WANNAN RAYUWAR CHAPTER 5

 WANNAN RAYUWAR CHAPTER 5

Fauziyya na shiga gida ta fada dakin ta ta kara fashewa da wani kukan lallai ta bata rayuwar ta shin meyasa bata amshi kaddarar da ta same ta bayan afkuwar komai ta kona ga Allah ba sai ta cigaba da sabawa Allah.

“Innalillah wainna illahir rajiun! Shin da ba mutu ina mai aikata zina fa? Lallai da na kasance asarar ra nazo duniya a banza na koma a babu. Na kasane yar wuta.”

Ido ta runtse tana mai daga hannun ta sama tana fadin

“Astagafurullah wa atubu’illaik! Ya Allah ka gafarta min ka yafe min ka yafe min dan darajar Annabi Muhammad (SAW) Allah ya yafe min ka shirya ni ka yafen min! Astagafurllah! Astagafurullah!! Astahagafurullah!!!”

Abinda tai tayi kenan dan sam bata cikin haiyacin ta tsoron duniya da tsoron azabar Allah ta sa ta shiga tashin hankalin da bata taba shiga ha. Tana halin nan kanin ta Al amin ya shigo mata da kayan da ta bari a soro ko ta kansu bata bi ba. Bandaki ta shiga ta dauro alwala sannan tazo ta hau Kan sallaya tana mai kai kukan ta ga rabbi samawati wal’ard akan ya yafe mata ya jikan ta ya shirya ta.

Haka tai tayi tana mai fadin astagafurullah har akai magarina ta mike tayi a sujadar ta ta jima tana kai kukan ta ga Allah akan Allah ya yafe mata ya shirya ta ya tsare ya’yan al umma. Tana idar wa ta dauki alkur’ani ta fara karantawa ko ta samu sauki yadda zuciyar ta ke mata azaba na radadin halin da ta tsinci kan ta a ciki. Wato ita tata kalar kaddarar kenan? To Allah ya bata ikon cinyewa ya shirya.

Ranar bata kara samun nustuwar ta ba sai kai kukan ta ga Allah da take tana danasani da nadama akan abinda ta aikata da kuma yin alkawarin ba zata sake komawa halin da ta shiga a da ba.

(Toh Allah yasa Fauziyya)

******************************************************************************************

Ahmad ne zaune a gaban Dadyn sa. Dady ya kalle shi yace

“Yaya dai Ahmad?”

Kan sa a kasa ya shagwabe fuska kamar zai kuka yace

“Dady ji nayi wai Momy ta tsaida biki na?”

Dan Murmushi Dady ya saki yace

“Haka ta fada min!”

Hannun Dadyn sa ya kama yace

“Please Dady kayi wani abu akai wallahi sam ni bana son Hannah akawai wacce nake so!”

Kallon sa Dady ya tsaya. Idon sa ne ya kawo ruwa, Dady yace

“To menene na kuka kai fa namiji ne mijin mace hudu ba zan ce a’ah akan maganar aure nan da mahaifiyar ka ba zance kai mata biyayya amman ka sani nima zan maka abinda kake so domin nima kana min biyayya. Kaje ka fara shirin bikin ka da Hannah bayan auren ku ni nai maka alkawaron zan shige maka gaba ka auri wacce kake so kaji.”

STORY CONTINUES BELOW

Kai ya gyadla yace

“Yanzu kai mata biyayya kamar yadda ka saba Allah maka albarka.”

“Amin Dady nagode!”

“Yaushe zaka tafin ne?”

“Ranar Monday zan koma!”

“Ok Allah ya kaimu!”

“Amin!”

Tashi yayi ya nufi bangaren Momy. A falo ya same ta tana kallo shiga yayi ya zauna a gefen ta ya daura kan sa a kafadar ta.

Murmushi Momy ta saki tace

“Ka dai kusa girma ka daina wadan nan abubuwan kai ba Auta ba ko Basma bata abinda kake!”

Fuska ya shagwabe tace

“Me kake so to?”

Kai ya girgiza mata. Ajiyar zuciya ta sauke tace

“An saka ranar bikin ka fa kai da Hannah!”

Kai ya gyada yace

“Allah kaimu lokacin!”

“Amin Ya Allah. Lokacin kadan ne dan haka yaushe zamuje a hado lefe?”

“Haba Momy har sai anje dani kawai in kin samu time ki shirya kije amman ni jibi Monday ma zan koma kuma kinsan ban da time na cinye hutu na na wannan year din!”

“Alright ai ba damuwa.”

Sallamar Basma da Hannah ce ta sa ya fasa maganar da zai yi.

Basma sanye da doguwar riga tayi rolling kan ta ita kuma Hannah ta saka riga da siket sun kamata sai dan karamin mayafi da ta yafa daga kan ta zuwa kafadar ta duk kirjin ta da bayan ta a waje ga kayan sun kamata.

Tsaki ya saki yace

“Daga ina kuke?”

“Kasuwa muka je!”

Ido ya zaro yace

“What a hakan?”

Ya fada yana nuna Hannah da hannun sa. Momy ya kalla yace

“Am Momy in an tashi hado lefe kar a sake a saka mata mayafi ko daya, sannan ki mata magana ban son irin wadan nan shigar tana fita maza na kallon ta a haka”

Yana gama fadin haka ya tashi ya fice ran sa a abace. Momy ce

“Hannah kina kiyayewa kinga Yayan ki bai son wannan shigar kinji “

Baki ta turo tace

“To Momy menene da shigar tawa dan Allah.”

Hararar ta Momy tayi tace

“Tin da yace baya so ba shikenan ba sai ki daina. Gashi nan yace sai hijabai za a saka a lefen ki ai.”

Idon ta ne ya kawo ruwa tace

“Momy dan Allah ki bashi hakuri.”

Ido Momy ta zaro tace

“Ai kema kina da baki je ki bashi hakuri kila ya sauko dan kinga yadda ya hau sama.”

Mikewa tayi ta fice tabi shi part din sa. Yana shiga ya shige dakin baccin sa ya cire kaya ya fada bandaki.

Tana shiga taga baya falo wannan yasa tayi Bedroom din sa. Baya ciki sai motsin ruwa da taji wannan yasa ta samu gefen gadon ta zauna. Bai jima ba ya fito daure da towel a kugun sa. Mikewa tayi ta matsa kusa da shi tace

“Please Yaya kayi hakuri kar a siyon Hijabai please!”

Wani kallo ya watsa mata yana mamakin yadda sam Hannah bata da hankali yanzu ta shigo ta gansa a haka amman ita ko a jikin ta. Tsaki ya saki yace

“Fitar min a daki nonsense!”

Zatai magana yace

“Nace get out ko?”

Da yadda yai maganar dole yasa ta tsorata ta fice a guje tana kuka. Tsaki ya saki ya kintsa sannan ya koma falon sa yana aiki a system din sa.

*****************************************************************************************-

Yau wata cikin ta goma sha a yadda take lissafi amman ba haihuwa ba alamar ta. Duk ta rame tayi fari fat da ka kalle ta sai ta baka tsoro ba kiba sai kato ciki wanda har jinyar ta yake.

Tafi sati bata da lafiya domin cikin ma daga jiya zuwa yau sam ya daina motsi da kyar ta mike ta nufi dakin Alhaji Kasim. Ya fito kenan zai fita. Yana ganin ta ya hade fuska yace

“Lafiya!”

STORY CONTINUES BELOW

Baki ta cije saboda yadda take jin ciwon tace

“Alhaji asibiti nake son zuwa fa. Ciki nan har ya wuce watan haihuwa!”

Wani kallo ya watsa mata yace

“Dan ya wuce watan haihuwa shine me? Kar ki matan wasu shekarau ake haifar su. Kuma kila ma lissafin naki ne ba dai dai ba.”

“Haka ne Alhaji amman wallahi daga jiya zuwa yau ko motsi cikin bayayi nima da ka ganni wallahi duk ban san me yake min dadi ba.”

Ta karasa maganar da kyar tana rike bayan ta.

“To langwai ni kam ban taba aurar mace irin ki ba langwai. Ke tin da na aure ki ko amarcin wata banci ba kika samu wannan cikin tin daga lokacin kuma me na kara sama a wajen ki sai dan ban zan laulayi. Nayi dana sannin aurar ki, wai ni nan naga yar fulani ashe haka kuka langwaye ai dan ba kara ni kam.”

“Dan Allah Alhaji ka bani kudin mota da na magani dan wallahi ba zan iya zuwa a kafa ba.”

“Ban dashi.”

Ya fada yana janyo kwandon maganungunan sa ya debo mata wasu sun kai biyar ya bata yace

“Ga wannan kisha Allah ya kara sauki. In bai daina ba in na dawo na kara miki wasu.”

Hannu ta saka ta amsa, ya fice tabi bayan sa tana goge hawaye. Fauziyya da ta fito daga daki taga Antyn ta a goge hawaye. Kai ta girgiza ta durkusa tace

“Ina kwana?”

“Lafiya!”

Yai gaba tace

“A dawo lafiya!”

“Allah yasa.”

Ya fice.

Mikewa tayi tayi dakin Antyn ta ta dan ita har ga Allah mantawa ma take da ita saboda halin da ta shiga itama yan kwana kin nan.

Zaune ta same ta cikin ma ya zauna tana goge hawaye tare da cije baki.

“Lafiya Anty ko jikin ne?”

Fuska ta ya mutsa dan yadda take jin jiki tace

“Debon ruwa nasha maganin nan.”

“Wane magani ba dai Baba ne ya baki ba?”

“Shine ya bani naje na fada masa zani asibiti shine ya bani magani.”

Kai ta girgiza tace

“Ba zaki sha ba Anty! Wai Baba likita ne da zai na baku magani kuna sha.”

“Fauziyya in ban sha ba ya kike so nayi?”

“Bari nazo muje Asibiti Anty wai cikin nan anya ma bai wuce lokacin sa ba.”

“Hmm ya wuce man. Amman Alhaji yace wai wasu sai sun shekara suke haihuwa.”

Mikewa tayi tace

“Baba kenan ko dan kar ya baki kudin zuwa asibiti ma ai ya fadi haka. Ina zuwa!”

Ta mike ta fita ta jima ba ta dawo da jaka da hijab a jikin ta. Tace

“Taso Anty an samo mana Napep!”

Ita ta taimaka mata suka fita. Asibiti gwamnati suka nufa suna zuwa aka ce ina katin ta. Nan ta kalli Haule tace

“Anty ina katin ki?”

“Fauziyya nifa ban taba zuwa awo ba.”

Ido dukkan su suka zaro daga Fauziyya har nurse da doctor da suke zaune.

Kai doctor ya girgiza yace

“A gaskiya ba zamu iya amsar ta ba dan kar wani abu yaje ya dawo ace mune.”

“Dan Allah ku taimaka mana bakuga halin da take ciki bane!”

Kai ya girgiza yace

“Gaskiya kiyi hakuri sai dai kuje wani asibitin!”

Haka suka tafi dan duk yadda suka so su duba ta ki sukayi. Wani asibitin suka je bayan sun bi ubanlayi aka zo kan su nan ma suka ce basu duba ta tinda bata taba zuwa awo ba dan kar suje a samu matsala. Sai da suka je asibitin gwamnati wajen guda biyar amman duk ba a amshe su ba wannan yasa ta mika ta wani private hospital suna zuwa aka amshe ta suka hau duba ta nan suka basu screening aka je akayo aka kawo.

Doctor ya tsorata sosai dan kwata kwata yaron ba a dai dai yake ba kuma da ya duba ma yaga bashi da ishashiyar lafiya, dan numfashin sa ma da kyar yake fita. Wannan yasa yace dole ai mata aiki dan in ba haka ba ko ita ko yaran ko dukka biyun zasu iya mutu.

STORY CONTINUES BELOW

Fauziyya yai wa bayanin komai dan haka tace a fara shirin aikin ai kuwa nan da nan aka fara shirin aiki. Da ta kira Baba a waya kan yaxo za ai wa Anty Haule aiki sai cewa yayi shi yana da abun yi bai zuwa. Ga iyayen Haule ba yan garin ba wannan yasa Haule tasa Fauziyya ta saka hannu.

Suna zaune kan a shiga aikin Haule ta dubi Fauziyya tace

“Nagode Fauziyya Allah ya saka. Amman ni jiki na yana ban da kyar zan rayu dan Allah Fauziyya in na mutu ki kular min daabinda xan bari dan Allah!”

“Haba Anty waccee irin magana ce haka ai ba mutuwa zaki ba yanxu an cigaba ba a mutuwa sai kwana ya kare”

“Duk da haka dai ni jiki na yana ban da kyar zan tashi.”

“Dan Allah ki bar fadin haka zaki tashi insha Allahu!”

Sai tai murmushi kawai. Tace

“Ki nemar min yafiyar Alhaji da abokan zamana da Kannen ku. Ni na yafe wa kowa. Allah ya yafe mana gaba daya.”

Nan Nurse ta shige ta fita da ita aka kintsa ta aka tafi dakin aiki da ita. Awan su uku suka fito hannun su dauke da Babyn da shima bai da lafiya aka ce sai an bashi gado.

Fauziyya ta amshe shi tace

“Ina Antyn?”

Kai Nurse din ta ta girgiza tace

“Allah ya amshi a bar sa.”

Baya Fauziyya tayi zata fadi Muhammad da shigowar sa asibitin kenan ya hange ta yayo wajen sai gani yai tayo baya zata fadi da sauri ya tare ta. Nurse din ta amshi Babyn. Kujera ya zaunar da ita. Ai kam sai ta fashe da kuka. Fadi take

“Anty bata mutu ba dan Allah kuce ta tashi!”

Duk ta fita haiyacin ta bata cikin tunanin ta. Nan tai ta kuka Muhammad na ta lallashin ta. A haka doctor ya fito yace azo a dauki gawar ta. Muhammad shi ya samo mota suka dauki mota aka dauke ta aka tafi da ita.

A gida aka kira Baba yaxo akai mata wanka aka shiryata aka sallace ta aka kai ta gidan ta na gaskiya. Ta samu mutane sosai. Fauziyya kam ta kasa gaskata wa dan gani take kamar karya ne. Lokacin anyi magariba wannan yasa ta koma gun Babyn dake can asibitin.

Da ta ganshi tai ta kuka. Shima Babyn da asuba Allah ya dauki abin da. Ita Fauziyya ta zata bacci yake ma dan an saka masa oxygen sai da nurse tazo duba shi taga ai ya mutu haka ta koma gida shima aka hada shi aka kai shi gidan gaskiya.

Mutuwar ta daki duk wanda ke cikin gidan Bama Fauziyya da Hafsa dan Sakina ma bata gari Samira ma bata kwana a gidan ba sai da ta dawo aka fada mata har da kukan ta. Dan Haule ba ruwan ta ba sawa ba hanawa baiwar Allah ce.

*************************

Hafsat da Fauziyya ne a daki Fauziyya na bata labarin Anty Haule yadda suka sha fama na zuwa asibiti har amsar ta da akayi tana yi tana kuka aka aiko tazo a waje.

Mikewa tayi dan dama da hijab a jikin ta ta fita. Tana fita taga Muhammad ne take gaban ta ya fadi kunya ta kamata. Har kasa ta durkusa ta gaishe sa.

“Ina yini?”

“Lafiya lou! Ya gida ya hakuri?”

“Alhamdulillah!”

“Allah mata rahama!”

“Amin!”

“Allah ya kyautata makwanci yasa mu cika da imani!”

“Amin!”

“To sai anjima!”

Ya juya mikewa tayi tana bin bayan sa da kallo. Juyowa yayi suka hada ido ya sakar nata murmushi. Itama murmushin ta mai da masa sannan ta shige gida da sauri.

A inda ta bar Hafsa anan ta same ta. Dan haka ta zauna. Farisa ce ta fito daga daki ta kalle su tace

“Ai anyi bakwai mu zamu koma bakin aiki!”

“Haba Farisa shin ke yanzu mutuwar nan bata zama izznah a gareki ba.”

Wani kallo ta watsawa Hafsa tace

“Ai mutu wajib ce tana kan kowa na sani amman gwara naci duniya ta da tsinke. Kan na mutu zan tuba na koma ga Allah.”

“Shin ke har kinsan lokacin mutuwar taki da kike fadin kan ki mutu zaki tuba ki koma ga Allah. Ki sani mutuwa na bin mu taku bisa taku a ko da yaushe zata ita daukar mu dan haka…..”

“Dan Allah Anty Fauziyya ki kyale ni na sani ai kinsan na sani ko? To ki kyale ni ke da an yi abu yanzu zaki fara yiwa mutum wa’azi ai kinsan dai ina da sani ni ba jahila bace ko?”

Kai ta girgiza tce

“Allah ya shirya.”

Hafsa da Farisan suka hada baki suka ce

“Amin!”

Sannan Farisa ta fice. Kallon Hafsa Fauziyya tayi tace

“Hafsa dan Allah ki bar biyewa Farisa. Ita tayi nisa bata jin kira *wannan rayuwar* sam ba mattabbata bace.”

“Anty Fauziyya nima na gane hakan amman Anty Fauziyya yanzu wa zai aure ni yaga kima da mutunci na bayan duk na gama zibar da su.”

Ta saki kuka tana fadin

“Inna lillahi wainna illahir rajiun. A banza mun bada mutunci mu da kimar mu. Duk Baba ne ya janyo mana ace kamar mu in anzo neman aure sai yace bamu isa aure ba bayan shi ba dauka nauyin cin mu shan mu da sutura mu yake ba wane gata zai mana in ba yai mana auren ba ai gashi nan muna ji muna gani ta dalilin hakan mun koma karuwai. Abinda ban taba zata zan zama ba so nayi da nai candy Baba yai mana aure amman ina ji ina gani lokacin da Usman ya shigo Baba yace wai har nawa nake, bayan girman da nayi yanzu Anty Fauziyya ko ke ai kin isa aure amman lokacin da Abbas ya fito kema fa cewa yayi wai baki girma ba shin jika mu zai yi ya sha bayan sun kai ko so yake mu kawo masa ya’yan shegu.”

Kuka ta fashe dashi tana fadin

“Mutuwar Anty Haule ta fargar dani rayuwa ina danasanin biyewa son zuciya da nayi. Ina dana sanin samu Baba a matsayin uba…”

Da sauri Fauziya ta rufe mata baki tana girgiza mata kai tace

“Uba uba ne komai yai miki kada ki taba zagin sa. In da laifin sa da namu muma. Kuma ba mu isa mu tsallake kaddarar Allah ba. Yanzu da muka farga kawai shine mu koma ga Allah ya yafe mana amman ni nasan rayuwar mu ta riga da ta lalace wanda ko a gaba zamu hadu da gori daga mutane har mazajen da zamu aura dan haka nake tsoron mazan ma. Lallai mun cuci kan mu sai dai muyi addu’ar Allah bamu ikon cinye jarrabawar mu ta karshe akan rayuwar mu dan nasan mun bata rayuwar mu ta yadda har mu koma ga Allah ba zamu taba mantawa a wannan rayuwar ba. Amman Allah gafuru rahim ne sai kiga Allah ya yafe mana. Yanzu ina son yadda ki dau niyar tuba to ki tuban ki yi nadama sannan kisa a ranki ba zaki kara aikata abinda kika aikata baya ba wannan sune sharadan tuba daga nan ki ta kai kukan ki ga Allah akan ya yafe miki insha Allah Allah zai yafe mana ya shiga lamiran mu. Sai abu na gaba dole mu farga mu kula da kannen mu dan kar su fada irin halakar da muka fada.”

“Haka ne Anty Fauziyya. Allah ya yafe mana ya shirya bayan mu da yan uwan mu da musulmai baki daya”

Rumgume juna sukai suna kuka.

**********

Baba Jummai bayan rasuwar dan ta da sati biyu ta koma bara da yaron ta guda biyu wato ta kara daukar dan ta daya domin ita ta gama yadda da barar ta ita ke taimkon ta ta samu naci da na sha ta manta da Allah shi ke bayar wa. Ta manta da ta yi sana’a tafi gane ta fita yana shan rana tana aika yaran ta suna bin gidaje da shaguna suna samo musu kudi. Wanda in ta fita tin safe sai dare sai ta dawo sannan tace zata daura abincin.

Dan ma yanzu Hafsa da Fauziyya da suka daina fita ko ina suna girki suci su da kannen su.

Kuma sosai suke jan kannen su a jiki in suna da bukata su tai maka musu. Dan Fauziyya ta siyi katon shago ta cka shi da kayan masarufi ta saka yaro yana kular mata dashi. Sannan ta biya musu jamb ita da Hafsat da Kanin su Dahir wanda shine babba a ‘da namiji a gidan. zasu koma makaranta.

Basu da aiki kullin sai addu’a da rokar Allah ya yafe musu.

Sakina da Farisa dai sai sun bushi iska suke dawowa gida. Sai Halima da Hajara da suma suke ficewa barar su

*********************************

Kabir ne zaune shi da Isma’il. Waya Isma’il yake da Halima yana fada mata kalaman dake kara narka mata zuciya da son Isma’il din. Kabir yana zaune ji yake kamar ya hadiyi zuciya ya mutu. Dan shi tausayin Halima yake daman ga son ta dake dawainiyya dashi dan ko bacci baya iya yi dan tunanin ta. Gashi ita ta gama yadda da Isma’il a ganin ta son Allah yake mata. Shin tayaya zai tsairatar da Halima daga halin abokin nan nashi.

Dabara ce ta fado masa dan haka yana ganin sun gama wayar yace dan bani na tura abinda nace maka zan tura. Wayar a miko masa yace

“Bari naje na dawo kan Baby na tazo.”

Tsaki Kabir yayi ya amshi wayar number Halima ya dauka sannan ya ajiye masa wayar. Ya mike zai tafi kenan ya dawo yace

“Har me?”

“Zan shiga shago ne!!”

“Ok nima daman yanzu zamu fita da Halima. Aboki saura rikis fa!”

“Me fa?”

“Na gama da yarinyar man!”

“Wai kai Isma’il me yasa baka tsoron Allah ne ka sani fa duk abinda kake sai an ma ya’yan ka kanwar ka ko matar ka.”

Idon Ismail ne yai jajir dan baccin rai yace

“Amman ban san baka so na ba sai yau Kabir yanzu ya’ya na ko matata kakewa wannan fatan dan Allah.”

Dafashi Kabir yayi yace

“Sam ba haka bane. Ina son ka ina fada maka ne dan ka nutsu kuma fadadde ne in dai kayi sai an maka dan haka ka nutsu. Kana lalata rayuwar yara.”

“Kamar ya ina lalata rayuwar yara duk wacce kaga na yi lalata da ita fa ita taso ban taba danne ya’yan mutane ba sai sun yadda.”

“Hmmm ka dai kiyaye tinda ba kyau Allah ya haramta.”

“Ai Allah mai gafara ne zai yafe mana kan mu mutu, ka nan da lokaci kadan ma!”

“Ka sani mutuwa dai bata alerting.”

“Please Kabir kar ka ruguza min jin dadi na da wa’azin nan naka.”

“To Allah ya shirya!”

“Amin!

Ya fada yai cikin shagon sa.

Kai Kabir ya girgiza sannan ya bar wajen. Wata waya ya dauko a motar sa sabuwa fil ya shiga office din sa. Number Halima da ya dauka a wayar Isma’il ya fara sakawa bayan ya saka har ya tafi kira sai ya fasa.

Ido ya lumshe wani abu na tsaya masa a kirji dan takaici da bakin cikin abunda Isma’il zai yiwa Halima ba bakin cikin sa kar yaso ta ba sanin shi ba son ta yake ba wata manufa ce kadai a ransa.

Mikewa yayi ya nufi tagar office sa dake saman shagon su. Yana tsayawa ya hangi Isma’il da Halima suna tafe yana ta mata surutu ita kuma sai murmushi take yi. Wajen motar su ya nufa ya bude mata ta shiga shima ya shiga ya tada motar ya bar wajen. Idon sa ya runtse yana jin kamar ya bisu ya fito da Halima daga motar amman ba hali.

Gun shakatawa ya kai ta kala kala ya dinga cika ta da kayan dadi sam bai nuna yana son ko da taba hannun ta a yau dan har kaf kaf yake in yaga zasu dan gogi juna. Ita kuma sai ta kara ji son sa dan yadda ta lura sam yana da kaf kaf bayan a lokacin zai iya mata komai da ta kama hannun sa ma da sauri ya janye. Wannan yasa ta kara yadda da aminta da cewa lallai Isma’il da gaske auren ta yake son yayi kuma son Allah yake mata ba na wani abu gare ta ba.

STORY CONTINUES BELOW

Shi kam Isma’il yana sane yake haka saboda sam baya gama nunawa mace true kalar sa sai a hankali a hankali wanda yau in ya nuna zulamar sa gobe zai nuna miki bai damu ba har ya baki hakuri akan abinda yai miki wannan ke kara sawa yan mata kara yadda dashi nan basu san halin sa ba.

****************************

Tin daga ranar kullum suna tare da Halima. Yau kamar kullun suna shiga wani restaurant zasu ci abinci bayan sun zauna an kawo musu abinci ne ya kamo hannun ta ya sumbata. Ido ta lumshe sannan ta zame hannun ta. Da sauri ya saki yana fadin

“Assatagafurullah in ina tare dake ne am total going bae gaskiya hakuri na ya fara kai karshe.”

Dan murmushi tayi dan ita a yadda yake ce mata yana son aure tana ganin kokarin sa dan bai taba nuna mata yana son ta bashi wani abu a jikin ta ba dan haka wani lokacin har tausayin sa take ji.

“Bae gobe na yanke shawara zan je gun Baba da kai na dan na nemi alfarmar zuwa zance kan azo saka rana kin yadda?”

Fuska ta rufe da hannun ta wai kunya.

Baki ya dan tabe yace

“Soon zanga karshen kunyar nan taki.”

A fili kuma yace

“Halima wannan kunyar taki na kara min son ki. Allah ya bani ke na jiyar dake dadin duniya.”

Shiru tayi yace

“Uhmm kin yadda naje gun Baba!!

Kai ta gyada. Yai wani murmushiyace

“Godiya nake mai tagwayen suna.”

Abincin ya debo a spoon yai hanyar bakin ta dashi da sauri ta kautar da kan ta tana yin kasa da kanta. Murmushi yayi yace

“Baby kenan wata rana da kan zaki ce in baki a baki fa.”

Murmushi tayi a haka suka gama suka tafi gida. Kullum da siyayyar da zai mata dan haka ya gama sace zuciyar ta da ta kuma gama yadda dashi.

Bayan kwana biyu kamar yadda ya fada Isma’il ya je gun Baba. Bayan isha’i yaje yasa akayo masa sallama da Baba. Har kasa ya durkusa ya gaishe shi. Baba ya amsa masa fuska a sake.

Kai a kasa yace

“Baba daman naga Halima ne ina son ta shine nake son a ban dama na zo in ta yadda dani na aiko ai mana aure.”

Shiru Bba yayi shifa ba auren ne baya so yayi wa yaran sa ba. Kayan dakin da zai siya musu ne ba zai iya ba. Yasan sai ya kashe fin dubu dari fa (Kuji wai dubu dari!)

A fili yace

“Haliman duka duka nawa take? Gani nake yaushe tai shekara gomama da za a ace ai mata aure. Shawara zan baka in zaka tsaya ta kara girma ne to amman gaskiya ba yanxu zan mata aure ba ga yayun ta nan ma fa duk ban musu ba sai ita karamar su.”

“To Baba na gode!”

Ya bashi kudi wajen dubu hamsin sannan ya mike ya tafi. Baba sai murna yake ya samu kudi.

Isma’il kuwa murna yayi tayi da baba yaki amincewa. Baba na shiga gida ya kira Yaya Babba. Yaya Baba na zuwa tace

“Alhaji lafiy?”

“Ina fa lafiya kira min halima. Yarinya na nema ta samin hawan jini wato yayen nata sunyi sun gama shine itama take son ta fara ko? Kira min ita.”

Mikewa Baba tayi ta kira ta suka shigo tare

Kallon ta yayi yace

“Yanzu Halima har nawa kike da zaki aikon da saurayi. Wato kin xama yar iska keman ko har nawa kike da zaki aure. Wallahi na kara jin haka sai ranki ya baci tashi ki bani waje!!

Da sauri ta mike ta fita idon ta na kawo ruwa. Daki ta shige ta fada kan tabarmar ta. Wayar ta ta janyo zata kira Number Isma’il sai taga an mata text da wata number budewa tayi. Taga an ce

‘Amincin Allah ya tabba a agareki. Hakika ina tausaya miki da fadawar ki tarkon Isma’il sam Isma’il bai dace dake ba ina mai baki shawara da ki nemi tsari dashi tin bai cutar dake ba.”

Tsaki tayi dan tasan karya akewa Isma’il. Isma’il yana son ta kuma son da ba algus ba zai taba cutar da ita ba.

Number Isma’il ta fara kira shigar sa gida kenan yaga kiran ta. Kuka ya fara sannan ya dauki wayar ta muryar sa a sanyaye

“Assalamu Alaikum”

STORY CONTINUES BELOW

Halima tayi sallama da kyar murya a shake kamar wanda yake cikin damuwar ya amsa sallamar muryaar sa na rawa kamar me zazzabi.

“Wa’alaikum salam!”

“Lafiya my love?”

“Ina fa Lafiya Bae. Baba ya hanani neman ki. Wayoo Allah wallahi Halima ba zan iya rayuwa bake ba mutuwa zanyibin har aka rabani dake. Da kyar na dawo da kai na gida. Bakiji zuciya ta kamar zata fashe ba dan Allah Halima kiyi wani abu kar Baba ya raba mu.”

Kuka ya fashe mata dashi, itama sai ta fashe da kuka taba fadin

“Yaya zanyi Isma’il yaya zanyi? Wallahi nina mutuwa zanyi in aka raba ni da kai kai kadai nake so.”

Kuka ya dinga mata yana fada mata shi mutuwa zai yi ba zai iya barin ta ba. Tana ta lallashin sa. Daga baya sukai sallama lokacin da yace mata zazzabi ne ya rufe sa. Dan har da karkarwa da murya irin ta marasa lafiya nan.

**********************************

Zaune take a kan cinyar sa ta makalkale shi, shi kuma sai wani shafata yake yi. Idon ta a lumshe wayar ta ta hau kara. Mika hannu tayi zata dauka ya hade bakin su yana son ya mantar da ita abinda take kokarin yi dan yasan Farisa yanzu zata iya cewa zata tafi in taga harkar gaban ta tafi mata. Dan haka yake son dauke hankalin ta. Farisa kuwa uwar wayo sai da ta janyo wayar ganin Hajiyar ta wato uwar dakin su da suke kira da Momy yasa ta saurin sakin sa tana kiran layin  nata. Can ta dauka. Ajiyar zuciya ta sauke tace

“Momy barka da yamma!”

“Yauwah Tauraruwa ta. Daman yau muna da taro dan kowa ya hallarta ke muke jira da yan uwan ki.”

“Ok ba damuwa gani nan!”

Ta mike daga jikin TJ wanda ya gama kamuwa yana son ya jita a cikin jikin sa ne kawai. Ido ya bude yace

“But Baby ki bari mu dan yi ko thirty minute ne man!”

Juyowa tayi ta watsa masa wani kallo tace

“I can’t but in zaka jira ni naje na dawo ne?”

Ta bude hannayen ta.

Mikewa yayi yace

“Muje na kai ki sai na jira ki!”

Juyowa tayi tana kallon sa tace

“Saboda an baka gadi ko me?”

“Ba haka bane Hajiya ta saboda matsayin ki ya kai ne. Ai ni a duniya ba wanda zan wa gadi sai ke!”

Baki ta tabe dan dai itama tana jin dadin mu’amala da shine amman da ba zata wani yadda dashi ba har ya kai ta ya jira ta su dawo tare.

“In taho ranki ya dade?”

“Taho!”

Ta fada tana yin gaba da sauri ya mike ya fita ya bude mata mota ta shiga shima ya zagaya ya shiga. A hanya ma sai abubuwan su suke sai kace ba driving yake ba.

Falo ne babba cike yake da matasan mata da manyansu. Kowacce tana ji da kanta da ganin tafi ‘yar uwarta.

Momy tana hakimce a saman kujera mai zaman mutum biyu ta kishingida tana zukar taba. Kallonsu takeyi d’aya bayan d’aya fuskarta dauke da murmushi. Kowaccensu tasha shiga ta alfarma saika rantse wani shagalin akeyi.

Daidai lokacin Farisa ta sanyo kai cikin dakim. Matasa da yawa dake mutanenta ne suka hau jinjina da ihu da murnar zuwan ta wasu kuma na haushin ganin tauraruwar ta ke haskawa.

Zama tayi nan yan matan suka fara zuwa suna mika mata gaisuwa, tana da zaune tana sakar musu murmushi mai bayyana hak’ora tare da mimmik’a musu hannu suna cafkewa.

Gefe su Anty Samira ne wato manyan masu aure kenan. gaisawa tayi dasu kafin ta mike ta isa ga Momy wacce ta zuba mata ido tana murmushi.

Dan durkusawa tayi a gaban ta tana fadin

“Na gaida uwar daki na. ranki ya dade tuba nake na jima ko?”

Momy ta ja hannunta ta zauna da ita gefanta tana dariya ga hakoran Makkah farare a hakoranta biyu na gefe da gefe.

“Baki laifin komai ba Farisa Taurariyar Taurari har yanzu dake ake damaw tauraruwar ki ba zata taba gushewa ba.”

Ihu dakin aka dauka wasu na jin dadi wasu na jin haushin yabon da uwar dakin su tai mata.

Daga haka Momy ta juya ta fara abinsa tarasu.

“Ina son kungiyar nan tamu tayi fice ba nan gida kano ba ba a nigeria ba har a duniya ya zaman to ana neman yan. Matan da iyayen cikin kungiyar nan. Ba komai zai sa haka ba kuwa sai kun kasance wayayyu mara sa kunya da fitsara. Tin da kika shigo harkar dole ki saka kunya a kwandon shara bayan nan sai matakin kariya daga daukar ciki dole ne ana kiyaye wa ana shan maganin dan daga ciki ya zo to zaki rasa kima da daraja. Wannan yasa Farisa take abinda take so dan tin fitowar ta Bariki bata taba yin ciki ba. Dan haka a kiyaye.”

Tafi aka dauka da sowa ana ta magana can tace

“Ya isa. Sai Maganata ta karshe ku sani, babu aure a tsarinmu. Nasha sanar maku koda ya kasance zakuyi auren, toh fa baifi na wata uku ba kin fito. Auren ba talaka ba mai hannu da shuni ki tabbatar kin tatso mana mai yawa kafin ki datse igiyar auren naki. Wannan shine jawabina. Batun balance kuma ina jiranku babu wacce batasan account number dina ba. In kana son kai aure baka da matsalar iyaye da waliyai kaje ka sanar azo a shirya kona. Ina fatan kun gane.”

Haka suka jima suna tattaunawa kafin taro ya watse Momy ta dubi Farisa wacce tayi mike zata tafi. Yan matan wajen sun rufe ta.

Hannun ta ta kamo suka fice a dakin. A compound suka zauna Momy tace

“Wai ina Fauziyya da Hafsa ne? Fauziyya tana son ta karya min darajar kungiya ta yadda tai suna da fice amman ace ta daina zuwa kinga yadda har yanzu ake booking nata kuwa!”

Baki Farisa ta tabe tace

“Anty Fauziyya ta ce ta daina harkar ynzu haka ma so take ta ja ra’ayi Hafsa na rasa meyasa sun kasa gane dadin *wannan rayuwar.* “

Murmushi Momy tayi tace

“Kyale su in sun san wata basu san wata ba. Muna zaune zasu dawo kawai kina kawo mana information akan su.”

“Angama uwar daki na.”

“Ai Farisa ke daban ce dole a koda yaushe tauraruwarki tana kara haskawa. Ba daga kananun ba daidai da manyan suna son mu’amala dake. Ina kuma ga an lek’a ga Hajiyoyinmu duk da dai kin nuna wannan baya kanki yanzu.”

Murmushi tayi ta girgiza kanta tace

“Uwar daki na kenan, me zanyi da jinsi irin nawa? Wannan babbar kazanta ce, wannan dinma da nakeyi fatana nan gaba na daina. Dan akwai target din da nake dashi da na gama shikenan fa.”

Momy ta kyalkyale da dariya tana mai dafa kafad’ar Farisa tace

“Bana fatan ganin ranar da zaki daina wannan san’ar batun neman jinsin ke kuma zan maki uzuri da alama bakisan alfanun jinsi ba sai nan gaba. Amman da kin gwada ko?”

Ta tande baki. Kamar mayyar. Murmushi Farisa tayi tace

“Sam bana son wannan kazantar bai taba ban sha’awa kuma yafi zina muni da illa dan haka ni insha Allahu bazan taba bin wannan hanyar ba.”

“Ja’irar kaya ashe har yanzu kinsan da sunan Allah?”

“Momy kenan komai kaddara ne fa amman nan da kike ganina yan gidan mu haddar kur’ani ce a kan mu. Kaddara ce ta jefa mu a halin da muke ciki.”

Ta mike ta kalli Momy tace

“Zaki ga sako sai anjima.”

Ta daga mata hannu ta fice.

Da kallo Momy ta bita dan tana son yan gidan su dan kyawawa ne yadda take son su bama Fauziyya wacce tayi al kawarin sai ta dandani zumar ta ko zata mutu domin kuwa a lokacin ita ta fara nunawa siyi harkar taki kuma tin lokacin ta daina zuwa gidan gaba daya shine yanzu ta daina harkar ma ai kam zatayi danasani. Tayi kwafa ta mike tayi ciki inda ake ya ciye ciye da shaye shayen su.

Pls a cigaba da voting dan shi n soyayarHaka ta cigaba da zawarci ganin Alhaji Kasim yafi wadan da ke son ta kashe mata kudi sai ta fara sauraron sa. Ba abinda baya bata ko ya siya mata. Nan ta fara jin dadin itama zatai auren gidan dadi. Uwar ta kuma tana mai yar wa da Umma habaici.

Ummu kuwa bata san wainar da ake toyawa ba. Abba dai ya fadawa Yaa Suleiman da Anty Zainab inda yace su kula da ita. Duk da service take a lokacin sauran wata uku ta gama. dan har DE ta siya zata juya masters.

Lokacin da ta gama. kan ta juya masters tace sai taje gida. Haka ta tafi wa da Yan gida tsaraba kala kala.

Zo kuga murna wajen Umma ganin yar tata dan daga gani suna lafiya gashi ta kammala degree har zata fara master. Ita dai sai godiyar Allah ya’yan ta suna cikin rufin asiri da wadata. Nan ta dinga fitar da tsaraba har da Mama da yayen ta.  Da tace zata gidan Rukky ne aka fada mata auren ta ya mutu. Har da kukan Ummu.

Da dare tana daki a kwance Abba ya aiko Khalil akan ya kira ta.

Mikewa tayi ta saka hijab ta nufi gun Abba dake falon sa. Zama tayi bayan tai sama sannu.

Kallon ta yake cikin so da kauna dan duk cikin ya’yan sa tafi kowa hakuri ladabi da biyayya. Magana ya fara yace

“Allah yai miki albarka Ummu a duk cikin ya’yana ina alfahari dake saboda yadda kike min ladabi da biyayya, dan haka ganin na isa dake yasa na yanke hukunci akan ki kuma ina fatan zaki min biyayya.”

Kanta a kasa ta rasa me mahaifin nata zai fada mata, gaban ta kuwa sai faduwa yake yi, nan ta daure ta amsa masa da

“Insha Allah!”

“Allah miki albarka ni nasan daman Uwa ta zata amshi abinda na zaba mata. Ba komai bane sai na daura miki aure da *mijin yayarki.* Ina fatan zaki min biyayya sannan kiyiwa mijin ki biyayya.”

Duk da abin ya zo mata a bazace bata taba kawo wa da haka ba amman sai ta daure tace

“Insha Allah Abba Nagode!”

“Allah miki Albarka, ya baku kema masu miku biyayya Allah ya baki zaman lafiya da zuri’a mai albarka.”

“Ameen Abba!”

Ta fada kanta a kasa.

“Tashi ki tafi Allah miki albarka!”

Ta mike ta fice ta isa daki. Ko ba a fada mata ba tasan da Yaa Mohammad aka daura mata aure. Abinda Abba ya fadamata sam bataji tana bakin ciki ba haka nan bata ji tana farin ciki ba. Sai dai tunanin ta ya tafi a tayaya Yaa Muhammad zai amshe ta.

Shin shi yana son tane ko kuwa? Ina tasan Anty Rukky yake so. Allah sarki shikenan ita ba zata aure zabin ranta ba sai Zabin Allah da zabin iyayen ta. Ba yadda zatai sai dai tana addu’a akan Allah yasa Zabin Allah da Iyayen ta ya zamar mata zabi na alheri wanda zatai alfahari dashi. Ta saka a ranta cewa zata yi biyayya ga mijin ta insha Allahu.

Sai washe gari Umma take fada mata ba yanzu zata tare ba sai Muhammad ya dawo daga karatun da ya tafi taji dadi sosai da hakan.

Kwanan ta biyu taji zaman garin ya ishe ta dan ba Rukky kuma ba Jannah dan haka ta fadawa iyayen ta suka amince dan sun san zata fi nutsuwa acan da samun kulawar yayarta.

STORY CONTINUES BELOW

Data koma ta samu Anty Zainab ta fada mata nasiha Anty Zainab tai mata sosai daga nan ta cire komai a ranta. Ta koma makarantar ta inda ta fara karatun ta ta samu aikin a wani private hospital take zuwa weekend tana cankasar albashin ta sai dai ta turawa Abba da Umma ko tayi alheri ga yan uwan ta. Dan har lokacin Yaa Suleiman shi ke mata komai.

Muhammad kuwa yana yawan kiran Abba su gaisa dashi dan so yake ya amshi Number Ummu amman yana jin nauyin tambayar Abba. Wata rana da sukai waya da Abba bayan sun gaisa yake cewa

“Abba ya mutan Abuja?”

Abba yace

“Suna lafiya ai Ummun ma bata dade da zuwa ba ta koma ma.”

“Allah sarki!”

Can zasuyi salama yace

“Abba ina bukatar Number wayar Yaa Suleiman!”

Nan Abba ya tura masa.

*********************************************************************************************************************************

Fauziyya ce kwance idon ta na zubar da hawaye wanda a yanzu su suka zamar mata abokan hirar ta. Hafsa ce bayan ta fito daga wanka ta zauna a gefen ta. Dafata tayi wannan yasa ta dawo daga duniyar tunanin da ta shiga. Mikewa tayi zaune tana goge hawayen ta wasu na zubowa.

Murmushin yake Hafsat ta saki tana fadin

“Anty yana da kyau mu amshi kaddarar da Allah ya daura mana muyi godiya da kuma Allah ya ganar damu tunkan lokaci ya kure mana.”

Wani kukan ta fashe da shi tana girgiza kan ta tace

“Hafsat mun cuci rayuwar mu mutuka. Shin tayaya zan zan iya manta *wannan rayuwar* da muka jefa kan mu a cikin ta. Ina kunyar mahallici na ina kuma kunyar kai na. Yaa Allah ka yafen ba dan hali na ba. Allah na tuba ka jikai na.”

Ta kifa kan ta a saman cinyoyin ta, hawaye na bulbula. Cikin kuka take fadin

“Mun cuci kan mu Hafsa mun bata *rayuwar* wanda nasan har abada ba zamu taba gyara ta ba kuma bakin ciki ma yana gaba domin a duk lokacin da mukai aure a lokacin zamu kara fuskantar wani kalubalen sai dai muyi ta rokan Allah. Allah ya bamu ikon cinye jarabawar sa. Amman ina meson tunasar dake da duk runtsi kar ki koma *wannan rayuwar* da babu riba a cikin ta ki koma ga Allah insha Allahu shi zai zama gatan mu.”

Rayuwar tasu kenan kullum cikin kuka da nadama akan *rayuwar* da suka fada kuma sunawa yar uwar su addu’a akan Allah ya ganar da ita itama. In kaga Fauziyya dole ta baka tausayi dan ta rame.

In ta tuna yadda ta shiga *rayuwar bariki* tana nadama da dana sani duk da ba a son ran ta bane amman ai da laifin ta. Jikin ta kam in ta shiga ban daki kamar ta zanja fata saboda dirza in ta tuna ta hada jiki da mazajen da ba halak din ta ba. Ranar kuwa bata iya cin komai.

*****     ******     ********

Halima kuwa ranar kwana tayi kuka akam abinda Abba ya aikata ga Isma’il wanda washe gari ta tashi da ciwon kai dan sosai son Isma’il ya shige ta ta kuma gama yadda dashi da aminta da son sa.

Da safe bayan ta gama abinda zatai ta ga Bai kira ta ba sai hankalin ta ya tashi. Wayar ta dauka ta fara neman layin sa.

Yana kwance akan gado dan ya shirya target yau ba zai je kasuwa ba zai yi amfani da wannan damar wajen samun Halima. Yana ganin kiran ya daga tsalle yana fadin

“Yess!!”

Komawa yayi ya kwanta yana daukar wayar. Cikin rawar murya kamar ta marasa lafiya ya amsa sallamar sa. Cikin tashin hankali tace

“Love ba dai jikin bane?”

“Baby ni nasan kwana nane ya kare mutuwa zanyi. Ya zanyi da rayuwa ta,”

Sai ya fashe mata da kuka.

Hankalin Halima in yai dubu ya tashi dan haka ta hau lallashi, tana fadin

“Kana ina yanzu kaci abinci? Ka sha magani?”

“Wa zai bani Halima. Ina kwance rai a hannun Allah. Ba mai taimako na daman dalilin da yasa nake son auren ki na samu abokin rayuwa. Halima ina son ki ina kaunar ki.”

Ido ta runtse ta mike tana fadin

“Gani nan nazo sai muje asibiti ko?”

STORY CONTINUES BELOW

Ta kashe wayar ta fita a dakin a firgice. Da Anty Fauziyya suka hadu tana sharar tsakar gida ko lura da ita bata yi ba ta fice a firgice. Da kallo Anty Fauziyya ta bita kawai.

Tana fita ta tsaida Napep ta hau ta nufi can gidan Isma’il. Kabir bayan ya shiga kasuwa ya nufi rumfar su Ismail sai dai akace masa bai shigo ba. Wayar sa ya dauka dan ya tambaya ko lafiya. ringing daya biyu ya dauka yana fadin

“Friend ya kake?”

“Lafiya me ya hanaka zuwa kasuwa yau?”

Dariya Isma’il ya saki yana shafa kan sa yace

“Duk yana cikin target dina da Halima. Kasan yadda mukai da Abban ta kuwa naje akan a ban dama ina zuwa zance sannan a turo amman dan rainin hankali wai yace nawa halima take bata isa aure ba. Zai ga kuwa bata isa aure ba lokacin da taje masa da ciki na a jikin ta.”

Ya fashe da dariya yana fadin

“Yanzu za a fara playing game din dan nasan yanzu tana hanyar zuwa waje na. Kaga kar ma tazo taji ina waya bye zan kira ka in ta tafi!”

Tin da ya fara maganar Kabir ya kasa ko da motsi saboda fargaba tunani yake ta yadda zai hana Halima karasawa wajen Isma’il. Office dinsa ya nufa da sauri har da gudu ya bude lokar office din ya dauko waya a ciki ya fara neman layin Halima amma har ta katse ba a dauka ba. Text ya tura mata yana mai nuni akan Isma’il ba mutum kirki bane kar ta shige masa sannan ya koma ya zauna yana dafe kan sa.

Halima tana shiga gidan ta shiga falonsa baya nan dan haka kai tsaye tayi cikin bedroom dinsa kwance ta same shi cikin bargo yana rawar sanyi da sauri tayi kan gadon tana janye shi. Idonsa jajir dashi nan ya hau sannu. Ta jima tana masa sannu sannan ta hada masa ruwan wanka a toilet ta shiga kitchen ta dafa masa tea.

Har toilet ta raka shi dan yadda jkin sa ke rawa. Ya jima ciki sannan ya fito ya saka kaya ta shigo da tea ta bashi ya sha ya sha magani sannan ya komavkan gadon.

Matsawa tayi kusa dashi tana fadin

“Sannu my love anya ba zamu asibiti ba.”

Kai ya girgiza yana fadin

“Baby gwara fa na mutu da na rasa ki wallahi na rasa ki mutuwa xanyi. Ina son ki Baby ban san ya zanyi ba son ki yai min mugun kamu rabani dashi kamar rabani da rayuwa tane.”

Sai ya fara rawar sanyi. Halima kuwa tausayin sa ya kamata ace wai duk saboda son ta ya shiga wannan halin. Hawaye ta fara tana tunanin ta yadda zata fitar da masoyin ta daga halin da take ciki.

Jin yana rawar sanyi yasa tace

“Zazzabin ne? Ya za a yi yanzu?”

Hannun ta ya kamo, yana murzawa yace

“Please Baby hug me ko na samu sassaucin abinda nakeji.”

Kallon sa ta tsaya kamar ba zata je ba. Hawaye ne ya zubo masa yace

“Kar ki damu in ba zaki iya ba nasan if u hug me zazzabin zai sauka please help me Baby!”

Janyo hannun ta yayi ya rungumota, yana sauke numfashi da ajiyar zuciya. Tayi lagwas a jikin sa. sun dauki tsawon mintuna a haka.

Halima jin saukar numfashinsa agadon bayanta ne, ya saukar mata da kasala ga wani irin feelings datakeji.

Numfashinta ne ya fara fita da sauri sauri wannan yasa yasan ta kamu, kara kankameta yayi ya dago kansa yana kallon fuskarta idon ta a rufe. Wani killer smile ya saki. Yana sakar mata nunfashin a cikin kunnen ta. Yana wani nishi nishi.

Can ya bude bakin sa a hankali cikin rawar murya yace

“Baby please can I kiss you,”

Tsigar jikin ta taji ta tashi ta kasa magana ta kara shigewa jikin sa dan yadda take jin jikin ta yana mata wani yamm. Wannan yasa yasan tana bukata kenan. Kan ta ya dago a hankali ya kalla idon ta dake a rufe.

Halima kyakyawa ce domin daman jinin gidan su kyawawa ne iyayen fulanin ne gaba da baya. Idon ta ta bude tana kallon sa. Wanda ya canja kala daga gani a matukar bukace take, kallon juna sukai kan tai kasa da idon ta dan bazata iya jurar kallon da yake mata ba. Shi kuwa Wani abu yaji ya tsarga masa tin daga tsakar kansa har tafin kafar sa abinda yasa jikin sa daukar rawa kenan.

Bakin sa ya daura akan na ta ya fara kissing dinta cikin kwarewa da salon sa na birkita yan mata. A hankali yagangaro habarta yana lasa, wuyanta, da kirjinta yana wani kiran sunanta yana shigewa jikin ta jikin sa na jarkarwa fadi yake

“Halima I love you, I can do without you,”

Hannun sa ya zura cikin rigar ta yana shafa dukiyar fulanin ta. Halima kuwa wani irin dadi ne yaka ratsa ta tun daga tafin kafarta har zuwa tsakiyar kanta, sai da ya dauki hour yana romancing dinta passionately. Sam bai gigin taba kasan ta ba kissing nata kawau yake yana wasa da kirjin ta.

Wannan salon sa ne sam baya nuna wa mace ga abinda yaje so da ita sai ta dabara. Isma’il ya iya tafiyar da mace fiye da tunanin mai karatu shiyasa da wuya mace ta Iya rabuwa shi sabida yanda ya kware da romance, bai ki ya lashe mace tas ba.

Ji yake kamar ya wuce domin jikin Halima ya gama tafiya dashi zai ce bai taba haduwa da mace mai dumin da ni’imar jiki ba duk da bai kai ga shigar taba. A hankali ya cikata ya koma gefe yana maida numfashi, ita kuwa Halima ji tayi dama yacigaba sabida dadin da takeji yana ratsata ga wani irin masifafen sha’awa datakeji. Bata taba jin yanayin da take ciki ba.

Kifa kan ta tayi akan gadon dan wata kunyar sa da taji tana ji ga jikin ta da yake mata wani iri dan muguwar sha’awar da take ji dan ta gama jikewa jakaf.

Mirginowa yayi kusa da ita yana fadin

“Baby dago kiji.”

Kasa tashi tayi. Nunfashi yaja yace

“Kiyi hakuri in ina tare ina kasa controlling kai na na fada miki na jima ina da bukatar aure gashi yanzu Abba ya kara ruguza min komai, daga jiya zuwa yau na tabbata da son ki shine rayuwa ta dan ta sanadiyar San danake miki nashiga matsanacin hali har na kwanta da ciwo wanda gashi yau da zuwanki na wartsake, da baki zo ba mutuwa zanyi ya kama hannun ta. Son ki ya gama tafiya dani Baby pkease ki fadan yaya zanyi?”

Tausayin sa a kamata dan yadda yake magana kamar yai kuka, bata san lokacin  da fadawa jiknsa ba shi kuwa ya rungumeta tsam, sai ta fashe masa da kuka dan ta rasa wane irin so Isma’il ke mata haka.

Lallashin ta ya fara yi yace

“Stop crying Baby menene nayi wan abu ko?”

Kai ta grgiza yana fadin

“Ban san wane irin so kake min ba My love. Ina tausayin ka My love.”

Gane ta dada a son da tausayin sa kuma ta yadda dashi ne yasa ya ce

“Baby na fada miki ban taba soyayya ba sai akan ki daga kallon ki naji na akamu Baby ba zan iya aurar wata macen ba saboda ke kadai nake so nayi rayuwar aure da ita ban san yadda rayuwa ta zata cigaba da kasancewa ba ko zan kai ko zan tafi na bar ki amman in na mutu ki sani ina son ki kuma son kine dalilin mut…..”

Hannun ta ta daura akan bakin sa tana girgiza kai. Tace

“Kar bar fadan ka zan iyai maka kome kake so in dai zai faranta maka yasa mu kasance tare har karshen rayuwar mu. Ina kaunar ka My love kai ne farin ciki na abun alfahari na.”

Haka suka dinga hirar su har yamma tai sallah sannan tace zata tafi nan ya bata kudin masu yawa tai masa sallama ta tafi.Da kallo ya bita har ta fita aransa yana kitsima yanda zai huta da Halima dan ya gama karantar ta tana da sha’awa sannan tana daga gani zatai niima in yai duba da ita da dumin jikinnta. wani murmushi yasaki dan yasan cikin sauki zai cika burinsa akanta

Kabir kuwa kasa komai yayi a office saboda damuwa kuwa har zazzabi ya rufe shi sai dayasha maganin zazzabi sannan yaji dama dama amman zuciyarsa wani irin zafi yake masa.

Shi tayaya ta shjga zuciyarsa da da yadda zai ya cire ta a zuciyar sa da tunanin sa da tuni ya cire ta ya huta ace wacce yake so yake jin zai iya mutuwa saboda son ta ita bata san yana yi ba wani dan iskacan zai bata mata rayuwa

Addu’a yake Allah cire masa son Halima amma kullum kamar kara masa wutar Santa ake a zuciyarsa.

Kai ya dafe yana fadin

“Ni kuma irin tawa jarrabtar kenan!”

Hawayen idon sa ya goge wasu masu zafi suka sake zubowa. Yana zaune sai ga kuran Isma’il nan kin dauka yayi dan yasan bai wuce ya bashi labarin yadda sukai da Halima ba bayan yasan in yaji zai ruguza masa rayuwa.

Text ne ya shigo yana dauka ya bude Ismail ne yace

“Friend tafa kusan shigowa hannu dan yau tazo gida kai abin dai sai mun hadu”

Ji yayi kan sa ya sara masa da sauri ya rike Kansa Ya na fadin

“Ya Allah kai ka jarrabceni da San Yarinyar nan ya Allah kacire min Santa a zuciyata alfarmar annabi.”

Da dare sun danyi waya dan ma yace mata bai da lafiya ne.

Washe gari ma bai fita kasuwa ba yace mata jikin ne amman da sauki wannan yasa bayan ta fita a gida ta tarzarce can kawai. Tana zuwa ta same shi kwance akan three sitter sanye yake da 3 qtr baki da armless shigar yayi mutukar kyau ga gashinsa sai kyalli tana son Isma’il ko dan gayun sa da tsabta. A ranta tace

“Allah ka mallaka min Isma’il!”

Yana ganin ta ya mike yana marairace mata shi a lallai bai da lafiya ita kuma duk ta rude ta nufe shi tana masa sannu.

Wuyan sa ta taba taji ba zafi wannan yasa tace

“Sannu My love.”

Murmushi yai mata ya kama hijab din jikin ta yace

“Baby ki cire hijabin mana kisha iska.”

Nuku nuku tafara yi tana tinanin yanda zata cire hijabin, jitayi kawai yace

“let me help you,”

cire mata yayi yai tozali da body huge din jikin ta ta kamata sosai, nan da nan yaji wani irin feelings, yakoma ya zauna idansa har sun dan kada, kasa dagowa tayi dan duk ta takura.

Binta yake da kallo yadda gashin ta ya kwanta a gadon bayan ta, ya sauke idon sa akan kirjin ta wanda yake a cike taf sai ya dan saki murmushi tunawa da yayi wai yrinya ce bata isa aure ba nawa take. Kai ya girgiza kai.

zama yayi kusa da ita jikinsa na gogan nata, a hankali ya janyo ta jikinsa yafara shinshina jikinta yana sakin wani numfashi. kan Kujerar suka zube ya hau yimata wani irin mahaukacin kiss, ba karamin kai zuciyarsa yayi nesa ba da ba abinda zai hana yayi sex. Halima kuwa ji take kamar su kwana suna a haka dan dadin da take ji.

STORY CONTINUES BELOW

Kamkame shi tayi tana sauke ajiyar zuciya sun jima sannan ta nutsu. Nan suka dan taba hira da xata tafi Har waje ya rakata tahau mota ta tafi. Shi kuwa daga nan motar sa ya hau ya fice dan Halima ta gama daga masa hankali ba zai iya jurewa ba wajen wata budurwar sa ya tafi dan ya rage zafi.

Halima kuwa tana mamakin mai turo mata text din nan kullum cikin kawo mata aibun Isma’il yake bayan ita bata ga wani aibun sa ba in ta kira an dauka tai ta hello hello amman ya ki magana. Wannan yasa ta daina duba text din ma ko an mata dan ita ta gama yadda da Ismail Dari bisa dari.

******************************

Fauziyya ce zaune akan sallaya dan idar da sallah la’asar din ta kenan, tana addu’a kanwar ta ta shigo ganin ta zaune akan sallaya ta kalle ta tace

“Anty Fauziyya wai kizo inji wani a waje!”

Kamar tace ba zata je ba sai ta gyada mata kai dan ko wane ma gwara taje tai masa kashe din kar ya kara zuwa wajen ta dan haka ta mike ta zura silifas din ta ta fice.

A tsaye ta same shi ya zubawa kofar gidan ido. Sanye yake cikin brown kalar yadi a wanke a goge ya masa kyau sosai ya kara kyau da kwarjini. Suna hada ido suka tsaya kallon juna sai Fauziyya ce tai karfin halin janye idon ta sannan ta koma soron gidan ya bi bayan ta.

Dan durkusawa tayi yace

“Ina yini?”

“Lafiya lou! Ya gida?”

“Alhamdulillah!”

Shiru ya biyo baya sai daga baya yace

“Fauziyya bukata ta dai na kara kawo wa ba zan taba daina kawo miki wannan bukatar ba har sai ranar da zan koma ga mahalici na. Wallahi Fauziyya da gaske nake son ki nake kuma da aure dan Allah ki amshi soyayya ta dan Allah ba danni ha.”

Shiru Fauziyya tayi a ranta tace

“Shin Wannan bawan Allahn yasan ko ni wacece kuwa. Naga alama in ban fada masa gaskiya ba bazai rabu dani ba.”

Dagowa tayi sai suka hada ido da sauri ta dauke kan ta tai kasa dashi tace

“Kayi hakuri ni ba zan iya amsar soyayyar ka ba dan Allah kay…”

“Saboda me?”

Ya fada a zafafe. Da sauri ta dago dan ta tsora ta. Kai ta hau girgizawa idon ta na kawo ruwa.

“Ki fadan dalilin da yasa bakya so na. Ki fada min ko dan ni talaka….”

“Ba haka bane!

Ta fada da sauri ta zube a kasan soron tana mai kara fashewa da wani kuka. Durkusawa yayi a gaban ta yana girgiza mata kai yace

“Ki fadan dan me bakya so na? Ki fada min dalili!”

“Saboda ban kai matsayin naso ka ba. Ban kai matsayin da kai ma zaka soni ba.”

Idon sa ne ya kada yai jajir yace

“Bana son irin wadan nan kalaman. Dan ba hujja bace na dalilin da zaki ‘ki so na ba.”

Majina ta ja tace

“Kasan wacece ni? Na fada maka ban cancanci kamili kamar ka yaso ni ba.”

Ido ta lumshe tace

“Nayi wasa da dama ta ta yadda na zama karuwa. Sam bakai kala da karuwa ba baka cancanci auren iri na ko son kamata ba. Na fada maka ko wacece ni dan haka dan Allah!!

Ta hade hannayen ta biyu tana rokar sa tace

“Dan Allah ka rabu dani ban cancanci ka soni ba.”

Tana fadin haka ta rufe fuskar ta da tafin hannu tana mai sakin kuka. Wani murmushi Muhammad ya saki yace

“Fauziyya kenan. Ban taba tambayar ki wacece ke ba domin na riga nasan wacece ke. Ban zo dan nasan wacece ba. Nazo wajen ki ne dan na amshi soyayyar ki kawai. Fatana yanzu shine ki amshi soyayya ta muyi auren mu.”

Dagowa tayi tana binsa da kallo kamar wata zararra tana kallon sa cike da mamaki, kasa daina kallon sa tayi tana mamakin sa shin anya yaji me tace masa kuwa. Kallon sa take tana girgiza kai tace

“Shin kaji me na fadi kuwa?”

Kai ya gyada yace

“Naji na kuma sani nace soyayyar ki kawai nake bukata.”

“Shin wane irin so kake min?”

“Ina son ki fiye da kai na. Ban taba son wata mace a duniya ba sai uwa ta daga ita sai ke.”

STORY CONTINUES BELOW

Kai ta girgiza tace

“Ba sona kake ba!”

“Me kike fadi ne Fauziyya!”

Ido ta lumshe hawayen idon ta suka zubo tace

“Kaje ka fara binciken wacece ni tukkina?”

Murmushin gefen baki yayi wanda dimple din sa ya lutsa yace

“Fauziyya kenan nasan komai game dake in nace miki nasan yadda gidan ku yake na yadda mahaifin ki bai son yai muku aure da yadda baya daukar dawainiyyar ku har ta jefa ku a rayuwar da kuke. Fauziyya ba abinda ban sani ba game dake da yadda aka kai ki aka bata min rayuwar ki. Nasan komai game dake nasan komai akan ki kuma a haka naji na gani nake son ki. Wallahi sonki nake Fauziyya da zuciya daya!”

Kallo sa take kamar wata sakarya, wai a hakam yace yana son ta. Anya kusa ita abin ma tsoro yake ba. Maganar sa ce ta dawo da ita daga tunanin da ta tafi.

“Ki yadda dani Fauziyya ina sonki wallahi.”

Kai ta gurgiza tace

“Anya kuwa? Tausayi na kake ji ko wani abun? Amman ba sona kake ba.”

Murmushi yayi mai ciwo ya kafe ta da idanun sa dake mata kwarjini bata iya kallon kwayar idon sa.

“Ki kalli cikin ido na zaki ga tsantsar son ki da kaunar ki. Son ki ya gama kama dukkan sassam jiki jijiyoyi da jinin jiki na. Tsayawa fada miki ina son ki ta fatar baki bata lokaci ne amman ki sani ina sonki kuma ba zan taba daina ki ba kuma ki sani ba zan taba barin ki ba gwara ma ki amince da soyayya ta.”

Yadda yake mata a yanzu sai ya sauya mata dan da zafin sa da confidence din sa yake maganar dan haka sai ta zuba masa ido tana kallon sa. Gane kallan da take masa ne yasa yai dai dai ta muryar sa cikin sanyin murya yace

“Please Fauziyya!”

Hannu ta sa ta goge hawayen idon ta sannan ta mike tana kallon sa. Juyawa tayi zata shige taji muryar sa yana fadin

“Ina kuma zaki?”

Bata juyo ba kuma batai magana ba. A hankali ya tako ya karaso gaban ta ya zuba masa idanun sa, yana fadin

“Baki ban amsa ba zaki tafi ki barni, ko so kike na mutu?”

Da sauri ta dago tana girgiza kai. Idanun ta ya kafe da kallo yana murmushi domin ya hango son sa a cikin sa. Idon ta tai saurin rufewa tna murmushin da bata san ya kubuce mata ba. Gefen sa tayi tai cikin gida. Binta yayi da kallo, kan sa ya shafa yana murmushi sannan ya kada kai yayi waje.

Tana shiga ta shige dakin ta ta fada kan gado tana murmushi. Filo ta janyo ta rumgume bata san me yasa take jin sanyi da nutsuwa a tare da ita na. Ita kadai ta dinga juyi tana murmushi. Hafsa da tin shigowa ta ta biyo ta ta tsaya kallon ikon Allah yaushe rabon taga Antyn ta a wannan halin na farin ciki lallai anjima.

“Lafiya Anty Fauziyya? Me aka samar mana?”

Ido ta bude da sauri ta mike tana girgiza ka.

Dariyq Hafsa tayi tace

“In tayi wari maji!”

Ta fice. Murmushi Fauziyya tayi ta koma ta kwanta tana mai tunanin rayuwa da komai. Take tsoro ya kamata shin tayiwa bawan Allahn adalci in ta bar shi a wannan halin na tunani kuwa? Sai taji tausayin sa. Yanzu yana wane hali? Shi da yake son ta gashi ta saka shi a damuwa bayan ita yana neman cire ta a tata damuwa.

Daman a zamanin nan za a samu wanda yasan kayi karuwanci har ya amice yaji ya gani yace yana son ka. Anya kuwa. To ita ko ba sonta yake ba in zai aure ta ai zata yadda taje tai bautar gidan mijin ta ko ta hutu a a dakin mijin ta.

Fuskar Muhammad ce ta farai mata gizo, fari ne tas kyakyawa yana da idanu ga hanci gashin kansa a kwance luf luf kamar na yan indiya. Fatar sa mai kyau ce fara tas duk da bai da hali, akwai tsafta da kula da kai ga kamshi.

Gaskiya Muhammad ya cika cikakken namiji. Wanda ko wacce mace zai kwadayin samun sa. Murya sa akwai dadin sauraro yanayin sa bai da yawan magana daga gani in yana yi yana takura kan sa ne sai yau da take ganin ydda yake mata abu cikin isa da nuna iko abin ya bata mamaki. Bai da abu sai rashin sa kawai wannan kuma ba matsalar ta bace da kudin wajen ta da tace zata bude shago zata bude sai ta daura shi akai suna rufawa kansu asiri.

Juyi tayi akan gado tana tuna abunda ta gani a cikin kwayar idon sa, tsagwaran son ta da tausayin ta ne da gaskiya. Kai ta girgiza. Tana fadin

“Allah kasa karshen wahala da bakin cikin rayuwa tane yazo. Amin!”

Ta fada Idon ta na kawo ruwa. A ranta tace

“Shin yau da a cikakiyar mace ya samen da zancen soyayya wacce irin murna da amsa soyayyar sa zanyi. Allah ka yafemin ka jikai na ka shirya yan baya.”

Take kuma ta fada duniyar nadama wacce take a cikin ta a koda yaushe. wanda in ta tuna take rayuwar ta da tunanin ta yake canjawa tai ta kuka da tuba ga Allah wanda shi ta saka a agaba a koda yaushe. Da kuma ta tuna da Muhammad sai ta saki murmushi taji sanyi a ranta. Tana fadin Allah shi ya turo mata Muhammad dan ya zama kariya kuma kiyaye ta ne.

To Alhamdulillah zata amshi kamar yadda ya nema sai dai addu’ar Allah ya kare ta daga shiga wani halin Allah yasa kuma Muhammad ya amshi kaddarar ta kamar yadda ya sani. Abunda ta dinga sakawa da warwarewa har aka kira magariba ta mike tayo alwala ta dawo ta tada sallah.Tin da ya koma gida yake sake sake Allah yasa Fauziyya ta yadda ta amshi soyayyar sa. Kasa komai yayi sai tunani yana cikin tunanin wayar sa ta hau kara dauka yayi ya duba yaga Mamahn sa ce dan haka cikin sauri ya dauka yana mai yin sallama.

“Assalamu Alaikum!”+

“Wa’alaikum salam Mai babban suna yanaji muryar ka haka ko dai baka da lafiya ne?”

Ido ya lumshe ya bude a hankali sannan ya girgiza kai yace

“Mamah ya kike ya gida? Missing dinku ne ke damu na.”

“No Mai babban suna dis ur voice there is something wrong behind it. Fada min kaji!”

Shiru yayi sai kuma yace

“Mamah akan wannan yarinyar ne!”

“Me kuma ya faru?”

“Mamah taki yadda dani taki ta gane da gaske nake son ta.”

“Ko sai na zo ne?”

“No Mamah I can handle it. But I really really need ur prayer.”

“Insha Allahu baka da matsala. In ita Alheri ce a tare da kai Allah ya karkato da hankalin ta kanka. In ba alheri bace Allah ya cire maka son ta.”

“Ameen Mamah but nayi Istihara amman dai itan ce.”

“Wai wane irin kyau ne da yarinyar nan!!

Murmushi yayi yace

“Mamah bashi ya ja ra’ayi na ba. Kinsan ni bana son mace mai kyau amman Allah sai ya dauran son mai kyau ba yadda na iya na amshi kaddara ta.”

“Mai Baban suna shin meyasa kake son yarinyar nan har haka?”

“Mamah wallahi ba dalili ni dai nasan daga kallo daya da nai mata Allah ya dauran son ta sai daga baya da naji labarin ta shine abin da ya karan son ta da tausayin ta.”

“Meya faru da su?”

“Mamah dare yayi amman gobe da safe zan fada miki komai.”

“Ok Allah ya kai mu Mai Babban suna ka kula da kanka. Kaci abinci ma tukkuna?”

“No amman yanzu zanci dan gobe ma da azumi zan mike.”

“Alright Sai da safen!”

“Aha agaida kowa. wai yaushe Abbi zai dawo ne?”

“Yace sai ka dawo shima zai dawo.”

Dariya yayi yace

“Lallai Abbi zan fada masa ni ban da nauyin dake kan sa dan haka ma ya dawo nima soon zan dawo dan da ta amince within one month zan aure ta dan na gaji da xaman gwaranci.”

“Iyee lallai wato yanzun kana son auren ko?”

“Yes! Mamah amman sai da na hadu da zabi na naji am eager to marry!”

“Ya dai kamatan sai da safe kafa ci abincin!”

“Insha Allah. Tnc!”

Yai peck din wayar sannan ya mike yana janyo flask din tea hadawa yayi amman da kyar ya samu ya sha ya kwanta.

Karfe biyun dare ya mike yaje ya dauro alwala sannan ya zo ya tada sallah. Ya jima yana mika kokon barar sa ya kawo bukatar Fauziyya yana kara addu’a Allah ya shirya ta ya sa albarka a abinda yake son yi. Ya jima sannan ya mike akan sallayar.

********************************************************************************************************************************************************************************

Duk hanyar da Isma’il zai bi dan mallake zuciyar Halima yabi kuma ya mallake ta dan bata ganin ko da gashi sai shi ta gama yadda dashi ba yaudarar ta zai ba dan a ko da yaushe yana nuna mata zallar son ta da kaunar ta duk abinda bata so bai mata.

STORY CONTINUES BELOW

Amman tundaga lokacin da ya fara romancing da ita yake yawan yi duk da daga wasan nin bai kuma mata wani abun dan ya nuna mata son ta da kaunar ya su suka sa har yake iya romancing nata. Yadda dashi da tayi shi yasa ta saki jiki da Isma’il.

Ta amince yana Santa da aure. Duk da tana yawan ganin ana mata text amman sai ta daina budewa da taga daga number ne sai ta goge dan ta gama yadda da Isma’il abinda yake fada bazai tabai mata haka ba.

Kabir kuwa indai Isma’il zai bashi labarin Halima ji yake kamar zuciyar sa zata fito da takaici da kishi. Ko da yaushe yana mata text amman ganin alakar su na dada gaba sai ya kawo a ransa ko bata dubaw wannan yasa ya canja number. Amman Halima ganin irin sakon da ake turo mata da waccen number na bata Isma’il yasa ta daina budewa shima.

Ismail kuwa kullum cikin sabon salon nuna mata so yake da kauna kamar ya hadiyeta shi yasa takara sakin jiki dashi.

Kabir kuwa son Halima a koda yaushe kara mamaye zucyar sa yake, kullum cikin rainon makahon San dayake mata yana kuma adduar Allah kada yabawa Isma’il damar bata Halima.

Duk da yana sane da yawan fitar da suke kuma shima Isma’il na bashi labarin duk abinda ke wakana a tsakanin su. Wannan ya kara mai kaimi wajen yi mata sako da nusar sa ita da wa’azi da nasiha amman ina Halima tayi nisa bata jin kira.

Yanzu da ya ga dama sai yaki zuwa kasuwa sai su hadu a gidan sa wanda hakan yasa sukai mugun sabo da shakuwa da suka kara yi yadda in zai romancing nata haka suke yi necked wani lokacin ma har wanka yake mata.

A haka yake koyar da ita abubuwa da yawa amman bai taba nuna yana som yayi sex da ita ba. Duk da yanzu sukai matakin katshe a romancing nata dan har fingering yake mata. Wanda Halima ta riga ta saba in ma bai mata ba ita zata shge masa ta tada shi har suyi.

Wani lokacin kuwa ji take kamar ya shige ta dan yadda yake tafiyar da ita mantawa take da komai sai dadi da take ji. Dan wani lokacin har haushin sa take ji Na yadda zai tada ta sa dai ya rumgume ta yan bubbuga bayan ta har ta samu nutsuwa duk da shima yana wani halin dan da ta tafi zai nemo me rage masa zafi.

Isma’il yana sane da duk halin da take ciki dan yace akwai lokacin da  yake jira. Sai ya gama sace zuciyarta yadda ko sex yai da ita da ya bata hakuri komai zai shige su cigaba da harkar su.

Yau bayan tazo, ta samu Isma’il zaune a falo kan sa ta fada tana fadin

“Wash My love yunwa nake ji fa.”

Kallon ta yake yana wani kashe idanu yace

“Ke nake jira ai yanzu na bayar a yo mana takeway!”

Ya janyo ledar ya sauka ya saulo da ita ya saka ta a tsakanin kafafunsa. Nan suka hau ci yana bata tana bashi har suka koshi ya muke ya shiga cikin dakin sa. Ruwa ya watsa sannan ya fito yana mikar da ita yace

“Muje nai miki wanka”

“No my love nifa kunya nake ji.”

Dariya yayi ya bata hanyar shiga toilet din. Tana shiga ta cire kayan jikinta ta fara wanka.

Tana gamawa tana kokarin daura towel yashigo bandakin. Rumgume ta yayo ta baya ya dura hannun sa a kirjin ta yana wasa dasu. Jin ba zai iya a tsaye ba yasa cak yadauketa yakai ta gado, ya kwantar da ita, kiss yaringa kai mata ko ina aranar wani nau’in wasa yaringa yimata Wanda bai taba mata irinshi ba tin tana toshe bakinta jin datayi bazata Iya cigaba da toshe bakinta ba yasata ringa kiran sunansa cikin wani irin yanayi.

Halima kuwa wasanin da Isma’il yake mata yau ya girmewa tunanin ta dan wata matsanan ciyar sha’awar ta kunno mata dan ji take ko zai bari ita ba xata Iya jurewa ba, yana cikin kokarin sakinta sai ji yayi ta kara kankameshi gam, nan ya cigaba da aika mata sakoni har kai kasanta

…………………………………………………………

STORY CONTINUES BELOW

Kabir kuwa yana gida ranar bai fita kasuwa ba yana kwance yana tunanin Halima kawai yaji kirjin sa ya buga da sauri ya mike yana kiran sunan ta. Komawa yayi ya zauna yana dafe bakin sa. Shiru yayi yana girgiza kan sa.  haka kawai ya tsinci kansa da shiga damuwa da kunci na ba gaira ba dalili kuma sai yake halakanta hakan da wani abu ne ke damun Halima ko ke faruwa da ita.

A haka Ismail ya dinga sarrafata sai da ya amshi martabar ta tsaf sannan ya fara kokarin zare jikin sa daga nata.  wani mugun zafi taji a kasanta, wannan yasa ta dan saki kara tana fadin

“Washhh!”

Sam a baya bata ji zafin ba dan Isma’il  ahankali ya tafiyar da ita, Take taji nadama ta kamata wannan yasa ta saki wani irin kuka. wai yau ita ta aikata zina.

Ji da yayi ya kasa jurewa yasa ya fara kiran layin Halima amman ya kira tafi sau nawa bata dauka ba. Hakan yasa yafara kiran layin Ismail amman shima bai dauka ba abinda ya lara daga hankalin sa kenan.

Halima kuwa har lokacin kuka take, duk rarrashin da Isma’il ke yi amman taki ta saurare shi. 

“Baby dan Allah kiyi shiru wallahi ban san tayaya haka ya faru ba na kasa jurewa ne. U know my problem na fada miki ina bukutar aure amman gashi mahaifin ki yaki yadda na fada miki ba zan taba iya auren wata ba bayan ke, wallahi Baby ban taba aikata wannan abin ba sai akan ki kuma ba komai ya jawo ba sai tsananin son ki. Dan Allah ki yafen na miki alkawarin bazan taba barin ki ba ke kadai ce matata wacce nake son ta zama uwar ya’ya na believe me Baby!”

Sam bata saurare shi ba bare ya sa ran zata tanka masa kukan ta kawai take yi.

“muje intaimaka miki pls!”

yace yana riko hannunta fisge hanunta tayi tace

“Please leave me alone u caused. Everything,”

“I know please let me help you, you need my help please.”

kara fisge hanunta tayi, ganin zata bata mishi lokaci yasa yadauketa cak yakaita bandaki, ya tari ruwa mai zafi, yasa dettol, aciki  ya dagata yasata acikin bahon.

Kuka ta kara saki saboda zafi da radadin da taji.

“Sorry kinji!”

Hawayen idon ta ya hau share mata yana mata sannu har ruwan yai sanyi ya canja mata wani sannan ya barta tai wanka.

Da kyar tayi wanka ta fito tana wata irin tafiya. Da sauri ya mike ya kamo ta ya zaunar akan gado ya dauko mata magani ya bata, amsa tayi ba dan taso ba ta sha kayan ta ta fara sawa sannan ta mike tana daura dan kwalin ta. Idon ta jajir dashi mikewa yayi yace

“Ina zaki Baby?”

Wani kallo ta aika masa sannan tayi gefe zata wuce. Jakar ta ya amsa ya saka mata kudi masu yawa ya mika mata. Bata kalle shi ba bare tasan me yayi ta amshi jakar ta fice zuciyar ta na mata zafi.

Tana fita ya lashe baki yana fadin

“Gaskiya Leemat u are so special ur sweet is more than honey. I will never leave now sai na koshi dake muje zuwa yan mata!”

Halima na shiga gida ta wuce daki kan katifar ta ta fada tana sakin kuka mai taba zuciya. Nadama ta cika ta shin tayaya  ta yadda  ta aikata wannan abun. Ido ta runtse, wani irin tsoro ne yakamata yanzu idan Allah yadau ranta acikin wanan yanayin mai zata cewa Allah, mutuwa da farat daya zata daukeka kirjinta yakara bugawa, a ranta tace

“Shin laifina ne ko na iyayena da sune silar jefani acikin wanan halin? innalillahi wa inna ilahi rajiun!”

Tai ta nanatawa, ido ta runtse tana hawaye tana fadin

“Ya Allah karka dau raina a lokacin da kake fushi dani, ya Allah kabani ikon bauta ma har karshen rayuwata, kasa nafi karfin zuciyata, Ya Allah kabani ikon raya sunnar manzo SAW kasa in mutu a inuwar aure,”

A haka tayi ta addu’oi ta Daga kwance har bacci yayi awon gaba da ita, wanda a cikin bacci ta dinga mugayen mafarkai.

Kabir kasa zaune yayi ya kasa tsaye, wayar sa ya kuma daukowa yana cikin neman layin Isma’il sai gano motar sa yayi ta shigo cikin gidan. Kan kujera ya fada yana sakin ajiyar zuciya.

Da sallama cikin nishadi ya shigo cikin dakin. Kallon sa Kabir ya fara da tuhuma. Dariya ya saki yana zama a gefen sa yace

“Lafiya dai guy naga missed cal naka ba adadi!”

“Ina ka shiga”

Ido ya lumshe sannan ya bude yace

“Ina tare da Baby nane!!

“Wacce Babyn taka?”

“Wacce Baby nake dating now bayan Halima.”

Baki Kabir ya tabe. Zama Isma’il ya gyata yace

“Aboki karshen tika tiki tak fa!!

A zabure ya juyo yana kallon sa cikin wani irin yanayi yace

“What did u mean!”

“Yau na san Halima mace, aboki baka ji yadda take ba ban taba haduwa da mace da ta kai ta ba 100% and kasan kuma me? Uhmm……”

Da sauri ya mike dan ji yake kamar yana caka masa wuka a kahon zuciya yace

“Malam shut up ace ka rasaa wanda zaka zo kana fadawa shashancin ka sai ni. Wai kai wane irin dan akuya ne. Haba Isma’il yarinya she is innocent amman sai da ka cuce ta. Shin wacce ribar zaka samu……”

Numfashin sa ne ya hau daukewa saboda tsabar bacin rai ya fada kan kujera yana danne zucyar sa idon sa jajir dasu. Isma’il ya tsorata da yanayin da yaga Kabir dan bai taba ganin sa a irin yanayin da ya ganshi ba.

Mamaki ya kamashi dan Kabir yasan yana neman mata amman bai taba shiga wani hali ba sai akan ya bata Halima ko dan ya ga halima ba ruwan ta. She is innocent as he say.

“Am sorry friend ban san me yasa nake wadan nan abubuwan ba.”

Wani kallo Kabir ya aika masa dashi yace

“Tilasta ka akai ko me? kana da kudin dazaka auri mata hudu, ko baka dashi?”

“Ina dashi Amman…..”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *