e hannunta yayi,
    “bazaki barni ba Aisha, zamu rayu a tare insha Allah”
   Girgiza kai tayi “ban taɓajin ciwon da nakeji ba a yau, ni nasan wannan ciwon shine ajali na” ta k’ara lumshe ido dak’yar take magana, tashi yayi yana k’wala ma likita kira,  tak’i sakin hannunshi, ya juyo yana kallonta, murmushi ta k’ara mishi,
    “kada ka manta da alk’awarinmu na dawo da Majeeda” sannan ta sakeshi, ya tafi duk jikinshi yayi sanyi, suna dawowa da likita har rai yayi halinshi, anan Majeed ya faɗi sumamme, yasha jinya sosae Asibiti kafin ya ɗan samu,
Bayan shekara ɗaya,
 Da mutuwar Aisha, Abdallah yanada shekara 10, ya zama ɗan saurayi, Maryam nada shekara 4, Majeeda ta zama babbar mace, ‘yar gayu da ita, kullum k’ara kyau take, idan ka ganta bazaka ce tayi shekarunta ba, har Gida Maryam ɗin Shaheed tazo neman yafiyarta, Shaheed ma har kuka yayi na zafin rabuwa da ita, bata rik’esu da komai ba ta yafe musu, sannan ta barma Maryam, Maryam k’arama don har lokacin Allah bai bata haihuwa ba,
   Majeeda ce tafe cikin Mota, tana tuk’i cikin natsuwa, duk da saurin da take zuwa gidansu Umman shaheed saboda kiran gaggawar da aka mata, mintoci kaɗan ta isa gidan, mai gadi ya wangale mata gate ta shiga, daga makaranta take duk ta shawo gajia, kai tsaye falon bak’i ta wuce,
   Kamar yanda suka saba idan zasuyi meeting, kowa ya hallara, zahra ce kawai babu, ta gaishesu sannan ta samu wuri ta zauna, kallo ɗaya data ma Majeed ta k’ara hango ramar da yayi sosae,
   Bayan ta samu wuri taa zauna, Abban Majeed yayi gyaran murya ya fara Magana,
      “Wannan karon ba Umarni bane muke baku, shawara ce muka yanke kuma duk saida amincewarku, abinda ya faru mu ɗauka k’addara ne, yanzu kuma dama ce garemu, mu cika Alk’awarin da mukai ma mahaifinmu, muna fatan wannan karan bazaku bamu kunya ba”
   Momie ce ta nisa, tun kafin kowah ya fara magana “Gaskia ni ban yarda da wannan hukuncin ba” su duka suka juyo suna kallonta, taci gaba da magana cikin fahimta,
      “Su duka yanzu ba k’ananun yara bane, kun manta abunda wancan haɗin ya haifar? Shiyasa ni ban cika magana ba, anma gaskia wannan lokacin bazan yarda a k’ara musu dole ba,  su koma halin da suka shiga wancan lokacin ba” Daddy ya katseta
    “Waye yace dole za’a musu? Suna da damar da zasu faɗi ra’ayoyinsu, karki manta da Alk’awari ne muka ma Mahaifinmu, ba don haka ba koda kansu suke so bazamu taɓa k’ara amincewa ba, kuma yanzunma idan har basu so bazamu k’ara tilasta su ba” shiru tayi bata k’ara magana ba,
   Abbah yace “ku muke saurare”, Majeeda kanta a k’asa tun tana kuka a hankali harta fara shesshek’a, Majeed ma sai dai tashi yayi ya fita, fuskokin iyayen nasu duk ta nuna rashin jin daɗi, sunyi jugum kowa ya kasa motsawa, message ya shigo wayar Aunty zainabu, ta ciro ta tana ganin daga Majeed ne ta buɗe da sauri, da k’arfi ta karanta yanda kowah zaiji,
    “Ki tayani godia Auntynmu, kunyarsu ta hanani furta komai, sun nuna mana soyayyar da babu abinda zamu biyasu da ita, Allah ya saka musu da mafificin Alkhairi, ya k’ara musu tsawon kwana” kowa a ɗakin saida ya murmusa, sunyi farin ciki sosae, Majeeda ma murmushin jin daɗi take, ta mik’e da gudu ta fita, kunya bata barta ta jira kowah ba, ta shige motarta ta wuce gida,
   Cikin lokaci kaɗan aka fara hidimar biki, shagali sosae akayi wanda ko bikinsu na farko ba’ayi ba, cikin sati biyu aka gama komai aka kai Amarya ɗakinta,
   Bayan en rakiyarta sun gama tafiya, ta shek’a wankanta, tayi kwalliya ta fitar hankali, ko ina jikinta k’anshi yake, ga wata doguwar riga data saka ta daifi babu, irin shigarda tasan Majeed yafiso, sai dai ta ɗaura zani daga sama,
     Yana shigowa tsaye yayi a k’ofa yana kallonta, duk’arda kanta tayi sannan wata irin kunya ta saukar mata, ya ware mata hannuwa alaman tazo ya rungumeta, cikin zolaya tace “yau kuma ina laidan da za’a jefeni da ita?” daria yayi,
    “rufamun asiri zaki jamun ɗauri,” itama tayi dariya,
   “nayi alwala fa, kai kawai nake jira”
    “tohm ranki shi daɗe”
  Ya shiga yayo alwala, ya fito, Sallah sukayi raka’a biyu kamar yanda manzon Allah ya koyar damu, ya daɗe yana kwararo musu addu’ar zaman lafiya, sannan sukai godia ga ubangiji,
    Ya rausayar da kanshi yana kallonta, rayuwarsu ta bayace ta dinga dawo mishi, wata irin soyayyarta na k’ara ratsashi, itama kamar hakan takeji, ta hure mishi idanu,
    “ka faɗa mana”
  “na rasa mezan faɗa ne, kullum k’ara kyau kike, bazaki taɓa tsufa ba”
   “kaima hakanne, babu wanda zaice kana da kaman Abdallah”
   “bazan iya bayyana miki farin cikin da nakeji ba da dawowarki gareni, wallahi ban taɓa sanin ina sonki da yawa haka ba saida na rasa ki, HARAMTACCEN ZAMA, ya k’are, Allah ya bamu ikon farantama juna har k’arshen rayuwarmu”
     “Ameen” ta faɗa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *