EL-BASHEER COMPLETE
EL-BASHEER
Na
Nuceeyluv😘
1-5
*****Kwance yake kan daya daga cikin kujerun parlon nasa, a yadda yake kwancen zaka tabbatar da shidin dogo ne domin kujerar ma ta masa kadan kawai ya kwanta ne, fuskar sa a matukar hade take babu alamar Annuri a tare dashi, wata irin qasumba ce ya tara tamkar shugaban en daba sam babu wani gyara, idonsa na kallon sama Alamar tunani ya tafi hakan zai nuna hasken fararen idanun sa tass tamkar madara, dukda ya tara kasumba hakan bazai hana a gane tsananin kyawun da Allah yyi masa ba, saidai idan kayi masa kallon tsanaki zaka hango yadda farar fatarsa tayi duhu, yyinda wata er rama kadan ta bayyana a gareshi *EL-BASHEER USMAN TAFIDA* shine cikakken sunan sa, dan zakutawa yyi daga kwanciyar da yake ya lumshe idonsa kamar me bcci.+
Sakkowar su kenan daga bene wani matashi da be kai el-bash ba yace,
“haj amma fa kina fama da kato a gida,”
wacce aka kira da haj ta tabe baki tace,
“ni wlh lamarin sa ma ya fara isata babu biyan bukata sai aikin wahala ni wannan *HAUKA* ta isheni nayi kokari ma da muke kwana da *MAHAUKACI* a gida daya wlh,”
matashin yayi dariya yace,
“Sannu fa haj gsky na yadda komai ma waje yake samu, shi da gidan ubansa kice kin gaji?
Haj ta bata rai tace,
“Toh yimin gori sale sai nasan bani da gado da gidan dan rainin hankali.”
Sale yana rike dariyar sa yace,
“Maida wukar hajjaju ai gadon ma gaba1 naki ne yyinda kika aika shi lahira shi da tsohon ubansa.”
“Haj ta washe baki tana tafi tace yanzu ka dawo hanya qanina salele”
Sale yace,
“Kefa wani lkcin Yaya suwaiba kinada Wulakanci meye kuma salele? Sai kace sillen kara”
Haj ta rufe bakinta dan tasan ta tabo inda bayaso tace,
“toh naji na daina Sale.
Sale yana tabe baki dan be gama hucewa ba yace,
“har yanzu baki samo solution bane?
Haj tace,
“kai Sale sau nawa zan maka mgnr? Na rasa inda ya boye takardun nan wlh ai da tuni mun aika shi,”
sale ya fara yin hanyar fita yace,
“ya kamata duk inda ya ajiye takrdun nan a samo shi dan wlh bazan kashe kudi a banza ba kin sani sarai gadon mu aka siyar dan kawai mu samu biyan bukata amma har yanzu shiru.”
haj ta bishi wajen suna karasa mgn tace,
“dadina dakai sale baka da hakuri, kana gani dai mahaifin sa baya kasar bare mu samu wani abin, shi kuma da muka *HAUKATAR* dashi mun duba ko’ina bamu samu takardu ba, gashi duk accnt dinsa a kulle bare mu kwasa dole sai da sanin sa,”
nisawa sale yyi yace,
“ni kinga tafiya ta saina dawo.”
haj tace,
“to shikenan nan itama ta juya.”
~
karar fashewar abubuwa ta fara ji a parlon, lekawa tayi ta window nan ta hango el-bash duk yyiwa parlon upside down, kujerar da yake kai ya juyata, haka sauran kujerun ma, komai dai ya hargitse, wani wawan tsaki haj taja kafin ta koma bangaren ta, dama bangaren nasa sukaje sukayi bincike ko Allah zaisa suga takardun da suke nema.
*
Wata irin wawiyar parking tayi a parking lot, sanye take da wani irin dinki da yyi matukar kama ta, duk wata sura ta jikinta ana gani idonta toshe yake da wani katon glass daya cika mata ido, kas-kas take tauna chewing gum dinta, yyinda take taku dai-dai kan takalmin ta me matukar tsini, *Sakina* kenan ‘yar gidan haj Suwaiba kuma a matsayin Agola a gidan Alhj Usman, A sangarece ta karasa parlon tana hura chewing gum irin na rikakkun en bariki ba tare da tayi sallama ba ta zauna akan kujera hade da dora kafa daya kandaya. Haj suwaiba dake parlon ta juye tana kallon yarinyar tata tace,
“sakina har kun tashi lecture?”
Sakina ta tabe baki tace,
“wlh momy na gaji skul saikace dole.”
momy tace,
“dan ubanki idan bakiyi karatun ba dame zamuyi kudi? Kina gani dai yadda nake fama na sama mana dukiya duk dan sbd kiyi Alfahari Amma na kula ke bakida hankali sai kace tinkiya,”
sakina tace,
“momy da wannan wahalar da kike ku aura min shi mana,”
momy tace,
“shi wa?”
Sakina batare da damuwa ba tace,
“El-bash.”
A razane momy ta dago tana kallon sakina tace,
“kina da hankali kuwa? *MAHAUKACIN* zaki aura? kai amma anyi gantalalliyar yarinya wlh, duk samarinki ki rasa wanda zaki so sai shi?”
Sakina tace,
“oh momy calm down da wasa nake ni me zanyi dashi? Haba wuce nan”
sai a lkcin momy suwaiba ta sauke ajiyar zuciya tace,
“haba yanzu naji sanyi a raina amma da kina nema ki samin hawan jini.”
Dariya sakina tayi tana me tashi dan tafiya dakinta.
~~
Tana shiga daki ta kira kawarta zee,
“sakna ya dai hop momy ta amince?”
Sakina tace,
“yaushe zata amince min? Daga mgn bakiga yadda ta wani gigice ba sai nace mata da wasa nake ina tunanin zamuje plan B kin sanni sarai idan na kwadaita da mutum sai inda karfina ya kare.”
Zee tace,
“wannan haka yake badan yana hauka bama ai gwarzon namiji za’ayi anan.
Sakina ta lumshe ido tace,
Bari tunamin zee inaji kamar nayi tsuntsuwa naje gareshi, wlh ina matukar kwadayin sa, ba hauka ba koma me yake wlh saina dandana shi.
Zee ta kwashe da dariya tace,
” ina yinki sakna big gal zanso naga yadda zaki kaya da mahaukaci.
Sakina tayi murmushi tace,
“kedai bari zan gwada sa’a ta.”
Zee tace Duk yadda ake ciki just hala me.
Sakna tace no p.
Nan dai suka katse wayar.EL-BASHEER
Na
Nuceeyluv😘
6-10. ( *Xoxo* 🤫🤪🏃🏼♀)
Kayanta ta fara cirewa, nan ta fara zaro acucin da tayi, Nonon ta yaji acuci haka nan hips dinta ashe duk iska ce bana gsky bane, sai yanzu ta dawo asalin halittarta ta koma wata sanda a tsaye Nonon ta dogaye sbd yanayin damkar su d ake yasa suka zube sai reto suke bra ke rufa mata asiri. mazaunai kamar marar tuwo, gashin kanta ma kari ne dan kitson Attach ne a akai. Toilet ta fada tayi wanka bayan ta gama tazo ta mulke jikinta da mai da turare dan tabe baki tayi tace, shi mahaukaci har wani kamshi ya sani? Mtwsss”
+
ta maida turaren, wata rigar bcci ta samu wacce ta bayyana surar jikinta sosai. After dress baka ta saka akai sannan tayi rolling da gyalenta, fitowa tayi nan ta tarar momy ta shige daki toh dama bayan magrib ne lkcin. Tabe baki tayi tabar parlon. Direct hanyar parlon sa ta kama.
Sanin ba wani hankaline dashi ba yasa ta tura kofar kawai, zaune ta same shi kasan kujera ya dafe kansa kamar wani me hankali, wutar parlon a kashe take dan haka ta kunna sai gashi hasken ya mamaye ko’ina, daidai lkcn shi kuma ya dago dan yaga haske yana kashe masa ido, fuskar nan a hade tamkar hadarin tsakiyar agusta babu alamar murmushi sam a tattare dashi kallon ta ya tsaya yi kamar yaga sabon halitta.
Sakina ta saki murmushi tana me fara cire rigar ta tace “yaudai gani a bangaren mafadaci an zama mahaukaci” tayi mgnr tana shekewa da dariya, daga ita sai er rigar ta, tafara juyi a gabansa nonuwan ta na reto tana kashe masa ido kamar tana mgn dame hankali tace,
“Darling kalli nan”
ta nuna masa kirjinta tana shafawa hade da shidewa, kamar wani status haka yake baya wani motsi, ganin duk abinda take yaki motsi yasa ta cire rigar gaba1. El-bash dake zaune ya mike da sauri kamar wanda ya tuna abu sai kuma ya dafe kansa ya fara tafiya hanyar dakinsa.
Wata irin dariya sakina ta saki tace,
“a’a mahaukaci ashe ka gane muje dakin,”
nan tabishi jale-jale da kayan nono suna reto kamar an ratayo agwagi a keke, dakinsa ta shiga nan ta ganshi ya kwanta saman gadonsa yana kallon sama, haurowa tayi saman gadon tana fadin wlh ka hutar dani ma haba mutum tun da lafiyar sa nake binsa ina bashi kaina yaki kula sbd rashin tausayi yaudai saina fanshe jan ajin da kamin tayi mgnr tana me cire pant dinta.
Karasawa tayi kan gadon tasa hannunta da niyyar cire masa wando dan so take ta mulmula shi dole dan kansa ya kunno wuta, sa hannun ta kenan yyi daidai da tsintar kanta da tayi jikin kofar dakin a kasa wanwar.
Wata irin karar azaba ta saki dan ta bugu sosai sai yanzu ta fahimci da kafar sa yyi ball da ita tun daga kan gado ta wurwuro har zuwa bakin kofa, tashi tayi dakyar ga mmkin ta sai ta ganshi still a kwancen da yake kamar dazu, wani irin tsoro ne ya shigeta a ranta tace na shiga uku kardai baqaqen Aljanun haukar sa ne sukayi wurgi dani? A fili tace,
“ba Aljanu ba ko ifiritai ne wlh yau tunda nazo saina samu abinda nakeso,”
komawa tayi tana tafe tana turo kirji hade da kama dayan nonon nata taje daidai kansa tace,
“kai kallo nan baka da mai ne a jiki da bakasan mace ba? Kaga kalli nan”
ta gwada jawo nononta tana sawa a bakinta tadan tsotsa tana lumshe ido hade da budewa tace,
“haka zakayi,”
bata daddara ba ta sunkuya kansa saitin bakinsa tana me kokarin tura masa nonon yasha sai kace jariri. Wata irin walkiya ce me matukar haske ta gifta mata a cikin seconds ba shiri ta zube a wajen sbd marin ya shegeta kwarai, bata ida jin radadin marin ba taji an damko wuyan ta, tsananin tsoro ne ya sake riskar ta ganin el-bash tsaye a kanta ya damko ta, fuskar nan tasa har wani shining take sbd rashin annnuri, damqa ya mata sosai yana wani irin gurnani marar dadin sauraro, kokarin kwace kanta tayi ta kasa, numfashi ma dakyar takeyi sbd azaba hannayen ta biyu ta hade alamar roko nufinta ya saketa dan babu damar mgn, ko kula da ita beyi ba dan idanun sa ma sama suke kallo, sakina fa taji wuya saiga hawaye na zuba a idanun ta tamkar an bude famfo babu damar ihu bare a kawo mata agaji, bata damu bama a duk yadda za’a ganta ita dai burinta ta kubuta daga wanan shaqa, hawayen ta ne suka fara taba hannayen sa sai nishin azaba take wata irin wujijjiga yyi da ita kafin ya hankada ta can jikin kofa ta daki da murfin kofar ta sake zubewa a wajen. Nannauyar ajiyar zuciya ta saki tana nishi dakyar ta zabura da sauri dan barin dakin, dakyr ta bude kofar sbd rikicewa da tayi, pant dinta a hannu ta karaso parlo, after dress dinta ta saka ta dauki rigar bccin itama a hannu tayi waje a guje cikin karfin hali dan sosai ta azabtu, cikin sanda ta sulala ta kofar baya can ta shige dakinta ba tare da momy ta ganta ba dan tana da tabbacin yanzun momy ta fito.
Jikita sai tsami yake dan wajen data bugu ciwo yake mata sosai ga wuyanta daya sha shaqa dan haka ta shige toilet ta hadawa kanta ruwan zafi dan gasa wajen zuciyar ta kuwa babu abinda take nanatawa sai dana sani na zuwa gun *EL-BASHEER* da tayi, ta kudurta a ranta ko kwadayin sa zai kashe ta bazata sake mararin zuwa wajen sa ba dan Ta kura baqaqen Aljanu momy da kawu sale suka hadashi dashi.
*****
*WANENE EL-BASHEER?*
El-basheer usman tafida kenan da daya tilo wajen haj hafsat da babansa usman, ya taso cikin gata da soyayyar iyayen sa dan shi kadai suka haifa, Alhj usman rikakken dan kasuwa ne dan Allah ya masa Arziki, wannan Arziki shi yaja haj suwaiba step mum din el-bash tayi shige da ficen ta har ta samu auren Alhj usman, tunda sukayi aure bata haifi kowa ba dama kuma bazawara aka aureta ganin bata da da yasa ta nemi izinin Alhj ta dawo da ‘yarta gabanta me suna sakina, umman el-bash tanada mutunci sosai dan bata da wannan kishin na hauka shiyasa ma da wuya kaji bakinta, sabanin haj suwaiba wacce dan arzikin taxo, sai kuma bata samu haihuwa ba bare tayi tunanin gado, wannan abu ya tsaya mata a rai matuka tunda ganan ta dauki karan tsana ta dorawa kishiyar ta dan tana ganin ta fita a komi, harta danta ma bakin ciki take dashi. Batare da wani tunani ba ita da kaninta sale suka bazama wajen bokaye lkcin el-bash baya kasar sbd yanayin aikinsa an turashi chaina bincikenan wani, haka nan alhji usman yana dubai harkar kasuwa, sai jin mutuwar haj hafsa sukayi wanna mutuwa kuwa ta girgiza su sosai.
*El-basheer* jami’in Sirri ne yasan kan aikinsa kwarai shiyasa ma haj take shayin yi masa wani abun dan babu fuska kwata2 a tattare dashi, sakina ‘yarta taso shi sbd ya cika irin namiji da takeso saidai kash bata samu fuskar hakan ba, ba koyaushe zaka ganshi yana dariya ba dan Allah ya bashi zuciya sosai yana da zafi kwarai hatta abokan aikinsa shayinsa suke, ko a wajen aiki idan aka turashi wani waje yana dawowa komai successful dan aikinsa na kyau yasan takan aikinsa, babban burinsa ya kama duk wani me lefi a kasar nan musamman masu shigo da haramtattu abubuwa cikin kasa, kama daga kayan maye har izuwa kan bindigu da en fashi da en kunar bakin wake ke mallaka, babban takaicin sa yadda ya lura yawanci dasa hannun manyan kasa akewa kasar zagon kasa.
Wannan abu na bata masa rai kwarai dgske. Wani muhimmin aiki ne ya biyo masa ta inda ya matukar girgiza gashi ance dole shi zaiyi dan Alqawari yyiwa kasa zaiyi aiki da gsky koda ya biyo ta kansa ne. Wato haj suwaiba zargi ya biyo ta kanta dan haka akeso yyi bincike, yana shirye shiryen wannan aiki, haj suwaiba da qaninta sale da wasu boyayyan yun suka hadu suka kaishi gurun wani qasurgumin boka ya masa aiki wanda ake kira sha yanzu maganin yanzu, dan sun fahimci matukar suna so suyi aikinsu dakyau sai sun batar da hankalin sa dan karma yasa musu ido, hakan kuwa akayi sai wayar gari akayi akaga el-bash cikin hauka tuburan dan gaba1 ya hargitsa part dinsa,yasa kaya a juye can kuma ya dinga buga kansa jikin bango har ya jima kansa rauni yana wani irin gurnani marar dadin ji, wannan Al’amari yyiwa su haj dadi kwarai yanzu aikinsu suke hankali kwance sannan next target dinsu su samu takardun da Alhj usman ya bawa el-bash ana gobe zaibar kasar.
Alhj usman besan da lbrin haukar dan nasa ba sbd shima be cika zama ba sai ya kwashi watanni yana harkar business dinsa tun bayan rasuwar haj hafsa yajin zaman kasar ya gundure shi, kuma yasan yanayin aikin dansa ana turashi aiki inda ba’a sanshi ba yyi watanni ba’aji lbrn sa ba ko a waya ma sbd yanayin aikin Sirri, a zaton sa ma yanzun wani aiki yake tunda baya samun sa a waya.
A wajen aikinsa sun bashi hutu sannan suna matukar tayashi da Addu’ah sosai, Suraj Ahmad frnd din el-bash ne sosai, aikinsu daya shi yake kula da abokin nasa dukda yanayin aiki amma yana samun lkci zaizo wajen sa, sai ya zamana idan bashi ne ya bashi abinci ba duk wanda ya bashi kifarwa yake ya barbaza shi a wajen.EL-BASHEER
Na
Nuceeyluv😘
11-15
Da saurin sa yyi parking a gidan sbd wani aiki daya rikeshi yau sam ya sha’afa be kawo masa food ba, dukda dare yyi kusan 9pm yanzu bayajin zai kyaleshi tunda yasan idan be bashi ba bazaici komi ba Suraj kenan yyi hanyar part din frnd din nasa, kamar yadda yasan zai gani haka yaga parlon komai ya koma upside down aje ledar hanunsa yyi ya fara gyara wajen dama babu me gyarawa idan bashi ne yazo ba, cike da tausayi ya isa cikin dakinsa dake sama, be samesa a dakin ba amma yaji karar zubar ruwa a toilet hakan yasa ya fahimci inda yake, zama yyi yana jiran fitowar sa, ba’a jima ba kuwa ya fito, El-bash yana ganin suraj ya saki murmushi wow ashe haka murmushi ke masa kyau? Har wasu dimples gareshi suna lotsawa ya salam! Abin dai so Masha Allah, fararen hakoran sa kuwa har wani sheki suke sai kace ba mahaukaci ba, suraj ya mike yana masa alama da hannu yace,+
“ka sameni a kasa.”
girgiza kai kawai el-bash yyi batare da yace komai ba.
Kayan bccinsa yasa bayan ya mulke jikinsa da cream hade da turare me dadin kamshi, kai lamarin el-bash akwai abin mmki idan yyi wani abun kamar me lpy wani lkcin kuwa idan ya birkice sai a hankali. Sakkowa yyi kasa nan ya tarar da suraj na jiransa, Suraj ya jawo plate daya dakko a kitchen yana bude ledar dayazo da ita yace,
“Srry na barka da yunwa ba lefi na bane kaji”
yyi mgnr yana kallon sa da murmushi, el-bash dai sai murmushin yake shima duk lkcin daya kasance da suraj baida aiki sai murmushi kamar wanda akayi masa bushara da gidan Aljanna, Suraj kuma tausayin frnd din nasa yake sosai dukda baya amsa masa hakan bazai hana yyi hira dashi ba shima yanajin dadin kasancewa dashi aminai ne na amana matuka, suraj ya tura masa plate din yace,
“bismillah muci,”
nan el-bash ya sake yin murmushi shima yasa hannunsa, nan suka fara cin abincin tare batare da sunce komai ba, can suraj ya sake kallon el-bash yace,
“frnd gsky muna mssn dinka a wajen aiki munyi rashin babban gwarzon jami’i,”
el-bash da ba ganewa yake ba ya sake yin murmushi, suraj duk jikinsa yyi sanyi sam bayason ganin frnd dinsa cikin wannan halin, to amma ya zasuyi? Haka Allah ya tsara, shima suraj din murmushin yake yyi sbd gaba1 tausayi ya lullube masa zuciya ya nisa kadan yace,
“Allah dai ya kawo mana karshen wannan abin Insha Allahu kaine bisa kansu frnd muna tayaka Addu’ah sosai”
yyi mgnr yana kama hannun el-bash ya hada da nasa ya dunkule yana girgiza kansa hade da murmushi, el-bash shima yyi kamar yadda yaga yyi wato ya girgiza kai yana murmushi. Kwashe komi suraj yyi ya mayar kitchen dake plate 1 ne nan ya wanke ya maida inda ya dakko dama ya saba yin hakan, dawowa parlo yyi nan ya samu el-bash ya koma kan kujera ya zauna, suraj ya zauna shima hade da kunna kayan kallo ya kamo tashar kwallo kusan 30mins lkcin 10pm yyi suraj ya kashe komi ya dafa el-bash yace,
“frnd am going,”
el-bash ya danyin murmushi kawai, suraj shima murmushin yyi yace,
“ok gudnyt, take care ok?”
El-bash ya sake sakin murmushi, Suraj ya juya kansa gefe yana kokarin maida kwallar da take shirin zubo masa ace mutum har mutum baida damar walwala? Kai duniya ana abubuwa a cikin ta, kallonsa ya dawo kan el-bash ya danyi masa murmushi yana me daga masa hannu, binsa da kallo el-bash yyi harya bacewa ganin sa.
Lumshe ido yyi yana me sake gyara kwanciyar sa. Suraj yana fitowa yaga alamar an wulga da sauri kamar inuwar wani abu, kunna wayarsa yyi ya haska wajen yaga bega komi ba, dan girgiza kai yyi yana cije lips yace,
_yeah i know, but it’s just the matter of time._ Nan yyi wucewar sa gun motar sa yabar gidan.
STORY CONTINUES BELOW

****
Wanke2 take a hankali tana share kwallar da take zubo mata, ji tayi an kira sunanta “ummiii…” Da karfi, tasan me kiran dan babu me mata hakan sai ‘yar uwarta jamila, juyowa tayi tana me kokarin maida kwallar data sake tarar mata tace,
“na’am.”
jamila tana daga can bakin kofa zaune tace,
“idan kin gama ga wanki na can kiyi min kinsan abinka da amarya sai ana harhada kaya za’a bar gida”
tayi mgnr tana dariya, yaken dole tayi tace “toh,” wata mata ce ta shigo gidan gyalenta a kai tana fadin gafaran kudai, jamila tace, “oyoyo inna ta har kin dawo? Allah sa an dace,” inna na kokarin zama kan takalman ta tace, “kedai bari dakyar hamisu me kujeru ya bani akan zan ciko masa kudin,”
jamila tace,
“kai hamisu akwai son kudi amma ina shiga gidan haruna komai zai wuce,”
inna tana washe baki tace,
“kwarai kuwa ai kin cafki dami a akala wlh yaron arziki”
jamila tace,
“kuma inna karkiso kiga motar sa be dade da siya ba wani dan siyasa ya bashi kinsan shima siyasa yake,”
inna tace,
“ke don Allah?”
Jamila tace, “wlh ai inna kin kusa zuwa hajji dan ina tunanin ya kusa zama gwamna,” inna na sake washe baki tace, “ai kuwa bashi yanzu na fara ci tunda na kusa zama surukar gwamna,” nan suka kwashe da dariya.
Ummi na jinsu zuciyar ta na zafi saidai babu yadda ta iya dan babu me share mata kuka yanzu tasan ta kara shiga maraici sbd rashin iyayenta da kuma kakarta me sonta.
****
*WACECE UMMI?*
Asma’u Ahmad shine cikakken sunan ta, suna zama anan kano unguwa uku iyayenta sun rasu tun batafi shekara 10 ba sanadin gobara daya kamasu cikin dare lkcin ummi nagun kakarta a garko, wannan rasuwa ta girgiza mutane da dama, domin mlm Amadu malami ne me tsoron Allah dan tuni ma ummi er shekara 10 tayi saukar karatun ta, nan wata islamiyya yake koyar wa, Kakar ummi ta shiga tashin hankali matuka dan tana son danta Amadu dukda yana dan fari, saidai yafi kaninsa Sabo kirki, mlm Sabo baida kirki sam ga son abin duniya sosai yake rufe masa ido, lkcin suma suna garko saidai gadi yake a kano gidan Alhji Usman Tafida, dake daki daya ne gobarar ta shafa sai sabo ya roki Alfarmar a bashi aron gidan kar a siyar kamar yadda akayi niyya zai rike ummi dake itama kakar ummi ciwo ya kama ta sbd shiga rudu da tashin hankali ga kuma tsufa, hakan kuwa akayi duk suka tattaro suka dawo kano da zama tare da ummi, shima yana da ‘yarsa kwaya daya me suna jamila ta girmi ummi da shekara biyu.
Ummi tana da siffar ta na hallita Masha Allah, sabanin jamila da ita baka ce gata nan dai daidai gwargwado Masha Allah. Tunda suka tasa sai ya zamana samari na tururuwan zuwa gun ummi, amman dake bata wani damu ba sai bata kula su, wani matashi dake can bayan layin su anace dashi Haruna, shi ya nacewa ummi har itama ta fara sonsa, tiryan-tiryan suka fara soyayya gwanin sha’awa har yana zance zai turo iyayen sa, ummi da wahalar gidan ta isheta dama tun da suka gama secondary babu damar yin gaba yasa tace zata fada a gida, ummi bata sani ba ashe jamila itama na matukar son Haruna kuma ba komi take hange ba sai dan kudin sa sbd ba lefi yanada rufin asiri, lkcin da ummi tayi mgnr zai turo jamila ta girgiza dan ba haka taso ba, caraf tayi dake tana wajen karma su inna su yarda tace sai ki bari ai a binciki waye shi kafin ya turo iyayen sa, ummi batare da damuwa ba tace toh.
Bayan tabar wajen jamila ta zuga inna tana bayyana mata irin arzikin da zasu samu idan ta auri haruna, inna da son kudi tahau kai ta zauna, kawu sabo na zuwa ta gaya masa shima yace ai dole d jamila ya dace dan itace babba dole ta fara aure kafin karama, ummi duk batasan me ake ciki ba sai kulli suke mata, ranar Alhamis da la’asar yazo kamar yadda ya saba yasa yaro a kira jamila, jamila na zaune taji ana sallama da ita, nan ta zari mayafi ta fita tana ganin haruna ne ta washe baki cike d farinciki, Daidai lkcin ummi tazo wucewa tayi mmkin ganin haruna tsaye da jamila sbd yadda yake nuna rashin son tarbiyar ta, da murmushi saman fuskar ta ta karasa wajen tace a’a yaya jamila ashe kinzo ku gaisa yau dai da alama za’ayi ruwa da kankara,
jamila ta watsa mata wani kallo tace ke dakata ya ina hira da masoyi na kice nazo mu gaisa? Wannan wacce irin tmby ce? Baki galala ummi ta saki tana kallon ta ta maida kallonta kan haruna taga yana kada keys din hannunsa hankalin sa bama a kanta yake ba,
Innalillahi wa’inna ilaihin raji’un ummi ta furta tana me kara karasowa wajen haruna tace ka dubi girman Allah ka gayamin meke faruwa wani abin nayi? Haruna ya dago yana binta da wani matsiyacin kallo yace dan Allah malama kija tsummman jikin ki kibar nan wajen duk kin cika mana waje da warin jaba ya karasa mgnr yana me toshe hancin sa,
Hhhhh jamila ta kwashe da dariya tace toh ke kinji warin jaba kike dan haka kibar mana waje kar kisa masoyina ya suma dan warin ki, ummi ta bisu da kallo wasu zafafan hawaye na neman sakko mata sai yanzu ta fahimci komai wato an rabata da haruna? Gudun kar hawayen ya zuba gabansu ta juya da sauri tabar wajen tana me matse kwalla, haruna da take gani taji dadi dan shine kadai masoyin ta a yanzu shima an rabata dashi wannan wacce irin rayuwa ce?
Tana kallo aka kawo kayan jamila, jamila sai iyayi take ana buga qirji za’a auri dan siyasa, yyinda ta bangare guda sun matsa mata akan ta fito da wani ko kuma a bata duk wanda suka so, sosai hankalin ta ya tashi tana fatan Allah ya hadata da nagari kawai dan yanzu kam ta kulle zuciyar ta babu zancen soyayya kuma.EL-BASHEER
Na
Nuceeyluv😘
*srry fans kun jini shiru ko? Wlh wni abu ne ya shamin kai, masu cmmnts inajin dadi kwarai da yanayin cmmnt dinku Allah ya barmu tare😘 masu cewa kwana biyu banyi typing ba to yaudai gashi😁👐🏻 aci gaba da gashi…🤺🏌🏻♀🤾🏻*
16-20
Kwatsam haj suwaiba na parlo taji dirin mota a harabar gidan, lekawar da zatayi ta hango Alhj Usman ne ya dawo, hankalin ta ya tashi matuka dan batayi tsammanin ganinsa yanzu ba, da sauri ta shige dakinta tana haki kamar wadda tayi gudu, Alhj usman ya iso cikin gidan nasa daya dade be samu zama cikin sa ba har zai gifta dake part din el-bash ne farko saiya hango kofar part din a bude, mmki ya kama shi dan yasan duk lkcin da yake gida yana gaya masa to amma tun yaushe yazo? Har zai je part din ya fasa nan ya wuce bangaren cikin gida, shigar sa parlo yyi daidai da fitowar haj daga daki tana yaken dole dan bataso dawowar sa yanzu ba, “sannu da zuwa Alhajina irin wannan bazata haka?”+
Alhj yyi murmushi yana zama kan kujera yace,
“kai haj ko bakiyi farinciki bane?”
Haj ta sake fadada murmushin ta tace, “haba ni na isa? Ai yanzu haka da kke gani nafi kowa farincinkin zuwan ka,” ta karasa mgnr tana me aje masa ruwa da lemo data dakko a fridge, Alhj usman yasha ruwa yyi hamdala yace, “wai yaron nan yana gari ne? Naga kamar part dinsa a bude,”
wani qullutun bakin ciki ne ya tirnike haj suwaiba kamar ta tashi ta shake shi ta huta da takaici haba ace mutum baida aiki sai son yaron sa? Komai zaiyi dansa shine first kome yake el-bash, zance yake el-bash sai kace wani dan gwal…..!
“Kinyi shiru kin zuba min ido hala baki gane me nake nufi ba?” Yyi mgnr yana son karantar yanayin ta, cikin sauri haj ta sauya yanayin ta Alamar tausayi hade da kokarin matso kwallar karya tana karya murya tace, “wlh Alhj bazaka gane bane bayan tafiyar ka mun shiga mummunan tashin hankali wlh”
“Subhanallah”
Alhaj ya mike daga kishingiden da yake yace “fito fili ki fadamin meke faruwa wani abu ya samu dan nawa?” Wani takaici ya sake rike haj Amma ta danne tana share kwalla tace, “wata rana ne el-bash ya dawo yazo nan ransa a matukar bace idonsa yyi ja sbd bacin rai ganinsa a haka hankali na ya tashi nace yarona meya sameka? Sai cewa yyi rikici ne ya hadashi da wani inyamuri yana mgn rai a bace yace wai dan yaga Allah yana bashi ci gaba ashe inyamurin haushin sa yakeji shi el-bash be sani ba, saida dan rikicin ya hadasu mutum budar bakinsa yace wlh sai kasan kayi fada dani zaka gani ka jirayi sakamako, shine fa ran el-bash ya baci yana gayamin yace har akwai wani bil’adam dazai tsoratani? Wlh duk abinda yake ji dashi zan sauke masa ba inyamuri ba ko shine dangin Aljanu be isa yamasa abinda Allah be masa ba.”
ta karashe mgnr tana me sake rushewa d kuka.
A razane Alhj usman yace, “da suka samu sabanin wani abu ya masa?” Haj tana girgiza kai kukan karya yaci karfin ta tace, “kasan inyamurai akwai tsafi toh bayan kwana biyu sai muka tsinci jin wata kara a bangaren sa muna zuwa muka ga ya hargitsa komai na parlon sa a takaice dai babu alamar hankali a tare dashi.”
murya na rawa Alhj usman yace, “kina nufin *HAUKA* Yake?”
Haj tace,
“Eh”
cikin muryar kuka.
Alhj Usman be sake sauraran ta ba ya fito daga dakin cikin sassarfa yyi bangaren dansa el-bash hankali a matukar tashe. Fitarsa keda wuya haj suwaiba ta kwashe da wata iriyar dariya tana tafi tace, “ai wlh haka ‘yan film suka ganmu suka bari wajen hada drama idan nice har abada ta bunnu kenan bazaka san gskyr lamari ba” tayi mgnr tana sake sakin dariya ta leka ta windo ta hango yana shiga part din ta tabe baki tace, “kaima a sannu zan maidaka wata halittar matukar naga zaka batamin lamari.”
STORY CONTINUES BELOW

****
A zaune ya sameshi ya mimmike kafa yana cilla ball to dama yakan taba kwallo a duk sanda ya samu dama shiyasa hannunsa a murde yake irinnna majiya karfi, to yanzun ma cillata yake sama yana ta dariya shi kadai sbd suraj ne ya dakko masa ya aje a parlon duk lkcin daya ganta sai ya dauko yyi ta wasa da ita tunda ya lura baya zuwa gun motsa jiki dake wani daki a part din nasa.
Kadan ya rage Alhj usman ya fadi sbd shiga firgicin abinda ya gani, “Innalillahi wa’inna ilaihin raji’un” Alhj usman ya fada yana me karasawa kusa dashi ya rungumo shi jikinsa, kamar kuwa el-bash ya sani yyi lamo a jikin baban nasa, Alhj usman yana shafa bayansa hawaye na wanke masa fuska yace, “tun yaushe kke cikin wannan halin? Wacce irin jarabawa ka tsinci kanka a ciki? Innalillahi Wannan tafiya tawa batayi min rana ba dole a samo mlmi yyi maka Addu’ah nima kuma zan tashi tsaye, duk wanda ya maida ka haka Insha Allahu zaiga sakayya domin Allah ba Azzalumin kowa bane sai wanda ya zalunci kansa.”
Yyi mgnr yana sheshsheqar kuka kamar ba babban mutum ba yana matukar son dansa shi kadai ne dansa Allah ya bashi yau ga halin tilon dan da yake ciki.
Suna haka aka bude kofa Suraj ne ya shigo da ledar abinci hannun sa kamar yadda ya saba, Alhj usman ya dago yana kallon me shigowar, ganin suraj ne yace,
“Suraj ashe abinda ya samu abokin ka kenan? Shiyasa fa nake masa fada ya rage zuciya domin wata zuciyar bata da amfani ba komi ake tankawa mutane ba domin shiru ma amsa ne dan wasu hanya kawai suke nema suga bayanka.”
Suraj ya sunkuyar da kai cike da tausayin Abba yace, “hakane Abba Insha Allahu zai samu lpy,” Abba yace, “yauwa kai kasan mutumin da suka samu sabani da el-bash?” Cikin rashin fahimta suraj yace,
“wa kenan?”
Abba yace, “inyamurin dayace zaiga bayansa,” suraj ya juya yana kallon el-bash lkcin el-bash yana lankwasa hannunsa ne yana wasa dasu hade dayin murmushin daya saba, Kana ya dawo da kallon sa kan Abba yace, “dama ya samu matsala ne da wani?” Abba yace, “haj tace matsala suka samu da wani inyamuri” suraj yace, “yaushe?”
Nan Abba ya kwashe komi yadda haj tace ya fada masa. Suraj ya tsurawa El-bash ido lkcin su yake kallo yana murmushi fararen hakoran sa na shining, suraj ya sauke ajiyar zuciya me karfi kafin ya lumshe ido ya bude yana kallon Abba a yanzu yace, “gsky bansan hakan ya faru ba kasan el-bash wani lkcin akwai zurfin ciki sai ka kasa gane ina yasa gaba, amma tunda haka ne zamu sake zage damtse da Addu’ah da kuma kama duk wanda keda hannu a ciki.” Abba yace, “karka damu suraj zan nemo wani babban malami dana sani yyi masa Addu’ah Insha Allahu za’a dace.” Suraj yace, “hakan muke fata koda yaushe a samu Nasara.”
Ledar hannunsa ya tura gaban el-bash yana budewa yace, “bismillah food.” El-bash yana murmushi ya dauki spoon ya tsaya, suraj ya sauke dan ya gane so yake suci tare, Abba da kansa ya kulle yace, “ya naga ka siyo masa abinci baza’a karbo masa na gida bane?” Suraj yace, “wlh Abba bayacin kowanne abinci idan ba nine na bashi ba, duk wanda ya bashi kifarwa yake ya barbaza a wajen.”
Wani irin tausayin dan nasa ya sake kamashi ga kara son suraj da yaji a ransa yaron yanada kirki kwarai, wannan shine aboki na amana ya tsaya maka a duk halin daka tsinci kanka shiyasa yake yabon sa domin yaron yanada kirki, Abba ya nisa yace,
“toh yanzu kullum sai kazo ka bashi?” Suraj yace, “kwarai kuwa ko na sha’afa bana kwanciya sai nazo.” Abba yace, “na gode sosai suraj Allah yyi maka Albarka Allah ya baku mata na gari.”
” Ameen Abba”
ya fada yana sunkuyar da kai sbd kunya. Abba yace, “amma wannan aikin kamata yyi ace mutum na kusa dashi sbd ko wani abu zai sameshi cikin dare za’a sani, Allah ma yyi haukar bata fita waje bace.” suraj yace, hakane naso na dawo ma nan gaba1 to abubuwa ne suke min yawa shiyasa ban dawo ba sbd yanayin aikin mu.”
Abba yace, “ina tunanin Aure zan masa sai a samu me taimaka masa tunda babu kowa….,”
wani irin tari el-bash ya fara yi tultultul…, sosai ya kware yana shidewa idanun sa sunyi ja, Suraj ya mike da sauri yace, “Abba na manta ban kawo ruwa ba.” nan ya dauko ruwan ya tsiyaya masa a cup har lkcin tarin be tsayawa el-bash ba, shi kansa Suraj tarin ne ya rikeshi yanayi tultultul, da sauri ya sama el-bash ruwa a baki shi kuma ya kafa robar a bakin sa, Abba sai sannu yake musu ya rasa gun wa zaije sai kawai ya sa hannunsa biyu yana shafa bayansu, dakyar tarin ya sake su suka koma haki, suraj ya sunkuyar da kansa yana kokarin danne tarin sa yyinda shi kuma el-bash idonsa suka kada sukayi jaa sbd yafi suraj shakewa. Cike da tausayi Abba yaci gaba da shafa bayansu har suka nutsu kafin ya mike yace zaije ya dawo dan saukar shi kenan. Suraj ne yace, “to Abba a fito lpy.” shi kuma el-bash yabi bayan Abba da kallo.
****
Da dare suna zaune da haj Alhj usman ya shiga zurfin tunani yana tunani a halin da dansa yake ciki wazai bashi ‘yarsa ya aura? Kai abin da kamar wuya, tunowa yyi haj nada yarinya kuma tabbas yasan zata rufa masa asiri tunda itama tasan kan lalurar kafin dai yaron nasu ya samu lpy..!
“Haba Alhj inata mgn kayi shiru.”
haj suwaba tayi mgnr tana kallon sa, Alhj usman ya sauke ajiyar zuciya yace,
“haj matsalar yaron nan ke damuna kwarai dgske na rasa ya zan kwatanta miki damuwar a mizani”
haj fa an tabo mata abinda tafi tsana, sosai ta danne bacin ranta tace, “ai alhji sai hakuri ni kaina idan na ganshi bakaga yadda hankali na ke tashi ba cike da tausayi ace mutum har mutum a fili kamar me hankali Amman a badini mahaukaci kai wannan abu da ciwo yake,”
Alhj usman ya sake gyara zama yace,
“shiyasa nake tafe da wata Alfarma nasan zaki sharemin hawaye,”
haj tace, “haba ai an zama daya Alhj menene kke nema yanzu na aiwatar maka dashi?” Alhj yyi murmushin jin dadi yana hango nasara a zancen yace, “gani nai tunda an zama dayan mezai hana mu kara kulla danqon zumunci?” Haj tace, “ban fahimceka ba.”
Alhaj usman yace, “mezai hana a hada ‘yarki sakina da yarona aure? Inaga yin hakan zaisa yaji dadi idan yana kallon wani kusa dashi kuma kinga mace tafi dacewa ta zauna a wajensa.”
~~~Tashin hankali wanda ba’a sa masa rana haj ta fada a ranta qirjinta na dukan uku2 a hanzarce tace,
“haba ai sakina ta samu miji dan har yaje wajen ubanta ya basu dama kuma Alhamudulillah suna son junan su, nima nayi irin wanna tunanin naka sai naga ta shaqu da wancan, amman mezai hana muyiwa sabo me gadi mgn? Naji kamar yanada yara mata shima yanada kirki sai ya bamu daya a ciki.”EL-BASHEER
Na
Nuceeyluv😘
21-24
Alhj usman yace, “kina ganin me gadi zai yadda ya bada ‘yarsa wa mahaukaci?” Haj ta sauke nannauyar ajiyar zuciya a boye ganin dabarar ta tazo mata da sauki tace, “sosai ma kuwa karka wani damu zan tmbyr maka shi.” Alhj usman ya numfasa yace, “toh shikenan Allah yasa hakan yafi Alkhairi.” “Ameen” haj ta fada tana murmushi dan sosai tayi farinciki komai yazo mata da sauki. A haka dai suka canja wata hirar.
~~~
Da saurin sa ya karasa jikin kofar yana knocking, haj dake zaune tace “waye?” Sabo gateman yace, “nine ranki shi dade kince nazo yanzu sakina ta fadamin da zata wuce” ya fada yana karya murya, haj ta tabe baki tace, “kana iya shigowa,” sabo me gadi ya isa parlon nata ya zube a wajen yana fadin, “hutawar ki lpy hajjaju makkatu ai daga ke ba qari kece kawai Ta Alhji fitilar gidansa.” haj ta lumshe ido tana me jin kanta na kara girma shiyasa takeson harka da sabo dan yana kuranta ta sosai, cike da izza tace, “ina tafe da wata mgn ne sabo saidai ban sani ba ko zaka yadda” sabo yace, “haba wane ni, Nidin banza ai kan kice ma na yadda dari bisa dari.” dan murmushi haj tayi tana me jinjina kwadayi irin na sabo tasan zai yadda ma sbd tsananin kwadayin sa da son abin duniya, tace, “naji kamar kace kana da yara mata ko?” Sabo yace, “kwarai kuwa dayar ma nan da sati za’ayi aurenta sai karamar bata samu miji ba shine muke fata ta samu a hada bikin a huta.” haj tayi murmushi wato komai yana tafiya nrml, tace, “idan ba damuwa so muke ka bamu dayar a hadata aure da yaron Alhj kaga baida lpy kula dashi sai mace kafin ya samu sauki,”+
wani irin farinciki ne ya mamaye sabo yana washe jajayen hakoran sa yace, “kai wannan abu da dadi yake yaushe zanki jinin ku haj? Ai kowa baya wuce kaddara fado masa idan wannan ne na yadda dari bisa dari kamar yadda nace tun farko.” haj a ranta tace, _tasan za’a rina._ yyinda kuma a zuciyar sabo yana farinciki zai samu dukiya matukar ya hada ummi da mahaukaci ai ko bata so dole ayi shidai ya samu kudi ko banza za’ace masa surukin Alhj Usman…., haj ta katse shi da fadin, “duk yadda mukayi da Alhj zakaji kana iya tafiya,” sabo baki har kunne yace, “toh..toh..toh.. Madallah a huta lpy.” Nan yabar ta a parlon.
Wayar haj ce tayi ringing dauka tayi tabar wajen tana me shigewa dakinta ta kulle, kafin tace, “Allah ya taimaki manyan gari da fatan kana lpy,” daga dayan bangaren akace, “Gari lpy haj kwana biyu baki leko ba lpy?” Haj tace, “kaidai bari Alhj Rabe megidan ne ya dawo shiyasa ka jini diff,.” Alhj Rabe yace, “ya kamata ki leko fa dan kaya sun iso dakyar ma muka samu suka iso garemu kinsan kasar yanzu an tsananta tsaro,” haj tace, “aiko dole nazo kamar yadda na saba ko yana gari, zan biya ta wajen Na’omi muzo,”
“That’s gud,.” Alhj Rabe ya fada, nan dai suka katse wayar.
*****
“Saude…Saude….” Da hanzarin ta ta fito dankwali a hannu tana kokarin daurawa tace, “lpy sabo naji kana zugamin irin wannan kiran?” Sabo yana kokarin zama kan tabarma yace, “kedai zauna na baki lbrin abinda ke tafe dani,” Inna saude ta zauna tace, “ina jinka,” sabo yace, “Arziki ne ke bibiyarmu saude,” “kai dan Allah?” Inna ta fada tana washe baki, sabo ya girgiza kai yace,
“kinsan yaron nan dan gidan Wanda nakema gadi?” Inna tace, “ni ina zan sanshi? Nasan dai me damara ne,” “Yauwa to shi kinsan yana ciwon hauka ko?” Inna tace, “kwarai kuwa ya warke ne?”
Sabo yace, “inaaaa sai abinda yaci gaba ma, to shine uban yaron daya dawo yaga halin da dan ke ciki ya yanke shawarar yyi masa Aure.”
“A haukan?” Inna ta katse shi da mgn tana zaro ido, sabo yace, “kwarai kuwa a hakan,” Inna tace, “wanne marar hankalin ne zai aurar da ‘yarsa ga mahaukaci?” Sabo yace, “ke dallah ana ga gabas kina ga yamma ki tsaya ki saurara mana,” Inna tace, “toh ai lbrin kane banga inda ya hadu da bayanin farko ba wato arziki na kiranmu,” sabo yace, mutanen gidan suka nemi na basu ‘yata ya aura kafin ya samu sauki,’
“kan ubancan.”
inna ta mike tana rike qugu tace, “bansan cewa ka fara sakin layi ba sabo sai yanzu, kai son duniyar taka har yakai ka bada jamila ga mahaukaci?” Sabo yaja tsaki Mwssstt, yace, ‘dadina dake bakyacin ribar zance iya jamila ce ‘ya a gidan nan?” Sai a lkcin hankalin Inna ya kwanta ta sake zama tana rage murya tace,
‘Ummi zaka basu?” Sabo yace, “toh dawa ta dace idan bashi ba.”
£Ahayye ayyuriyuriiiii….” Inna tasa guda bakinta har kunne tace, “kai shiyasa nake sonka sabo kanada basira ni wlh gaba1 na mance da itan ne kasan sha’anin biki ya matso kusa abubuwa sunyi yawa.” Sabo yana murmushi yace, “toh atakaice dai zuwa wani satin harda ummin za’a yiwa auren da yaron nan mahaukaci,” Inna ta sake yin shewa tace, kai amma baka tabamin Albishir me dadi ba sai yanzu,” dariya sabo yyi yace, “ke kika sani.”
~~~
Wannan shine sumanta na uku tana farfadowa sbd tsananin shiga tashin hankali da firgici, ta kara tabbatarwa lalle bata da wani sauran gata a duniya domin wanda take kallo a matsayin ‘yan uwanta sun koma makiyan ta, yo idan ba makiyi ba waye zai baka mahaukaci kana da lpyr ka? Ina ma aka taba aure da mahaukaci idan ba kaima baka da hankalin ba……”
“Kozaki mutu wlh sai kin aureshi” cewar sabo yana tsaye kan ummi da tunda suka sanar mata ta suma sbd tsananin firgici, wani irin hawaye ne me radadi suka sirnano mata a kumatu, dakyar ta mike zaune daidai lkcin kuma jamila ta kwashe dawata mahaukaciyar dariya harda hawaye tana fadin, “su o’o da angonta mahaukaci tab gsky zanga yadda za’a kaya zama da marar hankali hhhhh…” ta sake kwashewa da dariya inna na taya ta, sidaf ta mike ta shiga daki domin ji take wani quntullun abu me nauyi ya tsaye mata a kirji ta lura matukar taci gaba da zama tare dasu zata gamu da ciwon zuciya.
****
Tunda sabo ya amince sai shirye2 ya kankama, both bangaren Amare da Angwaye, yyinda Ango el-bash besan wainar da ake toyawa ba, saidai frnd dinsa suraj ya shiga lamarin bikin dukda ransa a jagule yake tamkar shi za’ayiwa auren sam baya maraba dashi, yasan yanayin abokin nasa badan halin daya tsinci kansa ba ai mace sai wacce yaso bare ma mata nawa ne suka nuna sonsu gareshi? Shidai da yanada iko tabbas da ya hana Abba bikin nan toh Amma ya zasuyi? Haka Allah ya tsaro abin zai kasance cikin Shirin su.EL-BASHEER*
_Wannan page din naku ne Mrs Tajuddeen tajra😍 da ummi zubairu😘inajin dadin yadda kukemin cmmnts Allah yabar kauna Ameen🥰_
Na
Nuceeyluv😘
25-28
Sale qanin haj ne zaune a parlon hajiyar suna mgn yace, “gsky haj na gaji da gafara sa banga qaho ba, koyaushe kice baki samu dama bane yaushe kikeso damar ta zo ne? Nifa wlh idan bazan samu kudin nan ba sai na tura abokai na su kashe mijin naki idan ya mutu ai dole a baki gado mu tattara dana dan nasa tunda ba hankali ne dashi ba muyi gaba” haj tace, “kaifa sale azarbabin ka ya cika yawa ance maka haka kawai ake kashe babban mutum batare da an shirya ba?” Sale yaja tsaki “to ke yaya ai naga abin naki ne kina sanyi-sanyi ni kuma komai da zafi-zafi nakeso,’ haj tace, “so nake wannan bikin daya baro mana na samu ayishi, kaga ko a harkar bikin nan ya sakar min bakin aljihu komai nace bani yake ko ita yarinyar akwati uku nasa akai mata sauran kudin 12 da yace ayi na makale ga sauran wasu hidimar dukfa ana samu.” sale yace, “nidai kin sanni bani da kyau, ana gama bikin mu aika shi.” haj tace, “ina tunanin wata shawarar idan nayanke zan gaya maka,” Sale yace, “yanzu naji mgn, ina ganalalliyar yarinyar nan ta tafi ne?” Haj ta hade rai tace, “nifa matsalata dakai kenan kushe min ‘ya, yanzu kuma me tayi?” Sale yace, “koma dai menene ki tmbyeta matsalar ku ce kinga tafiya ta saidai kafin na wuce miko min wasu kudin na samu na sigari.”
haj ta bude pos dinta ta cillo masa kudi tace, “aikin kenan mtwss” dariya sale yyi yace, “kardai ki zafafa akwai yarinya akasa,” haj ba tare data fahimci me yake nufi ba tace, “kaga ni jeka sai na kira ka,” sale yace, “ko bakice bama tafiya zanyi.” nan yyi ficewar sa.
+
***
Alhj Rabe ne ya kira haj daidai lkcn ta fito mota ta dawo daga unguwa, “Hello ina jinka Manyan gari” Alhj rabe yace, “karki manta akwai meeting da za’ayi nan da two weeks” daidai lkcin da zata gifta ta gefen part din El-bash tace,
“oh har ansa ranar meeting din?” Alhj rabe yace,
“eh akwai sabbin mutane ma da muka samu wanda suka kware wajen satar yara musamman en makaranta da ‘yan mata” Haj tayi murmushi tace,
“kai kace wannan karon Oga kwata-kwata zai halacci wajen…..” Diff…tayi shiru sbd hada ido da tayi da el-bash dake jikin window parlon sa ya nade hanayen sa a qirji fuskar nan babu alamar Annuri.
A tsorace ta saukar da wayar hannunta, saurin karasawa tayi jikin windon sai taga still direction din data bari yake kallo tana waigawa kuwa taga wata tsuntsuwa ce ta sauka tana dan yawonta a hankali kamar yadda tsuntsaye keyi idan sun sakko kasa, wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki tana jan tsaki
“ashe ma bani yake kallo ba,” tayi mgnr a fili, saidai wata zuciyar tata tace,
_”kamar fa itan yake kallo tun farko da alama, sai kace me hankali yana sauraron ta_
“Kai Amma kuwa dana shiga uku dan babu wanda yasan ina suke haduwa da kuma asalin waye ogansu na kungiya, kungiyar da jami’an tsaro sukayi mata caa suna neman ta ruwa a jallo sbd illar da sukema kasa da kuma mutanen cikinta…,
a razane ta sake juyowa tana kallon sa sbd tabar inda yake, sai kuma still taga direction din dazu yake kallo dan tabe baki tayi toh ni meyasa zan damu mutumin ma da bashi da hankali? Ko yaji ma yasan me nakeyi?
__Kinsan kuwa da da Hankalin nasa da kin muku babbar barna dan nemanku ake wanted wani irin bugawa qirjinta yyi sbd tunowa da wanene *EL-BASHEER* Jami’in Sirri na kasa, badan ta masa aiki ya haukace ba da tuni ya kamasu.
Da wannan tunanin ta karasa parlon ta.
Tana shiga ta tarar sakina a kwance kan kujera tana kallo, haj har ta zauna sakna batace mata komi ba, haj tace, “ke bakiga shigowa na bane?” Sakina ta da gyara kwanciyar ta tace,
“toh ni momy me zance?” Haj suwaiba tace, “ke kul baki kiyayeni ba wlh, ke banda rashin sanin ciwon kai me zakiyi da mahaukaci?” Na lura tunda kikaji lbrn auren sa kike ta kunci toh gwara ma tun wuri ki cireshi a rai ko kitattara ki koma gidan ubanki can kauye.”
Sakina ta mike zaune tana tura baki tace,
“nifa bawai ina sonsa bane kawai dai zan zauna dashi ne har na tayaku neman dukiyar sa,”
haj suwaiba tace, “dallah rufemin baki wawiyar banza, ai ko a wasa bana fatan kiyi aure d mahaukaci bare kuma dgske, dukiyar sa kuma ke zaki ce mana ga yadda zamuyi? Kul baki kiyayen ba.”
sakina ta mike tsaye tana dira kafa irin na tabararrun yara tace, “ai shikenan momy ni na hakura dashi tayi mgnr tana wucewa dakinta.
Haj suwaiba ta dafe kanta daya sara mata tace, “haba yarinya daya kina neman jazamin bala’i Mtwss tayi tsaki tana gyara zaman ta.
~~~~~
Ummi har wata irin rama tayi sbd tashin hankali, lkcn da aka kawo akwatin ummi guda uku taga en habaici da tashin hankali, kowa saida ya fadi ta bakinsa ana wannan akwati ko bazawara iyakaci kenan, abin nema ya samu gun jamila da qawayenta, nan suka saka ummi gaba da dariya kowa yazo za’a jawo akwati a nuna masa ana shewa, kowa yaga alamar inda ummin zataje ma ba zaman jin dadi zatayi ba, toh zama da mahaukaci ma ina yaga dadi? Kowa da abinda yake fada, unguwa kowa ya dauka ummi mahaukaci zata aura, mutane sai dariya ake mata musamman wasu da suke kallon ta a matsayin me girman kai sbd ba kula kowa take ba daga mazan har matan shiyasa abin yai mata yawa, kadan ne tsirarai masu tausaya mata. En Mata dayawa sunci burin rakiyar ummi dandai kawai suje su gano Ango mahaukaci, dan tabbas sunsan yana cikin qazanta da wari, ita kanta jamila amarya cewa tayi sai taje rakiyar ummi ta gano Ango mahaukaci, Ummi banda kuka ba abinda take, gaba1 ta zuqe ta lalace.
****
Yau ta kasance juma’a Rana me Albarka ranar da ake daurin auren ummi da el-bash, karfe 2pm za’a daura, dake a yanayin rashin lpy yake Ango sai Abba be wani yi taro dayawa ba.
Tun karfe daya Suraj ya kawo wa el-bash sabon dinkin sa daya sha aiki, tunda ya aje kayan el-bash be kalli inda suke ba, Suraj ya masa kwatance da hannu Alamar ya saka, el-bash yyi banza dashi, Abinka daya saba koyaushe kananun kaya zaka ganshi dashi, dakyar Suraj ya sashi dole ya canja kaya, qasumbar ma ba’a rage ba dan ki yyi, kamo hannunsa suraj yyi da nufin su fita suna zuwa daidai kofa ya tukare, Suraj yace,
“muje,”
el-bash ya hade fuska sosai yaki fita, Suraj ya dafe kansa ya tuna tabbas tunda el-bash ya fara hauka be kara fitowa waje ba, Dabara suraj ya sake masa akan ya fita nan ma yaki, saida Abba zai wuce ya hango su, nan yazo da saurin sa yace,
“lpy suraj baku fita ba?” Suraj yace,
“wlh Abba tun dazu nake fama ya fito yaki,” Abba ya kamo hannun El-bash yace,
“muje,” sai a lkcn ya fito, har bakin mota Abba ya rakasu sannan ya tabbatar ya shiga mota kafin ya barsu, suraj ne ya zaga dayan gefen ya shiga, sai security abokin aikinsu me suna Musa yaja motar, sauran frnds dinsu suka biyosu a baya.
Koda akaje wajen daurin Auren ma kin fitowa yyi, bare yaga jama’a sosai sai ya makale a mota, duk yadda akaso ya fito ki yyi sai hakura akayi, sauran mazan unguwar su Ummi ba haka suka so ba, gsky sunso suga mahaukacin ummi Amman yaki fitowa ga motar baqin glass ne bare a hango shi, dayawa abinda ya kawo su kenan sai basu samu yadda suke so ba.
Gyaran murya me sanarwa yyi, kafin ya fara cewa A wannan rana ta juma’a Ana daura Auren Asma’u Ahmad (ummi) da Angon ta El-Basheer Usman Tafida akan sadaki dubu Dari. Nan aka fara kabbara Ana murna aure ya dauru, dayawa wanda suka zo gulma sun cika da mmikin jin kudin da aka biya sadakin ummi, yyinda jamila da Angon ta Haruna akan sadaki dubu talatin. Kowa ya rude da zance sai kace nace ake.
Ummi dake jiyowa ta sake fashewa da kuka, yanzu kuma ta fahimci ma sayar ta akayi tunda aka biya wannan uban kudin, Allah sarki ita kuma haka tata kaddarar rayuwar tazo kenan sayar da ita za’ayi.
Sauran mutanen gida sai maida zancen sadaki ake, ba haka jamila taso ji ba, taso ace a sadakin ma tafi ummi, saidai bata sani ba ko a lefen ma ummi ta fita nesa ba kusa ba dandai haj suwaiba ta rage ne.
Haka dai akaci gaba da shagalin biki, Abba yace yanaso a kawo Amaryar a ranar, hakan kuwa akayi bayan sallar Isha aka fara shirye2 kai Amarya ummi wacce ta hade cikin lace dinta daya daga cikin na akwatin ta, dinkin dai gashi nan dai, sai gyale da aka yafa mata, zugar mutanen da suka shirya dan zuwa kai Amarya Allah yai yawa dasu, kowa so yake yaje yaga dakin ummi da mijin nata, ummi dai takaici ma ya hanata cewa komi haka dai take binsu kamar jela.
Motocin da akazo daukar amarya ma Abin ba’ace komi dan kuwa Abba mota ya bayar aka tafi kwaso masu kawo amarya, besan meyasa ba haka kurum yaji 100% auren ya kwanta masa. Masu niyyar zuwa kuwa sunyi murna dan kuwa an samu abin hawa. Yyinda a bangaren su Suraj abin ba’ace komi harka ce ta iyaye babu yadda zasuyi auren ma ba farinciki suke dashi ba bare kuma a tura zugar motoci kamar za’a dauko Sarauniya, Tabbas da El-bash a yadda yake ne da bazai taba auren ‘yar me gadin gidansu ba.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
*I’m so sorry my fans nasan kunsha jirana dukda nace amin uzuri amman nasan kauna ce tasa still anamin mgn prvt naci gaba, to ga el-bash ya dawo zamu ci gaba da gashi…*🔥🔥
_WANNAN PAGE DIN SADAUKARWA CE GA DUK WANI ME BIBIYAR EL-BASH_
29-30
Har cikin gidan aka shiga da motocin abinka da taron mata sai ihu ake ana guda, nan dai aka kamo hannu ummi akayi bangaren El-bash da ita.
El-bash tunda ya dawo ya cire manyan kayan dake jikinsa ya sauya kanana kamar kullum, zama yyi ya harde kafa daya kan daya ransa a matukar bace sai lankwasa yatsun hannun sa yake, tun kafin yabar gidan ransa yake bace har kawo yanzu Yana a wannan yanayin aka kawo amarya.
Masu kawo amarya sai gulma ake ana yau za’a ga mijin ummi mahaukaci, jamila ce kan gaba wajen bude kofar parlon ta tsoma kafarta ciki, wanda suka rike amarya na biye, kafin ummi tasa kafarta ciki saida tayi bismillah, sannan sauran en baya aka shigo yuuuu…., jamila da tayo gaba tayi turus ganin mutum a zaune fuska a daure, sauran ma da suka shigo tsaye sukai, jamila tayi matukar girgiza da ganin el-bash da tayi, ba haka taso ganin sa ba, kai anya wannan handsome guy din shine El-basheer mijin ummi? Wata kawar jamilan ce da suka shigo daga baya tace, “yadai jamcy kinyi shiru ko bakiga mahaukacin bane?” Jamila tayi saurin wayancewa ta kwashewa da dariyar yake tace,
“kedai bari sailuba ai ban zaci haukar takai haka ba, wannan irin kasumba kamar an shuka ciyawa,”
nan sauran jama’ar aka kwashe d dariya, ummi dai wani qululun takaici ne ya kulle mata a qirji, wai ace mijin da take aure yau shi aka zagaye ana kallo kamar wani sabon halitta?
Basu dade ba suka fara tafiya dan raka jamila, jamila dai har suka bar gidan tana juya abin a ranta, sai kullawa take tana kwancewa, babban tashin hankalin ta ma shine yadda taga ana barin gidan aka koma yaba kyau da tsari irin na halittar el-bash.+
Kowa anan ya barta a tsaye sanye da lullubi tana kallon kasa, ko sanin fuskar wanda aka daura matan ma batayi ba,
ganin sun watse yasa ta zauna nan tsakiyar parlon tana jiran ikon Allah dan batasan mezai faru ba nxt, kanta ta kifa tana ci gaba da share kwallar da taki tsaya mata tuntuni,
Oga el-bash kuwa yadda aka shigo aka same shi, haka aka tafi aka barshi dan babu abinda ya canja baya ga rashin annurin sa daya karu.
Kwas…kwas…kwas…ummi dake zaune ta fara jin takun takalmi, kirjin tane ya bada wani dam…kafin tayi wani tunani taji anja wani wawan tsaki, Sakina ce ta shigo tana tauna chewing gum, kafin ta fisge gyalen ummi, ummi tayi saurin dukar da kanta sakina ta sake jan tsaki a karo na biyu tace,
“ke dan ubanki warning nazo na miki tun wuri dan haka ki bude kunnen ki kiji, wasu zafafan hawaye ne suka sake wanke fuskar ummi yau ga ubanta dake kabari an zagesa batare da tayi lefin komai ba,
sakina taci gaba tace, “kina mgn ne da Sakina matar da el-bash zai aura idan ya samu lpy, tun wuri kiji dawai ban yadda ki bada kai ga mahaukacin nan ba, dukda nasan zai tsaremin kansa amma ki sake kula, kada maitar ki ta tashi kiyi masa fyade….
_Yah Subhanallah_
ummi ta furta jikinta na rawa sai a lkcin ta bude ido tana kallon sakina, bakinta narawa tace, “ni wlh anti ko yanzu ma kikeso ki gaya masa ya sakeni banason wannan zaman ki taimaka.”
Sakina ta tabe tana murmushin gefen baki na mugunta ta kalli el-bash dake bayan ummi dake ta juya masa baya, tsurawa pink lips dinsa ido tayi tana lashe baki ta lumshe ido kafin ta dawo da kallon ta kan ummi data sunkuyar dakai kasa tace,
“matukar kika kiyaye sharuda na zaki samu sakin ki a hannu yana samun lpy dan ba irinki yake da burin aure ba,”
ummi ta girgiza kai tana share hawaye, Sakina ta mike tsaye tana tauna chewing gum tace,
“Good.”
Sake kallon el-bash tayi taga yanzu ita yake kallo sabanin da dayake kallon wani directon wani irin durar ruwa cikin ta yyi ganin yadda fuskar sa take a matukar hade, ko second bata kara ba tabar parlon da sauri.
da ummi zata lura da ita tabbas data hango tsantsar rikicewa da rudewar da tayi. jawo gyalenta kawai tayi ta lulluba.
Ba’afi minti biyar ba sai ga haj suwaiba ta shigo parlon ita d wasu frnds dinta, ummi najin su batace komai ba, wata kawar haj ana ce da ita sahaba tace, “hajjaju masu surukai,” haj suwaiba ta yatsina fuska tana zama kan daya daga cikin kujerun paron tace,
“sahaba kenan ina kika taba jin aure da mahaukaci? Ai wanda ya aureshin ma shima tababben ne,” sauran suka sa shewa wata tace, “kinsan aikin masu gidan rana yanzu sai ya maidaka marar hankali,”
haj ta dan ja tsaki tana kallon ummi da kanta ke duke kasa tace,
“ke baki iya gaida manyan ki bane?” Ummi da tun dazu qirjin ta ke dukan uku2 bakinta na rawa tace,
“ina yinin ku,”
“mwtsss”
haj taja tsaki tace, “Alhj ma dasa kai wahala yake ko mene amfanin wannan auren oho,”
tayi mgnr tana juyawa direction din da el-bash yake, yanzu kuma kansa duke yake yana matsa hannun sa, juyo da kallon ta kan ummi tayi tace,
“yadda makwadaitan iyayen ki suka ji suka gani wajen baki mahaukaci haka kema zaki ji ki gani, a tsarina banason mutum me sa’ido, banason mutum ya shiga sabgata idan ban sashi ba, banason gulma duk abinda kika gani a gidan nan kiyi kamar baki gani ba, kazalika duk abinda kikaji a gidan nan kiyi kamar baki ji ba,, matukar kika kiyaye wa’annan zaki zauna lpy dani, kiji da mahaukacin mijin ki kawai dan dama dan shi kikazo ina fata kin gane?”
Wani irin tashin hankali ne ya ziyarci ummi, ita kuma wacce irin kaddara ce take neman nufota kuma? Bayan wacce take ciki ta auren mahauka…,
“kinyi shiru”
haj ta katse ta, da sauri ummi ta shiga girgiza kanta tace, “toh haj Insha Allah zan kiyaye” nan haj ta mike tana fadin “dadai yafi” sauran frnds dinta uku suka bi bayanta nan suka bar part din.
Suna fita ummi ta dafe kanta a fili tace,
“Innalillahi wa’inna ilaihin raji’un” na shiga next level…. Taku again taji ana nufo kofar ta, abin fa ya daina bata mamaki ya koma bata tsoro toh kuma waye zai shigo? Dama haka auren yake? Kodai dan ta auri mahaukacin ne?….bata ida tunanin ba taji anyi sallama.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
31-33
Suraj ne ya karaso cikin parlon hannun sa dauke da leda, zama yyi yana kallon ummi da kanta ke duke a kasa, dan tabe baki yyi ya juya kallon sa wajen el-bash dake kusa dashi, el-bsh shi yake kallo ba yabo b fallasa, suraj ya danyi murmushi yace, “yau kuma frnd har dani akejin haushin?” Yyi mgnr kamar yana mgn dame hankali, el-bash kam har yanzu fara’a batazo fuskar shi ba, saidai babu wannan hadewar fuskar kamar dazu, suraj ne ya juya kallon sa kan ummi da tayi zuru tana jinsa, yace,
“Amarya bakya lefi bakya mgn ne? Ko dole dai sai mun sayi bakin,”+
ummi a hankali tace,
“ina wuni”
er dariya suraj yyi yana kallon el-bash d shima shi yake kallo, yace, “ai bakiyi lefi ba ydda ake siyan bakin kowa haka za’a sai naki” ummi dai ta dukar d kanta kasa batace komai ba, Suraj yyi gyaran murya sannan yace,
“Ummi”
“Na’am”
ummi ta amsa, yaci gba da cewa
“nasan tuntuni kinsan kalar mijin da kika aura, a wannan zamani ba kowa ne zai yadda ya auri me irin halin da mijin ki ke ciki ba, to amma kowa da kaddarar sa, bamusan wacece ke b ummi, dan bamusan halin ki ba, to koma a ya kike inason dan Allah ki zauna da abokina d zuciya daya, a lokutan baya frnd dina yanason mutum me amana, ya tsani munafiki, kinga wa’annan biyun? Toh kiyi taka tsantsan dasu, again haukarsa ba irin wacce kika saba kallo ko ji bace, dan haka ki kula. Hop dai kina fahimta?”
A hankali ummi tace,
” Insha Allahu zan kiyaye,”
suraj yace, “gud fr u.”
aje mata leda yyi a gabanta yace “saidai kiyi hkuri ummi da irin auren d kikayi, dakin ki yana sama shine a bangaren hagu, sai ki shiga kema ki huta.”
Ya salam ummi ta furta a ranta, to amma ya ta iya? Dama ta gaji d zaman wjen dan haka ta mike, har ta fara taka beni suraj ya tsayar da ita yace, “kin manta ledar a wajen ai taki ce” ummi ta karba cike da kunya tayi godiya sannan tayi gaba.
Suraj nadawowa ya tarar da El-bash yna zaga parlo yana kaiwa hannun sa naushi, suraj ya karasa da sauri gabansa a hankali yace,
“frnd lpy kke zaga parlo?”
El-bash ne ya dago da kansa yana kallon suraj, wani irin jan baya suraj yyi sbd firgita da ganin yanayin sa gaba1 idonsa ya fara canja kala, a dan dake suraj yace,
“what?”
Cike da fada-fada El-bash yace,
*”i’m tired”*
da sauri suraj yakai hannun sa kan bakin el-bash ya toshe yana waige-waige, dake zuciya tazowa el-bash wuya a zuciye ya ture suraj, suraj duk karfin sa saida yyi kamar zai fadi, hankalin suraj fa ya tashi, musamman da yaji cikin karaji El-bash yasake fadin,
*”i’m not afraid of them u know that?”*
A hanzarce suraj ya isa gaban el-bash duk wani sauran karfin sa ya tattaro, ya rike hannayen El-bash ya hadesu waje daya da nasa nan ya fara jansa dakyar el-bash na cijewa, dakyar dai suraj ya jashi wani dki dake nan parlon, suna shiga ciki Suraj ya datse kofar, juyowa yyi yana haki yna kallon El-bash daya zauna gefen gado sai huci yake kamar wanda yyi gudu, Suraj ya jawo kujera ya zauna gabansa yana kallon El-bash cikin kasa d murya sosai yace,
“what’s wrong with u today? Do u want to destroy all our plans or what? I know u did kind of this work even more than this, baka taba complain ba so why now?”
El-bash cike da fada-fada yce,
“all cox of this madness aka auramin jaririya, an cuceni and u know it, the girl is not my type at all, nasan abin zai jawo min matsala bazan karbi wannan aikin ba gwara wani can da ba’a sanshi ba yyi.”
“calm down”
suraj ya fada yana dan buga bayan sa, yace,
“wannan auren beci ace ya tunzuraka hk ba, kanada right kaci gaba da zama da ita ko ku rabu duk wuqa da nama yana hannun ka, but for now karka bawa Abba kunya plsss.”
Dunqule hannun sa yyi yana dan dukan dayan hannun a hankali yyinda kuma yake dan hura iskar bakinsa a hankali, shiru dakin yyi kusan 5mins El-bash yace,
“how about the work?”
Suraj ya sauke ajiyar zuciya dan yaga alama frnd din nasa ya sakko, sake kasa da murya yyi yace,
“kafi kowa sanin bangon gidan nan kunne ne dashi, duk yadda ake ciki zamuyi mgn a inda muka sabayi, amma yanzu kam time din amarya ne.”
yyi mgnr cike d tsokana yana dariya, duka el-bash ya kawo masa suraj ya goce da sauri ya bude kofar ya fito, Koda suka iso parlo Suraj sallama yyi masa ya tafi, shima El-bash daukar ledar sa yyi ya haura sama.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
*Wannan page din naku ne en grp dina EL-BASHEER FANS, na gode da kauna😘*
34-35
Ko kallan kofar d ummi take beyi ba ya shige dakinsa da yake bangaren dama, yana shiga ya fada toilet wanka yyi kafin ya fito, kulle dakinsa yyi kafin ya dauko system dinsa dake gefen gadon sa koyaushe, zama yyi kasa ya bude ta wasu danne-danne yyi saiga hoton su haj suwaiba ya bayyana, yana kallon duk abinda sukeyi kamar kullum, camera ya manna musu a parlo batare da sunsan da zaman ta ba, duk abinda ya faru yana ganin su, haj ce zaune da wa’annan frnds din nata d suka zo parlon sa dazu sai hira suke, wacce ake kira sahaba tace, “kuna sane da wannan meeting din ya matso nan da sati biyu?” Haj tace,
“ai Alhj Rabe ya fada min nima” dayar da ake kira ziyada tace,
“aini tunda babu oga kwata-kwata a wajen sai naji meeting din ya sane min,” haj suwaiba tace,
“kefa matar nan akwai son maiko ya kike da Alhjin ki ne sanata bello?”+
“Mtwss..”
ziyada taja tsaki
“toh me ake da wannan? Kullum aiki, meeting baida time din gida kina ganin bazan kosa ba nima na fito? Ai yadda yake neman yara mata ya huta to haka nima nake haduwa da Alhazai irinsu Alhji Mai kano…..,” kifff taji an danqe bakinta, haj suwaiba jikinta na rawa
“tace baki da hankali ne ziyada?” Ziyada ta kwace bakinta tace,
“da nayi me fa?” Sahaba ta karbe zancen da fadin
“Komai ma kinyi kina nema kiyi mana barota banda hauka waya fada miki ana fadar sunan oga a ko’ina?” Haj suwaiba tce,
“sbd Allah fa tayani bata amsa.” Ziyada ta dafe kanta kafin tace, “banda abinku waye na cikon hudun nan da kuke jin tsoron kar yji? Inace mu uku ne a parlon?” Haj suwaiba tace,
“a’a tsautsayi da bacin rana ake gudu,”
“mtwss” ziyada taja tsaki tana saba gyalenta a kafada tace,
“kunga nayi nan tunda ku a tsorace kuke,” haj sahaba tace, “daga fadar gsky,” haj ziyada tace,
“gwara na tafin kawai” nan ta musu sallama.
Tana fita haj suwaiba tace, “aikin bnza kome oga zaiyi da ita? Da fuska kamar tawa a wajen,” haj sahaba ta kwashe da dariya tace,
“bakida krki fa,” haj suwaiba tace, “yo ai itace da abin haushi ai irin wanda oga yake so sune yara emmata matasa masu jini a jika, ba irinta ba data bushe arziki ya boye tsufan ta,”
dariya sahaba tayi tace, “wahala ce bata isheta ba. Nan suka koma wata hirar.
~~~~
“Next level,” El-bash ya furta yana kokarin rufe system din yanzu yasan zasuyi meeting, saidai ba ogansu, toh amma waye Alhji Mai kano? Wannan ai ba suna bane ya fada yana dafe kansa, wayarsa dake kasan pillow ya jawo kiran suraj yyi, suraj dake shirin bcci ya daga yace, “kai ango lpy?”
“Mtwsss” el-bash yaja tsaki “kaifa dan iskane wani lkcin k manta aikin dake gabanmu ne?” Suraj yyi dariya “afuwan oga ashe zancen na aiki ne, inajin ka akwai wani improvement ne?”
El-bash ya sanar masa duk abinda yaji, suraj ya numfasa yace,
“tabdin, wannan mutumin ya boye asalin sunan sa ne, amma hakan ma an samu ci gaba zamuyi kokari mu binciko waye mai kano?”
El-bash yace, “hakan yyi,”
Suraj yace, “toh mezai hana mu kama su a wannan meeting din da zasuyi?” El-bash yace,
“kana manta yanayin aikin ka, kana tunanin idan mun kama yaransa zai fito ne? Saima ai ya sake boye kansa sannan ya dasa wasu sabbin en qungiya, kuma kaga wanda muka sani en kungiyar sune target dinmu a wajensu dole zamuji komai,”
Suraj yace, “hakane, amma idan abin zai jamu dayawa zamu fara musu damqi dai-dai.”
El-bash yace, “wannan ma point ne.” nan sukayi sallama.
Bayan sunyi sallama El-bash ya jawo abincin sa yaci,bayan ya gama ya wanko bakinsa yazo ya haye gado, saida ya lumshe ido ya tuno ashe fa yau ango yake? Wni takaici ne ya kama shi badan Abba b gsky bazai yadda ba, a rasa wacce za’a bashi sai jaririya? Kai da gani ma raino aka bashi, mtwss yaja tsaki a fili yace, “ranar da zan gama wnnan aikn ranar zan datse aurena da ita dan bazan yadda na takura ba gwara na samo type dina,” haka dai yyita sake-sake karshe dai yyi Addu’a bcci ya sace shi.
****
Amarya ummi, tunda ta shiga dakin ta tsaya kallon yanayin sa, dakin dai gashin nan dai, akwai gado sai wardrobe da mirror ko kan mirror babu irin jeren nan na kayan kwalliya, akwatinan da aka kawo mata ma gasunan a gefe, abin dai gashi nan dai kamar ba dakin amarya ba, ummi dai ta rasa me yake mata dadi a duniyar nan, lalle ta cika marar gata, toilet ta fada tayi wanka ta fito daure da towel tasan ma ba shigo mata za’ayi ba dan haka ta zauna ta shafa manta hankali kwance, akwatinan ta shiga budewa nan ta dauko rigar bccinta, ta saka, saida ta gama shirinta tsaff ta jawo ledar d aka bata dan wata iirin yunwa takeji rabonta da abinci tun safe shima bana kirki taci ba, tana budewa taga gasassiyar kaza da fresh milk, hankali kwance ta fara cin kazar ta, bayan ta gama ta aje sauran cikn fridge data gani a dakin, wanko bakinta tayi itama tazo ta kwanta, harta lumshe ido ta tuna angon nata fa ba hankali ne dashi ba, shin ko yaci abinci? Ko yana can ma kasa oho, to itafa har yanzu bata ga kalar fuskar sa ba, kuma itama batajin ya ganta, ko ya yake nema oho, taso tashi ta fito taga ko yaci wani abin tunda baida hankalin tmby taji wani nannauyan bcci ya kwashe ta sbd yadda ta tara bcci dayawa a kanta, dan tunda bikin y karato bata bcci cikakke koyaushe tana kuka tana salla tana neman zabin Allah gareta.
Asuba ta gari Umm-El-bash😂EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
36-37
Sai around 9 ta farka da salati a bakin ta dan tun bayan da tayi sallar Asuba ta koma bcci, wanka tayi tasa atamfar ta riga da skirt da hijab dinta iya gwiwa ba wata kwalliya tayi ba ta fito, dakin dake kallon nata ta zubawa ido, tana kyautata zaton ko dakin mijin nata ne tunani take ta shiga taga halin da yake ciki ne ko ta tafi? Yi tayi kamar ta shiga sai kuma ta fasa ta wucewar ta, sakkowa kasa tayi, nan tayi tsaye ta rike qugu tana karewa parlon gidan kallo, parlon dai babu datti amma yana bukatar mopping sbd kura yo dama yaushe zaiga gyara mutumin ciki ba hankali ne dashi ba? Taji wata zuciyar tana fada mata, hanyar wani corridor tayi taga wata kofa tana budewa taga ashe kitchen ne, ganinsa tayi shima ya hada kura sosai saidai inda aka jera plate a wanke suke, banda wajen ko’ina kurace dashi, dafe kanta tayi tana hango toh inaga dakinsa kuma? Uwa uba toilet? Ya tsaftar wajen zata kasance? “Oh Allah! Ummi ta furta tana rolling eyes dinta, tana tunanin akwai babban aiki a gabanta, fitowa tayi ta danyi gaba da tafiya a corridor din nan ta hango wani fili a gabanta, a ranta tace so gidan haka yake da fadi? Garden ta gani a gabanta tsuntsaye sai shawagi suke, garden din ba wani girma ne dashi ba dan karami ne sadai zaka shaki ni’ima awajen sbd sanyi me dadi da iska ke kadawa, inda aka aje kayan mopping da shara ta gani, abinda take nema kenan, dan haka ta kwaso dawowa parlo tayi ta fara sabuwar shara duk kujerun kifesu tayi ta fara sharo duk wani lungu da sako na parlo,
+
Cikin few minutes ta share ko’ina har kitchen dama ba wata shara ce ssai ba be wuce en ladodu ko paper, dawowa tayi tahau mopping tadan jima kafin ta gama kitchen ta koma nan ma tayi, tana bakin corridor dazai fitar ka waje ta kofar baya ta dafe bayanta tana fadin “washh,” gsky ta gaji ainun mopping dacin rai yake, dukda itace me aikin duk gidansu bata taba yin irin mopping din yau ba, toh inama zatayi tsakar gidansu iya simintine rabi kuma kasa? Dakyar ta sake dukawa ta kwashi kayan aikin tayi gba, can ta zubar d komi ta dauraye kayan da tayi amfani dsu dake akwai tap a wajen, inda ta dauka ta mayar, hijab dinta data nade ta wareshi ya koma yadda yake, dan zagawa garden din take tana kara kallon wajen dan so take inda tayi mopping ya bushe dukda ta sakarma wajen fanka ta bude Windows dan ya bushe da wuri, kusan 10mins tana wajen, ta tashi tadawo parlo, ya bushe din kuwa, nan ta rufe windows ta sakar da labule sannan ta rage gudun fanka kujerun data kife ta dawo dasu daidai, daga gefen inda aka aje TV taga freshener ta dauko tahau fesawa lungu da sako, saiga parlon yadau kamshi, zama tayi kan kujera tana lumshe ido kai gsky a rayuwa tana son tsafta da kamshi, bude idonta tayi ta zubawa ko’ina na parlon ido hatta Plasma ma sheki yake sbd yasha mopping, komai dai kyalli yake, duban agogon parlor tayi taga har 10 yanzu, a ranta tace ko ya tashi? Bata ida tunanin ba taji taku daga stairs,
wani irin bugawa qirjinta yyi toh idan yana duka fa? Ya ilahi, ta furta jikinta na dan shaking.
***
Tunda ya tashi ya fada toilet yyi wanka, dama shi sai wajen 9:30 to 10 yake farkawa, harga Allah daya tashi ya manta ma da wata mace a gidan, saida yazo yana saka kayansa ya tuna da ita, dafe kansa yyi yanajin wani bacin rai na taso masa wannan shi ake kira a daki mutum a hanashi kuka ba damar mgn, cike da kasaita ya fara takowa daga sama dan ko kallon dakinta ma beyi bama yanzu zaton sa tana ciki, saidai tun kafin ya karasa parlon yaji wani baqon Al’amari ya zayarce shi, be ida mmkin ba saida ya karasa sakkowa, wannan changes daga ina? Yyiwa kansa tmbyr, ssai yyi mmkin ganinta a wajen a zaune dukda wa’annan tarin mmkin nasa sam babu alamar sa afuska, dan fuskar nan a daure take tamau kamar hadari a kasaitance yazo ya zauna a kujera ya dauke kallon sa daga kanta.
Sauke ajiyar zuciya tayi sai ynzu hankalin ta yadan kwanta, zaton ta tunda hauka yake yna ganinta zai iya dukan ta ko wani abin. Ji tayi ana knocking tashi tayi taje ta bude tana tsammanin ganin en gidan, sai taga sabanin haka, Suraj ne hannun sa dauke da basket, taji dadin ganinsa kwarai dan taga yafi kowa hankali a duk wanda sukazo mata jiya, ita mutanen gidan ma tsoro suke bata, da er fara’a ta karbi basket din tana gaishe shi, suraj shima da fara’a yace,
“Amaryarmu da kanki?”
dan murmushi tayi batace komi ba ta shigo da basket din ciki, suraj ya karaso yna fadin,
“Ashe ma tare kuke da angon na katse muku lkci,”
yyi mgnr yana kallon El-bash a sace, aiko ya samu tsarabar harara daya mako masa shima a sace. Er dariya suraj yyi yana kallon ummi data sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun ta yace,
“Amarya ni zan wuce office yanzu sauri nake ga breakfast nan kiyi sannan dan Allah ayi kokari a bashi shima yaci kinji.”
ummi cike da kunya da tsoro tace,
“Toh.”
suraj yamike yana kallon El-bash yace, “bye,” El-bash kamar an hura mai wuta dan bacin rai, a ransa yace, _lallema suraj ka raina ni wannan jaririyar ce zata bani food? Mtwssss…_ Yaja tsaki kasa2 suraj har ya fita yana er dariya dan ya fahimci inda fushin frnd din nasa ya dosa.
Tsoron ummi ne ya karu tana tunanin ta ina zata fara bawa zabgegen saurayi abinci? Dagowa tayi ta kalleshi daidai lkcin shima ya juyo suka hada ido ya sake tsuke fuska sosai, yyinda hantar cikin ummi ta kada ssai sbd tsabar firgitar ganin yanayin sa.EL-BASHEER*
*My Facebook fans, Nuceeyluv Novel house and khaleesat haiydar Novels, wannan page din naku ne na gode da comments🥰🥰 ANATARE🤝🏻*
38-39
Kallon basket din tayi tana nazari sake maida kallon ta tayi kansa taga yanzu kuma wani gefen yake kallo yana dan matsa hannun sa, karo na farko kenan data tsaya masa kallon tsaf, dukda side din fuskar take gani hakan besa ta kasa gane cika da yawa irin na sumar gemun sa ba, gaba1 saje d gemun sunyi tsawo suna bukatar gyara, karo na farko kenan da taji wni irin tausayin sa yana shigar mata zuciya, wato hankali ma wata babbar kyauta ce da ubangiji kema bawansa, shi zai banbanta ka da sauran halittu irinsu dabbobi,
kwalla taji tana shirun sakko mata sbd tsananin tausayin El-bash da yake mata kawanya a zuciya,
Tanaji a ranta wannan auren wata jarabawa ce da Allah yakeson jarabtar ta da shi tunda kowanne bawa baya wuce kaddarar sa a rayuwa tayi Imani Insha Allahu zata rungumi wannan jarabawar kuwa hannu bibbiyu fatan ta kawai Allah ya bata ikon cinye wannan jarabawa.
Sauke ajiyar zuciya tayi tana kara share hawayenta dan tausayi.
+
Tashi tayi daga inda take d nufin zuwa inda yake dan ta kudurce a ranta zatayi yaki da duk wani fargaba ko tsoron sa da take, cike da nutsuwa ta karasa gabansa ta zauna a kasa shi yana saman kujera suna facing juna, zubamai ido tayi tana kara kare masa kallo.
Al’amarin El-bash kuwa bayan haushi da yakeji na abinda suraj yyi masa, sai haushin ya koma kan ummi, duk abinda take yana kallonta ta gefen ido, yana mmkin kukan kuma me takeyi? Mtwsss shifa shiyasa yaji ya tsani auren Jibeta yadda take kuka ita kadai kamar an dake ta sai kace wata karamar yarinya mtwsss ya sake jan tsakin a ransa , ransa ne ya sake baci yadda yaga tazo gabansa tayi gwalam kamar mayya tana kallon sa, kai anya ba mayyar bace? Yaji wata zuciyar na bashi amsa, ji yake kamar ya tashi yahau bugunta kawai ya huce takaici, saidai matsalar shi ko a gabansa baya bari a zalunci mace bare kuma Ace shi zaiyi zaluncin Inaaa ba halinsa bane, Allah ya zubamar tausayin su, idan kaga yyiwa mace abu to ta kaishi karshe ne.
A bangaren ummi kuwa zubamar idon da tayi yana kara narkar da ita tausayin sane, harma ta kasa boyewa abinda ke ranta ta fara mgn a fili kamar tanayi dame hankali, cikin tausayawa tace, “sannu kaji, Allah ya baka lpy, cuta ba mutuwa bace Insha Allahu zaka warke kaji? Yauwa indai sharrin Aljanu ne zan tayaka da Addu’ah Insha Allahu zkaji sauki kaji?”
Kukane yaci karfinta sbd yadda take ganin mutum har mutum ba hankali gsky yana cikin jarabawa ta ubangiji saidai Allah ya yaye masa.
Dagowa tayi tana kallon sa tace, “yi hakuri kaji? Bari na baka abinci koh,” tayi mgnr tana mikewa dan jawo basket, gabansa ta ajiye ta juyo tana kallon sa ta nuna masa basket din tace,
“Kaga wannan karka taba shi ina zuwa” tayi mgnr kamar tana mgn da yaro zaton ta kar tabar wajen ya jawo abincin ya kifar kamar yadda taga sauran mahaukata Nayi.
Da dan saurinta kuwa tayi hanyar kitchen plate ta dauko da cups, tana dawowa taga be taba ba harda sauke ajiyar zuciyarta zama tayi ta zuba soyayyen irish da egg ta kawo gabansa ta aje, flask ta bude ta zuba ruwan tea mantawa tayi bata dauko spoon ba ta mike, har zata tafi ta sake dawowa da baya tsoronta kar yasa hannu a cikin ruwan zafin, gabansa ta matso tana nuna masa plate da cup din ta rike kunnen ta alamun warning karya taba, tana yin haka ta juya ta tafi.
Zuciya fa ta zoma El-bash wuya, ransa banda daci babu abinda yake, wato yana mata kallon jaririya ita ta maida shi ma dan tatsitsi sai kace wani yaronta tana masa abin yara, be karajin haushi bama sai dayaga ta rike kunne alamun warning ji yai kawai zuciya ta ingiza shi ya dauki plate din ya zubar da abinda ke ciki.
Daidai lkcin ummi ta fito a kitchen ta hango barnar da yakeyi, a tamanin ta karaso gabansa duba da taga yadda yadauko cup din ruwan zafi shima yana shirin zubarwa, a hanzarce ta cafe cup din har ruwan ya zubar mata a hannu, “washhh…”
Ummi tafada tana yarfe hannu sbd zafin daya ratsa ta, dukda zafin da taji be hanata saurin kawar da hannun sa ba dan kar ruwan ya tabashi, saida ta aje cup din ta riko hannun sa for the first time tana matsawa cikin sigar tausayawa tace,
“Dafatan bakaji ciwo ba koh?” Tayi mgnr tana shafa hannun hade da hura masa iskar bakinta duk ta damu, tasan da yanada hankali bazaiyi makamancin irin haka ba.
Tana a wannan halin aka turo kofa babu ko sallama, sakina ce ta shigo jiya dakyar tayi bcci sbd kishi batason kowa ya rabi el-bash kokadan, dakyar ta samu hanyar satowa jiki ta shigo part din dan kar momynta ta ganta.
“Kan uban can”
sakina ta fada da karfi tana sake matsowa kusa da ummi ta fisge hannun ummi dake kan na bash da take matsa masa, tace,
“ke karuwar inace zaki dinga shafamin miji? Kin manta duk Waring din da nayi maki koh?”
Cike da tsananin mmki ummi tace,
“me nayi na karuwanci anan kike aibanta ni haka?”
“Iyeeeee..!
sakina ta wara baki tana kallon ummi tace,
“eh lalle daga ganinki kin masa fyade jiya kin gama kallon abin dole idonki ya bude,”
kan ummi ya daure sosai tace,
“kamar ya fa?”
Sakina tace,
“kamar uwarki dan ubanki shegiya tsohuwar kila…..”
bammm taji an gwarata da bangon parlo kafin tayi auni taji an kai mata naushi a hanci saiga baki da hancin sakina ya fashe yana jini, El-bash ne me wannan aika-aikar dama kadan yake jira sai gashi ya fara saukewa akan sakina kafin yajuyo ya fara hargitsa kujerun parlon zuwa upsidedown.
Can karshen beni ummi ta makale jikinta na karkarwa, ta matukar tsorata da halin da taga El-bash, ashe haka haukan yake? Tab dole ta fara tofa masa Addu’ah kafin ta sake matsawa inda yake.
Ganin El-bash ya birkice yasa sakna ta kwashi tsumman jikinta tayi gaba da sauri, koda ta fito ta hango Abba da haj sun nufo part din, da sauri ta boye bayan mota dan karsu ganta, saida suka wuceta ta samu ta wuce itama.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
40.
Shigar su parlon kenan suka tarar da tarin aika-aikar da El-bash yyi, da sauri Abba ya isa gareshi yana rike hannun sa yace, “Subhanallah haj tayani gyara kujerar can na zaunar dashi,” haj suwaiba tadan yatsina fuska, ita fa batason a takura mata kan mahaukacin nan mtwss, Abba ne ya juyo ya kalleta tana tsaye kamar dazu daga bakin kofa yace, “bakiji bane…..,” be ida mgnr ba yaji ana kokarin gyara kujera,
Ummi ce ta gyara kujerar tana sunkuyar da kai sbd kunya tace, “Abba sannun ku da zuwa ga waje nan bari na gyara sauran ku zauna,” kallonta Abba yyi yana me jin dadi a ransa lalle da alama be yiwa dan nasa zaben tumin dare ba ya kara yabawa da nutsuwar ta kwarai,+
zaunar da El-bash yyi yace,
“sannun ki kinji Allah yyi maki Albarka”
tace, “Ameen” cike da kunya d kuma jin dadi rabon da ace mata Allah ya maki Albarka tun iyayenta na raye.
Tabe baki haj tayi tana kallon su a ranta tace,
_oho dai sai kuyi ta fama da mahaukaci._
Takowa tayi ta zauna kan wata kujerar da ummi ta gyara, zuwa lkcin ummi har ta kusa share inda ya zubar da abincin. Abba ya kalli El-bash cike da tausayawa har lkcn yana rike da hannun sa yace,
“Allah ya baka lpy Basheer”
Haj tanaji ta sake mere baki tana me ayyanawa a ranta indai El-bash ne shi da warkewa sai a kiyama.
Shigowar ummi yasa Abba ya dago da kansa yana amsa sallamar ta da tayi, wajen su ta iso tana me durkushewa a gabansu tace,
“barkanku da safiya Abba da fatan kun tashi lpy.”
Abba da murmushi dauke fuskar sa yace,
“Lpy lao ummi ya kwanan bakunta”
Ummi cike da kunya tace,
“Alhamdulillah”
a yatsine haj tace,
“ya akai mutum na hauka baki iya zuwa ki kamashi ba har saida mukazo a haka zakuyi zaman?”
Ummi na tsugunne ta kasa banbance halin da take ciki, shin kunya ne ko mmki? Itadai tasan ba itace ta tsokalo shi ba hasalima sai gani tayi ya mike yana zabgar matar datazo dazu wacce ta kasa fahimtar mene alakar ta da El-bash da take ikirarin mijinta ne, kanta ya kulle sosai lkcin da taga yana jibgar ta shin dama masoya ne tun asali ko makiya?
Abba ne ya katse shirun da fadin,
“haba haj baki ganin kokarin da tayi ne? Be kamata ki jefeta da wa’annan kalaman ba, ko banza idan kika duba parlon nan da kyau kinsan ya fara dawowa hankalin sa.”
Haj tace,
“Daga fadar gsky Alhji baka gnin yadda take gudunsa? Da bamu zo ba saidai yyi ta hauka har ya gaji da hauka ya daina haukar……”
“Enough”
Abba ya fada d dan kaushi yaci gaba da fadin,
“Hauka..hauka..haukaaa sai fada kike sbd Allah wannan wacce irin kalma ce marar dadi? Idan baki sani ba kisani wannan kalmar tafimin kowacce irin Kalma me daci a duniyar nan ya kamata ki dinga saisaita kalaman ki akan El-bash zan iya yin komai idan nace komai ina nufin komai ma a kansa.”
Tashi tsaye haj tayi tana me rage sautin muryar ta cike da dan kukan munafurci tace,
“yiii… Alhj sai kace min gori kkson min, iyakata kkeson nunamin, matsayina akan Bashari kkeson isar min ba lefinka bane nawa ne dana nuna kulawata a kansa, tana gama mgnr ta fice.”
Girgiza kai Abba yyi yana mejin daci a ransa, tsaf ya fahimci irin tsanar da suwaiba take ma dansa, yanason rabuwa da ita amma ya kasa, ya rasa me ta tsare masa ita ba haihuwa suka hada ba, gashi bason tilon dansa take ba, yana tunanin lkci yyi da zai rabu da ita.
Ummi hankalin ta ya tashi matuka, batason ganin manya na sa’insa agabanta, bare yanzu sa’insar akwai rabon sunan ta a ciki, itakam ta tsorata gsky, adan tsorace tayi ta maza tace,
“Ab…Abba.. Dan Allah kayi haku..ri”
tayi mgnr bakinta na rawa, murmushin dattako Abba yyi yace,
“karki damu kinji? Karki sa wannan a ranki kinji?”
Ummi a ladabce tace,
“Toh.”
Abba yace,
“good, kinci abinci?” Ummi ta girgiza kai, Abba yace, “Subhanallah inace suraj ya kawo muku?”
Ummi tace, “eh gashi can ma,” Abba yace,
“me kike jira bakici ba ko so kke ulcer ta kama ki?”
Ummi ta mike ta jawo basket din dazu Allah yaso ma da saura sosai a ciki ta gayawa Abba yadda ta kasance dazu saidai bata fadi zuwan sakna ba. Cike da tausayi Abba yace,
“sannu kinji, Insha Allahu zai warke daga wannan cutar, yanzu zuba kici sai ki zubo nasa na gwada bashi ko zaici,”
Ummi tace,
“Toh”
nan tayi yadda yace.
El-bash duk yana sauraran su saidai a jima ya hura iskar bakinsa yana me jin zafi a ransa, dazu ji yake kamar ya kama haj suwaiba ya gwarata d bango irin yadda yama diyarta, saidai taci darajar Abba, Amma muddin taci gaba da tunzura shi tofah yana dab da gwada haukansa a kanta.
Koda Abba ya bashi yaci sosai, ummi dake gefe tanacin nata a hankali taji dadi kwarai da taga yaci, koda ya koshi Abba ya mike tsaye ya kalli ummi yace,
“Zan wuce office inada baki na makara idan na dawo zan biyo tanan Insha Allah”
ummi a kunyace tace,
“Toh Abba a dawo lpy Allah ya tsare.”
“Ameeen”
Abba ya amsa yana mejin dadin Addu’ar ta.
****
Hankali tashe ta fada dakinta, wayarta dake kan gado ta dauka number kaninta sale ta dannawa kira, bugu biyu sale ya dauka yace yadai yaya ko ta samu ne? Haj suwaiba hankali a tashe tace kai wanne samuwa? Muna zaune ruwa zai balle mana ya kamata duk inda kke kazo dan mgnr bata waya bace, sale yaja tsaki yace nifa matsala ta dake kenan yaya kwana-kwana ki fito direct kima mutum mgn yadda zai gane mana, haj suwaiba tace toh kullin da mukayi ma Alhaj na rufin baki fa da Alama ya fata sakwa2 mutumin da be iyamin musu dazu ya karamin tanadi, ya kamata ka hanzarta kazo musan nayi. Sale yace dole ma nazo, ki jirani zuwa gobe,haj tace toh sai naji ka, nan suka katse wayar.
Sauke ajiyar zuciya tayi tana tunanin da alama zata karbi shawarar sale a aika Alhji lahira kawai, dan yana neman hanata rawar gaban hantsi.*EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
41.
Shiru tayi ta fada kogin tunani, tabbas sai yanzu take fahimtar ya lamarin gidan yake ashe ba itace ta haifeshi ba haba no wonder taga daga Abbansa sai frnd dinsa suke tausaya masa, toh amma mene dalilin haukar tasa? Shine abinda bata sani ba sam..
Yyinda take wannan tunanin haka shima El-bash ya samu damar zuba mata idonsa a kaikace, kwance yake kan doguwar kujera yana facing dinta idonsa a lumshe kai kace bcci yake, nan ko ba bccin yake ba kawai ya zuba mata ido ne, ya kasa banbance a wanne matsayi ya dace ya aje ta a zuciyar sa, shin matarsa ko er raino? Gsky yanda yake kallon young fuskar ta sam bata isa aure ba, amma yana mmkin yadda take da hankali kamar wata babbar mace, zuciyar sa ta bashi kawai ya barta a matsayin Kanwarsa tunda ya lura kamar bata da mugunta akwai hankali.
+
Mikewa ummi tayi duk zaton ta el-bash bcci yake, a fili ta furta “tunda bcci kke bari naje na gyara dakin ka” tana gama fadar haka ta haura sama. Binta da kallo el-bash yyi yana kara mmkin karfin hali irin na ummi.
Koda ta shiga dakin haka ta ganshi tsaff sai tashin kamshi yake, mmkine ya isheta data ga komai neat, babu kura kamar ana gyara wajen, kan gadon ne dai a yamutse babu gyara, toilet dinsa ta leka nan ma tas ta ganshi, a fili tace, “oh ikon Allah shi kuma nasa ciwon kenan na masu tsafta ne,” hijab din dake jikinta ta cire nan ta yaye bedsheet din kan gadon duba wardrobe dinsa tayi taga kaya a hargitse, rike kanta tayi tace, “ya salam wannan shine tsaftar biri a moda,” zaro wani bedsheet tayi ta dawo kan gadon ta lailaye shi, kan wardrobe din taje nan ta fara gyarashi tana sa komai inda ya dace, ta bata lkci sosai kafin ta gama gyaran wardrobe din sai gashi wajen yyi kyau, shi kansa dakin sai daukar ido yake dan ya hadu matuka. Tana ganin komai normal ta fito a dakin tana zura hijab dinta, daidai lkcn shima ya sawo kai ba zato sukayi gware dashi,
“Auucch….” Ta furta taja baya tana dafe goshin ta shima lkcin ya rike gefen kirjinsa data buga, hannunsa rike da kirjinsa bawai yaji ciwo bane a’a kawai zuba mata ido yyi yanaso ya mata sannu babu dama dan yasan me hankali ne kawai zaiyi abu yasan daidai ne ko akasin haka,
Abangaren ummi kuwa tsorata tayi da taga ya zuba mata ido ya kuma rike kirjinsa daidai inda ta buga, tunanin ta ko taji masa ciwo ne? Wayyo Allah gashi bazai iya fada ba amma ga yadda ya zura mata idon nan kila gwaren da sukayi ya shige shi.
Cire hannunta tayi akan goshinta da hanzari ta isa gareshi tana me jawo hannun sa ma’ana ya taho cike da tausayi tace,
“sannu kaji? Nice koh? Yi hakuri ban san ka taho bane”
duk tayi mgnr tana jansa bakin gado, zaunar dashi tayi tadan rankwafa ta cire inda ya dafe din tana kallon wajen tace, “sannu bari nazo ina zuwa” nan tayi hanyar toilet da sauri, yyinda shi kuma El-bash ya zama kamar wani statue yana kallon ikon Allah, hannunta rike da wani dan bowl me dan ruwan dumi ta fito dashi, sunkuyawa tayi tana kokarin zaro dankwalin ta so take ta dumama masa wajen wai kar ya tashi,
lura da hakan yasa el-bash yace a ransa gsky yarinyar nan tama maidani buloras sai kace banda kashi ko wanda mashi ya suke shi? Ita har nawa take dan sunyi gware yaji ciwo? Wato itace me dauriya shi rago? Wannan tunanin yasa El-bash ya hade fuska yaga yadda za’a kwaye masa jiki a masa dannar kirji.
Hankalin ummi baije kansa ba, saima kokarin tsoma dankwalin ta da tayi ta dangwalo ruwa, saida ta dago zata masa ta tuna ba’a balle rigar ba, sai a lkcn taji kunya ta kama ta, ita meya kaita kallon kirjinsa? Haba ai da kunya, to amma haka zaki barshi yyita jin ciwo har gun ya tashi? Ki tuna fa ba hankali ne dashi ba, taji wata zuciyar ta bata shawara,
“yess hakane”
ta fada a fili, maida dankwalin tayi cikin ruwa, ta dago manyan idonta tana kallon sa da dan murmushi tace,
“kanaji ba, kayi hakuri ni bazan kalleka ba kumama ni kunya nakeji, amman sbd lpyr ka haka zan jure kaji?”
Tyi mgnr tana masa kwatance da hannu, ita sam bata lura bama fushi yake duk tunanin ta zafin ciwo ne, dan haka ahankali takai hannun ta kansa, da sauri el-bash ya rike rigar sa yana sake bata rai sosai, Ummi tace,
“lpyrka fa nakeji kayi hakuri ba zafi,”
ta sake kokarin jan rigar ya sake riketa, ganin ruwan zai huce yasa ummi ta tattaro hijab dinta ta aje shi side, saiga gashinta ya sauka gadon bayanta baki wuluk dashi ita dama ko kitson aure batayi ba, dan rankwafawa tayi lallausan dukiyar fulanin ta suka danyo saman rigarta farare tas dasu babu alamar zane ko narkarwa a jikinsu sun dace kwarai da red bra din data saka kowa yagansu yaga fresh Milk.
Sam ummi batasan rigarta tayi hakan ba burinta kawai ta danna masa wjen, hannun ta tasa kan nasa tayi kokarin cirewa sai gashi kuwa ya sakar mata, balle rigar tayi dama be wani sa singlet ta ciki ba saiga faffadan kirjinsa ya bayyana kwantaccen gashin kirjinsa luff daya sha gyara baki sai ya kara kawata qirjin nipples dinsa gwanin ban sha’awa duk wata cikakkiyar mace me lpy ta kalli kirjin saita girgiza
toh hakan ya kasance da Ummi, ji tayi kirjinta ya bada wani dammm wata irin kasala ta saukar mata, da sauri ta kauda idonta a kansa tana me rintse idonta gaba1, a kasalance ta fara laluben ruwan har ta tsoma dankwalin ta matse duk idonta a rufe,
laluben kirjin tayi batayi aune ba ta lalubo harda nipple dinsa guda daya ji tayi wani irin shock ya sake janta da sauri ta janye hannun jikinta na rawa, dayan hannun me tsumman takai kirjin dan ta dannan batare data fahimci wanne direction take dannawa ba sbd idonta a rufe yake, dake bata sani ba ashe dayan nipple dinsa take ta matsawa da dankwalin hannun ta, idan ta maida ruwa ta dawo sai tasa a tsakiyar kirjin ko dayan nipple din, gaba1 ta gama luguguta masa nipples inda ta bugeshi daban inda take matsawa daban.
Al’amarin El-bash kuwa tunda ta cire rigarta ya girgiza da ganin halittar na fulanin ta, lalle hausawa sun iya mgn da sukace rashin sani yafi dare duhu, yana mata kallon yarinya rainanta zaiyi ashe abin ba haka bane, sosai y shagala da kallon Albarkatun kirjinta har baisan lkcn daya saki hannun sa ba, ko lkcin data bude masa kirji ta rintse ido abun yaso bashi dariya amma ya dake, hannunta daya tabashi ji yyi ya dauke wuta gaba1 sbd laushin da yaji tamkar audiga,
hankalin el-bash ya tashi sanda ta fara matsa masa nipples yaso janye jikinsa sbd gaba1 tasa masa kasala amma ya kasa saima enjoying abinda take yake, ji yake kamar susa take masa, har wani lumshe ido yake shima, Duk sanda yadan bude ido kallon na fulanin ta yake, abin ya zame masa biyu ga susa ga dadin kallo yanajin kamar abun na jansa ya latsa nata itama, gaba1 el-bash ya fara sakin layi sai numfashi yake saukewa a hankali,
Ummi duk tunanin ta na zafin ciwo ne tunda ba kallon sa take ba batasan yanayin da yake ciki ba, jin ruwan yyi sanyi ta tashi da niyyar zubarwa,
El-bash ya dauke wuta sosai bayason ta daina dan abune da bai taba shiga yanayin da yake ciki ba yanzu abinka kuma da lafiyayyen namiji duk ya birkice baiso a daina, lura da yyi zata tashi yyi surin sa mata kafa, ummi btyi aune ba taji zata fadi tayi taga-taga ta fada kansa shi kuma yyi baya suka zube kan gado sai ga ummi kan tsakiyar qirjin el-bash, ta tsorata matuka dan haka tayi kokarin tashi, shi kuma mutsuniyar ta sake birkitasa tayi, besan lkcin daya birkitata ta dawo kasan sa ba tana saman sa.EL-BASHEER*
*masoyan wannan littafi ina matukar ji daku irin sosai dinnan😍, saidai wani hanzari ba gudu ba🤔 ina mmkin yadda wasu readers din suke kin bama writer uzuri karshe ma ace dan anga ana neman buk shiyasa ake wulakanci🤔 sbd Allah idan mutum yyi wulakanci ribar me yaci? Sbd ku fa muke rubutun nan, idan bamu turo ba ai bazamu jika mu shanye ba🤦🏻♀dan Allah kuna hakuri plss👏🏻 kuyi hakuri da wannan ba yawa.*
Na
Nuceeyluv😘
42.
Hankalin Ummi ya tashi sosai, hankalin ta be kara tashi ba sai data ga yana kokarin kissing dinta, da sauri ta damke bakinta tana tureshi da iya karfin ta, dake karfin ba daya ba sai ya kasance kamar ba turashi take ba,
Al’amarin el-bash kuwa sam ya manta da yanayin aikinsa gaba1 ta ruda shi musamman ya taba fatar jinkin ta sai yaji taushi, goga mata kirjinsa yake a nata yanajin yanayin laushin su, hannayen sa dafe da fuskar ta dan karamin pink lips dinta na birgeshi shiyasa ma yyi kokarin kissn dinta ta damke bakin ta, sakko da hannun sa kan kirjinta yyi da niyyar kawai ya latsa mata su…..gam..gam….gam…
+
Sukaji ana knocking da karfi, Innalillahi El-bash ya fada a ransa yana me mirginawa can gefe hade da dafe kansa, a razane itama ummi ta mike tana me godiya ga Allah daya kawo mata taimako, to amma waye me masu knocking? Tmbyr da tayiwa Kanta kenan dammm kirjinta ya bayar tunawa da tayi ba hankali ne dashi ba koma waye ya ganta zaice fyade tazo ta masa, “wayyo Allah,” ummi ta furta daidai lkcn da aka sake knocking…
Juyawa tayi taga el-bash kamar me bcci ya lumshe ido ko motsi bayayi yadai takure kansa ya rungume hannayen sa akirji kamar me jin sanyi, hijab dinta ta jawo ta saka sannan ta nufi kofar, a hankali ta bude tana tunanin wa zata tarar a bakin kofar?
“Ha’a amarya da kanki? Kuyi hakuri dan Allah emergency yasa nazo har nan na kasa hakuri,”
Ummi ta sunkuyar da kanta kasa dan kunya takeji matuka,
“tace laa ba komai ai suraj yana ciki”
tayi mgnr tana barin wajen da sauri ta fara taka step, da sauri suraj yace,
“zaki ga kaya a kasa ni na kawo, idan na sakko zan miki bayani,”
“Toh”
ummi ta amsa a takaice tana dan kara saurin ta duk kunya ta isheta.
~~~~
Shiga dakin yyi yana rufowa, kallon el-bash yyi da sauri yahau girgiza shi yana fadin “i know frnd ba bcci kke ba ka tashi,” ya fada yana girgiza shi, el-bash ya ture hannun suraj da karfi yana fadin,
“Abeg ka kyaleni naji da abinda ke damuna”
ya fada adan tsawace, baya suraj yyi yana karema el-bash kallo yace,
“frnd? Don’t tell me…?”
Yyi mgnr yana gwalalo ido. Sam suraj be fahimci halin da el-bash ke ciki ba daya gane da bazai tsaya masa surutu akai ba, wani irin feeling me zafi ne ke nukurkusar el-bash shiyasa ma ya takure waje daya yana matse cinyar sa jikinsa sai tsuma yake, banza yyi ma suraj be ce masa uffan ba, ganin haka suraj ya sake dafa kafadar sa yana sake fadin,
“ka fara rainon ne?”
Yyi mgnr yana kumshe dariya dan tsaf ya fahimce shi yanzu, ture hannun el-bash yyi yana fadin,
“kai wanne maye ne me shegen naci? Nace ka fita ko?”
Suraj yadan dara kadan yana fadin,
“baka bani amsa ta ba ai”
“Mtwsssss… wai mene?”
El-basheer ya sake mgn da karfi yana wara masa manyan idonsa da suka fara rinewa zuwa ja, dan dakewa suraj yyi yana shanye dariyar sa dakyar, a hankali yace,
“A dinga kai zuciya nesa dai karka manta a yanayin aiki kke, idan kuma zaka sanar mata gskyr toh?”
Yyi mgnr yana wara hannun sa, harara el-bash ya doka masa yana sake rintse idonsa, suraj ya sake yin er dariya yana tafiya hanyar waje yace,
“Akwai abinda ya kawo ni, zamuyi mgnr anjima idan kaji sauki, zata kawo maka mgni”
yana gama mgnr ya fice. Binsa d tsaki el-bash yyi yana dan cize bakin wahala.
****
Koda ummi ta sakko kan kujera ta zauna, gefe guda ta takure akan kujerar har lkcin jikinta be daina bari ba kogin tunani ta fada na abinda ya kasance da ita dazu, shin kodai a Aljnun el-bash akwai jinnul Ashq masu son mata bata sani ba? To idan ba haka ba wannan baqon Al’amarin daga ina? Saikace me hankali? Kai kanta ya kulle fa??? Hmmm…. Tausake ajiyar zuciya tana dan tankwashe hannun ta.
Wata zuciyar tace baida hankali fa, bayan wannan kam ai ya cika namiji…. dadai lkcin ummi ta rufe idonta tana sake jin kunyar tunanin da tayi…
sallama taji a bayan ta tadan juyo a razane sam ta manta da suraj na sama, amsawa tayi tana gaishe shi dan dazu bata samu damar gaishe shi ba,
fuska suraj yyi be nuna komai ba kan fuskar sa, yadda suka saba mgn yyi yana dan tsokanar ta yace,
“amaryar mu ashe ma baida lpy naji jikin nasa dadan dumi kinga kayan can ko?”
Ummi ta girgiza kai, suraj yace,
“kayan abinci na kawo muku bari na tayaki sawa a kitchen dukda an zuba masu nauyin a store saidai ki gyara mazaunin komai, idan kin duba waccar ledar akwai kayan tea pls ki hada ruwan zafi na Lipton sai ki matsa lemon tsami kikai masa yasha kinji,”
ummi tace,
“toh daka barshi ma saina karasa kaiwa kayan tunda ba yawa zan iya,”
suraj yace,
“ohk ni zanje sai nazo dubashi,”
“toh”
ummi ta sake cewa a takaice.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
43
Kamar yadda yace hakan kuwa tayi komai ta kwashe shi, sharp2 ta hada masa ruwan Lipton da lemon tsami, bayan ta zuba a cup ta saka sauran a flask ta dauka tayi sama dashi.
Batare da tayi knocking ba ta tura kofar, daidai lkcin el-bash yana zaune ne gefen gado kansa a duke ya rike kasan cikin sa, ummi mmki ne ya isheta ainun, wai meke damunsa haka? Ta tmbyi kanta, a hankali tà karasa wajen ta dan dafa kafadar sa ya dago kai yana kallon ta, ummi ta girgirza da ganin yadda manyan fararen idonsa suka canja kala zuwa ja kamar me fama da ciwon ido,+
Lipton din hannunta ta mika masa sai taga ya karba ba musu, dukda yanada zafi amman haka taga yana kurba da sauri2 kamar ya samu abin dadi, tass ya shanye ta sake tsiyaya masa na flask taga ya sake karba wannan karon rabi yasha ya mika mata sauran,
yana gama sha ya koma kwanciyar sa yyi luff, yyinda ita kuma ummi ta fita da kayan taja masa kofar sa.
*****
“Sale kyi wani abu akan wannan lamarin Alhaji fa musu ya fara min,” cewar haj suwaiba.
Sale yaja tsaki “yanzu so kke yaci gaba da rayuwa ko a kashe shi?”
Haj suwaiba tace,
“zamansa baida amfani a aikashi lahira kawai.”
Wata mahaukaciyar dariya sale ya saki yana tafa hannu yace,
“yanzu kika shigo gari hajjaju makiratu, karki damu duk sanda zai fito ki sanar dani sbd mu zama cikin shiri ko cikin dare zamu duro mu kashe shi?”
Haj ta danyi shiru can tace, “kuzo cikin daren zaifi sauki kar a kashe shi da rana a sami matsala na shiga uku.”
“Toh shikenan ni zan wuce”
haj tace, “madalla saina jiku,”
nan sale ya fito yana murna burinsa ya kusa cika.
*****
3am wato tsakiyar dare lkcne da kowa yake surnana bccin sa, yyn da wasu suke tsaye kan kafafun su suna ibada dan neman yaddar ubangi, Allah ya sanyamu cikin yardaddun bayinsa Ameeen.
Dake sale yasan takan gidan shiyasa abokan nasa ‘yan fashi basu sha wahalar shigowa ba dan ya musu kwatancen komai, shi be biyosu ba sbd kar Al’amari ya baci Allura ta tono garma.
Basu tarar dame gadi ba a wajen sai basu wani damu ba suka shige.
Sidaf2 suke taku har suka gifta ta bangaren el-bash, yana jikin window yana kallon su daya bayan daya, yadda ma suke wani sanda ma sai abin yaso bashi dariya a fili yace,
“aikin banza ashe ma kananun kwari ne mtwssss.”
Saida suka gama shigewa tsaff kafin el-bash yyi mgn wani dan karamin abu ne a kunnen sa yace,
“you guys are u ready?”
“Ever ready Sir!”
Yaji sun bashi amsa, facemask yasa ya sake rufe idonsa da glass ya fito.
****
Haj suwaiba tasan mezai faru bata cika kwana dakin Abba ba koda basu samu sabani ba, bare kuma ace an samu, koda taje da niyyar kwana Abba yyi mmki dan beyi zaton zuwanta ba yanzu tunda sun samu sabani, be kara mmki ba saida yaganta da kwalliya tana masa murmushi, Abba bece komai ba yana kallonta kawai, haj suwaiba ta sake fadada murmushin ta tace,
“haba Abban Bashir kamar bakayi farincikin zuwana ba,”
Abba yace, “no bance ba” yyi mgnr adan dake dan be gama hucewa ba, haj suwaiba tace, “haba mana Alhaji na idan kan abinda ya faru ne dazu kayi hakuri kaji? Yanzu kam na gane gskyr ka kuma zan gyara ai bashir dana ne”
ta karasar mgnr tana murmushi, Abba yadan murmusa kadan kawai beyi mgn ba, haj suwaiba tace, “dgske nake fa na gyara” Abba da er dariyar sa yace, “ya wuce amman nasihar da zan miki itace ‘ya’ya da dukiya ba’a ketar su bakasan wa zaka mora ba koda bayan na mutu ne El-basheer ai abin ki kula dashi ne dukda ba yaro bane.”
Haj tace, “kayi gsky Alhji za’a kiyaye” Abba yace, “Good for u” yana me gyara kwanciyar sa yace ta kashe wutar dakin bcci yakeji kuma da wuri zai fita gobe. Haj tace, “toh” tana me tashi ta kashe.
Dake cikin duhu ne sai doka masa harara take tana dariya kasa2 tace masu yaro kaida ganin mahaukacin danka ai sai a barzahu tasa dariya tana toshe baki.
Tsakiyar daren sukaji an banko kofa lkcin ma Alhji yana kan sallaya salla yake, ya sallame kenan yaga mazaje a kansa,
“Innalillahi wa’inna ilaihin raji’un Alhji ya furta yana karema samarin ‘yan fashin kallo
.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
44
Wata irin dariyar basawa ‘yan fashin suka bushe da ita suna tafa hannu, daya daga cikin su yyi mgn cikin muryar tatattun ‘yan daban nan yace, “kai ka rike salatin ka watakila zai maka amfani zuwa an jima kadan”
“Subhanallah”
Abba ya furta yana fadin “kudi ya kawo ku ko me kuke nema?” .
Babban cikinsu yace,+
“Ashe tsohon kansa na ja, saidai ba kudi ne ya kawo mu ba ranka zamuyi awun gaba dashi” yyi mgnr yana saita bindiga a kirjin Abba,
Abba cikin karfin hali yace,
” ‘yan samari kenan banda abinku wake daukar ran mutum idan ba Allah ba? Saidai ko ya zama sanadi, mutuwa koyaushe na riskar mutum yanzu ko anjima so koda na mutu a yanzumutuwa ba kune kuka sa na mutu ba illa kaddarar mutuwa tane a sanadin ku wanda hakan baya faruwa sai Allah yaso….”
“Dallah yi mana shiru”
ogan nasu ya dakama Abba tsawa yana kokarin danna harbi dan still bindigar na kirjin Abba,
Daidai lkcn haj suwaiba ta farka dama ba bcci take ba, a razane haj tace,
“yau mun shiga uku mun lalace mezan gani da mugun ganin Alkaba’i Alhji?”
Tayi mgnr tana dora hannu a kai, ran Abba be tashi baci ba saida yaji furucin haj, a hasale yace,
“ke wacce irin mutum ce daga tashi ba salati ki dinga fadin an shiga uku?”
“Alhji sbd Allah kashe ka fa naga ana shirin yi? Wayyo jama’a taimako, yau ga ranar mahaukacin danka be isa yazo ceton ka ba sbd yana hauka ta karasa mgnr tana matse hawayen karya, dan mgn take me kama da gugar zana farincikin ta yau za’a kawo karshen komai ta huta.
Rintse ido Abba yyi sannan ya bude ya kalli samarin yace,
“what are u waiting for? I said what are u waiting for??? Ku harba manaa….” Yyi mgnr da karfi,
ogan ciki yace,
“kut***mar uba tsawa kke min?”
Ya daga bindigar zuwa goshin Abba yace, gwara na tarwatsa maka kwakwalwa mekan kifi, ji kke tassss………,”
haj suwaiba dake kan gado saida ta diro kasa a matukar tsorace, dakin yyi shiru na wasu ‘yan dakikai, ga Alhji a gefe guda.
Cikin taku irin na kwararrun jami’i yake yi a tsakiyar su fuskar sa ya rufe da facemask yyinda ya sake sa bakin glass ya toshe idonsa, yanda ya rufe jikinsa gaba1 da wuya ka gane shi, *EL-BASHEER* kenan gaba1 sun zagaye ‘yan fashin sai ga ‘yan fashi sun zube a kasa yyinda jami’ai suka zagaye suka zagaye su el-bash a tsakiyar su, kallon idon su yyi yaga sunyi wuqi-wuqi girgiza kai yyi yana mejin bakin cikin yadda samari matasa ke lalata rayuwar su a wannan zamani musamman a kasar nan tamu ta naija, komai sake tabarbarewa yake,
Haj bakinta na rawa tace,
“suwaye ku dan Allah?”
Babu wanda yyi mgn a cikinsu suna jiran umarnin ogane kawai, El-bash ya kalli abokan aikinsa da suka sha facemask yyi masu alama da hannu, wani anace dashi musa yace,
“haj da zakiyi shiru tabbas da hakan zaifi maki Alkhairi,”
haj da bakin ciki ya isheta sbd ba’a kashe Alhji ba tace,
“Ai dole nayi mgn tunda anzo cecen mijina da ace tun wuri an harbeshi basu tsaya shirita ba da tuni ya sheka ai”
tayi mgnr tana matse hawayen bakin ciki saidai wannan bakin cikin na takaici ne, a yanayin mgnrta me hankali ne kawai Zai fahimci da biyu tayi mgnr,
Wato tana mgn ne da harshen damo,
dan murmushi el-bash yyi me ciwo tsaf ya fahimci inda ta dosa wato tanaso tace meyasa ‘yan fashin basu kashe abbansa da wuri ba suka tsaya shiririta har aka kamasu?
Girgiza kai yyi yama suraj alamar a fitar da samarin waje, dama duk an damqe su nan aka tisa keyarsu gaba.
Shi suka bari karshe, yana cikin dakin hannayen sa a Aljihu ya kalli side din Abba, wato ya juyawa haj baya kenan, cire glass dinsa yyi yadan zamo da mask din murmushi ya sakar ma Abba yana me daga masa hannu ya sake maidawa ya rufe sannan ya maida hannayen sa Aljihu ya fice cikin takunsa na isa.
Tsabar mmki ma kasa motsi Abba yyi, shi kadai yagan shi anya dansa ne *EL-BASHEER?* kodai mafarki yake? Tabdin wato akwai sarkakiya a wannan Al’amarin baida masaniya, to yana nufin ba mahaukaci bane ko me?
Sbd mmki ma kasa mgn yyi dan kansa ya kulle matuka. haj ce ta matso kusa dashi tace,
“meya maka daya juyamin baya? Ko ka sanshi ne? Koshi ya sanka?”
Sauke ajiyar zuciya Abba yyi daya fahimci bata gane waye ba dan tunda yaga wannan sarkakiyan yasan akwai wani boyayyen Al’amari wanda el-bash yasan shi…
“mgn nake kamin shiru. Alhji….”
“ke dallah rufamin baki” Abba ya fada cikin fada-fada.
Haj ta tsorata matuka, gefe ta samu ta zauna tana dafe kai hankalin ta a matukar tashe.EL-BASHEER*
*_Shimfidar fuska ta wuce ta tabarma tallafamana kar so ya samu yin kuka 🎤Idan gamu gaki sae muji muna farin ciki yake nusy love ki taemakemu.🎤🎼🎼🎼🎼ga Yan group suna bidanki🎤silar bash muke kiranki😘😁😁_*
_Wannan page din naki ne Qawata Amintako😛me waqa🤣🤣🤣 dake da sauran en group EL_BASEER FANS masu amshi da rawa😂wanga abu ai dole na garzaya da gudu🏃🏼♀na muku typing sbd ya burga ni😍 inayin ku irin sosai sosai dinnan😘_
Na
Nuceeyluv😘
45
Dakinta haj ta koma hankali tashe ta dauki wayarta sam bata damu d cewa dare ne ba ta danna kiran sale dake bcci ya daga kiran yace,
“yaya da fatan ya sheka koh?” Wani wawan tsaki haj taja tace,
“sale wa’anne irin sakarkarun yara ka turo?”
Sale ya mike zaune yace,
“dur***n uwa su babawo ne sakarkaru?”+
“Toh idan ba sakarkaru ba dolaye kke so nace?”
Haj ta katse shi cikin takaici, sale yace, “bur*** uba wai me kike nufi ne?”
Cike da tsantsar takaici haj ta sanar masa abinda ya faru, mikewa sale yyi tsaye ya malmalo ashar
“kut***r ubannan kayyasa billahillazi bamu ga ta zama ba duk yadda za’ai kiyo asubanci muje gun boka dan tsito a rufe mana bakinsu karsu ambaci sunan mu dan ban shirya mutuwa yanzu ba.”
Wata nannauyar ajiyar zuciya haj ta sauke sai yanzu taji fiye da rabin tashin hankalin ta ya ragu, cikin sauri tace,
“ka saurari zuwana” tana gama fadin haka ta kashe wayar.
****
Koda ya koma daki canja kaya yyi zuwa na bcci, cikin lallausan bargon sa ya shige ya jawo pillow ya kifa kansa a kai, ji yyi kamshin pillow ya canja, take Al’amarin daya kasance dashi dazu ya dawo masa, anya shine kuwa? Wai meya hau kansa dazu ne daga kallon yarinya duk ya rikice? Duk shige da ficen na kasashe daban2 dayake akan makamar aiki ga mata nan iri2 be taba rikicewa a kansu ba sai wannan little babyn?
Why only her? Sake rungume pillow yyi yana feeling kamar itace a wajen kamshinta data bari a wajen yake sake sashi hangota lkcn da take ta mutsiniya tana neman tsira, zumbur ya mike daga kan gadon ji yyi jikinsa kamar yana shirin komawa gidan jiya mmki yake dama shidin har haka yake da feeling ko kuwa dan haduwa da ita ne? Yes yanajin feelings time to time dan shidin lafiyayyen namiji ne saidai ba kamar irin yadda yakeji yanzu ba.
Hanyar toilet yyi nan ya dauro Alwala dan ya lura idan ya kwanta tunani ne zai cika masa Brain maimakon yyi bcci, nan ya tada kabbarar sallah, dake har hudu tayi asuba ta kawo jiki anan yyi sallar asubar sa, bayan ya idar ya haye gadonsa wani irin nannauyan bcci yyi awon gaba dashi.
~~~~
Ko takan Abba haj batayi ba ta fice a gidan, tana zuwa dama sale a shirye yake nan suka tafi a motar haj, dake asuba ne akwai sauran duhu haka haj tayi ta tsala gudu har suka gangara wani daji dake gaba da kano kadan, a gefen hanya ta aje motar suka fito da hanzarin su, dama tunda suka hadu babu mewa kowa mgn har sukaje.
Can sukaje wata er bukka dake kwaya daya jal a dajin, zuwansu keda wuya sukaji dajin an kaure da dariya meban tsoro saidai ga mmki su haj ko a jikinsu da alama dai sun saba d zuwa wajen. Wani dan siririn baqin tsojo ne ya fito hakwaren sa jajaye zaqo2 shima yana dariyar, can kuma sai dariyar ta dauke ya tsuke fuska yana muzurai da wani mitsitsin idanun sa, daidai lkcin su haj sun zauna gabansa kenan sale yace,
“An gaishe da boka dan tsito duk wani boka meji da kansa a bayanka yake sha yanzu mgnin yanzu, dama wata buqa…….”
“Na sani”
boka dan tsito ya katse sale yana daga masa hannu wato ya dakata, sannan yace,
“Badai a rufe musu baki ba?”
Haj bakinta na rawa tace,
“Eh tabbas hakane”
wata irin dariya ya kwashe da ita kafin ya gimtse yace,
“An gama.”
Farinciki ya lullube haj ta zuge jaka nan ta dire masa rafar kudi bugun abuja, boka dan tsito yace,
“kunsha da kukazo da wuri yanzu kuwa duk tmbyr da za’ayi musu bazasu taba fadar sunan ku ba”
da murna suka hau godiya yace, su tashi su tafi.
A guje kuwa haj suka iso cikin gari sbd sharara gudun da take, sauke sale tayi tace zasuyi mgn idan sun natsu, sannan ta karaso gida lkcn gari be gama haske ba gidan shiru kowa ya koma bcci, hamdala tayi da taga komai ya taf successfully,
cikin sanda tayi wuf ta fada dakinta, gyalenta ta jefar batare da canja kaya ba ta zube kan gadon ta nan bccin da batayi ba yyi awon gaba da ita.
*******
Dake komai an aje musu a kitchen yasa ummi tana gama gyara dakinta tayo waje, leka dakinsa tayi taga yanata bcci, zuba masa ido tayi a ranta tace kamar a tashe shi ya amsa yadda taga yana bccinsa hankali kwance, batasan meyasa takejin tausayin sa ba all the time musamman idan tana kallon sa, saje da gemun daya cika masa fuska take kallo duk yyi yawa gashin yana buqatar gyara, sa hannu tayi tadan shafo afili tace,
“Bari na gama aiki nazo na aske gemun nan kamar ciyawa kuma duk rigimar da zakai saidai kayi saina aske”
tayi mgnr still hannun ta nakan gemun tana shafawa, saida ta gama jagwalgwala gemun ta fito tana ja masa kofa tunda taga bcci yake.
Oh! rashin sani akace yafi dare duhu domin tun lkcn data shigo yasan da zuwanta kawai likimo yyi yana jiran yaji me zatayi, shi abin nata ma ya daina bashi mmki saima dariya lalle yarinta me dadi wai shi za’aima aski? Lalle wannan little din akwai karfin zuciya, zaiga kuwa ta inda za’a masa gyaran fuska. Nan ya sake nadewa a gadon yana jiran tsammani.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
47
Jikinta ne ya fara rawa so take ta kwace kanta amma ta kasa sbd rikon da yyi mata bana wasa bane, kokarin jawo jiqaqqen towel dinta take ta rufe jikinta amma abin ya faskara saima gani tayi el-bash yyi wurgi da towel din kasa innalillahi ta furta a ranta kenan yau me zata gani? Batason ya kallar mata jiki dan haka tayi saurin fadawa qirjin sa ta kankame shi sosai yadda babu yanda zaiyi ya kalleta dan ta harde shi, a nata tunanin daya ganin mata jiki gwara ta mannu dashi.+
A bangaren el-bash kam Besan sanda ya furta “Ya Subhanallahi” tabbas da ace hankalin ummi kwance yake da taji mgnr sa, amma ina gaba daya ya birkita mata tunani batajin komai, shima hankalin nasa ne ya tashi musamman data manne masa a qirji yanajin na fulanin ta na yawo a qirjin sa, hannun sa na rawa ya koma shafa duk wani sassa a jikin ta duk yabi ya haukace mata, ummi hankali tashe ta sake kamkame shi kamm hawaye nabin kumatun dan babu damar kuka tunda bakinta still yana cikin nashi.
Saida ya gama jagwalgwala ta son ransa kafin ya sakar mata baki, da sauri ummi ta sake shi taja gefe ta hade kai da gwiwa tana kuka, ji tayi yana watsa mata ruwa cikin jin haushi ta dago kai ta debi ruwan ta watsa masa, gni tayi yyi murmushi ya sake diban ruwan ya watsa mata, sake debowa tayi ta watsa masa tana wurga masa harara, yanzu kam fararen hakoran sa ta gani a waje yana washe mata baki besan meyasa ba komai tayi sai ya birgeshi sai ya dauketa kamar abin wasa shiyasa ya kasa rike dariyar sa yana murmushi,
mmkii take idan yyi wani abin saikace me hankali, a razane tayi saurin sauka a bahon ganin yana shirin cire wando sa gaba daya, tana shirin sauka ya jawota ta fado kansa ji tayi kamar ta tsaga kasa ta shige sbd jinta da tayi a jikinsa babu komai, kokarin karasa cire mata dan sauran mutuncin ta yyi amma ta kasa hanashi sbd kasalar daya saukar mata gaba1 jikinta ya mutu, tanaji tana gani ya subale mata komai sun koma yanzu babu abinda yyi masu tazara, batada da wani option sama Da ta rufe idonta dan bazata iya kallonsa a haka ba.
A bangaren el-bash hakan take gaba1 jikinsa a tsume yake tun dazu bare yanzu da babu abinda ya musu tazara, dakyar ya karasa cire mata komai jikinsa na bari, niyyar sa yyi musu wanka su fice amma abin yaci tura dauriyar sa ta kare, kwanto da ita yyi jikinsa yaga ta rufe ido, gashinta ne ya bazu cikin ruwan fuskar ta ce kawai a waje amma sauran jikin suna ruwa, wasu gashi da suka hawo kan fuskar ya janye, tsura mata ido yyi yna karewa halittar ta kallo, dan murmushi yyi yana mmkin kunyar ummi ji yadda ta wani rufe idonta kamar me bcci sai yadda aka juyata yafada a ransa,
jingina yyi ya juyo da ita kan kirjinsa suka hade, Ya Rahmanu Ya Rahimu, abinda ummi tayi ta nanatawa kenan a ranta tuni ta sake tsunduma cikin wani baqon yanayi wanda bata taba tsintar kanta a ciki ba,
Kissing dinta ya shiga yi kota ina yana sake matse ta a jikinsa, numfashi yake fitarwa da sauri da sauri ummi najin yadda kirjinsa ke up and down, hannayen sa cikin sumar kanta duk ya yamutsa mata su, ji yake kamar ya kusance ta a lkcn amma zuciyar sa na tausayin ta, yadda ta saduda shi ya kara bashi tausayi bayaso ya bata mata rai dayawa shiyasa ya gwammace ya samu ko yayane dan relief a jikinta,
dakyar ya iya kyaleta hakan ma yasan dole yasha lemo idonsa duk ya kada yyi jajur, a hankali ya masu wanka ya dauko ta, tanaji yake komai har lkcn bata bude ido ba, saima duniyar tunani data lula tana tunanin el-bash da yanada lpy kuma zasu kasance irin love birds dinnan tabbas da tafi kowa sa’ar miji dan bata taba ganin miji so romantic irinsa ba, tmbyr anan itace idan ya dawo hankalin sa zaiso ta kuwa? Ji tayi ya katse mata tunani da shafa mata mai ashe sun iso bedroom kuma dakinta,
saurin bude ido tayi ta fahimci a dakinta suke be taba shigowa ciki b sai yau, gni tayi idonsa yyi ja kuma yana mata komai cikn sanyin jiki, batasan meya canjashi haka ba dan haka ta tashi tsaye kayanta data aje kan gado tun dazu da niyyar idan tayi wanka ta saka ta dauko, doguwar rigace ta saka, juyowa wajensa tayi taga ya jinginar da kansa ya dafe goshi dama kan kujera yake, matsawa tayi da sauri ta dafa shi, jijjiga shi tahau yi tana fadin what’s wrong? Duk ta gigice sbd yadda taga ya canja ga towel daure a qugun sa, dan bude idonsa yyi ya kalleta ya kuma lumshe ido bece komai ba,
jawo mai tayi tahau shafa masa da sauri, dakinsa taje ta dauko kayansa irin wanda taga yafi sasu kananan kaya wandon 3qtr, rufe idonta tayi ta yaye masa towel sannan ta fara kokarin sa masa, dan murmushin karfin hali yyi danshi lkcn ya bude ido, saida ta gama sa masa kayan ta bude ido taga idonsa a bude yana kallon ta, jansa tayi da nufin ya kwanta tunda taga baida kuzari yaja hannunta suka fito waje,
zaton ta daki zaije sai taga suna sauka kasa, da dan sauri suke tafiyar ummi na biye dashi kamar jela tana mmkin ina zasu? Gani tayi sunyi hanyar kitchen, direct inda ake aje lemon tsami ya je, nuna mata yyi da hannu ba tare da yace komai ba, ummi tace,
“oh zaka sha?”
Gani tayi ya zuba mata ido still be amsa ba,
“Okay na gane bani 2mins”
ta fada tana debo guda biyu zata wanke taga ya biyota da daya a hannun sa kato, wara ido tayi tana kallon sa tace,
“kai baka gudun tsami ne?”
Ita ummi duk batasan dalilin shansu ba. Gani tayi ya bata rai ya juya zai fice, da sauri ta kamo hannun sa tana fadin,
“Okay i’m sorry!”EL-BASHEER*
48
Na
Nuceeyluv😘
Tsayawa yyi be juyo ba, hakan yasa ummi tayi saurin wanke lemon ta samu wuqa ta yanka, debo su tayi ta kamo hannun sa suka fito dan ruwan tea data dafa yana kan dining data kai dazu, kan dining suka yada zango taja masa kujera suka zauna, hada masa tea tayi ta matse lemon ta mika masa, da saurin sa kuwa ya dinga sha da zafi2 ummi dai sai zuba masa ido tayi tana kallon sa yadda yake sha ko zafin ma da alama bayaji bare uwa uba tsamin,+
yana lura da ita yyi fuska kawai kamar be gani ba, tass ya shanye saidai me? Kamar besha komai ba haka yakeji, sam beji ya samu releif din komai ba saima marar sa data kulle tana ciwo, dan dafe kasan cikinsa yyi kansa a kasa idonsa yyi jaaa shi yasan tashin hankalin da yake ciki ya rasa ina zai tsoma kansa yaji dadi, dan matsowa ummi tayi ganin ya duqar da kai ta dafa shi tana fadin oya saura aci abu me nauyi, tayi mgnr tana dan matsa kafadar sa dan ya dago,
hakan da tayi batasan sake tsomashi tayi cikin wutar abinda ke cinsa ba, dayan hannun sa yasa ya janye nata hannun, zatayi mgn kenan taji ana knocking, da sauri ummi ta dauki hijab dinta dake kan kujera wanda ta aje ta tafi bude kofar, duk abinda tayi el-bash na kallon ta kasa2 nutsuwar ta ita ke sake birgeshi.
Tana bude kofar taga suraj, da dan murmushi fuskar ta tace, “ashe babban bako ne a gidan” suraj shima yana er dariya yace, “amaryarmu dafatan na sameku lpy”
ya fada yana zama, ummi tace, “lpy lao ya mutanen gida” suraj yace, “Alhamdulillah ina mutumin?” Ummi ta nuna masa hanyar dining area tace, “gashi can” suraj ya mike tsaye yace, “lpy kuwa ya dukar da kansa?” Ummi tace, “ehto lpy b kalau ba,”
“Subhanallah”
suraj ya furta yana nufar wajen, ummi tace, “zan shiga cikin gida mu gaisa kafin ka ganshi” suraj yace, “okay ba matsala a dawo lpy,” ummi tace, “toh” sannan ta fita.
Tana fita suraj ya zuba masa ido na wasu seconds tuni ya gano matsalar abokin nasa, sai yaji ya bashi tausayi hannu yasa ya buga table yana fadin,
“itace matsalar ka?”
El-bash ya dago kai yana hararar sa yace,
“ban sani ba dan sa ido”
dariya suraj yyi yace,
“kaga shawara zan baka yanzu, yarinyar nan halal dinkace frnd so why not kayi abinda Allah ya halatta maka? Naga bata da matsala tanada hankali nayi maka bincike sosai a kanta, kanada zabi kaje mata a yadda kake yanzu ko ka gaya mata gsky i know zata rufa mana asiri har mu kammala aikin mu.”
Hmmmmm….! El-bash yaja dogon numfashi dakyar ya fara mgn yace,
“Frnd bazaka gane bane wlh a yadda nakejin kaina banajin yarinyar nan zata iya dauka na coz she’s still little baby i don’t want to hurt her tausayi take bani ya karasa mgnr dakyar yana cije lips.”
Wata er bazawarar dariya ce ta kwacewa suraj batare daya shirya ba,
“uhummm like seriously?”
Suraj ya fada yana er dariya, bata rai el-bash yyi yana fadin,
“kaifa iskancin kane banaso wannan dariyar shikiyancin ta meye?”
Dan daidata dariyar suraj yyi yace,
“kaine dalilin dariyar ai, kazo kana wasu maganganu wanda basuda tushe”
cike dajin haushi el-bash yce,
“me kke nufi?”
Suraj yace,
STORY CONTINUES BELOW

“ah to ji nayi ka ambaci wani suna little baby tana little din take gigita ka? Abeg ya kamata idan bcci kke k farka dan kasan inda kasa gaba zabi ya rage ma me shiga rijiya”
ya fada yana wara hannu irin I don’t care dinnan.
Banza el-bash yyi masa bece komai ba, suraj yace,
Kai nifa da nine a situation dinka da tuni na kaddamar dan aikin nan baze hanani komai ba akan me zan takura kaina da lemon tsami? Duk sai kaje ka salance kanka ai ka dawo baka da taste.”
Duka el-bash ya kaima suraj suraj ya goce yana dariya, el-bash yace,
“Banza maye da ganin ka matar ka ta shiga uku wlh kai ni bansan meyasa ma duk sanda na fada halin nan kke zuwa ba sai kace Aljani”
ya karasa mgnr yana hararar sa, er dariya suraj yyi yace,
“Allah ke jefo ni nake zuwa daidai time din.”
“Mtwssss..”
El-bash yaja tsaki bece komai ba.
“yauwa me ake ciki game da mutanen nan? Kwanan nan fa sace-sacen yara yyi yawa ya kamata asan abin yi,”
dan tsaki el-bash ya sake ja kafin yace,
“we will talk later,”
dan murmushi suraj yyi yace,
“okay na fahimci matsalar”
ya fada yana er dariya, yanzun ma banza el-bash yyi masa.
******
Wannan shine karo na farko da ummi ta shigo side din haj, knocking tayi, daidai lkcn kuma haj na tare da sale, har yanzu bata gama huce takaicin rashin nasarar su ba, adan tsawace tace,
“wayene?”
Ummi tadan tsorata kadan amma tadan dake tace,
“nice,”
da mmkin jin muryar mace haj tace,
“shigo”
dan sam bata rike muryar ummin ba tunda ba shiga sabgar juna suke ba, a hankali ummi ta tura kofar hade da sallama, haj baki wangale tace,
“oh kece toh sannu”
ta fada fuska ba yabo ba fallasa, ummi tadan risina tace,
“barkanku da safiya haj,”
haj suwaiba ta danyi yake tace,
“barka dai zauna mana,”
ummi ta dan dosana da kujera duk ta muzanta da irin kallon da sale yake mata tun dazu data shigo. Haj ce ta tabo sale daya zama kurman wucin gadi tace,
“yadai?”
Washe baki yyi yana kallon haj ya juyo ya kalli ummi yace,
“haj wannan fa?”
A fakaice ta wurga masa harara tace,
“kai matar Bashari ce,”
dariya sale yyi yce,
“kur’ani an cuceta wannan gaula-gaula mahaukacin? Wlh da ace shi kare ne da yyi barna to amma dai meye marabar sa da karen tunda ba hankali.?”
Ummi ji tayi kamar an dauki mashi an soka mata sbd zafin mgnr da taji ana yabama mijinta. Haj ce tadan dungureshi tace,
“kaifa idan ka fara zuba sai kace ruwan sama,”
“toh ai gskyne hajjaju, ke yarinya kyakkyawa bakiji a ranki an cuceki ba a hadaki da mahaukaci?”
Ya kare mgnr da kallon ummi, kamar ta tashi ta zabga masa mari haka takeji amma ta hadiye abinda ya tokare mata, bata bashi amsa ba ta kalli haj suwaiba da Alama abinda sale ke fada be wani dameta ba, murmushi me ciwo tayi tana tashi tsaye tace,
“haj sai anjima dama na shigo ne mu gaisa”
“Toh”
haj tace a takaice. Sale yabi bayan ummi da kallo yana lashe baki, ummi na fita sale yace,
“kan uban can wannan hadadden gold din aka bawa mahaukaci hajjaju?”
Haj taja tsaki tace,
“kai bansan akuyanci me ka gani anan?”
Sale yace,
“tabdin gsky kina bukatar wankin ido dan bakya gani,”
haj suwaiba tace,
“zamu tattauna abinda ke gaban mune ko zaka tsaya shiririta?”
Mikewa sale yyi yace,
“kinga tafiyata sai na dawo,”
tsaki haj tayi batace komi ba matsalar gabanta ma ta isheta gashi ance ta kawo yara goma asha jini a qungiya.
~~~
Rai bace ta koma part dinsu nan taga har suraj ya tafi sai el-bash dake kan doguwar kujera ya rike ciki yana auna maganganun suraj na dazu.
Dining area ta wuce dan yunwa takeji ta zuba abinci ta fara ci.
El-bash ya bita da kallo yana nazarin fuskar ta da alama akwai abinda aka mata dan yaga ranta a bace yake, zaiso ji lumshe idonsa yyi yana jira ya danji dama2 dan ya haura sama yaga abinda akai mata.
****
Sale na fitowa ya fara tunanin duk yadda za’ai wannan dak’walar kazar (ummi) bazata subuce masa ba dole ya lashi zumarta tunda mijin ba hankali so kwace goruba a hannun kuturu bazatayi wahala ba.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
49
Abba da sauri ya fara hada takardun sa yanaso ya koma gida dan duk yau rabin hankalin sa yana wajen El-bash, yanaso ya kawar masa tarin tambayoyin da suka dirar masa a zuciya, gam…gam…gam.. Yaji ana masa knocking dan tsaki yaja dan so yake ya tafi amma baki sai zuwa masa suke, ci gaba da bugun akayi, badan yaso ba yace,
“yes come in”
suraj ne ya bude kofar hade da sallama, ganin suraj ne ya saki ransa hade da murmushi yace,
“zauna mana suraj ya fada yana nuna masa kujera,”
dan dukawa suraj yyi ya fara gaishe da Abba cikin girmamawa, Abba ya mika masa hannu dan suyi musabaha cike girmamawa Suraj ya mika nasa hannun, Bayan sun gaisa suraj ya zauna, Abba yace,
“ya aiki?”
Suraj yace,
“Alhamdulillah, dama Abba wata mgn ke tafe dani”
Abba yace,
“Inajin ka suraj gayamin,”
suraj yace,
“mgnr akan *EL-BASHEER* ne nasan tun daga jiya wayewar yau akwai tarin tambayoyin da suke dankare a zuciyar ka.” Abba an sosa masa inda yake masa kaikayi ya sake gyara zama yace,
“Tabbas mgnr ka haka take domin kun jefa tunani na a duhu inason nasan me kuke shiryawa game da aikin ku?”
Wata doguwar takarda suraj ya mikawa Abba yace,
“duk wasu bayanai da kke bukata Abba yana ciki, saidai kafin ka karanta inason na fada maka wani sako da aka bani na sanar maka, sakon biyu ne duk wanda aka fada maka ba’aso kace komai akai, na farko idan kaji hakuri zakayi, na biyu kuma zai girgiza ka ko ya baka matukar mamaki”
Da mmkin Abba yace,
“ka sake jefani cikin sarkakiya me kke nufi?”
Suraj yace,
“Sakon farko shine a yanzu daga nan babu inda zaka wuce sai airport nine ma zan kaika dan saura mintina kalilan jirgin ku zai tashi zaka bar kasar duk wasu abinda kke bukata yana bayan mota a cikin travelling bag, sako na biyu Albishirin ne zaka hadu da UMMAN EL-BASHEER, HAJ HAFSAT TSOHUWAR MATARKA da kke tunanin ta dade da mutuwa toh tana raye zaka sameta a kasar da jirgin ku ya sauka.”
a matukar kidime Abba ya jawo kwalar suraj jikinsa na rawa yace,
“me kuke shiryawa a kaina? Yaushe na fara wasa daku har kuke neman rainamin hankali?” yyi mgnr yana girgiza suraj duk hankalin sa ya tashi anya yaran nan ba rikakkun mahaukata bane? Toh idan ba haka ba ta ina mutum ya mutu kuma ya dawo? Sunkuyar da kai suraj yyi yana kokarin maida kwallar data taho masa sbd tausayin Abba yasan za’a rina ya fada a ransa, sake shi Abba yyi ya dawo kujera ya zauna hade da dafe kansa, cike da ladabi suraj yace,
“Abba lkcn da Ummah ta rasu kana nan?”
Kamar Abba bazaice komai ba can yace,
“Ina dubai”
Suraj yace,
“So Abba ka yadda d mgnr mu shiyasa ma nace idan ka shiga jirgi ka karanta paper nan.”+
Hayaniya suka fara jiyowa daga wajen kamfanin Abba, Da sauri suraj ya leka ta window dake acan sama office din Abba yake, da sauri ya juyo gun Abba yace,
“Abba u see time dinmu na wucewa”
Abba yace,
“me ka gano?”
Daramm…, da sauri Abba ya mike jin karar bindiga na tashi, hankali tashe Abba ya dauko wayarsa yana laluben number, suraj ya kamo hannun Abba yace,
“wa zaka kira?”
“Alhji Rabe mana shi zan kira”
Da sauri suraj ya dafe wayar yana fadin,
“Noo.., just follow me”
Ya fada yana jan hannun Abba, gaba1 ma lissafin Abba ya kwace ya kasa fahimtar ta ina wannan lamarin ke barkowa, baida zabi daya wuce bin bayansa, cike da dabara cikin kwarewar aiki da taimakon Allah su suraj suka samu damar escape akan harin da aka kai kamfanin, can baya inda suraj yyi parking suka nufa nan ya tura Abba ciki da sauri sbd hango wasu da suka biyosu yyi, a zafafe yyi ribas ya manni motar a guje.
“Ohhh shittt…”
wanda suka biyosu wani daga ciki ya fada yana dukan dayan hannun sa naushi, Wayarsa ya zaro ya dannan kiran number, Daga can bangaren akace,
“komai nrml?”
” Oga kayi hakuri yyi escape”
“Mtwssssss Very stupid”
aka fada ana kashe wayar cikin jin haushi.
Tunda suka fara falfala gudu suraj be tsaya ba sai a airport, cikin hanzari suka fito mota, lkcn saura 5mins jirgi zai tashi, hankalin Abba duk ya kasa kwanciya yace,
“suraj wai meke faruwa dani ne? Meyasa ake farautar rayuwa na?” Suraj yace,
“Abba muna aikin mu bisa tsari ko baka kasar nan idon tilon danka akanka yake duk wani move naka yana gani kanada tarin makiya hagu da damanka, a dalilinka ya maida kansa mahaukacin dole”
Kama hannun sa suraj yyi yace,
“Abba yanzu ba lkcn mgn bane dan duk amsar ka naga takardan nan barin ka kasarnan a yanzu shine mataki na biyun nasarar aikin mu” Abba zaiyi mgn yaji ana kiran sunan sa haka ya hakura ya tafi suraj na daga masa hannu. Saida yaga tashin su sannan suraj yabar airport, saidai wannan karon wata motar ya shiga wani daya lullube jikinsa da bakaken kaya har fuska shike driving din.
*Nasan fans zasu ce wata sabuwa😃 karku damu komai zai warware** 🏌🏻♀🏌🏻♀🏌🏻♀EL-BASHEER*
*NUCEEY LUV NOVEL HOUSE FACEBOOK* wannan page din kyauta ne a gareku naji dadin yadda kukemin Sharhi❤
*EL-BASHEER FANS GROUP* wanna page din tukwice ne a gareku, yadda kukemin comments abin na birgeni Allah yabar kauna❤
Na
Nuceeyluv😘
50
Saida sukayi nisa da airport me driving din ya sake daukar wata hanya daban, saida sukayi tafiya me dan tsawo suka iso wani makeken gida, har a lkcn babu wanda yyi mgn, ba tare da bata lkci ba me gadin gidan ya wangale kofa, habawa tun daga gate din gidan mutum ya kalla yasan an zuba naira sosai bare ace ya shigo, abin ba’ace komai, parking yyi ya kashe motar nan suka fito hannun me driving din rike da system, da dan sassarfa suka karasa cikin gidan, suna shiga ya yaye fuskar sa, sai ga fuskar *EL-BASHEER* ta bayyana, suraj ya sara masa yana fadin,
“Gwaska”
dan hararan sa yyi yace,
“ni da Allah zauna muyi abinda ya kawo mu inason komawa gida” suraj yace,
“kodai kanason komawa wajen little baby?”
Yyi mgnr da sigar tsokana,
“Mtwss…..”
El-bash yaja tsaki yana fadin,
“kanada matsala wlhy”
yyi mgnr yana operating system, zama suraj yyi yana er dariya kawai. Kusan mintina ya dauka yana danne2 a system din har ya gama kafin yace,
“kaga duk wasu bayanai da muke son samu muna samunsu sannu a hankali, mutanen nan zasuyi meeting nan da jibi kuma a wannan ranar babban nasu zaizo Alhji mai kano da kaji suna fada, so zamu sa ido sosai a kansu, Mgnr kamfanin Abba kuma Alhji Rabe ne yasa a kashe Abba sbd yanason kamfanin ya dawo hannun sa gaba1 kuma yana ganin banda hankali ba komai zan iyayi akai ba, and again….,”
dol..dol..dol. Wani red abu ya fara signal daga gefen system din, da sauri el-bash ya danna tare da manna karamin abu a kunnen sa, mgnr Alhji rabe yaji da haj suwaiba suna mgn, Dan haka ya tsaya sauraro, ji yyi Alhji rabe na fadin,
“ke suwaiba Mahaukacin gidan ki kuwa na gske ne?”
Haj tace,
“ban gane ba me kkeso kace Rabe?”
Alhji rabe yace,
“keni je ki dubamin part dinsa yana nan?”
Haj suwaiba tace,
“Ina gidan kawata haj sadiya yanzu Amma bari naje na duba tunda ba nisa”
Kit Alhj Rabe ya katse wayar yana huci dan ya dade yana shirya yadda zai kashe Abba amma rana daya an wargaza masa shirinsa daya dau tsawon lkci yanayi.+
Da sauri ya fisge abin kunnen sa ya mike tsaye yana kashe system, suraj yace,
“me kaji?”
Cewa yake,
“suraj muyi sauri aikin mu zai baci”
“Innalillahi”
suraj ya fada shima yana mikewa, suna tafe el-bash na zayyane masa komai, a hanzarce suraj ya karbi car key wajen el-bash, shi kuma ya rufe jikinsa kamar dazu, a 360 suka manni motar a guje, tsakanin su da gida kusan tafiyar minti 25 ce, yyind haj suwaiba befi 15mins ta isa gidan ba, A bangaren Alhji Rabe ma kasa nutsuwa yyi ya zari motar sa ya fito da sauri shima tafiyar sa be wuce 20mins ba da gidan.
Ana wata ga wata ko waye zai fara isa.?
******
Abba yana cikin jirgi abin duniya duk ya ishe shi, zaro takardan nan yyi ya fara karantawa kamar haka:
_Assalamu Alaykum, Abba nasan a yanzu da kake karanta wasikar nan kana cikin rudani da tashin hankali, saidai inaso kayi hakuri bisa tarin abubuwan da na boye maka, badan komai nayi hakan ba sai dan sbd ku iyayena, Abba kisan da aka zo yi maka da dare ba kowa bane yasa a kashe ka ba sai matarka haj suwaiba wannan shirin tane,._
Wani jiri ne yaso kwashe Abba sbd shiga tsananin rudani da tashin hankali, Lalle hausawa sun iya mgn da sukace Ashe makashin ka yana tare dakai, yanzu zaman cin amana take dashi be sani ba? Kaiii duniyaaa…, sake ci gaba da karatun yyi,
_mgn ta biyu kuma Alhji Rabe daka dauki Amanar dukiyar ka ka bashi har ka dorashi bisa kamfanin ka na kano shine yasa a kashe ka dan kamfanin ya dawo nasa ya dade yana wannan kullalliyar yana shakkar yi ne sbd yana kallo na da kuma yanayin aiki na, a lkcn na zarge shi sai dana maida kaina mahaukaci na tabbatar da zargina ya zama gsky, Hmmm Abba kasan meyasa na maida kaina mahaukaci? I know zakaso kaji amsa, to wannan amsar tana wajen ummana ka gaishe min da ita idan ka isa kasar Pakistan, itace ma zata tarbe ka tana jiranka a airport, yanzu bayanan dana maka a dunkule suke ummana ita zatayi maka fashin baqi uwa uba zata gaya maka meyasa ta zabi boye kanta tsawon lkci a matsayin ta mutu? Fatan Alkhairi Allah ya saukeku lpy Abba._
Wata irin zazzafar zuface ta dinga ketowa Abba ta goshi ta cikin jiki,mamaki da Al’ajabi ne suka taru sukayi masa dirar makiyiya, wai meyasa yanzu Amana tayi karanci ne a duniya? Kowa kokarin gyara kansa yake, baya manta haduwar sa da rabe turin baro yake lkcn ya gama secondary baida halin ci gaba,
idanuwansa na zubda hawaye yazo neman taimako gun Abba mahaifiyar sa ba lpy zai biya kudin mgni, Alhji usman akwai tausayi ya dauki kudi ya bashi, bayan taji sauki yazo da mahaifiyar tasa yi masa godiya, Alhji usman yace ai ba komai dan Allah yyi musu badan su gode ba lkcn El-bash na jss3, sunji dadi matuka, har zasu juya ya sake kiransu yace yama sunan ka? Yace Rabe, yace dakyau ka gama kr2 ne? Eh na gama ban samu ci gaba ba ina sana’ar turin baro, Alhji usman yace Eyya kace babanka baya raye? Eh ya fada yana risina kai, okay yanzu me kkeson karanta idan ka samu hali?
Rabe yace Business Admin, wow good choice Alhji usman ya fada, yace ka kawo min takardun ka zan nema ma buk Insha Allahu zan dauki nauyi, da murna shi da babarsa kande suka hau masa godiya. Nan dai suka tafi. Tun daga wannan rana Alhji usman ya dau nauyinsa kuma yana masa Alheri sosai, babar rabe tana girmama Alhji usman kullum tacema danta duk sanda kaci amanar mutumin nan ban yafe maka ba,
a haka ya gama kr2 Alhji usman ya jawo shi ya dora kan kamfanin sa na kano, Rabe an koma Alhji, sai gashi hasada da kyashi sun fara masa yawo a zuciya, ji yyi a ransa yanason yafi Alhji usman kudi da matsayi saidai babu hanya, Suwaiba itace me musu sharar office ita taja Alhji Rabe kungiya tunda taga yanada zalama, kuma itama so take yyi mata hanya ta auri Alhji usman, ba bata lkci kuwa ya zubawa Ahji usman mgnin Asirin da ta karbo dan ya aureta, sbd haka kurum jininsa be hadu dana haj hafsat ba da kuma danta El-bash.
Wani dogon numfashi Abba yaja sbd tunanin da yyi lalle ya kara yadda dan Adam butule ne ba duka suka san Alheri ba.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
51
Sosai suke falfala gudu kamar zasu tashi sama har wasu masu tukin na lekowa ta window ana zagin su sbd irin mahaukacin gudin da suke, saidai basu kula ba sbd wutar dake gabansu suke son kashewa,
bangaren haj suwaiba driving take nrml tunda batasan akwai masu son rigata zuwa gida ba, haka ma Alhj Rabe nrml ne saidai yafi haj sauri, a cikin gudin da suke suka hango Alhj Rabe a gabansu, a rikice suraj ya juyo yana kallon El-bash da tun dazu yakejin kamar ya fisge driving din yace,
“Kaga Alhj Rabe fa da Alama can zaije” El-bash ya daga kai ya hango motar sun kusa kamo sa, kallon suraj yyi yace,
“kara gudu idan kaje saitin sa ka bade shi da hayaki sai ka sake manna gudu”
daidai lkcn sun iso wajensa Suraj ya bade gaban Alhj Rabe da hayaki sannan ya zuri motar a guje suka bace masa, Tul…tul..tul Alhj Rabe yahau tari yana toshe hancin sa hade da dage glass din mota sbd hayakin daya shaka, dan saurara gudunsa yyi yana jan tsaki a fili yace,
“yazu haka yaran nan ne da suka sha giya suka bugu suke mana tukin ganganci akan titi mtwss….”
Yaja tsaki, sam be lura da kalar motar bama tunda sun bacewa ganinsa,
Basu dade da wuce shi ba suka hango haj suwaiba na shirin karya kwanar layin gidan, El-bash yace,
“mubi ta bayan gida ka saukeni basai mun hada hanya da ita ba”
“okay”
suraj yace nan suka canja hanya inda zata kaisu ta bayan gidansu, basu dau lkci ba kuwa sai gasu a bayan gidan, Ta can inda garden dinsa yake saitin wajen suka tsaya, da sauri ya fito mota ya kama katangar wajen ya haye, yana dira kasa suraj na barin wajen da sauri, koda suraj ya fito fili daga nesa ya hango haj suwaiba tana shiga cikin gidan, dan sauke ajiyar zuciya yyi yana fatan sunsha.
+
El-bash na dira yabi ta corridor dazai sadashi da cikin parlo kai tsaye, yyi sa’a ummi bata parlon kamar dazu, direct dakinsa ya wuce, aiko yana shiga yaji ana knocking kofar parlo, da sauri ya canja kayansa zuwa kanana sannan ya fito waje, daidai lkcn ummi ta fito a daki, kallon sa tayi kamar tayi mgn sai ta share har yanzu ranta a bace yake akan abinda aka mata da safe, ya rigata zuwa parlon saidai yana zuwa ya zauna kamar yadda ya saba ya hade rai sosai. Be jima da zaman ba ummi ta bude kofa, haj ce ta sako kai tace,
“wanne sabon kinibibi ne ake danna sakata a parlon? Me zakici da mahaukaci banda abinki”
ummi batace komai ba ta bar mata wajen ta dawo ciki ta zauna, turus haj tayi ganin El-bash kan kujera yana lankwasa yatsun sa kamar yadda ya saba sometimes, wata sassayar ajiyar zuciya ta saki a boye sbd a tsananin fargaba take dan muddin akace el-bash nada hankali kashinta ya bushe, zatayi mgn kenan sukaga an fado musu parlon, ba kowa bane sai Alhj rabe sai zabga sauri yake babu sallama ya fado musu, Ummi bata taba ganin sa ba dan haka ta mike a tsorace tace,
“baba lpy?”
Alhj Rabe be amsa mata ba sai tmbyr daya jefo mata yace,
“tun yaushe yake zaune anan?”
Ummi da mmki tace,
“Tun safe mana ai nan ya saba zama duk sanda gari ya waye akwai matsala ne? Ko me mgni aka samo?”
“Mtwsss…”
Alhj Rabe yaja tsaki cikin jin haushi batare daya bata amsa ba ya fice a parlon, sai ga haj ma ta bishi, binsu da kallo El-bash yyi kasa2 yana dariya a ransa kananun kwari kawai, abin ya daurewa ummi kai dan haka tabi bayansu, zata sa kafa ta fita kenan taji an fisgo ta hade da maida kofar akasa mata lock,
a kidime ta juyo dan batasan waye ya mata hakan ba, amma ina kafin ta tantance waye anyi sama da ita, ji tayi kurum an fara tafiya ana taka stairs ba’a direta a ko’ina ba sai a dakin El-bash, mikewa tayi tana binsa da kallon mmki, A hankali tace,
“lpyr ka?”
Gani tayi ya fisgo ta jikinsa, Kwace kanta takeson yi yaki barinta, dan har yanzu lemon dayasha shima be masa aiki ba dauriya kurum yake tun dazu, sakar mata nauyinsa yyi sai gashi tayi laushi, hakan ya bashi damar kissing dinta aduk inda yaso a jikinta, dake duguwar riga tasa sai besha wahalar zuge zip dinta ba, tuni ya rike Albarkatun kirjin ta ya fara sha tamkar jariri,
ummi fa ba dutse bace dan duk lkcn da yyi romancing dinta tana shiga yanayi sosai, a wannan karon kam mika wuya tayi, da hannunta tasa ta dinga balle botir din gaban rigar sa, sai gashi wasan nasu ya canja salo, domin itama duk inda ya latsa saita rama a ganinta ita kadai yake bari a yanayi idan ya jagwalgwala ta, shiyasa itama tasa a ranta saita rama batasan ta sake kunna El-bash bane, sun kwashe mintina suna romancing junan su, El-bash har mantawa yake da wai yana pretending hauka, a wasan nasu yaji ya samu sassauci ssai fiye da lemon tsami, dan haka ya rungume ta tsam ba tare da yyi motsi ba har na tsawon dakika uku, kafin ya saketa a hankali yana mirginawa gefe, ummi itama gefen ta koma ta sauke numfashi a hankali hade d lumshe ido jikinta ba riga dan bra dinta ma tana kasa inda El-bash ya jefar,
Tsurawa kirjin nata ido yyi, yadda suke fresh koyaushe shike kara birgeshi, yanason maida ta mace sosai amma idan ya kalli fuskar ta sai ya ganta very young amma fa kirjinta acike yake haka ma hips dinta. Dan numfashi yaja kadan ya mike akan gadon ya nufi toilet, ummi najin alamun wankan sa itama ta kwashi sauran kayanta ta koma dakinta.
*****
Su Alhj Rabe na zuwa harabar gidan suka tsaya, haj tace,
“wai duk mene ka tada hankalin ka a kansa?”
Alhj rabe yaja tsaki tabbas haj batasan abinda yake kullawa ba dan a tunanin ta ko yana tsoron El-bash kar yanada hankali ne ya kamasu dan dama jami’an tsaro su suke nema ruwa a jallo, tsakin ya sake ja ya canja mgnr da fadin,
“kinsan Alhj mai kano jibin nan zaizo gari ya kamata ace mun kula ssai sbd tsaro”
dariya haj tayi tace,
“haba Rabe ban sanka da tsoro ba wlh to duka shi marar hankali meya sani? Ni duk ka dagamin hankali ma wlh inace wani abu ne, indai akan haukan Bashari ne karka daga hankalin ka akai domin inada tabbatacin boka dan tsito bazai min karya ba kai nifa yadda yacemin Dandalin baqaqen Aljanu ne a kansa irin fitinannun nan masu wuyar barin mutum baka ganin yanda yake hade rai koyaushe? Ai sune suka maidashi haka babu alamun Rahama a tattare dasu.”
Dan sauke ajiyar zuciya Alhj Rabe yyi ya danji sanyi kadan, to amma abinda ya daure masa kai waye ya taimaki Alhj Usman? Kamar yadda yaransa suka fada masa? Abin ne da caza kai….,
“baka yadda bane?” Haj suwaiba ta katse tunanin sa,
“Ah na yadda mana Kuma hankali na ya kwanta sosai”
haj suwaiba tace,
“haka nakeson ji, badan Sakina taje kauyan ubanta bama ai da itace zata duba mana kafin muzo”
er dariya Alhj Rabe yyi tunowa da yyi Sakina tana gidansa na hutawa tun sati biyu da suka wuce ashe karya tayi agida tace taje kauye.
Haj da batasan dariyar me yake ba itama sai ta biyeshi da dariyar tana daga masa hannu lkcn da yake shiga mota, Baba me gadi yana daga can yana jinsu ganin zasu kalleshi ya kara radio a kunnen sa yana goga aswaki, Haj ce tace me gadi bude masa mana, da sauri ya bude yana daga masa hannu shima,
Baba me gadi kanin Baban ummi daya bada auren ta sam yaki barin gadin kamar yadda Abba yaso yace shikam yana nan Har sai ranar da El-bash ya samu sauki sbd shi ya kawo shi, ganin haka Abba ya ninka Albashin sa, sometimes ummi takan je su gaisa saidai fa sai ya gadama ya amsa, shiyasa ba koyaushe take zuwa ba.
~~~~
Cikin Rahamar ubangiji Su Alhj Usman jirgin su ya sauka karfe shidan safe a babbar birnin Pakistan, a cikin jerin masu saukar Abba ya shigo sahun su, nan ya fara raba ido cikin zaquwa dason ganin Matarsa, duk inda ya wulga baiga kowa ba, yana nan tsaye sai ji yyi an rufe idonsa ta baya.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
52
Wanka ta sake tayi sallah ta fito waje sai lkcn tayi tunanin abinda zata musu d dare na rana ma taga be wani ci ba, sharewa tayi ta zauna kawai ta dauki remote tana kokarin canja channel, ji tayi ana kokarin bude kofar parlon su, da mmki ta mike ta isa kofar dan lkcn bayan magrib ne, tana budewa tayi baya a tsorace, Sale ne a bakin kofar ya wangale mata baki yana dariya danno kansa ciki yaso yi ummi tayi saurin maida kofar, da karfi ya tare yana sake maida kofar baya, a lkcn ummi riga da skirt ne a jikin ta gashi bata sakko da hijab ba sanin cewa dare ya fara yi, kutso kansa cikin parlon yyi yana sake washe baki yace,
“haba er kyakkyawa mene naga duk kin wani birkice sai kace kinga dodo?”
Yyi mgnr yana karasowa ciki, ja da baya ummi tayi tace,
“lpy ka shigoma mutane da wannan daren?”
Yana tsaye hannunsa a saman wandon sa ya kama irin yadda wasu mazan keyi yace,
“haba beauty irin wannan kora da hali kamar baki gane me nazo yi ba”
ya karasa mgnr yana kashe mata ido daya,
“Yah Subhanallahi!” Ummi ta furta tana dora hannu akai tace,
“kai kana hauka ne? Pls ka fitar min a parlo kafin wlh na tara maka jama’a”
tayi mgnr jikinta na rawa sbd tsoro yau taga ta kanta waye zai ceceta gun wannan bugaggen? Dariya sale yyi yana sake jan wandon sa sama hade d sake rikewa yace,
“ke wlh babu me hanani kwana dake yau tunda naga alama bakiyi dacen mijin dazai kawar miki da kaikayi ba”
yyi mgnr yana lashe baki hade da nufo wajenta zai rungume ta,
+
a gigice ummi ta juya tayi hanyar stairs tana waigen sale daya taho da saurin shima duk ya matsu ya kawar da sha’awar sa shi ko a tsaye yyi ya huta dan tun daya ganta ya kasa nutsuwa da begen surar ta, garin sauri da waigen baya da take yasa tayi missn step sai gashi tayi luuuu… Zata fadi ba zato tajita a jikin mutum ya rungume ta tsam a kirjin sa, wata wawiyar ajiyar zuciya ta sauke dan ta gama sadaukarwa ta fadi Allah ya tsare ta.
El-bash kenan tun shigowar Sale yake tsakiyar stairs din ya zuba hannayen sa cikin Aljihun wandon sa yana kallon su, fuskar nan tasa a hade tamkar hadarin tsakiyar Agusta ransa a matukar bace yake kamar yaje ya shaqe sale ya huta yakeji.
Dan dam… Sale yyi sbd yadda yaga El-bash babu wasa sam a fuskar sa ko banza yana masa kwarjini, dan dakewa yyi yana yake yace,
“aikin banza nan din wajen buya kikazo kome? Mtssss anyi asararriya” yyi mgnr yana ci gaba da takowa stairs din, a tsorace ummi tayi nufin zare jikinta daya rungume ta gudu daki taji el-bash ya sake matse ta a jikin shi, a kidime tace,
“pls ka sake ni zai illatani dan Allah.”
Banza yyi da ita, Sale na karasowa Cikin zafin nama El-bash yyi ball dashi sai ga sale wul…wul…wul.. Yana gangarawa kasa, sale be sake tantance kansa ba yaji an kaimasa shaqa, saiga idon sale ya fito gwala-gwala dan azaba, kokarin kwace kansa yyi ya kasa, El-bash na tsaye ummi ta rungume shi ta baya duk a tsorace take,
saida yaji wuyar shaqa el-bash ya sake shi, tuni sale ya fara tari dakyar, shirin guduwa yyi El-bash ya riko shi zuwa yanzu sale ya kasa daurewa yace,
“dan Allah kuyi hakuri yaku baqaqen Aljanu bazan sake shiga sabgar ku….”
Be karasa mgnr ba yaji an sake dauke shi da tagwayen mari har sau hudu tuni bakin sale ya fashe yana fitar da jini,
kwallar azabace ta fara tararwa Sale yau ya shiga ukun sa yaje hannun maza, be gama hucewa da zafin ciwo ba yaji an sake hankada shi sai gashi ya gwari da kofa, d sauri ya mike dakyar ya bude kofar ya fita har zai rufe kofar ya leko yana kallon ummi be daddara ba cikin haki yace,
“kuma wlh kisa a ranki ko cikin dare ne saina dawo lkcn wannan Mahaukacin karen yyi bcci zan…..”
garammm yaja musu kofar yna barin wajen a guje sbd ganin El-bash ya nufo sa gadan gadan.
A bangaren ummi har ta fara jin dadin an huce mata takaicin da sale ya cusa mata d safe d kuma yanzu, hankalin ta ya sake tashi da taji yace zai dawo ko cikin dare ne.
Zama tayi kan kujera ta dafe kanta hankali tashe, El-bash ya juyo ya kalleta dawowa yyi kusa da itan ya zauna shima batare da yyi mata komai ba saima zuba mata ido da yyi, Dagowa ummi tayi tana kallon sa lkcn ya kawar da nasa kallon, a fili tace,
“wai meyasa mutane basu da imani ne? Meka tare musu kam? Shin wanda hankalin sa ya gushe shi ba mutum bane? Meyasa wasu keda son kansu ne? Why? Whyyyy……..????” Ummmi ta karasa mgnr muryar ta na rawa sbd kukan daya taho mata, kanta ta kifa kan cinyoyin El-bash ta fara rusa kuka me matukar taba zuciyar me sauraro, ji yyi gaba1 jikinsa yyi sanyi, sai yake ganin anya baya cutar ta kuwa? Kodai ya nuna mata lpyr sa kalau yake? Zuciyar sa tayi rauni matuka domin har cikin zuciyar sa yakejin kukan nata,
hannayen sa yasa ya karasa jawota jikinsa gaba1 ya rungume ta tsaf a jikinsa yana dan bubbuga bayan ta, ummi a wannan lkcn babu abinda take bukata sai lallashi dan haka ta sake kankame shi sosai tana fitar da sauti me cike da tausayi, sunyi kusan 20mins a haka har ummi taji zuciyar ta tayi sanyi ba kamar dazu ba, dan haka ta mike a hankali tana zare hannun El-bash zaton ta bcci yyi a haka sbd taji ya daina motsi, tana tashi ya bude idonsa yana kallon ta, batace komai ba ta mike tayi hanyar kitchen, ruwa da cup ta dauko ta dawo parlon har lkcn yana a yadda ta barshi,
zama tayi ta bude ruwan ta tsiyaya rabi cikin cup, dakko ruwan tayi ta kalleshi taga ita yake kallo, dan murmushi tayi sannan ta kauda kai, bismillah ta farayi sannan ta fara hura iskar bakinta da Addu’o’i fatan ta idan ma akwai wani kulli kan El-bash Allah ya warware shi.
Duk abinda takeyi El-bash yana kallon ta sannan yana jinta tunda a fili takeyi, dan murmushi yyi yana kara jinjina karamci irin na ummi, wato da haukan gske yake haka zatayi ta fama dashi? Allah sarki ya fada a ransa, miko masa cup din tayi taga ya karba, bismillah yyi a ransa sannan ya shanye ruwan tass, Ummi taji dadi matuka sbd btayi tunanin zaisha ta sauki haka ba. Food dinsa ta dauko masa nan ma data zuba yaci abin ya mata dadi har itama ta samu damar ci haka kawai taji ta cikin nishadi sbd a plate daya sukaci.
*****
Juyi take cikin blanket da taji dan motsi sai ta firgita sbd mgnr Sale ta kasa fita ranta da yace komai dare zai shigo, dukda tasa lock a ko’ina hankalin ta be kwanta b gani take zai iya balla musu kofa ya shigo, bata da wani option sama d ta gudu dakin El-bash ko banza ta samu security, shawarar kuwa tabi, ta fito a dakin ta da sauri daga ita sai sleeping dress doguwa iya cinya sai zani data dora akai, cikin sa’a ta murda dakin taji a bude, da sauri kuwa ta shige hade dasa lock, tana jiyowa taga El-bash tsaye jikin mirror da dan karamin towel daure a qugun sa wani towel din a saman gashin kansa yana tsane ruwa da alama wanka ya fito, Ummi tace, “na bani,” juyowa yyi yana kallon ta yana mmkin meya kawota dakinsa a wannan lkcin? Ummi kamar tasan tunanin da yake tace,
“am…ah…yauwa nace ba?”
Ta fara masa Alama da hannu,
“yau zan dan kwana a dakin ka sbd tunanin mgnr sale ta kasa fita raina ina tsoron yazo cikin dare”
tayi mgnr tana kwatanta masa yanayin mgnr kamar wani kurma, ganin yazuba mata ido ta nufi gadon, pillows din kai ta jera a tsakiya sannan ta kalleshi taga still ita yake kallo saidai zuwa yanzu hannayen sa ya rungume kan kirjin sa,
“yauwa ni zan kwanta anan kai kuma can”
Ummi tayi mgnr tana nuna masa,
_”Bala’i”_
El-bash ya furta a ransa yana me binta da kallo, ummi bata lura da irin kallon da yake mata ba tayi kwanciyar ta tana jan blanket dinsa tare da tura masa rabin bangaren sa shima idan ya hau yaja.EL-BASHEER*
*godiya ta musamman ga en group din EL-BASHEER FANS, naji dadin kulawar ku gareni kuma Alhamdulillah naji sauki, sauran fans wasu sun sani banji dadi ba 2days kuma sunmin Addu’ah suma na gode a lot*
*Yau da gobe sai Allah, jiki da jini dan adam ajizi, a dinga ma juna uzuri plss👏🏻* ( _ga masu cewa muna wulakanci bama typing_ 😊😊😊)
+
*SONSO FISABILILLAH, ALL EL-BASHEER FANS*
Na
Nuceeyluv😘
53
“Hmmm…..!” El-bash yaja ajiyar zuciya yana shafa sumar kansa gani yyi dgske ummin rufe ido tayi, a fili yace,
“lalle yarinyar nan so kike ki kasheni da raina”
yyi mgnr kasa2 yana me juyawa ya kalli madubi, karewa halittar sa kallo yyi yana wani tunanin daban,
“hmm….!”
Yasake sauke ajiyar zuciya hade da murmushin gefen baki, dan cije lips dinsa yyi yana me jawo cream dinsa me kamshi yana mulke jikinsa a jima kadan sai yyi murmushi ya cije lips a haka ya gama shafe-shafen sa ya samu turare me dadin kamshi ya feshe jikinsa, wando kawai ya dauka ya sanya jikin ya dauki towels din yakai toilet ya shanya,
dake bcci ne a idon ummi harya fara fisgar ta shiyasa ma batasan lkcn daya gama shiri ba, matsowa yyi gaban gadon ya sake karewa pillows din kallo data jera ta musu tsakani, dan murmushi yyi a ransa da alama dai yasamu tsuntsu daga sama gasasshe, jerin pillows din ya fara jefarwa kasa yana mgn a fili kasa2,
“dan banza haka kurum zaka shiga tsakanin ma’aurata ni da ko duminta banji ba daidai da 20mins”
ya karasa mgnr yana jifa da pillow na karshe,
hayewa gadon yyi ya juyo da fuskar sa gefen da take, gani yyi tana bccin ta hankali kwance ga dan bakin ta nan dake bashi sha’awa yyi shape kamar zero, haka na fulanin ta dake birkitar dashi yana kallon su ta transparent rigar data saka babu bra a ciki sbd bata cika son bcci da bra ba, zanin data daura yadan zame dama rigar iya cinya ce so data kwanta sai ta sake yin sama hakan ya bashi damar karewa santala-santalan fararen cinyoyin ta kallo, hannu yakai zai shafo su ya fasa, bedside lamp ya kashe kafin ya matsa kusa da ummi sosai, jawota yyi ta shige jikinsa,
ummi sama2 taji hakan saidai dake tana da son jiki sai ta sake manne masa a kirji bcci yana idonta,
“Huuuu…!”
El-bash yaja wata boyayyar ajiyar zuciya sbd yadda yaji ummi gaba1 a jikinsa, take tsuminsa ya fara harbawa tsikar jikinsa ta tashi ssai, damko gashin kanta yyi yana shafawa a hankali yyinda yake hura iskar bakinsa, ummi a firgice ta bude ido tana kokarin kwace kanta jikinta na rawa tace,
“na shiga uku Nayi gudun barewa na tadda zago”
Tayi mgnr tana kokarin kwace kanta, wannan mutsiniyar da take shi ya sake birkita El-bash, kokarin cire mata riga yyi ummi ta tsorata jikinta na rawa tace,
“dan Allah ka kyaleni zan barma dakin ka ma….”
bata karasa zancen ba taji ya hade bakinsu waje daya, duk yadda ummi taso kwace kanta kasawa tayi saima jinsa da tayi yana fitar da numfashi sosai yana sake damkar ta kamar wanda zai tsaga kirjinsa ya shigar ta ciki, ji tayi ko’ina na jikinsa yana rawa sai kissn dinta yake kota ina yana juyata duk inda yaso, gaba1 ya birkita mata nata lissafin itama, ada kwacewa taso yi amma daga baya irin abubuwan da yake mata saiya zarta tunanin ta, irin abunda yake mata duk wata mace me lafiya ta hadu da el-bash dole ta mika wuya,
hakan ta kasance da ummi, ita kanta takai makurar da bazata iya jurewa ba, dan haka ta fara taba duk inda tasan ya taba mata, hakan da ummi tayi sai ya canja salon wasan nasu har takai ga El-bash ya nemi hakkin sa, ummi gaba1 ya gama jikata da salon kaunar sa, dan haka ba bata lkci ta amince batasan dawar garin ba saida taji ya shigeta, wata gigitacciyar kara ta saki tana kokarin ture shi.
El-bash yyi nisan da bayajin kira dan haka ko sauraran koken ummi beyi ba, saida Al’amura suka wakana El-bash ya dawo saiti yyinda ummi ta jigata har tana sauke ajiyar zuciyar wahala, Gefe ya koma ya kwanta ya jawota saman kirjinsa ya rungumeta tsam kamar ance za’a kwace masa ita, duk wani saukar numfashin ta jinsa yake har cikin ransa,
ita kuwa sai ajiyar zuciyar take azaba ta isheta, tana tunanin baida hankalin dazai kula da ita taji ya rungume ta, taji dadi kwarai daya nuna mata kulawa dukda yana halin hauka, badan azabar da takeji a kasan ta ba zataso su kasance a hakan batasan meyasa ba taji wani bahagon sonsa na fisgar ta, ada tafi maida hakan tausayin sa take ashe abin ba haka yake ba, yanda takeji a ransa ya wuce a kirashi d tausayi kawai saidai ace SO,
A bangaren El-bash ma kusan tunani daya suke da ummi, ada yana mata kallon wacce ta cancanci ya mutunta sbd kulawar ta gareshi sai kuma yaji yanda yake jinta a ransa ya wuce a kirashi da iya hakan saidai ace wacce kke KAUNA, shin dame zai sakawa ummi? Ta bashi farincikin dabe taba samu ba a rayuwa, ta zauna dashi a daidai lkcin da ya kamata ta kyamace shi, ta amince masa batare data san meye makomar ta a gareshi ba, itakam wacce irin sassanyar zuciya Allah ya bata? Gsky ta cancanci fiye da komai a wajen sa, yana kammla aikin gabansa zai shayar da ita zumar kaunar sa zai riritata zai bata dukkan rayuwar sa wannan Alkawari ne yyi mata ya karasa tunanin yna me sake kissing din kan lips dinta,
ummi tanaji tayi shiru dan ji take kamar sonsa na fisgar ta, a hankali ya zameta daga jikinsa lkcn 12am na dare, dakyar ya mike ya wuce bathroom yana zuwa ya hadama kansa ruwa yyi wanka, sake hada ruwan dumi yyi ya dawo daki, ummi na kwance taji anyi sama da ita, yana sata ruwan zafi ta bude ido da sauri tana matsar hawaye sbd radadin da taji data shiga ruwan zafi,
fitowa El-bash yyi ya dawo daki, dukda ba wani baci bedsheet din yyi sosai ba, amma saida ya yaye ya sake shimfida me taushi, dayan ya nufi toilet dashi, lkcn ummi tayi luf cikin ruwan dumi tanajin dadin yadda yake shigar ta, cikin washing machine ya saka, sannan ya jawo mata kofar ya dawo daki ya tada sallar nafila, yana me godiya ga Allah daya bashi wannan babbar kyauta me tsoka,
harya idar ummi na toilet sai canja ruwa take daya huce ta canja wani, lkcn daya shiga yaga tana kokarin jawo towel alamar ta gama, tana ganin ya shigo ta rufe ido da tafikan hannun ta, dan kauda kansa yyi yana murmushi, kafin ya juyo a ransa yace nan din kunyata takeji? Ah lalle kunyar bata gama tafiya ba yyi mgnr yana nadota a towel, har kan gado ya direta sannan ya dauko cream dinsa ya shafa mata sbd yaji yanayin garin dadan sanyi, wani gajeran wandon sa da singlet dinsa ya miko mata, karba ummi tayi ta saka tana kokarin kama gashinta daya hargitse,
binta da kallo El-bash yyi yana karewa halittar kirjinta kallo, dukda babu bra haka suke tsaye nipples dinta na masa wlcm, ganin zata kama kanta da ribbon ya rike hannun ta, ummi ta tsaya kallon ikon Allah, kan mirror taga ya aje shi sannan ya dawo kan gadon, jawota yyi ta fada jikinsa, yaja musu duvet ya rufe su, hannu yasa ya kashe bedside lamp, sannan ya sake rungume ta tsam a jikin sa, ba tare da bata lkci ba kuwa bcci yyi gaba dasu.
ASUBA TA GARI Umm-El-bash.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
54
A banagaren Abba kuwa koda yaji an rufe masa ido ya saki sassanyar ajiyar zuciya, juyo da ita yyi ta dawo gabansa ya rungume ta tsam a jikin sa, itama umma rungumar tasa tayi, sunyi kusan 5mins a haka suka saki juya, Abba ya zuba mata ido ko kyaftawa bayayi tambayoyi ne fal ransa amma ya rasa ta ina zai fara? Kazalika canjawar haj Hafsat shike kara narkar dashi yadda yaga ta koma kamar er 28yrs sai kace ba ita ta haifi El-bash ba, murmushin dake kan fuskar umma ya kasa gushewa ranar da ta dade tana jiran abin kaunar ta yazo, ganin irin kallon da yake mata ta hura masa iska a ido,
firgigit Abba ya dawo daga duniyar tunanin daya tafi, murmushi yyi yace,
“Umman Basheer kece kuwa?”
Er dariya haj Hafsat tayi tana me kamo hannun sa tace,
“muje mota tsayuwar ta isa haka kana bukatar hutu”
Abba yyi dariyar shima yace,
“hafsana kinsan kallon ki kadai ya isa ya kori duk wata gajiya dake tattare dani”
haj hafsat na driving tayi smiling kana tace,
“kana nan dai kamar yadda na sanka” Abba yace,
“a kanki babu abinda zai canja, burina yanzu naji meyasa kuka zabi boyemin gsky keda murdadden dan naki” dariya ce ta kwace ma umma, Tana me karya kwana cikin wani kerarran gida ta juyo tana kallon Abba tace,
“duk abinda yyi halinka yyi gado like father like son”
tayi mgnr tana kokarin fita a mota, Abba shima fitowa yyi yace,
“haka dai kke fada kamar kullum.”
har cikin wani hadadden parlo umma takai Abba tana fadin,
“lale marhaban ya Habibi”
tayi mgnr tana kamo hannun sa suka zauna, Farinciki ya kama Abba yaushe rabon da yaji irin wa’annan kalaman? Umma tace,
“Wanka first, Abinci second, hutawa last”
tayi mgnr tana qirgawa da hannu Abba yyi murmushi yana tuna baya yadda suka kasance a zaman su, kullum cikin nishadi suke da faranta ran juna.
+
~~’~~
Bayan Abba yayi komai ya huta, umma ta shigo dakin sa, lkcn yana duba abu a system tasha wanka sai kamshi take itama, da fara’a ta karasa inda yake ta zauna, Abba ya ture system din gaban sa yace,
“so am all ears.” Haj hafsat tayi murmushi tace,
“ohk.”
Sannan ta fara da….
*FLASH BACK* ( _WAIWAYE ADON TAFIYA_ )
……….”Kamar yadda ka sani mu biyu ne matan ka Alhj, Bawai dan ina uwargida ba ko kuma ace kishi ba, a’a gsky kawai nakeson na fahimtar dakai, kafin nan zanso kasan cewa Alhj Rabe wanda ka maida shi mutum shine yake cin amanar ka ta karkashin kasa, abinda nakeso ka gane anan shine, Silar auren ka da Haj suwaiba ba kowa bane sai Alhji Rabe shine wanda ya taimaka har aka shawo kanka ka aureta, shima da sharadin idan ka aureta zasu hada kai suci amanar ka, karkace qage na mata No,
bayan shigowar ta gidan ina fahimtar duk wani karan tsana data doramin musamman kan *EL-BASHEER* kasan meye dalili? sbd kawai bata haihu dakai ba domin abinda ya kawota shine *GADO* abinda mafi akasarin mata keyi yanzu kenan wasu badan Allah suke auren me kudi ba saidan *GADO* kana tunanin mace na sonka nan kuwa tunani da hango ranar mutuwar ka take abinda kuma su matan basa ganewa shine Rai dayan nan dai a hannun Allah yake, babu meyi maka komai ba tare da Allah yasa hakan yana cikin kaddarar ka ba, So duk lkcn daka fita waje harkar kasuwa zai kasance Alhji Rabe na yawan zuwa gidan musamman idan yaga shima Basheer baya nan,
wata rana Me gadin gidan namu yazo har part dina ya gaishe ni, bayan mun gaisa sai naga ya tsaya nace,
“lpy mlm sabo?”
Mlm sabo yace,
“haj Abinda ake a gidan nan ne naga yana muni dayawa mezai hana Kisa Bashari yasa ido a Al’amuran gidan nan?” Lkcn daya gayamin hankali na ya tashi nace,
“kai mlm sabo me ake a gidan dahar kazo kana min mgn ni dana ke ciki ban sani ba?”
Mlm sabo yace,
“Allah yaja daran haj Wato a zahirin gsky Ana bin dunduniyar Alhj a gidan nan ya kamata a farga”
a razane nace masa,
“kai mlm sabo banason soki burutsu na en aikin gida, banason gulma, dan haka fice ka bani waje kafin ranka ya baci”
mlm sabo ya mike jiki a sanyaye yabar prt dina saboda naki bashi kofar dazai warware min abinda ya kawo shi, so tinda ya tafi hankali na ya kasa kwanciya, sai zaga parlo nake, dakyar na yakice abinda ke raina na daina tunanin a ganina shaidan ke neman samun nasara a raina harya fara min huduba akan abokiyar zamana.
STORY CONTINUES BELOW

Wata ranar Asabar na fito zanje part din suwaiba sbd naga kwana biyu bamu hadu ba, dukda ba zaman Mutunci ake ba amma kulawa da wanda kuke tare kamar ka sauke hakki ne na Addini tunda tafi kusa dani, Naje zanyi knocking kenan naji muryar namiji da farko na dauka sale kaninta ne sbd shima yana yawan zuwa, sai naji sabanin haka, yi nayi kamar nayi knocking din kawai sai naji muryar Rabe yana fadin,
“kewai har yanzu bakiyi batan wata bane?” Sai naji suwaiba tace,
“wlh har yanzu shiru shi babu kaima babu,”
*”shi babu kaima babu”*
Na sake maimata kalaman,
abin ya daure min kai matuka na kasa fassara kalmomin nan biyu, ji nayi Rabe yaja tsaki yace,
“da alama bakida sa’a ne, banda haka yau 3mnths da barin Alhj kasar kuma tunda ya tafi nake sasukar ki a gado amma ba wani result kuma bayan na tabbatar wa kaina nidin Sharp shooter ne tuni nake dirkawa mace ciki tun a kwanciyar farko.”
“Innalillahi wa’inna ilaihin raji’un”
shine abinda nayita maimaitawa kenan, hankali na ya tashi matuka, har kafafuna suka kasa daukata, na tankwashe a bakin kofar ina zufa, bana labe, banda niyar labe, amma abinda naji shiya sani dakatawa, hankali na be sake tashi ba saida naji Suwaiba na fadin,
“kaifa Rabe baka da hakuri wani lkcin, kaidai kayi fata daren yau na samu ciki ko mun samu *GADO*”
Rabe yace,
“da zanfi kowa farinciki dan na tsani yaron nan *EL-BASHEER* yake ko Eba”
Suwaiba taja tsaki tace,
“mtwss oho masu, kaga ya batun Qungiya ne? Kasan hodar mayen da aka kawo satin daya wuce harta kare ya kamata mu karo da wasu makaman yaki dan akwai wani gari da zamu tura yaran mu can akai hari muna tunanin akwai ma’adanai ta wajen dole a tada hankalin Al’uma dan musamu damar sace komi ba tare da hankali yakai kai ba.”
“Correct ta wajena” Rabe ya fada yana cewa,
“har kin tunamin da inda muka kai sumame can wata kasuwa har yau sai bincike ake an kasa gane komai ‘yan wahala.”
dariya sukayi gaba1 inajin karar tafin su da Alama tafawa sukayi, Hankali na ya dugunzuma bansan lkcn danayi wata gigitacciyar kara ba, musamman dana tuna kasuwar da aka kai hari harda kanina Yusuf daya ragemin bom ya tashi dashi musamman da akace kusa da tafkeken shagon sa abin ya faru wanda faruwan abin rashin sa saida na kwanta hospital idan ka tuna….
Ta karasa mgnr tana jan zuciya sbd kukan data dinga yi yyinda take bada lbrn.
Wannan karar tawa ita ta ankarar dasu, ni a lkcn har suma nayi sbd naji abinda ya girmi tunani na, mutuwar yusuf ta dawo min sabuwa fil, ashe haka muke zaune da disaster bamu sani ba? Ban tashi farfadowa ba sai a gaban makiyana sun sani a tsakiyar parlo su suna zaune kan kujera kowa ya dora daya kan daya ana karkada kafa.
Mikewa nayi da sauri ina matsawa baya danni tsoro ma suka fara bani da alama basuda digon imani a ransu duba da yadda suke bina da matsiyacin kallo,
“Ke dakata,”
naji suwaiba ta dakamin tsawa, Rabe ya zaro er karamar bindiga aljihun sa yace,
“ko ki nutsu muyi mgn ko mu tarwatsa kanki yanzun nan”
kasa motsi nayi sbd naga rashin imani muraran a idon su, Suwaiba tace,
“ko ba’a fada ba munsan kinji komai toh yadda babu wanda yasan abinda muke kullawa mutanen gari ana kallon mu da mutunci baki isa kiji mu kyaleki ba, sharadi zamu baki yanzu, cikin ukun nan ki zabi daya idan kinki yanzu a tarwatsa kanki, na farko shine dole kibar gidan nan kiyi nesa damu kada ki sake waiwayen shi ma’ana kinyi sallama dashi kenan sannan mu bayyanawa duniya kin mutu wannan shine hukuncin jin asirinmu da kikayi, idan kin musanta hakan zan kashe mijinmu Alhj usman dan ni ba matsalata bace dan ya mutu, sannan mu kashe Danki Bashari kinga kenan bake ba shi dukiya ta dawo garemu muci karen mu babu babbaka, a karshe kuma muna iya kashe ki yanzun nan idan kin kawo mana wargi, So zabi ya ragema me shiga rijiya”
haj Suwaiba ta karasa mgnr Rabe na gyada kai.
Tunda naji ta ambaci kalmomin nan nasan zasu aikata, sune kungiyar {HSK} H:Hodar iblis, S:shan jini, K:kunar bakin wake. Sune wanda jami’ai suke neman su ruwa a jallo amma an kasa samun su saima abubuwa dake kara tabarbarewa Matasa sun fada maye harda matan ba’a barinsu a baya, kidnapping yyi yawa, kazalika kai hare-hare sai yawaita yake, duba da irin barnar da sukewa Al’uma na zabi nabar cikin ku nayi nesa daku, sbd wani kuduri daya zomin arai daidai lkcn,
sai a lkcn na kara fahimtar me mlm sabo yakeson fahimtar dani game da Al’amuran gidan.
Ban bata musu lkc ba nace na amince, wata irin dariyar mugunta suka fashe da ita harda rike ciki, kafin Suka wani sha kunu, sannan Rabe yace,
“ke hafsatu kike ko hansai?”
Zuba masa ido nayi ina kallon ikon Allah wato duniya tazo karshe wanda ka kawo inuwa shi ke kaika rana abinda nayi tunani dashi kenan a lkcn, yaci gaba da fadin,
“wabillahil lazi by mistake naga me kamarki a hanya saina tarwatsa kanta, na tarwatsa danki da ubansa, kuma kar kiga munce ki tafi ki samu damar kaiwa kara, hahaha”
ya saki dariya sannan yace,
“Tabbas zaki wahalar da kanki domin HSK Association tana kunshe da manyan kusoshin kasar nan a ciki so you better careful”
yyi mgnr yana tashi tsaye, sai ji nayi yace,
“as from now ki biyoni na ajeki nesa da gari dan ko dakin ki ma bazaki koma ba bare a samu leaking”
Yyi mgnr yana karasa fita.
Wasu zafafan hawaye haj hafsat ta dinga fitarwa tana gogewa wasu nabin baya, Hanci taja sannan taci gaba da mgn…….*EL-BASHEER*
*Wannan page din kyautace a gareku…*
_Mrs Tajuddeen tajra, ummi sulaiman, Fatima Muhammad Abba, Queen dimple😊, My qawa Amintako🤪, qawalli Na’ima❤_
*Kuji dadin ku😍 na gode da comments🥰*
*My Fans akwai masu comments suce Gsky Nuceey kina WUTA🔥🔥😢😢 na hadaku da girman Allah ku daina fadin haka👏🏻😦 kumin Addu’ah ko sharhi is okay🥰👌🏻*
55
Banda wani zabi sama da nabi shi, haka na fito suwaiba nabin bayana, har bakin motar Rabe mukaje dama bakin glass gareta duk wanda ya shiga babu me ganinka, daga can gate mlm sabo yana hango mu saidai da alama bazai fahimci me ake ciki ba, Haka na shiga suwaiba na banko min kofa, Itama gaban motar ta shiga sannan suka dage glass din baya yadda babu me kallon abinda ke baya, daidai zamu fita suwaiba ta dan rage glass tana kallon mlm sabo dake rike da radio tace masa kai sabo zan fita idan sakina ta shigo kace ba nisa nayi ba yanzu zan dawo, gyada kai mlm sabo yyi yana fadin a dawo lpy ya koma ya zauna yana sake kara radio a kunnen sa, naso ace nayi mgn da mlm sabo saidai ba halin haka, lkcn da muka fita a gidan na juya ina kallon gate din, naga hankalin mlm sabo ya dawo kan motar ya zuba mata ido kamar me tantance wani abu sabanin da daya nuna halin ko in kula lkcn da suke masa mgn, har muka bacewa ganinsa naga still be daina kallon mu ba, a haka har muka bar unguwar,
+
hmmm.. Haj Hafsat taja ajiyar zuciya tace kasan meya faru? Taci gaba ban sake tantance kaina ba sai a wani dan karamin daki, cikin wani dan karamin gida, a lkcin a gigice na farka hade da salati a bakina, ina cikin salatin naga wata yarinya ta shigo da sauri tana fadin sannu Umma, binta nayi da kallo sbd nasan babu me kirana da wannan sunan sai Dana Basheer, take na fashe da kuka tunowa da nayi abinda ya sameni su Rabe shaka min hoda sukayi harta bugar dani bansan ya akai na kasance a dakin ba, Kiyi hakuri umma, naji yarinyar ta sake fadamin, hankali na ya kasa kwanciya da inda nake, nace ke yarinya a ina nake nan? Nijar, a firgice nace Innalillahi Nijar? Me kuma zakuyi min anan bayan rabani da dukkan farinciki na da kukayi? Ba kunce na bar rayuwarku ba? Kuma na amince me kuma yyi saura?
Gani nayi yarinyar tana girgiza kai tana fadin Subhanallah, Subhanallah Allah ya tsaremu da yin wannan mummunan aikin, mmki ne ya sake kamani nace ke kodai Aljana ce ban sani ba? Wara ido tayi tace Meyasa kikace haka umma? Nace kince ina nijar, banji kina hausar su ba, sannan banga wani mahaluki ya leko ba, banji motsin kowa ba, ba dole nayi zargin haka ba? Gani nayi tayi murmushi abinda ya sake tsundumani cikin mmki kenan ina jiran naji ta bakin ta, can tace, Umma Ki kwantar da hankalin ki nima er Nigeria ce, yadda kika ganki anan nima wannan shine karon farkon zuwa na kuma a dalilin ki nima nazo, Gyara zama nayi sbd abinda ke fitowa a bakinta ya daina bani mmki sai Al’ajabi nace ga dukkan Alamu akwai muhimman bayanai a tattare dake, ki sanar dani kafin na nausa wani wajen kamar yadda makiyana suka nema,
Gyara zaman itama tayi tace, da farko dai ana kirana da suna Husnah, Nima cikakkiyar er kano ce, babana shine ya turoni na kula dake sbd wasu ayyuka da suka sha kansa, amma kam tabbas shiya ceceki, ko nace tare dashi mukazo inda makiyan ki suka watsar dake, ya hadani da wani tsohon mutum yayan Abokin sa shi kuma ya tafi, yayan abokin nasa be cika zama a gida bane shiyasa baki gansa ba, kuma gidansa yadan fita daga wajen gari, abokin danki suraj yana kasar yyinda shi El-basheer baya kasar kuma ba’a samun sa a waya,
Sbd wani aiki da aka turashi, kai tsaye babana ya kira suraj ya sanar masa dukkan abinda ke faruwa dake, lkcn shima yaje kaduna kan wani case, a take yace ma babana ya baki mafaka kafin yazo zuwa jibi, babana beyi kasa a gwiwa ba yyi duk yadda zaiyi ya baki taimako cikin hukuncin ubangiji, duk inda makiyan ki sukabi haka muke binku a baya, har muka ga inda suka aje ki suka tafi, babana besha wahala ba da yaga inda aka ajeki ya kira wani abokin sa shine ya hadamu da yayansa dake zama a wajen gari.
Nace mata Husnah waye wannan baban naki? Sannan ina mamanki? Dan murmushi tayi tana girgiza kai tace babanta be bata damar fadar koshi waye ba sbd Allah yyi dan haka karta sake ta fadi waye shi, duk yadda naso ta fadamin ki tayi, haka na kwashe 3days muna tare, yarinyar ‘yar arziki ta shiga raina sosai, duk yadda naso shan cikinta ta fadamin qi tayi, haka na hakura sbd nasan akwai special people da suke abin Alkhairi batare da sun nuna ba,
kamar yadda suraj ya Alkarwanta sai gashi a gidan da yamma, a lkcn har ya sanarma basheer halin da nake ciki dan ya samu wayarsa daga baya, hankalin basheer ya tashi matuka, ransa ya baci ainun, zuciyar sa tayi quna sosai, yana tsaka da aiki a Pakistan yace zai dawo, dakyar suraj ya taushe shi akan subi komai asannu, badan yaso ba ya hakura sbd anason a kama masu lefin dayawa dama ana ta binciken case din en HSK Association an rasa bakin zaren da za’a kama, wanda yyi nasarar samun zaren saidai aji mutuwar sa sun kashe shi,dan da sun fuskanci ana binciken su yanzu zasu kashe mutum, toh abin sai yazo masa faduwa tazo daidai da zama sai suka yanke shawarar shi da suraj ya karbi case din, sun bar shawarar a haka yyinda suraj yyi duk abinda zaiyi nabar kasar batare da an samu akasi ba,
dakyar muka rabu da husna sbd munyi sabo, naso ma mu tafi tare nanma taki, tace babanta bazai barta ba, na nemi ta fadamin me takeso tace ba komai, nace mata ta dubi girman Allah sau daya dai yadda ta faranta min ita da mahaifin ta su bani dama na faranta musu, sai a lkcn tace burinta daya tayi kr2 son samu ta karanci bangaren tsaro na sirri dan tanada burin bawa kasa gudunmawa musamman dan ganin wargaza qungiyar HSK Association, na jima ina kallon ta sbd yadda naga ra’ayin daga zuciyar ta yake fitowa bawai a baki kawai ba, murmushi nayi nace husnah banda abinki kina mace ina ke ina wani aikin jami’an fararen kaya? Karki manta fa ana iya turaki wata jahar,
husnah tayi dan jim kafin tace for once in my life zanso na bawa kasata gudunmawa, wannan kungiyar zanso ace dani aka wargaza ta da ikon Allah, wlh umma tunda naji lbrn ki naji na tsani mutanen nan tun kafin na gansu, Yadda naga ta jajirce nace Allah yyi jagora daga nan muka rabu, nabar wa suraj duk wani nauyi na university dinta da take bukata, wannan abun daya faru Basheer be sani b, dan kai tsaye mukace masa wani bawan Allah ya taimake mu, koda yaso jin ba’asi mukace muma bamu sanshi ba,
Da nazo Pakistan basheer shine ya tarbe bi,ya kama min haya sbd shi a hotel yake yana binciken wani, haka nayi rayuwata anan tare da basheer dan daya samu hutu wajena yake zuwa wani lkcn shi da suraj a haka yasai min wannan gidan muka dawo ciki.
sosai basheer ya tsananta bincike akan su, dan hausawa sunce idan baka iya kama barawo ba sai ya kama ka shiyasa yake binsu ta karkashin kasa, kwatsam ranar basheer ya kirani yaga kullin da suwaiba ita da kaninta sukeyi akan su haukatar dashi, daidai lkcn kuma aka bashi ragamar case dinsu, a ranar da sukace zasuje gun boka ayi masa aiki, aranar bamu rintsa ba kwana mukai muna kai kukanmu wajen Rabbil Izzati, kwana biyu da zuwan nasu sukayi plan kawai yyi haukar karya dan aikinsu yafi tafiya successfully b tare da an fahimci hakan ba, haka kuwa akayi ya maida kansa mahaukaci, sai murna suke zaton su magani ne yaci basu san cewa ba hakan bne, a haka yyi ta zama dasu yana samun nasara a kansu sosai.
Wannan shine karshen Boyayyen abinda baka sani ba, haj hafsat ta karasa mgnr tana jan zuciya sbd kukan da tayi har muryar ta na dashewa.
Jawota Abba yyi jikinsa ya rungume tsam yana dan buga bayanta, dauriya ce kurum irinta namiji dan duk wanda ya kalli idon Abba zaiga yadda ya kada yyi jajir.
*CIGABAN LABARI*
……oh ko su el-bash an farka?😂EL-BASHEER*
Wannan page din Sadaukarwa ce ga…
*AUNTY MAIJIDDA MUSA, Comments dinki na dabanne inajin dadin shi a lot😍*
Na
Nuceeyluv😘
56
Around 9am ummi ta farka, ganinta tayi manne a jikin el-bash sun qanqanme juna sosai kamar wanda za’a dauke dayansu, idanun ta fes ta dora kan fuskar el-bash da yake bcci hankali kwance, gani tayi kamar wanda yake smiling sbd yadda fuskar sa take shining, haka kawai ta tsinci kanta da smiling din itama tana tuno daren su na jiya, rufe fuska tayi dan taji kunya sbd tunanin da tayi, a hankali ta zare hannun sa daya riketa ta maida masa pillow a hankali, cikin sanda tabar dakin dan bataso ya farka,+
dakinta ta koma ta wuce toilet direct, ruwan dumi ta shiga ta dinga gasa kanta, zuwa lkcn taji sauki sabanin cikin daren su, saida ta gama tazo ta shirya ta fito dakin, kitchen ta wuce ta fara hada musu breakfast tana gamawa ta dauraye abinda ta bata sannan ta kwaso breakfast din a katon tray ta kawo shi tsakiyar parlo ta aje, kafin ta koma dakin el-bash dan ta tashe shi.
Tsaye ta same shi yana taje kansa da alama har yyi wanka ma ya shirya tunda har yasa kaya, da mmki ta zuba masa ido tana kallon sa, abinda bata sani ba shine,
El-bash ya rigata farkawa kawai ya tsaya kallon tane yana tasbihi ga Allah S.W.A daya bashi kyautar ta batare da wayon sa ba ko dabarar sa, Tabbas da an biye tashi bazai aureta ba, dan farkon ganinta da aka kawo masa ita ya raina ta dan bata cikin irin matan da yakeso sbd yarinyace, sai gashi little baby ta zarta tunanin sa, little baby ta koma Big girl wacce za’a saka a cikin irin matan nan First class, tunda ya farka tunanin da yake kenan sannan be gaji da kallonta ba saida yaji ta fara motsi shiyasa ma yyi saurin lumshe ido yana kallon ta kasa2 dariya taso bashi dayaga ta kafe shi da ido tana smiling danne dariyar yyi amma dukda haka saida fuskar sa ta nuna sbd smiling din daya bayyana akai,
Tausayi ta bashi lkcin dayaga zata fita, da ace ba akan aikinsa yake ba da tabbas ya riritata a wannan ranar, ranar da bazata taba goguwa ba a kundun tarihin sa, so yyi ya tashi sai ya fasa sbd yadda yaga ta saka masa pillow alamar bataso ta tashe shi, tana fita shima ya fada toilet yana wanka yana smiling hade da rungume hannayen sa a kirji yana tunanin inama ummi ce a wajen da wankan zaifi bada citta.
Ko yanzun ma yana kallon ta ta mirror, ya lura da mmkin dake dauke kan fuskar ta, juyowa yyi yana murmushi ya tako har gaban ta, ji tayi kawai ya jawota jikinsa ta fada kirjin sa, baya yyi suka zube kan bed, zame kanta tayi zata tashi ya rike ta kam, shinshina jikinta yake kamar tsohon maye turaren jikinta yake shaka lips dinsa yasa kan wunyanta yana dan bata peck, ummi ganin abinda yake ta tureshi tana rike kumatun sa tana jijjigawa kamar karamin yaro tace,
“Breakfast… Breakfast is ready.
Tayi mgnr tana bubbuga lips dinsa, gani tayi yyi murmushi har hakoran sa na bayyana,
“huh!”
Ummi ta hura iskar bakinta ta haye kan ruwan cikinsa ta zauna tana jan lips dinsa tace,
“ina mgn ma dariya kkemin ko? Toh zan yanke wannan.”
Tayi mgnr tana sake jan lips din.
“Auuchh”
ya sakar mata kara, da sauri ta saki lips din tana dariya sbd yadda taga ya rike bakin yana mulmulawa irin yaji zafin nan,
“Rago kawai”
tayi mgnr tana dariya hade da masa gwalo, gani tayi zai tsafko nata da alama ramawa zayyi ta sauka a kansa da sauri ta kuma bar dakin a guje,
da sauri ya bita sbd yasan akwai ciwo a jikinta, dan haka yabiyo ta dan ya kamata ta daina gudu, amma ina ummi zaton ta kamata zeyi ta kara gudun ta tana taka stairs, Ya fita sauri dan haka ya mika hannu zai kamata ummi ta tsorata tayi mssn stairs sai gashi tayi sufa zata fadi cikin zafin nama el-bash ya damko ta ta fada jikinsa, jikinta ne ya fara rawa sbd ta tsorata ainun rikeshi tayi qam ko motsi ta kasa yi, ganin haka el-bash ya dauketa tamkar er baby,
ci gaba da tafiya yyi akan stairs din, ita kuma tayi wani lamo a jikinsa, hakan yasa El-bash cikin wani yanayi yana murmushi shi kadai.
Daidai sun shigo tsakiyar parlon aka banko kofarsu batare da anyi musu knocking ba,
“La’ilaha’ilallahu mezan gani yau ni Sakinatu”
Sakina tayi mgnr tana tafa hannu, zama El-bash yyi ummi nakan cinyar sa ko kallon inda sakina take beyi ba, ummi ta gane sakina ce dan haka tasa a ranta baridai yau daya tayi mgnin matar nan ko ta sakar mata mara tayi fitsari.
juyowa ummi tayi tana kallon sakina datayi tsaye a kansu tana tafi, dan yatsina fuska ummi tayi kafin tace,
“lafiya?”
Wani kululun bakin cikine ya tokare sakina tace,
“eh dole kice haka tunda naga wuyanki ya isa yanka kin gama lalatamin miji”
tayi mgnr tana hucin takaici tana fatan ace itace kan cinyar El-bash ba ummi ba. Dan murmushi ummi tayi tace,
“idan mijinki ne whynot kizo ki tare? Ko dama haka auren yake miji na gida mata na gantali.”
“Kut**r uba me kke nufi?”
Sakina tayi mgnr, Rolling eyes ummi tayi tace,
“bakya gane hausa ne?”
Idan ran sakina yyi dubu toh ya baci, Hannu ta kawo zata wanka mata mari taji an kwashe ta da tagwayen mari biyu, a gigice ta matsa baya tana shafa kumatu,
“El-basheer meyasa haukan ka yake fadawa kaina? Me wannan tsohuwar kilakin ta baka harta shanye ka haka?”
Wani matsiyacin kallo taga ya wurga mata tayi saurin nufar kofa kafin ya bata kashi, daidai zata fita ta juyo tace,
“kuma wlh yanzu zanje a auramin aure dashi saina kaskara ki idan na shigo ciki kuma idan bariki ne kinzo gidanshi”
dariya ummi ta kwashe da ita irin na tura haushin nan tace,
“So?”
“Au haka kikace?” Sakina ta fada,
“yeah”
ummi tace a takaice, kwafa sakina tayi tana me banka musu kofa tayi waje.
Tana fita ummi ta dubi El-bash taga ransa a bace,
“Oh No..”
ta fada tana jan kumatun sa, El-bash murmushi yyi sbd bayason yabar bacin ran ya rinjaye shi dan yau ranar farinciki ne a wajen sa, ganin yyi murmushi ummi ta mike ta jawo breakfast dinsu, nan ta hada musu tea ta jawo plate na irish da egg ta sa musu tsakiya, mika masa cup din tayi ya karba, memakon yasha sai ya miko mata bakinta hakan ta fahimci bata zaiyi ta bude bakinta, itama bashi tayi a haka suka dinga ciyar da kansu.
*****
“Sallama dai” aka fada ana daga murya hade da jawo akwati, “Innnnaa….” aka sake kwala kira, Inna dankwali a hannu ta fito a daki tana fadin,
“wanne jarababben ne yake kwadamin sallama da sanyi safi…….,”
mgnr tace ta makale sakamakon ganin erta jamila tana tiriniya da akwati,
“Ke lpy?”
Jamila tace,
“Inafa lpy Inna, yo sakoni yyi aikin banza kamar wani abin arziki akeci a gidan.”
“Innalillahi”
Inna ta fada tana tafa hannu hade da sallallami, tace,
“yanzu Haruna abinda zai saka mana dashi kenan? Yau naga tsinannen Yaro.”
Jamila na zama kan kujera tace,
“yo can matsalar sa wlh, ga maza akan layi nan banda kaddara me zanyi dashi.”
Inna itama ta gyara zama tace,
“wai meya hadaku haka?”
Tsaki jamila tayi,
“kin sanni inna inada zafin zuciya akwai kishi to shi baida mgn sai ta ummi komai ummi zance yake ummi kamar wani zararre ni kuwa nace bazan iyaba tunda dan abinda na aureshi ya kare ya sakeni kawai, shine yamin saki biyu.”
Zaraf Inna ta mike tana gyara daurin zani tace,
“yaci malafar ubansa tashi muje ya cike ukun mu zaiwa wulakanci? Me za’ayi dashi irin tsiya”
tayi mgnr tana jawo zani kan kofar dakinsu ta lulluba a kanta tace,
“muje”
tashi jamilan tayi sukayo waje inna na surfa bala’i.
~~~~~
Baram aka tura kofar parlo, haj suwaiba na zaune tana breakfast tace,
“ke lafiya kike bankomin kofa haka?”
Tayi mgnr tana kallon sakina. Sakina ta zauna akan kujera tace,
“momy idan kinason farinciki na ki auramin *EL-BASHEER*”
Wani irin tari ne ya kama haj suwaiba sakamakon kurbar tea da tayi zancen Sakina ya shigeta.EL-BASHEER*
*Afuwan fans, hakuri, a kara hakuri, ni nasan kunmin uzuri👏🏻*
_Mom Asas, sumy, mom maheer, billy chocolate, Amina maradun, hadiza, ummi apipa,_
Kunada yawa fa…😨 wannan page naku ne saura zamu hadu a next page Insha Allah.
*SONSO FISABILILLAH😘*
Na
Nuceeyluv😘
57
Saida ta saisaita kanta kafin tace, “kikace me?”
“Abinda kunnen ki yaji momy”
haj suwaiba tace,
“ke kinada hankali kuwa? Uban me zakici da yaron nan kika nace masa haka?”
Sakina tace,
“sonsa nake burin aurensa nake, kuma haukan da yake ba kowa bane sila sai ke momy wlh kunmin buqulu da kuka haukatar dashi, kuma wlh idan ba’a…….,” kauuuu.. taji an kwasheta da mari momy na huci kanta sbd takaici tace,
“ni zakiyiwa tijara sakina? Dan ubanki nawa kike? Ki rasa wanda zaki so sai yaron da nafi tsana a duniya? Kuma da kike mgnr hauka, d ban haukatar dashi din ba kin isa kikai lbri? Ko kuwa duk abinda nake dan wa nakeyi? Inada ‘yar data wuce kine? Idan an samu yadda akeso waye zaifi jin dadin? Kul na sake jin bakin ki kan lamuran nan kona saba miki wlh.”
“Yiiii…,”
Sakina ta fashe da kuka tace,
“ni wlh bakya sona momy inda kina sona zaki so abinda nakeso, harma wai ni za’a rainawa hankali a gidan nan? Gadara fa takemin dashi wlh bata isa ba dan El-bash nawa ne.”
ta karasa mgnr tana kara fashewa da kuka. Haj suwaiba ta matsa jikin kujerar ta zauna a nutse tace,
“ita wa din?”
“Ummi mana”
Sakina ta fada da sauri tana me kara jin takaici a ranta, shiru haj suwaiba tayi ta tafi zurfin tunani, wani murmushi mugunta tayi sbd tunowa da+
_haduwar su meeting da zasuyi next week da gobe ne sai aka daga kuma a wannan meeting mai kano zaizo wato gang leader a ranar dazai sauka dayawa ana kai masa kyawawan enmata yyi fasikanci dasu a daren ranar washe gari a bawa dodon tsafi jinin yarinyar da ya gama lalata da ita yasha to a cikin members duk wanda yyi dace yarinyar daya kawo mai kano ita ya zaba ana masa karin girma sbd martaba abin da suke, sannan su wa’annan emmata sato su ake wanda ba’a zaba ba su zama bayi masu bauta, toh ita duk wanda take kaiwa bata nasara dan haka zata kai ummi ko zata dace ta samu tambarin girma ta hannun dama a cikin members._
wannan shine gajeran tunanin da tayi kuma tayi na’am dashi, kafin ta dafa kafadar sakina tace,
“yanzu wannan er yarinyar ce dama ta daga miki hankali shine nima kikeso nawa hankalin ya tashi?”
Sakina na jan zuciya tace,
“ke kike mata wannan kallon amma yanzun kam kan mage ya waye taci jar miya.”
Haj suwaiba ta danyi murmushi tace,
“idan a kanta ne sai mu batar da ita ya zama naki ke kadai”
“yeeeey….”
sakina ta juyo ta rungume momy tace,
“shiyasa nake yinki wlh kinsan takan makirci, toh amma taya zamu btar da ita batare da kowa ya farga ba?”
Haj suwaiba tana dariya tace,
“kibar wuqa da nama a hannu na kawai.”
“Na bar miki”
sakina ta fada tana mikewa tsaye hade da shafa ciki tace,
“yunwa nakeji wlh.”
Haj suwaiba tace,
“toh nima baki barni nayi nawa karin ba sai kije kitchen ki debo mana muci.”
“Toh momy” sakina ta fada tana yin hanyar kitchen yyinda momy ta bita da kallon yarinta dan kam wayo tayi mata dan nata buqatar badan ta yadda da auren ba.
******
Saida ya bari ta shiga kitchen tana abincin rana ya koma dakinsa da sauri, kiran suraj yyi suka gaisa ya sanar masa meeting fa sun daga sai next week,
“kaiiii…..”
Suraj yafada yace,
“wlh mutanen nan sunada matsala har mun gama zama ready zasu canja lamari?”
“Mtwsss..” El-bash yaja tsaki dan yana ganin shi akafi cuta so yake ya gama aikin nan ya huta dan ya gurji amarcin sa me lasisi yanada maganganu dayawa da yakeson furtawa ga ummin sa amma babu dama sai zaman kurame “mtwsss” ya sake jan tsaki a karo na biyu. Suraj yace,
“mgn muke naji sai jan tsaki kke”
“Bazaka gane bane suraj amma kam ni sukafi cuta.”
Suraj yace,
“hakuri zaka kara kasan aski yazo gaban goshi yafi zafi.”
“Hmmmm…” El-bash yaja ajiyar zuciya yana kara hango nisan 1week a wajensa,
“Bye”
kawai yace a takaice ya kashe wayar yana maida ta inda ya saba ajewa ransa duk a bace.
~~~~~~
Knocking suke na fitar hankali kamar zasu balla kofar, gam…gam..gam…, Haruna dayake dakinsa kwance yanajin ya samu salama yau ya taso rai a matukar bace zaiga yau wanne mahaukacin ne yake buga masa kofar gida, inna na jikin kofar tana surfa bala’i yyinda jamila ke gefe, basu san ya taho ba, shi kuma haruna da biyu yazo buda kofar yana zare sakata dake ta baya ne budewa ya hankada kofar da karfin sa yadda koma waye me nacin bugun shima yaji inda da dadi, luuuu…, inna tayi taga-taga zata fadi sbd turawan da yyi ya sameta har tayi baya, duk yadda jamila taso tareta saida inna ta zame ta fadi hade da gangarawa cikin wata kwata dake gefen hanya,
“Yeeeey…. iya ruwa fidda kaii, Hhhhh”
wasu samari dake nesa dasu suka fada suna sheqewa da dariya da alama irin marasa kunyar nan ne. Kunyace ta kama jamila tace,
“Innalillahi”
ta fada tana dora hannu akai,
“Ke rikemin hannu na tashi bawai ki tsaya kallona ba”
Inna ta fada tana yunkurawa dakyar, duk yadda haruna yaso mazewa kasawa yyi saida ya dara, dariyar sa ita ta fargar dasu da tsayiwar sa a wajen, cikin borin kunya suka haushi da fada, jamila tace,
“ashe dai baka da mutunci ban sani ba? Uwata ta fadi kana mata dariya?”
“Ke kuma meye hadina dake?”
Ya fada yana yatsina fuska kamar be taba saninta ba, Cikin jin haushi inna tace,
“kai haruna idan kai ba shege bane ka haifu cikin iyayen ka na sunna ka karasa sakin da kayima ‘yata ya zama uku kaga idan kwantai zatai a gari.”
Ran haruna ya baci yana kallon inna da dan guntun mutunci a idon sa sbd ummi dan duk wanda ya rabi ummi yana ganin darajar sa to amma da alama so take ta kankare sauran, Ba tare da bata lkci ba yace,
“taje na tsinke sauran igiyar dake tsakanin mu shikenan?”
“Ahayyye Rasss…” Jamila ta fada tana rike qugu tace,
“daidai kenan dan wahala inna muje”
ta fada tana kama mata hannu. Sun danyi nisa haruna ya daga murya yace,
“azo a kwashe sauran kaya ko na watso su waje.”
Inna ta juyo tace,
“aiko baka fada ba wannan dole ne tunda bada kudin ubanka aka siya ba.”
Rufe kofar gidan yyi yana fadin,
“gayyar tsiya.”
Su inna sunzo daidai gun samarin nan sukaji an sake kwashe musu da dariya wani ya sake duban zanin inna dake digar ruwan kwata har yanzu yce,
“wa yaga kaza a ruwa”
yyi mgnr sauran na kwashewa da dariya,
“uwarku ce kazar shegun yara marasa tarbiya”
inna ta juyo ta fada musu hakan. Dariya suka sake kwashewa da ita da alama ta zamar musu abin dariya. Yyinda jamila ta sake jawo hannun inna dan suyi sauri subar unguwar.
••••••••
Koda ummi ta fito kitchen sai taga el-bash baya wajen data barshi, dan haka itama ta haura saman dakinsa ta wuce tana budewa ta ganshi ya kwanta yyinda ya nade hannun sa baya ya dafe keyarsa dasu, idanunsa na kallon sama kamar me tunani bacin ran dazu be gama gushewa a fuskar sa ba, a sanyaye ta karasa gaban gadon ta zauna a gefen sa tama rasa me zatace, to mema zatace mutumin da baida hankali?
Zamanta kusa dashi shiya fargar dashi zuwan ta, tausayi ta bashi dayaga ta zauna tayi jugum yasan baya rasa nasaba da halin data tarar dashi ta fahimci yana cikin damuwa, ita ya zubawa ido daidai lkcn itama ta juyo suka hada idon, gani tayi ya mata murmushi wata boyayyar ajiyar zuciya ta saki tana maida masa da nata murmushin ta rasa meyasa batason ganinsa cikin damuwa, gani tayi ya wara hannun sa alamar tazo, da murnar ta kuwa ta fada saman qirjinsa yasa hannayen sa ya rungume ta tsam, a tare suka sauke ajiyar zuciya.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
58
Kissing dinta ya fara yi kota ina yana lasheta kamar ya samu sweet, kokarin cire mata kaya yyi dan hankalin sa ya fara tafiya ummi ta rike rigarta dan bata manta darensu na jiya ba, badan yaso ba ya saurara dan shima yana tausaya mata danma dai tanada dauriya ne kawai, shiru sukayi na wasu minutes kafin ummi tayi yunqurin tashi, toilet dinsa ta shiga danyin wanka, ta gama cire kayanta kenan taji ya bude kofar, wara ido tayi tace,
“pls ka fita wanka zanyi”
ta fada tana masa alamar nuni da yatsa, gani tayi ya fara cire kayansa, bata manta haduwarsu ba ranar, tayi saurin jawo kayanta zata maida ya rike mata su, wurgi yyi da kayan ya dauketa cak ya tsunduma ta cikin ruwan data tara shima yabi bayanta.
+
******
Koda su inna suka isa gida sai suka tarar da mlm sabo shigowar sa gidan kenan, binsu da kallo yyi lkcn da suke zama yace,
“daga ina kuke haka nazo gidan ba kowa?” Inna tace,
“daga wajen tsinannen yaron nan muke haruna”
mlm sabo yace,
“meya hadasu harda zagi haka?”
“Toh ba dole na zagesa ba? Wai sbd shi tantiri ne ya saki jamila” inna ta fada tana kumfar baki,
“Saki?”
Mlm sabo ya fada hankali tashe,
“Ehmana saki biyu yyi mata shine na sata a gaba nace muje ya cike sauran dan bamu gaji wulakanci ba.”
“Innalillahi wa’inna’ilaihin raji’un” mlm sabo ya fada yana rike kai yace,
“haba saude ya da girman ki kike abin yara?”
“Ban gane ba?” inna ta tmby tana tsare shi da ido, cikin jin haushi yace,
“kin kashe mata aure mana memakon naji sasanci kikaje musu wannan abinda kukayi duk shiriritace wlh Mtwsss”
yaja tsaki,
“Kai sabo yaushe ka fara canjawa ban sani ba? ‘Yarka fa aka cima mutunci”
mlm sabo ya kalli jamila da tayi tsumu2 cikinsu yace,
“ke tashi kibar nan”
sum2 tabar gun kuwa, kafin ya maida kallon sa kan inna yaga ta zare masa ido, abinda yaso fada ya makale sbd shakku daya darsu a ransa, cikin nutsuwa ya canja akalar zancen yace,
“ba canjawa nayi ba, gani nayi ‘yan mata sunyi yawa a gari haka ma zawarawa, to ita Allah ya rufa mata asiri da aurenta kin tsinka mata shi ba’asan wanne kalar miji zata aura ba nan gaba.”
Inna tace,
“Idan dan wannan ne ai tazo gidan sauki, suma mazan akwai su dayawa a gari jamila son kowa kin wanda ya rasa tana gama idda zata samu miji kai kafin ta gama ma zasu fara taruwa ana jira sai wadda ta zaba.”
Zuba mata ido yyi yasan jamila duk kamannin ta ta debo ya girgiza kai kawai ya bar musu gidan.
Yana fita jamila ta fito tana tura baki, inna tace,
“kyaleshi muna nan dake sai yazo yana karamar murya idan yaga kin samu Alhji”
dariya jamila tayi tace,
“harna hango ina fantamawa yadda nakeso”
“sosai ma kuwa” inna ta fada tana dariyar itama,
“Yauwa waini inna na tmbyeki?”
“Inajinki”
inna ta amsa,
“wai ya lbrn ummi ne tunda tayi aure tazo kuwa?”
Inna tace,
“me zatazo tayi? Ai tun da akayi auren nasa sabo yyi mata gargadi karta soma zuwar mana gida dan mun gama bayarta kenan taje ta karata da wannan mahaukacin kilama ya gama karairaya ta dan inajin lbri a gari mahaukacin irin riqaqqun nan ne basajin mgni” dariya jamila tayi tace,
“kai zanso ganin idon ummi yanzu haka ta lalace kilama har wankin kashi take masa hhhhh” tayi mgnr tana dariya, inna ma dariyar tayi, jamila tace,
“aiko gobe zanje na gano mana rahoto” inna tace,
“kwarai kuwa amma kiyi baya2 kar ya sauke haukansa a kanki” jamila tace,
“ai dole ma nayi taka tsantsan”
ahaka dai sukaci gaba da gulmar ummi suna dariya.
••••••••
Washe gari ummi na gyara parlo yyinda el-bash ke zaune kan doguwar kujera yana bin duk wani move dinta da kallo, knocking sukaji ummi ta jawo hijab dinta ta saka, zuwa tayi ta bude kofar wara ido tayi tana mmkin wacce ta gani a kofar, farinciki ne ya kamata da fara’a tace,
“oyoyo jamila” jamila tayi sakarere tana kallon ummi data canja mata lkci daya kamar ba itan ba, shigo mana ummi ta katse mata tunani, shigowar tayi tana me sake bin ummin da kallo tace,
“ke anya mahaukacin kika aura?” Tayi mgnr tana zagaye ummi batare data lura da el-bash yana parlon ba, dan yake ummi tayi tace,
“zauna mana jamila ko ruwa fa baki sha ba”
tayi mgnr tana juyawa hanyar kitchen,
“kan uba”
jamila ta furta a hankali tana rike qugu, juyowar da zatayi taha El-bash kan kujera fuskar sa babu alamar fara’a ya gane fuskar matar tun ranar da suka kawo masa ummi ya fahimci akwai wata a kasa tsanin su abinka ga wanda yasan kan aikin sa.
STORY CONTINUES BELOW

Kusan diriricewa tayi, dan tayi mugun tsorata da ganinsa ga kuma mmki fal ranta dataga ya canja babu wannan qasumbar me yawa, yyi fresh dashi duk wanda ya ganshi bazaiyi zaton baida lpy ba.
“Gashi”
taji ummi na mgn a bayanta. Adan kunyace ta juyo sbd ta tarar ta tana karewa mijinta kallo.
Basarwa ummi tayi bata nuna ta ganta ba, tace,
“ga kujera ki zauna”
tayi mgnr tana zama itama. Zama jamilan tayi ta zubawa ummi ido tace,
“wai ya naga abubuwa haka?”
Ummi tace,
“kamar ya fa?”
“Uhum yadda lbri yake zuwane ba haka na gani ba”
ummi tayi murmushi tace,
“kinsan shi lbri idan za’a bayar dadine dashi mutum be sanin sanda zai kara mai gishiri.”
Jamila ta tabe baki itafa ba yanda taso gani ba kenan, can tace,
“kuma haka kike ta fama da wannan garjejen qaton a gida?” Ummi tace,
“ban fahimceki ba?”
“Toh ai gani nayi ba hankali har kika iya jure kashi da fitsarin sa” rintse ido ummi tayi tana tunanin yadda mutane suka kasa fahimtar El-bash yanda kasan A/C haka yake a waje zafi a ciki sanyi fahimtar da tayi masa kenan adan zamanta dashi. Yyinda jamila ta samu damar juyawa gefen El-bash tana kare masa kallo musamman data ga ya lumshe ido, tana ayyanawa a ranta inama ita aka bawa mahaukacin dan kallon fuskar sa kadai ya isa a zauna dashi.
Ummi na bude ta sake kama jamila na kallon el-bash, wani irin abu taji yazo ya tokare mata kirji da sauri tace,
“jamila tashi muje dakina ki gani ranar da kukazo babu dama.”
Dan yatsina fuska jamilan tayi bataso ta musa ummi ta gane asirin zuciyar ta dan haka tabi bayanta tana dan juyowa ta kalleshi a sace.
Yini jamila tayi a gidan koda taje dakin ma kasa zama tayi dan haka tace zata sauka kasa, ganin haka ummi ta riko hannun el-bash ta maida shi daki tana fita kuwa yyi dariya yanajin dadi a ransa ashe ummi na sonsa haka? Tunda ya hango kishi a idonta, takaicine ya kama jamila tace tafiya zatayi, ummi kuwa ta hado mata sha tara ta arziki, har bakin gate ta raka ta, lkcn mlm sabo na zaune ummi ta matsa ta gaishe shi ya amsa mata sama2 babu sakin fuska kamar kullum, a sanyaye tabar gun tanajin wani iri a ranta,yyinda jamila tayi tafiyarta gida wani daci na taso mata arai, duk yadda za’a sai an aura mata El-bash ai ba cikinsu daya da ummin ba kazalika ba ubansu daya ba ehe. Haka tayi ta sakawa da warwarewa harta isa gida.
~~~~~~
Bayan kwana biyu, suraj ya kawo musu ziyara gidan shi da wata yarinya wacce bazata wuce sa’ar ummin ba anace da ita Aisha, lkcn ummi suna parlo tana kallo ta juya taga el-bash ya zubama kallon ido, sai taji ya bata tausayi a tunanin ta ita kadai keyi batasan kuwa shima kallon yake kamar ita. Suna hakan suraj sukazo, ummi da fara’a ta tarbesu shima el-bash murmushi yake batare da yace komai ba, kusa dashi suraj ya zauna ita kuma yarinyar me suna Aisha ta zauna kusa da ummi suna gaisawa, ummi tace,
“oh sai yau suraj aka kawo min aysha” aysha tayi dariya tace,
“kuma lefin shi ne” suraj yana dariyar shima yace,
“au hademin kai zakuyi dan na hada ku?” Ummi tace,
“ai gskyne”
suraj ya kama hannun El-bash yace,
“bari naja abokina muje baya muma mu hada kai”.
dariya sukayi masa a tare sukace,
“kodai zancen kurame ba”
dariya el-bash yyi sbd ya juya musu baya bazasu ganshi ba, suraj yace,
“hakan ma yafi dadi ya zuramin ido na gwalala masa ido”
daria suka sake yi masa be kara cewa komai ba sukabi ta corridor din kitchen inda zai sada su da garden din part din.
Suna tafiya Aysha tace,
“ummi ko awaya bakya nemana, inason nazo gunki wlh toh abubuwan ne sai a slow yanzun ma dan kince nazo na miki kitso ne” ummi tace,
“kinsan ba waya a hannu na, idan na rikema wazan kira tunda kullum muna tare”
cikin tausayi aysha tace,
“Allah ya bashi lpy”
“Ameen” ummi ta amsa tana fadin kafin su dawo,
“kama min kan nawa wlh tunda nayi auren nan bega kitso ba” aysha ta cire gyalenta tace,
“kawo kayan kitson nayi miki ko shida ne”
ummi ta haura sama ta kawo nan aysha ta dinga mata kitson sharp2 ta gama. Ummi ta tashi tace,
“kai gsky ya kamata ki bude saloon aysha”
aysha tace,
“koh?”
“Ehmana kitson masha Allah”
ummi ta fada tana shafa kai.
*Wacece Aysha?*
Aysha Yusuf budurwar Suraj ce wanda ake shirye-shiryen bikinsu nan da dan wani lkci, da tuni ma anyi bikin suraj ya roki Alfarma a kara masa lkci sbd aikin da suke gudanarwa musamman na a mutu ne ko ayi rai?? Yana gamawa za’a sha bikinsa, to el-bash ma haka yaso idan sun gama ya nemi macen aure sai gashi auren yazo masa yna tsaka da aiki to dama haka Allah ke ikonsa kana naka ne yana nasa kuma nasan shine daidai. Suraj da yawan lokuta idan yazo yana hada ummi da aysha a waya har sukayi sabo kamar sunsan juna, mutunci ne me tsafta ya kullu a tsakanin su.
••√√√
Suraj ya kalli El-bash yace,
“jibi ne fah”
“Insha Allah” El-bash ya fada yanajin kamar ya jawo jibin tazo kusa, suraj yace,
“ya naga sai doki kke ko akwai wani abune?”
Dan murmushi El-bash yyi ya rike kirjinsa saitin zuciyar sa yace,
“nan wajen ya kosa ya fitar da abinda ke ciki” da mmki suraj yace,
“kai nifa ban gane ba”
El-bash ya harareshi yace,
“Ummina mana na kosa na sanar mata *ABINDA KE RAINA* i so much love her”
yyi mgnr yana lumshe ido yanaji a ransa inama ummin ya furtawa hakan, wata irin dariyar shakiyanci suraj yyi yana rike ciki yace,
“Gske kke kuwa?” Bude ido el-bash yyi yana murmushi, suraj murna ta kama shi dan bayaso ummi tasha wahalar banza, cikin tsokana yace,
“but when? How? Little ce fah.”
El-bash yce,
“toh sai kayi kuma kaifa iskancin ka nada yawa mtwss”
dariya suraj ya sake yi yace,
“haba maida wuqar ai dole na tayaka murna yanzu ka shigo system din”
“toh sharukhan uban soyayya”
El-bash ya fada yana hararar sa, suraj yace,
“haba waneni ai ka wuce tunani na yanzu ni dan kallo ne”
El-bash yace,
“kaga mu koma bangaren aiki.”
Nan suka fara lissafin yadda zasu kasance a wajen.
°°°°°
A daren ranar haj suwaiba ta gama tsara yadda zasu dauke ummi, duk wani shirinta ta gama tsaf.
Yyinda a bangaren ummi haka kawai ta dinga jin faduwar gaba, tun safe takejin haka saidai faduwar gaban be tsananta ba kamar yanzu da dare yyi, harta kwanta ta mike dan a dakin el-bash take, batason tashin sa ta fita a hankali lkcn besan da fitar ta ba sbd bcci yake, ummi dakinta taje tayo Alwala sbd bugun qirjinta ya tsananta, ji take kamar akwai abinda zai sameta me muni dan haka ta kabbara sallah dan kai kukan ta wajen Rabbi,
kusan kwana tayi tana sallah hade da tilawar Qur’an duk wata addu’a data sani ba wacce bata karanta ba, ummi har asuba taje a takaice dai bata iyayin bcci a ranar ba, anan dakinta tayi sallah idonta duk ya kekashe babu alamun bcci jikinta yyi sanyi kalau.
El-bash be farka ba sai asuba anan yaga ummi bata nan, zaton sa toilet taje yaji ba motsi nan yasa a ransa kila dakinta taje dan haka shima ya fada toilet danyin Alwala.
Koda ummi tayi asuba bata fasa Addu’ah ba hankalin ta ya tashi sbd matsanancin faduwar gaba da takeji, sam bazata iya bcci ba da rana ta fito ta tashi ta gyara daki, bayan ta gama ta leka dakin el-bash taga yana bcci jawo kofar tayi ta gangara kasa, nan ta gyara parlon tsaf taje tayi musu breakfast tana tsaka da jera abincin ya sakko, murmushi tayi shima ya maida mata da murmushin yana wara mata hannu, zuwa tayi ta fada kirjinsa ya rungume ta yana kissing dinta. A haka suka karasa kujera ta jawo musu abincin.
Saida suka gama cin abincin taji wani irin nannauyan bcci yazo mata, kan kujera ta koma ta kwanta dan batajin zata koma sama dan idonta yyi nauyi. El-bash ganin ta kwanta ya gyara mata kwanciyar sannan ya haura sama sbd aikin da zasuyi gobe yana bukatar shiri mekyau.
Barinsa wajen keda wuya aka turo kofar parlon a hankali, ummi ta manta bata rufe ba, dan haka aka samu damar shigowa, mutum biyune masu shigowar kowa ya rufe fuska, haj suwaiba ce da erta sakina, wani farincikine ya kamasu da alama bazasu wahala ba, cikin sauri haj suwaiba ta ciro farin kyalle ta manna a hancin ummi, batare da bata lkci ba suka sungumi ummi wacce ta zama kamar gawa, har cikin mota suka ajeta,
lkcn haj suwaiba ta aiki mlm sabo badan tana bukatar aikan ba saidan bataso ya gani tunda ya hada dangantaka da ummi, sakina ta koma part dinsu da sauri yyinda haj suwaiba ta fice da ummi a tamanin.
El-bash besan wainar da ake toyawa ba saima yana aikine a jima yyi murmushi sbd gab yake daya balle zuciyarsa dan gayama abar kaunar sa ummi abinda ke ciki, jawo wayarsa yyi ya kalli hoton ummi daya dauka tana bcci, wayar yakai bakinsa yyi kssn dinta yana mannawa a kirji zazzafar soyayyar ummi na ninkuwa a ransa.: *EL-BASHEER*
*Zanyi amfani da wannan dama wajen sake miko SAKON TA’AZIYYA GA ‘YAR UWA NANA HAFSAT(MISS XOXO) na rashin MAHAIFI da tayi, ina rokon ALLAH (s.w.a) daya jikansa da RAHMA, ya GAFARTA MASA, yakai HASKE KABARIN sa, MANZON RAHAMA ya karbi BAQUNCIN SA ya ALBARKACI ABINDA YA BARI AMEEN, Dashi da dukkan ‘yan uwa MUSULMAI wanda suka rigamu gidan GASKIYA, Muma idan tamu tazo ALLAH yasa muyi kyakkyawan karshe AMEEEN*
Na
Nuceeyluv😘
59
Sosai take falfala gudu har sukayi kamar zasu bar garin kano, sunyi nisa sosai kafin haj suwaiba ta gangara wata hanya inda ta ninku cikin daji, tayi tafiya medan tsawo inda ta sadata da wani tamfatsetsen gida a dokar daji, sbd yanayin dajin bazama ka dauka akwai gida mekyau haka ba, batare da bata lkci ba gate man dinsu ya bude mata kofa direct inda suke parking tayi, wasu jibga-jibgan motoci ne reras bisa layi masu sheki dakyau wannan yana wane wannan a fagen tsada da kyau, da alama haj taso makara kenan tunda har an taru ssai haka, cikin sassarfa ta kashe motar kafin ta kashe wayarta dan babu me shiga da waya ciki dan haka ta barta a motar, zagawa tayi ta bude wajen ummi tana nan yashe kamar yadda ta ajeta tun farko, sanin daukar da sukayi mata dazu bata da nauyi yasa ta tattare hannun rigarta ta dauki ummi kamar er baby nan tayi hanyar da zata sada ta ga parlon gidan.
+
Tinkis…tinkis.. Ta isa tsakiyar parlon rike da ummi batare da tayi mgn ba sbd ba’a sallama a wajen, da yawan mutane an hallara dama tun ana gobe meeting ake haduwa a gidan zasu kwana washe gari a tattauna sannan a watse, dan haka duk wanda yazo wajen babu fita sai an gama,
Wani shirgegen katon mutum ne a gabansu zaune a kasa babu riga baki wuluq dashi sai kaqon tumbi ya rataya wasu layoyi a wuyansa yana tsiyayo jini a wani tulu yana sha ga ‘yanmata nan reras gabansa an jere kowa na fatan ace zabinsa aka dauka, Mudu Mai kano kenan shugaban su wanda jami’an tsaro ke neman sa ruwa a jallo, a cikin enmatan wasu suma bcci suke wasu ko idon su bude aka kamo su haka haj suwaiba ta aje ummi a cikin jerin su, still ummi na bcci sbd abinda aka shaqa mata sai ta zama ita ba’a raye ba ita ba matacciya ba.
Bayan ta ajen ummin taje ta shiga wani daki ta fito sai gata ta canja zuwa wasu jajayen kaya nan kusa da sauran mutanen ta zauna itama suna jiran jin ta bakin leader nasu.
******
El-basheer ganin zaman bazai gamshe shi ba ya aje komai dan komawa parlo ya ganta da gaske, maida wayar yyi kafin ya fito dakin, cikin murmushi yake takowa kasa saidai me? Yana isowa yaga babu ummi a wajen, tunani yyi ko komawa daki tayi? Maybe wata zuciyar ta bashi amsa, zama yyi kan kujera yana me rufe idonsa ummi kawai yake kallo, ji yyi ya kasa hakuri ya mike dakinta ya nufa harya dora hannun sa kan handle din kofar ya cire yana me cusa kansa cikin gashin sa tunani yake to idan yaje mezai ce? Just pretend like always zuciyar sa ta bashi amsa, dan murmushi yyi yana cije lips dinsa kadan yace
“maybe ma bcci take” ya fada kasa2 yana me tura kofar, wara ido el-bash yyi sbd ganin dakin wayam ba ita ba alamar ta, a hanzar ce ya tura kofar toilet yaga bata nan, ha’a? Ya furta yana me kama habarsa to kodai garden taje? Ko kitchen? Nan ya sakko da sauri kitchen ya fara dubawa ba ummi, garden ma ba ummi abu kamar wasa yana nema ya dawo babba hankalin el-bash ya fara tashi,
duk wani lungu da sako na part din ba inda be duba ba, Something bad is happen yaji zuciyar sa lkci guda ta bashi amsa, batare da tunanin komai ba El-bash ya isa ga camera yanason ganin abinda ya faru yasan dai haka nan ummi bazata fita ba besani ba, tun daga fitowar haj suwaiba da sakina a bangaren su har kawo parlon sa camera ta nuna masa, daidai sanda suke kinkimar ummi El-bash ya saki wata irin kara jikinsa na tsuma, gashin jikinsa suka mike idanun sa suka canja kala a matukar haukace ya fito adakin sa yana haye 3step na beni sbd sauri,
direct part din su haj ya nufa yau haukan karya ya kare hakuran sa yakai makura Zuciyar sa har daci take sbd bakin ciki, baram…ya tura kofar parlon nasu da kafa daidai lkcn sakina tana zaune kan kujera tana shan fruit salad hade dayin kallo tanaji a ranta ta kusa zama matar El-basheer, a gigice ta tashi sbd yadda ta ganshi kafin tayi wani yunquri El-bash ya damki wuyanta cikin karaji yace,
STORY CONTINUES BELOW

“where is she? I said where is she????”
Ya fada cikin wata gigitacciyar kara me cike da karaji.
Mamaki, Al’ajabi, Tsoro, Tashin hankali. Shine ya saukarma sakina lkci guda, rabon dataji muryar El-bash tun kafin ya fara hauka, ta rasa gane inda ya dosa shin ya samu lpy ne? Ko kuwa haukan nasa zai sauke mata? Ko….ya katse mata tunanin lkcn da yyi wurgi da ita har tana bugar bango, Ransa ya sake baci sbd shirun da tayi masa, kujerar gefensa ya kaima wani wawan bugu ta kafa sanda ta hantsila baya cikin tsawa ya sake fadin,
“dan ubanki ina uwarki take ko kin samu matsalar ji ne?”
Tsoro ya sake kama sakina jikinta na rawa tace,
“ta..ta..ta..fita waje dazu.”
“That means wani waje ta tafi da ummi?”
Ya jefo mata mgnr yana tsareta da ido, hankalin sakina yasake dugunzuma zuwa yanzu ta fahimci da real *EL-BASHEER* take mgn ba wancan mahaukacin ba, wani guntun fitsari ne ya zubo mata batare data shirya hakan ba, Bata iya cewa komai ba sai daga masa kai da tayi, jikin El-bash ne yake tsuma tamkar yana filin yaki zuciyar sa ta kara daci yace,
“i’m sure, i’m very sure idan wani abu ya samu ummi i will killed the two of you”
ya fada cikin matsanancin bacin rai yana me kaiwa plasma tv naushi a take kuwa ta ragargaje.
Yana gama fadin haka ya fito a parlon yana me danna kwado a kofar danma kar sakinan ta gudu.
Cikin sauri ya nufi parking space motar sa daya dade behau ba ita ya shige be damu da irin kurar da tayi ba, a guje ya manno ta ganin hakan yasa mlm sabo ya wangale gate din tun kafin ya iso. Ko kula dashi beyi ba ya fice a gidan. Wayar suraj ce ta shigo masa dan haka yadan sassauta gudun kafin ya cira,
“haba ina ta kiranka tun dazu ina ka shiga?”
Suraj ya fada,
“Ummi”
el-bash ya furta a takaice, Hankali tashe suraj yace
“meya samu ummin?”
El-bash ya hadiye wani maqaqin daci daya tokare masa a makogwaro dakyar kafin yace,
“sun sace ta.” “Innalilahi wa’inna ilaihin raji’un”
Suraj ya fada yana ci gaba da fadin,
“where are you now?”
El-bash ya fada masa daidai inda yake. Suraj yace,
“i will be right away in the next 10mins just wait for me pls.”
Ya fada yana kashe wayar dan yasan yanzu El-bash baya cikin nutsuwar sa dan haka bazai fahimci ina suka kai ummin ba tunda tunanin sa ya fita daga aikin sa.
Ba’afi 10mins din ba kuwa sai ga suraj a napep yana zuwa ya karbi key shi kuma el-bash ya koma dayan side din yana huci kamar wanda yyi dambe. Kallon sa suraj yyi yace,
“yanzu daka fito ina zaka?”
“Wanne irin banzan tmby ne wannan? Taya za’ai a sace min the love of my life kace ina zanje? Mtwsss..”
El-bash yyi mgnr cikin jin haushi yanaji a ransa kamar yyi tsuntsuwa ya ganshi gaban haj suwaiba bashakka zai iya kasheta a wajen.
Dan murmushi suraj yyi yace,
“”ba nufina kenan ba frnd kayiwa tmbyr gurguwar fahimta,
Komai nason nutsuwa sbd muyi kyakkyawan bincike”
kala el-bash be sake cewa ba sai huci da yake zuciyar sa na tafarfasa, Suraj yaja motar suka tafi kai tsaye wannan gidan da suka taba zuwa ya nufa dasu yana Addu’a a ransa Allah ya basu nasara kar plans dinsu ya samu matsala a takaice dai shima hankalin sa a matukar tashe yake.
~~~~~
Saida ya shanye cikin tulun nan na jini kafin yyi wata irin gyatsa me kara hade da fitar da wani irin wari. Kallonsu yake daya bayan daya kafin yace,
“kowa yasha abinda ke gabansa”
yyi mgnr cikin wata irin murya marar dadi kamar an shaqe sai kace wanda yake mura. Take kuwa su haj suwaiba suka daga cup din gabansu dake cike da jini suka shanye, suna gamawa Mudu ya dawo da kallon sa kan emmatan da aka jere masa wasu na ajiyar zuciya sbd kukan da sukaci wasu kuma na yashe har lkcn hodar bata sake su ba irinsu ummi.
Fici-ficin idonsa ya zuba musu yana lashe baki har ya kawo kan ummi harya wuceta kuma saiya sake dawowa ya zuba mata ido duk cikin emmatan ummi ta fisu kyau ya zubawa zara-zaran gashin idonta kallo hade da dan karamin pink lips dinta inda ya dace da dogon hancin ta daidai gwargwado kirjinta dake cike tam ya nacewa kallo har besan lkcn daya karaso gareta ba.
“Waye ya kawo wannan?”
Ya fada yana nuna ummi, haj suwaiba farinciki ya kamata da alama itace me nasara wannan karon, cikin zumudi tace,
“nice”
tayi mgnr tana murmushi.
“Good job”
ya fada yana me murmushin shima yace,
“na zabi wannan sleeping beuty din a kaimin ita dakina”
da murna haj ta taso ta kinkimi ummi ta kaita dakinsa tana sheka dariyar mugunta dangwarar ta tayi tace,
Er banza karshen ki yazo saura mahaukacin naki da ubansa idan ya dawo daga kasar daya lula”
tayi mgnr tana ficewa a dakin jin kanta take ta zama ta hannun dama itama za’a girmamata.
Mudi ya kallesu yace,
“masu matsala suzo su fara mgn kafin gobe mu tattauna”
nan wani ya mike yace,
“gaisuwa nake mudu mai kano uban fasa taro ciwon idon jami’an tsaro sunyi sun kasa haka zasu barka wannan karon matsala ce tafe dani daya zuwa biyu”
“an baka dama” mudi ya fada yana kada buzun hannun sa, mutumin yace,
“kasuwace taki gaba taki baya so nake na samu customers yanda sunana zai zaga cikin jahar da nake harma da makota.”
Mudu ya fashe da dariya yana girgiza kai yace,
“ka kawo kan jarirai guda goma wanda basuyi sati ba da haihuwa a bawa dodanniya jini tasha tabbas bukata zata biya.”
“Godiya nake” mutumin ya fada yana zama. Wata mata ta mike tace,
“gaisuwa nake murucin kan dutse baka fitoba saida ka shirya matsala daya ke tafe dani”
“an baki dma”
mudi ya fada yana girgiza kai. Matar taci gaba
“matsalar itace so nake na samu magoya baya a jam’iyar da nake dan samun kujerar sanata kowa ya soni ya zabeni.”
Wata irin dariya itaama yyi mata kafin yace,
“Kije kiyi zina da kare maniyyin da kika fitar ki dinga shafa shi a jikin ki sai ki kawowa dodanniya idanuwan yara en kasa da shekara biyar guda ashiri bukata zata biya”
“Nagode”
matar ta fada tana murmushi.
Haka suka dinga fadar matsalar su ana gayamusu abinda zasu kawo har kowa ya gama fada. Kafin Mudi ya kalli haj suwaiba da tun dazu ta matsu a gama taji matsayin ta, yace,
“ba’a taba kawo min mekyau kamar wannan ba idan yadda take dakyau haka kasanta keda dadi zaki samu kyauta me tsoka.” Farinciki ya mamaye haj suwaiba tace,
“shugaba za’a dace idan an gwada.”
Girgiza kai yyi sanna ya mike yabar musu wajen mutanen na hira shi kuma zai qaddamar da kusancin ummi dan a bawa dodanniya jininta da asuba.
••••••
Dakyar ya samu el-bash ya yadda suka shiga gidan, cikin sauri suka kwashi guns dinsu da suka tanada sbd ranar sunsan gurun bazai rasa tsaro ba, nrml kaya suka sa sannan suka fito El-bash yce,
“naga kasa munyi shirin can kuma kasan ummi zan nemo”
suraj na latsa wayar sa dan hankalin sa yafi yawa kanta yace,
“kace haj suwaiba ta dauke ta?”
“Eh”
ya amsa a dakile. Girgiza kai suraj yyi yana fadin
“pls ka tsaida hankalin ka waje daya dan naga alama kana neman manta aikin dake gabanmu kuma duk akansu haj suwaban ne baka tunanin can takai ta?”
“Innalillahi wa’inna ilaihin raji’un”
El-bash ya fada yana dafe kansa sam idea din batazo masa ba ya shiga rudani hankalin sa be sake tashi ba saida ya tuno abinda en kungiyar suke “ahhhhh…….., ya saki kara me ciwo yana me cusa hannayen sa cikin gashin kansa jikin sa ne ya kama bari sbd tsananin tashin hankali da bacin rai. Suraj kansa hankalin sa a tashe yake da alama ayau zasuyi operation dinnan basai gobe ba, wayarsa ya dannan ya sanar da sauran jami’an yana gaya musu yadda abubuwa zasu kasance. Yana gamawa ya maida hankalin sa kan driving yana kallon wayarsa.
Yyinda El-bash yakai kololuwa wajen tashin hankali, besan sanda ya fara sumbatu ba yana me fadin,
“i’m sure i will killed them, i’m very sure i will destroyed them, if any body touch my wife i will cut him into pieces”
haka yyi ta jera mgn yana dukan dayan hannun sa hade dayin huci me zafi. Suraj kam sai gudu yake falfalawa yana fatan kar a samu matsala dazai samu meyin driving shima kam daya zauna gefe dan a matukar rude yake.
°°°°°°°
Mudi na shiga dakin ya samu wani ruwan tsafi yyi wasu tofin tsafi kafin ya watsawa ummi, a firgice ummi ta farka tana salati a bakinta, cikin sauri mudi ya kama bakin ummi tana kokarin kwacewa ya zuba mata ruwan tsafin nan a bakinta, kafin kace me ummi ta fara tari da karfi kusan 5mins ta dauka tana tarin kafin ta daina dago kanta tayi tana kallon mudi tamkar wata wawiya, wata irin dariya mudi ya saki yana shafa cikin sa buzun dazu ya dauka yana girgizawa yace,
“dodonniya da alama ta manta kanta, ta manta ita wacece, a yanzu sai yadda mukayi da ita cikin umarnin mu hhhhhh….”
ya sake sakin dariya marar dadin sauraro.
Wato sirrin ruwan tsafin shine duk wanda aka bawa yasha to a take brain dinsa zata juye, zai manta kansa, zai manta shi waye, zai manta wanda ya sansu, bashi da wani tunani sai wanda mudi ya umurce ka dashi haka yakema duk macen daya zaba wacce zai kusance ta.
Toh da Alama ummi aikin ya kama ta dan har zuwa yanzu kallon sa take kamar taga sabon halitta. Ana haka mudi ya fara tube wandon sa yana me nufar ummi hade da lashe baki.*EL-BASHEER*
*My Facebook fans wannan pages din naku ne, da ace da dama dana lissafo ku anan to amma yawanku bazai isa na rubuceku ba, kudai kusa a ranku NUCEEY Tana yinku irin SOSAI dinnan😍*
Na
Nuceeyluv😘
60
Still ummi kallon sa take tamkar wawiya harya iso gabanta yana lashe baki, wandon ya ida cirewa ya rage masa sauran gajeran wando, yana kokarin cire gajeran wandon yaji jikinsa ya saki alamar baida karfin dazai iya kusantar mace a halin yanzu, hannu ya zura cikin gajeran wandon ya laluma sai yaji abu kamar lagwani yyi lakwam ya kuma kankance gwalalo mitsi2 idon sa yyi yana me nufar toilet da sauri take yyi zigidir yana kallon kansa
“Ahhha…..”
ya saki ihun bacin rai sbd ciwon kankancewar sa daya dawo ya manta sam ciwon na zuwa masa time to time bezo da mgnin ba. Da sauri ya fito daga toilet din bintir…bintir babu komai jikinsa abu na lilo yyinda tumbi ke sakwar-sakwar NonNon sa kamar na mata duk ya sakko, har lkcn ummi na kallon direction din daya barta ta koma kamar wata gunki,
+
“Yake dodanniya….,”
Mudi ya furta da karfi yana me kada buzun hannun sa yyi tsaye tsakiyar dakin,
“Ki bani mgnin dazan warke yanzun nan kodan na samu damar cika miki aikin ki.”
Ya fada yana daga kansa sama. Shiru dakin yyi can sai ga wata jar wuta ta bulo ta tsakiyar ceiling iya kan dodanniya ne ya bullo hakoran ta zaqo2 fuskar ta meban tsoro tana dalalar jini yyinda idanuwan ta ke fitar da hasken jar wuta tace,
“kai mudu mene zaka dameni a daidai wannan lkcn bayan kasan gobe ne haduwar mu?” Tayi mgnr cikin fada cikin murya marar dadi kamar me kukan mage dan sai mutum ya nutsu zai fahimci abinda take fada.
“Ya shugabata Mazantaka ta yyi lakwam inason ya dawo daidai dan kaddamar da aiki”
“Puhahahaa….hihihihi…” Dodanniya ta saki dariya marar dadin sauraro tace,
“dama akan wannan ne ka kirani?”
“Eh ya shugabata” ya fada yana risinar da kai,
“Angama” Dodanniya ta fada tana kallon wani waje take wani koko ya fito cike da ruwan tsafi a ciki,
“Gashi nan ka tsoma a ciki har na tsawon sa’o’i biyar saika girgiza zaka dawo zam-zam kai kamar ta doki, mgn ta karshe kuma karka sake ka sake kirana idan na tafi dan akwai abinda zanyi zamu hadu goben.”
“Godiya nake ya shugabata”
ya fada cikin farin ciki, Dodanniya ta saki ihu tana fadin,
“dakinka yau akwai zafin tsiya.”
ta fada tana me bacewa da sauri.
Ko a jikinsa tunda ya samu abinda yakeso, cikin sauri ya isa ga kokon yana me kamo halittar sa yana tsomawa. Tsomawar sa keda wuya yaga abu ya tafi luuuu….., kafin ya farga ya koma dan mitsil tamkar na jarirai.
“Ahhhhh…..”
ya saki ihu a firgice yana mikewa da sauri hade da tale cinyoyin sa ya hango shi can sama.
“Na shiga uku”
ya furta yana me rufe bakinsa da sauri jikinsa na rawa hankali a tashe, Dakko buzunsa yyi zai kira dodanniya ya fasa sbd kashedin datayi masa, mazari ya farayi tsakiyar dakin yana fadin,
“ya zakimin haka dodanniya keda nace karfi nakeso saiki maidamin abu kamar na jarirai?”
Yyi mgnr ransa a bace sam beso tace karya sake kiran ba sbd Allah mezai cewa sauran members? Wannan ai abin kunyane a gareshi.
Juyowa yyi yana kallon ummi zuwa lkcn ta kifa kanta kasa,
“Shegiya bcci kike” ya fada yana kai mata bugu, da sauri ta dago kanta jikinta na rawa tana jiran umarni,
“Dakko min wando na a toilet”
ya fada cikin jin haushi sai kace itace ta kankance masa gaba. Ko karasa mgnr beyi ba ta mike da sauri ta isa inda ya aiketa, babu bata lkci ta kawo masa wargajejen wandon sa ya maida yana mejin haushin be more jikinta ba.
“Dalla matsa min a waje kije can ki zauna ina gama shan giyata zaki min tausa”
yyi mgn yana mata nuni da inda zata zauna, zungi2 kuwa ummi tayi yadda yace, jawo giyarsa yyi ya samu glass cup ya tsiyaya daidai zai kai bakinsa yaji ance daram……, kaiwar da beyi ba kenan ya mike da sauri cikin mmki dan wannan karar babu shakka ta bindiga ce, da sauri ya jawo kayansa yasa kafin ya dauki bindigar sa yayo waje,
“Where is my wifeee……,???”
kalmar data doki dodon kunnen mudi kenan yaji an fada cikin karaji, karasowar sa parlon yaga duk members din an zagaye su wasu an musu rauni parlon ya hargitse da alama anyi artabu be sani ba,
“Can’t you say anything????”
El-bash ya sake fada cikin tsawa yana me pointing haj suwaiba da gun a goshi. Yyi daidai da sakin fitsarin ta kenan a karo na ba adadi, Idan ana fadar rudani, firgici, tashin hankali, to shine ya dirar ma haj suwaiba kala bata iya furtawa ba sbd tashin hankali ta kasa banbance a wanne yanayi take ciki,
“Who are you?” El-bash yaji an katse shi, besan da tahowar mudi ba sannan be juya baya ba,
“Look at ur back El-bash”
yaji suraj na fada mishi hade da masa nuni da hannu dukda Shima hankalin sa tashe yake amma ganin ummi a bayan mutumin ya saki boyayyar ajiyar zuciyar farinciki, yana murmushin Nasara yace,
“ur wife”
A take kuwa El-bash ya juyo da sauri. Besan lkcn daya nufi wajen ummi ba kadan ya rage ya kama ta yaga wargajejen mutum ya janye ta, A hasali yace,
“kana hauka ne? Matar tawa kke rikewa?” Yyi mgnr yana kokarin wanka masa mari,
“Stop…”
Mudi ya fada yana rike hannun El-bash kafin yace,
“ka fara sanin matsayinta a yanzu kafin ka yanke hukunci domin dis gal is mine saida umarni na take komai kai a takaice dai bata san ka bama yanzu she loss her memory ta manta komi dan haka ka tsaya iya matsayin ka.”
“Whaaaaattttt…..”
El-bash da suraj suka fada a tare hankalin su a matukar tashe, Cakumo wuyan mudi El-bash yyi cikin karaji yake fadin,
“me kukai mata? Tsafeta kukayi?”
Yyinda suraj ya matso kusa da ummi a rude yana fadin,
“Ummi wai baki gane muba?”
Yyi mgnr yana karkada hannun sa wajen idonta, Kikam ummi ta tsaya batace komai ba saima kallon mudi da take,
“Innalillahi wa’inna ilaihin raji’un” suraj ya fada yana dafa kansa yyinda sauran jami’an dake zagaye suma hankalin su a matukar tashe.
“Ummi why? Why ummi? Ya zaki mana haka? Taya hakan ta kasance? Ummin pls say something?
Suraj ya ida mgnr muryar sa na rawa kamar wanda zaiyi kuka duk wata sauran nutsuwar sa ta tafi da alama yana dab da zama El-bash shima ya haukace musu gaba1 jiyai kansa ya cushe babu mafita.
Dakyar Mudi ya kwace daga shakar da El-bash yyi masa cikin karfin hali yake masa dariyar mugunta yace,
“kanaso ka tabbatar da hakan ne?”
A zuciye El-bash yakai masa naushi hanci mudi ya goce yana me nufar ummi fisgo hannun ta yyi ya dora gun a hannun ta yace,
“harbe min shi.” Qamm ummi ta rike gun din ta isa direction din daya nuna mata zata aiwatar da abinda ya sata.”
“Hasbunallahi wani’imal wakil, Lahaula wala quwatu illa billah, Allahumma ajirni fi musibati….,”
Abinda Suraj ke furtawa kenan wasu zafafan hawaye na sakkowa idonsa cikin azama ya isa gaban El-bash ya tsaya ya sadaukar da a kashe shi akan a kashe El-bash din.
A bangaren El-bash kuwa ya zama speechless duk wani magudanar jininsa ta tsaya tunanin sa ya kwance be samu karfin jiki ba saida suraj yasha gaban sa, da sauri ya ture suraj din dan kar ummin ta harbe shi daidai lkcn kuwa ummi ta karaso tana me dora gun din a saitin Kirjin El-bash.EL-BASHEER*
61
“Dakyau Emmata ba haka zakiyi ba” mudi ya fada yana karasowa kusa dasu, “dan jawo bindigar baya ummi ta dawo da ita baya, yauwa danyi sama wajen goshin sa” ummi tayi yadda yace,
“aha dakyau kansa nakeso ki fasa”
yyi mgnr yana komawa daga bayan El-bash yace,
“yauwa dan sake daidaitawa”
ummi tayi,
“aha gud zan kirga uku saiki harbe shi understand?”
Ummi ta girgiza kai,
“Weldon”
mudi ya fada yana dariyar mugunta yyinda sauran Sauran jami’an suka zaro guns dinsu zasu harbi mudi, hannu El-bash ya daga musu alamar su bari suraj a fusace yace,
“baka ganin abinda yake shirin sata?”
Hannu El-bash yasa a bakinsa alamar yyi shiru kafin ya rufe idonsa. Mudi yana ci gaba da dariya yace,
“aha ‘yammata 3…2….1 Go……” Darammmm….. Ummi ta saki harbi, Shiru dakin ya dauka sbd dayawa wasu idonsu a kulle yake kowa na cikin firgicin abinda ya faru,
“Wasssshhhh…..”
sukaji sound wani dabam na fitowa da sauri kowa ya bude ido wanda idonsu ke bude kuwa daskarewa sukai a wajen, mamaki ne ya kama mutane ganin mudi durkushe a kasa yana ihun azaba ga hannun sa na fitar da jini inda bullet ya huda
“Wayyyo Hannu na”
mudi ya sake fada cikin radadin azaba.+
“Yeeessss Suraj ya furta cikin farin ciki yana fadin Oh ya Rabbi Thank you” Yyinda El-bash ya daskare a wajen sbd mamakin ummi sai kallonta yake ya kasa furta wani words ko kiftawa bayayi.
“Hhhhhhhhhhhh…”
sukaji Ummi ta kwashe da dariya har tana kwarewa, Matsawa tayi gaban Mudi tace,
“Gsky duk inda akai da jaki sai yaci kara hhhhhhhhh Kaiii wlh am trying da harna iya rike dariyana zuwa yanzu” tayi mgnr tana nunashi kafin taci gaba,
“Kai gaka Arnen kafiri ko? An gaya maka Addu’ah tana faduwa kasa banza ne? No kayi kuskure”
tayi mgnr tana buga katon tumbinsa da gun tace,
Tumbin haramun kenan so ya kaga acting din? Tsakanin ni da ku waye winner? Yanzu ka tabbatar da tsafin ku karyane ko? Mtwss lusari.”
Tayi mgnr tana juyawa gaban haj suwaiba data sake tsurewa tace,
“Suwaiba ko?”
“Hhhh…”
ummi ta saki dariya,
“gsky bansan cewa brain din kifi ne dake ba sai yau keda wancan munafikin”
Ta nuna Alhj rabe daya rude sbd firgici dan tun zuwan El-bash ya daskare,
“I know kuna mmki ko? Hmm kadan daga cikin aikin *SS* jami’an sirri masu farin kaya, Mutum ya zauna long time cikin *HAUKA* a zaton ko aikin ku ne koh?”
Ummi tayi mgnr tana me harbin Alhj Rabe a cinya,
“Ahhh…..”
Ya saki ihun azaba,
“Oh da zafi?”
Tayi mgnr tana zaro ido,
“Ah lalle this is just the beginning” tayi mgnr tana murmushi, ta koma da kallonta kan suwaiba tayi wani guntun murmushin gefen baki,
“A zaton ki dabarar ki tasa har kika dakko ni? Kin dauka bcci nake? Oh kinyi zaton shakamin hoda yyi aiki? Mtwsss Gsky ban taba gnin mekan dusa ba irinki, koda yake kinyi kokari da kika karasa cika mana aiki tunda kika kawo ni inda zamu sameku cikin sauki batare da munsha wahalar ina kuka boye ba, kinsan dalili?”
Ummi taci gaba,
“kalli nan”
ummi ta zaro karamin abu a kanta cikin kitson ta tace,
“duk inda kuka cusani Abokan aiki na kallon ku sbd camera dake cikin kitso na.”
Gaba1 idan ka cire sauran jami’ai da suraj babu wanda be fada cikin tafkin mamaki ba hardai El-bash daya kasa fahimtar ina zancen ummin ya dosa.
“Karbi wannan” ummi ta fada tana me harbin suwaiba a kafa,
“wayyyo na shiga uku na lalace”
Suwaiba ta fada tana me kama kafarta shi kansa mudi be daina gurnani ba,
“Baki lalace ba tukun saikin fahimci idon mutum uku ne a kanki cikin gida daya
*”EL-BASHEER, MALAM SABO AND LASTLY HUSNAH”*
Cikin tsananin tashin hankali da mmki haj suwaiba da Alhj Rabe ke binsu da kallo,
“wacece Husnah?” Haj suwaiba ta tmby dakyar,
Dadai lkcn El-bash ya kamo hannun suraj yana fadin,
“kai kun sani a duhu kodai ta zauce dayawa ne haka? Me take cewa kam????”
Suraj na murmushi yace,
” *ASMA’U AHMAD Wasu suce UMMI/HUSNAH* amman dai anfi kiranta da ummi, yarinya me hazaqa da juriya kenan itace ta taimaki UMMAH bisa umarnin mlm sabo Gateman nasan baka sani ba amma kam ummi tana cikin aikin da mukeyi.”
“Whattt…..”
El-bash ya fada cikin tsananin mamaki inda mgnr ummi ta katse shi yaji tana bada command
“Sir Bala pls take them to the hospital”
tayi mgnr tana nuna su mudi data harba,
“and Sir Abdul, Emanuale, muktar, Pls a kwashe sauran members”
“okay Ma”
sukayi mgnr suna sara mata. Nan jami’ai suka fara aikin da ummi ta sasu, sai lkcn Ummi ta juyo wajensu El-bash, Suraj ta sarawa shima ya sara mata yana fadin,
“Good job but kin razana mu daga yadda muka shirya”
“don’t worry I will explain abinda yasa nayi hakan later”
“No problem”
Suraj ya fada yana barin wajen. Kallonta ta koma kan El-bash daya ke tsaye yana ganin abin kamar a film ta sake matsawa dab dashi cikin girmamawa ta sara mai 👩🏻✈ a hankali El-bash shima ya maida mata martani 👨🏻✈, Kallo suka kafe junansu dashi can ummi ta katse shirun da fadin,
“I’m sorr……,”
bata karasa ba ya jawota jikinsa ya hade bakinsu waje daya dan abinda yakeji game da ummi ya zarta tunanin sa.
“Oga easyyy”
suraj ya fada yana dariya yyi saurin karasa fita su kansu sauran jami’an fecewa sukai da wuri dama sun gama titsa keyarsu babu kowa ya rage daga ummi sai El-bash.
Cikin shauki suke kissing junansu harma suka kusa zubewa a wajen, dakyar suka saki junan su ummi na dafa kai,
“What?”
El-bash Ya tmby,
“my head”
ummi ta fada tana rikewa, a rikice El-bash ya dauketa da sauri ya fito waje, motar data rage yahau suraj ya bar musu dan har sunyi gaba, ganin yadda ya tada hankalin sa ummi ta kalleshi tace,
“karka damu fa stress ne kawai komai zai zama nrml kasan ban samu bcci ba throughout yesterday i think abinda ya haddasa kenan”
“no Baby banson abinda zai sameki”
yyi mgnr yana me bawa motar wuta.
“Murmushi ummi tayi tana maimata sunan daya kirata dashi oh ya Rabbi finally hasashe na ya zama gsky ta fada a ranta tana lumshe ido.
Direct hospital yakai ummi. A yadda yaje musu a birkice sbd ummi har lumshe ido take, gado suka bata kafin aka daura mata drip bayan tasha Allurar bcci.
*Aha masu kuka suna dariya a musu gwalo wooo😝😝😝, Ina masu tunanin Ummi itace HUSNAH🗣🗣🗣toh ku matso mu cashe💃🏻💃🏻 dan HASASHEN KU ya zama GASKIYA*🤸🏻♀🤸🏻♀🤸🏻♀🤸🏻♀EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
62
Ganin tana bcci ya nemi wata nurse ta kular masa da ita zaije gida sharp2 ya dawo. Yana zuwa gidan direct part din haj suwaiba yyi, nan ya samu sakina na kakarin amai harta galabaita da alama ta dade tanayi. Mtss yaja tsaki a ransa yana fitowa a part din, waya yyi aka turo wata mace ta kwasheta itama aka kaita hsptl din da su haj suwaiba suke.
***
Sai around 9am ummi ta fara motsi har ta bude idonta fes reras ta gansu cikin dakin da alama zaman jiranta suke,
“sannu Husnah”
taji wata murya daban tai mata mgn, juya kanta tayi taga umma ce tana mata murmushi, da murna ta yunkura zata tashi daidai lkcn El-bash ya turo kofar dan yaje gurin likita ne yana musu complain ta kwana tana bcci shi gsky so yake yaga ta farka,
“Oh No baby”
Ya fada da sauri yana karasowa gaban gadon yana fadin,
“wannan ai aikina ne dakin bari nazo saina daga ki”
yyi mgnr yana kokarin dagotan ita kuma ummi na nokewa sbd kunyar su Umma ga suraj da Mlm sabo a wajen,
“to marar kunya ku samemu a gida”
Umma tayi mgnr tana murmushi itama ta fice ashe tuni su Abba sun fece, Dan shafo kansa yyi yana murmushi shi ya manta ma da mutane a wajen idonsa ya rufe, memakon su tashi saima zama yyi gefen gadon yana dan rankwafawa gaban ummi sukayi dab da juna,
“To yadai kike cuno baki?”
Yyi mgnr yana daga mata gira, dan hararar sa tayi kafin tace,
“ba kaine ba”
“da nayi me?”
“Kasa naji kunya mana”
tayi mgnr tana murguda baki,
“You koh”
yyi mgnr yana wara mata ido kamo bakin yyi zai mata kiss aka turo kofa.+
Fasawa yyi ya maida hankalin sa kan kofar, likita ne ya shigo yana fadin,
“Yanzu kam komai nrml kuna iya tafiya ku karasa acan”
yyi mgnr yana murmushi, murmushi El-bash yyi yana mika masa hannu yace,
“Thanks”
“your are welcom” Dr. Ya fada yana barin wajen. Suma wajen suka bari yana rike da ummi kamar za’a kwace masa ita.
Driving yake dayan hannun sa yana kan hannun ummi yana murzawa a hankali yyinda yake juyowa time to time ya kalli ummi,
“mutum ya maida hankalin sa kan driving dai”
ummi tayi mgnr tana kallon window kamar ba ita tayi mgnr ba,
“I can’t believe cewar kema SS ce” Juyowa tayi tana kallon sa tace,
“Why?”
Dan daga kafadar sa yyi yace
“just imaging how, When, and why all this happened Batare dana fahimta ba tuntuni”
dariya ummi tayi tana fadin,
“to mene abin mmki tunda kasan yanayin aikin”
tayi mgnr tana murmushi, Shima murmushin yyi yace,
“so all this abubuwan da kike u known everything”
yyi mgnr yana karya kan motar gidan, gyada kai tayi tana murmushi,
“Wonderful” El-bash ya fada yana me budema ummi kofa.
A haka suna zance suka isa parlon nasu, umma suka tarar kawai sauran sun tafi akan zasu dawo later,
“oyoyo my daughter”
Ummah ta fada tana warama ummi hannu, cike da kunya taje ta rungume umma tana dariya nan suka zube kan kujera, ummi tace,
“Ummah kamar a mafarki wlh yaushe kukazo?”
Umma na murmushi tace,
“ai na fada miki when the game is over zamu diro kasar so 8am muka iso”
dariya ummi tayi tace,
“gsky I’m happy so much happy to see you wlh.”
“Toh ni kuma sai ace na koma inda na fito” El-bash ya jefo tasa mgnr hannun sa rungume a kirji shinan yyi fushi ba’ayi welcoming dinshi ba. Dariya sukai masa ummah tace,
“are you jealous?”
“No ummah but….” Gwalo ummi tayi masa,
“you see ummah gwalo takemin”
dariya umman tayi tace,
“bari naje part dina ummi kiyi wanka dan kiji dadin jikin ki sai kuzo muci food a part dina.”
“Thank you Ummah”
ummi ta fadi tana rakata har bakin kofa, tana rufe kofar juyowar da zatayi taji ta buge mutum,
“oh sorry”
ummi ta fada zata kauce,
“Wlh yarinyar nan kinma rainani sai wani hademin kai kuke irin kunsan junan nan tuntuni.” Ummi tana dariya tace,
“jealousy”
“who?”
Yyi mgnr yana kamo kunnen ta,
“Pls bada kai nake ba ka sakar min kunne” Sakar mata kunne yyi yace,
“matsoraciya” aiko yana sakin kunnen tayi hanyar stairs da gudu tana fadin,
“yauwa ehe dakai nake jealousy”
Binta yyi kafin ya iso ta shige daki da gudu ta datse. Kwafa yyi ya wuce nasa dakin shima dan yin wanka.
STORY CONTINUES BELOW

~~~~~~~
Fes ummi ta fito cikin wata Arabian gown wadda tayi matukar amsar jikinta tayi rolling da gyalenta tayi kyau matuka musamman data gyara gashinta tayi parking tuni ta warware kitson da akayi mata dama sbd aiki akayi.
Fitowar ta yyi daidai da fitowar El-bash shima OMG! Kowannen su ya fada a zuciyar sa tsantsar kyan da El-bash yyi kai abin ba’ace komai, shigar kananun kaya yyi wanda sukayi matukar amsar sa gashin kansa ya gyara sajen sa ya sake masa gyara ya dawo real El-bash ba fake ba, Son kowa burin kowacce mace me jini a jika kin wanda ya rasa a kowanne bangare dai abin ba’ace komai.
Kamo hannun ummi yyi yace,
“aha yanzu wa na kama?”
Zaro ido tayi tace,
“pls I’m srr….,” bakinsu ya hade waje daya har saida ya kwashe janbakin data shafa kafin ya saketa, dan bata rai ummi tayi tana cuno baki tace,
“duk ka batamin kwalliya”
murmushi yyi yace,
“mgnin me tsiwa kenan kuma idan ba’a dena cuno baki ba tam…” Tuni ummi ta daidaita bakin tasan halin kayanta in and out.
Har part din ummah sukaje, ashe tuni El-bash yasa aka gyara sbd yasan da zuwan su. Ummah da Abba suna kan dining table suka isa, gaishe su sukayi kafin Ummah tace,
“bismillah”
dan komai ya zama ready ci zasuyi. Saida sukayi kat kafin suka koma parlo dukansu, lkcn ma har suraj ya dawo suka shigo shi da mlm sabo. Addu’ah aka bude taron dashi kafin Abba yace,
“nasan dukkannin mu anan munsan meya tara mu, koda yake ba sabon abu bane ko kullewar kai sai iya El-basheer ne da nasan zaiyi mmkin shigowar ummi cikin aikin su, to Masha Allah yanzu haj hafsat zatayi masa bayanin komai sai abin da ba’a rasa ba da su mlm sabo zasu kara akai.”
Ummah tayi murmushi kafin tace,
“Babu abinda zance da bayin Allah nan sai Godiya da fatan Allah yyi musu sakayya da mafificin Alkhairi, samun nagari a wannan zamani sai an tona, kazalika samun Aboki nagari sai anyi bincike sosai kafin a samu, El-basheer nasan bakasan ummi ba amma kanada lbrn yarinyar data taimaka min lkcn da azzaluman nan sukaso Ganin bayana ba, Toh yarinyar dai itace Ummi ko Husnah bisa umarnin mlm sabo ta baro gida ta tsaya tare dani har tsawon kwanaki dan ta zauna dani.
Duk abinda sukayi sunyi ne dan Allah harma mlm sabo ya bata umarnin karta fadi waye ya turo ta, to a lkcn na hakura badan naso ba har na tafi bayan na matsa ta gayamin abinda zan mata badan na biyasu ba saidan kawai kyauta. Nan ta bukaci fadawa harkar SS sbd lbrn zalincin da taji mutanen nan sunyi, naso ta canja wani bangaren sai naga bilhaqqi da gsky so take dan haka nace ba matsala na danqa komai wajen suraj sbd abin harkar ku ce, bayan na sakkwa a Pakistan mukayi waya da ita a wayar suraj sai na sake bata shawara tayi wani course din idan yaso ta gama sai tayi training kawai na SS tunda dalilin da yasa takeson yi sbd wa’annan en kungiyar ne wato HSK Asso…., ta karbi shawarata tace zatayi mgn da babanta, wato kanin mahaifinta mlm sabo, nayi murna sosai na kuma kara daraja mlm sabo domin tun farko shiya fargar dani daga bcci da nake,
Already kunsan me nake nufi, so ummi sunyi mgn inda mlm sabo ya amince tayi kr2 saidai basaso matarshi ta sani sbd zata iya hanawa anan suraj yace wannan ba matsala bace, akwai budurwar sa Aysha tana level one a buk nan ya hadasu da aysha cousin dinsa ce mamarta kanwar mamarsa ce nan ya fayyace ma maman aysha komai, ta basu shawara a turo ummi kamar tana zuwa gidan aiki daga nan su wuce skul da aysha yadda dai matar mlm sabo bazata sani ba. Hakan kuwa akayi Innar jamila zaton ta duk a cikin cusgunawar ummi ne mlm sabo ya samo mata aikatau duk wata zan tura kudi a matsayin kamar albashin ta haka zasu karbe suna murna ummi na wahala, so sai ya kasance duk wani kayan kr2n ummi yana gidan su aysha harta gama kr2n ta na business Admin ta tafi training na wasu months akan SS, duk wannan abun Allah besa kun hadu da ummin ba.”
Umma ta karasa mgnr da murmushi tace,
“mlm sabo akwai abin fada?”
“Komai kin gama fada ai, fatana Allah ya tsare gaba.”
Ameen duka suka amsa.
“Suraj fa?”
Umma ta tmby, murmushi yyi yace,
“ummah Kin gama mgn Fata nagari akoda yaushe”
Ameeen suma suka amsa kowa da murmushi kan fuskar sa.
“So mene baka gane ba?” Tayi mgnr tana kallon El-bash daya sake tsundumawa cikin tafkin mmki, So yake yace meyasa aka boyewa Inna gskyr kr2n ummi amma yaji nauyi koma dai meye ummi ya kamata ya tmby tunda alama ya nuna akwai wata a kasa,
“Ba komai ummah”
Ya bada amsa yana murmushi.
“Masha Allah” umma ta fadi tana me rufe taron da Addu’ah, nan kowa ya fara tashi akan zasu hadu wajen aiki on Monday tunda yau Saturday.
••••••
Hura masa ido tayi tace,
“wannan kallon fah? Kasan tunda muka dawo wajen su ummah nasan akwai mgn a bakin ka” murmushi yyi yana jawota jikinsa yace,
“na rasa ta inda zan fara ne”
Tace,
“me?”
“Godiya mana.” Ya bata amsa,
“Shiiii…”
ummi tasa hannun ta abaki tace,
“pls ba wannan mgnr sbd Allah mukayi badan a gode ba”
“Yeah i known but…..”
“plsss….”
ummmi ta fada tana rufe kunnen ta,
“Ohk, Ohk. Naji akwai tarin tmby bakina”
“inajin ka”
ummi ta fada tana kallon sa.
“Meyasa Kuka boyema innar jamila har basu san kinyi kr2 ba?”
Murmushi ummi tayi tace,
“idan ta sani ba zanyi kr2n ba.”
“Meyasa?”
Ya sake jefo mata tmby,
“hmm kamar yadda ka sani mlm sabo kanin mahaifina ne mlm Ahmad, mlm sabo ya hadu da irin matan nan ne marar tsoron Allah,yadda kasan waina haka take juyashi sai ya zama ra’ayinta shine nasa abinda tace shine daidai, to dama ba wani karfine dashi ba, Inna kuma akwai son zuciya, lkcn da iyayena suka rasu sun barmin abinda Allah ya basu, to ya tsone ma Inna ido harta sa mlm sabo ya karbi gadona suka kuma dawo kano da zama cikin gidan babana dan da shi kadai yake zuwa kano ya koma Garko, a haka tana zuga shi har suka cinye abinda aka barmin, tasa ya karbo ni a garko na koma tamkar ‘yar aiki zagi da hantara ba wanda bana gani mlm sabo be isa ya hana ba saidai ma a taru dashi a cimin mutunci sbd yana mugun tsoronta,
Idan muka zauna ni dashi wato idan basa gidan sai yyi ta bani hakuri yace dan Allah na tayashi Addu’ah duk abinda yamin bawai har zuciya bane shikuma tasa kaddarar kenan. Idan naji ya fadi haka sai na daina tausayin kaina nakoma kan nasa, so sai ya kasance a zahiri mlm sabo mugu ne a gareni amma a badini yafi kowa tausayi na dan ni kadai dan uwansa ya haifa ya bari wani lkncn ma har kukan takaicin abinda yakemin yake. To amma ya ya iya? Dole abin sai Du’a’i, to sai ya kasance duk lkcn da muka zauna tare yana bani lbrn yanayin gidan da yake aiki, tun kafin na hadu daku tausayin halin da kuke ciki ya gini a zuciyata har nakejin dama ni wata ce da tabbas na kawo karshen Azzaluman nan masu baqar aniya,
Ana nan haka rana tsaka Mlm sabo yazo gida da sauri Allah yaso a kofar gida ya sameni, cikin sauri yace nahau mashin dinsa mu tafi, nace ina? Yace kedai hau. A takaice dai bamu tsaya a ko’ina ba sai a nijar sbd tun a hanya ya ari motar abokinsa muka dinga bin wata mota ashe ummace a ciki, cikin sahara sukaje suka wurgar, Allah yaso basu ganmu ba, bayan mun isa ya kira wani abokin sa daya sani a nijar nan ya gaya masa bukatar sa shine ya hadamu da yayansa dake bayan gari. A takaice dai muka dauke umma har gidan ya kaimu, bayan komai ya zama settled ya juyo a 360 dan karsu rigashi zuwa gida, ban fada maka ba tsohon driver ne kafin ya fara aikin Gadi.
“Huh..!”
El-bash ya furzar da iskar bakinsa yana girgiza kai yace,
“Tmby ta biyu, Lkcn da aka kawo ki na fuskanci kina cikin tashin hankali, Like kamar bakyason auren, ko kuma nace taya zancen auren ya fada kanki? Ya kikaji da akazo miki da zancen?
Naga kowa yazo saiya dungure miki kai yana miki warning, suraj ma dan iska harda pretending kai mutanen nan kunsha dani a lot.”*EL-BASHEER*
*Saqon Godiya ta musamman ga wa’annan grps din masu bibiyar littafina, Fans din cikinsu masu bina da Addu’ah inajin dadi kwarai Alkhairin Allah ya biku aduk inda kuke Ameeen.*
•HOME OF NOVELS (na xoxo)
•MEYE ASALINA GRP (na mmn ysp)
•MUTUMCE KUWA?
•UMMU HANAN NOVELS
•MUSHA KARATU ( na ybk)
•TAURARUWA (na queen)
•BA UWATA BACE FANS
•ZAINAB NOVELS
•••••••••••
Ga dukkan sauran wanda ban samu sasu ba tabbas sakon ku na isowa gareni Addu’ar da kukemin Allah ya biyaku da mafificin Alkhairi Ameen.
Na
Nuceeyluv😘
63
Murmushi ummi tayi kafin tace, “why are you asking all this questions? I known u perfectly know how your work is, it’s just an acting, dukda dai ban kawo a raina zamuyi aure ba dan har mun shirya aure da wani qaddara ta shigo ciki su jamila suka juyar masa tunani ya koma kanta a lkcn na shiga tashin hankali kam ba karya tunda ni banda sunanka bansan waye kai ba, toh kasan komai Allah ke lamarin sa sai tashi guda ya juya komai time din da haj suwaiba ta nemi mlm sabo ya bada ‘yarsa tayi hakan ne sbd ta qasqantar da abun, a zaton ta kwadayi yasa ya amince mata, batasan kanta ta rufta ba, a time din daya fadamin abinda ke faruwa na razana ssai sbd bansan ya halinka yake ba, bansan ya zaka daukeni ba, amma saiya nunamin wata dama ce dazamu cimma burinmu cikin sauki suraj ma ya karfafa min gwiwa, sannan suka jamin kunne dole nayi hakuri na danne komai nayi acting kamar na shiga damuwa tayin auren kai nafi kowa ma shiga tashin hankali sbd kar su inna su gane ban damu ba tunda kallon hauka suke maka, haka karsu haj suwaiba su fahimci da wata manufar nake zaune su samin ido, and lastly You idan ka fahimci nasan komai bazaka saki jikin ka dani ba shiyasa komai nakeyi kamar bansan komai ba.”
“So har tausayina da nake gani a idon ki acting ne?”
Yyi mgnr zuciyar sa na bugawa kar ace shi kadai yake sonta ita kuma acting take.+
“No”
yaji ta furta a hankali,
“huh!”
Ya saki boyayyar ajiyar zuciya, kafin yaji taci gaba da fadin,
“as i say it earlier tausayin ka ya ginu a zuciyata tun kafin na hadu dakai”
Wani sanyi El-bash yaji a ransa kafin ya matso da fuskar ummi kusa dashi, can kasan makoshin sa yace,
“Do u love me?” Dan wara idonta tayi kirjinta na bugawa so take taji kalmar daga gareshi bawai ya tmbye ta ba, dan haka ta dan maze cikin dauriya tace,
“i don’t know”
“Whatt..?”
El-bash ya fada hankali tashe yace,
“me kike cewa haka? Ko har yanzu kina son wancan mutumin?” Yyi mgnr muryar sa da kaushi ransa na daci sbd kishi, A tsorace ta kalleshi taga ya juye El-bash mahaukaci cikin sauri ta kwace jikinta daga gareshi tana fadin,
“mene kkeyi haka?”
“Tmby ma kike?” Yyi mgnr yana tasowa tsaye jin zuciyar sa kawai yake tana zafi idan ya tuno ummi ta taba soyayya da wani bashi ba, ganin ya taso ta juya a guje tayi hanyar stairs kofar sa ta gani a bude tayi saurin fadawa dakin kafin ta rufe kofar harya tura, bata da wani option na ta qame a tsaye, hakan ya bashi damar kamata ya mannata da jikin bango yana fadin,
“Do u love me?” Cikin karfin hali ummi ta fara dukan kirjinsa tana fadin,
“sbd Allah kai kana sona ne? Do u love me?” Ta maimaita mgnr itama tana tsare shi da ido,
“Yeess I love you, i really love since the first time i saw You”
Yyi mgnr yana kallon cikin idonta hade da aika mata zazzafan sako me wuyar fassarawa, ummi ji tayi kamar an tsunduma ta a Aljanna dan dadi, tun daga tsakiyar kanta har tafin kafarta takejin kallon sa a jikin ta, lumshe ido tayi murya can kasan makoshi tace,
“I love you too”
Tayi mgnr tana bude idonta a hankali hade da aika masa martanin zazzafan kallon da yake mata,
“OMG!”
El-bash ya furta yana me hade ta a kirjin shi, bakinta ya laluma ya fara bata wani hot kiss saiga tsayuwa ta gagaresu,
dukkansu cikin shauki suke hakan yasa tsayuwa ta gagaresu, batare da bata lkci ba El-bash ya daga ummi sai kan lallausan bed dinsa, Anan suka fara juyi kan gadon suna kissing junan su, dayan bayan daya kowanne ya taya dan uwansa cire kayan jikinsa, El-bash hannun sa har bari yake sbd ba karamin dauriya yyi ba 2days tunda yasan ummi be sake yi mata komai ba sbd tausayin ta da yake gashi tanada dauriya, toh da alama ciwo ya gama warkewa dan da kanta yau ummi ke tayashi,
hakan ya sake jefashi cikin shauki da zazzafar kaunarta, bakinsa saman nipples dinta dayan hannun yana murza dayan na fulanin ta a hankali can kasan makoshin sa yace,
“I love you Baby wallahi i Adore you Baby, Baby pls don’t leave i’m All yours really Love you I’m Sure to God!”
Ya fada cikin shaukin madarar kaunar ummi yana sake hargitsa ta.
Ita kanta ummi ya hargitsa mata Tunani, kalaman da yake jifanta dashi har cikin kokon ranta takeji, tanaji a ranta ta cika kasaitacciyar mace, Ranta yyi fari tass dan batasan lkcn da take tayashi komai ba sbd yadda yake jifanta da kalamai,
“Allah yyi maki Albarka, Allah ya biyaki da Aljannah, Oh God! Babynah…..!”
El-bash ya furta cikin matukar shauki ummi da hanzari ta rufe bakinsa da nata sbd yadda yake mata zuba kamar kanya.
*****
Kamar baby haka ya nadota daga toilet, koda yake a toilet dinma saida aka bata lkci kafin ya kyaleta suka fito, gefen gado ya ajeta kafin ya fisge towel din jikinta ya dawo ba komi a jikinta.
“Ahhhh…!”
Ummi ta furta tana kare kirjinta yyinda ta sake dukawa dan rufe cinyar ta,
“Mene?”
El-bash ya furta yana dago ta yyinda yake dariya kasa2 yasan dalilin karar ta,
“pls ka miko min towel”
“No mai zan shafa miki”
Dan dago da fuskar tayi tace,
“kuma sai an cirema mutum towel sbd Allah?”
“Yess you are my baby yanzu na gama miki wanka fa mene za’a boye min?”
Yyi mgnr yana mata gwalo, turo bakinta ummi tayi tace,
“gsky nidai aa kalleka fa kai da towel a jikin ka saini sbd Allah” tayi mgnr idonta na ciko da Kwallah,
“Kema cire”
yyi mgnr yana matsowa gabanta, rintse ido tayi tana fadin,
“pls kar a lalatani” dariyace ta kwacema El-bash kafin yace,
“shikenan bude idonki ustaziya”
“Ahhhhh…….” ummi ta sake sakin ihu tana me jawo blanket ta rufe jikinta da kanta a ciki tana fadin,
“plss mana meye hakan?”
El-bash yace,
“meya faru”
Yyi mgnr yana danne dariyar sa,
“pls ka maida towel dinka ko kasa kaya.”
“Lallema yarinyar nan”
yyi mgnr yana janyo bargon data rufe kanta yace,
“ko ki taso ki shafamin mai nima na shirya ki, ko na maimaita.”
Da sauri ummi ta dago kanta idonta a rufe tace,
“matso na shafa maka ni na hutar dakai basai kamin ba”
“kinma isa yarinya” ya fada yana kwantawa kanta yace,
“aha second round tunda baki shirya ba”
Ba yadda ummi ta iya haka ta tashi tana kauda kai ta shafa masa cream, shi kuwa sai dariya yake mata kasa2,
“haka kurum mutum ko kunya yazo yana tsaye gabana.” Ummi tayi mgnr tana cuno baki. Matso da ita yyi ya cike sauran gab din gabansu yace,
“maimaita abinda kikace yanzu ki sake wanka.”
Dif ummi ta dinke bakinta sbd a yadda suke tsayen ma babu kaya gashi ya hade jikinsu ji tayi jikinta na amsawa.EL-BASHEER*
Na
Nuceeyluv😘
64
“Matsoraciya” El-bash ya furta yana dariya, “eh naji” ummi tace tana murguda masa baki.
****
Bayan duba su haj suwaiba an cire musu bullet har anyi dressing wajen, yyinda sakina kuma ta samu rabon ciki inda hankalin ta ya tashi matuka, cikin tashin hankali haj suwaiba ta kama sakina tana fadin,
“wanne dan iskan ne ya dirka miki ciki?”
Ba wni alamar tsoro a ranta tace,
“Rabe”
“Whatttt….?”
Haj suwaiba ta fada tana dafa kai,
“yau na shiga uku na lalace ya akai duniya take neman juyamin baya ne?”
Haj suwaiba ta fada cikin kuka tan me dora hannu akai,
“mlm ki mana shiru”
wani ya leko ya musu mgn sbd ihun da take, ana haka ma sai gasu El-bash, sawa akai aka fito dasu, duk kunya da dana sani ya lullube su, haj suwaiba basu sake shiga rudani ba saida suka ga Ummah tsaye gabansu, a gigice ta kamo sakina ta boye bayanta, ita kuwa sakina jikinta ne ya fara bari tunda ita a matsayin ta mutu ta sani, Rabe kuwa kasa tsayuwa yyi ji yake kamar a tsaga kasa ya shige haka yakeji musamman daya ga har Abba a wajen, Da murmushi umma ta karasa gabansu tace,
“toh ya kukaga ikon Allah? Kun dauka na mutu ko? Koda yake baku manta wannan ba ta nuna ummi dake gefen El-bash, Lkcn da kukai watsi dani Allah ya turo min su, dake Allah shi yake hukuncin sa harta zauna tsawon lkci tare daku baku san tanada masaniya da mummunan nufin ku ba, hmm..” Ummah ta tabe baki,
“Suwaiba da Rabe kenan a har kullum ku dinga tunawa hassada ga mai rabo taki ce”
tayi mgnr tana murmushi ta koma gefe,
Abba ya matso yace,
“suwaiba tun bayan barina kasar nan na tsinke igiyoyin aurena dake, koda can banyi ra’ayin auren ki ba Qaddara ce ta shigo ciki, dan haka indai duniyace yanzu kika fara ganin yadda take juya miki baya, kai kuma Rabe hmm…..”
Abba ya sauke ajiyar zuciya ransa na zafi, Dama akwaishi da zuciya amma tun a gida ummah ta tause shi, Kwafa yyi dan ji yake kamar yyi kwallo dashi, can yace,
“irinku kune masu sarewa mutum gwiwa akan taimako, kanaso ka taimaka amma sbd gurbatattu irinku wasu keqin yi, Rana dubu ta barawo, Rana daya tak tamai kaya Sbd Allah nayi maka sannan a dalilinka bazan daina taimako ba, kai kuma abinda kamin na barka da Allah wanda ya tsareni daga sharrin ku.”
Yyi mgnr ransa na baci, zai juyo kenan yaji an dafa masa kafa cikin yanayi na nadama, Rabe yace,
“na rokeka da girman Allah ku yafemin karka barni da Allah, wlh iya lefin dana aikata ma na daukar hakkin wasu da wanda basuji ba basu gani ba na cutar dasu na kashe rai dayawa na lalata farincikin wasu shi kadai ma masifa ne a gareni bare yanzu kacemin baka yafe ba ai na shiga uku, dan Allah ka tausayamin Alhj ku yafemin Dan Allah”
yyi mgnr yana kallon su daya bayan daya. Su kansu su haj suwaiba dukawa sukai suna neman gafara.+
Kusan few seconds Ba wanda yace komai, can Abba yace,
“Allah ya yafe mana gaba1”
yana gama fadin haka ya fice, Zuciya me rauni ummah kanta girgiza kai kawai tayi ta tafi, sai ya rage suraj, El-bash da ummi, ummi ta kalli El-bash da fuskar sa take a hade tun dazu tayi sa’a kuwa sun hada ido, ta kama hannun sa ta matsa a hankali kafin tayi masa signal da ido tanaso taji shima ya yafe, ita yake kallo gefen zuciyar sa na sanyi yyinda dayan side dinta ke zafi idan ya tuna abinda sukai masa, Sake matsa hannun sa tayi da dan karfi ya dawo daga duniyar tunanin daya tafi, kallon su sakina yyi ta zuba musu ido kuwa kamar ta cinye su hardai data ga sunyi kyau kuma sun dace da juna, sake hade fuska yyi kafin ya girgiza kai shima, be bata lkci ba yaja ummi suka fice.
Suraj ya matso wajen su suma, ya kira sauran jami’an yace a hade su da sauran members irinsu Mudi, Dama su kadai aka kira tunda abin na family ne sauran kuma na hukuma. Haka aka tisa keyar su zuwa wajen, haj suwaiba da sakina na kukan nadama.
~~~~~~
Direct kotu aka wuce dasu inda koti tayi zaman farko dasu tun daga wajen aka samu kwararrun shaidu babu bata lkci Alkali Ya fara karanto hukuncin su.
STORY CONTINUES BELOW

Alkali ya gyara zaman glass dinsa kafin ya karanto cewa dukkanin su za’a musu hukunci kisa ta hanyar rataya sbd dukkansu sun kashe rai bama daya ba, Ita kuma sakina zatayi shekara tara a gidan yari tare da horo me tsanani idan ta haihu sbd taimako data bayar wajen son salwantar da ummi da suka so yi.
Nan fa ‘yan HSK Association suka fara kururuwa mazansu da matansu suna masu nadamar abinda suka aikata, Daya bayan daya ake fita a cikin kotun har su ummi suma sun shiga mota,
Shiru ummi tayi hade dayin tagumi, El-bash ya juyo a karo na barkatai yana kallon ta ya kamo hannun ta ya matsa a hankali, dago kanta tayi tana kallon shi, A nutse yace,
“ya naganki so silent haka? Akwai wani abu ne?”
“Hmmm….”
Ummi ta sauke ajiyar zuciya a hankali tace,
“Abinda nagani ne ya sani sanyin jiki da shiga tashin hankali” El-bash na juya steering yace,
“Me yafi saki laushi haka?”
Dan lumshe ido tayi kafin tace,
“hukuncin da aka yanke musu ne naga kowa na ihu yana kururuwa lauyoyi na jansu suna kuka sai ya tunamin da ranar gobe Alqiyama Naji cewa hukuncin duniya kenan suna wannan ihun ina ga kuma ace a filin kiyama mutum yake? Ace gashi an maka hisabi kana da tarin zunubi haka mala’iku zasu jaka su saka a wuta cikin umarnin Allah, Yah salam!”
Ummi ta karasa mgnr muryar ta na rawa sbd tashin hankalin da take hangowa. Dan sake matsa hannun ta El-bash yyi yace,
“mgnrki gakyne baby, shiyasa a kullum akeso ka aikata Alkhairi da rokon Samun Rahamar ubangiji Amma kam abinda akeyi a duniyar nan ya qazanta wasu tabbas sunsan abinda suke aikatawa zunubi ne amma sai kiga ko a jikinsu Hmm Allah dai kawai yasa muyi kyakkyawan Karshe dan wata shari’ar sai a lahira.”
“Tabbas hakane” cewar ummi tana me goge hawayen ta.
Gani tayi ya dauki hanyar unguwar su, da sauri ta kalleshi taga ya mata murmushi, Itama murmushi tayi tace,
“rabona da gida tunda aka kai maka ni” Tayi mgnr farinciki na cika zuciyar ta dukda batasan irin tarbar da zata samu ba. Sosai El-bash yaji dadi dayaga farinciki bayyane fuskar ta sabanin da datake a cunkushe, a haka suka karaso kofar gidansu, dadan saurin ta takama kofa zata bude El-bash ya riko hannun ta,
“baby irin wannan saurin haka ai saiki barar min da kayana”
cikin rashin fahimta tace,
“wanne kayan?”
“Ajiyata mana kika sani ko nabar ajiya jiya?”
Hararar wasa tayi masa ta kwace hannun ta ta fito, dariya yyi kawai yana me dora kansa a steering.
Sallama ummi tayi daidai lkcin Mlm sabo ya fito a bandaki rike da buta,
“a’a ummi kece yau a gidan”
ya fada cike da fara’a, ummi da murna itama ta duqa tana gaishe dashi kafin tace,
“ai tare muke”
ta fada cikin jin kunya,
“a’a kuma kika barshi a waje? Tashi kice ya shigo”
yyi mgnr yana kwalama inna kira,
“Saudee…”
“gani mlm naji kamar kana mgn sama2 waye yazo?”
“Ummi ce”
ya fada da fara’a,
“Ummmi?”
Inna ta fada tana zaro ido. Daidai lkcn kuma su ummin suka shigo,
“basu taburma mana”
mlm sabo ya fada ma inna, inna bata taba ganin El-bash ba wannan shine karonta na farko, kallo daya tayi masa ta shiga hankalin ta wani irin shakkar sa ta darsu a ranta, ko karasa mgn mlm sabo beyi ba ta jawo taburma tana washe baki,
“lale marhababu ashe manyan baki ne a gidan”
Inna ta fada tace,
“bismilla ku zauna” zama su kayi duk farinciki ya lullube ummi taga canji wajen inna, Suna gaisawa saiga jamila ta shigo bagazam2,
“Laaaa Ummi yau da mahaukacin kike tafe?”
Jamila ta fada tana kama baki,
“yauwa inna kin ganshi ko ke kince yana hauka? Wlh kamar me lpy”
Haka kurum inna taji tsoro ya kamata sbd abinda jamila take fada, cikin azama ta kamota tace,
“ke meye haka zaki mana shirmen naki koh?” Inna ta fada tana mintsinin jamila gefe daya kuma tana washe baki hade da fadin,
“sai kunyi hakuri fa shirme ne da ita kema ummi kinsan halin rashin hankalin ta ko”
dan murmushi ummi tayi yyinda mlm sabo ya girgiza kai kawai, El-bash yyi gyaran murya kafin ya fara mgn,
“Inna kune bakuda lbri amma nikam ba mahaukacin gske bane asalima ni jami’in tsaro ne na sirri yanzu haka ma daga kotu muke an yanke ma mutanen da nayi hauka sbd dasu hukuncin kisa”
a gigice Inna ta furta,
“mun shiga uku kai yaro Allah yasa ba kashe mu muma za’ayi ba”
ta fada bakinta na rawa, jamila kuwa kusan suman zaune tayi hankalin ta a tashe ta kamo hannun ummi,
“dan Allah ki yafemin abinda nayi miki karkisa ya kashe ni nima wayyo Allah”
ta fada idanun ta na kawo ruwa,
“Sabo ka taimaka ka nema mana gafarar ummi wlh bazan sake yi mata komai ba mun tuba”
Inna ta fada itama kamar tayi kukan.
“Ko bakuce ba ai na yafe muku inna wlh ban rikeku a raina ba, banda wasu ‘yan uwan da suka wuce ku saidai fatan Allah ya yafe mana gaba1”
“Mungode kinji” suka fada a tare, kafin inna ta kalli El-bash,
“yaro kaji ta yafe mana ko? Dan Allah karka hadamu da hukuma”
Inna ta fada a tsorace, dariya suka bashi yadda duk suka gigice lkci daya, mlm sabo kam dan kallo ya koma, El-bash yace,
“tunda ta yafe muku to kun tsira sai a kiyaye gaba”
“ai Insha maka Allahu anyi na farko anyi na karshe ko kallon hadarin kaji bazai hadamu da ita ba”
“dakyau”
El-bash ya fada yana tafa hannu,
“Toh Amma dan nan meyasa ka zabi zama mahaukaci tsawon lkci haka?”
Inna ta tmby da dan shakku a tattare da ita, El-bash yyi murmushi kafin ya fara bata bayani tiryan2 har kawo yanzu da suke zaune.
“Tabdin ashe mu nafila ne zunubin namu” inna ta fada tana dora hannu akai,
“Lalle na yadda zakaran da Allah ya nufa da cara……”
tayi mgnr cikin yanayi na nadama sbd yadda taji ummi har tayi kr2 basu sani ba, duk yadda taso ummi ta wulakanta a idon duniya ‘yarta jamila kuma tauraruwar ta haska Allah beso ba domin abinda ya kaddara shi yake faruwa bawai abinda bawa yyi ra’ayi ba, duk namada ta shigesu nan suka farga daga mummunan mafarkin da suke. Mlm sabo yaji dadi kwarai dayaga Nadama sosai a fuskar su, ita kanta ummi har wani sanyi takeji a ranta, kazalika El-bash ya fita shiga farinciki dan Alkawari ne yyi duk abinda zai sanyata farinciki matukar be kauce shari’a ba to zai zama kan gaba wajen tayata.
Bayan tattaunawa da neman yafiya anan mlm sabo yyi musu wa’azi me ratsa jiki, saida suka shafe sa’o’i suna zaune kafin El-bash sukai shirin tafiya tare da Alkarwanta Ummi zatazo harma suje can danginsu Garko.
••••
Lkcn har yamma tayi ummi ta maida hankalin ta kan El-bash da yake driving a hankali tace,
“Thanks you”
“For what?” El-bash ya juyo yana tmbyr ta,
“Everything”
“You deserved it, even more…”
Yyi mgnr yana daukar wata hanyar, Ummi tana murmushi tace,
“la’asar fa yyi amma naga kai wani hanya kkebi ina kuma zamu?”
“Shiiii…”
El-bash ya sa yatsan sa a baki a hankali yace,
“sace ki nayi” Wata bazarar dariya ummi ta saki tace,
“ka manta ne? Bana sacuwa”
ta karasa mgnr da dariya, shima dariya yyi yace,
“tab baby saura kiris ki fasamin kai da bullet ko”
“hhhh…”
ummi ta sake dariya har tana tafa hannu tace,
“Action…🤙🏻,”
Tayi mgnr tana gwadawa da hannun ta daidai lkcin kuma El-bash yyi parking gaban wani gate, kai da ganin yanayin gate din kasan naira ta jiku a jikinsa bare akai ga bude gidan, da sauri ummi ta juyo zatayi mgn taga yasa yatsa a baki alamun tayi shiru, muqut ta hadiye mgnr ta sannan ta zubawa sarautar Allah ido,
Bude mata kofa yyi ya kamo hannun ta, a haka suka karaso gaban gate din El-bash ya tura da hannun sa daidai lkcin aka fasa balloons hade da sakar musu ihu ana tafi,
“Happy 1yr Anniversary!”EL-BASHEER*
*Ina masoya El-bash? Na lungu dana sako, WhatApp fans a Facebook? Ku matso kusa domin yau page din naku ne, Ga duk wanda yake bibiyar Novel dinnan har zuwa yanzu Sakon jinjina ne a gareku, EL-BASHEER na muku fatan Alkhairi a duk inda kuke🤙🏻*
Na
Nuceeyluv😘
65
“Wow” ummi ta furta da murmushi, a saitin kunnen ta El-bash ya rada mata, “welcome to our new home” ya fada yana kashe mata ido daya hade da murmushi, “OMG!” Ummi ta furta tana me rungume El-bash cikin farinciki,
“love birds sai a bari mubar gidan ko”
suraj ya katse su Aysha na gefen sa tana murmushi dan sun birgeta hakama sauran frnds din su suraj, dariya aka sakar musu hakan yasa ummi taji kunya tana me sunne kanta kasa, El-bash ya harari suraj,
“Ka samin bby taji kunya dan sa ido kawai”
“daga fadar gsky” Aysha ta amshe,
“au bayansa kikebi koh?”
Suraj yace,
“kaga mlm magrib na matsowa muje a gudanar da komai”
nan suka isa cikin farfajiyar gidan da aka qawata ta, bayan gaishe2 nan akaci aka sha cikin murna a hankali kowa kuma ya watse tare da musu fatan zaman lpy nahar abada. Ssai kuwa ummi sun tsinci kansu a farinciki marar misaltuwa.
+
Kallon yanayin parlon take kai abun ya birgeta da gani komai sabo ne a gidan, El-bash ne ya rungumo ta ta baya saitin kunnen ta yace,
“Ya kikaga tsarin wajen? Komai yyi daidai ko a canja?”
Juyowa ummi tayi tana kallon shi tace,
“duk wannan abubuwan nace a canja?” Ta fada da mmki dan ita har santin kayan parlon take sbd tsaruwa da kyau,
“Girman ki ne princess”
murmushin farinciki tayi ta rungume El-bash tana fadin,
“I love you Bae.”
“Love you more baby”
El-bash ya fada yana cirata sama nan yyi hanyar stairs da ita.
•••••••
Kafin wani lkci tuni an rushe gidan mlm sabo an tsantsara masa na gani na fada sai kace gidan Alhji, koda yake ya kusa zama Alhjin tunda wannan layyar suna sa ran dasu za’ayi haj bisa kyautar Abba, yyi godiya harya rasa abin cewa, sukam fadi suke duk abinda sukai masa basu biyashi ba, Wani tafkeken shago El-bash ya budema Mlm sabo a kwari, shagon da ganin girman sa ya lodi dukiya me yawan gske, mlm sabo har hawayen farinciki yyi su kansu su inna abin ba’ace komai rayuwa ta canja sai sam barka sai matsala daya haryau babu manemi gun jamila, hakan yasa ummi ta bada shawarar ta shiga makarantar yaki da jahilci kuma suka amince harma da islamiyya ta hada.
****
Gidan Abba yasha gyara sosai ya zamana ummah ce kadai a gidan sai sabbin ma’aikatan gidan da aka kawo mata da sabon me gadin su, tsuhuwar soyayyar su suke rakashewa da Abba abinsu cakwai.
~~~
Fitowar su wanka kenan, El-bash ya jawo cream yana fadin,
“yau dai nine first tsaya na shafa miki” ummi tana dariya,
“kai Bae Allah wayo kkemin”
“Dgske Baby”
ya fada yana shafa mata a fuska, Da sauri ummi ta ture hannun sa tana toshe hanci,
“meya faru?”
Ya fada yana binta da kallo, wani abin ta jawo tana goge cream din daya shafa mata da sauri2 a hanzarce ta mike zata tashi El-bash ya kamo hannun ta yace,
“wai menene?” Cream din hannun sa ta nuna masa tace,
“wari”
“wari kuma?” El-bash ya furta da mmki, yasan ba cream din da takeson kamshin sa kamar shi, daidai hancin ta yakai cream din yace,
“Shinshina kiji fa” yyi mgnr yana kai mata dab da hanci, Ummi ji tayi cikin ta ya wani irin juyawa cikin azama ta hankadar da cream din gefe ta kwace daga hannun El-bash, ta nufi toilet, biyota yyi da sauri daidai lkcn yaga tana ta kwarara Amai, hankali tashe yace,
“baby anya lpyrki kuwa?”
Ya fada yana wanke mata baki, saida ta dan samu nutsuwa ta kama kanta tace,
“kaina kemin ciwo kawai fa, ba wani abu bane sai cream dinnan da yakemin wari harya sani amai.”
“No baby we need to see Doctor” El-bash ya fada yana kama hannun ta, kayanta ya sanya mata shima ya saka kafin ya dakko ta hade da key din mota suka fito,
STORY CONTINUES BELOW

direct hospital ya kaita cikin few minutes dan babu nisa, gwajin farko da akai ma ummi ya tabbatar tana dauke da cikin wata uku, habawa kuzo kuga murna wajen El-bash har yarasa ina zaisa ummi yaji dadi.
Ummi har mmkin murnar El-bash take koda yake ba abin mmki bane idan ta hango zunzurutun kaunar da yake nuna mata, bata dauke ga mmkinta ba saida taga ummah da Abba suna murna kamar su maida ta ciki, ita har kunyama taji sbd El-bash daga hsptl can ya wuce dasu, Ummah cewa take,
“husnah ki saki jikin ki aini mamanki ce, gayamin me kikeso? Me kike sha’awa?”
Ummi saidai ta rufe fuskar ta kawai, El-bash dake gefe yace,
“Yauwa ummah naga kwanan nan tasa kilishi a gaba tanaci, idan akwai ya kamata a kawo maybe taci”
ya fada yana dariyar ummi data harareshi a sace,
“Aiko baza’a rasa ba bari na duba”
ummah ta mike, Tana fita kuwa ummi takai masa bugu a kirji tana fadin,
“wlh Bae kadau bashi”
dariya ya mata hade da gwalo yace,
“ai yanzu na gano sirrin haba no wonder kiyita cin Kilishi har bakya gajiya da tauna ashe kayana ne yake girma”
ya fada yana shafa marar ta,
“Allah zanyi kuka”
ummi ta fada cikin shagwaba,
“oh sorry my sweety na tuba”
ya fada yana kama kunnen sa, suna haka akayi knocking ummah ta aiko da kilishi me yawa, ummi tun kafin a bude taji yawunta ya tsinke, yarinyar na fita, ba bata lkci ta jawo shi gabanta tanaci har wani lumshe ido take dan dadi. El-bash kam wayarsa ya dakko yana mata vedio batare data sani ba sai kallonta yake cikin sha’awa da birgewa.
°°°°°°°
Suraj ya miko masu IV yace, “gasu nan an bugo” Su ummi suka dauka suna gani, IV din yyi kyau dama anata shirye2 bikinsa da aysha yanzu duka saura 2weeks bikin.
“Kai ammafa sun hadu”
ummi ta furta tana murmushi, El-bash yace,
“frnd kace saura kiriss..”
ya fada yana dariya,
“Insha Allahu” suraj ya fada yana ci gaba da fadin,
“badan unborn dinmu ba ai saikun cashe sosai”
Dariya sukai gaba1 ummi tace,
“karka daga masa kafa shi zai iya ko dambe ne”
“kuttt….”
El-bash ya fada,
“wato ke kin samu salama ko”
suraj yace,
“ai dole ma ka ware”
El-bash yyi murmushi,
“idan ban ware a bikin frnd dina ba a’ina zan ware”
“oho maka dai” suraj ya fada yana dariya hade da shirin tafiya, har bakin mota El-bash ya rakashi kafin, ya dawo.
Ummi na zaune inda ya barta, yana zama ta shige jikinsa dan idan akwai abinda tafiso to turaren daya saka a jikinsa, shiyasa kullum take manne dashi kamar mage ta bangaren El-bash kuwa gaba ta kaishi dan a wayance yana rakashewa ne abinsa, ko akan kujera yanzu sai su lula duniyar maji dadi.
~~~~~
Biki yyi biki, inda Ango Suraj da amaryar sa aysha suka rakashe, El-bash ya taka rawar gani sosai a bikin har suraj ya rasa bakin godiya El-bash cewa yake amintar su ta wuce a kirasu abokai sai ‘yan uwa na jini, tabbas hakane domin kowa ya shaida hakan a fili da badini aminai ne na gske, ita kanta ummi ba’a barta a baya ba dan tayi nata bajintar sosai a bikin, zumuncin su ya sake karfi da Aysha, abin dai sai sam barka.
*****
Bayan wata tara ummi ta haifo kyawawan twins dinta duk maza akasa sunan Abba da Abban ummi, wato Usman da Ahmad ana musu Alkunya da Abulkhairi da Ameer, Ranar suna Naira tayi kuka ummi taga kauna a kowanne bangare lkcin aysha itama tana dauke da tsarabar cikin ta, suma lpy lau gwanin sha’awa suke zaune da suraj dinta, Yara bulbul dasu kamar ka sace su ka gudu sun tsatso kyau ta kowanne side.
*****
Bayan ummi ta zubar da wanka, El-bash yazo mata da Albishir me tsoka, nan ya sanar mata manyan stores daya bude mata inda aka zuba kayan kitchen da cosmetic na mata wannan harda gudumawar Ummah a ciki sbd kara karfafawa ummi Business data karanta, bazai tafi a banza ba dole a amfanu dashi, Rasa bakin godiya ummi tayi sai Addu’ah da fatan gamawa lpy take musu, tun daga lkcin liyafa taci gaba a gun ummi nan El-bash ya fara rakata kasashen duniya tana saro kaya bayan honeymoon da sukaje wata uku da suka wuce nan suka bar twins a hannun ummah, kasa ta karshe da suka ziyarta itace kasa me tsarki daga nan suka dawo gida aiko a wannan tafiya an sake samun rabo, shiyasa ma kafarta kafarsa wajen sarin kaya sbd tsaro.
Sosai El-bash ya samu Karin girma yyinda suraj ya zama mataimakin sa a koyaushe dai suna tare cikin aminci.
~~~~
A bangaren su haj suwaiba kuwa tuni aka yanke musu hukuncin su tun lkci beyi tsawo ba, ita kuwa sakina sbd firgici da shiga tashin hankali yasa cikin jikinta ya zube tun daga lkcin ta fara karbar hukuncin ta na horo me tsanani da zaman shekara tara gidan yari, tayi dana sani yafi a kirga.
•••••
Bagaren mlm sabo ya koma Alhji sabo, cikin rahamar Allah kasuwa tayi Albarka da wuya ka shiga kwari kayi tmby ba’a nuna maka shagon sa ba abindai sai sam barka dan tuni suka dinke da mutanen Garko yanzu suna zumunci sosai, Inna ta koma haj dan Itama ta sauke, jamila an kara hankali nan ta samu wani mutum yace yana son ta saidai yanada mata uku da yara itace ta hudu, cikin farinciki ta rungumi auren dan shine kaddarar ta ita kuma, ta dandana zawarci babu dadi fatan ta duk wata bazawara Allah ya kawo mata miji na gari dan shine rufin asirin ka.
°°°°°°°
Shekara kwana, hakan ta kasance domin Alhaji El-basheer ya tara iyali da hajiya Asma’u Ummi/Husnah, yaransu hudu, Abulkhair da Ameer an zama samari dan har suna shirin zana WAEC, sai Fatima anace da ita imaan tana Jss3 yanzu, sai kuma Little Suraj yana Js1 yaran ba karamin ji da kansu suke ba sbd yadda suka tsatso kyau ta kowanne bangare ga naira tayi male2 a jikinsu. Shi kansa Suraj Ya tara yaransa uku, Shahid, Al’amin, Surayya. Abin dai sai Masha Allah.
Tsantsar So da kauna shine kullum abinda El-bash da ummi suke nunama junansu, Duk wanda ya gansu saisun bashi sha’awa, kuma duk wanda ya musu kyakkyawan duba zaisan Lalle Ummi tayi dacen gwarzon namiji me nuna tsantsar kulawa da tarairaya kamar *EL-BASHEER*
*ALHAMDULILLAH*
_Dukkan Godiya ta tabbata ga Allah S.W.A daya bani damar rubuta wanna Littafin, ina rokon Allah kurakuren da nayi a ciki Allah ya yafe min, sakon da nakeson isarwa ya samu duk wanda ya fahimci littafin Ameen