RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 11 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 11 BY HALIMA K/MASHI

 

 

ya’ kwana suka sha soyayyarsu. Tsaraba ta yo masa

masu yawa, kayan sawa, agogo da sauransu. Tana

sonshi da kananan kaya, kuma su ta kwaso masa. Ya ce,Da na sani na ba ki kudin kayan baby kin sayo a can

Ta ce,Momy ta ce, sai an je Dubai don mun

duba babu wasu sabon yayi a can

Shatima ya ce,Amma online za ku siya ko?”

Ta ce, “A’a su Momy za su je karshen watan

nan”Ya ce,

“Nawa zan bada?”Tace Ka bada yanda ka ke da shi, Dady ya cika”.Ya ce, “Hamsin ya yi?”

Ta dube shi tare da zaro idanu, “Hamsin kuma?Ko kudin durowa ba zai kai ba®

‘ Ya ce, “To ni dai kin san Allah a cikin account

dina dubu dari biyu ne da arba’ in. yanzun sai dai in ba

ku dari-dari ke da Nafisa. Can kudin makarantar Salma

inà zaton za su koma Monday din nan

Amna ta ce,Ka bada haka din

Ya kira Natisa, ga ta ga Amna, ya ce, zai ba su

dubu dari-dari kudin siyayyar haihuwa. Nafisa ta ce, to

sun gode.

Bayan fitarta Amna ta ce, “Kawai ka yi transfer

zuwa account din Momy, don ba zan iya ce mata komai ba. Kudin durowar baby din ma ai ya fi darin”Ya ce, “To ni kam karfina kenan’

Ta ce,Ai ita ma jikanta ne sai ta cika Ya yi murmushi, tare da fadin,

“Haka ne

Salma tana cikin damuwa, Shatima ba ya zuwa duba ta da safe kamar yanda ya saba. Ta kan leka ta

window ta ganshi yana shiga dakunan sauran. Ta yi kuka ta gaji, domin ta san karatunta ya zama labari. Kuma ko ranar girkinta da wuya ya shigo dakinta. Ya

daina ba ta kudin nama, komai dai ya tsaya mata cak!A lissafinta yau litinin, kuma yau za su koma makaranta, ta ce ba za ta shirya ba, sai wata zuciyar ta

ba ta shawarar cewa, ta shirya ta ga me zai faru? Tsaf

Ta yi cikin kayan makaranta, amma ta kasa kari. Ta je window ta tsaya tana leken fitowarsa. Tana kallo ya

shiga gurin Aliya da Amna, don akin Nafisa ya

_kwana. Tana ganin ya yi gurin motarsa, Nafisar ta raka

shi, ita ma ta fito ta gaida Nafisa. Da kyar ta amsa sannan ta nufi motar, ya riga ya shiga ya tada, har yana

yin baya. Ta dan bubbuga gilashin. Yanda ya waiwaya cikin harara ta san ya ganta tunda ta zo gurin.Ya waiwaya ya kalli Nafisa, ta shige dakinta

sannan ya sauke gilashin. Da sauri ya katse ta daga

gaisuwar da ta soma yi cewa,Yaya ina.

Ya cE

“Adana gaisuwarki bana bukata”

Ya sa hannu a gaban aljihunshi ya ciro dari

biyar ya jeho mata,

“Ga shi ki hau mashin, ba za ki

Kara shigar min mota ba

Ta duka ta dauka, sannan ta dago ta kalli

fuskarshi, a tamke bai ko kalli inda take ba ya zuge

gilashi. Salma ta juya fuskarta fal damuwa, don sun yi

kadan ta sani ba dakatar da karatunta ba sai dai tana jin

ya rage ma karatun nata karsashi A makaranta babu wanda bai gane tana cikin

damuwa ba, Salma Dankasa ta matsa da son jin damuwar aminiyar tata, sai ta ce mata ba ta jin dasi ne

kawai. Ko da ake musu karatu tana dai sauraro, amma

ba ta fahimta.

Salma Dankasa ta ce, ta raka ta asibitim cikin

makaranta. Salma ta ce, a’a ba za ta je ba, tana da

magunguna a gida.

Ranar ita ce da miji, ga shi kuma bai ba ta

kudin cefane ba, don haka sai ta dumama sauran

miyarta ta dafa farar shinkafa. Karfe shida da rabi na

yamma tana wanka sai ta ji motsin shigowa da kaya.

Ta san Shatima ne, amma ba ta san kowane irin kaya

ba ne. da ta fito shi ta gani tare da wani suna kokarin

shiga da katifa cikin daya daga cikin dakuna biyun da

babu komai.

Ya dube ta, “Zo ki kwashe tarkacen da ke cikin

dakin nan”

Da sauri ta shiga, babu wani tarkace sai *yan

kayan da ba ta fara amfani da su ba. Ta maida su a

durowar kicin. Dakin babu datti don kullum sai ta

share shi ta goge ko da babu komai. Ya sa katifa da filo

guda biyu. Kafet din tsakar daki duk a Kasa ita, dai

tana zaune tana kallonshi, da ya gama kuma suka fita.

Ta Ieka dakin, har zanin gado ya saka. Bayan is’ha’I ta

ji shigowarshi, ta fito sai ta ganshi da talatijin, da tasoshi ana canzawa. Sai tara da rabi ta ji fitarsu tare, taje kicin ta hada mishi abinci. Tana fiowa yana

shigowa, don haka yana shiga dakin i’ta ma tana shigowa Tun kafin ta yi taku na uku a dakin ya katse

mata hanzari da cewa,

“Ko ma da shi, na koshi”

Washegari ma da safe bai dubi abin karinta

ba, ya aje mata dubu daya wai na cefane da kuma na

makaranta. Salma ta ce, “Na gode

Bai tanka ba ya fice.

Ta shirya ta nufi

makaranta. Duk satin ba ta da sukuni, babu walwala ba

ta damu da kudin da ya rage mata ba. Damuwarta ya

yafe mata su koma Kamar da. Sai dai yiwuwar hakan

da kyar ne, domin yanda Shatima ke mu’amalantarta a

yanzu tamkar bai taba saninta ba, ko kuma babu wani

sabo a tsakaninsu. Duk ranar da yake dakinta ba ya

zama a falonta sam in ya dawo ma ba zai shigowa sai

bayan isha, kuma abincinta tuni ya daina ci, ya ma fada

mata cewa ta daina zuba mishi. Tana kallo tsakanin

Aliya ko Nafisa duk wadda ya ga damar cin abincinta

sai ya sa ta kawo masa har dakin.

Haka kuma da safe yana da

“yar karamar hiter

da kayan tea sai ya hada abinshi, in kuma yana son

dankali ko wani abu haka, sai ya sa matansa su kawo masa.

Tun Salma tana kuka har ta dake ta saba da

sabuwar rayuwar da ya tsirar musu ita da shi. Ba za ta

tuna dariyarshi da ta gani ta karshe ba. Ba ta taba

tsammanin haka yake da daukewa da dakewa ba sai da

matsalar nan ta shigo. Yanzu shakkarsa ma take yi, da wani mugun tsoronsa da ya darsu a zuciyarta.

Wataranar asabar tana shanya kayanta tana

sauri taje ta yi assingment sai ta ga shigowar motoci

guda biyu. Ko ba a fada ba ta san bakin Amna ne, dan su ke zuwa akai-akai, kayan haihuwa ta ga ana shiga da

su, tun daga kan gadon jarirai zuwa durowa da sauran

kaya. Salma ta yi murmushi har zuciyarta ta yi doki zasu sami jarirai a gidan. A fili ta ce,

“Ashe zamu sha suna?”

Kayan da ke cikin akin baki aka fito da su

zuwa barandarta, aka jera kayan jaririn a ciki komai

blue mai haske. Amna ta kalli dakin ji take yi tamkar

ta haihu yanzu. Ta sa hannu tana shafa cikin ranta fal farin ciki

Haka da Shatima ya shigo ba a dakin yake ba,

dakin Nafisa yake amma sai ya nufi dakin saboda

ganin gadon Amna a waje. Ya shiga, tana zaune a kan

kujera a falo tana kallon wani shiri da take bi a tashar

Africa. Ta dube shi tare da amsa sallamarshi, ya isa

gurinta da tambaya,

“Shin me ya faru a dakin can na ga

kaya a waje?”

Ta ce Kama ni in mike”

Ya kamata tare da fadin,

“Sannu”. Suna shiga

dakin, Shatima ya rungume Amna ta baya yana shafa

cikinta, ya ce,

“Har na kosa baby ya zo gaskiya dakin

nan ya yi kyau, sai na ji kamar ya zo yanzun”

Amna ta shafa hannuwansa da ke kan cikinta, taCe,

“Wallahi honey ni ma haka na ji. Allah dai ya saukeni lafiya

Ya ce,Ameen-ameen kullum addu’ata kenan

“To kin ki mu je a yi miki awo

Ta ce,Ni fa ba a nan zan haihu ba, Dad ya ce

England za mu je a can aka haife ni”

Shattima ya saki amna cikin sauri ranshi yai mugun baci yace,

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *