ALLURA CIKIN RUWA BOOK1 CHAPTER 1 BY BILKISU S. AHMAD FUNTUA

ALLURA CIKIN RUWA BOOK1 CHAPTER 1 BY BILKISU S. AHMAD FUNTUA

 

 

Ni asiya yusuf mutumiyar malunfashi ce a

unguwar Kofar Fada. Malam Yusuf mahaifina

mutumin Katsina ne, haifaffen wata unguwa

wai ita Galadanci. Ya dawo Malumfashi ne da zama a

wurin Malam Bawa Kanin tsohonsa,

wanda a.

lokacin yana da shekara ashirin da daya a duniya. Mahaifina mahaddacin Alkur’ani ne, amma ba shida ilimin zamani.

Yana nan zaune a Malumfashi

rannan kwasam sai aka bude makarantar yaki da jahilci,

nan take sai mahaifina ya shiga. Da ya sami kimanin

shekara daya da rabi, lokacin ya iya karatu da rubutu da lissafi. Sai Kanin tsohonsa ya nemar masa aiki a Majalisar Yanki ta nan cikin Malumfashi a matsajin

Masinja. Kwanci tashi har Allah ya hada

shi da abokiyar rayuwa wato mahaifiyata

mai suna Aishatu, mutuniyar wani kauyen Kuka Sheka. Wata rana ta zo cin kasuwa ita da kawayenta, a daidai

lokacin mahaifina ya taso daga aiki yana bisa

kekensa, sai ya ci karo da ita, a nan take ya rinka binsu har Allah ya ba shi sa’a ya sami magana da ita. Ta shaida masa kauyensu, ta kuma gaya masa iyayenta

-fulani ne amma zaunannu.

Nan dai ta yi masa bayanin yadda in ya je za

su sadu ba tare da ya sha wahala ba, ya kawo sule biyar ya ba ta. Ta ce, a’a ya barsu. Ya dai nuna mata yar damuwarsa saboda ta ki karba, har ya kara dacewa,

“Kin ji Hausawa sun ce Sadakin soyayya kyauta Ta yi murmushi ta durkusa ta sa hannu biyu ta kara tare da godiya.

Bayan kwana uku da haduwarsu, mahaifina

ya ga ya dace ya kai mata ziyara ta tabhatar wa kansa yadda Aisha ta dauke shi a zuciyarta, ya yi kuwa sa’a Aisha ta amshe shi da kyau da kyau. Sai da ya yi kamar zuwa uku wajen ta, sai aka

neme shi da ya turo manya, saboda an ga mutane sun fara kawo hari a kanta, a nan mahaifina ya shaida

mata zai yi hanzarin yin hakan, domin kanin

tsohonsa ya fara tuntubarsa a kan maganar aurensa.Mahaifina ya sami Kanin tsohonsa Malam Bawa, ya shaida masa komai da komai tun farkon haduwarsa da Aisha har zuwa inda aka nemi ya kawo magabatansa.

A nan Malam Bawa ya shirya da kansa tare

da wasu mutane har zuwa kauyen Kuka Sheka. Sun fara isa wajen hakimin kauyen da yake amini ne ga Malam Bawa, ya shaida masa dalilin zuwan su da

bukatarsu.

Hakimi ya ce,

“Kun yi dace da samun gidan

mutunci, saboda ubanta dattijo ne ainun, kuma ga su

irin kyawu. Fulani ne amman zaunannu”

Daga nan suka isa gidan yayan mahaifinta,

bayan an gama gaisawa irin ta neman iri, ya ce masu babu komai idan an bincika an ji daga bakin Aisha ta

amincé da Yusuf, to za su ji aike daga Hakimi.

Suka yi sallama, suka kawo kudin neman

aure suka bayar. Bayan kamar sati biyu da zuwa su,Hakimi ya ba da kyakkyawar shaida a kan irin su Malam Bawa, aka aiko

an ba mahaifina auren

mahaifiyata. Aka yi biki dan lokaci kadan, Malam Bawa ya gyara musu wani sashe a cikin gidansa, suka yi zamansu tare da iyalansa.A wannan

lokaci ne na zaman amarci

mahaifina ya rinka nuna ma mahaifiyata karatun Mahammadiyya da na boko, inda har ta iya rubuta wasika ta kuma karanta da ajami da kuma boko.

Kwanci tashi da ta sami shekara biyu sai ciki

ya rinka bayyana a jikinta, wata rana ana hira

tsakanin mahaifina da mahaifiyata, sai gardama ta turnuke tsakanin wadannan

bayin Allah, inda mahaifina ya ce,

“Aisha Allah ya ba ki ‘ya mace mai

kyau kamar ki in sanya ta a makarantar Islamiyya,

sannan in sanya ta makarantar boko ta yi ilimi har sai ta ce ta gaji. Kin san wanna zamanin babu wani abu da za ka yiwa danka sai dai ka ba shi ilimin

neman lahira, daman abin da Allah ya ce kenan. Ko kuwa ya ya kika gani?”

-Ta dube shi tare da murmushi, sannan ta

sunkuyar da kai, ta ce,

“‘Ka ji wani irin zance wajen

Malam, abin da duk kake so da

ya?yanka wallahi

shi nake so. Ku maza ai kun fi mu kaifin hankali, har

abada iyaye abin da zai zama alheri ga ‘ya’yanmu shi suke nema musu Ta kara sunkuyar da kai ta sa yatsanta cikin

baki, ta-ci gaba da cewa cikin jin kuna, “Ni kuwa a nawa ra’ayin na fi son da namiji wanda zai rinka

taya ka aikin gona nan gaba, kuma kullum rokona Allah ya bani mai kama

da kai in sami da

kyakkyawa kamar ka, na sami fuska irin taka da hanci dan siriri har baka, ga manyan idanuwa farare, bakinsa dan karami mai dan fadi, labha sirara,

dogon mutum mai dan kauri kadan, ga shi mai yauki a bisa kumatunsa na hagu, a nan za a tsara masa fasali wanda zai yi masa kyau kwarai ainun”Ta ci gaba da cewa,

“Tun farkon gamuwa ta

da kai bahu abin da nake rokon Allah irin Allah yasa

kai ne mijina, in haifa maka ya’ya masu kama da kai, sannan in roke ka ayi masu dan fasali irin naka.

Haba! Ai kullum ba zan gaji da gyara musu ba, ina mai kallon su ina jin dadì tare da masoyanmu Sai Babana ya yi dariya ya ce,

“Aisha ai kin

fini kyau, ke mai jar fata kamar tsada, ga kyan fuska,ga gashi har gadon baya, ga ki girkakka abin so ga duk wani da namiji.murmushi na ga’

Aisha idan kinayi yar siririyar wushiryarki har bana kaunar in fita in barki don sha’awa.

Amma babu komai, Allah ya bamu

“ya yan da yawa suma su biyo ki, wasu kuma su biyo ni, zanji abin da mutane za su rinka fad, Allah Ubangiji yabamu masu albarka,

ya kuma bamu masu jin maganar iyayensu”

Mahaifiyata ta ce,Amin”

Rannan ciki ya bunkasa kwanakinsa sun cika,

ya kuma nuna alamar zai fito kowa ya ganshi, da misalin karfe tara na safe bayan mahaifina ya fita zuwa wajen aikinsa, sai ciwon nakuda ya turnike mahaifiyata.

Daga nan matar Malam Bawa ta shaida wa

Malam Bawa,a ka samo mata rubutu ta sha, aka shiga jira, aka shirya taren bako.

Can misalin karfe daya da rabi na azahar, sai

haihuwa ta kunno kai, kafin karfe uku an gama   komai anguwarzoma ta wanke

da, ‘ta wanke wa mahaifiyata dakinta ta kunna mata turaren wuta.

Ita kuwa mai haihuwa aka yi mata wankan

jego kamar yadda ake yi a al’adar Hausawa. Wannan rana kuwa Laraba ce, kai da ganin wannan yaro kasan ya ci sunansa Balarabe ba ma sunan rana kadai ya ci ba.

Mahaifina yana isowa gida yana gunguro dan

kekensa, ba tare da ya san abin da ke nan ba. Sai Malam Bawa ya tare shi da yi masa barka mai dakinsa ta haihu, da namiji na nan kwance. Nan da nan ya kafe kekensa ya shiga cikin dakinsa, tsofaffin da ke dakin suna gasa wa jariri cibi, suka yi masa barka, sannan suka mika masa sabon zuwa.

Ya yiwa mahaifiyarmu sannu, sannan ya

amshi jariri ya dube shi da kyau, ya yi masa kiran sallah ya tofa masa a kunnensa na dama, sannan yayi ikama ya tofa masa a kunnensa na hagu tare da

addu’o°’in shiriya, ya bi duk jikinsa ya tattofa masa. À daidai wanna lokacì ya dubi mahaifiyata

fuskarta cike da fara’a, ya ce,

“Allah ya amshi

addu’ arki ya bamu da namiji, ni kuma ya amshi tawa ya bamu mai kama da ke”

Ta yi murmushi ta ce,

“Kai dai Malam baka

gajiya da tsokana Haka

dai aka yi ta hidimar haihuwa.

‘Yan’uwan Baba suka z0 daga Katsina, ita ma nata

‘yan’uwan suka z0 daga Kuka Sheka, aka yi suna bisa gwargwadón abin da Allah ya hore musu, aka

radawa jariri sunan Malam Bawa, wato Abubakar. Washe gari iyayen mahaifiyata suka nemi tafiya da

ita wankan bangwali a bisa al’adar

mutanenmu, aka amince masu. Bayan ta yada

wanka da wata hudu aka shiryo ta komo dakinta.

Haka rayuwa ta kasance tsakanin Inna da Baba.Mahaifina mutum ne mai kamun kai ba shi da wasa ko kadan, duk mutanen unguwarsu sun san shi

a kan irin wadannan halaye nasa, haka wajen aikinsa

duk da an san masinja ne karamin ma’aikaci, amma

ana mutunta shi saboda ya kama kansa kwarai da

gaske.

Bayan shekaru biyu da haihuwar Abubakar

suka dauke shi daga bakin shan nono, yana da shekaru uku cif ni kuma na bullo kai, kamar mu guda da mahaifina kamar ya yi kaki, na dauko kalar jikinsa wankan tarwada.

Ranar suna aka rada mini suna Asiya, wato

sunan mahaifiyarsa don tunawa da ita. Aka yi mini

dan fatali mai kyau daf da hancina. Nan ne ma

dangin mahaifina da suka fito daga Katsina suka ce

sai an sake wa Abuhakar nasa don bai fito sosai ba. Haka haihuwa ta bude musu, ina da shekara

uku aka haifi kanina aka sanya masa suna Yusuf

wato sunan mahaifinmu, Innarmu ce ta zaba. Shima

ya shekara uku sannan aka haifi Zainab, wato mu

hudu kenan, mata biyu maza biyu.

-Ni da Zainab kamar an tsaga kara, Yusuf da

Abubakar su ma kamar su daya. Ina da shekara

takwas na yi nisa kwarai wajen karatun Islamiyya, a

wannan lokaci har na shiga aji uku a firamare,

saboda na yi ido wajen karatun Islamiyya ban sami wata matsala ba a wajen na boko.

Abubakar shi kuma lokacin yana da shekara

sha daya, har ya dauki jarabawar makarantar shiga

sakandire. Shi kuma Yusuf ya shiga bana.

A wannan lokaci ne mahaifiyata ta yi Barin

ciki wata hudu, wanda ta sha wuya ainun. A wata rana na dawo daga makaranta, na gaji da yake

tsakaninmu da makarantar akwai ‘yar tazara, na kwanta bisa katifa a dakin mahaifiyata.

Zuwa can mahaifina ya dawo daga wajen

aiki, Abubakar ya gunguro masa kekensa, nace,Baba sannu da zuwa Ya ce,

“Yauwa Ummi, lafiya aka kwanta? Ko

da yake yau alhamis babu Islamiyya

Hmmm mu tara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *