WANNAN RAYUWAR CHAPTER 6
“ina dashi amma……”
“amma mei? bakada hujja har awajen Allah ka gwamace kayi ta sabon Allah, Isma’il ba kasan mata nawa ka lalata ba, kasan mata nawa ka budawa ido suke aikata zina, ko kasan girman zunubin da kake aikatawa kuwa, inkasan kana da sha,awa kayi aure mana, amman bazakayi ba ka gwamace kai ta lalata, ya’yan mutane, Shin ka manta duk abinda kayi sai an maka kana da kanne zakai aure za kuma ka haife shin in su akai wa haka zakaji dadi.”
Kai ya girgiza yana jin abokin nasa. Kabir yace
“A gaskiya Isma’il abokanta ta da kai tazo karshe dan ba zan zauna da mutumin da ba zan fada masa yaji ba. Kuma kowa yasan ka nima da halin ka za ana kallo na dan haka ba zan iya cigaba da abokanta da kai ba.”
“Haba friend u know dat I can’t leave without u!”
“In har kuwa haka ne sai dai in zaka bu sharadi na if not wallahi Allah Isma’il bani na kai”
“Menene sharadin?”
Isma’il ya tambaya.
“In har kana San in cigaba da abota dakai, u have to make a promise to me, zaka auri Halima, now tunda kai kafara sanin ta ya mace.”
“But her father will not get her marriage now!”
“I know but it’s a promise duk lokacin da Baban ya yadda zaka aure ta.”
“Naji kayi hakuri ka yafen!”
“Ba kai min laifi ba friend. Allah zaka nemi yafiyar sa da Halima”
Kai ya gyada.
Wayar sa Kabir ya ja yana dane danne. Isma’il yace
“Ya naga kana hade rai to.”
“Kar na hade? Isma’il baka taba batan rai kamar yau ba.”
“Haba friend ba mun aje matter ba.”
Kafada ya dage kawai. Nan Isma’il ya dinga jan sa da hira ammn sam ya kasa sakewa dan zuciyar sa a kuntace take ga zafi ga kishi ga tausayin Halima.
***** **** *****
Halima kuwa sai da aka kira magariba ta tashi da wani ciwon kai wannan yasa ta mike a daddaf ta shiga tai wanka ta dauro alwala ta tada sallah. Tana idar wa taji vibration din wayar ta janyowa tayi tana ganin Isma’il ke kira taki dagawa. Da ta tsinke ma taga misaed call nasa yayi twenty, tsaki ta saki tana shirn ajiye wayar ya kara kira kin dagawa tayi da taga zai dameta ta kashe wayar gaba daya dan wani irin haushinsa takeji.
********************************************************************************************************************************************************
Muhammad kuwa yana yawan kiran Abba su gaisa dashi dan so yake ya amshi Number Ummu amman yana jin nauyin tambayar Abba. Wata rana da sukai waya da Abba bayan sun gaisa yake cewa
“Abba ya mutan Abuja?”
Abba yace
“Suna lafiya ai Ummun ma bata dade da zuwa ba ta koma ma.”
“Allah sarki!”
Can zasuyi sallama yace
“Abba ina bukatar Number wayar Yaa Suleiman!”
Nan Abba ya tura masa.
A haka ya fara jin soyayyar Ummu bama in ya zauna yana tunanin abubuwan da Ummu tai masa wanda yake kara jin son ta. Ta tausaya masa a rayuwa ta kaunace sa shi da iyayen sa to shikan me zai yi in ba ya saka mata da soyayyar sa ba. Ga alherin mahaifin ta da mahaifiyar sa agareshi. Tabbas Ummu ta cancanci ya so ta fiye da komai.
STORY CONTINUES BELOW

In yana tuna surar ta kuwa sai yaga Ummu bata da aibu sam dan a kyau kamar larabawa take. Ba ta da kiba tsayin ta dai dai gwargwado fara ce tas mai idanu da hanci mai fara’a ko da yaushe Gata a cike take daga saman ta har kasan ta. Ga kunya da tabiyya bata taba iya kallon mutum sai dai kullum kan ta akasa. Tabbas Ummu ta cancanci a so ta dan duk wanda ya samu Ummu kuma yasan ya gama dacewa.
Yakan kira Yaa Suleiman su sha hira abinsu dan sun saba sosai lokacin da Yaa Suleiman yaje umrah ma sun hadu. Yana son yai waya da Ummu amman bai da number ta kuma ya kasa cewa a turo masa. Sai dai in sunyi waya da Yaa Suleiman yace Yanzu Amaryar ka ta shiga daki ko ta tafi makaranta haka dai.
Shekarar sa daya acan amman ya zama wani babban Alhaji yayi kiba yai kyau dan yana cikin jin dadi. Ba tare da sanin kowa ba yasa aka siya masa fili anan kano aka soma gina masa.
A lokacin da ya gama karatun sa kuwa rike shi sukai dan yai musu aiki wmd ya samu alherai masu yawan gaske a zaman da zai yi dan ya sa a gyara gidan su kuma ba abinda bayawa Hajya kullum cikin sa masa albarka take ga business dinsa da suke shi da kanin sa.
Yana zaune ya fara kiran layin Yaya Suleiman yana dauka yace
“Ina yini Yaa Suleiman?!
“Lafiya lou kanina ya aiki da karatu?”
“Alhamdulillah Yaa Suleiman. Yasu Anty da Ummu?”
Dai dai shigowar Ummu kenan ta dawo daga makaranta da shigar ta dai dogiwar riga ce sai hijab da Nikaf da ta daura. Kallon ta Yaa Suleiman yayi yace
“Ka ganta yanzu ta dawo daga makaranta. Bari na bata ku gaisa.”
Mika mata wayar yayi yana fadin
“Angon ki ne.”
Fuska ta rufe da hannun ta tayi ciki da sauri dan kunyar Yayan nata take. Sai da ta shiga dakin ta ta tuna da wayar ma nayi wannan yasa ta kallo screem din ai kuwa bai kashe ba dan haka ta kara a kunnen ta cikin jin nauyi tayi sallama da muryar ta mai dadin da sanyi
“Assalamu Alaikum!”
Muhammad dake can sai da ya lumshe ido dan yadda muryar tadake shi har ta saikar masa da kasala. Yace
“Wa’alaikum salam Ummu ya kike ya gd da karatu?”
“Alhamdulillah! Ya karatu?”
Ta fada cikin jin kunya.
Yace
“Karatu Alhamdulillah!”
“Allah taimaka!!
“Amin!”
Sai sukai shiru kowa ya rasa abinda zai fadi. Can yace
“Karanto min number ki.”
Nan ta karanto masa yace
“To sai anjima!”
Sukai sallama. Yana jin wata nishadi da farin ciki a tare dashi.
Mikewa tayi ta bawa dan Anty Zainab ta shiga tai wanka ta canja kaya ta tafi dining dan taci abinci. Bayan ta gama ta nufi falo inda kowa ke zaune.
Yaa Suleiman ne ya kalli Ummu yace
“Kun gama soyayyat!”
“Kai Yaya gaisawa fa kawai mukai!!
Dariya yayi yace
“Kinga tsaya in fada miki kar ki tsaya sanya da Muhammad ko jin kunya kice mijin yar kine a dane wannan amman yanzu naki ne ke zaki koya masa son ki dan haka ki kula kiyi wa iyayen mu dashi biyayya zaki ga ribar biyayyar.”
“Insha Allahu Yaya!!
“Yauwa. Nasan yanzu baifi wata shida ya dawo ba kema kuma karatun ki saura four month kinga da ya dawo sai ki tare kuje kusha soyayyarku ko?”
Fuska ta rufe a bayan Anty Zainab tace
“Kai Yaya!”
Dariya yayi ya mike yana fadin
“Bari naje na dawo!”
Suka hada baki suna fadin
“A dawo lafiya!”
Ya amsa da Amin ya fice. Zaman gidan su Anty Zainab zama ne na fahimtar juna da shakuwa da wasa da dariya ba ruwan Yaa Suleiman ki
Kowa jan sa yake har ya’yan sa bai kyale ba.
STORY CONTINUES BELOW

Duk da yai arziki ba ruwan sa yadda yake a da haka yake a yanzu bai wa matar sa katamga ga komai nasa. Haka Ummu sai abinda take so ga yadda yake wa Abba duk wata ya aika masa da kayan abinci da kudi tin Abba na fada har ya daina sai saka albarka.
Rukkayya kuwa zawarcin ta take ci da tsinke tayi kyau tayi kiba ta kara haske bata da damuwar komai sai jin dadi samari kala.kala.na zuwa wajen ta amman a ciki Alhaji Kasim yafi kashe mata kudi dan duk wata akwai percentage din ta banda in yazo ya kawo mata kaya lesses kaya kudi haka in yai tafiya. Kai sai abinda take so.
Duk da bata son gidan kishiyoyi amman Anty Sailuba da Mama kullim cikin zuga ta suke suna fadin
“Tin da yana son ki ai sai abinda kika ce baki ga yayar ki bane ita kece tana da kishiyoyin.”
Wannan yasa ta fara sauraron sa har yake kawo mata maganar auren ta tinda a lokacin Haule ta rasu.
*********************************************************************************************************************************
Kwance take tana bacci dan ranar littinin ne azumi take wajen karfe biyar da rabi sai ga kanwar ta nan ta fado cikin dakin tana fadin
“Anty Fauziyya kizo inji wani a waje!”
Mikewa Fauziyya tayi tana mutsuka ido tace
“Je kice wane?”
Da gudu ta fita kan wasu mintina ta dawo tace
“Wai yace Muhammad!”
Sunan ta nanata sannan tace
“Je kice gani nan.”
Ta mike ta shiga bayi ta wanke fuskar ta ta fito ta saka hijab din ta Ash kala wanda ya kara mata kyau kamar wacce tai kwalliya.
Yana tsaye a soron gidan sanye da Ash kalar yadi sai hula da da takalmi duk bakake da agogon sa shima baki. Yai kyau ko da yake daman me kyau ne. sai tashin kamshi yake.
Tana ganin sa taji wani sanyi da nutsuwa a hankali ta karasa soron sannan ta dan duka tace
“Ina yini?”
Sam bai ji gaisuwar ba dan tin da ta fito ya nemi nutsuwar sa ya rasa. Shi dai Allah ya jarabce shi da son Fauziyya. Dagowa tayi tana kallon sa ta daga masa kai alamar
“Lafiya!”
Murmushi ta saki kawai yana mai dauke kai yace
“Ya kike? Yau naganki so weak me yake faruwa?”
“Ba komai!”
“No ki fada min gaskiya baki da lafiya ne ko wani abu na damun ki?”
Kai ta girgiza yace
“To meyasa?”
Shiru tayi yace
“Please Fauziyya ki dauken a matsayin dan uwa ba wanda ke son ki ko neman auren ki ba.”
“Bacci nake!”
“Baccin la’asar ko dai baki da lafiya ne?”
Ya tambaye ta dan yaganta duk ba karfi. Kai ta girgiza tace
“Azumi nake!”
Murmushi yayi yace
“Kar dai raguwa zan aura ace just azumi ya sa kinyi sanyi haka. Anya zaki iya daukar bukatata!”
Dagowa tayi tana kallon sa sai ya ce
“Ni kinga nayi kalar masu azumin ne?”
Sam bai ba dan da kwarin sa da karfin sa har yafi lokutan da take ganin sa. Ka ta girgiza yace
“Nima azumin nake amman kinganni ba wata gajiya bare sanyin jiki. Kema ki zama jaruma kamata kinji.”
Murmsuhi tayi. Shima murmushin yayi yace
“Ya gidan to?”
“Lafiya!”
Kai ya gyada yace
“Ya batun soyayya ta.”
Kai tayi kasa dashi. Yace
“Kunya ta kike ji!”
Shiru tayi yace
“Ina mai fatan da ki amshi soyayya ta.”
Dagowa tayi tana fadin
“Muhammad ba soyayyar ka naki amsa ba sai ganin da nayi nida kai sam bamu dace da juna ba. Kai kamili ne ni kuma ba…..”
“Ya isa Fauziyya!”
ya dago yana kallon ta sannan yace
“Bana ce miki ki daina kawon wannan maganar ba. Ni naji na gani ina son ki a haka!”
Dagowa tayi tana kallon sa. Kai ya gyada mata yace
“Ina son ki da zuciya ta ba wasa kuma.”
“Amman yana da kyau kasan ko ni wacece!”
Murmushi yayi yace
“Nasan ko ke wacece amman ina sauraron ki.”
Shiru tayi tana wasa da yatsun ta zara zara wanda Muhammad ya kurawa ido yana kallon su sun burge shi. Wai shin komai na Fauziya mai kyau ne?
“Da farko nasan kasan sunana Fauziyya Kasim. Mahaifi na dan kasuwa ne yana da rufin asiri. Tin da na tashi mata hudu nake gani a cikin gidan mu dan da daya ta fita wata za a maye da ita. Duk da nice ‘ya ta uku amman ina da kanne sun fi ashirin wanda da yawa iyayen su basa gidan. Sam mahaifina baya sauke hakkun iyalan sa wannan ya janyo iyayen mu mata suka fara neman hanyar da zasu ciyar damu. Munyi makarantar allo da isilamiyya har sauka munyi haka boko da kyar mukai gradution duk da mun fito da sakamako mai kyau amman mahaifin mu yace hai da kudin da zai samu a makaranta. Haka muka cigaba da zaman gida. Lokacin da samari suka fito in sunje gun mahaifin mu sai yace nawa muke ai ba mu isa aure ba. A lokacin fa na kai shekara sha takwas kuma nayi graduation to me zan yi zaman gidan tinda ba karatu zanci gaba in ba aure ba amman sam Baba yace bamu isa aure ba.
A garin jajibe jajiben iyayen mu Maman mu ta hadu da wata kawa wacce ita ta bata shawarar ta kai mu mu samo mata kudi. Wata rana Maman mu ta debe mu ta kai mu gun kawar tata a lokacin ne aka kai ni gun Kamal.”
Kuka ta fashe da shi. Matsowa Muhammad yayi ya mika mata handkerchief yana mai fadin
“Kiyi hakuri ki daina kukan nan yana taba zuciya ta.”
Dagowa tayi tana kallon sa. Shima kamar zai kukan kan ta tai kasa dashi ta daura da yadda Kamal ya raba ta da mutuncin ta (ku tina a page 09) tana fadar inda Kamal ya raba ta da mutuncin ta sai ta kara sakin wani kukan mai zafi da taba zuciya. Shi kansa Muhammad dauriyya yake amman idon sa yai jajir dashi dan baccin rai da bakin ciki.
“A lokacin da ya dawo dani gida da kudade da kayayaki na dau alkawarin ba zan sake ba na tuba duk da ba a cikin hayyaci na na aika ta ba. Amman wani abun mamakin bayan kwana biyu na tashi da wata matsananciyar sha’awa wacce ashe Farisa ita ta saka min kwaya wannan yasa ta kaini gun Kamal tin lokacin take mun haka tin bana jin dadin rayuwar har na fara jin dadin ta duk da ban da wani kwanciyyar hankali kullum ina mai kai kuka na ga Allah.
Haka na dinga rayuwar bariki dan har nema na ake ban san dalili ba amman maza na fadin ina da wani sirri na daban dan dayawan su sun so su aure ni.
Lokacin da ka farai min magana a ranar na bar kasar nan nabi Kamal wata uwa duniya mun sha soyayya ni da kamal ranar da na dawo shine ka kara biyo ni ida akan kana so na.”
Ta dago ta kalle shi hawaye na kara zuba a idanun ta. Hannu ya saka yana goge mata hawayen yana girgiza kai alamar ta daina kuka. Dauke idon ta tayi daga kallon sa tace,
“Ranar nayi nadamar fadawa ta karuwanci dan daga ranar na kamu da son ka. Nayi kuka kamar zan mutu saboda kazo a okacin da ban dace da kai ba ina ma a lokacin baya ne lokacin da ban da wata kazanta.”
Nunfashi ta ja tana mai sauke ajiyar zuciya saboda kukan da take sha sannan tace
“Washe gari da ciwon kai na tashi inda Kamal ya ce naje ya kaini asibiti duk da yana tunanin kewar sa ta sani ciwo na fito zani na haduda wanna almajirar wacce ta ce tana son gani na wannan yasa nace gani a ranar ta bani tarihin rayuwar ta wanda ta fada a da. Lanarin da ya taba ni ya taba rayuwa ta na baro gidan ta ina kuka ina neman gafarar Allah akan yayafe mun kar na mutu a wannan halin.”
Muhammad ta kalla idon ta na zubar da hawaye.
Muhammad ta kalla tace
“Tin lokacin na cire rai da rayuwa na tuba nai nadama na koma ga Allah. Wannan dalilin yasa ko ka aiko naje bana fitowa dan ciwo nayi sosai naki naje asibiti ne na kwamace Allah ya cigaba da azabtar dani. Muhammad na fitar da rai da zan aure ko zan auren nasan ba zan samu kima da daraja agun wanda zan aura ba.
Farisa taki ta shiryi sam Hafsa ma sanadin mutuwar Anty Haule ta tuba.
Hakika rayuwar dana zab’arwa kaina ba rayuwa ce ta abun tutiya da tak’ama ba. Rayuwa ce tamkar ta dabbobi, inda mutum yake da damar yin kowane kalar sab’o ba tare da tunanin makomarmu ba. Na tafka kuskure a rayuwata Muhammad. “+
Ta karashe tana mai sakin wani kukan. Muhammad baisan sadda ya janyo hannunta ba ya sanya cikin nashi, a lokacin hawayensa sun kasa tsayawa sai zuba sukeyi. Yana son cewa wani abu sai kuma ya fasa gami da sakin hannunta ya janyo handkerchief data rike ta kasa goge hawayen dashi ya mka mata.
“Kiyi hakuri.”
Ya fada murya a dusashe.
Ta dago kwayar idanunta tana dubansa, yayi amfani da wannan damar ganin bata da niyyar karb’ar handkerchief din ya kai hannu zai share mata fuska,ta rike hannun tana girgiza masa kai kafin ta mayar mishi da hannun kasa. Dariyar bakin ciki ta saki tana mai kauda kanta
“Kada ka wahalar da kanka ga fidda hawayen da bazasu taba daina zuba ba a rayuwata Muhammad. Banajin zan daina zubar hawaye. Banajin ina da sauran dama na jin dadi a rayuwata. Don haka kabar sharemin abokan rayuwata, na tabbata su kadai sukafi kusanci dani, banason suma a rabani dasu. In nai kukan ina jin sauki a rai na bani da wanda zan kaiwa kuka na ya lallashe sai Hafsa wacce itama kanwa ce ya kamata na rarrashe ta itama.”
Fauziyya ta fadi cikin sheshek’a kuka. Ya sunkuyo yana duban fuskarta sannan yace
“Nayi maki alkawarin idan har ina raye Bazan barki ba Fauziyya. Daga yau inaso ki bani damar kasancewa mai share maki su, idan ina raye Ni Muhammad bazan k’ara barinki kiyi rayuwa makamanciyyar wannan ba zan baki gata da baki taba samun irin…….”
Sai kuma yai shiru yana kallonta itama shin take kalla. Kai ta dauke yace
“Kin tafka kura kurai da yawa a rayuwarki Fauziyya ciki kuwa babban shine cigaba da rayuwar bariki maimakon ki kame kanki da mutuncinki, a’a saima zuciya data kwasheki kika maida kanki karuwar gaske. Kinyi ganganci kin manta da dokokin addininki daya hanemu aikata zina. Ki godewa Allah ma a gefe kina da iyayenki da yan uwa, wasu fa basu da ko daya, wasu rayuwarsu har su mutu cikin kunci da bakin ciki sukayin ta amma basu fada karuwanci ba, illa sun kasance masu tawakkali da mik’a zuciyoyinsu ga Allah.”
Fauziyya babu alamar jin haushin maganar da Muhammad ya fada a fuskarta saima kallo da take binsa dashi tana murmushi kafin daga bisani hawayenta su zubo. Ganin hawayen ya sanyashi tsayawa da maganarsa
“Ina fatan ban b’ata ranki ba Fauziyya?”
Ta girgiza kai tana dan murmushi hawaye na kara zubowa a idon ta.
“Wallahi baka b’atamin ba Muhammad. Asalima burgeni kayi ,dadi nakeji a kasan zuciyata. Tunda na soma harkar barikanci, babu wanda ya taba yunkurin gayamin gaskiya sai Almajirar nan Na’ima da kai. Tun farko haduwarmu saida na fahimci kai din daban kake. Ban kara sakankancewa da lamuranka ba saida na hadu dakai a karo na biyu. Wanda anan son ka ya kara shiga ta. Tabbas Muhammad kai mutumin kirki ne wannan ne yasa nayi mamakin yanda kazo kake so na da aure”
STORY CONTINUES BELOW

Murmushi Muhammad yayi ya numfasa ya gyara tsaiwa kafin ya dubeta
“Ki amshi soyayya ta kila Allah ya amshi tuban ki ne ya aiko miki ni. Ina son ki Fauziyya.”
Murmushi ta saki tace
“Ai na fada maka tin gani na da kai na farko na fara son ka, sai jiya da ka tafi na kara tabbatarwa da kai na ina son ka. Amman…”
“Amman me?”
Ya katse ta yna kallon kwayar idon ta.
“Ina jin tsoro!”
“Tsoron me?”
“Kar a gida ace baza ka aure ni ba.”
“Sabod me to?”
“Saboda ni karu…”
“Shut off my friend.”
Ya fada a tsawace kamar zai kai mata bugi.
“Kada ki karakirankanki da wannan sunan na rokeki dan Allah.”
“Am sorry!”
Ta hade hannayen ta biyu tana langwabar da kanta.
Murmsuhi ya saki yace
“Bakya laifi ai.”
Kiran sallah magariba da yaji ana yi ne yasa yace
“Kinga ansha ruwa muna waje ko?”
“Lah eh bari a kawo maka ruwa kasha kai alwala ko?”
“Nagode!!
Tayi cikin gida ta kawo masa purewater mai sanyi da ruwan alwala. Sha yayi yai alwala sannan yace
“Bati naje masallaci zan aiko miki da abi shan ruwa sai dai kiyu hakuri ba yawa na talakawa ne.”
Murmushi tayi tace
“Ni kam ka barshi nagode!”
Tayi ciki. Da kallo ya bita yana girgiza kai. Kan ya shiga masallaci ya bawa wata mai koko da kosai kudi yace a zuna kosan dari biyu kokon dari sai shi kuma kokon hamsin kosan dari ya shiga yai sallah.
Yana fitowa ya amsa yayi gidan su Fauziyya. Tana shiga ta fasa kwai ta soya tayi sallah xata hada tea kenan aka aiko mata da sakon Muhammad amsa tayi tana girgiza kai. Maltina da ta soyo ta dauka ta saka a leda ta bawa yaron akan ya kai masa. Ya fita ta sha kokon da kosan sannan ta koma daki dan ta kwanta kan ayi kiran isha’i.
Har ya tafi yaron ya kai masa. Amsa yayi yace
“Kace mata nagode!”
Ya juya ya tafi.yana zuwa gida ya sha ruwa sannan ya fito dan yin sallah isha’i. Yana idarwa ya koma gida.
Nan Mamin sa ta kira suka sha hira duk da duk abin ta kan Fauziyya ne yana bata labarin yarinya. Take tausayi da son yarinyar ya kamata tace
“Ya kamata kaje gun mahaifin ta.”
‘Haka ne Mami nan da gobe ko jibi zani insha Allah.”
“Allah bada sa’a Amin nagode da addu’ar ki uwa ta gari.”
Murmushi taui tace
“Son kenan in ban maka addu’a ba wa zan wa. Allah maka albarka.”
“Amin”
“Me kaci da kasha ruwa?”
“Koko da kosai sai yanzu zan sha malt wacce surukar ki ta bani.”
“Iyeee a samin!”
“Kai Mami abn soyayya ne fa.”
“Iyee zakaci kaniyar ka na daina sam maka abu in Abbi ya kawo min”
“Am sorry Mami!”
“Shikenan asha lafiya sai da afe.!
“Allah bamu alheri.”
“Amin!”
Ya kashe wayar yana sakin murmushi. Ya dauki malt din ya bude ya fara sha yana lunshe ido
****************************************************************************************************************************************************************************
Washe gari tana kwance abin duniya duk ya ishe ta ta rasa me zatayi wai yau ita ce tayi zina ta rasa kimar ta da darajar ta. Hawaye ne ya zubo mata ta rasa me zatai taji dadi jin duniyar take duk tai mata zafi da kunci. Yanzu in Isma’il ya aure ta mai zata kai masa bayan ya amsa tin a waje in ta tuna haka sai ta kara fashewa da kuka tana me neman yafiyar ubangiji akan ya yafe mata ya kawo mata tallafi.
STORY CONTINUES BELOW

Wayar ta tin jiya da ya ishe ta nata kunna badan sam bata son abinda zai kara hada ta dashi a yanzu.
Hajara da ta dawo tin jiya take tambayar ta lafiya amman sai tace mata kanta ke ciwo. Yanxu ma bayan ta shirya zata fita ta shiga ta same ta a kwance idon ta a lumshe wannan yasa ta zata bacci take dan haka ta juya ta fita.
Isma’il kuwa tinda ya kira yaji bata dauka ba hankalin sa ya tashi san har ga Allah Halima ta masa matsala daya ce ya riga ya santa a waje amman da zai manage ya aure ta. Amman duk da haka bai gama shan zumar ta ba dan haka dole ya lallabata. Wannan yasa da rana ya shirya ya nufi gidan su Halima.
Parking yayi a kofar gidansu Halima direct ya fito ya tsaya a bakin kofar. Hajara da ta fito zata tafi bara kenan ta ganshi gane shida tayi dan tasan yana son yayar tata ta saki fara’a tana fadin
“Ina yini?”
“Lafiya lou Hajara. Ya gida?”
“Lafiya bari naje na kirata,”
“yauwa kice mata na Dade da zuwa inata kiran wayarta akashe,”
Juyawa tayi tai cikin gidan.
Dakin tashiga taje tasamu Halima a kwance, tace
“Anty wai ni har yanzu ciwon kan ne?”
Kai ta gyada mata kawai. Hajara yace
“Sannu ni Anty wlh dariya kike bani inkina rashin lafiya sai kiyi ta kuka kamar wata yarinya, to nasan yanzu zaki warke, ur love yazo tun dazu, yana soro wato har kin fada masa shiyasa yazo duk hankalin sa tashe ko. Kai Anty kinyi dace wallahi. Allah ya bamu I taku kuna burge ni ke da Yaa Isma’il Allah dai ya kaimu lokacin.”
Halima kuwa tana jin ance Isma’il yazo gabanta ya yanke yafadi,
“Ni nace yazo ne gashi kaina ciwo yake sis jeki ce masa banida lafiya please.”
Kallon ta Hajara ta tsaya yi dan tasan halin Halima ko bata da lafiya indai lokacin fita yayi zata fita taje su gaisa da Isma’il ko da tana ganin sa ne ta dawo amman yau ita ke cewa ace bata da lafiya. Bayan ita da kan ta tace mata ko tana ciwo in taga Ismail warkewa take.
“Kallon fa?”
Halima ta fada tana share hawayen idon ta.
Murmshi Hajara tayi tace
“Yaa Ismail zai sha shagwaba akai auren nan.”
Tsaki tayi ta koma zata kwanta. Hajara tace
“Haba Anty Amman Yaa Ismail nace miki yazo ko? ko fada kukayi ne kike boyemin Anty?”
“Fadan me zamuyi?”
Ta fada dan bata son Hajara ta gane wani abun.
“Amman Anty ke kika fada min ko baki da lafiya kika ganshi warkewa kike kuma yanzu nace yazo amman kice ace baki da lafiya.”
Sanin halin Hajara da wayo da kuma bin didigi yasa ta mike ta dauki hijabinta tasa.
Kallon ta Hajara tayi tace
“haba Anty haka zaki tafi ko hoda baki shafa ba,”
“Hodan me zan shafa ni dabani da lafiya ni ban hanya na wuce.”
Matsawa tayi tana fadin
“Toh Anty ko turare kya fesa ai.”
Tsaki ta sakin tayi waje amman sai da Hajara ta biyo ta a tsakar gida ta shafa mata turaren sannan ta koma daki ta mayar
Tana fitiwa ya bita da kallo ita kam ko kallon sa batai ba sai kasa da tayi da kan ta wani kuka taji ya taho mata.
Isma’il matsowa yayi gabanta, ya kama hannun ta suka fita cikin mota suka shiga gidan baya.
Kan ta a kasa taki yadda ta dago ga kukan da take yi. Kan sa yayi kasa dashi yana leken fuskar ta.
“Halima!”
Yakira sunanta da sanyin.
ko dagowa batayi ba amma jin muryar sa da tayi cikin sanyi da alama shima yana cikin tashin hankali sai taji haushin sa da take ji yaragu a zuciyarta, kara kira sunanta yayi, bata kulashi ba, dan haka ya fara magana cikin salon yaudara yana fadin
“Nasan namiki laifi da banida kalaman dazan gaya miki ki yarda dani, banida bakin dazan baki hakuri Halima. nasan na miki laifi dan Allah dan Annabi kiyi hakuri, ki yafemin, ayanzu nafara sanki karki ga abinda ya shiga tsakaninmu zai sa na canza miki, A’a bazan taba canza miki, kuma abinda ya faru tsakanin mu wallahi bansan yanda akayi nakasa controlling kaina ba, ki yarda dani, please!”
Ya fada muryarsa na rawa, still batayi furta ko kalma daya ba, amma jikinta yayi sanyi riko hannunta yayi ta fisge, tace
“Kar ka kara gingin taba ni naji amman abinda ya faru a tsakanin mu tsautsayi ne amman me yasa ka kasa biyo ni gida a jiya kaji halin da nake ciki da ban dau wayar ka ba.”
“Haba Halima me kike so kice ne. Kada ki manta nima sabon hannu ne a harkar nan wallahi har yanzu jiki bai dawo dai dai ba kuma kinsan motata bata nan. Gashi time din yamma yayi ko bayan magariba naxo naxo ina tsoro nazo na tadda Abban ku ya dawo in ya ganni yace me?”
Juyowa tayi tana kallon sa tace
“Kome zai je ya kawo amman kasan a halin da nake tayaya nazo gida. Isma’il ka cucen ka rabani da martaba. Ka rabani da mutunci na Wanda kowace mace ke sha,awar taga takai shi gidan aurenta, ko aure mukayi mai zan kai ma, nasan tsanata zakayi.”
Ta fada muryarta na fita dakyar, sabida kukan data sha,
“Baby bazan taba juya miki baya ba, wallahi da zan bude zuciyata kiga irin San danake miki da kin daina kokwanto akan San da nake miki,”
Habarta ya dago yace
“Baby nah san danake miki ba dan jikinki nake san ki ba, dan haka abinda yafaru tsakaninmu, sanki bazai taba Raguwa azuciyata,”
Hawaye ne ya fara zubowa daga idon sa. Hannun ta ta saka tana share masa. Dagowa yayi yana kallon ta yace
“Ki yafe min!”
Hannu yasa a aljihunsa yaciro wani zoben gwal kirar Dubai, mai dan girma,yakamo hanunta ya zura mata a yatsarta na tsakiya,yacire wani azurfa dake yatsunta,ya zura ahanunsa,wanan zoben alkwari ne tsakaninmu,wani hawayen farinciki ke zubowa Halima.
Isma’il kuwa ganin ya shawo kanta, yacigaba da mata alkawaririka ita kuwa ta saki jiki, ta manta duk kuncin datake ciki
Hawaye ne ya fara zubowa daga idon sa. Hannun ta ta saka tana share masa. Dagowa yayi yana kallon ta yace
“Ki yafe min!”+
Hannu yasa a aljihunsa yaciro wani zoben gwal mai dan girma, yakamo hannunta ya zura mata a yatsarta na tsakiya, ya kalli yadda zoben yai mata kyau. Kissing hannun yayi yace
“Wannan alkawari nane ni dake mutu ka raba.”
Wani hawayen farin ciki ke zubowa Halima, Isma’il kuwa ganin ya shawo kanta, ya cigaba da mata alkawaririka ta kuwa kara saki jiki ta manta duk kuncin datake ciki………..
Sun jima dan sai da ya wanke duk laifin sa sannan ya bata wata katuwar leda da aka cika da shopping kala kala na ciye ciye da sutura har da sabuwar waya ai kam taji dadi sosai haka ta fito tai cikin gidan zuciyar ta fes dan Isma’il yace ba zai bar ta ba.
********************************************************************************************************************************************************************************************************
Hannah ce ta mike ta shiga falon Momy. Momy dake zaune tana neman layin Ahmad tace
“A’ah ina lallen?”
Fuska ta bata tana turo baki tace
“Yanzu Momy dan Allah Yaa Ahmad ba zai yadda ai yar dinner nan ba please so yake kawaye na su rainani haba Momy please kiyi masa magana nasan zai ji ki.”
Murmushi Momy tayi tace
“To Allah yasa ya yadda dan kinsan Halin Ahmad sa kafiya.”
Hawaye Hannah ta fara Basma ce ta shigio tana fadin
“Wallahi Anty Hannah za a farai min!”
“Ba sai a farai mikin ba.”
Ta fada tana hararar ta.
Dariya Basma tayi tace
“Uhmm Momy kunyi waya da Yaa Ahmad din ne? Yaushe zai zo!”
“Yanzu nake neman layin nasa dai a kashe.”
Ta fada tana kallon Hannah tace
“Hannah jeki ayi lallen kar dare yayi”
“Mikewa tayi ta fita tana turo baki. Basma tace
“Ina tausayawa Anty Hannah wallahi.”
“Da me?”
“Yaa Ahmad sam bai son ta Momy.”
“Kar na kara jin wannan maganar kuma in anyi auren ai zai so ta.”
“Uhmm to Allah yasa.”
“Amin!”
Ta fada tana fadin
“Amman Momy gaskiya ni ko ba zai zo ba ai mana abin mu!”
“Bare zai zo ma. Ai shiyasa ya kashe wayar tasa wallahi yayi wasa gobe ya ganni a Abujan.”
Mikewa Basma tayi tace
“Gaskiya dai Yaya yaci ya dawo gobe fa za ai bridal shower!”
“Uhmm!”
Kwafa Momy tayi tace
“Wallahi Zai zo ya samen ne.”
Mikewa Basma tayi tace
“Bari naje Anty ta gyaran kai kan a zo min lallen.”
“Ok!”
Ta fice.
***** ****** ****** ****** *****
Kwance yake duk abin duniya yai masa yawa ga auren da za ai masa ga mafarkan Hafsa da yake yi kullum tana me neman taimakon sa.
Ya kasa gane kan mafarkin nasa akan me take neman taimakon sa bai sani ba wannan ya kara masa wutar son ta wanda yadauki damarar ceto ta ya taimaka matan.
STORY CONTINUES BELOW

Duk da yasan weekend din nan ne bikin sa amman ya yanke shawara sai friday zai shiga kano Saturday a daura aure wannan yasa ya kashe wayar sa dankar Momyn sa ta dame shi dan yasan in ya kunna bataki tace ya dauki hutu ya tawo ba.
A gida kuwa ana ta shirye shirye dan ranar alhamis bridal shower, Friday dinner asabar daurin aure da kai amarya. Wanda gidan Dady ne ya gina masa shi da kansa, kuma shi yayi wa amarya komai na gidan.
***** *** *****
Momy ce ta mike tayi bangaren Dady yana zaune yana kallon new ta shiga kallon ta yayi yace
“Hajiya ta lafiya ne?”
Zama tayi tana hade fuska hadi da hararar sa tace
“Ai duk kai kake daure masa gindi?”
“Wa fa?”
“Kai maka sani.”
Murmushi tayi yace
“Me d’an nawa yayi ne?”
“Haba Dadyn Ahmad ace har yau Ahmad ba zai taho ba.”
“Haba Momyn Ahmad kinsan fa irin aikin sa ko? Menene zaki tada hankali yanzu ko yana nan ko baya nan ai za a daua auren ko?”
“Bare ma yana nan!”
“To ki kwantar da hankalin ki Ahmad yana nan zuwa kinji.”
“Uhmm Daman ai kai kare shi akai.”
Yai murmushi yace
“Ba dole ba dan Allah ki daina bata ranki akan Ahmad ni nasan Ahmad yana nan zuwa.”
“To shikenan!”
***** *** *****
Karfe uku ya shigo garin Kano amman bai zarce ko ina ba sai gidan su Hafsa ba abinda yake so sai ya ga Hafsa amman tin uku da kwata har hudu yaje yai sallah bai ga mai kamar ta tafito ba. Har biyar yana unguwar a cikin motar sa. Kuma sam bai da alamar ko niyyar tafiya.
Dady da yaji shiru har time din Bai shigo ba yasa ya fara neman layin sa yana ganin kiran Dady ya dauka yana fadin
“Barka da yamma Dady!”
“Barka kadai kana ina ne?”
“Dady na iso tin dazu yanzu zan karaso gida ne na tsaya wani abu ne?”
“Ok sai ka karaso!”
“Toh!”
Har ya juya zai tafi ya hange ta ita da Fauziyya sun fito sanye cikin Hijab har kasa. Ajiyar zuciya ya sake yana mai kara jin son Hafsa a ransa. Yana zaune suka zo zasu gifta su wannan yasa yai saurin fitowa daga mota yana fadin
“Assalamu Alaikum!”
Juyowa sukai a tare suna mai amsa sallamar tasa.
“Barkan ku da yamma.”
Ba wanda ya amsa masa sai kallon sa da suka tsaya. Makulli mota yasa yana dan sosa kai yana satar kallon Hafsa yace
“Dan Allah minti daya mana!”
Wani kallo Hafsa ta watsa masa. Fauziyya tace
“Ku shiga daga soro nan ai kunyi kan hanya ko?”
“Kai Anty!”
“Jeki bari naje na dawo!”
Baki ta tura tayi cikin gidan ya biyo bayan ta ransa fes kamar wanda aka wa kyauta.
Tana shiga ta tsaya ta harde hannayen ta a kirjin ta. Dagowa tayi a karo na farko tana kallon sa take taji kirjin ta ya buga dan ba karami kyau gareshi shi ba ga kwarjini wannan yasa tai saurin yin kasa da kanta.
Zai magana kenan wayar sa tai kara yana dubawa yaga Basma dan haka ya dauka yace
“Ya akai Little?”
“Yaya kana ina ne?”
“Yanzu zan taho!”
Momy ce a amshi wayar tana fadin
“Wallahi Ahmad ranka zai baci na baka minti shirin in ganka a gida yanzu nan.”
“To Momy gani nan!”
Wayar ya kashe yana kallon hafsa yace
“Am sorry gashi ana jira na amman dan Allah ki ban number ki zan kiraki “
Kamar kar ta bayar sai kuma ta bashi. Kallon a yayi yace
“Suna fa?”
“Hafsat!”
“Uhmm nice name. Nagode sai anjima.”
Juyawa tayi tai ciki shi kuma ya fito da sauri dan amsa kiran momy dan jinsa yake kamar wani wanda akai wa kyauta tinda yau ta samu sunan ta da number ai an kusa wuce wajen kenan.
Yana shiga gidan yaga ana fita a motoci za a tafi gun dinner bai damu da mutanen da ya gani a cikin gidan ba haka ya kusa kai har falon Momyn tasa. Bata falo dan haka ya wuce bedroom din ta bayan ya gaisa da mutanen dake falon a zauna.
Tana zaune taci uwar kwalliya kai ba kace ita ce ta haifi Ahmad ba dan yadda ta dawo kamar yar sha takwas.
Yana ganin ta yayi gun Momy yana fadin
“Barka da dare sweetheart.”
Hararar sa tayi yace
“Tuba nake Hajiya ta Amarya kuma uwar gida a gidan nan daga ke ba kari.”
Murmushi ta saki ya zauna akan tiles din dakin yana fadin
“Affuwan aiyuka ne sukai min yawa sweetheart but ai gani na iso ko? Ya gida da taro?”
“Alhamdulillah.”
Ta mika masa wata leda dake akan gadon tace
“Maza kaje ka shirya na baka minti ashirin kaji ko?”
Amsa yayi ya gyada kai ya fice a dakin. Bangaren sa yayi wanka ya shiga yayi sannan yayi sallah magariba da isha’i yana idar wa ya bude ledar kayan. Wata golding kalar a ciki yaga hula da agogo. Sakawa yayi ya feshe turaren sa.
Masha Allah take ya fito a angon nasa. Yayi matukar kyau kamar ka sace shi ka gudu. Shi kansa yasan yai kyau yana shirin fitowa daga dakin Momy na kawo kai komawa yayi ta shigo tana kallon sa hadi da sakin fara’a domin dai itama yayi mata kyau.
“Shige muje!”
Ta fada tana saka shi a gaba. Yana fita ta yi gun motar da suari ya bude mata gidan baya ta shiga shima ya shiga a take Driver ya tada mota suka bar gidan.
Suna cikin mota Momy ta dauki waya tana kira ringing daya biyu Basma ta dauka. Momy tace
“Kuna ina ne?”
“Muna hanya zuwa gun Dinner.”
“Alright ku jira mu a kofar wajen gamu nan karasowa.”
“Alright Yaa Ahmad ya karaso ne?”
“Eh muna tare.”
“Yeee kace dinner ta cika dinner ango ya karaso.”
Hannah dake gefe ce ta ci kwalliyya ta gaji da haduwa tace
“Ya iso ne?”
“Yes!”
“Yeee!”
Ta fada tana rumgumar Basma. Dariya Basma tayi tana fdin
“Kar ki bata kwalliyar man.”
“Ai shine kuma Yaa Ahmad bai gani ba.”
Sukai dariya.
A cikin compound din suka tadda motar su Momy suna zuwa Momy ta sanar da abokan ango da kawayen amarya su fito su shiga da ango da amarya.
Nan MC ya bada sanarwa ba ai minti biyar ba aka jere kawayen ango da amarya sai da suka jere sannan ango ya fito a mota ran nan nasa a bace. Bai ko kalli inda Hannah take ba.
Ya tsaya Hannun sa Basma ta kama ta sakala a cikin na Hannah abinda ya haifar masu da wani shock wanda yasa ya dago yana kallon ta ita ma kallon nasa take. Sai yau ya taba tsayawa ya kalli kanwar ta sa har wani abu ya shiga ransa. Tayi kyau har ta gaji da yin kyau.
*Toh fah Halima da Isama’il ya part din nasu? Shin da gaske Isam’il zai daina. Ku bawa Halimaa shawara. Ga kuma Amarya da Ango me xaku ce tsakanin sa da Hafsa?*
Ya tsaya Hannun sa Basma ta kama ta sakala a cikin na Hannah abinda ya haifar masu da wani shock wanda yasa ya dago yana kallon ta ita ma kallon nasa take. Sai yau ya taba tsayawa ya kalli kanwar ta sa har wani abu ya shiga ransa. Tayi kyau har ta gaji da yin kyau.
Shi yai karfin halin janye idanun sa. Domin Hannah ta kasa janye nata bata taba ganin Ahmad yai mata kyau irin na yau ba. Ya gama tafiya da ita daman ita tana sonsa.
Shima a ransa fadi yake
“Daman haka yarinyar nan take ba laifi zan gyara mata zama mu zauna tare da amarya ta Hafsat.”
Ya fada yana murmushin tunawa da yayi yau ya samu number ta yaga kuma gidan su. Ji yake kamar ma har ya aure ta. Tunanin Hafsa shi ya saukar masa da fara’a akan fuskar sa har ake zaton na auren ne.
A haka aka shiga hall din har suka zauna agun zaman su. Duk abinda ake gaba daya rabin hankalin sa naga a tashi yaje yaji muryar sahibar tasa. Amman ina taro ake kamar ba a san dare yayi ba dan sai karfe sha biyu aka tashi.
Yana fitowa ya shige motar gida ya amshi key wajen driver yana fadin zai bayar a kawo masa yanzu. A guje ya bar wajen.
Yana zuwa ya bada motar a mayar ya shige bangaren sa. Kayan jikin sa ya cire ya fada ban daki. Wanka yayi ya fito ya saka kayan bacci. Kan gado ya fada yana salati domin kuwa ya gaji tin da ya dawo bai huta ba.
Wayar sa ya janyo da nufin kiran ta sai yaga sha biyu da rabi da minti tara.
“Dare yayi.”
Ya fada yana shiga message. Text ya tura mata mai dadi sannan ya ajiye wayar yana addu’a. Bacci me dadi ya debe shi da mafarken Hafsat.
Hafsat kuwa bayan ta shiga gida tunani ta fara. Anty Fauziyya ce ta shigo ta zauna a kusa da ita tace
“Ya dai sister?”
“Tsoro nake ji Anty.”
“Tsoron me?”
“Ina son aure kuma ina tsoron abinda zan fuskanta.”
Dafata Anty Fauziyya tayi tace
“Ki kwantar da hankalin ki kina addu’a Allah ya daura miki abinda xamu iya kuma Allah ya yafe miki. Insha Allahu! Allah zai kawo miki tallafi ta inda bakya zato ba gani nan ba. Na fada miki halin da nake ciki da Muhammad tin ina yakice shi har na hakura na bawa zuciyata abinda take so. Kema da sannu zaki samu mai tallafawa rayuwar ki ya cire ki daga *wannan rayuwar* damuke ciki kinji.”
Kai ta gyada. Anty Fauziyya tace
“Ya kukayi da shi?”
“Uhmm ya amshi number ne?”
“Ok amman ina son in dai da gaske yake kar ki boye masa komai.”
“Saboda me?”
“Saboda gwara ya sani tin kan ki shiga ki fuskanci matsala.”
“Anya kuwa Anty xan iya. Sam bana son tuno *wannan rayuwar* sam.”
“Duk da haka. Ni kina ganin zan yi fargaba nan gaba in Muhammad yasan koni wacece bayan a yanzu ya riga ya sani.”
“Anty kenan son da Mubammad yake miki ba irin namu bane. Kuma ni ba zan ce zan tsaya neman wanda yake miki irin son nan ba dan wahala zai ji. Kema Allah ne ya dube ki ya kawo miki shi.”
“Kema Allah ne ya dube ki ya aiko da wannan dan ni har ya kwantan tin yanzu.”
“Toh Allah yasa mu dace.”
“Amin ina wayar taki?”
“Ba caji.”
“Ok muje muyi sallah ko?”
“Toh Anty.”
Suka mike suka fita sukayo alwala .
STORY CONTINUES BELOW

******** ******** **********
Daga masallaci ya fito ya kalli agogon hannun sa karfe tara da kwata tinda yai sallah isha’i yake masallacin yana tilawa sai yanzu ya fito. Daga nan direct gidan su Fauziyya ya isa. A kofar gida ya tsaya dai dai lokacin da kanin Fauziyya xai shiga gidan ya kira sa.
Yana zuwa yace
“Dan Allah in ka shiga kace ana sallama da mai gidan.”
Sannan ya zaro naira hamsin ya bashi. Yai godiya yai cikin gidan.
Da gudu yaron ya dawo yace
“Wai yana zuwa.”
Bai fi minti uku ba sai ga Baba ya fito sanye da yar shara yana ganin Muhammad yai masa kwarji dan haka ya mika masa hannu sukai musabaha Muhammad na gaishe shi. Baba yace
“Sai dai ban gane ka ba.”
“Sunana Muhammad Ahmad Muhammad nazo neman auren yar ka Fauziyya.”
Shiru Baba yayi yana kallon Muhammad. Can yace
“Amman nawa Fauziyyan take?”
“Nima naga hakan amman ganin inason ta yasa nace bari na fada maka. Bana bukatar komai na auren ta za a daura aure ne kawai na dauke matata.”
Baki Baba ya washe yace
“Ah to madallah ai ba matsaka ka turo iyayen ka a tsaida lokaci kawai kai ni ko yanzu kace ai sai ayi.”
“Ah Baba zan dai aiko kuma in na aiko bana son ya wuce sati biyu insha Allah!”
“Ba komai dan nan ina jiran zuwan nasu.”
“To madallah ni zan tafi.”
“Ka gaida gida ina jiran zuwan nasu fa.”
“To Baba”
Muhammad ya tafi ransa ba dadi. Yana farin cikin Fauziyya ta kusan xama tashi yana kuma taya Fauziyya bakin cikin samun uba marar ilimi da sanin ciwon kai. Ace aga ‘yar sa ace yana son ta yace ba da komai xa a kai ta ba ya yadda ba bincike yace ko a lokacin a daura aure. Lallai dole ya sanar azo ayi komai a wuce wajen kar wani kuma yaje ya nuna kudi a bashi shi tinda bai bada komai ba.
Haka ya isa gida yana saka da warwara yana shiga gida babbar wayar sa ta hau kara yana dubawa yaga Ummi ce. Dauka yayi cikin damuwa nan da nan hankalin ta ya tashi ta hau fadin
“Mai babban suna me ya faru?”
“Ba komai Umni.”
“ka tabbata?”
Kai ya gyada bai bata amsa ba.
“Dan Allah ka fadan in da damuwa na gane damuwar ka bata wuce ta Yarinyar nan me kuma yake faruwa yanzu?”
Tabbas ba komai zai fadawa mahaifiyar sa akan matar da xai aura ba kar ta tsane ta duk da yasan mahaifiyar sa ba zata fara haka ba dan haka yace
“Ni da nake cikin farin ciki ance in turo Me xai damen Ummi?”
“Da gaske kake?”
“Eh sati biyu za a saka dan ki tafi hadowa sirikar ki lefe. Tsarin gidan su ba ayiwa yarinya lefe miji shi zaiyi kayan daki amman ni naji na dauki dukka biyun duk da ban fadawa mahaifin nata ba na bar shi in ta shigo a bata.”
“Masha Allah hakan yayi son ya zancen biki tinda naga lokacin kadan ka saka.”
“Ummi duk wasu taro basa so daga daurin aure shikenan zan taho da matata ayi komai anan.”
“Masha Allah. Allah ya sanya albarka. Next week zani Umrah sati biyu zanyi daga nan zan zarce a hado lefe na dawo sai ayi shagalin biki hakan ya maka?”
Abinda yake so kenan dan akwai plan din da ya tsara dan haka yace
“Sosai ma Ummi. Allah kara arziki da girma. Ba zan taba biyan ki ba sai dai nai ta miki addu’a farin cikin rayuwa ta.”
“Kar ka damu dole ai nai maka in ban maka ba wa zan wa? Kana faran ta min. Allah baka nasara da sa’a akan duk ahinda ka saka a gaba Mai babban suna. Allah ya sa ayi bikin nan sa’a ya baku zaman lafiya.”
“Amin Ummi dare yayi kije ki kwanta ki huta.”
“To dan Albarka kaci abinci dai ko?”
“Naci.”
“To Allah tashe mu lafiya.”
“Amin!”
Ya katse wayar yana cire kayan jikin sa. Ruwa ya watsa ya kwanta a katifar dakin sa. Yana mai murmushin ya kusa mallakar Fauziyya. Allah bashi Fauziyya. Wai yau wa ya ganshi ya mallaki fauziyya. Bakin sa yaki rufuwa sai kace yaga ya mallak ta 😀
***** ************ ******
Baba na shiga gida ya shige dakin sa. Murna yake zai rage daya ba tare da ko sisin kobon sa ba. Yaya Babba da ta shigo taga yana ta washe baki 😀 kamar wanda aka biyawa makka tace
“Alhaji lafiya naga sai washe baki 😀 kamar gonar auduga?”
“Ke abin farin ciki ne ya sameni cikin nan da sati biyu zan fara rage ya’yan gidan nan.”
“Ka kai su ina?”
“Dakin mijin su.”
“Alhamdulilah ka yadda yanzu su turo mazajen ne?”
“A’ah mutum daya na yadda da ya turo dan haka ban son ma su sani gaba dayan su itama sai dai taji nace ta fito ta bishi ba tare da tasan angon ba ko bata sani ba.”
“Amman dai ya kamata ka tambaye ta kaji ko?”
“A’ah dan tace bata so inyi yaya?”
“Amman kayi bincike dai ko?”
“Wane bincike ne taje tayi hakuri da halin sa.”
“Haba Alhaji aure fa zakai musu ba siyar dasu ba.”
“Kinga in ba zakiyi addu’a ba ki bimu da Ido.”
“To Allah ya kyauta.”
“Amin!”
Ya fada. Mikewa tayi ta fita tana kara mamakin halin mijin nan nasu.
****** *** ******
Washe gari da yamma wajen biyar da rabi sai gashi a kofar gidan su Fauziyya. Aikawa yayi tazo bata dauki lokaci ba ta fito sanye da doguwar riga da farin hijab. Tayi kyau duk da batai kwalliya ba sai tashin kamshin turare take mai sanyin dadi.
Suna hada ido suka sakarwa da juna murmushi. Ta durkusa tace
“Ina yini?”
Tarbiyyar Fauziyya na burge shi. Ya saki murmushi yana fadin
“Na samu farin cikin zuciya ta lafiya?”
“Alhamdulillah sai dai kewar ka jiya ban ganka ba.”
Kai ya shafa yace
“Na yini addu’a Allah yasa Baba ya yadda ya ban auren ki abinda ya hanani zuwa kenan.”
Murmushi tayi tai kasa da kanta Murmushi yayi yace
“Jiya fa nazo gun Baba.”
A razane ta dago idon ta na kawo ruwa tace
“Me yace?”
“Baba yace na kara hakuri baki girma ba.”
Hawayen idon tane suka fara zubowa. Murmushi yayi yace
“Am sorry beauty please goge hawayen kiji yadda mukai.”
Bata goge ba sai cewa tayi
“Ina sauraron ka.”
“Baba ya bani dama na turo in na turo za a daura aure a lokacin in yaso ke tare nan da sati biyu ya kika ce?”
“Haba dai da gaske?”
Ta fada tana dariya. Kai ya gyada nan ta goge hawayen ido ta tace
“Amman dai ai ka bari na dan kintsa ko?”
“Sati.biyun sun isa ki kintsa.”
“Gaskiya sun min kadan.”
“Sai dai fa kiyi hakuri.”
Murmushi tayi tace
“Ya akai Baba ya yadda?”
“Ina ruwan ki?”
“Babu.”
Yai dariya haka suka dan taba hira ta soyayya dan kiran magariba yasa sukai sallama ya tafi ita kuma ta koma ciki tana mai farin ciki.Isma’il ne kwance suna waya da Halima, sai tsarata yakeyi dan tun daga lokacin da ya santa ‘ya mace taki sakin jiki dashi, kamar da shi kuwa bazai bari ta subuce masa a yanzu ba dan gaskiya ta wuce yanda yake tinani dan gaskiya sai a tara mata dayawa ba a samu, mai niimar ta ba, duk da ya san mata da yawa amman bai taba tarrayya da macen da tai masa kamar Halima ba.+
Kasancewar Isma’il dan duniya ne yasan duk logic din da zai bi ya shawo kan mace, a haka yayi ta cusa kansa awajen Halima yana nuna mata bashi da sama da ita.
Kasancewar Halima mai raunin, sanyi ga hakuri, ga zafin San da takeyiwa Isma’il yasa ta amince zai aureta, kuma ta cigaba da yadda dashi da kalaman sa. Amma bata kara gigin kara zuwa gidan sa ba.
Kabir kuwa bawan Allah yana nan yana fama da San Halima a zuciyarsa, yana ta addu’a Allah ya cire ta a ransa tinda abokin sa ya yadda da zai aure tan. Amman ina kullum son ta kara shigar sa yake.
A wannan lokacin Isma’il ya kara tusa son sa a zuciyar Halima ya kuma kara manne mata. Dan duk yadda take dan share shi a farko yanzu duk sai ta daina.
Yau bayan ta fita bara da zata dawo suka hadu a hanya ya bata nama da lemo. Gida ta koma lokacin ana kiran sallah magariba. Wanka tayi tai sallah. Tana zaune har akai isha’i tayi sai wajen tara tazo kwanciyya taga ledar da Isma’il ya bata wannan yasa ta bude naman da yawa sai lemo guda daya.
Naman ta diba ta bawa yaran gidan su dan su raba ita kuma ta shiga daki ta hau ci ta gama ta shanye lemon ta. Kan shinfiddar ta ta hau lokacin da wayar ta ta fara kara kenan. Dauka tayi ta saka a kunnen ta.
Yadda yai sallama da wani nunfashi ji tayi tsigar jikin ta ta tashi. Sabida yanayin garin na sanyi ga kwayar sha’awa da ya saka mata a lemo wannan yasa ta fara jin wani abu na yawo a jikin. Hira suke har wajen sha daya lokacin da wata muguwar sha’awa ta taso mata. Take ta fara tinanin moment din da sukayi spending tare a baya. Yadda yake mata da sarrafa ta da romacing nata.
Ji tayi ba abinda da take so illa ta kasancewa dashi, ko taji saukin abinda takeji, Isma’il kuwa mai karantar yanayin mace tin daga kallon ta muryar ta da motsin ta yake ganewa. Dan haka yana jin sauyin muryar ta da ya canja dan ba a haka suke magana a farko ba. Yanzu sai wani dan nishi take tana shhh kamar wacce taci yaji.
Wannan yasa ya dauko wata hirar ta in sunyi aure ga yadda zai na mata na ya dinga burkita mata tunani da lissafi. Sai da ya kai in ya mata magana ma bata iya bashi amsa yai mata sallama akan dare yayi dan har biyu da wani abu tayi.
Zai kashe wayar kenan yaji tace
“Gobe kana gida ne ko xaka kasuwa?”
“Kai hutawa xan danyi.”
“Alright kila na biyo “
“Oh da gaske wallahi daman nayi missing naki yanzu in mun hadu muntuna kadan mun rabu.”
“Uhmm!”
Ta fada. Yace
“Sai da safe kiyi mafarki na.”
Ya kashe wayar yana wani killer smile. Text ya tura mata wanda ya kara kashe zuciyar ta da tunanin ta ji take da da hali a lokacin zata tafi gun Isma’il.
*
Isma’il washe gari kin fita yayi duk da yai niyyar fita target din sa da yaga ya dano yasa ya fasa.
Halima kuwa har ta tashi da safe bataji karfin jikin ta ba. Allah Allah take rana tayi ta tafi wajen isma’il. Ai kuwa karfe biyu ta shiga ta yi wanka ita ce dirje can wanke can ta fito ta tsara kwalliya tai kyau da ita ta bade jikin da tuare. Gidan Isma’il ta nufa.
Tana shuga ta saka key ta rufe sannan tayi ciki tana sallama. Baya falo wannan yasa tayi hanyar bedroom tana kiran sunan sa. Har ta isa bakin kofa ta fasa ta juyo dai dai lokacin da Isma’il ya fito daga wanka kenan daure da towel a kugun sa.
STORY CONTINUES BELOW

Yana fitowa tana juya baya zata koma ta xauna. Wannan yasa ya rungumota ta baya yana fadin
“Oyoyo I Miss u Baby na.”
Juyowa tayi tai hugging nasa back tace
“Miss u more.”
Danshin jikin sa shi ya kara haifar mata da wata sha’awar. Kasa tayi da kanta fuskarta ya dago yayi kissing din lips dinta softly ta lumshe ido, ya cikata yayi ya zauna ya zaunar da ita a gefen sa. Kamo hannta yayi, ya kura mata ido, sunkuyar da fuskarta tayi dan bazata Iya jure irin kallon da yake mata ba.
“Baby kina sona kuwa?
Dagowa tayi tana kallon sa tace
“Wacce irin tambaya ce wannan?”
Murmushi yayi yace
“Saboda yadda nake jin son ki kamar zai fasa kirji na ya fito shiyasa ke kina jin haka kuwa?”
“Fiye da haka ma My love.”
“Halima!”
Yakirata dawani murya mai rikita ta.
“Na’am!”
Ta amsa can kasan makoshi.
“Wallahi am earger naga na mallakeki a matsayin matata dan gaskiya yadda nake kewar ki kamar zan mutu. Jikina ke kawai yake muradi. Kizo muje a daura mana aure a boye kawai.”
“A’ah Isma’il hakan bai dace ba mu kara hakuri naji Baba ya fadawa Mama zai fara aurar da mu kaga ai lokacin ya kusa ko?”
“Baby anya zan iya jura har wancan lokacin kuwa?”
“Haba ka zama jarumi mana.”
“Ni wannan ba zancen jarumta fahh.”
Ya karasa maganar da jan nunfashi yana daura kansa a kafadarta yana shinshina wuyanta, a hankali yafara mata kiss a wuya ya gangaro kirjinta, tuni wuta ya daukewa Halima.
Nan ya farai mata shagwaba yana wani jan numfashi. A haka yayi ta mata salo iri iri, batasan lokacin data fara mayar mai da martani ba
Daukar yayi ya kaita bedroom, sai daya kwashi kusan hour yana romancing dinta, sai daya tabbatar ta kamu, yakai hannu zai cire mata pant ta rike gam tana girgiza kai, sakin ta yayi ya mirgina gefe,
“Baby baki yadda dani bane ko me? Ni dan zan aure ki. Kinsan a halin da nake ciki kuwa a yanzu. Hakika yadda nake bukatar ki in har baki bani kan ki ba zan iya mutuwa.”
Kara ya saki yana rike marar sa yana fadin
“La’ilaha illah wayoo zan mutu marata.”
Hawaye Halima take tana fadin
“Haba Isma’il kar ka mutu ka daure kaga bai dace ba kuma ni ina tsoro kar gaba kace baka so na.”
“Har yanzu kina tan tama akan son da nake miki ko? Naji ki tashi ki tafi in na mutu kya yadda da ina son ki.”
Nan ya juya yana kara rike mara yana kuka har da hawaye yana cije baki. Cikin kuka tace
“Ba haka bane.”
“Nace ki tashi ki tafi tinda baki yadda dani ba. Tayaya zan juyawa rayuwa ta baya.”
Hawaye take tana girgixa kai. Numfashi ya hau ja da sauri da sauri yana rike da marar sa. Yana fadin
“Dan Allah Halima ki taimakan kar na mutu.”
Fadawa kan sa tayi tana fadin
“Kada ka tafi ka barni.”
“In bakya so na tafi na barki u have to help me please.”
Kai ta gyada yace
“Kin yaddai?”
Tana kuka tace
“Eh!”
Dan ba a son ranta zata kara aikatawa ba. Dan ita so tayi su tsaya iya romancing kawai.
Rumgume ta yayi ya dinga lashe hawaye idon ta yana fadin
“Thank you Baby I really love you u, kin ceci rayuwa ta. “
Ita dai bata kara magana ba sai hawaye dake zuba kamar famfam bai damu ba ya cigaba da abin da yake yana sarrafata har ya shige ta…………………
************************************************************************************************************************************Da daddare bayan ta fito daga wanka taji wayar ta na ringing dubawa tayi taga ba number kasar nan bace ajiyewa tayi ta shafa mai ta fesa turare kara kira akai lokacin tana gaban durowa dubawa tayi kara ganin number ce ajiyewa tayi ta saka rigar sannan ta nufi firij din dakin ta dauki robar nono ta sha ta mike kenan sako ya shigo cikin wayar. Dubawa tayi sai tace
“Kin yi bacci ne?”
Da number dai da ake ta kiran ta. Reply tayi da
“A’ah waye?”
“Angon kine.”
Ya dawo mata da amsa. Ajiye wayar tayi bayan taga sakon nasa dan kunya ma ya bata.
Text ya karai mata yace
“Ya kike ya daren?”
“Alhamdulillah ya kake?”
“Gani nan ina kewar iyali.”
Shiru tayi bata bashi amsa ba. Kara turo mata da sako yayi yace
“Kizo ki deben kewa?”
“Me zan maka?”
“Me mace ke wa mijin ta Ummu nah.”
“Kai Yaa Muhammad ni ban sani ba.”
“Hmmm ko?”
“Eh mana.”
“Shikenan na bar ki in kin tare na ga baki sani ba.”
Bata bashi amsa ba. Wannan yasa ya kara turo mata da sako yana fadin
“Ina son jin muryar matata.”
“Kana da iko akan hakan ai.”
Yaji dadin reply dan har da murmushi sannan ya fara kira. Ringing daya biyu ta dauka da sallama a bakinta.
Jin sanyi da dadin muryar ta yasa ya lumshe idon sa sannan ya bude ya amsa da tashi muryar mai dadi da saka nishadi.
“Me kike yi ne yanzu?”
Ya tambaya yana katse shirun da sukai.
“Shirin bacci.”
“Nazo muyi tare?”
Ya tambaya. Shiru tayi tana rufe fuska. Murmushi yayi yace
“Amman ai kinsan wata rana dole tare zamu baccin ko? Kinsan me kila in ban kusa dake ma ki kasa baccin.”
“Kai Yaa Muhammad.”
“Eh mana.”
“Ni ka bar wannan maganar.”
Ta fada a shagwabe.
“Ni ina so to.”
“To!”
Ta fada a sanyaye.
“Am sorry to na daina.”
“Haba dai Yaa Muhammad ka cigaba Allah ba komai.”
“Gimbiya ta bata so dan haka na bari.”
Murmushi tayi kawai. Yace
“Ina su Anty Zainab da Yaa Suleiman”
“Sunyi bacci?”
“Ya’yan ta nawa ne yanzu?”
“Biyu ne tana da cikin na uku.”
“Masha Allah. Allah ya raya yayi nusu albarka”
“Amin!”
“Sauran wata nawa ki gama karatun ne?”
“Wata hudu ne.”
“Masha Allah lokacin sauran two month na dawo.”
“Kai amman abin yai sauri.”
“Ko?”
“Eh!”
“Ni kam banga saurin sa ba saboda bana tare dake.”
“Kai Yaa Muhammad ai zaka dawo ka samen ne.”
“Haka ne shyasa nake Allah Allah na dawo ai.”
Murmushi Ummu tayi yace
“Dare yayi kije ki wanta gobe kina da ckul ko?”
“Eh!”.
” Da karfe nawa?”
“10am.”
“Ok in na kira kan ki fita to. In ban kira ba sai kin dawo ki kular min da kanki.”
“Insha Allah “
“Sai da safe.”
“Allah ya tashen mu lafiya.”
“Amin!”
Suka kashe wayar. Kwanciyya tayi tana mai sakin murmushi. Ita kam in tana tare da Yaa Muhammad ta kanji farin ciki a ranta me hakan ke nufi.
Shima kwanciyya yayi yana lumshe ido yana mai jin sanyi da nutsuwa a ransa yasan Ummu akwai iliimi yana fatan tayi amfani dashi dan Rukkayya ma tana dashi amman bata amfani dashi. Allah yasawa matar sa son sa kamar yadda son ta ya kanai naye zuciyar sa. Ido ya lumshe yana maii tuna hirar da sukai. Murmushi ya saki yana gyara kwanciyyar sa. Idon sa a lumshe yana hasaso yadda Surar Ummu take.
A cike take kyakyawa da ita domin tafi duk yan gidan kyau da komai. Ga ilimi hankali nutsuwa. Hakika Abbah masoyin sa ne ya dauki yar sa ya bashi ya kuma bashi wacce tafi kowa soyuwa a gun sa. Lallai Abba uba ne gare shi ko da Ummu ko babu ita. Domin ya nuna masa so sosai.
A haka bacci ya dauke shi da tunanin Ummu kala kala da mafarken ta.