SAMU
CHAPTER 3
Anan na ajiye kan dinning na wuce na koma daki nayi kwanciya ta.
Wani zuciyan yace kar na sake na fara daukar wannan salon iskanci
Wani yace min to me zakiyi musu in ba dai takaici kike nema makan ki ba ki barsa zai gaji ai ko giya ne komin karfin sa dole ka ya sake sa wata rana ..
A hakan Har nayi bacci na bai shigo ba..
Yau da safen ma ko kula ni baiyi ba ya fice..
Alhamdullhi, yau kam kwana uku ya kare tun da ya tarkata ya koma dakin ta ban sake ganin idon sa ba sai da ya dawo daga office around 6.30 na yamma..
Nan ne na lura da wani abun mamaki, ni dai tun jiya nake ganin ta da wani riga da skirt na atamfa shine kuma ajikin ta har yanzu bata sauya ba, sai dai bata daura dankwali ba ta fito daga daki ta same sa har yayi wanka yayi isha’i.
anan yayi zaman sa akan dinning shiru ba ajera komai ba data zo saita zauna gaban sa sai yauqi take ba har Ya gaji ya tambayar ina abincin sa?
Tace Abinci kuma desire??? Uhmm wallhy bana jin dadi shiyasa ban yi ba ..
What? Me kike nufi da bakiyi ba wallhy yunwa nake ji zuwairah,…
Ta dan sauke karamin tsaki cos habit dinta ne, nace bana jin dadi jabir wallhy bazan iya shiga kitchen ba …
Batare da bata lokaci ba, yace”To ya zakiyi dani?wai ma meke damun ki bayan gaki nan garau nake ganin ki, ta dan daure fuska tace baya na ke ciwo..
“baya kuma? Ohh uhh god shine ko dan indomie bazaki iya daura min yanzu ba..
ah’a gaskiya ni bazan iya ba,to ka fita mana ka siyo gaskiya ni baya na na ciwo bazan iya komai ba.
Ta turje sam Haka suka yi ta
“Hmmm ya dawo ya sauke ajiyan zuciya, ya daga wayar sa kamar zai kira amma yasan sam baya cin abinci a wajen sai ya kuma ajiye wayar ya kure ta da kallo ..sosai cikin sa ke kukan yunwa gashi ya sa rai yau zaici abincin amarya for the first time..
Shikam har ma ya manta da yanayin da ya zo ya same ta, ba kwalliya ba komai alaman ma bata yi wanka ba tukun..
Amma ya marairace yace , ni gaskiya ki san yadda zakiyi da ni i dont eat out, ki dai daure kinji desire ko dan indomie nasa abiki na pls..
ta dan ja jikin ta ko kallin sa bata yi ba, cos ita daman in ana lallabata take jin kanta na hawa..
Lokacin ni kuma na ajiye plates din abincin da na gama ci kenan a kitchen doya da miyan kwai zan wuce na je room dina ban ko juya na dube su ba
Ta dube ni a fakaice tayi saurin dada tamke fuska ta soma magana kamar bata ma lura da ni din ba” tace rashin lpya fa nake yi jabir,…wallhy baka da imani ta sa muryan kuka
Ni gaskiya bazan iya ba kawai ka sa wani ya maka tunda bazaka siyo a waje ba..
Ta mike ta wuce daki ta barsa anan…
Ina shiga dakin ko zama banyi ba na ji ya ya shigo, yace samha”na jiyo na kalle sa daganan bance komai ba..
Yadda na daure fuska ya sa shi dan jan lokacin kafin Yace akwai abinci a gidan ? Nace ehmm akwai…
ya dan yi shiru daga bisani yace get me some im hungry…
nace ai ba ayi ba tukuna,
Cikin karfin haki ya ce ohhh, don bayi ba shine ni bazan ci abinci ba ?
Nayi masa shiru na dada daure fuska ta ..cikin kukkuni nace ai ba mani zakayi ma wannnan tambayar don ba bani ce da girki ba
Yana ji yayi kwafa ya koma yana kallo na”yace to ai shikenan Samha naji, zuwairah bata jin dadi pls get me somthing to eat tunda haka kike so nace miki..
Story continues below

Nayi shiru ban dai kalle sa kuma Banyi musu ba na wuce naje kitchen din, minti kadan na dawo mai da indomie da daddafen kwai..
“Tsaban yadda yunwa ta cinye sa bai tsaya mun wani tsegeran ci ba ya zauna tass ya lashe har yana zufa..’
Kofar daki na na rufe na yi kwanciya ta ina juy8,
dariya abun ya so ya bani i just wonder if jabir is possed akan yarinyar nan.
Washe gari da safe wajen karfe 8 na fito har nayi breakfast na koma still bata fito ba sai naji knock a kofar falor , ina kan kokarin kama handle na bude sai naji muryan sa nayi mamaki dama har yanzu baije aiki ba..?
Thats none of my business na basar, na kama kofar na bude
‘Da gudu ta rungume ni nace sis zainab?
Sannu da zuwa na kamo ta nace im sooo happy to see you…Itama sai faffadan murmushi take sakar min tana miko min bags din ta,
Nace”shigo mana sis, shigo ciki ya hanya na dada a jawo troleyn ta ciki tana bina da amshi cike da fara’a..
Zaynab step sister jabir ce amma su suna zama a sokoto ita da mijin ta …
Jabir Yana mugun kaunar ta cos ita ce kawai ke iya sauraran sa most of the time in yana cikin matsala har ana ce musu twins..
Naji za’a yi wannnan nidai Kar dai na dawo na same ki kamar jiya, kinji na gaya miki…
da masifa ya fito bai ma gan mu ba..ita ne abayan sa da nitiyn ta sai yauqi take tana yatsine.
.
Jabir?sis zaynab tace da murmushi na wuce gaba na basu waje.
Tuni mood dinsa ya sauya ,yace ,Oh my god zainab…ure soo welcome yaushe kika taho toh, why dont you call me ya dan dada a rude..
Tace”Comn quiet,ai nayi ta kira baka dagawa me kake yi har yanzu agida na dauka ai kana office ..
Ya ce ,oh yea im late wallhy, ke dai yanzu ki huta bari naje na dawo..
Suka yi sallama zai fice , yace pls sis ki dan turo min samha ,tace toh ta shigo ta same ni har na ajiye kayan nata tace naje yana kira na
A tsaye nagan sa yana kan duba agogon sa a matse , nace gani..
Uhumm, zuwaira zata je asibiti jikin nata ba kanta sai ki taimaka ki mata abubuwan da ya kamata….ni na tafi.ya juya abunsa bai ma jira amsa ta ba..
Cikin raina Nace kutuma hmm lallai ma jabir zaka zo ka same ni..
Anan dai na kauda maganan na zauna ina entertainh din sis zaynab..
Har wajen 1.30 na rana munyi sallah munci abinci
Sis tace, wai ni har yanzu amaryan bazata fito mu gaisa bane?
Da shike mun saba sosai da sis nace zata fito mana skika sani ko ciwon amare ne ya boye ta ?
Tayi dan murmushi tace, hmmmm samha ai naji anata labarin ta ne nidai ban yarda ba amma ai dole na tambaya tunda na zo har yanzu bata fito ta duba ni ba..
Nace ,ah a sis hwanda ma da baki yarda ba, yanzu halan ma bata sani ba ne don jabir yace bata jin dadi sosai shiyasa ma ki kaga nayi mata girki..
tace aiyo to why not ki kaini na duba ta..
Nace to shikenan nan muka mike…
Zuwairah Waya take yi sai tambade dariyar ta take ,daga nan bakin step din kofar corridor munaji amma sai muka basar,
Muka cigaba da hirar mu muna tahowa..
Story continues below

Salam alaikum, sis har zata shiga na riko hannun ta alaman mu jira ta amsa…a hujajan ta ajiye wayar cikin gatse da kaurin murya tace ni waye ne kam?
Sis ta budi baki tana dubana ,
nayi sauri nace mune zuwairh, samha ce,.
tsakin nan dai ta sake saukewa sa usual tace ok..
Muka shigo..
kallon yanayin dakin ya hanani sakewa na sake magana ga nan gadon a wargaje babu gyara da duvet din alamar anan take kwance tuntuni..
Gefe guda Ga nitin ta da boxers dinsa nan ayashe kasa gefe da gadon kai kayan kan mirror ta ma a warkaje yake bare aje ga jikin ta,
“Ina kwana, ta daure tafada cikin daure fuska cos ta san yanayin da muka ga dakin ya sa mu yin shiru.
Nace lpya na dan taba sis da tuni ra shiga duniyar tunani muka karasa zan zauna sis tace ah’a kar ki zauna samha ai ba dadewa zamuyi ba..
Nace ok, ganin bazata gaida sis ba nace zuwairah wannan fa step sis din jabir ce ta zo daga sokoto, tana so ku gaisa…
Ta dan watsa mana harara duka tace ehmm uhumm to sannu..
Sis tace tabbb, sannu? Nayi saurin mata ido sis ta dan kada kai tace, ok sannu kema
..tace yawwah ,
Dan shiru ne ya ratsa nan sai tace uhmm ni bacci nake ji dama zan kwanta,
ta kau da kai tana dan jan qamshi,
sis ta tsaya kallon ta tana tabe baki
Nace “ayyah ya jikin to,
tace da sauke nace to Allah ya kara sauki
sis bata bari na sake magana ba tace samha muje ko
Nace ok..
Muka fice sum sum a dakin
Tsaki ta ja ta koma kan wayar ta ta cigaba
Tunda muka kai site dina sis ke masifa tana maganganu “ni ai ba sa’ar ta bane wallhy ko shi jabir ma na girme sa da watanni har takwas bare wata banzar yarinyar da zai kawo cikin gidan sa..
In banda hakuri nidai ba abunda nake mata..
Duk na kawo mata cewa ai amarya ce kuma jabir na kokari duk kuma hakan normal ne a farkon aure.
sis tace sam wannan ba ta da da’a shima zai zo ya same ni..
Wani za agwada wa raini wata kazama ma da ita..
nace shhhhhhh sis dan Allah ya isa haka..
Hakan muka zauna nayi komai a yadda na saba yi,
Yana dawo yau yasan baida matsalan komai don yace nayi girkin
So wanka yayi yayi sallah ya kimtsa ya fito,
Zaune muke tara da ita yau kam am sa mu saiya sutura , wani dogon rigan kanti ta sa kalar orange ta taho ta zauna dab da shi a dole itace mai miji,
Shikuwa ganin idon mu da sis Sai neman batsarwa yake amma ina , in tayi tayi sai yace mata zuwairah sauki ya samo kenan ko?
Tace ah a, desire har yanzu inajin kashin baga na na suka.
Sha’awar naci abincin kawai ya sa na fito dama ni banci komai ba tun da ka fice,
..dukan mu muna shiru ta cigaba da zuba mana ruwan iskan ci da kisisina ko magana yake da sis sai ta daure fuska ta shiga tsitt da yawo tana tsaki
Anan ma ran sis ya dada baci har ta tashi ta bar dinning din tun kafin ta koshi
Ko ajiki na sai da nayi nak kafin na tashi na basu wuri..
Sauri take tajeta dan kwashe kayan dake wargaje akasa kafin ya shigo ya gani don haka bata ja shi sunje dakin ba kamar yadda ta saba..
Story continues below

Yana shiga dakin sa sis
Ta biyo sa..yace my siis kece ashe dama ina shirin..tace stop jabir, ya isa haka wallhy raina ya baci.. ta daure fuska
Yace ah’a twin sis yau kuma me nayi miki, tace jabir how cud you ?
Me wannan nake gani agidan nan wannan ne matar da ka kawo mana
Sai rainin tsiya da rashin da’a..
Yace pls enough, ya isa haka zainab what rubbish..
ohhh kinje ana gaya miki karya da munafurci kinzo zaki haura kai kema ko?
Sis ta dada bata ta kai tace”munafurci?kaima ma kasan na fi karfin wannnan am talking about waht she did to me ..nan ta dan gaya masa abun da ya faru..
Ya ce to sai me..she is sick kema ai kince samha ta gaya miki..
kawai ki saurara In ta warke zata miki yadda kike so but for now im tired
Ni bana son fitina pls leave me alone..ya daure fuska ya juya mata baya …
Tace jabir hakan ma zaka ce yace yes..
Kawai ki je sai da safe..ta jiya a zuciye ta bar mai dakin..
Iya hakuri na ba anty amma sam taki akan cewa gobe zata bar masa gidan sa tunda bai ya ganin rainin da zuwairah ta ke yi dama don ganin amarya ya sa ta zo cos she dindt attend the weding
Washe gari Da safe ma hakan ne ya faru cos agaban ta yace na sake yin girki ma zuwairah…
ban ko amsa ba ta cafke tace masa bazan yi ba ai tunda zuwairah na da karfin kwana da shi ta fito tayi abincin ta…
Sis ta kasa gane logon abun nasu sabida ta riga ta harzuga da halin zuwaira sai ta rika masifa cikin bacin rai tana gaya masa bakaken maganganu
Daman zuwairah na nan daf abayan sa da shike a falou muke
Anan ta sa masa kuka ta soma cewaa ai dangin sa sun tsaneta basu tausayanin ta,gashi bata da lpyaa amma ana zagin ta , an juya musu kai akanta an sa sun tsane ta,
Anan ma ya tsaya ya zuba ma sis rashin m..
ni kaina nasha mamakin yadda jabir ke cire jijyan wuya akan kar sis ta sake shiga harkan matan sa.
Ni ma bai barni ba sai da ya azalzala min cewar sa bani da imani kuma idan ya dawo banyi abunda ua sani na zan ji ajiki na…
Ya wuce ya fita
Kuka sis ta rika yi tace samha?wannan jabir ne yaushe ya dawo hakan? Har da cewa zakiji ajikin ki, samha gaya min gaskiya jabir din dukan ki ya keyi?
na damu matuka zan yi magana ta dada borewa tace
Shi din waye da zai ajiye wata yana kwana da ita ke kina musu abinci ?
A sanyaye Nace kiyi hakuri sis,yanzu ne,kuma na farko ne kawai amma sam sis taki ta bar maganan tayi fushi sosai sai surutu take
Daga bisani ma ta tattara kayan ta ta wuce tasha..na roke ta har nagaji hakura na kyaleta na dawo gida…
Abubuwan na damun sa
..amma hakan yake dannewa abtunanin sa daga yanzu zai sa ido akan zuwairah sosai don dangin sa kusan kaf din sun nuna masa bata da tarbiya
Amma babban problem din shine baya son ya dago magana ta hana sa sex in yazo neman ta.
Nikam tunda lokaci na san akwai babban yaki agabana don kuwa bazan dauki yi mata komai ba tana kwana da miji ta samu bakin raina ni nan gaba ba..ance icce tun yana danyen sa a ke langwasa shi..
So yau Ina gama shirya abinci na yi zaman diris ina jiran sa ya dawo ayi ta kare …
Ko da ya dawo Bai kula kowa ba ya shiga ya kintsa tsaf ya zauna ya ci abincin sa …ko loma biyar baiyi ba ta fito stil ta sa nitie as usaual ta fara karo masa kwarkwasa yana shiru dai bai bata fuska ba don tunani sun soma yi masa traffic tunda ya lura cewa zis zainab tayi fushin dagaske ta bar masa gidan
…hankalin sa ya dan tashi amma yaki ya nuna sosai..
Amma chan dare ya ja wajen 12 ta ja shi jikin ta Ba don ya so ba haka ya biye mata suka kwashi gara anan falo kafin cahn dare ya shigo daki na…
Banyi bacci ba don haka ma mike na zauna..
Zai ja bargon ya kwanta na kwace nace ina da magana da kai jabir,
Fuska ba yabo ba fallasa Yace ok, ina jin ki..
Zan yi magana ya dakatar da ni da cewa kar ki bata min lokaci samha just go straight to the point
“abun ya sosa min rai Nace kayi hakuri jabir bawai bazan maka biyayya akan abubuwan da kake so bane,.amma gaskiya maganan Wani baida lpya wani yayi girki bazan lamun ta ba nayi na karshe kenan don haka kasan nayi..
Yace what? Akan me..meye amfanin zaman ku ku biyun idan bazaku taimaka ma juna ba…
Na mike tsaye na kalle sa cikin azamaan da ya dade baiga nayi irin sa ba..
nace badai zan dauka ba jabir kasan bana gaya maka magana akan son raina sai dai don samun ciganban zamn lpyar mu ko..
Nima nan ina fama da lalura dauriya nake yi nake aikin gidan nan..duk rashin lpyar da matar ka take baza dai a hada shi da wahalan da mai juna biyu ke sha ba juna biyun ma na wata 7 a gaskiya bazan iya ba..
In har ka na so ana taimaka mata tun Wuri ka nema mata mai aiki nikam na gaya maka,
nayi shiru na daure fuska ta tam bana ko kallon sa bare ya dame ni
Yayi shiru, yana kallo na hakikanin gaskiya ya kasa kawo points sai yace hmmm kya ji da shi dai samha.. Akan nace kiyi girki kike gaya min magana haka?
To Duk dai munafurcin mutum haka zai ganni ya barni..
Nace ohhoo dai, ni dai na fada maka kenan…
daga nan na wuce na shiga batrum na kimtsa kaina na fito na kwanta..
Shima bai kula ni ba Tun daga wannan rana ban sake gane ma jabir ba banda wukakanci ba abunda nake karba wajen sa..
Ranar da zuwaira ta karbe girki dafarko yana ta zumudi,
amma daga bisani hatta kitchen din sai da yasa akayi masa spray saboda wariin kaurin abinci
Soyayyen ko dai 8nce konananen plaintain kuma an zubar da shi ya kai sau biyar a dustbin a haka ya hakura ya dafa indomie dakan sa ya ci
A ranar Kuka ta dinga raira masa duk dama ya gano ta sosai kamar fa bata iya girki bane,.. amma sai ya so maida masifan kaina ba gaira ba dalili.
ba komai bane illah yasan yanzu nace bazan taba karba mata abinci ba.
Kullum idan kwanan zuwairah ce wajen girki sai ansha da shi amma bazai taba mata agaba na ba sai sunje daki
Nikuma sai ya sauke min borin yunwar nasa a kaina
Ya ci min fuska agaban ta iya son ransa ..
Nima hakan na turje bana taimaka mata da komai din..
Tun Da na soma i don’t care attitude na kuma dauke kai akan kowa da komai agidan shima sai ya dage wajen sa kafar wando daya dani
Duk dama Dan dolen sa ya sa zuwairah agaba ta soma daukar ayyukan gida kamar yadda nima zanyi na gama haka itama ta fara in kwanan ta ya zago.
Daga nan Sosai halayen zuwaira suka soma bayyana min karara kamar daman dai nine ban san yanayin tsananin kazantar ta da ballagan cin ta ba..
Gaba daya tiles din kitchen ya soma dishewa yanzu ni kaina nakan sha wahala kafin na tsaftace wasu abubuwan da muke using tare ,.
tukun ya duk da kowa da nashi ne amma har ankai biyu daga nata bola saboda tsaban yadda ya kone ya yi loosing qualitin sa da baki ..
Gashi In tana girki har tsoro nake,hankali na baya kwanciya kar wata rana wuta ya kama mu don ko wani abinci bul bul zata bul bula masa wuta kamar tana filin yaqi,
Wanka kuma kamar akuya haka suke da ruwa wannan ma bai dame ni ba kamar yadda ta nace da yawo a gidan da nite gown tamkar wacce ba a kawo ta da kayan akwati ba in tayi ne ta dan dauro zani akai .
Bangaren jabir kuwa sam ya kasa samun nitsuwa shi yanzu ba ma rashin girki ke damun sa ba…
Da chan ya dauka gajiya da ciwon bayan da take yawan complain yasa bata tsaftace wajen amma ya lura kamar habits dinta ne
Gashi bata son sallaj..wankan tsarki ma shi ya dauka makan sa alhakin in sun gama sex ya shiga tare da ita ya sata tayi yana dubawa,
Yanzu kam har ya saba da yadda ya tafi ya bar dakin haka zai so ya samu..
Gashi yanzu bai da lokaci
In yazo kawai sai dai yayi masifan ya bi ya karkade boxers dinsa akasan floor ya kaisu dakin sa ya tara ita kam bata ma daga nata bare na shi…
A duk lokacin Dayayi mata wani masifa mai tsanani haka fir zata hana shi sex tayi ta gaya masa bakaken maganga nu…
A hakan Babu yadda ya iya, sabida yanzu yayi zuciya bayayi da ni, nima na nuna masa tafi nono fari,.
Shiyasa duk azaban wulakanci ya koma ya na dauka…
Haka zai lallabata gobe ma ba shi zai hana su sake kwabewa ba
Ranar Abun ya ishe sa
ina kwance naji shi,.
Ina kwance shiru Hannu ya kawo zai taba ni na firgita na mike
Ya wani daure fauska Yace min meye haka..nace masa kar ya taba ni bana so..
Ya jawo ni da karfi, na gantsara maa cizo a hannun sa..cikin masifa nace ka tashi kaje chan inda kasaba ni ka kyale ni bana yi..
Ya ce bazan je ba anan zan karba dole zaki iiya min bukatuna ..na kan rasa irin rashin Kunya irin na jabir wai shin ba shi bane yake ce min yana da wacce ta fini akan gado?..ranar fa har gori yayi min akan zuwaira
….amma sai gashi yau ya dawo wai na bashi..
Haka muka dinga yi har ya karbi hakkin na shi as usual ba wani dadi sai tulin bacin rai,..
Story continues below

sai kawai na soma shiru shiru bana dai amsa shi,sannan zanyi masa abunda ya ke so muddin akan gado ne ban damu ba…
Don yanzu ma na dan samu sauki sauki bana jin yanayin da nake ji ada chan sosai ga shi ciki na ya girma sosai..
shima kwana biyun sai naga ya shiga hankalin sa baiya wani nuna min rashin hankalin sa a fili kamar da ,ina lura,.. it seems like zumudin amarcin ne ya dan fita ajikin sa
but we are not in good time ne yana harkan sa ina nawa..
Ana haka, ..karime ta kawo ziyara ma zuwaira niki niki da kayan mata a buhun bakko bag
Nice da girki..so ina kitchen a lokacin
Amma Dan wulakanci sai suka ki zaman dakin nata suka zo falo sai shewa suke suna hira kamar gidan kaji..
Yau abubuwan da suke faruwa wanda banjiba bansani ba sai yau naji a bakin zuwaira.
Kafff ta kwashe labarin yadda take cin jabir da yadda jabir yake mata itama akan gadon babu gargada babu kwana ta zuba ma karime
Tadi yayi dadi Har blackmailing dinsa data keyi in tana so ta samu cikar burin ta akan wasu abubuwan tace shi yake bata kudi take tarawa ta ke tura ma karimen ta mata shoping kayan mata daga maiduguri..
Inji ta wai komai ta sa ido a gidan
Musamman ma dangin sa da bata shiri da kowa…
In kuma yayi motsi ko takk yace sai tace bashi ba sexx..
tuni sai ya rusuna ya lallabata don ya san ba samu yadda yake so zaiyi awaje na ba..duk ta sa a cikin labarin nata
Karime sai hangame baki take don kuwa ta ji dadin abun aganin ta ai kwalliya ya biya kudin sabulu,
Tace to ita wannnan bushiyar fa me kike jira da ita..wato ni kenan”
zuwairah ta dan leko tayi dariya mai sauti bata ce komai ba, karime ta cigaba
Tace meye aikin ta agidan ko da shike ai ko da na shigo ma ke kadai nake gani fa,kawata kece star, full option, mowar mai gida, sukayi tafi zuwairah tace yesss ooo..fada da kaurin murya
Karime tace tabbasss ga mallakar miji ga shi dole yayi biyayya ai kema kinsan tamkar ke kadai ce to me ya rage..
“Tace dama fa,.in ba nikadai ba har na isa ina karban kudin kaya wajen sa kuma ya debo su loadi ya bani..ai kinsan girkin dayafi maka dadi konawa ne zaka kashe masa wajen kayan miya …
Ire iren hirar da suka yi kenan kuma ina jin su suma suna sane sarai da hakan,amma nayi kyam naki na bar zuciya ta ta debe ni
Tunda naje daki Zuciyan nawa ke bugawa ,amma bana so na bari ta dimauce da tunani nace ko da gaske ne jabir yana gaya mata banda taste kamar kwatami..amma meyasa zaimin Haka?
Abun ya mugun sosa min rai bana wasa ba…
Duk da ena fushi But i neva tot of na fara amfani da maganin mata irin nata sai na ce to shikenan zanje na nemi shawara in Har cikin ne har yanzu ke sani haka zan ti hakuri
In ba shi bane kuma sai na nami gyara cos na tabbata zama da zuwairah ba karamin jihadi zai zame min Ba nan gaba..
Haka na harhada naje aka sake duba ni amma babu komai normal nake haka ma abun ciki na….
na kuma nemi shawara anty hanifah tace min kawai nayi hakuri komai zai wuce..
na dawo gidan sai dai kamar an tsawwala komai ne ma bayan tafiyar karime da sati guda abubuwa suka dada jagube min
Jabir Ya soma nuna min karara zai iya komai akan dadin gindin zuwairah..
Har yake cemin wallhy shi yaa fara ganin kamar dama itace first love dinsa bai sani ba sai yanzu…
Raina yana baci amma Bana taba reacting in yana gaya min Magana baya kuma tashi gaya min Sai yagama amfani da ni son ransa .
In Ya fuce nayi ta kuka kamar zan cire raina amma nakasa gaya ma kowa komai…
Story continues below

Abu sai gaba gaba yake kamar wani tsafi Yanzu kam ma dan fadan kazantar da yake mata ya dena sai lallabi,
Ta samu dama yanzu sosai har aikin hidan takan sa shi ya yi da sunan soyayar gasu wai zasu sa min Bakin ciki,
To musamman in yana weknd dashi da ita ne a kitchen ko da kuwa ranar girki na ne duk sai su Kwabe waje .
Gudun raini da bakar magana ya sa na fita hanyar su bana tankawa har suci su kare….
Zuwairah ta dada bankadewa A kullum yaumin wani sabon sara take fito wa da shi na wannan karon yafi tsamaro don karara take gaya masa ya bata kudi ta tara na siyar kayan aiki…
Shi dai yana so ya san meye ne don inta siya bata nuna masa wasu abun sai wanda taga ya mata..
Gashi sam bata san me ake nufi da cewa nagode ba, sometimes in Ya bayar ma sai ta yi complain din Baza su ishe ta..
Duk yana hankare amma rudin zuciya da dadin gindin zuwairah ya shagaltar da shi baiya iya tabuka komai sai abunda tace mafi akasari…
Ina gefe Duniya tayi min zafi
Cikin raina babu dadi sosai na soma ramewa
Abun ya ishe ni ,..
yau ana saura kwana Biyu na shiga wata na takwas na yanke hukunci na je dakin sa na same sa da sassafen Allah…
Hijabi na sanya mai kyun tsari picth wanda ya dadaa fitowa da hasken fuska na..
Na yi sallam a ladabce na tsuguna gaban sa ban damu ba duk da ma bai amsa ba..
Nace ina kwana jabir,…
Ya nemi waje ya dake yace to, lpya kuwa?
“Na dan sauke kai na kasa nayi shiru na dan lokaci guda zai yi magana na dago cikin wani irin sigar yaudarren magiya cike da nadama nace dan Allah kayi hakuri jabir ka yafe min…
” yana kallona shiru,..acikin ransa Sai ya rude ya rasa me daya zaiyi, gaba daya ya kasa kamo komai ba wani bangaren ransa ya kwanta don dama so yake nayi masa hakan tuntuni na amsa nayi masa laifi akan komai shine da gaskiya,
Sai dai wani bangaren ya san ya zalunce ni sosai ya kuma ci amana na..
nikam na qudira zan saukake komai tsakani na da shi koma yaya ne na amince aje hakan..
don gidan mu nake so na tafi gaba daya nagaji da zama da shi amma bana so muyi rabuwar a haka im already feelling miserable zaman da nake a karka shin sa..
Haka na cigaba da kuka agaban sa ina kawo kalamai nasu taushi masu kashe zuciya..
Karshe dakan sa ya dago ni daga kasa ya zaunar da ni bakin gado ya kasa cewa komi,
Sai ya isa haka samha ita ok,
Ai Magana ya wuce a waje na..
Nasan tausayi na kawai yaji da hakki na dake binsa
Ban damu ba na share hawaye na nace na gode..
Nayi masa alkwarin bazan sake masa abunda ya saba zaman auren mu ba..
Daga nan muka dawo normal sai dai shi ya ke shan wahala sam ya kasa sakewa da yadda Na dawo da kaina tamkar baiwar sa sai yace nayi nayi bana kuma fasa zuwa gaishe sa da gyara masa daki da sauran su..
Na dada dawowa sokuwa agaban idon sa dama chan bana shiga hidimar zuwaira,ni ka dai nasan me nake ji a raina
Sati guda Kawai nayi hakan Na lura ta sha jinin Jikin ta,duk da bidirin haukar na su sai ya dena bari suna yin wasu abubuwan a inda zanji ita kuma ba hakan takeso ba…
Yanzu baya min Fada ko tsiwa agaban ta
A cikin na sati biyun kawai sai ta soma kawo bori ba gaira ba dalili..
Haka kawai in ya sani masa abu misali dauko masa ruwa ko wani aika sai ta zo ta bangaje ni amma itace zata fada kasa tana zagi na…
Ni dai bana amsawa muyi tayi,.amma guda daya in na gaya mata har hawaye takan yi yakan mata zafi sosai.
Sai dai bata fasawa Abun mamaki ranar dakan sa ya karbe min baki yayi mata tas tas yace bazai lamunci raini ba kuma ya soke hakan agidan sa…
Ranar ta sha mamakin sa matuka .don masifa yayi kamar zai wanka mata mari sabida abinda tace min..
Itama ta bore Tace masa wallhy shi da zaman lpya agidan sa ya kare kenan Tunda ya bi baya na ba irin magangan da bata fada ba..
A lokacin Ina shiru agaban su ina kwasar points a kwawalwata washe garin ranan ne na samu dama na gaya masa qudiri na na cewa ina son haihuwa ta ya kasance achan gida gaban iyaye na…
Yaki har yaki amma Na kawo masa reason cikin salo na dana saba ..na nuna masa cewa zan taya shi ta kowa ni hanya wajen samun kwanciyar hankali da zaman lpya a tsakanin sa zuwaira.
Don haka ina ganin idan bana nan na wani lokaci wani abun tan ma Zai ragu zata fi samun nitsuwa ta saurare shi Har na kawo masa cewa ita zuwairh ma yarinya ce tana bukatar kulawar sa sosai ,.in ta na gani na kishin irin namu na mata bazai bari ta nitsu ba kuma duka alhakin mu nakan sa yayi hakuri ya bata dama a cikin kwanakin da bana nan ya fahimtar sa ita manufar mu..
na kuma nuna masa a shirye nake na zauna da ita lpya idan na dawo daga jego bazai taba samun akasin haka ba.
Yaji dadin wannan shawara tan amma bazai iya nuna min sosai ba sabida kunya na ya soma taba ransa..
So har zan iya saurin mancewa sa abubuwan da ya min so sooon na daura makai duka laifin kamar ban damu ba?..
Kawai sai ya bani dama naje gidan na haihu zai duba ya gani..
Naji dadi sosai na je na shirya na sanar da su mumy
Washe gari da safe ma Na fito ma zan tafi naga ya shirya…
Yace shi zai kaini har kaduna…
Ban yi musu ba duk dama Allah Allah nake na rabu da shi don wallhy bana kaunar gani fuskn sa..
Sosai nake so na rabu sa shi na huta ma raina
Na daure nayi na mata na buga sallama daga bakin kofar ta amma
Zuwaire ko ta leko bare ta amsa ni har muka fice
A motar nasa zan iya girka sau nawa mukayi magana har ya kaini gidan mu..
Hira sosai suka yi da su mama da kowa da kowa kamar ba abunda Yake afkuwa a gidan mu
Su mumy har da bashi tsaraba ya kawo ma amarya…
Sai wajen asr ya tashi tafiya anan na ya dauko 50k ya bani ya kama gaban sa..
Wani sassanyar ajiyan zuciya nayi
Na gode ma Allah.
Kwana biyu kacal nayi agida amma an dame ni da tambayar ya na rame amma haka firr naki fadan komai har mumy ta kyale ni akan ko cikin ne ya jeme ni..
Ni dai yanzu tunda na bar musu gidan zan haihu gaban iyaye na shikenan Banida da case.
Kafin nan ranan da ya kaini gida dawowar Sa
Ya zo ya samu zuwairah ta hada tarkacen ta wai zata bar masa gida…
Tun Daga kofa ya soma salati, tana shiru sai kada kafa take gana watso masa harara..
Yace meye haka kayan maye wannan ?
Ta mike tsaye ta watsa masa mugayen kallo tace hey malam dakata, dama kai nake jira ka sauwake min anan zan bar maka gidan ka
..munafuki kawai azzalumi,macuci ta watsa masa harara tana dirin masifa mai zafi..
Tsayawa yayi a daskre zai yi maganan ma ta katse sa tace kai tsaya.
Zaka bani ta karda na ko sai na nuna maka asalin wacece zuwairah?
Ke baki da hankali ne
kanki daya kuwa..?
Tace ban sani ba ni dai ka bani takarda na ehe,…bazaka raina min hankali ba ni fa ba kamar wancan abun da ka ajiye agidan ka bane..
Ta cigaba da diri..
Ya so yayi masifan shima amma sai ya tuno da maganan da nayi ta masa a daki jiya akan yarinta da kuma kishi ke damun zuwaira ya sa ma ranshi ruwan sanyi ya tarbiyan tar da ita
A yanzu dai shi ya kamata ya nuna mata hanyar zaman lpya..
He knows he need her ko dan bukataun sa da take biya masa sosai yadda yake so..sai ya sa aransa kawai zai kawo gyaran no need for tension..
Bata hankara ba taji ya kamo hannun ta yayi daki Da ita, bawai bata tsorata bane don duk iskancin ta tana mugun Tsoron duka amma tsaurin ido ya sa ba a ganewa..
Yana kaita nan dakin nata ya birkice mata da wasu irin launin romance ita kanta ta kasa kamo setin tashan sa…
Yana shafo ta yana sumbatar ta ta ko ina sosai tun suna tsaye har suka zube kasa..
Wani ihu ta buga mai dauke da dandanon dadi jin yatsan sa yakai kan hq din ta ta dada kan kame sa,aransa yace in kin san wata ai baki san wata ba ni ne zaki dauko min salon tashin hankli
Hannu ya dada cusawa yana fingering dinta ta cikin pants dinta..
Kafin ta tashi ya riga ya koma dakin sa yayi wanka har ya kwanta bai tashi ba sai da yaji muryan ta a kansa..
Jabir ka tashi, ni ka ka tashi
Ta dan daure fuska tana shagwaba…
Bayan ya tashin Mika yayi ya mike zaune yana kallon ta ,yace yaya dai madam har kin tashi?.tayi masa shiru zai kamo hannun ta tace
Ni ka kyale ni wallhy fada tsakanin dakai bai kare ba..
Ya tashi ya jawo ta kusa yace me kike so to?Sai ta kasa cewa uffan ba dan ba har cikin zuciyan ta ta fada ba ..dama so take ta kawo masa borin zata rabu da shi don ta maida shi don ya roke ta ta zauna sai ta dawo da shi wawa shasha sai abunda datayi da shi akan jikin ta.. Gani take kawai ta mallake jabir..
Gashi ta daura kanta akan sabon tsari na maganin da karima ta kawo na mallaka,yanzu bata damu dana dadin bama tafi so ta samu jabir a tafin hannun ta sosai..
Amma yau din sai ya tsammace ta da wannan move din nasa batayi tsammani zai juya abun haka ba,
Yace haba desire calm down mana, to gaya min Me kike so..
Ta soma masifa, dama haka halin ku yake,namiji daga ya sami sauyin yanayi sai su nuna halin su ina nine har kake wulkantawa jiya a gaban wata ?
bai bari ta karasa ba .yace comn desire, wannan maganan ba ya wuce ba,.kawai nifa bana son fitina ne and nasha gaya miki bana son raini ko? nafiso ayi zaman lpya agidan nan ai haka yafi…
Ta dan murguda baki tayi tsaki…kawai kace ta karo wulkanci kana so ka juya min baya..
wato har na dena maka sugar ko jabir..ta dan marairace masa
Story continues below

Yace look ke yanzu in har aka fadi haka zaki yarda? kema kinsan bana hada ki da kowa duk duniya babu mai kamar zaqin ki da dadin ki..i dont mind yanzu ma ayi min ramukan gayya .
ta dan yi murmushi tace ohhhh dama bashi na dauka kenan ko?
Ta hauro sama zata same sa..ai tuni ya shako wani warin bakin atake yaji ya tafi offf sai ya dan tsime fuska ya mike tsaye cikin salo..yace tsaya muje muci abinci don gaskiya banda karfi yanzu..
Ya san zata bata rai sai yayi saurin kawo wasa cikin maganan yace yau dai so kike aga miji yana neman ceto daga hannun matar sa …
Ta mike tace ai to abincin babu kasani ban yi ba,.
Yace babu komai muje ki tayani na dafa indomie
Suka kai kitchen din tare, a haka ya soma jan ta da hira akan abuwa musamman ma girki..
Anan yake jin ta tana zuba har ya gane ashe ita kam zuwairah abun fa tun daga gida ya soma ..
wannna tallen abincin data yi da bin layi shi ya hana ta sanin komai a kitchen.
Ita dai ta je ta dawo taci in banda taliyan murji da yan kwabe kwaben kayan kwalam ba abunda ta iya…..
Shikuma gashi sam baicin Wayannnan …
Hade da ta zo ta samu waje anan din sai ta kara sama ranta son jiki da bin gado ana juyi da waya a hannu..
A daren ranar bayan sun kmmala cin indomie jabir ya fice majalin sa da abokan sa
Aka dan taba hira..yanzu kam tsokana ke shiga tsakanin su da su usman cos sosai jabir yake nuna musu yakai wani matsayi a fannin sex life dinsa tunda ya hadu da zuwairah..
Ana cikin hakan ma ta kira shi , ya sabulee jiki ya shiga mota yana tafiya anan ne shaukin ya kira ni yaji ya nake jiki ya kama sa..yayi dialing call din amma
Kamar ya yanke haka yaji amma sai na dauka…
Aladabce muka gaisa ..yana jira yaji nace ko ya isa lpya nayi masa shiru nace ya lpya dai ko da wani abu ne..yace a”ha ki gaida su mumy sai da safe na ce to sai da safe na katse waya na..
Tun daga ranar shikenan jabir ya shiga wani irin rayuwa…
it seems Wannnan maganin da zuwaira ta soma using ba ordinary bace don Kuwa har da jinin al’adan ta aka hada shi kuma sha take yi ba ji ba gani kamar wani abun asiri ..
Akwai wani ma hayaki da sirace gaba daya ta gauraya kanta…
Shikan sa idan ya dosu dakin sai da yaji wani dummm akan sa kamar ciwon kai ko duhu..
Daga Ranar ne ta zage ta nuna masa kwarewar ta fiye da kullum ya dauka ko don duk kwanciyar hankalin yanzu bana nan ne,.
Amma ita kadai ta san tarkon data ke so ya haura kai..
In suna yi Wani irin dadin baki ke deben sa…sai ta kama bakin sa ta toshe sai kuwwwa yake yana
tumbatsa,cewar sa in ta rabu da shi mutuwar sa ya zo..tafadi duk abunda take so zai mata a duniya..
A hakan dai ta daure bata tambaye shi komai ba a nata hikiman tana masa talala ne sai yayi zurfi ta ci uban sa
Don yanzu so take tayi masa mai kankat
Yadda karima ta bata shawara cewa in ta dage ta kama shi sosai sai dai a aika min da takardan saki ba dai na dawo gidan ba..
Toh she have to do what she have to do sabida kariman ma yanzu ta koma katsina basu sani ba ashe acan inna ta shirya za’ayi mata aure…
Sun riga munyi nisa yanzu na tabbata sai maganan waya..
Sati guda zuwairah ta dauka tana shiri tana kuma tana dada zirma jabir da salo na ban mamaki..
Lokaci guda ya dawo golo sai ta ce yi bari, ko yi kafin ya motsa
Yanzu ma cikin salon nata in tana zaune a akan kujera toh shi yana kasa yana danna mata kafa .
In tana kwamce yana sama yana danna mata baya kamar marar hankali..
Ga tsinannen kazan ta but sai yaji ya kasa tsawatar matan ma kwata kwata
A nashi banzan tunani gani yake tsantsar son ta ne ke sa shi aikata komai
Ai dama ance macen da ta ke jajircewa wajen biya ma miji bukatun sa tafi kowa kaunar sa
A wasa wasa ta dawo da shi kamar bawan ta,…
Dama Kitchen din mu tuni ya dawo kamar wani deen din masu naman kasuwa sai kudaje dake fita kan kwananuka ko ena yayi datti ba kyan gank altho shi yake dafa indomien yaci
Bai da time din Da kuma zai yi wani wanke wanken ko gyaran falo.
Ga shi yanzu baida bakin magana sai tace ayi a bari
In ya dawo kuma yana zama zata soma azabtar da shi da salon ta.
Ina sati na na uku a gida amma sau daya daya kira daga nan bai sake kira na ba..
Abun bawai baiya damuna bane aMma bana ko kwatan ta nuna ma kowa am forcing myself to feel ok while im not.
Da safiyar Allah ta fito tana kwance, sai danna layin kira take amma ya ki shiga
Nan ta buga tsaki tayi jifa da wayar..
Cahn ta mike ta shiga daki ta rarumo jakar ta kudin daya ke bata tasoma kirgawa ” saura dubu 150
Tayi tsaki..wai meyasa karime zata kashe waya wannan wani irin iskan ci ne tanayi tana huci tana huro hanci…
Gashi jabir bai dawo ba har ana neman karfe 9 da rabi na dare abubuwan suka cunkusu suka bata mata rai..
Can ta sa hijabi ko ena zata oho sai taji karar wayar ta na kara
Tana zinkayo sunan dake kira
A hujajan ta dauke tace”
Yar bur UbA har kin hargitsa min tunani tun safe nake naman ki
Karime tace ke rage murya, kina ina ?
Ta e Ena gida mana.
Tace yawwa bari na koma gefe
Ita dai zuwaira jira take, nan karime ta dawo tare da ajiyan zuciya tace ke
Tawa ta same ni,
ta gwalo ido waje ta ce lpya dai ko karime ?
Tace lpya amma kar ki daga hankalin ki na san wannan ba komai ba ne
Haba karime wannan wani irin maga na ne ki gaya mun abu mana..
Ana karime tace” kinsan bura uban da inna tayi min Wani banzan malami ta aura min anan katsina fa
aure? Zuwairah ta ce cikin mamaki,
Akan me laifi kikayi mata?
tace ke bani da wani sauran bayani..yanzu haka na fito ne a sace nake kiran ki…ki nitsu kijini da kyau zuwairah
Nasan ba lallai mu sake waya ba kinji dokokin zaman gidan mutumin wane fir’auna..dole nayi a hankali
Cikin rashin jin dadi zuwairah tace
To me kike nufi kenan karime nifa gashi na tara kudi zan baki ki karo min kaya satin ukun nan wallhy nayi amfani da su dayawa duk sun ja kqsa..
tace amma kina samun biyan bukata
tace eh sosai ma . Yawwwa yawwa to ki mance dani kawai zuwairh
Ke dai kiyi amfani da damar kin anan kano ma akwai masu kayan irin namu har online ki duba..
Incase idan baki ganni ba ki shiga kasuwa dakan ki..
Zuwairah bata ji dadi ba amma ta daure ta amsa da to.
A haka suka yi bankwana Basu ma yi sallama ba karime ta kashe wayar ta
10.0pmJabir ya kammala don yau Wani contracts ne ya taso masa ya tsaya jajircewa akai yana aikin sosai..
Bai neme wayar sa din acikin hanklin sa ya kashe ya san idan zuwaira ta kira ko da baiso ya je haka kawai zaiga ya tashi ya je..
Abubuwan sun dame ta sosai da dai tafi jin dadin
Ace tana gida tayi aika kawai akawo mata magani gashi yau an rabata da karime..
Ko ena wannan yaje oho? Tafada tana sake danna layin sa just in time ya bude kofar,
Kallo ta bishi da shi, alaman gajiya duk ya bayyana a akan fuskan sa maimakon ta sa fuskan rahma sai ta kawo na bacin rai ta daura..tace
Daga ina kake?.ta dake tana challa masa harara
Murmushin karfin hali ya kufce masa bai amsa ba ya karaso shigowa ya ajiye laptop bags din dake hannun sa,
Wai shin ba daki nake magana ba dubi fa karfe kusan 10 da rabi yanzu ne lokacin da zaka dawo min
Ya dan dube ta, fuska ba yabo ba fallasa yace to sannu mai gida zuwairh‘ ba sannu da zuwa ba komai zaki haura min da fada lpyar ki kuwa?.
Ta dan yi tsuka mai dauke da hartzuka zata sake magana ya dakatar da ita..yace
Zuwairah bana son fitina na gaji..aiki suka yi min yawa bani da lokacin wani magana yanzu
Ya wuce dakin sa abunsa.
Wanka ya fada, ya dan kimtsa kansa kadan ya fito bai ganta ba yasan tayi fushi ne,.ya shiga kitchen as usual babu komai ..anan yayu durus yana kare ma wajen kallo.
Oh Allah na ko zan kawo mai aiki ne kawai,?.wannan datti har ina ?yafada sounding so disturbed..
Juyawa yayi ya koma ya hada ruwan zafi ya sha tea sannan yaji dama dama..
Yasan ba zai kwashe ta dadi da zuwairah ba so sai ya sake ransa ya dan huta kafin ya wuce wajen ta..
Yau kam ta dan tattara kayan da ake kunshe su akan gado kuma ta dan gyara gadon sai dai tamkar da ba agyare bane cos wani wajen yayi kasa wani yayi sama bedsheet din ma upside down ta sa..
Yana shigowa ta daure fuska ta juya masa baya
Gashi yanzu sam sam ya kasa gane ma hankalin sa a duk lokacin da ya ganta sai yana jin wani irin shu’umin shawart a gaba daya ya kasa samun control din kansa..
Haka ya daure ya sauke kansa ya yi lallami , laifin da bana shi ba sai da ya karba yace tayi dai dai da ta gaya masa hakan, shi dai dan Allah kar ta hana sa kwana da ita ..
Wani dadi take ji aranta kafin ta tashi
Zama tayi tana watsa masa mugayen kallo, tace wallhy bazaka ci ni ba jabir, tunda nice zaka na gaya magana son ranka
Wai kai wani irin marar hankali ne marar tunani? Ce maka ayi ni kamar matar nake da ban san darajan kaina ba..
Ya sunkuyar da kai cikin lallami yace kiyi hakuri zuwairah ai nace laifi na dauka ko pls can we go to bed now, wallhy na gaji kuma ..ta ce ya isa… Ena damuwar ka kenan mu kwanta yace ehm
Ta so ka biyo ni,
Ya mike madel madel yabi bayan ta..
Kitchen ta kaisa tace ,kaga yau wata banzar mata ta zo gidan nan duk adalilin ka tayi min deban albarka wai ita kanwar ummah .
Har da cewa ni kazama tana min gorin akan matar ka msssw,
yace subhallah waye wannan,kina nufin anty harira ta zo
tace kayi min shiru da Allah nasan kaine munafukin da kake gaya musu bana tsafta,tph da ni baiwar ku ce da zan na maka komai..
Nawa kake biya na da kake ci na kowani dare to wallhy bazan lamun ta ba in har yau kana so ka kwanta da ni ka wanke kwanakan nan tsafff gobe in ta dawo na gaya mata wanda ya kawo ni ya tsaftace gidan dakan sa ..ta ja tsaki
Nan Ya dago ido kamar shanyayye yace, haba zuwairah ya zaki na gaya min haka? wacece wannan din da zata zo ta hada ni dake …tace ban sani ba
Kawai kamin abunda na saka idan nayi bacci kuma wallhy kar wani yace zai daga ni eheh…
Kaiwa nan ta fice ta kyale sa..
Zugum yayi na dan wani lokaci cos sam sam ya dena gane makansa gaba daya in zuciyan tunanin ya zo masa sai yaji yayi sanyi kawai bazai iya rayuwa babu zuwairah ba saii dai ya bita a hankali.
Anan ya soma bude kwanukan da suka dade anan sink wasu ma its like sun kai 3 weeks din anan sun bushe har zun soma husa ta ciki
Ruwa ya bude akan saboda hamamin warin da yake tasowa na tsamin abinci wanda mafi akasari ma indomie ne
Gashi bai wani iya sosai ba albarkacin da cahn ya kanga yadda samha take yi, ya soma gano abubuwan
Sannu hankali sai da yay amai kusan sau uku kafin ya samo daman daurewa dishess din duka ya jera su.
Sai ya ji ya gaji,
Ga shi ya dauki lokaci sosai “
Ko kafin ya koma ta riga ta rigingine kamar wanda take bacci alhalin tana jinsa ….
So take ta tabbatar ta mallake jabir da jikin ta kafin ta soma baza asalin mulkin ta, aganin ta in ta karkare ko magana bai isa ya mayar mata ba nan gaba..
Haka kuwa ta hana sa taba ta ,yana ji tana gani tayi kwanciyar ta, gashi ya sha wanke wanke, ya kuma kwana da tsananin shawa’ar ta..SAMU YAFI IYAWA – passage 14 – Page 3
*🍒🍒SAMU YAFI IYAWA🍒🍒*
Passage 14
Ko da safe data farka bata gansa ba, shikam yayi shiri tuni ya fice office anan ma sai ta daura wani niyyar akan cewa zata gyara masa saiti akan hakan daga yanzu dole yana neman izinin ta kafin ya fice..
Dakin ta shige ta fara lalabun ledojin kayan maganin ta , gaba daya saura amfani daya su kare tsaki ta ja, don yau so take tayi overdose awuce gurin bata son mallaka na wucen gadi ta fiso mijin ta atafin hannun ta..
Nan Ta dau mayafin ta babu wanka babu komai ta sambada powder da jambaki ta kama hanyar cikin gari..
Ko da ta iso anguwar Wahtsap ta sake dubawa taga adress din gidan hajiya maman gayu da suka yi pc chats ,.
Nan saiga wsu mata su biyu dayan ta manyata sosai daya kuma budurwa ce kamar ita sai ta karaso ta same su.
Salam tayi musu suka tsaya,tace dan Allah ina tambaye ne
Ko nan ne layin gidan maman gayu?
Matar tayi dan yatsine mai dauke da murmushin ashe duk kayi daya muke…tace “eh nan ne..
Muma nan zamu je dayan budurwan tafada..
Ajiyan zuciya zuwairah tayi tace alhmdll,ahh toh naci sa’a, suka kama hanya matan suna shiru cos sun gane ita kamar ba yar garin nan bane..
Gida ne wanda ya amshi sunan sa na gidan ba haushe,sosai da sosai mata ke ta ambaki ana ta surutu kace kace, alamun ma fada akayi
Wata mata ne ke tsaye ana danne ta,sai zagi take kwarrowa
Dukan alamu kishiyoyi suka hade wajen siyan kayan mata, sai aka samun akasin munafurci da kutsiri tsomi na yan hada waje..
Daga gefe zuwairah tayi shiru don dama ance mata wannan matar ta shahara ,bisa ga dukan alamu shaharanta ya sa har ake mata cinkuso ga shi har ana fada,
Dadi ta ji aranta wani bangaren zuciya yayi sanyi dama ta gama daga hankalin ta akan rabuwar su da karime..
Wannan matan da suka shigo da su sai kallon ta suke, dayan ta kssa hakuri ta zo ta same ta,
Tace baiwar Allah amma ke bakuwa ce ko?.
Zuwairh tace eh ba a gari nan nake ba amma aure ya kawo ni..ta dan gyada kai tace ai naga alama.
Toh taso muje gefe
Nan suka kebe gefe guda
Anan ta soma jan zuwairah da hira tana gaya mata logon gidan maman gayu…”tace in kina son aiki ki zuba kudi, amma kika sake hajiya ta san ke mai matse hannu ce ba wani tasirin da zaki gani..tace Allah ko?
hira suka dan taba zuwairah har da mata kwantancen gidan ta kafin nan An gama sulhu an kama bin layin karban magani..
Matan nan mai suna maman abdu, ita ta ma zuwairah jagorah har da karyan cewa yar uwan ta ce, anan ta taimaka mata aka sake bata maganin mata amma na mallaka..
Abuwawan a leda ne kamar taura sun kai kwallo guda 50 tayi masa lakanin da cewa daga cahn kasar sudan ake samuwa siririn bakaken larabawa ne kudin sa dubu saba’in70.
A take Zuwaira ta fito da kudin babu wanii shakku sabida yadda maman gayu ke tsula magana da tsegeranci anan ya sa ta kasa nuna nata halin anan ma ta dada ganewa ashe ko agidan giya ma akwai babbba
Jabir tunda ya tafi aiki ya kashe wayar sa, it seems like in baya tare da zuwairah ba abunda yake damun sa normal yake jin kansa
Amma muddin ya zo gidan shikenan ya dawo soko dolo marar hankali.
Anan ma aikin sa kawai yake ba tsayawa dan dolen sa ya soma cin abincin restaurant…
Duk su usman suna lura amma ba wanda ya ce masa komai daga cikin su..
Zuwairah na dawo gida ta baje maganin nan a dan roba dama maman gyu tace mata ta tabbata ta shanye su tasss tasss yau sune abincin cin ta kar ta hada da komai..
Haka kuwa ta baje a falo tayi ta gamutsawa acikin ta baji gani , sai ruwan data ke dura makan ta
Abu gashi nan ba zaki ba ba bauri ba wani irin fatak..amma haka ta dura tsaban gajiya anan ta bar kwalleyan ta wuce dakin ta ta kwnta bacci..
Story continues below

Hakan yau ma da ya dawo da daddare shi yazo ya tattara wajen ta sa shi shara da kimtsi, kafin ta bashi jikin ta,
Da shike Abun ya hadu masa da yunwan ta da yake jiya, sai ya haukace mata sosai ta gama daukowa ko din karfin maganin ne ya soma aiki atake atake..
Daga nan ta soma bada karfi, washe gari ta sake komawa tace tana son abata dayawa wanda zata ajiye ba sai ta fito ba,
Anan aka mata list din kudi kusan dubu dari biyu da hamsin
Kudin hannun ta bai cika ba ta koma dakin sa ta bude drawer ta takato kan su ta samu kimanin 9ok ,
Ta shiga birkita ko ina sosai sai da tayi kaf kaf ma dan kudaden dayake ajiye a gida for emgency duka ta kai ma mman gayu aka bata magani..
Maman gayu Tace mata ba sai kin ajiye ba duka zakiyi amfani da su
Sai su zauna ajikin ki daram daram na tswon lokaci har shkera guda
Akwai wani ganyen da ssaken itace zata dafa tana sha tana wanka da shi babu sabulu.
Sai wani ruwan tsami shima zata tafasa shi tana tsarki da shi wai cewr su zai matse ta gam gam.
Sai wasu gantsaun kulli har guda biyu akan tana turare farjin ta da shi.
Unfourtantely sai gashi a washe garin ranar jabir yayi tafiya zuwa abuja.
Daga nan kuma zai je kasar waje wani aikin campaing na project din su very important..
Da kyar ta yi hakuri ta dena zagin sa akan hakan dayayi bai sanar da ita ba,
Dadin haushin hakan ya sa ta sa azama tayi dagaske wajen durje wayannan hadin ajikin ta..
Dama ai yace kwana biyar kawai zaiyi,
By then ma maganin ya gama jikewa sosai ajikin ta,
Sai dai fa cikin kwana biyu da ta shanye bata jin komai har yanzu in banda dan banzan kaikayin gaba da wani rin kona kona a kirjin ta…
Sam ta kasa samun sukuni sai juye juye take akan gadon ta ba adadi..
_Daga bangaren samha_ ,
sosai na soma warewa ina kai kukan na ma Allah sosai akan lamarin aure na.
Wani bin in ina addua na kanso bakin na ya furta Allah ya sa jabir ya aiko min da takardan saki amma sai na kasa yin hakan
A kullu yaumin ji nake is better na ce Allah ya zaba min mafi alkhairi akan nayi maganan rabuwan namu gaban Allah…
Komai na bar ma ciki na anty hanifa ma ban sanar da ita komai ba, baiya kirana amma kullum acikin kokarin rufa masa asiri nake don su mumy kar su sake tambaya na komai akan zaman namu.
Ciki na satin sa na kusan karshe , yau kwanan jabir uku a u k ina idar da sallahn isha’i, kirar sa ya shigo dai dai lokacin da anty salamatu kanwar mahaifiya na ta shigo.
Hannu na mika na dauka wayar naga nunber ya bambamta dana kasar na sai kawai na basar ban dauka ba,
Tace samha ba kiran ki ake yi bane wai..nace mumy bansan number bane inaga kuma bama kasar nan bane..
Batace komai ba ta cigaba da jera kayan da suka siyo na tatallin haihuwa na, duk sun sa rai ko yau ko gobe,
Kiran nan ya bi ya dame mu baki daya abun ya ishe ta tace toh ki dauka mana in ma baki san me kira ba ai kya sanar da su ko?
Nace eh kam hakane bari na dauka, na sa hannu a karo na karshe ya dauka tare da sallama…
Dan shiru ya biyo baya sai da na sakwecwaa salam alaikum sannan ya iya bude bakin sa ,cikin sanyin murya yace samha?
Wani rasss rass kirjin ya buga rabona dana ji muryan jabir yau kusan wata daya kenan,
Ina wuni, na fada bakina har na dan rawa…yace lpya ya kike?
Nayi shiru zuciya ta ne ta soma min zafi gaba daya zai naji haushin sa ta turnuke ni ,hawaye dam suka ciko min
Story continues below

Mumy na dan lura da ni alaman itama so take ta ji waye ya kira ni da unkonw number daga kasar waje sai na waske nace lpya lau ,ai bansan kai bane naga ba nunber ka bane..maganan da nayi ya bashi karfin gwiwa
Ita ko mumy tun da ta fahimta sai ta wuce ta bani waje
Yace yeah, nayi tafiya ne, in fatan kuna lpya dai ko yaya su mumy da sauran mutanen gida..
Nace lpya..daganan nayi shiru na bata awajen
Shikn sa ya san akwai magana abakina but why im i not saying anything ko na dena damuwa da shi ne?
Ko ajiki na, na daure na dada danne haushin da nake ji, nace banajin karfin jiki na ne amma na warke yanzu..
Yace Allah ya baki lpya..ban tsaya amsa har karshe ba nace masa nagode sai da safe..
Ya dan yi shiru sannan ya kashe wayar,
Don daga jin yadda murya ne ke shaking yasan bana jin dadin magana da shi
Ina ajiye naga sakon kudi 200k da ban hakuri, akan lokacin da ya dauka bai kira mu ba..
Kuka na fashe da shi na ban mamaki gaba daya sai naji na shiga mummunan halin takaici, banma san tsanan shi nake ji ko wani daban ba.
Kukan na zage ina yi har ban san sanda mumy salamatu ta shigo ba..
Ji nayi kawai nayi tacw subhalhi samha?meya same ki
Na dago cikin shehhaka ina neman saita kaina amma na kasa, kukan na sake fashewa Da shi.
Ta damko ni cikin tashin hankali ,tana tambaya na meya same ni amma nayi mata shiru sai kukan nake yi,…
Ta karbe wayan nawa ta duba ta ga sakon sa ne na gama karantawa ga alert din kudi nan ya shigo…
Tace samha bangane ba, tashi kiyi min magana dama chan waye yake kiran ki?idan ba jabir ba, Naga kince kuna waya da jabir ko wannan din ba shi bane .
.nace shine mumy,.. tace to meya faru,?samha meke damun ki? Wato dama da gaskiyan su maman ki kenan Kina boye mana wani abu ko”?
Na sunkuyar da kai ina hawaye tace, ki gaya min ko sai kin tara min mutane nace ah’a ah mumy zan gaya miki amma dan Allah kar ki gaya ma kowa ke dai ki taimaka min bazan iya rikewa ba ne..na dada fashewa da kuka..
Hankalin ta ya tashi amma ta daure ta dago ni na zauna kusa da ita..
Anan ta share min hawaye ta dauko ruwan ta bani na sha tace ina jin ki samha meye damuwan ki,
Ajiyan zuciya nayi sannan na dan cire kawaici da kunya na gaya mata muhimman abubuwan da suka faru tsakanina da jabir da irin zaman da muke yi da shi yanzu…
Ko kafin nagama naga ruwan bacin rai ne ke tsiyaya fuskan mumy amma duk da haka bai kai nawa ba danake ji kamar antabao min Wani likin ciwo ne dana bisine..
Mumy tace tab di jam samha?..ai kinyi wauta da baki sanar da ni a shi din wa?
Wato jabir har ya iya munafurcin da zai ajiye ki agidan sa yana wulakan ta ki duk dama ke yar uwan sa ce? Ta kada kai tace
Amma babu komai ta share min hawaye tana rarrashi na, haka dama aure ya gada ke kam kiyi hakuri kinji samha..? Na miki alkwari bazan gaya ma kowa ba tun da suma idon su ya rufe komi aka gaya musu sun dauka shikenan,ni nan zan nemo maki mafita
Ki bani lokaci kadan nayi tunani..
Nace toh mumy nagode..
Kudin daya turo tace kar ki taba masa kudin sa zaizo da kafar sa har nan gidan ai zaki haihu ko? To zanga ko bazai zo sunan ba ai..
Dan nasiha tayi min sannan ta kama hanya tayi waje ta barni.
Wani sabon nitsuwa nake ji sabida magana ne wanda na dade da shi araina ban sa mu damar fitarwa ba sai yau..
Bangaren zuwairah kuwa,
Ganin kullum zata kira jabir baiya tafiya din bai kira ta da nunbr kasar wajen ba tukuna saboda aikin sa,hakan ya sata harzuka ga yunwa na mugun damun ta ba ta iya abinci ba , ta kuma kashe kudin gidan kaf ba halin fita siyo wani abu.
Abun sai ya hadu mata da ciwon mara mai tsanani ga shi wannan kaikayin gaba kullum karuwa yake ,tun tana ganin kamar maganin maman gayu ne ki jikowa a marar ta har ta soma jin ba dadi
Akwanan jabir na biyar a uk yau 10 days rabon sa da kano.
Yau ta sa rai zai dawo don haka zuciyan ta fall yake zata cigaba da ga inda ta tsaya..
Ko ba don komai bama ta samu ta dena dirkan shayi dare da rana dan suke sustaining din ta..