DOCTOR HASSAN💊💊💊
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romantic and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a duk inda kuke da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni yanzu ma gani tafe da Hatsabibiyar da tafi INDO sheɗanci.
*Bazan taɓa manta alherin ku gareni ba masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin littafin RUƊANIN ZUCIYA BIYU gaskiya naji daɗin ƙaunar ku gareni, domin kuwa kun sayi wannan littafin fiye da yanda nake zato to yanzu ma gani tafe da sabon labari mai rikitar da mai karatu.*
Ku dai ku kasance dani mu tsunduma cikin wannan labarin.🖊️📖
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*Book One*
*Page 1 to 2*
*_____________________________________*
Alhamdulillah ala kulli halin, na godewa Allah daya bani damar sake dawo muku da sabon book ɗina, wanda nake da tabbacin zaku samu nishaɗi a cikin sa, tare da tsantsar darasin zamantakewar Rayuwa mussaman zama irin na babban gida Soyayya tausayi cin Amana ban dariya, ɗan uwa ƴar uwa ina kike maza taho mu haɗe dake cikin wannan labarin mai matuƙar zaƙin zuma tare da garɗin madara taho domin kema a dama da ke nidai fatana na kawo muku Abunda zai amfane ku.
Wannan labarin yana tafe ne da salo na mussaman .
Please idan kina da interest akan wannan book ɗin ki fara binsa tun yanzu kar sai nayi nisa kice min daga farko.
Sharhin ku shi nake buƙata.
*Mu kafta* ⛹🏻♀️⛹🏻♀️⛹🏻♀️⛹🏻♀️⛹🏻♀️⛹🏻♀️⛹🏻♀️
*BABBAN BIRNIN MAIDUGURI BARNO STATE*
Jihar da ta tara Barebarin Asali birnin kanuri.
*Unguwar GRA*
____________Fitowa yayi daga tollet ƙugunsa ɗaure da towel, ɗaya kuma ya ɗaura a kansa yana tsame ruwan jikin sa, dressing mirro ya ƙaraso ya jawo table ɗin dake wajen ya zauna yana cigaba da tsame ruwan jikin sa, sanda ya tsame ruwan tas sannan ya ajiye towel ɗin a hanun bed, lotion ya jawo mai ƙamshin gaske ya fara mulke jikinsa dashi, sannan ya hau gyara gashin kansa shima da mayuka masu ƙamshi sanda ya mulke ko ina na jikin sa da lotion sannan ya ɗauki body spray ya dinga feshe jikinsa dasu sanda ya fesa kala uku kafin ya miƙe tsaye ya je drower ya buɗe ya ɗauko set ɗin kayan sa Blue Black ɗin wandon jeans ya saka tare da rigar suit fari yasa tare da ɗauko ribin dark blue ya ɗaura a wuyan rigar gyara kwalar rigar yayi sannan ya ɗauko suit ɗin ya saka , komai cikin nutsuwa yake yinsa sannan ya ɗauko takalmi sau ciki zama yayi bakin bed ɗin ya sunkuya yana ɗaura igiyar takalmin.
” Assalamu alaikum”
Yaji sallamar ta, shuru yayi ba tare daya amsa mata ba ya cigaba da ɗaure igiyar takalmin, Sau uku take sallamar amma yayi banza da ita kamar baiji ta ba ya cigaba da abunda yake yi, sai a na huɗun ne ya amsa mata can ciki kamar wanda baya son Maganar nan ma sanin darajar Sallamar yasa ya amsa mata idan ba kana kusa dashi ba bazaka ji ya amsa sallamar ba, ita kanta ganin da tayi bakin sa yayi motsi ya sata fahimtar sallamar ya amsa mata, ƙarasowa tayi har gaban sa ta tsaya jikinta a sanyaye ta sunkuya tare da saka hanu zata karɓi igiyar takalmin ta ɗaure masa, yayi saurin bige hanunta yana cigaba da ɗaure wa, cikin sanyin jiki ta masa magana da Sweet voice ɗin ta tace.
” My Doctor breakfast is ready.”
Shuru Yayi Still bai kulata ba, kuma sarai yana jinta sai ma ƙara haɗa fuskar sa da yayi tamau babu alamar annashuwa cikinta, ɗagowa yayi tare da ɗaukar agogon sa ƙirar gucci ya fara ƙoƙarin ɗaurawa a hanunsa, a karo na biyu ta ƙara cewa.
” I Say Doctor breakfast is ready please jiya ma fa haka ka kwana babu abunda kaci ko ruwan tea baka sha ba, haka ka kwana ya kamata kafin ka fice kasa ko da ruwan tea ne a cikin ka bana son kana fita da yunwa bana jin daɗin hakan.”
Ɗago lumshashshun idanunsa yayi masu kama dana mai bacci fuskar sa kuma a matuƙar ɗaure ya dubeta sannan ya fara magana cikin Slow VOICE ɗinsa da kuma faɗa faɗa.
” Wai meyasa ke mayya ce kam *FALMATA*!!!!, Meyasa kika addabi rayuwata ce, nace miki na tsaneki ki daina damun rayuwata ki daina shiga Cikin lamari na, Wallahi Falmata na miki tsanar da ban taɓa yiwa wani ɗan adam shiba, na tsaneki na tsani iyayen ki ina Zaune dake ne a dole Saboda kin zamo min ƙarfen ƙafa ba yanda zanyi dake, Banza ƴar Mayya, dan Allah ki fita a cikin rayuwata, nace bazan ci abincin ki ba ko ana dole ne Get Out of my room Mayya!!!!.”
Ya ƙarasa maganar yana nuna mata ƙofa, hawaye ne suka gangaro daga daradaran idanunta, ta ɗago tana kallon mijin nata cikin matsanancin damuwa da tashin hankali, sunkuyawa tayi ta durƙusa da gwiwowin ta ta fara magana cikin rawar murya mai cike da alamun kuka.
” Karka min haka mijina Please ka daina hukunta ni da laifin da ba nawa ba, asali ma bani da hanu ciki, kana azabtar dani da yawa Doctor, kaine duniya ta, bani da wani farin cikin daya wuce naka, meyasa sanda ka koya min Soyayyar ka sannan zaka juya min baya, Ka ji tausayi na ka cire ni cikin *LAMARIN GABAR CIKIN GIDAN MU TABBAS AN ƁATA ZUMUNCI* amma ni meye nawa ciki da zaka juyawa Soyayyar mu baya, *INA SOYAYYAR DA KACE KANA MIN, KAINE FA KA ƊAUKA MIN ALƘAWARIN CEWA BAZAKA TAƁA RABUWA DANI BA, KOMAI TSANANI KOMAI WAHALA KANA TARE DANI MEYASA YANZU KA TSANENI LOKACI GUDA* ina sonka MIJINA kaji ƙaina?”
Ta ƙarasa maganar cikin matsanancin kuka, tunda ta fara Maganar ya zuba mata Lumshashshun idanunsa yana mata kallon tsana da kuma tausayi sanda ta dire maganar tukunna Yaja tsaki mai sauti sannan ya sunkuyawa ya ɗebi wayoyinsa dake bedsite drower da key ɗin motar sa ya juya da niyar ficewa ba tare daya tanka mata ba, yaji ta riƙe ƙafafunsa, Runtse idanunsa yayi sanda yaji hanunta a jikinsa, Yana jin wani abu na yawo tun daga babbar yatsar sa har cikin kansa tsayawa yayi cak.
” Please My Doctor ka taimaki Rayuwata ka tausaya min, Ka dawo da Soyayyar mu ka ji ƙaina, Wallahi zuciyata ciwo take min, karka bari na mutu ta sanadiyyar ka kaine gata na, kaine rayuwata ina sonka DOCTOR.”
Cin jin wani ƙarin tsanarta ya saka ƙafarsa ya naushe ta da ƙarfi sanda ta bige kanta da jikin bed ɗin, da sauri ya saka kansa ya fice daga cikin bedroom ɗin, kanta ta riƙe tana jin yana mata zafi, hawaye kuwa wani ne yake bin wani saman fuskar ta, sosai take kuka harda shashsheƙa, takurewa tayi a gefe tana cigaba da kuka zuciyarta kuma cike take da baƙin ciki, Duniyar gabaki ɗaya ji take ta isheta, kullum baƙin ciki shine abokin hirar ta, ta rasa farin cikin ta tun sanda wannan mummunan ƙaddarar ta afku tsakanin mijinta d iyayenta, mijinta mai tsananin ƙaunar ta wanda ada baya son ɓacin ranta wanda kullum shine abokin hirarta shine amininta, shine mai share mata hawayenta amma yanzu shine mutumin daya fi kowa tsanar ta, shine ya maida ita ABOKIYAR GABAR sa, Tabbas rayuwa ta juya mata ba tunda har ta shiga tsakanin ta da mijinta, sanda taci kukan ya isheta sannan ta tashi ta goge hawayenta, ta faɗa saman bed ɗin nasa tana ajiyar Zuciya, rigarsa daya cire ta rarumo ta rungume a ƙirjin ta, tana shaƙar ƙamshin turaren sa, ji take tamkar shi ta rungume, sai famar ajiyar Zuciya kawai take, tana nan rungume da rigar har bacci ɓarawo yayi nasarar sace ta tana sauƙe ajiyar zuciya.”
Shi kuwa yafi 30 minute yana zaune cikin motar ya ɗaura kansa jikin matuƙin motar pictures ne ɗan ƙaramin elagment a ajiye cikin motar, Sosai yake ƙarewa pictures ɗin kallo kafin yasa hanunsa ya shafa sa hawaye ne yake tsiyaya saman fuskar sa, *AUNTY JALILA DA UMMAN SA* sune kawai suke masa yawo a cikin zuciyarsa shikenan ya rasa *AUNTYN SA DA ABBAN SA* anbar *UMMAN SA* kuma cikin jinya, taya zai iya yafe musu bayan ya rasa farin cikin sa duk ta sanadiyyar su, ya daɗe zaune cikin motar kafin ya ɗago kansa ya goge hawayen sa, motar yayiwa key, ganin tahowar sa yasa mai gadin saurin wangale masa makeken get ɗin gidan, Yana ɗaga masa hanu, shima hanun ya ɗagawa Baba mai gadi ya ciro kuɗi dubu goma ya miƙa masa cikin sanyin halinsa yace.
” Gashi Baba kuɗin da na maka alƙawari jiya kayi hkr 20k nayi niyyar baka, so yanzu babu kuɗi a gida gaskiya dole sai na biya bank na ciro, so kayi hkr da wannan sai kaje ka fara Siyan maganin kafin na ƙara maka wani abu.”
Yana godiya baba mai gadi ya amsa yana cewa.
” Mai yawan kenan ranka shi daɗe na gode sosai Allah ya ƙaro zumunci ya tsareka ya bawa Umma lafiya na gode.”
Murmurshi kawai ya masa tare da amsawa da Amin kafin ya fice daga cikin gidan rufe get ɗin Baba yayi sannan ya zauna saman tebur ɗinsa yana cewa.
” Oh ni iro har yanzu wannan yaro yaƙi sakin jikinsa tunda wannan al’amari ya faru kullum yana cikin damuwa, babu walwala kwatakwata a fuskar sa, duk da shi ba ma’abocin dariya bane amma ai kullum fuskar sa ɗauke take cike da haiba da kuma murmurshi, Allah ka daidaita lamarin waɗannan bayin naka, Allah ka kawo ƙarshen wannan lamarin ka bawa Mahaifiyar wannan bawan naka mai tausayi da jin ƙan na ƙasa dashi lafiya ka bayyana masa ƴar uwarsa da mahaifinsa, itama Hajiya ko zata samu farin cikin ta ya dawo kamar da mace mai tausayi da kyauta tana cikin damuwa.”
Ya ƙarasa maganar yana ajiyar Zuciya..
Shi kuwa doctor titi ya harba yana dreving a hankali, zuciyarsa kuma cike da ƙunci kwatakwata ya tsani dosar family Hause ɗin nasu sai dai babu yanda ya iya dole ya kamasa yaje tunda akwai Umman sa kwance babu lafiya, ringine ɗin wayar sa ne ya dawo dashi daga tunanin da yake, kallon sa ya kai kan screen ɗin wayar yaga sunan *IB* ya bayyana hanu yasa ya ɗaga wayar tare da cewa.
” Ina sauraronka IB.”
Murmurshi IB Yayi daga can kafin yace.
” Kana ina ne yanzu Doctor.”
A taƙaice ya basa amsa da cewa
” Ina hanya zanje family Hause wani abune yake faruwa.”
” Okay to shikenan idan ka fito daga Family Hause sai ka samu ka biyo Hospital domin kuwa akwai matsala wacce jiya doctor Saif ya mata oppretion sun bata ruwa tasha daga farfaɗowar ta cikin ya ɗan hau.”
Da ƙarfi Ya furta.
” What!!!!! Suka bata ruwa tasha mahaukatan inane su, bayan sanda na gargaɗe su da cewa karsu bata komai tasha idan ta farfaɗo mtssssss!!! Ka bani 30 minute ina zuwa insha Allah bari naje na duba Umma amma ka kira DOCTOR Saif yanzu maza ku shige da ita ɗakin operation nima ina zuwa.”
” Okay ba damuwa Allah ya kawo ka lafiya.”
Kashe wayar doctor Yayi yana tsuka tare da furta ” wasu mutanen sam basu da hankali” a haka ya shigo cikin unguwar tasu ta *BULUN KUTU TSALLAKE* dake cikin Local govt na *MAIDUGURI*, jihar *BORNO* wani ƙofar gida na gargajiya yayi parking ƙofar gidan cike yake da Dattawa suna zaune a babbar taburma sai wani Dattijo dake zaune a saman farar kujerar roba da alamu dai wannan gidan na sarauta ne irin sarautar cikin unguwa, fitowa Doctor Yayi ya tako zai shige cikin gidan, sai ya hango Kawu Dauda, da har zai wuce ba tare daya nufi wajen da dattijan ke zaune ba, sai kuma ya dawo yazo ya sunkuya cikin sanyin muryar sa yace.
” Kawu Dauda sannu da hutawa”
Tare da miƙa masa hanu sukayi musabaha gaisawa yayi da sauran dake zaune bai ɗaga kai ya kalli wannan dattijon dake zaune a saman kujerar ba, wanda fuskar sa take naɗe da rawani, ya miƙe zai shige cikin gidan yaji muryar kawu, Dauda yana ce masa.
” *HASSAN* baka da hankali ne, baka ga *BAFFAN KA* bane baka gaishe sa ba,ko ka manta dashi ƙanin ubanka ne kasa kai zaka wuce, rashin ɗa’a fa ba halin ka bane naga yanzu ka ɗauko wani halin banza wanda a baya baka dashi.”
Shuru Doctor Yayi yana tsaye yana sauraran Kawu Dauda, sai da ya ƙarasa maganar tukunna sannan ya saka kai ya shige da sauri ba tare daya tankawa Kawu Dauda ba domin kuwa bazai iya gaishe da wannan baƙin azzalumin ba, Kawu Dauda duban wannan mutumin yayi yace.
” *YALLAƁOI* kayi hkr na rasa ya akayi Hassan yafi kowa ɗaukar wannan lamarin da zafi, duk da nasan yana da zafin zuciya, amma abun nasa yayi yawa insha Allah zan masa faɗa komai zaizo ƙarshe zai gyara.”
Gyara zaman sa yayi wanda aka kira da yallaɓoi ɗin, sannan ya fara magana.
” Karma ya gyara dan ubansa idan sunga dama su cigaba da gaba damu daga su har yan uwan nasa har duniya ta tashi, ɗan banza wanda ya yi gadon tsiya a wajen uwarsa kuma wallahi idan sukayi min iskanci sai na kore su daga cikin gidan naga uban da zai dawo dasu.”
Gabaki ɗaya dattawan dake wajen kallon sa suke cike da mamaki, wai zai koresu daga gidan nasu gidan da aka haifesu gidan ubansu ikon Allah lallai ZUMUNCIN wannan gidan ya lalace, Kawu Dauda baice komai ba.
DOCTOR da bai ƙarasa shigewa bane yaji Abinda yake cewa ya dawo cikin sauri da ɓacin rai.
Jin muryar sa sukayi yace.
” Idan ka fasa korar mu daga cikin wannan gidan ka raina Allahn daya halicce ka, idan ka isa kai mai iko ne da faɗa aji dan Allah karka barmu mu kwana a cikin gidan nan ya idan kuma ka barmu mun kwana baka ci sunanka ABUBAKAR ba mtsss, shasha…….
Yana ƙarasa maganar yayi shigewar sa cikin zafin rai gabaki ɗayan su kallon mamaki suke bin DOCTOR HASSAN dashi Lallai ɗan zaki ya girma.
Kawu Dauda ya furta tare da tashi ya bar wajen, yana Allah ya kyauta, shi kuwa wannan bawan Allah zuciyarsa takai har wuya domin kuwa gani yake Hassan ya tozarta shi amma babu damuwa sai yayi maganinsu kamar yadda yayi na ubansa.
To fa ina kake/ina kike maza biyoni mu ninƙaya cikin wannan labarin mai matuƙar daɗi cike da nishaɗantarwa tare da tsantsar Soyayya kudai ku kasance da.👇🏻
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(Ummu Nasmah ce)*
🥰
[8/27, 9:27 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romantic and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
Waɗanda suke buƙatar Complete document na Ruɗanin Zuciya biyu ƙofa a buɗe take zaku samesa akan farashi mai sauƙin 200 Naira only ku tuntuɓeni ta 08147537180.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 3 to 4*
*_____________________________________*
✍🏻_________Shigar sa tsakar gidan ya samu sai famar dambarwa ake, tare da cacar baki, *MAI KANTU* ta dage sai famar lailayo ashar take tana makawa yayin da *FANNA* take maida mata da zagin, da yawa daga cikin mutanen gidan sun fito sunyi carko-carko suna kallon faɗan, Doctor tsayawa yayi turus yana kallon su cike da ɓacin rai, wani irin mungun kallo yake jefawa ƙanwar tasa *FANNA* da ta tsaya harta biye wannan Yar barikin marar mutunci Iya mai kantu, cikin tsawa yace.
” Keee!!! *FANNA* maza zoki bar nan ko kuma na ƙaraso na taka miki wuya a wajen, ban hanaki faɗa da JAHILAI BA oya shige daga wajen.”
Ya faɗawa *FANNA* Still Yana jifanta da mungun kallo bakin ta *FANNA* ta tura sai kuma idanunta suka ciko da hawaye cikin rau rau da ido tace.
” Yaya Umma na fa suke zagi tun ɗazu ita da *KALTI YA GANA* (KALTI yana nufin Umma ƙanwa ko kuma yar Mahaifin ka) shikenan yaya sai nayi shuru na barsu suna zagin Umma sai kace wanda banda Zuciya.”
Runtse idonsa kawai yayi cikin ƙunar rai da kuma tsanar family ɗin nasu, ya tsani zuwa gidan saboda, gutsiri tsome da baya karewa a cikin gidan, cikin sanyin muryar sa yace.
” *Shifa jaki duk yanda akayi dashi sai yaci kara sannan kuma ai shi jahili bazai taɓa yin aiki irin na masu hankali ba* dan haka wannan ya daina damunki duk wanda ya *zagi uwar wani uwarsa ya zaga* shige mu tafi.”
Wani raɗaɗin Maganar *Doctor Hassan* YA GANA DA MAI KANTU suka ji, cikin takaici ta tashi ta dinga surfawa Doctor magana, wanda shi bai san ma tana yiba tuni yasa *FANNA* a gaba sun shige part ɗin mahaifiyar tasu.
” Ka faɗawa Uwarka *YAMURAN* tana can tana kwance naɗe baƙin ciki ya kusa kashe ta itace jahilar ba muba, ɗan iska marar kunya, ina matsayin ƙanwar ubanka ko kunyar kira na jahila bakayi ba, marar mutuncin banza.”
*Yagana* ce tace.
” Kinga fa kumfar bakin banza kikeyi Mai kantu, shifa ya shige sashin Nakassashiyar uwar tasa, dama kin rabu dasu baƙin cikin su shine zai kashe su, kinga ni kizo ma ki rakani wajen Uwar marassa Zuciyar nan *Falmata* akwai maganin da *Aunty YANA* ta bani na kai mata, ko zata samu ɗan Iskan mijin nata Hassan ɗin ya sassauta mata jeki ɗauko mayafin ki mu tafi.”
Taɓe bakin ta Mai kantu tayi, tare da cewa.
” Ni babu inda zani, Waye zai sassauta matan wannan ɗan Iskan mijin nata mai zuciyar fir’auna shine zai sassauta mata, wanda muma da muke ƙannan Ubansa bai ɗaga mana ƙafa ba bare kuma Matar sa kina gani yanzu fa ya gama faɗa min magana, ita dai Falmata ta gamu da Wahala tunda tace ita bazata rabu dashi ba, tana kuma tare da Wahala dan ubanta, idan Soyayya zata biye haka zata ƙare cikin nadama da zubda Hawaye saboda ta gamu da ɗan iskan miji, dan haka ku ƙyaleta wannan Uban Yan taurin kan tsiyar ma, Asiri ba kamasa yake ba, dan haka kuma daina wahalar da kanku a banza ni ba inda zani na wahalar da kaina da yawun baki na a banza ita ba ganin laifin mijinta take ba kina mata magana zata fara karesa tana ɓata rai ita a dole bata son ana zagin mijinta, shegiya wai ita SOYAYYA a zamanin yanzu ana daka ta soyayya ne, Soyayyar banza Soyayyar wofi yanzu ina Soyayyar take da zaki taɓa tunanin zai wulaƙanta tane, gashi yanzu wahalar take famar kwasa kullum yana gasa mata gyaɗa a hanu ita kuma marar zuciyar banza sai famar liƙe masa take kamar ruwan gam.”
” Himm!!! Kinga *Aunty Yana* ba yadda zatayi ba, domin kuwa ta rantse da Allah sai ta, dawo da Hassan tafin hanunsu tace shiɗin ma da yake tausayin uwar tasu, nan gaba koda kallon inda take bazaiyi ba, kinga nifa ƴar aika ne, ganan laya dai ta bani tace naje a saka masa ƙarƙashin katifar sa, kuma kinga yanzu ne dai-dai sawa baya cikin gidan kinga bari ma kiga na tafi tunda ke bazaki ba.”
Yagana ta ƙarasa Maganar tana tashi, taɓe bakin ta Mai KANTU tayi tare da cewa.
” Hmm!!! Sai kuje kuta fama da sassaƙar da babu ranar gamata su dai iyayensa kunyi nasarar ganin bayan su, amma shi kam abune mai kamar wuya domin idan juninki sammako ne, to kuwa da alama shi a hanya ya kwana, kinga tafiyata.”
Ta ƙarasa maganar tana barin wajen, Yagana kafaɗarta ta ɗaga sannan ta shige part ɗin Yana mahaifiyar Falmata.
Doctor da Sallama ya shiga ɗakin mahaifiyar tasa, *AJIRAM* ne ta amsa tana cewa.
” Sannu da shigowa Yaya.”
” Yauwa sannu AJIRAM Umman bacci take ne.?”
” Ehh yaya Bacci ne ya ɗauke ta, amma gaskiya yau tana fama da Matsalar Numfashi, jiya munyi magana da BELLO yake sanar dani akwai wani Dattijo mai bada magani a ƙauyen *BINISHED* ance yana bada magani sosai akan matsalar ciwon da aka rasa kansa, shine nace ko za’aje a gwada ko Allah zaisa a dace, tunda ciwon nata ba na asibiti bane, sannan ance yana bada taimako sosai mussaman ga mutanen da suka ɓata aka nemesu aka rasa, kaga sai mu masa zancen ɓatar Baba da Jalila ko Allah Zaisa mu dace.”
Shuru Doctor Hassan yayi yana kallon Umma dake kwance tana jan Numfashin ta da ƙyar, sosai yake jin tausayin Mahaifiyar tasa wani sa’in idan ciwon ya tashi mata kamar ciwon hauka haka zata dinga fisgar gashin kanta tana ƙoƙarin ciresa daga kanta ko kuma ta dinga ƙoƙarin zata cire kayan jikinta, wani sa’in kuma numfashin tane yake ɗaukewa, ajiyar Zuciya ya sauƙe yana duban AJIRAM yace.
” Okey zan tuntuɓi bellon naji yanda abun yake, idan har malamin Allah da Annabi ne bana shirka ba, to zamuje mu gwada, zamu kai Umma koma inane muddun zata samu lafiya, Allah ya baki lafiya Umma yasa ƙaffara ne, Allah ya yassare miki wannan ciwon Umma na.”
Ya ƙarasa maganar cike da tausayin halin da mahaifiyar tasa take ciki sannan ya jefawa AJIRAM tambaya.
” AJIRAM yaushe zaki koma gidan ki ne, dan ya kamata ki koma kar mijinki ya ga kamar mun masa rashin adalci, zan ɗauko *HAJJO* zata zo ta zauna da Ita kafin Allah ya bata Lafiya tunda ita tana zaune a gida babu aure mijinta ya rasu ina ga hakan zaifi ko, ni dama *HAJJA MERO* ta bani izini tuni da na mayar da ita gidana, to ta hana na rasa me wannan tsohuwar take nufi.?”
AJIRAM duban ɗan uwannata tayi cike da tausayin kansu tace.
” Yaya idan banyiwa Mahaifiyata jinya ba, waye zai Mata, shima idan har ya kasa min uziri akan mahaifiyata, bai min adalci ba, mu Huɗu ne kawai ƴaƴan data haifa daga Aunty Jalila sai kai saini sai kuma FANNA kai namiji bazaka iya mata jinya ba, domin ba komai bane zaka iya mata a matsayin ka na namiji, FANNA kuma tayi ƙanƙanta ga ɗaukar ɗawainiyar jinyar mahaifiyar mu, kaga dole ne a kaina, na jinyace ta, Amma babu damuwa idan har HAJJO zata yarda domin kuwa duk ɗaya muke, tunda itama hajjo Ƴace a wajen Umma, ƴar ƙanwar Umma ne, kaje ka tuntuɓeta idan ta amince sai na koma gidan nawa amma dole kullum nazo na dinga duba umma.”
Numfashi Doctor ya sauƙe yace.
” Hmmm!!! Ba damuwa insha Allah Hajjo bata da matsala zata amince, mu cigaba da addu’a Allah ya kawowa Umma sauƙi cikin gaggawa.”
” Ameeen yaya, FANNA tashi ki ɗauki tsintsiya ki share cikin gidan nan.”
Da to FANNA ta amsa sannan ta tashi ta ɗauki tsintsiya ta hau shara, Doctor Hassan tashi yayi tare da ciro kuɗi masu yawa ya bawa AJIRAM yace.
” Gashi ki riƙe a hanunki ko akwai Abunda zaku buƙata koda bana kusa, munyi magana da malam Sani ga wannan kuɗin kuma ki basa, yace zasuyi sauƙar ƙur’ani gobe suna so zasuyi yanka sai ki basa idan ya aiko, sannan ki tabbatar kin bata maganinta da zarar lokaci ya cika, Bari naje na gaishe da *HAJJA* daga can zan wuce Hospital insha Allah zuwa dare zanzo naga jikin nata.”
” To yaya a dawo lafiya Allah ya tsareka.”
” Ameeen AJIRAM.”
A tsakar gidan ya tsaya tare da kamo kunnen FANNA ya murɗe, ɗan ƙara ta saki sakamakon jin zafin da tayi, cemata yayi.
” Ke ba!!! Ina baki jin magana ta ko, nace ki daina biye musu kuna hayaniya baki ji ko, to daga yau na sake jin kunyi faɗa da wani cikin gidan nan, ko ranki sai ɓaci, kinji ko bakiji ba.”?
Ya mata Tambayar yana zaro mata Ido tare da sake mata kunnen, bakin ta ta tura tace.
” Naji yaya bazan sake ba.”
Ficewa yayi, FANNA ta tura baki tana cewa.
” Allah bazan ƙyale duk wanda ya zagi Umma na, ba sai dai ka kasheni yaya amma duk wanda ya zageta nima sai na zagesa ehe.”
Sashin su matar tasa ya nufa wajen kakarsu mahaifiyar Baban su, wanda take zaune sashin su matar tasa, *AUNTY YANA* tana zaune ita da Mairama tana tankaɗen garin tuwo, ya shigo ko Sallama babu, kansa tsaye zai shige ko inda suke bai kalla ba, ɗago kanta Aunty yana tayi ta dubesa cike da jin haushin rainin daya mata, kamar ba Uwar matar sa ba, ɗafa tayi tare da girgiza kai ta tashi tare da tare gabansa tana cewa.
” Tsaya ƙaramin marar kunya, marar mutunci”
Tsayawa Doctor Yayi ba tare daya kalleta ba, nan ma ya tsaya ne saboda ta tari gabansa, hanu ta miƙa masa tare da cewa.
” Bani Takardar sakin ƴata, mun gaji da Auren tsiya Auren da babu mutunci Auren tarkace dan haka sakar min ƴata idan kana da zuciya nacaccen banza kawai marar zuciya.”
Runtse idonsa Doctor Yayi yana jin wani irin tsanar surkar tasa yana ƙara shiga cikin zuciyarsa, gefen ta ya matsa zai raɓe ya shiga ta ƙara matsawa ta taresa tana cigaba da cewa.
” Nace ka Sakar min ƴata ko, kai wani irin marar zuciya ne kam, ka saketa, ta fara gajiya da ganin baƙin cikin ka, dan wallahi bazan tsaya na zuba ido ina kallo ka kashe min yarinya ba, Dan haka sakar min ita.”
Dariya maganar ta, taso bawa Doctor, idanunsa ya ɗago da suka sauya kala ya fara mayarwa Surkar tasa magana son ransa kamar wanda yake magana da sa’arsa, wannan shine karo na farko daya fara kiranta da sunanta darect ba tare daya lulluɓe ba.
” *YANA* ya kamata zuwa yanzu ace kin fita a hanya ta, ki daina garajen tare min gabana domin kuwa daf nake dana tureki ki faɗi har ƙasa muddun baki fita cikin rayuwata ba, ƴarki kuma nace bazan saketa ba, sai randa ta yanki jiki ta faɗi hawan jini ya kayar da ita ko kuma ciwon zuciya ya kamata, a wannan ranar sai kizo zan baki takaddar ƴarki, sannan ina miki Albishir da cewa yanzu ma *FALMATA* ta fara ƙunsar baƙin ciki a cikin gida na.”
AUNTY YANA sake baki da hanci tayi tana kallon Doctor, wai yau ita *HASSAN* yake kallon tsabar idonta yake faɗa mata maganar da yake so, mutumin da a baya yake mata biyayya tamkar uwar da ta haifesa yau shine yake neman zaginta haushi ne yasa ta cakwami wuyan rigarsa tana cewa.
” Idan ka fasa yasar dani a ƙasa ka raina Uwarka *YAMURAN* kuma wallahi dole sai ka sakar min ƴata ko kaƙi Allah.”
Murmurshi yayi yana duban hanunta dake riƙe da rigarsa, zuciyarsa tana tunzurasa daya tankaɗeta kawai ta faɗi ƙasa, HAJJA dake cikin ɗakinta ne taji hayaniyar AUNTY YANA ya sata fitowa da sauri, tsayawa tayi tare da riƙe baki ta rafka salati tare da tafa hanu.
” Innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un!!! Ni Mero yau kuma ina ganin wani baƙar lalacewa wai Surukace ta riƙe wuyar rigar Mijin ƴarta, Lallai Yana baki da ta ido, ta sakesa kafin na ɓata miki rai shashancin banza kawai.”
Aunty YANA ƙin sakar masa riga tayi tana jijjiga tace.
” Allah HAJJA bazan sakar masa riga ba sai ya Bani takaddar FALMATA tunda ba ƙanwar uwarsa bane sai ya Rabu da ita ai, akan me zai zauna yana wahalar min da yarinya dan ubansa shi wayee.”
Doctor leɓen bakin sa ya cije yana kallon AUNTY YANA kallo na tsana da kuma wulaƙanci, kafin ya dubi HAJJA yace.
” HAJJA idan wannan matar bata sakar min riga ba ko, to wallahi za’ayi mummunan abun kunya yau a cikin gidan nan domin kuwa zan hankaɗa matar nan hankaɗar da idan ta faɗi wallahi sai ta karye sannan ta daina zagin ubana yafi ta ita da wannan shashashan mujin nata daraja da mutunci.”
HAJJA cike da haushi da kuma fara gajiya da masifar iyalan gidan nasu ta taho tana cewa………..
Tirƙashi akwai ƙura fa cikin wannan book ɗin, tare da cakwalkwalin cakwakiya ku dai ku biyoni mu jone tare⛹🏻♀️⛹🏻♀️⛹🏻♀️⛹🏻♀️
*Please my fan’s Share and comments*
08147537180
*ALƘALAMIN RASHEEEDAT USMAN✍🏻*
*(Ummu Nasmah ce )*
[8/27, 9:30 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romance story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 5 to 6*
*_____________________________________*
✍🏻__________”Sakar masa riga, wai ke meyasa sam baki da hkr ne kam yaƙi ya Saki Falmatan nace yaƙi ya Saki Falmatan ko kuma ke ki rubuta mata sakin idan kin isa marar mutunci ɓace ki bani waje kafin na ɓata miki rai.”
HAJJA ta ƙarasa Maganar tana bige hanun Aunty yana dake cakwame da rigar Doctor, sakin rigar AUNTY Yana tayi ranta a matuƙar ɓace ta juya tayi ɗakin ta, tana kuma jin takaicin wulaƙanta mata ƴa da yakeyi, Doctor juyawa yayi da niyar ficewa ma daga sashin gabaki ɗaya domin kuwa ransa yayi matuƙar ɓaci, Muryar HAJJA yaji tana ce masa.
” Ina kuma zaka daka juya, ai duk baƙar zuciyar ta ka zaka tsaya mu gaisa dai ko dan ubanka, to maza ka dawo muje uwar ɗaka dama ina neman ka.”
Babu musu Doctor ya juyo ya dawo, har cikin ɗakin HAJJA suka shiga a bakin gadon ta Doctor ya zauna tare da gaishe ta, ta amsa tana cewa.
” Hassan na fara gajiya da wannan masifar gabar taku ta fara yawa, Abunda ya faru ya riga ya faru, meyasa kowa bazaiyi hkr ba, duk kaima zargi kake bawai kana da tabbacin abinda kake zargi a kai ba, kana gani fa mutanen unguwa har gulmar gidan nan suke, haka bai dace ba sam gidan sarauta ne fa Babban gida amma a zauna ana abu na rashin mutunci, to na fara gajiya da wannan abun kunyar da kuke jawo mana, dole ne kowa ya ajiye gabar nan, a dawo da ZUMUNCI kamar da ko kuma duk na ci ubanku, Sannan ita MATAR KA meye laifin ta, da zaka dinga mata rashin imani, nan fa ka zauna a gabana nida Marigayi Sarki Allah ya jiƙansa ka dinga kuka da mukace bazamu baka aurenta ba, duk saboda tsoron lalacewar Zumunci, Amma kuka daka tsalle kuka dire kai da ita ku lallai kuna son junanku haka muka hkr muka yarje muku akayi Auren nan, amma shine yanzu zaka dinga wulaƙanta yarinya, kaji tsoron Allah Hassan ka kasance namiji mai kyautatawa iyalin ka, ka daina wahalar da wannan yarinyar idan ƴan iska na suka juyo kanka Hassan zanci ubanka kun sanni kaf ɗinku kun san halina bawai sanyi nayi ba ido kawai nayi shuru na zuba muku to ka kiyaye ka gyara kafin na juyo kanka.”
Shuru Doctor Yayi yana sauraran HAJJA sai da ta gama maganar tukunna yace.
” HAJJA kinfi kowa sanin baƙin zaluncin da aka mana a cikin gidan nan, wannan gabar da ake yinta mu bamu da laifi dan mun ƙauracewa alaƙa tsakanin mu dasu, HAJJA ko kene a halin da muke ciki iya abinda za kiyi kenan, HAJJA sune sanadiyyar Ɓatar Babbar yarmu AUNTY JALILA, suka ƁATAR DA ABBAN MU, suka KWANTAR DA UMMAN MU, jinya duk inda muka kaita cewa ake *SAMMU AKA MATA* waye zaiyi mana wannan aikin idan basu ba, Saboda kawai tsananin son sarautar su ta tsiya haka kawai su tarwatsa mana farin ciki, sannan kuma ace a zauna lafiya wallahi HAJJA yanzu muka fara gaba dasu, ai tun farko na sanar dake cewa zan sake musu yarsu kikace baki yadda ba, dan haka FALMATA bazata ƙara samun farin ciki a gida na ba, dole itama sai ta ɗanɗani baƙin cikin da muma iyayen ta suka ɗanɗana mana, HAJJA bazan ɓoye miki ba, Ina son Falmata sai dai a yanzu nafi jin zafinta fiye da Soyayyar da nake mata, zuciyata bazata iya bawa Falmata farin ciki ba a yanzu Saboda ƙiyayyar da nakewa AHALIN TA yafi Soyayyar da nake mata tasiri a cikin Zuciyata Soyayyar ta ta fara fice min a raina ki gafarce ni HAJJA bazan iya dawo da farin cikin mu kamar daba a cikin gidana bazan iya ba, saboda ina ganin baƙin Falmata da Iyayen ta hajja koda kasheni zakiyi bazan taɓa sassautawa Falmata.”
Ya ƙarasa maganar idanunsa sunyi jajajur yana kuma duban action ɗin HAJJA, HAJJA ma kallon sa take cike da tausayin sa, da kuma tausayin jikarta Falmata wanda bakin fentin da babu hanunta a ciki ya shafeta, tasan har yanzu Hassan zuciyarsa tana tafasa game da rashin Ƴar Uwar sa JALILA da yayi da kuma Ɓacewar Mahaifin sa, ita kanta HAJJA har gobe cikin tashin hankalin ɓatar ɗannata take, cikin faɗa hajja tace .
” To ita FALMATA meye laifin ta da zaka sakata a cikin wannan lamarin Hassan ka dawo hankalin ka fa.?”
” Hmmm!!! HAJJA idan ita bata da laifi, Iyayen ta ai suna dashi, dan laifin iyayenta shiya shafeta, kinga HAJJA kifa daina zare min Ido kinsan dai anmin rashin adalci ko, kinga ni na tafi domin kuwa bani da lokacin zama ina ɓata yawun bakina akan waɗannan mutanen marassa imani, Kuma HAJJA ki faɗawa wannan shashashan ɗannaki Abubakar ya fita a harkata ya daina zagi na, idan ba haka ba wata rana sai na cire masa haƙorin gaba saboda babu mutunci yanzu tsakanin mu dashi bare kuma girmamawa.”
Hajja kwanon da yake gabanta ta ɗauka tare da wurgawa Hassan saurin sunkuyawa yayi kwanon ya bigi bango cewa Hajja tayi.
” Sai kazo aini ka fara zubawar haƙwaran tunda nice a gabanka, Hassan ka kiyayi duniya wallahi, komai tsiyar Abubakar dai ƙanin ubanka kuma ƙanin uba shima ubane hanu bazai goge ba haka kuma ruwa bazai wanke baa.”
” to Hajja ni dai ba ubana bane shi, Allah ya kiyaye ya zamo ubana”
ya ƙarasa maganar yana ficewa daga cikin ɗakin salati HAJJA tayi tana cewa.
” Tafiya zakayi Hassan bamu gama Maganar ba, cap lallai Zumunci ya lalace wai yau ɗan ADAMU ne yake cewa Abubakar shashasha, na shiga Uku ni Maryam, Allah ka kawo min ɗauki ya daidaita min tsakanin Zuri’a ta, Allah karka bawa sheɗan damar nasara akan su.”
Ta ƙarasa addu’ar tana rafka tagumi, shi kuwa doctor da ya fito a inda ya samu su Aunty YANA yanzu ma anan ya gansu wannan karon harda YAGANA a wajen, kansa ya ɗaga ya fice ba tare daya dubesu ba, AUNTY YANA tsaki taja bayan ficewar Doctor tace wa YAGANA tashi muje na baki saƙon, tashi Yagana tayi tabi bayan ta suka shige ɗaka YAGANA ne ta dubi Aunty YANA tace.
” Oh ikon Allah Aunty YANA dama haka ashe wannan yaron Hassan ya miki mungun raini, hmmm lallai abu ya girmama sai kace ba Surukarsa ba.”
Aunty YANA cewa tayi.
” Kedai Yagana bari kawai, kin san tunda wannan shegiyar ƴarinyar munafuka tayi Aljanu ta tona mana asiri cewa mune muka musu Sihiri, ta dinga faɗe faɗe shikenan yaron nan ya tasomu a gaba kamar zai kashe mu kuma wallahi bai isa yaga bayan mu sai dai mu muga bayan sa.”
” Hmmm!!! Aunty YANA aini yau Abunda ya miki ya bani tsoro, koda yake kina dai-dai dashi nasan zuwa kwana kaɗan ne zai dawo hanunki sai yanda kikayi dashi, ki ci ubansa iya son ranki.”
Dariyar Aunty YANA tasa tare da cewa.
” Aikuwa bazan taɓa ƙyale yaron nan ba, muddun bokaye basu kare ba a duniya, sai na sashi shida kansa ya wulaƙanta uwar tasa da yake wannan gabar a kanta, kinsan yanda ake juya masa a tanda, nan gaba kaɗan haka zamu juya Hassan a hanun mu nida ƴata Falmata, kinga YAGANA yarda dake yasa nake sanar dake sirri na, kuma kema ina sanar dake ne saboda ina da naki sirrin a tafin hanuna, yanda kina fallasa nawa zan fallasa naki, dan haka ki riƙe min nawa nima sai na riƙe miki naki, yanzu ki tashi ki tafi gidan Falmata ki kai mata wannan LAYAR kina tsaye ki tabbatar kunsa a ƙarƙashin katifar sa, idan kin min haka kin gama min komai.”
” To amma Aunty YANA ni Matsalar bata waje na, tana wajen Falmata domin kuwa cewa zatayi bazata yiba, kinsan ta da shegen Ustazancin tsiya, cewa fa take shirka muke aikatawa, sannan Aunty YANA Ina tsoron kar Falmata ta sanar dashi, kinsan halin sa zai iya zuwa har cikin gidan nan ya shuka min tsiya.”
Shuru Aunty YANA tayi tana nazarin Maganar YAGANA domin kuwa tasan halin ƴarta sarai zata aikata Abunda yafi haka indai akan Soyayyar wannan ɗan Iskan yaron ne, duban Yagana tayi tace.
” Kijeki Yagana kice mata nine na aiko ki, idan ta miki musu ki kirani a waya dan ubanta ai ƴancin ta nake nemar mata shegiya marar zuciya kamar ba nono tasha ba.”
Yagana da to ta amsa mata sannan ta tashi ta fice.
Cikin mintuna ƙalilan Yagana ta isa gidan Doctor sanda ta ƙwanƙwasa ƙofar kafin mai gadi ya leƙo ya buɗe mata kasancewar ya san daga gidan su Uban gidan nasa take, gaishe ta yayi ta amsa babu yabo babu fallasa.
Darect Part ɗin Falmata ta shige babu kowa cikin falon sai mai aikin ta, taɓe baki tayi tare da duban mai aikin tace.
” Ke!!! Ina uwar gijiyar taki take Falmata?”
Sunkuyawa Ladiyo mai aiki tayi tare da cewa.
” Ina kwana Aunty.”
Tsawa Yagana tayi mata tace.
” Keeee!!! Bana son shashancin banza, gaisuwa na tambayeki, cewa nayi ina Falmata ko kurma ce ke.?”
” Kiyi hkr Aunty, Aunty Falmatan tana ɗakin DOCTOR tun ɗazu ta shige.”
Tsuka Yagana taja tare da cewa.
” Shi Hassan ɗin yana nan ne.?”
” A’a baya nan tun safe daya fice bai dawo ba.”
Yagana bata sake cewa komai ba ta wuce bedroom ɗin Doctor Hassan, tana kwance idanunta biyu tayi shuru alamun tana cikin matsanancin damuwa sai bushashshen hawaye dake kwance gefen fuskar ta, tunanin da ta shiga baisa tasan da zuwan Yagana ba, harta zauna sai da ta taɓa ta tukunna, tayi firgit git ta farka cikin tsoro duk a tunaninta, DOCTOR ne ya dawo, ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafe kanta tace.
” Aunty Yagana, yaushe kika shigo.”
Bakinta Yagana ta taɓe tare da cewa.
” Ina zaki ji shigowata tunda kin saka kanki a cikin duniyar tunani kina neman kashe kanki akan namiji guda ɗaya tal wanda ina da tabbacin a yau kika bar gidan sa zaki samun wanda ya fisa komai, kin zauna kina neman sawa kanki Hawan jini a banza akan wanda bai damu dake ba.”
Gyara ɗaurin ɗankwalinta tayi Falmata cikin sanyin halinta tace.
“Ina son mijina Aunty Yagana bazan iya rabuwa dashi ba, kuma duk abinda yake min bana ganin laifin sa, domin kuwa iyayena sun cutar dashi da yawa, Aunty Yagana na rasa me zanyi na daidaita lamari na da mijina wlh ina sonsa amma shi ya tsaneni yanzu kwatakwata bashi da lokaci na ko kallo na baya son yi.”
Tsuka Yagana taja tare da cewa.
” Ai kuwa tafe nake da yadda zaki gyara zamantakewar ki da Shi romio ɗin naki uwar marassa zuciya.”
Gyara zaman ta Falmata tayi tare da matsowa kusa da Yagana tace.
” Aunty me zanyi Doctor ya daina Wulaƙanta ni.”?
Layar Yagana ta ciro tare da nuna mata tace.
” Da wannan zaki dawo da hankalin mijinki kanki .”
Falmata cike da jin haushi take duban Yagana tace.
” Aunty Yagana laya ce fa wannan.”
Yagana cewa tayi ” eh laya ce itace maganin matsalar ki, da zarar kin saka masa a ƙarƙashin wannan katifar tasa yana kwanciya magana ta ƙare sai yanda kikayi dashi, Aunty YANA ce ta karɓo ta jiya a wajen malamin ta.”
Tunda Yagana ta fara Maganar Falmata ta zuba mata ido sai da takai aya sannan Falmata tace .
” Bana buƙatar maganin matsalata daga wajen boka, ba tun yau na fara faɗa muku haka ba, a wajen Ubangiji nake neman maganin matsalata kuma insha Allah zai kawo min ƙarshen ta, Aunty Yagana na rasa me yasa kuka nacewa mushirikin Mutum keda Mama gaskiya bazan iya cutar da mijina ba, ki mayarwa mama layarta kice mata bana buƙata ta tayani kawai da addu’a Allah ya kawo min ƙarshen matsalata.”
Yagana cikin jin haushin Falmata tace.
” Abinda yasa kike shan wahala kenan wannan tsoron Allahn naki, ke ga wacce kika fi kowa tsoron Allah ai kuwa kina nan kina shan wahala, an faɗa miki kowa kika gansa yana zaune a gidan sa lafiya da mijinsa to ba haka ya zauna ba, sai da ya haɗa da malami, bari na kira Aunty YANA na sanar da ita kince bazaki karɓa kiyi amfani dashi ba idan yaso sai ki mata musun ita ”
” Aunty Yagana, dan Allah ba sai kin kira Mama ba, ni fa bazanyi Amfani da wannan layar ba koda na karɓa jefar da ita zanyi, kinga time dawowar DOCTOR yayi yanzu haka nayi imanin ya na hanya ki tashi ki tafi kar yazo ya sameki rai ya ɓaci kinsan halinsa.”
Falmata ta faɗawa Yagana hakane kawai dan ta samu ta tafi badan Hassan zai dawo ba domin kuwa dawowarsa babu lokaci sai sanda yaga dama.
Taɓe bakinta Yagana tayi tare da miƙewa ta zari jakarta tana cewa.
” Bani kuɗin nafef ke kika sani da wahalar ki jiki magayi ai.”
Falmata ɗago kanta tayi tace.
” Wallahi bani da ko sisi Aunty kiyi haƙuri dan Allah.”
” Kuɗin nafef da zaki bani ma baki dashi, hmmm!!! Cap Lallai akwai matsala, to sai anjuma.”
Ficewa tayi tana sababi ita dai Falmata jingunuwa tayi da jikin bed ɗin tana jinjinawa rashin tsoron Allah na mahaifiyarta ayi mutum baida tawakalli da yarda da ƙaddara shi boka ne kawai zai yi masa maganin Damuwar sa, tsuka Falmata taja tare da tashi, tollet ɗin DOCTOR ta shiga ta wanke tas sannan ta fito ta gyara masa shimfiɗar gadon nasa, ɗakin ma mopping ɗin sa tayi sannan ta fito falo, Ladiyo ƴar aikin ta ta samu zaune ta zubawa tv Ido tana kallon tashar Mbc Bollywood inda suke series mai taken *ZAUJIZ ZAUJEN* da alamu kallon yana mata daɗi, zama itama Falmata tayi tare da sakin murmushi Falmata a Kwaita da son mutane sam bata nuna ƙyama ko banbanci tsakanin ta da Ladiyo tamkar ƙanwar ta haka ta ɗauki Ladiyo Falmata cewa tayi.
” Ladiyo har kin gama aikin kenan kin zauna kallo, kedai kina son wannan series ɗin.”
Murmushi itama Ladiyo tayi tare da cewa.
” Ai Aunty tun dazu shigar Aunty Yagana na gama aikina, kuma Aunty ai series ɗin yana da ƙyau fa sosai saboda akwai soyayya.”
Dariya Falmata tayi tace.
” Ikon Allah Ladiyo sarkin son Soyayya, to Allah ya kawo miki miji na gari wanda zaku sha soyayya, yauwa idan kin gama kallon zan aikeki Monday market ki sayo min ganyen alayyaho, yau gwate zamu sha cikin gidan nan.”
Da to Ladiyo ta amsa sannan suka mayar da hankalinsu ga tv sai dai ita Falmata sam tunanin ta yana kan matsalarta ne idanunta ne kawai suke kan tv, ajiyar zuciya ta sauƙe tana jinjinawa girman matsalar dake gabanta, haka ta kasance cikin wannan yanayin.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Shi kuwa Doctor bayan ya fito daga cikin gidan nasu Darect Asibitin sa ya wuce dake unguwar *Gwange Sabon Layi* Babban privat Hospital ne wanda akayi rubutu da manyan baƙaƙe a makeken get ɗin *AJIRAM MALA SPECIAL HOSPITAL* shigewa ciki yayi, parking yayi a gefe kafin ya fito cikin izza da isa ya nufi cikin Hospital ɗin, nurse gaishe sa suke yana ɗaga musu hanu harya ƙarasa ciki, office doctor Saif zai wuce, sai ya jiyo wani sauti mai kamar hayaniya a woman word, har zai shige sai kuma ya fasa ya nufi word ɗin jin hayaniyar tayi yawa, koda ya shiga turus ya tsaya yana kallon ikon Allah, domin kuwa wata ƙaramar yarinya ce ta gagari kusan nurse Biyar, sai famar magana yarinyar take da ganinta kaga cikakkiyar ƴar *ƘAUYE* ko da yanda kake jin tsantsar zallar ruwan Barbarci a bakinta babu mis ko kaɗan da Hausa haka kuma yanayin jikinta ya nuna daga ƙauye ta fito duk da babu wata ƙazanta a jikinta.
” Na rantse da Allah babu wanda ya isa a cikin ku ya min allura azzaluman banza kawai baku da aiki sai cin zalin Mutane kunsa farin kaya kamar wasu Gawawwaki sai famar allure mutane kuke saboda zalunci to wallahi nikam uwar kuturu ma tayi kaɗan ballan tana ta makaho babu ubanda ya isa ya min allura a cikin ina ji ina gani da idanuna.”
Haushi da takaici ne ya cika wani tsohu dake zaune gefe da sandar sa a hanu cikin jin haushi yace.
” Ke dai *AI’SA* kin shiga Uku da wannan shegen bakin naki da baya mutuwa, baki da lafiyar ma bakin ki bai mutu ba, to ko kiyiwa mutane shuru ko na tashi naci ubanki da wannan sandar kin dai san halina yau naga tsiya a wajen yarinya, na kawo ki domin na sama miki lafiya shine xaki zo nan ɗin ma ki sai da mana da hali kina min iya shege to baki isa ba dole sai anyi wannan allurar ko zaki mutu.”
Nurse ɗin gabaki ɗayan su sun jiƙe da zufa tsabar uwar kokuwar da suke da yarinyar da aka kira *AI’SA* ita kuwa bakinta yaƙi mutuwa wannan dattijon yana dasa aya ta ɗaura da mayar masa da martani.
” Ni dai wallahi *BA’KURA* ban shiga Uku ba tunda ban mutu ba nida bakina ina ruwan ka dani, Ni nace ka kawo ni wajen waɗannan azzaluman ina cewa kawai kayi magani zaka saya min a cikin garin mu koma, to wallahi Allah ko zaka kasheni bazanyi wannan allurar ba, yanzu fisabilillah shikenan sai na tsaya ina kallo a soke ni da wannan kifiyar wallahi bazan yadda ba babu ruwan ka da ciwo na ka ƙyaleni idan mutuwa ma zanyi na mutu, ai dai ba nice ƴarka ba, ya’yan ka sunan kana kallon su ni sai kaga dama kamin addu’a, eheee.”
Ta ƙarasa maganar tana murguɗa masa baki DOCTOR dake tsaye ya harɗe hanu yana kallon dramar ce ya sashi murmushi mai sauti, ” Lallai wannan yarinyar ba dai daru ba, sai famar magana take tsau-tsau bakinta ko gajiya bayayi” cikin zuciyarsa yake wannan zancen ƙarasawa yayi ya taka har cikin word ɗin tare da cewa nurse ɗin dake riƙe da *AI’SA* ɗin.
” Ku saketa wannan ai ta fiku lafiya ma, yanda ta gagare ku.”
Sakinta sukayi Nurse Khadija tana cewa.
” DOCTOR wallahi bata da lafiya koda sukazo sanda aka musu gwajin maleria da typort kuma duk tana dasu a jikinta yanzun ma allurar typort ɗin zamu mata shine duk taƙi sakin jikinta sai famar dambe take damu.”
Carap AI’SA tayi tace.
” Kaji masharranta, meye kuma materia, to aniyar ku ta biku babu ƙatuwar matar da ta isa ta min wannan allurar komai girman ta koda kuwa ta kai bishiyar kuka girma ba………..”
Tsawa DOCTOR HASSAN ya daka mata tare da cewa.
” Shut’up, karna ƙara jin maganar ki cikin word ɗin nan, shegen Surutu cau-cau ko gajiya bakya yi” kallon BA’KURA DOCTOR yayi tare da cewa.
” Baba Amma dai wannan yarinyar tana da matsalar aljanu ko, ko kuma ta taɓa samun matsalar ƙwaƙwalwa ne, naga kamar babu saiti a kanta.”
” Likita Babu aljanu a jikinta ko taɓin ƙwaƙwalwa, kawai tsabar sheɗanci ne da kuma rashin kunya ya mata yawa, yanzu haka da kaji tana wannan bakin wallahi a hakan ma bata da lafiya ne da abinda zatayi sai yafi haka.”
Ajiyar zuciya DOCTOR HASSAN ya sauƙe, ita kuwa sai famar murguɗa masa baki take, ficewa ma tayi daga word tana harare harare tare da riƙe ƙugu, DOCTOR HASSAN duban Khadija yayi yace
” Ki rubuta musu magani kawai ki bar allurar.”
Yana faɗa musu haka ya fice abinsa, Khadija maganin ta rubuta ta bawa BA’KURA tace yaje ya duba chemist ya saya karɓa yayi tare da basu hkrn abinda AI’SA ta musu sannan ya fito, dube dube ya fara babu AI’SA a wajen sandar sa ya dogara, ya fito daga cikin asibitin a waje ya same ta zaune a bakin wani dakali sai famar kalle-kalle take, sandar sa ya ɗaga ya kwaɗa mata a bayanta, a razane ta tashi tare da rarumar dutse ta juyo a fusace zata zabgawa BA’KURA, Allah ya rufa asiri sukayi ido huɗu dashi ta sauƙe hanunta ƙasa tana huci.
” Wallahi Allah ya rufa maka asiri BA’KURA ban rufe idona wallahi da yanzu na lotsa maka kai, to wai ma me na maka da zaka ci zalina yanzu idan ban yafe maka ba fa ka mutu mai zaka cewa Ubangijin ka, ni dai Allah idan baka daina duka na da wannan sandar ba wata rana nice ajalinta sandar nan sai dai kuma ka sake nemo wanda zaka ɗingisa wannan gurguwar ƙafar taka dashi…………….”
Dariya BA’KURA yayi tare da ƙofa kawai suka shige cikin wani madaidaicin Chemist ya miƙa musu katin maganin suka basa kuɗin suka faɗa masa 2k ya cire ya basu sannan ya sakata a gaba suka wuce ƙauyen su………
08147537180
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(Ummu Nasmah ce)*
[8/27, 9:31 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*Na*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a duk inda kuke so da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
Waɗanda suka ce Document ɗin Ruɗanin Zuciya biyu suke so, to ga dama ta samu na gama na kuma haɗa Complete document idan kina so zaki samesa a 200 Naira only 08147537180.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*Book One*
*Page 7 to 8*
*____________________________________*
*ƘAUYEN BINISHED*
________✍🏻 Motar da suka hau tafiyar 40 minute ne ya kaisu mashigar ƙauyen nasu, a bakin ƙauyen aka sauƙe su, sannan suka kama hanyar shiga cikin ƙauyen, ƙauye ne sosai wanda bashi da yawan mutane, jejin Allah, idan kinga gidan kara ɗaya kafin ki sake ganin wani gidan sai kinyi tafiyar minti 15 mutane ɗaɗɗaya zaki dinga haɗuwa dasu, da haka har suka ƙarasa nasu gidan *AI’SA* da gudu ta ƙarasa cikin gidan sai kuma ta fashe da kuka tana ƙwalawa *KAKA* kira.
” *KAKA KAKA KAKA* !!!!”
Kaka dake zaune cikin bukkar ta ta jiyo kiran jikar tata, amsawa ta hau yi itama tana washe jajayen haƙwaranta da ta rinasu da gwarango.
” Lale maraba da dawowa ƴar albarka yarinyar kirki shigo gani a cikin bukkata zoki sanar dani wani shegen ne ya saki kuka, yanzu na tashi muje naci ubansa.”
Ƙarasowa cikin bukkar tayi tana kukan munafurci ta zauna ta hau shure-shure da ƙafa tana cewa.
” *KAKA KAKA KAKA*!!!!!”
Matsowa Kaka tayi kusa da AI’SA ta dafa mata kafaɗa tana cewa.
” *AI’SA* wai ko dai kin makance ne da kika je cikin garin nan gani ina kallon ki kina kallo na amma tsabar shashanci kita ƙwala min kira yuwa wata makahuwa me aka miki a cikin garin.”?
Kuka AI’SA ta fara tana mutstsike idon ta na karya tare da gyara zama ta fara shiryo ƙarya.
” Kaka an cuceni a cikin garin nan da mukaje, BA’KURA shima ya cuceni, kaka kinsan me yacewa wani koɗaɗɗen likita, suka dinga zagina wai cewa fa suke waini nake da shafar aljanu wai mahaukaciya ce ni Allah kaka idona idon wannan koɗaɗɗen likitan sai na shuka masa tsiya wallahi, sai ya gane Ruwa ba sa’an kwando bane, kuma kaka tsabar mungunta irin ta BA’KURA ba cewa yayi zamuje ya saimin nagani ba, to wallahi kaka ƙarya ya miki, mungunta yamin ya kaini su min allura.”
Salati kaka ta tafka tana tafa hanu tace.
” Haka BA’KURA zaimin, na ɗauki amanar ki na basa amma tsabar tsiya yace Ke ɗin ce mai shafar aljanu, to ƙarya suke kinfi ƙarfin aljanu, domin kuwa kina da Ni, ni ɗin nan da kike gani na san manya manyan aljanu guda bakwai, kuma yanzun nan zan baki addu’ar su, aljani ko wuta suka hura kibi ta ciki ki wuce, kuma shima BA’KURA zai san ya ci amanata, kinga *AI’SA* buɗe kunnenki na baki addu’ar aljanu karma bakin su ya kamaki kinsan wani mutum bakin sa guba ne.”
Tura baki AI’SA tayi tace.
” Kaka akwai wata addu’a ne bayan wanda Baba ya bani ta surorin baƙara da Falaƙi da nasi.”
Kaka cewa tayi
” Ke dallah wannan addu’ar da zan baki itace tafi komai korar aljanu su aljanun sune suka bani addu’ar da kansu, ke kinsan waye ni kuwa to bari kiji addu’ar, *SHUKURAJU MANGA GINNI, SHURƁANJO MANGA GINNI, MAHALFINI GA ALLAH GA SURATUL WALIYIL GINNI*.” kinga wannan addu’ar dana baki sahihiyace sunan manya manyan aljanu ne idan kika yita to karkiji tsoron aljanu na faɗa miki ko wuta suka hura shige ta ciki ki wuce sanyi ƙalau zakiji babu zafi.”
Fanta ƴar AI’SA dake kwance kan gadon kaka tana jin duk abinda suke faɗi ne, ta saka dariya dama dariyar cinta take tun sanda aka fara addu’ar cikin dariyar Fanta tace.
” 🤣lallai kuwa zaki ƙone ƙurmus babu mai ciro ki, yau naji wata addu’a a wajen kaka to waima ke kaka a ina kika gamu da aljanun har suka baki addu’ar😄”
Ta ƙarasa maganar cikin dariyar domin kuwa sosai kaka yau ta bata dariya ” su SHUKURAJU MANGA GINNI manya manyan Aljanu😄 cikin zuciyarta ta yi maganar, AI’SA kuwa kallon kaka tayi ta kalli Fanta tare da dakawa fanta harara cikin rashin kunya tace.
” To ke kuma uwar gulma da saka ido waye ya saki cikin zancen mu da kakata, to wai kina nufin Kakan ƙarya ta miki, kuji ƴar shishshigin tsiya dai”
Zaro ido Fanta tayi ganin lokaci guda Ai’sa tana neman tada mata da fitina a wajen kaka to ma idan banda raini Ai’sa ce zata ce mata shegen shishshigin tsiya Fanta za tayi magana Kaka ta rigata da cewa.
” Barni da ja’ira Ai’sa to dan ubanki buɗe kunnenki kiji inda muka haɗu da MANGA GINNI ya bani wannan addu’ar”
Taɓe baki Fanta tayi tare da jefawa Ai’sa mungun kallo, kaka labari ta fara basu.
” A kwai wani lokaci munje jeji da Ba’na muna tsaka da tafiya cikin jejin nan kawai sai naji an kira sunana ance.
” Ke *YA KWALO* zoki karɓi goro, kinsan dana juya kawai sai nagan su aljanun sai bikin suna suke yanda muke bikin sunan mu suma fa haka suke nasu harda maroƙa da makiɗa , na cewa Ba’na bakaji ana kirana bane sai cemin Ba’na yayi Ke Ya KWALO ki kiyayi kanki me zakije kiyi a wajen Aljanu, nace ni sai naje yana tsaye na ƙara wajen su, suka bani goro mai yawa sannan MANGA GINNI ya bani wannan addu’ar, kinji inda na samu munafuka uwar gulma, ni nayi zaton ma bacci kike ashe shuru kikayi kina mana gulma.”
Tashi Fanta tayi tana dariya har tana riƙe ciki ta fice da ga ɗakin Kaka, domin kuwa wannan ba addu’a bace surkullen kaka ne kawai da kuma gigin tsufa daya fara cimmata, Tsuka Ai’sa taja tare da cewa.
” Kaka kina kallon tana miki dariya, tana fa nuna alamun ƙarya fa kenan kike mata, hmmm bazaki tashi ki bita har wajen Maman ba ki hukunta ta shine kika zauna kina kallon ta, duk zuciyarkin nan kaka wannan fa raini ta miki.”
Ai kuwa kamar wanda ta tunzura kaka ta miƙe tare da sandarta tana cewa.
” Ai kuwa gaskiyar ki ne Ai’sa tashi muje, naje har wajen Ferebuwayen naji idan itace ta sata ta dinga mai da min da zance.”
Tsalle Ai’sa ta saka tare da tashi tabi bayan Kaka, Fanta suna zaune da ita da Mama da kuma wansu Kacalla, sai dariya suke fanta tana basu labarin addu’ar kaka, basu ankara ba sai ji sukayi kaka tana cewa.
” Umhum ƴar Albarka Kinji zancen ki ya dawo ko AI’SA ashe da gaske Uwar taku ce take sawa a rainani a cikin gidan nan to dake wato Ferebuwaye Ni kika raina ko to bani kika Raina ba, uwarki AI’SA Wanda kika laƙabawa wannan yarinyar sunanta ita kika Raina bani ba, sandarta ta ɗaga ta kwaɗawa Kacalla a kansa tana cewa, kaikuma munafukin Allah kana namiji kana shiga cikin mata gulma to tashi kabar wajen.”
Kacalla idonsa ya ɗaga yana yiwa Ai’sa alamun zan riƙeki, kafin yace wa kaka.
” Ban tashi ba kizo ki ɗagani idan kina da ƙarfi kuma kinga wannan sandar da kika kwaɗa min akan wannan tujajjiyar mai kama da bulugari zan rama na lahira sai ya fita jin daɗi ga ta nan babbar munafuka tana biye dake kina kiran wani munafuki kaji tsohuwa da jaraba haka kawai kizo ki samu a gaba akan wannan shashsheƙar ta sakoki gaba.”
Mama doge bakin Kacalla tayi tana cewa.
” Karna ƙara jin bakin ka tashi ka fice Kaltin abokiyar wasan kane (dake haka take kiran kaka dashi), ɗauki abincin marar lafiyar da aka kawo ka kai musu kafin mahaifinku ya dawo daga gona.”
Tashi Kacalla yayi yana hararar kaka ya ɗauki abincin ita kuwa kaka ƙwafa tayi sanda yazo fita da gangan ya jide ƙafar AI’SA ji kake gum ta faɗi ƙasa, dariya Kacalla yasa tare da saurin shigewa yana cewa.
” Gobe ki sake munafurci ina dai-dai dake.”
Kaka salati tasa tana cewa.
” Ferebuwaye kina kallon baƙar muguntar da Kacalla ya yiwa wannan yarinyar ko, kina kallo ko, bari uban nasu ya dawo zai shiga tsakaninki da waɗannan baƙaƙen mugayen tashi kinji.”
Tana callara kuka ta tashi tare da riƙe kanta da ta bige, tana tsalle.
” Na rantse da Allah bazan yadda ba sai na rama wallahi bazan yadda ba, da gudu ta juya zata bi Kacalla Mama ta daka mata tsawa.”
Dawo nan karki yadda ki bisa wallahi idan kuma kika bisa bayan ya dako ki nima ƙara miki zanyi, tunda baki da mutunci baki da kunya, ba yayanki bane da………..”
Kaka ce ta dakatar da Mama tana cewa.
” To ya isheki haka zaginta, sai ku daketa tunda jaka ce ita, to naga ɗan iskan da zai daketa a wannan gidan Ferebuwaye ki kiyaye ni Allah zan iya sawa BA’GAJI ya sakeki kibar gidan nan akan wannan yarinyar muddun baki fita harkarta ba.”
Hanun AI’SA taja suka bar wajen tana sababi.
Mama dai shuru tayi bata kula Kaka ba amma cikin zuciyarta tana jin takaicin yanda ta lalata AI’SA yarinya duk ta zama marar kunya babu wanda ya isa ya mata faɗa daga ni har ubanta bamu isa da ita ba ya Allah ka shirya min AI’SA.
Mama tayi Maganar tana ƙwafa tare da cigaba da iza wuta, Fanta ma tashi tayi bata ce komai ta ɗauki garin tuwo ta fito waje ta fara tankaɗe itama tana jinjinawa Rashin Kunyar AI’SA.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*CIKIN MAIDUGURI*
DOCTOR shine bai dawo cikin gidan sa ba sai misalin goma na dare, lokaci ne ya ƙure masa a Hospital ko gidan nasu bai samu ya koma ya duba jikin Umman sa ba, tsap ya sami falon sai tashin ƙamshi yake ita kuwa Falmata tana zaune ɗaya daga cikin kujerun falon tasha kwalliya cikin wandon jean three cutter da kuma wata ƙaramar best wanda tasha mata jiki, gashin kanta kuwa ta ƙullesa da Ribon ko ɗan kwalo bata sa ba sosai tayi kyau, Ganinta cikin falon yasa DOCTOR ya fasa yin sallamar da yayi niya, kansa ya ɗauke tamkar bai ganta ba ya wuce Bedroom ɗinsa, wani irin tuƙuƙun baƙin ciki Falmata taji a cikin ranta duk wannan kwalliyar tayi ne ko zata samu ta burgesa amma ko arzikin kallo bata samu ba a wajensa wannan wacce irin ƙiyayya ne haka, wani irin girman laifi na masa haka “anya kuwa iya ƙiyayyar iyayena ne yasa DOCTOR yake gwada min wannan tsanar ko dai na masa wani laifi ne mai girma wanda ni ban sani ba, Allah gani gareka kana kallon halin da nake ciki Allah ka sauƙaƙa min wannan baƙin cikin dake damun Zuciyata” duk cikin zuciyarta take wannan zancen, hawaye ne ya gangaro mata daga idanunta hanu tasa ta goge tare da jingina kanta jikin kujerar ta rufe idanunta tana jin ƙirjinta yana mata ƙuna.
Shi kuwa DOCTOR wayar sa ya ajiye da kay ɗin sa a bedsite drower sannan ya hau cire kayan jikinsa towel ya ɗauka ya ɗaura a ƙugunsa sannan ya shige tollet wanka yayi, bayan ya fito daga wankan ne ya tsane ruwan jikinsa da ƙaramin towel body spray kawai ya fesawa jikinsa sannan ya ɗauki wasu blue ɗin sleeping dress ɗinsa na maza ya sanya a jikinsa, wayoyinsa ya ɗauka ya fito falo, darect daining table ta nufa, Falmata dake zaune har yanzu a inda ya barta ne ta zaro idanunta ganin DOCTOR ya nufi daining domin kuwa ko a mafarki bata taɓa tsammanin zai ci abincin gidan ba, saboda ya juma baya cin abincin ta, gashi ƙwate tayi ɗan kaɗan bata dafa dashi Bama, “yau kuma na shiga Uku ta furta a zuciyarta” cike take fal da tsoro, shi kuwa zama yayi a daining ɗin kawai ba tare daya ce mata komai ba, danne danne kawai ya hauyi da wayarsa cike da tsoro Falmata ta tashi ta nufe sa tsayawa tayi tare da cewa.
” Kayi hkr DOCTOR banyi tunanin……..”
Tsuka mai ƙarfi yaja tare da ɗaga mata hanu.
” Please leave me alone, ki daina shiga rayuwata fa, wai dole ne sai kin haɗa rayuwarki da tawa, ko dole ne sai kin min Magana Mtsss!!! Duk sanda Allah ya haɗa ka rayuwa da Maye ka shiga Uku ni kuma tawa jarrabawar kenan Auren irin tsiya, mema zai hana ba za kiyi maita ba, kinsha nonon Yana mtsss!!!.”
Ya ƙarasa maganar cikin tsaki, yana maida idanunsa kan wayarsa, Falmata wani irin raɗaɗi taji yanda DOCTOR yake zage mata iyayen ta babu ko kunyar idanunta, idan ba kunnenta ne suka jiye mata ƙarya ba kamar ma kiran sunan mamanta yayi babu ko sayawa, bata so magana amma dole sai tayi koda kuwa kasheta DOCTOR zaiyi.
” Kana kirana da mayya banajin zafin sa sosai, amma sai dai yau da ka danganta maitar da Mahaifiyata sai naji yamin ciwo sosai a cikin Raina, Doctor Sunan mahaifiyata ka kira fa baka saya ba, karka manta da komai lalacewar iyaye ɗansu yana sonsu, bai kamata ka ciwa iyayena mutunci a gabana ba, tunda ko ba komai surukan ka ne, baka kyautatawa zuciyata ba, DOCTOR.”
Ta ƙarasa Maganar cike da rauni hawaye na zuba daga idanunta, tunda ta fara Maganar doctor yake sauraron ta ba tare daya dakatar da ita ba, sai da takai ƙarshe tukunna kafin ya ɗago ya kalleta yana sakin murmushin gefen baki kafin yace.
” Hmmm!!!! Ai daman zafin shi nakeso kiji, Idan na kira sunan mahaifiyarki sunan mahaifiyata na kira, ko kuma ni ta haifeni ne, ƙarya nayi ba YANA ake kiranta dashi ba, ko dan bakiji na kira asalin sunan nata ba, YAHANASU, komai lalacewar iyaye tabbas ƴaƴan su suna sonsu amma ba irin lalacewar iyayenki ba na rashin albarka, tir da iyaye irin naki, sannan tunda naci mutuncin iyayenki ai sai kimin hukunci, bana ɗaukar iyayenki a matsayin surukai na, ina ɗaukar sune a matsayin wanda aka zalunta da wanda yayi zaluncin ma’ana dai ina ɗaukar su ne a matsayin azzalumai maha’inta waɗanda bazasu gama da duniya lafiya ba Mtsss.”
Ya Kawo ƙarshen maganar tare da buga table ɗin dake gabansa ya miƙe ya bar Falmata tsaye cikin tashin hankali da munguwar damuwa, bakinta nauyi ya mata ta kasa magana jin mugayen kalaman da DOCTOR yake faɗa mata, kuka ta saki tare da shigewa Bedroom ɗin ta da gudu ta faɗa saman bed ɗin ta tana sakin kuka mai cin zuciya, sosai take kukan tana Allah wadarai da halin iyayenta da suka ja mata tsana idan har sun aikata abinda DOCTOR yake zarginsu dashi me zatayi ta dawo da DOCTOR hayyacin sa domin ta fara zargin cewa DOCTOR baya cikin tunanin sa, anya kuwa wannan abubuwan da suke faruwa basu sashi ya fita daga hayyacin sa ba kuwa…………………..”?
Vote.
Share.
And comment.
08147537180
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*
[8/28, 5:34 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤️ *Love and romantic and funny story* ❤️
*Na*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a duk inda kuke so da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
Waɗanda suka ce Document ɗin Ruɗanin Zuciya biyu suke so, to ga dama ta samu na gama na kuma haɗa Complete document idan kina so zaki samesa a 200 Naira only 08147537180.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*Book One*
*Page 9 to 10*
*____________________________________*
_______✍🏻sosai Falmata take sambatu cikin kuka daren ranar Falmata baccin ta kaɗan ne, washe gari da ciwon kai ta tashi mai zafin gaske koda wanka ma daƙyar ta iya yinsa ta dawo ta kwanta shuru tayi tana tunanin rayuwarta ta baya har yanzu hawaye bai daina gudu a fuskar ta ba, ina ma ana tariyo Rayuwar baya tabbas da ta tariyo tata ko zataji sauƙin damuwar ta.
Shi kuwa DOCTOR ƙarfe tara ya fito daga Bedroom ɗinsa cikin shirin sa na fita aiki, breakfast ya gani jere saman table da alamu dai Ladiyo ce tayi, daining table ɗin ya nufa domin kuwa yunwa yake ji sosai jiya babu abinda yasa a bakin sa, plast ya jawo ya haɗa tea mai kauri bread ya ɗauka tare da ƙwai, ya fara ci a hankali, sanda ya gama sannan ya goge bakin sa da tissue jakarsa ya ɗauka sannan ya fice ba tare daya duba Falmata ko lafiya ba kasancewar bai ganta ba kuma ya saba kullum ta saba shigowa ta gaishe sa koda kuwa bazai amsa ba, ita kuwa tana kwance taji tashin motar sa alamun ya fita wasu hawayen ne suka ƙara sauƙa mata masu ɗumin gaske, wato ko mutuwa tayi sai dai idan ta ruɓe aji warin ta DOCTOR bazai shigo ya duba halin da take ciki ba.
Cikin wannan yanayin ta kasance, har kusan ƙarfe 12 na rana tana nan kwance cikin Bedroom ɗin ta bata fito ba Ladiyo ce ta shigo Bedroom ɗin da Sallama, amsa mata Falmata tayi muryar ta adashe kasancewar kukan da tasha, ƙarasowa Ladiyo tayi ta gaishe ta tare da cewa.
” Aunty Lafiya tun safe baki fito falo ba.”
Murmushin da yafi kuka ciwo Falmata tayi tace wa Ladiyo.
” Kaina ke ciwo Ladiyo”
” Ayya sannu Aunty Allah ya baki lafiya dama baƙuwa kikayi Ƙawarki Aunty MAJI shine nace fa nazo na sanar dake.”
” Kice mata ta ƙaraso.”
Tashi Ladiyo tayi taje ta sanar da Maji, maji ƙarasawa tayi cikin Bedroom ɗin Falmata, a bakin bed ɗin ta zauna tana ƙarewa ƙawar tata kallo tace.
” Falmata lafiyar ki kuwa kinga yanda kika rame kikayi duhu, idanunki duk sun zurma, Zaki kashe kanki Falmata akan ɗa namiji da bashi da tabbas, ki dawo hankalin ki ki cire damuwar DOCTOR a ranki idan ba haka ba zaki sawa kanki cuta kin daina zuwa makaranta anyi lectures da yawa babu ke gashi har ana daf da fara test abinda ya kawo ni kenan na sanar dake gobe ki shiryawa zuwa school idan ba haka wallahi za kiyi rippit.”
Tashi Falmata tayi ta zauna tare da goge hawayen dake bin fuskar ta tace
” Maji damuwa ai ta zama dole a gareni babu ta yanda zan iya gogeta a zuciyata muddun ba farin ciki na bane ya dawo, nida banza ɗaya nake a wajen DOCTOR baya son koda gani nane Maji, ban san mena masa ba, shi yana ɗaukar laifin iyayena ne yana ɗaurawa a kaina, Ban taɓa jin inda aka ɗaura laifin wani a kan wani ba sai DOCTOR, wallahi maji bana jin daɗin zaman gidan nan duk yanda naso na fahimtar da DOCTOR mu samu masalaha yaƙi fahimta Maji ba dole damuwa ta dameni ba, shiyasa komai na duniya naji ya fita a Raina, makarantar ma naji bana son zuwa saboda koda naje babu abinda zan gane, sai da nutsuwa ake gane karatu Maji, ni kuma bani da nutsuwa.”
Shuru Maji tayi tana jin tausayin ƙawar tata, hanu Maji tasa ta gogewa Falmata hawayen ta .
” Hakane ƙawata tabbas akwai ciwo ace mijinka ya juya maka baya, ni lamarin mijinki yana bani mamaki wai duk Soyayyar da yake miki kamar zai haɗiye ki yanzu babu ita ta juye ta koma tsana, kai gaskiya DOCTOR baya ƙyautawa ko kaɗan, amma ƙawata ki cigaba da hkr insha komai yayi zafi zaiyi sauƙi babu abinda bazai wuce ba sai ikon Allah, ki cigaba da masa biyayya kamar da karki fasa, koda yana hantarar ki, bautar Ubangijin ki kike yi, sannan abinda nake so dake ki rage yawan damuwa karki sawa kanki hawan jini, sannan ki koma makaranta shima zai ɗebe miki kewar wata damuwar domin yafi zaman da kike ke kaɗai a gida, insha Allah farin cikin ki zai dawo kuma nima zan tayaki da addu’a .”
” Hakane Maji na gode insha Allah gobe zanzo school, Ya Mama.”
” Mama lafiyar ta ƙalau tace ma na gaishe ki.”
” Ina amsawa.”
” Kawata da alamu dai bakici komai ba tun safe Ko naga kamar kinyi yanayi da mai jin yunwa.?”
Ajiyar Zuciya Falmata ta sauƙe tace.
” Wallahi kaina ke ciwo ban fita falon bama tun safe ina nan kwance wanka kawai nayi.”
” To ai kuwa ya kamata ki tashi muje kici abinci sai kisha magani idan yaso ki dawo ki kwanta nasan baza’a rasa magani ba a gidan likita.”
” Akwai a Bedroom ɗin sa.”
To tashi muje ki ɗauko kizo kisha koda ruwan tea ne sai ki kwanta nima ba jumawa daman zanyi ba, zan shige shagon saloon ne zan wanke kaina ”
Tashi Falmata tayi tana cewa.
” Nayi zaton fa wuni zaki min har ina murna, kice kuma tafiya zakiyi gaskiya ban so haka ba.”
” Kinga Hajiya tashi muje kisha magani ina kallonki kafin na tafi.”
Murmushi Falmata tayi tana tashi tare da cewa.
” To Mama Maji muje.”
Dariya Maji tayi sannan ta tashi suka fito falon tare, Falmata Bedroom ɗin DOCTOR ta shige ɗauko magani ita kuma maji ta shige daining table ta haɗawa Falmata tea, Falmata na zuwa maji ta miƙo mata tea ɗin tana cewa.
” Gashi karɓi kisha.”
Karɓa Falmata tayi tana kallon Maji cike da ƙauna, domin kuwa ƙawarta ce tun na yarinta tare suka girma komai tare suke yi, Babu wanda yake son yaga ɗaya daga cikin su yana cikin damuwa, suna ɗaukar damuwar ɗaya daga cikin su damuwar su duka, Falmata tea ɗin tasha haɗe da maganin sannan ne maji tace.
” To Allah ya baki lafiya ni zan tafi sai mun haɗu gobe a school dan Allah ki rage yawan damuwa da tunani saboda kare lafiyar ki.”
Murmushi Falmata ta saki tare da cewa.
” Ameen insha Allah zanyi ƙoƙari wajen ganin na kiyaye, ki gaishe da Mama.”
” Za taji” Maji tace tare da ficewa, Falmata ma Bedroom ɗinta ta shige ta kwanta, bata juma da kwanciyar ba bacci ya ɗauke ta.
Zaune yake a office ɗin nasa, bayan ya ɗan samu nutsuwa na duba patient ne ya ɗaga wayar sa, My dear sister na gani a rubuce, jikin screen ɗin wayar ringing ɗaya AJIRAM ta ɗaga.
” AJIRAM ya jikin Umman dai, yau ban samu na shigo ba, na fito a ƙurarren lokacine gashi kuma ina da wanda zan duba a wannan lokacin ya jikin nata.”
Daga can AJIRAM tace.
” Eh to da sauƙin musulunci amma yau tun safe bige-bige take tun ɗazu hankali na yake tashe, gashi ni ɗaya ce Fanna bata nan.”
Cikin tashin hankali DOCTOR yace.
” Subabanallah yau kuma bige-bigen ne ya tashi, yanzu ya kenan ko nazo ne.”
” A’a ba sai kazo ba da sauƙi domin da na mata hayaƙin maganin nan bacci ya ɗebeta.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya sauƙe tare da furta.
” Alhamdulillah, ina zuwa da yamma naga jikin nata ki kula da ita sosai idan kinga abinda bazaki iya ba kiyi kirana.”
” Shikenan to sai kazo.”
Kashe kiran DOCTOR yayi, yana jawo wata farar takadda gabansa, Nocking ɗin ƙofa yaji anyi.
” Yes come.”
Buɗe ƙofar Maji tayi ta shigo da Sallama, murmushi DOCTOR yayi ya amsa sallamar tare da cewa.
” Yau babbar baƙuwa ce kenan nake da ita.”
Dariya Maji tayi tana zama tace.
” Ga dai ƙaramar baƙuwa, Ya aikin.”
” Aiki Alhamdulillah amma ba daɗi, kwana biyu kin ɓuya bana ganinki ko a online ne.”
Murmushi Maji tayi tace.
” Dama aini ba gwanar hawa online bane, amm DOCTOR wajen ka fa nazo Allah yasa na samu lokacin kasancewar nazo maka lokacin da bai dace ba lokacin aiki.”
Murmushi DOCTOR yayi yace mata.
” Aikuwa kin iya zuwa a Sa’a domin kuwa yanzu ina Free ne aikin yayi sauƙi.”
” To Alhamdulillah haka nake so, amm DOCTOR nazo ne game da Case ɗinku da Falmata, a gaskiya DOCTOR baka kyautawa Falmata domin kuwa kana zaluntar ta da yawa kaga kuwa yanda Falmata tayi baƙi ta rame ta fita hayyacin ta, sai kace ba Falmata ba, wai dan Allah DOCTOR na tambayeka ashe dama laifin wani yana shafar wani? Taya dan iyayenka sun haifeka sai ace halinku ɗaya ko ka manta da cewa nacacce yana fitowa a cikin rayayye haka kuma rayayye yana fitowa a cikin macacce, idan har mukace zamu dinga hukunta yara da laifin iyayensu, to wallahi mu jira sakamakon Ubangiji, dan Allah ka gyara zamantakewar ka da matarka, domin kuwa Allah ya baka mace ta gari wacce ko wani namiji yake neman irinta domin kuwa irinsu wuya suke yanzu bako wace mace bace take iya juran wulaƙanci daga ɗa namiji, dan koni nan bazan iya jura ba, dan Allah DOCTOR karka bari Falmata ciwo ya shigeta bata cancanci wulaƙanci daga gareka ba.”
Shuru doctor yayi yana sauraron Maganar Maji, sanda ta gama kafin ya kalleta yana sakin murmushi yace.
” Gaskiya Maji son kanki yayi yawa wato nine ma na zalunce ta, ba su bane suka zalunce mu, hmmm !! Baki san yara suna gado halin iyayensu ba kenan, to ki sani yau yaro yana gadon halin iyayensa, kinga Maji Nifa bazan iya kyautatawa Falmata domin kuwa idan na kyautata mata dole iyayenta zasuji daɗi ni kuma Bana buƙatar jin daɗin su, nafi buƙatar na gansu cikin ƙasƙanci da tashin hankali tabbas macacce yana fitowa daga cikin rayayye haka kuma rayayye yana fitowa daga cikin macacce, wannan faɗin Ubangiji ne, amma ana gadon hali, bazan miki karya ba Maji bazan iya dawo da farin ciki na da Falmata ba kiyi haƙuri kawai lokaci kawai nake jira da zan bata takaddar sakinta kowa ya kama gabansa.”
Maji wani irin haushin DOCTOR taji danne ɓacin ranta tayi tace.
” Saki fa kace DOCTOR, to ina soyayyar da kace kana mata a baya ina wannan soyayyar da kuke yiwa juna tamkar ɗaya zai haɗiye ɗaya, ina take, DOCTOR baka da tabbacin cewa iyayen Falmata sune suka ɓatar da Baba da Aunty Jalila Zargi kawai kake yi, baka da tabbas, DOCTOR na zo nan ne na faɗa maka gaskiya ka dawo hayyacin ka kafin lokaci ya ƙure maka Falmata tana maka biyayya tana kuma shanye wulaƙancin da kake mata kabar ganin tana sonka , wallahi duk sanda ka cikawa Falmata ciki DOCTOR zata bushe maka ta daina jin tsoron ka, kazo kuma kana neman tanƙwarata ta kasa tanƙwaruwa, kashi ma yazo ya fika daraja a gareta, ka dawo hankalin ka kasan me kakeyi kafin lokaci ya ƙure maka bana so kazo kana danasani.”
Dariya DOCTOR yayi yana ƙarewa Maji kallon baki da hankali kafin yace.
” Kinsan Hausawa sukace so tsuntsu ne yakan tashi daga wannan reshen ya koma wata, to haka nima babu soyayyar Falmata a cikin zuciyata, bazan taɓa danasani ba danna rabu da Falmata irin tsiya.”
” Duka ai irin naku ɗaya ne da ita domin kuwa jini ɗaya ne yake yawo a jikinku, idan irin tsiya ne ita kaga kuwa ai irin kune, idan har haka soyayya take da juyawa masoyinta baya to tabbas soyayya hatsari ne, DOCTOR ka sani cewa idan ka ci amanar Falmata Allah ba……….”
Dakatar da Maji DOCTOR yayi yace.
” Ya isa haka Maji ina ganin mutuncin ki bana son mukawo matakin da zan gaya miki maganar da bata dace ba, mubar maganar haka idan ita kaɗaice ta kawo ki, kina iya tafiya.”
” DOCTOR korata kake daga office ɗin ka saboda na faɗa maka gaskiya.”
” Saboda kin faɗa min son ranki dai, ba gaskiya ba.”
” Okay to na gode sai anjuma Allah ya baka hakuri idan har a cikin maganganu na akwai masu zafi.”
Ta ƙarasa maganar tana nufar hanyar fita DOCTOR dakatar da ita yayi yana zaro kudi daga aljihun sa dubu biyar ya ƙirgo yace.
” Ga wannan kiyi kuɗin adaidaita, Ib baya nan ya fita dana basa kay ya mayar dake.”
” Na gode bana buƙatar kuɗin ka, ina da na nafef, ka riƙesu zasu maka amfani.”
” Haushi na kikaji da bazaki karɓi kyautar dana baki ba.”
Murmushi Maji tayi tace.
” Akan me zanji haushin ka?”
” Akan kina zargina da zaluntar ƙawarki.”
” Wannan ba zargi bane abinda yake a zahiri ne.”
Tana faɗin haka ta fice da sauri, DOCTOR SAIF da zai shigo office ɗinne suka ci karo da Maji, ko kallon sa batayi ba ta shige, shi kuwa kallon mamaki ya bita dashi a ransa ya furta lafiya, yarinyar da duk inda ta ganni sai ta gaishe ni munyi wasa da dariya kafin a rabu, shigewa office ɗin yayi da Sallama ya zauna yana cewa.
” Me yake faruwa.?”
Ɗago kansa DOCTOR yayi a taƙaice yace.
” Meka gani.”?
DOCTOR Saif amsa ya basa da cewa.
” Abinda idona ya gani, kai Malam meya sami Maji naga ta fita daga office ɗin nan cikin ɓacin rai.”
” Baka tambayeta daka ganta.”
Tsuka DOCTOR Saif yaja tare da cewa.
” Bana son rainin hankali malam ya ina tambayar ka kana ƙoƙarin mai dani shashasha……………..”
08147537180
Kuyi hkr yau ban samu nayi Editing ba, sannan ku sani cikin adduar ku zan shiga axam.
Vote
Share
And comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*
[8/29, 8:59 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤️ *Love and romantic and funny story* ❤️
*Na*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a duk inda kuke so da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
Waɗanda suka ce Document ɗin Ruɗanin Zuciya biyu suke so, to ga dama ta samu na gama na kuma haɗa Complete document idan kina so zaki samesa a 200 Naira only 08147537180.
Bari nayi rawa da girgiza son so nake muku my FAN’S gaskiya naji daɗin yanda kuka amshi wannan book ɗin hanu biyu, ko wani group na shiga ruwan sharhi nake gani gaskiya naji daɗi sosai😘😘😘😘
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*Book One*
*Page 11 to 12*
*____________________________________*
_______✍🏻 Murmushi DOCTOR ya saki yana kallon DOCTOR SAIF kafin yace.
” Kaima dai kasan tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi, wai tazo min da wata banzar magana ne akan wannan yarinyar Falmata, wai nine nake zaluntar Falmata kai kaji wata banzar magana da son kai irin na Maji.”
Taɓe bakin sa DOCTOR SAIF yayi yana hararar DOCTOR yace.
” Sai ka mata rashin mutunci ko nasan amsar bazata wuce haka ba.”
” To akan me zan mata rashin mutunci meta min, amsa kawai na bata daidai da Maganar ta.”
” Hmm!!! Haba DOCTOR halinka ne ban sani ba wannan maganar kuma ai wanda bai sanka bane zaka faɗawa, shakka babu ka mata rashin mutunci, Kuma koda bansan abinda tazo maka dashi ba, nasan gaskiya ta faɗa maka tabbas kana zaluntar matar ka DOCTOR, kuma Falmata bai kamata ta samu wannan mungun sakamakon a wajen ka ba ka mata yayi ace kana riritata kamar ƙwai, ka sani Falmata fa ta soka a lokacin da baka da komai, sisin da zaka kashe, baka dashi sai an baka, a wannan lokacin idan baka manta ba samari ne masu kuɗin gaske suke zuwa wajen ta, amma taƙi su tace lallai kai take so, duk da a lokacin kakan nunku basa son Auren zumunci saboda gurɓacewar zumunta, haka Falmata ta dage sai da aka muku Auren, sanda gomnati ta ɗauki nauyin karatun mu haka yarinyar nan tayi haƙuri tana kallo ka tafi India ta jiraka a ɗakin mahaifiyar ta har tsawon shekaru bakwai ka gama karatun DOCTOR ɗin ka, ka dawo kayi sati ɗaya rak ka koma sakamakon aikin da suka ɗauke ka acan, nan ma kayi shekara biyu sannan ne ka dawo ka ɗauke ta kuka koma tare kafin daga baya ku dawo gida Nigeria, yanzu DOCTOR wannan matar data yimaka wannan soyayyar itace abar wulaƙantawa a wajen ka, ya kamata kafin ka yanke mata hukunci ka dinga tunanin baya, wallahi kaji tsoron Allah, ka daina azabtar da baiwar Allah.”
DOCTOR ɗago kansa yayi yana duban DOCTOR SAIF yace.
” Gori kake min kenan, to naji tamin halacci sai kuma akace su cuceni ko, to ban riritata kamar ƙwai ɗin ba, kaga DOCTOR SAIF dan Allah tashi ka tafi office ɗin ka, kaima idan wannan maganar zaka min na gode.”
” Gaskiya ne ai baka so, shiyasa zaka koreni, Allah ya shirya ka, amm jiya ka iso kuma na fita bamu haɗu ba, Ib ya sanar dani cewa wai a mayar da matar nan opression room.”
” Eh nine nace a maida ta saboda ya sanar dani cewa, sun bata ruwa tasha wai har cikin nata ya kumbura.”
” Kai Ib ma dai wani lokacin shashasha ne, bafa tasha ruwan ba, sun dai ɗauko zasu bata sai Allah yasa na shigo na hana su bata, kuma matar tana da tunbi ne shiyasa ina ga zaiga kamar cikin ya kumbura.”
DOCTOR cewa yayi.
” Ehh ya faɗa min jiyan dana zo, harma naje na duba ta DOCTOR SAIF bari na gudu ina son zanje na dubo jikin Umma.”
Tashi DOCTOR SAIF yayi tare da cewa.
” Okay nima bari na shige office ɗina.”
Tare suka fito DOCTOR SAIF ya wuce shima DOCTOR ya shige parking space ya ɗauki motar sa ya fice daga Asibitin ya shige family Hause ɗin nasu, kamar ko yaushe ƙofar gidan cike yake da mutane musamman dattawa, shi kuwa SARKIN yana zaune a tsakiyar su, taɓe bakin sa DOCTOR yayi ya ƙaraso wajen tare da sunkuyawa suka gaisa da dattawan ɗaya bayan ɗaya, sai dai Sarki ko YALLAƁOI zance bai samu kallon mutunci a wajen DOCTOR ba bare kuma gaisuwa, haka shima bai kulasa ba gudun ya tsinkasa a cikin talakawan sa, yau dai tsakar gidan babu taron gulma domin kuwa babu kowa sai yara dake famar wasansu, sashin su ya wuce da Sallama ya shiga, Hajjo dake tsaye bakin randa tana ɗibar ruwa ne ta amsa masa da.
” Ameen wa’alaikumussalam , ɗan halak kaƙi ambato, yanzu nake tambayar BULAMA kai yake cemin shima yanzu yake tambayar BELLO kai.”
” Kice kamar yadda nima nake neman ki kenan, Ina kuka haɗu da Bello shima nemansa nake.”
” Yana cikin ɗakin ka ƙarasa bari na kaiwa AJIRAM ruwa bayi, ina zuwa.”
Shigewa DOCTOR yayi cikin ɗakin Umman, bata nan da alamu sun Kaita tollet ne wanka, zama yayi gefen katifa tare da miƙawa Bello hanu yana cewa.
” Bawan Allah jiya na kiraka shine baka ɗaga ba kuma baka biyo kira na ba.”
Dariya Bello yayi tare da cewa.
” Bana kusa ka kira nazo kuma zanbi kiran taƙi shiga, ya aikin.”
” Aiki Alhamdulillah, jiya AJIRAM take sanar dani cewa kunyi magana akan wani mai magani da yake ƙauyen BINISHED ko.”
” Eh tabbas munyi magana, kuma gaskiya ana samun dace sosai a wajen sa, dan akwai wani mutum a bayan layin mu, shima shigen irin ciwon Umma ne, wallahi da aka kaisa can ya warke sosai.”
” To amma Bello ina dai ba ɗan tsubbu bane dan gaskiya bana son muje wajen boka.”
Dariya Bello yayi yace
” A’a wallahi ba ɗan tsubbu bane malami ne na gargajiya sannan kuma ruƙiyya, babu tsubbu a tattare dashi.”
Numfashi DOCTOR ya sauƙe tare da cewa.
” Okay ba damuwa insha Allah zamuje, kamar Ranar asabar tunda ranar ce weekend, to amma waye zai mana jagora kasan dai ni ban taɓa shiga cikin wannan ƙauyen ba.”
Bello cewa yayi.
” Zamuje tare nasan ƙauyen Saboda tare mukaje dasu, kuma malamin ya sanni sosai, wannan ba matsala fatan dai Allah yasa mu dace.”
” Ameen ma je Asabar ɗin, Ina BULAMA ne kam kwana biyu bana ganin sa.”
” Ai kuwa yanzu kikayi saɓani, dan bai juma da fita daga gidan nan ba ka shigo.”
” Okay.” Doctor ya furta a taƙaice, AJIRAM da Hajjo ne suka shigo riƙe da Umma sun mata wanka kwantar da ita sukayi, DOCTOR duban mahaifiyar tasa yayi da idanunta suke buɗe kamar zaka mata magana ta amsa sai dai ina babu baki, hanunta ya riƙe tare da cewa
” Sannu Umma Allah ya baki lafiya.”
Duban Hajjo yayi yace.
” Hajjo alfarma nake nema a wajen ki, ina son zaki dawo ki karɓi AJIRAM jinyar Umma, ita ta koma gidan mijinta ta kula da yaranta, tunda kinga ke kina zaune a gida ba aure.”
Murmushi Hajjo tayi tace.
” Haba Hassan har sai ka nemi alfarma a wajena dan kawai na yiwa Umma jinya nima fa uwata ce Umma babu abinda bata minba a rayuwata, dan haka babu komai AJIRAM ta koma gidan ta, ni zanyiwa Umma jinya.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya sauƙe cike da jin daɗi yace.
” Hakane na gode Hajjo, to ke Kuma AJIRAM, gobe zaki koma gidan ki, idan Hajjo ta ɗauko kayan ta, sannan ranar Asabar zamuje wajen mai maganin da Hajjo zamu tafi karki ce zaki zo ki zauna a gidan mijinki idan yaso daga baya sai kije ki dubata.”
Nisawa AJIRAM Tayi tace.
” Shikenan yaya Allah ya kaimu goben.”
Da ameen ya amsa, Hajja ce ta shigo da Sallama, amsawa sukayi DOCTOR ya ɗaga ido ya kalleta yana sakin murmushi, Hajja kusa da DOCTOR ta zauna tana sakin masa dundu a baya tace.
” Ja’iri jiya da ka gudun yanzu bamu haɗu bane.”
Dariya DOCTOR yayi tare da cewa.
” Kinga Malama Hajja, ni bana son yawan Magana karki dameni.”
Dariya Hajja tayi tana duban Umma tace.
” Sannu Yamuram kina fama da bautar Ubangiji, Allah ya baki lafiya Allah ya sa zakkar jiki ne” kallon DOCTOR Tayi tace.
” Hassan yanzu babu inda za’a kai Yamuram haka za’a barta a gida, nifa gaskiya bana jin daɗin zaman ta haka ba tare da annemi wani me magani an Kaita ba , duk da kuna karɓowa amma dai ya kamata a ƙara dagewa.”
DOCTOR cewa yayi.
” Hajja yanzu ma maganar da muka gama kenan munji labarin wani mai magani a ƙauyen BINISHED zamuje can Ranar asabar zamu kaita.”
” Yauwa to Alhamdulillah hakan yafi ai”
Hajjo ce tace.
” Sannu Hajja ina kwana.”
Murmushi Hajja tayi tace.
” Hajjo lafiya lau ya uwar taki Merama”
” Lafiyan ta lau tana gaishe kuma.”
” Muna ansawa da kyau,”
AJIRAM ma gaida Hajja tayi tana cewa.
” Ina zuwa haka Hajja naga kinsha sari, unguwa ne.”?
” Gidan wannan ja’irin wannan wannaki zanje na dubo Falmata, kwana biyu shuru babu labarin ta, tashi ma mu tafi ka sauƙeni.”
Hajja ta ƙarasa maganar tana jan kunnen DOCTOR, doctor bai kalli Hajja ba yace.
” Da banzo ba kuma waye zai kaiki.?”
Dariya Hajja tayi tace.
” Kuɗina ne zasu kaini.”
DOCTOR cewa yayi.
” Yanzu ma kuwa sai kuɗin naki su kaiki domin kuwa ni ba gida na nufa ba asibiti zan koma.”
Hajja cewa tayi.
” Baka isa ba wallahi dole sai ka kaini idan yaso ka juya asibitin.”
Juyowa yayi ya fuskanci Hajja yana ƙare mata kallo yace.
” Zaro min idanun da kike ne zaisa naji tsoron ki na kaiki, ke dai malama bini a hankali kawai na kaiki.”
Tare suka saka dariya Hajja tace
” To naji angon Hajja, ka dai san bama faɗa ko, tashi mu tafi uban masu gida.”
Dariya DOCTOR yasa tare da miƙewa yana cewa AJIRAM.
” Ina FANNA taje ne ban ganta ba.?”
AJIRAM cewa tayi.
” Na aiketa gida na, amma ina ga tama kusa dawowa.”
Okay ya amsa yana cewa Bello.
” Sai Asabar ɗin ka shirya zan kiraka, Hajja muje na sauƙe ki na wuce.”
Tashi Hajja tayi suka fice mota DOCTOR ya buɗe mata ta shiga sannan shima ya zaga ya shiga yaja motar suka tafi.
DOCTOR hom ya danna a ƙofar gidan mai gadin ya fito da sauri ya buɗe get ɗin, a compaunt ɗin gidan DOCTOR ya tsaya tare da buɗewa Hajja yace.
” To Bismillah fita ni juyawa zanyi.”
” Kai!!! Wai dama da gaske asibitin zaka koma.”
Dariya DOCTOR yayi yace.
” Au dama kinyi zaton wasa nake miki, asibiti zan koma ban gama aikina ba yaushe zaki koma na turo azo a ɗaukeki.”
” To Allah ya tsare a dawo lafiya, eh to ina ga zuwa ƙarfe biyar.”
Ta ƙarasa maganar tana fita da Allah ya kaimu DOCTOR ya amsa sannan ya juya ita kuma Hajja ta shige cikin gidan……….
Vote
Share
And Comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(Ummu Nasmah ce)*
[8/30, 7:26 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤️ *Love and romantic and funny story* ❤️
*Na*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a duk inda kuke so da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
Waɗanda suka ce Document ɗin Ruɗanin Zuciya biyu suke so, to ga dama ta samu na gama na kuma haɗa Complete document idan kina so zaki samesa a 200 Naira only 08147537180.
Bari nayi rawa da girgiza son so nake muku my FAN’S gaskiya naji daɗin yanda kuka amshi wannan book ɗin hanu biyu, ko wani group na shiga ruwan sharhi nake gani gaskiya naji daɗi sosai😘😘😘😘
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*Book One*
*Page 11 to 12*
*____________________________________*
_______✍🏻 Murmushi DOCTOR ya saki yana kallon DOCTOR SAIF kafin yace.
” Kaima dai kasan tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi, wai tazo min da wata banzar magana ne akan wannan yarinyar Falmata, wai nine nake zaluntar Falmata kai kaji wata banzar magana da son kai irin na Maji.”
Taɓe bakin sa DOCTOR SAIF yayi yana hararar DOCTOR yace.
” Sai ka mata rashin mutunci ko nasan amsar bazata wuce haka ba.”
” To akan me zan mata rashin mutunci meta min, amsa kawai na bata daidai da Maganar ta.”
” Hmm!!! Haba DOCTOR halinka ne ban sani ba wannan maganar kuma ai wanda bai sanka bane zaka faɗawa, shakka babu ka mata rashin mutunci, Kuma koda bansan abinda tazo maka dashi ba, nasan gaskiya ta faɗa maka tabbas kana zaluntar matar ka DOCTOR, kuma Falmata bai kamata ta samu wannan mungun sakamakon a wajen ka ba ka mata yayi ace kana riritata kamar ƙwai, ka sani Falmata fa ta soka a lokacin da baka da komai, sisin da zaka kashe, baka dashi sai an baka, a wannan lokacin idan baka manta ba samari ne masu kuɗin gaske suke zuwa wajen ta, amma taƙi su tace lallai kai take so, duk da a lokacin kakan nunku basa son Auren zumunci saboda gurɓacewar zumunta, haka Falmata ta dage sai da aka muku Auren, sanda gomnati ta ɗauki nauyin karatun mu haka yarinyar nan tayi haƙuri tana kallo ka tafi India ta jiraka a ɗakin mahaifiyar ta har tsawon shekaru bakwai ka gama karatun DOCTOR ɗin ka, ka dawo kayi sati ɗaya rak ka koma sakamakon aikin da suka ɗauke ka acan, nan ma kayi shekara biyu sannan ne ka dawo ka ɗauke ta kuka koma tare kafin daga baya ku dawo gida Nigeria, yanzu DOCTOR wannan matar data yimaka wannan soyayyar itace abar wulaƙantawa a wajen ka, ya kamata kafin ka yanke mata hukunci ka dinga tunanin baya, wallahi kaji tsoron Allah, ka daina azabtar da baiwar Allah.”
DOCTOR ɗago kansa yayi yana duban DOCTOR SAIF yace.
” Gori kake min kenan, to naji tamin halacci sai kuma akace su cuceni ko, to ban riritata kamar ƙwai ɗin ba, kaga DOCTOR SAIF dan Allah tashi ka tafi office ɗin ka, kaima idan wannan maganar zaka min na gode.”
” Gaskiya ne ai baka so, shiyasa zaka koreni, Allah ya shirya ka, amm jiya ka iso kuma na fita bamu haɗu ba, Ib ya sanar dani cewa wai a mayar da matar nan opression room.”
” Eh nine nace a maida ta saboda ya sanar dani cewa, sun bata ruwa tasha wai har cikin nata ya kumbura.”
” Kai Ib ma dai wani lokacin shashasha ne, bafa tasha ruwan ba, sun dai ɗauko zasu bata sai Allah yasa na shigo na hana su bata, kuma matar tana da tunbi ne shiyasa ina ga zaiga kamar cikin ya kumbura.”
DOCTOR cewa yayi.
” Ehh ya faɗa min jiyan dana zo, harma naje na duba ta DOCTOR SAIF bari na gudu ina son zanje na dubo jikin Umma.”
Tashi DOCTOR SAIF yayi tare da cewa.
” Okay nima bari na shige office ɗina.”
Tare suka fito DOCTOR SAIF ya wuce shima DOCTOR ya shige parking space ya ɗauki motar sa ya fice daga Asibitin ya shige family Hause ɗin nasu, kamar ko yaushe ƙofar gidan cike yake da mutane musamman dattawa, shi kuwa SARKIN yana zaune a tsakiyar su, taɓe bakin sa DOCTOR yayi ya ƙaraso wajen tare da sunkuyawa suka gaisa da dattawan ɗaya bayan ɗaya, sai dai Sarki ko YALLAƁOI zance bai samu kallon mutunci a wajen DOCTOR ba bare kuma gaisuwa, haka shima bai kulasa ba gudun ya tsinkasa a cikin talakawan sa, yau dai tsakar gidan babu taron gulma domin kuwa babu kowa sai yara dake famar wasansu, sashin su ya wuce da Sallama ya shiga, Hajjo dake tsaye bakin randa tana ɗibar ruwa ne ta amsa masa da.
” Ameen wa’alaikumussalam , ɗan halak kaƙi ambato, yanzu nake tambayar BULAMA kai yake cemin shima yanzu yake tambayar BELLO kai.”
” Kice kamar yadda nima nake neman ki kenan, Ina kuka haɗu da Bello shima nemansa nake.”
” Yana cikin ɗakin ka ƙarasa bari na kaiwa AJIRAM ruwa bayi, ina zuwa.”
Shigewa DOCTOR yayi cikin ɗakin Umman, bata nan da alamu sun Kaita tollet ne wanka, zama yayi gefen katifa tare da miƙawa Bello hanu yana cewa.
” Bawan Allah jiya na kiraka shine baka ɗaga ba kuma baka biyo kira na ba.”
Dariya Bello yayi tare da cewa.
” Bana kusa ka kira nazo kuma zanbi kiran taƙi shiga, ya aikin.”
” Aiki Alhamdulillah, jiya AJIRAM take sanar dani cewa kunyi magana akan wani mai magani da yake ƙauyen BINISHED ko.”
” Eh tabbas munyi magana, kuma gaskiya ana samun dace sosai a wajen sa, dan akwai wani mutum a bayan layin mu, shima shigen irin ciwon Umma ne, wallahi da aka kaisa can ya warke sosai.”
” To amma Bello ina dai ba ɗan tsubbu bane dan gaskiya bana son muje wajen boka.”
Dariya Bello yayi yace
” A’a wallahi ba ɗan tsubbu bane malami ne na gargajiya sannan kuma ruƙiyya, babu tsubbu a tattare dashi.”
Numfashi DOCTOR ya sauƙe tare da cewa.
” Okay ba damuwa insha Allah zamuje, kamar Ranar asabar tunda ranar ce weekend, to amma waye zai mana jagora kasan dai ni ban taɓa shiga cikin wannan ƙauyen ba.”
Bello cewa yayi.
” Zamuje tare nasan ƙauyen Saboda tare mukaje dasu, kuma malamin ya sanni sosai, wannan ba matsala fatan dai Allah yasa mu dace.”
” Ameen ma je Asabar ɗin, Ina BULAMA ne kam kwana biyu bana ganin sa.”
” Ai kuwa yanzu kikayi saɓani, dan bai juma da fita daga gidan nan ba ka shigo.”
” Okay.” Doctor ya furta a taƙaice, AJIRAM da Hajjo ne suka shigo riƙe da Umma sun mata wanka kwantar da ita sukayi, DOCTOR duban mahaifiyar tasa yayi da idanunta suke buɗe kamar zaka mata magana ta amsa sai dai ina babu baki, hanunta ya riƙe tare da cewa
” Sannu Umma Allah ya baki lafiya.”
Duban Hajjo yayi yace.
” Hajjo alfarma nake nema a wajen ki, ina son zaki dawo ki karɓi AJIRAM jinyar Umma, ita ta koma gidan mijinta ta kula da yaranta, tunda kinga ke kina zaune a gida ba aure.”
Murmushi Hajjo tayi tace.
” Haba Hassan har sai ka nemi alfarma a wajena dan kawai na yiwa Umma jinya nima fa uwata ce Umma babu abinda bata minba a rayuwata, dan haka babu komai AJIRAM ta koma gidan ta, ni zanyiwa Umma jinya.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya sauƙe cike da jin daɗi yace.
” Hakane na gode Hajjo, to ke Kuma AJIRAM, gobe zaki koma gidan ki, idan Hajjo ta ɗauko kayan ta, sannan ranar Asabar zamuje wajen mai maganin da Hajjo zamu tafi karki ce zaki zo ki zauna a gidan mijinki idan yaso daga baya sai kije ki dubata.”
Nisawa AJIRAM Tayi tace.
” Shikenan yaya Allah ya kaimu goben.”
Da ameen ya amsa, Hajja ce ta shigo da Sallama, amsawa sukayi DOCTOR ya ɗaga ido ya kalleta yana sakin murmushi, Hajja kusa da DOCTOR ta zauna tana sakin masa dundu a baya tace.
” Ja’iri jiya da ka gudun yanzu bamu haɗu bane.”
Dariya DOCTOR yayi tare da cewa.
” Kinga Malama Hajja, ni bana son yawan Magana karki dameni.”
Dariya Hajja tayi tana duban Umma tace.
” Sannu Yamuram kina fama da bautar Ubangiji, Allah ya baki lafiya Allah ya sa zakkar jiki ne” kallon DOCTOR Tayi tace.
” Hassan yanzu babu inda za’a kai Yamuram haka za’a barta a gida, nifa gaskiya bana jin daɗin zaman ta haka ba tare da annemi wani me magani an Kaita ba , duk da kuna karɓowa amma dai ya kamata a ƙara dagewa.”
DOCTOR cewa yayi.
” Hajja yanzu ma maganar da muka gama kenan munji labarin wani mai magani a ƙauyen BINISHED zamuje can Ranar asabar zamu kaita.”
” Yauwa to Alhamdulillah hakan yafi ai”
Hajjo ce tace.
” Sannu Hajja ina kwana.”
Murmushi Hajja tayi tace.
” Hajjo lafiya lau ya uwar taki Merama”
” Lafiyan ta lau tana gaishe kuma.”
” Muna ansawa da kyau,”
AJIRAM ma gaida Hajja tayi tana cewa.
” Ina zuwa haka Hajja naga kinsha sari, unguwa ne.”?
” Gidan wannan ja’irin wannan wannaki zanje na dubo Falmata, kwana biyu shuru babu labarin ta, tashi ma mu tafi ka sauƙeni.”
Hajja ta ƙarasa maganar tana jan kunnen DOCTOR, doctor bai kalli Hajja ba yace.
” Da banzo ba kuma waye zai kaiki.?”
Dariya Hajja tayi tace.
” Kuɗina ne zasu kaini.”
DOCTOR cewa yayi.
” Yanzu ma kuwa sai kuɗin naki su kaiki domin kuwa ni ba gida na nufa ba asibiti zan koma.”
Hajja cewa tayi.
” Baka isa ba wallahi dole sai ka kaini idan yaso ka juya asibitin.”
Juyowa yayi ya fuskanci Hajja yana ƙare mata kallo yace.
” Zaro min idanun da kike ne zaisa naji tsoron ki na kaiki, ke dai malama bini a hankali kawai na kaiki.”
Tare suka saka dariya Hajja tace
” To naji angon Hajja, ka dai san bama faɗa ko, tashi mu tafi uban masu gida.”
Dariya DOCTOR yasa tare da miƙewa yana cewa AJIRAM.
” Ina FANNA taje ne ban ganta ba.?”
AJIRAM cewa tayi.
” Na aiketa gida na, amma ina ga tama kusa dawowa.”
Okay ya amsa yana cewa Bello.
” Sai Asabar ɗin ka shirya zan kiraka, Hajja muje na sauƙe ki na wuce.”
Tashi Hajja tayi suka fice mota DOCTOR ya buɗe mata ta shiga sannan shima ya zaga ya shiga yaja motar suka tafi.
DOCTOR hom ya danna a ƙofar gidan mai gadin ya fito da sauri ya buɗe get ɗin, a compaunt ɗin gidan DOCTOR ya tsaya tare da buɗewa Hajja yace.
” To Bismillah fita ni juyawa zanyi.”
” Kai!!! Wai dama da gaske asibitin zaka koma.”
Dariya DOCTOR yayi yace.
” Au dama kinyi zaton wasa nake miki, asibiti zan koma ban gama aikina ba yaushe zaki koma na turo azo a ɗaukeki.”
” To Allah ya tsare a dawo lafiya, eh to ina ga zuwa ƙarfe biyar.”
Ta ƙarasa maganar tana fita da Allah ya kaimu DOCTOR ya amsa sannan ya juya ita kuma Hajja ta shige cikin gidan……….
Vote
Share
And Comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(Ummu Nasmah ce)*
[8/31, 12:50 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romance and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 13 to 14*
*_____________________________________*
*Sanda na faɗa nace dan Allah duk mai interest akan wannan book ɗin ya bibiya tun daga farko, shine kikayi kunnen uwar shegu dani, da zarar na buɗe data na ina samun saƙo sama da 150 mutane da kuma na group, ana tambayata DOCTOR HASSAN daga farko dan Allah da wanne zanji da typing ko da turo muku daga farko😩*
________✍🏻 Hajja a ƙofar falon ta tsaya tare da Sallama bakin ta kusan Uku tana sallama Falmata dake zaune tana dogon tunani bata jiyo ta ba, Hajja haɓa ta riƙe tana cewa ” ikon Allah gida ata sallama babu mai amsawa sai kace ba gidan Musulmai ba” ƙofar Hajja ta tura ta shigo kanta tsaye turus ta tsaya tana bin Falmata da kallo, “ashe dama tana falon ina sallama shine tamin shuru tsabar iya shege” ƙarasawa Hajja tayi tana cewa.
” Wato tsabar iya Iskanci shine ina sallama kika min shuru ko.”
Ta ƙarasa maganar tana zama kusa da Falmata, shuru nan ma Hajja taji Falmata bata amsa mata ba, Hajja cike da tsoron ko ta mutu ne yasata girgiza Falmata sai yanzu ta dawo hayyacin ta, cike da tsoro a firgice ta dubi Hajja sai kuma ta sauƙe ajiyar Zuciya tare da kwantar da kanta jikin kujera, tace.
” Kin tsorata ni wallahi Hajja, yaushe kika shigo banji ba.”
Taɓe bakinta Hajja tayi tana cewa.
” Ina kuwa zakiji shigowata Fatuma, kin sawa kanki tunani kina neman kashe kanki, wai ma tukunna Fatuma kin dubi kanki a madubi kuwa yanda kika rame kika ƙwanjame kika fice cikin hayyacin ki, ko dai ciki ne dake Fatuma.”
Ajiyar zuciya Falmata ta sauƙe cikin sanyin jiki domin kuwa Hajja yau itace ta biyu da tace ta rame, duban Hajja tayi tace.
” Hajja bani da wani ciki, kin san dai matsalar da nake fama da ita ta matsalar mahaifa kinga kuwa ai Hajja babu ni babu saka rai ga samun ciki, ku dai min addu’a Allah yasa na samu maganin da zai sa na samu sauƙi.”
Cike da tausayin jikar tata Hajja tace.
” Hakane Fatuma Amma ai shi ɗan adam baya fidda rai ga rahamar Ubangiji, kiyi haƙuri Insha Allah kema zaki goya ɗanki a bayan ki, har kuyi wasa da dariya dashi.”
” To Allah ya amsa wannan addu’ar taki.”
Hajja ameen tace tare da cewa.
” Amma Fatuma, yanzu na fuskanci matsalar da tasa kika yi wannan bak’ar ramar wato HASSAN shine matsalar rayuwarki ya zamo miki barazana ko, yanzu Fatuma duk wanda ya kalleki tabbas yasan kina cikin tashin hankali, abinda na guda kenan a baya na ƙi yadda da ki Auri Hassan saboda shi Mutum ne mai zafin zuciya da rashin haƙuri sannan kuma bashi da fahimta, sannan shi idan ya tashi zartar da hukuncin sa idanunsa rufewa suke baya tantance fari bare kuma baƙi babu wanda ya isa ya dakatar dashi da aiwatar da nufin sa nafi ki sanin waye Hassan a hanuna ya taso tun yana ɗan yaye, ke kuma macece mai haƙuri nasan zaki cutu da Auren sa, koda wannan al’amari bai faru ba tsakanin sa da iyayen ki, dalilin kenan da yasa naƙi wannan Auren tun farko, Fatuma soyayya ta rufe miki ido kikace lallai ke shi kike so, wannan halayyar tasa ta zafin rai da rashin haƙuri yasa Hassan yake hukunta ki da laifin da babu hanunki ciki, yanzu sanar dani wani irin mungun abu Hassan yake miki yasa har kikayi wannan ramar!!!!.”
Falmata duban Hajja tayi tana tuno da hanyar da Hajja ta nuna mata kafin Auren ta da DOCTOR, ajiyar zuciya ta sauƙe tace.
” Hajja babu komai tsakanina da mijina babu wani mungun abinda yake min, kawai Hajja wannan ramar da kike gani nayi, Allah ne kawai ya kawo ta bawai dan bana jin daɗin Aure na bane, mijina yana kyautata min iya ƙarfin sa bai rageni da komai ba, Hajja karki zargesa domin kuwa bai sani cikin faɗansa da iyaye na ba.”
Murmushi Hajja tayi tana duban Falmata cikin faɗa da tsawa tace.
” Karki maidani shasha wacce bansan me nakeyi ba, kinsan dai ni ba yarinya bace ko na haifi ubanki na haifi Uwar ki, dan haka baki Isa ki ɓoye min matsalar Auren ki ba domin kuwa ko bakin ki da zuciyarki sun ɓoye to tabbas fuskar ki ta nuna, dan haka ki sanar dani me Hassan yake miki, dan ubanki dole auren ki yazo ƙarshe da Hassan ko yaƙi Allah, domin kuwa bazan zuba ido ina kallo ana cutar da rayuwarki ba!!!.”
Cikin mungun ɓacin rai Hajja take wannan maganar, Falmata idanunta ne suka zubo da hawaye cike da tashin hankali tace.
” A’a Hajja karki shiga tsakanina da igiyar Aure na, wallahi Hajja ina son mijina bazan iya rayuwa idan babu shiba ba, Hajja kimin rai ki ƙyale wannan maganar, kije ki cigaba da min addu’a Insha Allah Ubangiji zai kawo min sauƙin lamura na kashe min Aure bashi bane masalaha a cikin wannan lamarin, tabbas DOCTOR Yana cutar dani amma Hajja ina son mijina a haka.”
” Wallahi baki isa ba Fatuma bazan zuba ido rayuwarki ta lalace ba, Fatuma ki daina biyewa soyayya domin kuwa tana gabda kaiki lahira, ki dubi ya rayuwarki zata inganta ki samu farin ciki, ki tashi ki ɗauko mayafin ki mu tafi gida kinbar Auren Hassan kenan daga yau har gaban abada, zan Kuma ci ubansa yau zaisan ya wulaƙanta ki yau naga zalunci, shiyasa YANA ta dage lallai sai ya sakeki ina hanata ashe ita ta gano abinda ni ban gani ba, ki tashi ki ɗauko mayafinki mu tafi ”
Falmata cike da damuwa take duban Hajja, muryar ta na rawa tace.
” Babu halin na saka ƙafa na biki Hajja ba tare da izinin mijina ba, saboda idan na biki bada izinin sa ba, zan fita ne cikin tsinuwar Mala’iku dan haka kiyi haƙuri Hajja bazan iya barin gida na ba, kije kimin Allah ya daidaita tsakanina da mijina, zanfi jin daɗin haka fiye da kashe min Aure da zakiyi, ina son HASSAN Hajja bazan iya rabuwa dashi ba .”
Hajja riƙe haɓa tayi tana tir da Soyayyar da Falmata take yiwa Hassan domin kuwa tana Soyayyar wahala ne Soyayyar da zata Kaita ta baro ta, Hajja sosai ranta ya ɓaci cewa tayi.
” Bazaki bini ba ko, kin gwammace ki zauna cikin wahala da kibini na sama miki farin ciki, wai wannan wata irin soyayya kikewa Hassan, ke fa Soyayyar ki bata da riba, anya kuwa akwai zuciya a ƙirjinki Fatuma ki zauna namiji yana taka ki amma a hakan kina nan maƙale a gidan sa kin gwammace wahalar da yake baki ta kashe ki idan yaso sai a fito da gawarki ko, to kinyi ƙarya dan uwarki da ubanki, na yadda bazaki bini yanzu ba, amma zaki taho idan ya baki takaddar ki.”
Hajja tana gama faɗin haka ta juya a fusace, Falmata kuka tasa mai cin rai tana tsoron abinda zaije ya dawo domin kuwa tasan halin Hajja sarai kamar yunwar cikin ta.
Hajja kuwa adaidaita ta hau, ta shige gida cike da ƙunar rai sosai yau ranta ya ɓaci taji baƙin ciki sosai da ganin halin da Falmata take ciki, mai adaidaita yana sauƙe ta Hajja ta basa kuɗin sa, shigarta cikin gidan part ɗin su DOCTOR ɗin ta shiga AJIRAM na zaune ita da Hajjo suka ga Hajja ta shigo cikin matsanancin ɓacin rai ko sallama batayi ba, AJIRAM ce tace.
” Hajja lafiya me yake faruwa.”?
Hajja bata bata amsa ba sai cewa tayi
” Ki kira min Hassan a waya, kice yazo yanzun nan ya sameni duk abinda yake ki ya barsa yazo dan ubansa.”
Tana faɗin haka ta juya ta fice daga part ɗin.
Cike da mamaki AJIRAM take duban Hajja matar da suka fita tare da Hassan ɗin suna wasa suna dariya yanzu kuma ta dawo a haka, AJIRAM wayarta ta ɗauka ta dannawa DOCTOR kira ringin ɗaya ya ɗaga tare da cewa.
” Lafiya kuwa meke faruwa yanzu fa nabar gidan.”?
AJIRAM ce masa tayi.
” Lafiya, Hajja ce tace kazo yanzun tana jiranka duk abinda kake wai ka ajiye kazo ka sameta.”
” Hajja kuma, yanzu fa muka rabu da ita, lafiya.?”
” Wallahi yaya ban sani ba, tace dai kazo yanzun nan.”
” Okay gani nan zuwa yanzun nan.”
Katse kiran DOCTOR yayi cike da mamaki, tashi yayi ya ɗauki kay ɗin motar sa, ya fito daga office tare da cewa nurse fatuma ta cewa DOCTOR SAIF yazo ya rufe masa office ya ƙarasa maganar yana ficewa, motar sa ya shige ya mata kay, cike da tunani harya iso ƙofar gidan, parking yayi tare da shigewa cikin gidan part ɗin Hajja ya shige Darect, bata tsakar gidan, ɗakin ta ya shige yana cewa.
” Wai Hajja meke faruwa ne kam, har kin dawo ne wai ”
Ya ƙarasa maganar yana ƙarasawa kusa da Hajja dake tsaye tana riƙe da kunkumi, mari Hajja ta ɗauke DOCTOR dashi, a firgice DOCTOR ya dafe gefen fuskar sa, bai gama dawowa hayyacin sa ba Hajja ta ƙara ɗauke sa da wani marin kafin ta fara Magana cikin ɗaga Murya
” Ubanka ne yake faruwa!!! Nace ubanka ne yake faruwa, ɗan iska marar mutunci, azzalumin banza, me kake ɗaukar kanka, nace me kake ɗaukar kanka, banza a banza, to bari kaji na faɗa maka dan ubanka bazan saka Ido ina kallon ka ka kashe Fatuma wallahi ƙarya kake, me ta maka kake neman kashe ta wani irin baƙin azzalumi ne kai, kana da tabbacin cewa iyayenta sune suka ɓatar da ubanka, waye shaidar ka, ka saka yarinya a gaba kana azabtar da ita, hmmm, yanzu idan Ubangiji shine ya ɗauki ran magaifinka aka ajiye maka gawarsa a gaban ka, zakayi gaba da Ubangiji ne ko kuma zaka daina Bauta masa saboda ya ɗauki ran ubanka, to bari kaji, idan ka fito ɗan halak a cikin uwar ka da ubanka ka bani takardar sakin Fatuma, ka saketa dan ubanka, banza azzalumi wanda baka san darajar ɗan adam ba.”
Tunda Hajja ta maresa har zagin da take masa DOCTOR a tsaye yaƙe ƙyam yana duban Hajja, cikin mungun ɓacin rai idanunsa sunyi jajur kamar gauta ajiyar zuciya kawai yake sauƙewa yana jin kamar ya haɗiyi zuciya ya mutu tsabar baƙin ciki, sosai zuciyarsa take tafasa tare da sake rura wutar tsanar falmata da iyayenta a cikin ransa Magana ya fara cikin ɓacin rai shima.
” Hajja marina kikayi akan Falmata, Hajja nine banza a banza kike kirana kuma azzalumi akan Falmata, Hajja duk zalunci da aka mana baki gani ba mune ma kike kira da azzalumai, kin fifita Falmata akaina Hajja.”
” Na fifita a kanka!!! Nace na fifita ta akan ka dan ubanka, wawa marar lissafi da tunani, idan ka cika mai Zuciya ka saki fatuma, zuciyarka ta banza da wofi da kana da zuciyar ai bazaka zauna da ita ba baƙin mungu wand……….”
Cike da murɗar ɓacin rai da baƙin ciki DOCTOR ya dakatar da Hajja.
” Ya isa Hajja!!! Ya isa ba dai akan Falmata kike min wannan zagin ba hmmm!!!.”
Ya ƙarasa maganar yana cije yatsa.
Itama Hajja cikin tsawar tace.
” Bai isa ba ubana zuwa zakayi ai ka dakeni ba tsawa zaka min cikakken tantiri marar mutunci azzalumin bawa to ko ubanka bai isa ya dakatar dani ba idan ina magana bare kuma ƙaramin ɗan iska.”
DOCTOR hanunsa yasa da ƙarfi ya daki gini cike da haushi, tare da hura isa mai zafi a bakin sa wani irin mungun Sabuwar tsanar falmata ne yake ji a cikin ransa, ficewa yayi da sauri, saura kadan ya bige Aunty Yana dake tsaye tun sanda ta juyo hayaniyar su tazo wajen, Aunty YANA murmushi ta saki cikin farin ciki ta ƙara cikin ɗakin Hajja tana cewa.
” Abinda nake faɗa miki kenan kika kasa ganewa, Hajja yanda yake zaluntar yarinyar…………”
Hanu Hajja ta ɗaga mata tare da cewa.
” Rufe min baki, keɗin ma kanwar lasa ce, duk abinda ya sami ƴarta ki ai laifin kune ya shafe ta, fice min daga ɗaki munafukar banza, ƙulle ƙullen ne bakya yi dukkan ku a tafin hanuna kuke, kallon ku nake tar da idanuna kuma duk na kusa maganin ku, fice bana son munafurci ”
Aunty YANA fita tayi siɗi siɗi tana tura baki, tana ƙunƙuni.
” Ai kuwa baki san ina ƙulle ƙulle ba tunda ƙulle ƙullen nawa ban taɓa biyo dashi ta kanki ba, da yanzu baki da bakin zagina, ko tsintsiya na baki nace ki share tsakar gidan nan sai kin share, ayi masifaffiyar tsohuwa ta addabi mutane.”
Ta ƙarasa maganar tana shigewa ɗakin ta, Hajja kallon Yagana dake kwance tayi a gefen ta tayi shuru tana kallon su tace.
” Tashi kema ƙaramar munafuka kinje kin kashe Auren ki, kinzo kin sani a gaba, kema na kusa dawowa kanki muddun baki fitar da miji kin bani waje ba, ki tashi kije ki kira min Yayanki Bukkar acan fadar.”
Yagana tashi tayi ba tare da cewa Hajja komai ba gudun kar masifar ta dawo kanta, ta shige kiran YALLAƁOI wanda Hajja ke kiran sa da bukkar.
Yana zaune Yagana ta samesa, ta sanar dashi sakon Hajja, kusan tare ya tashi suka shigo da Yagana, amma ita Yagana bata koma ɗakin Hajja ba tayi ɓangaren Yalwa matar baffan ta, yallaɓoi da Sallama ya shiga ɗakin mahaifiyar tasa, waje ya samu yana cewa.
” Sannu da hutawa Hajja.”
Wani irin mungun kallo Hajja tayi masa tace.
” Saboda kun barni nayi hutun, nace kun barni nayi hutun ne, munafukai waɗanda sam baƙwa ƙaunar zaman lafiya a Rayuwar ku.”
Ta ƙarasa maganar tana zama yanda zata fuskance sa, yallaɓoi cike da mamaki yake duban Hajja yace.
” Allah ya huci zuciyarki Hajja laifin mena miki.”
” Au!!! Tambayata ma kake laifin ka, to bari kaji na faɗa maka, bazaku kashe ni da baƙin ciki ba, Bukkar duk inda ka kai ɗan uwanka MALA kayi gaggawar dawo dashi idan kuma kashesa kayi ka binnesa babu wanda ya sani, to ka sanar dani a tono sa YA’YAN sa suga gawar sa, sai a samu zaman, dole ne ku gyara zamantakewar ku dan haka faɗa min ina kakai MALA DA JALILA.”
Da sauri yallaɓoi ya ɗago idanunsa a kiɗime yace.
” Wani irin Magana kike nine zan Hallaka ɗan uwana Hajja, Allah ya rufa min asiri banyi wannan lalacewar ba Hajja, taya zan Hallaka ɗan uwana wanda yafi kowa ƙaunata a duniya, wallahi wallahi wallahi ban san komai game da ɓatar Ya Mala ba, ki yadda dani Hajja.”
Hmmm!!!! Kaji munafukan Asali to ban yarda da kai ba, Bukkar nasan yanda kake son sarauta babu abinda bazaka iya aikata wa dan haka na ƙara baka umarni a karo na biyu kaje ka fito min da Ɗana da Jikata, idan kuma kaƙi na tabbata Hassan bazai taɓa ƙyale ku ba, zai fara kashe ƴarku da baƙin ciki ya kawo muku gawarta ya ajiye muku, sannan ya hanaku zaman lafiya kaga daga ni kuma sai na tattara kayana na bar muku gidan na koma gurbin gidan ubana, idan yaso sai ku kashe kanku.”
Hankalin yallaɓoi sosai ya tashi da kalaman mahaifiyar tasa, ya rasa ta ya zai fahimtar da ita bai san komai game da ɓatar ɗan uwansa, cike da tashin hankali yace.
” Hajja……….”
Dakatar dashi tayi tace.
” Bana son na ƙara jin komai daga bakin ka na gama baka umarni sakamako nake jira, tashi ka barmin ɗaki”
Tashi yayi ya fita cikin sanyin jiki da kuma damuwa, shi a ina yasan zai samo YaMala………
Ɗakin matar tasa Yana ya shige ya zauna tare da riƙe kansa yayi shuru cike da damuwa, yana dake zaune ta dubesa tace.
” Abban Falmata meya sameka ka shigo haka rai ɓace.”
Ɗago idanunsa da sukayi jajur yayi yace.
” Yana wai Hajja ni take zargi da ɓatan ɗan uwana, kamar yadda ƴaƴan sa suke zargina, Hajja ma tabi sawun su, wai naje na nemo mata Yamala duk inda na kaisa hmmm!!! Sunƙi su yarda cewa bani da hanu cikin wannan al’amari.”
Ya ƙarasa maganar cike da ƙunar rai Aunty YANA bakin ta taɓe tare da cewa.
” To sai me tunda basu yadda ba, sai su kasheka tunda suna zargin ka, kaga karka wani saka damuwar su cikin ranka bare kuma ya dameka.”
Tsuka YALLAƁOI Bukar yaja ba tare daya kuma cewa Yana komai ba domin kuwa ita ba fuskantar damuwarsa za tayi ba, ganin haka da Yana tayi itama ta watsar da zancen.
Shi kuwa DOCTOR ransa a matuƙar ɓace ya hau motar sa, ya figeta da ƙarfi, tsabar ɓacin rai idanunsa ko gani basa yi sosai, burin sa kawai shine ya gansa gashi ga Falmata, da wannan mungun tunanin yake dreving.
Allah Sarki baiwar Allah ita kuwa Falmata tun fitar Hajja daga gidan take cikin tashin hankali, tasan halin Hajja sarai yau bazata ƙyale DOCTOR ba, muddum Hajja ta sami DOCTOR ita kuma ta tabbata yau kwanan Auren ta ya ƙare, ta kasa zaune ta kasa tsaye sai kaiwa da kawowa take, ai kuwa kamar wanda aka tsikareta da sauri ta ɗauki wayar ta, numbern Maji tayi kira cikin Sa’a kuwa ta ɗaga Falmata cike da tashin hankali tace.
” Maji ki taimake ni kar Aure na ya mutu idan Aure na ya mutu nima mutuwa zanyi.”
Maji cikin ɗaurewar kai tace.
” Auren ki ya mutu, kuma, me Kuma ya ƙara shiga tsakaninku dashi.”
” Ba dashi bane Maji Hajja ne, yanzu tabar gidan nan cikin ɓacin tace lallai yau sai DOCTOR ya sake ni, na tabbata indai suka haɗu tabbas saki sai ya wajaba a kaina ki taimakeni ki dakatar da Hajja kisan yanda zaki hanata yiwa DOCTOR Magana.”
Maji tsuka taja tana cewa.
” To wai ma sai me idan ya sakeki meye amfanin Auren kin nan idan banda cutuwar da kike yi, da zakiji shawarata da kin bar Hajja ta ƙwata miki ƴancin ki, ta hakane DOCTOR zai fara fahimtar mahimmancin ki daga Ranar da kika kauce masa, Soyayyar da kike nuna masa tayi yawa itace take ƙara hura masa kai wajen ganin ya wulaƙanta ki, yana ganin koma me zai miki ai bazaki iya rabuwa dashi ba, wai ina zuciyarki take ne Falmata ki tashi ki ƙwaci yancin ki mana, meye amfanin Auren mutumin da baya ganin darajar ki da na iyayen ki da suka haife ki har ya ganki ya Aura, ki dawo hankalin ki Falmata.”
Cikin shashsheƙar kuka Falmata tace.
” Maji ba wannan maganar nake buƙata daga gareki ba yanzu, so nake ki dakatar da Hajja, ina son mijina bazan iya rabuwa dashi ba, koda kuwa naman jikina yake yanka kullum, zan zauna dashi a haka, ki taimakeni Maji karna rasa igiyar Aure na.”
Cike da jin haushin Falmata Maji tace naji zan dakatar da Hajja amma tukunna ki kira DOCTOR SAIF ya fara raba DOCTOR da wayoyin hanunsa tukunna, gudun kar kafin na isa gidan ku Hajja ta rigani kiran sa idan har kinyi haka to Tabbas zan dakatar da Hajja.”
Falmata da to ta amsa cikin sauri ta kashe kiran Maji, ta fara neman numbern SAIF sau uku tana kira zai shiga amma baza’a ɗauka ba, cikin tashin hankali Falmata ta yasar da wayar hawaye na gudu saman fuskar ta, shikenan ta shiga Uku yau zata rabu da farin cikin ta, tana cikin wannan tunanin taji wayar ta yana Ring saurin dubanta ta kai kan wayar Doctor Saif ke kira cikin sauri ta ɗaga, ko Sallama bata amsa ba tace.
” Saif kuna tare da DOCTOR ne.?”
Tambayar da ta jefa masa kenan, jin muryar ta cikin damuwa da alamun kuka yasa DOCTOR Saif cewa.
” Bama tare dashi ya fita tun ɗazu, lafiya Falmata meke damunki.”
Da ƙarfi Falmata ta furta “na shiga Uku……………..”
????????????????????????
Tabbas akwai ayar tambaya a cikin wannan cakwakiyar family……..
Shin mai zai faru, DOCTOR zai sake FALMATA?
Ina labarin AI’SA wata irin gudummawa zata bayar cikin wannan labarin ?
Shin Umma zata sami lafiya?
Shin mahaifin DOCTOR da ƴar uwarsa suna raye ko sun mutu?
Shin idan ba YALLAƁOI BUKAR bane da YANA sukayi sanadiyar rasa iyayen DOCTOR to waye ne?
Sannan su wannan family kansu ya suke rayuwarsu kafin faruwar wannan mungun al’amarin?
Amsar ku tana tattare cikin wannan littafin amma ta hanyar 👇🏻
*Kuna iya nuna min soyayya ta hanyar siyen littafinan na DOCTOR HASSAN akan Naira 300 kacal,zaku iya biya ta wannan account ɗin 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK ko kuma ku tura katin MTN ta wannan number 08147537180,sannan ku tura shaidar biya a ita ko a 08147537180 Nagode masoya,ina maraba da masu sayan ɗaya ko sari*
*Kumin adalci dan Allah kar wacce ta zageni dama bance free book bane, idan ya miki ki saya idan bai miki ba ki barmin kayana, amma dan Allah karki zageni ina maraba daku masoyana kiyi ƙoƙarin ganin kin biya naki domin kuwa tuni har an fara biya*
Akwai waɗanda suka bani kuɗin su a cikin group ɗina na Ruɗanin Zuciya biyu so dan Allah kumin magana ta pc sai nayi adding ɗinku a paid group.
Vote
Share
And Comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/1, 6:24 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romance and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 15 to 16*
*_____________________________________*
________✍🏻 Yasar da wayar Falmata tayi cikin tashin hankali ta zauna rasa ya zatayi da kanta tayi, idan har Hajja ta sami DOCTOR bata san wani irin abu bane yau zai faru tsakanin ta da DOCTOR, hawaye ne sharshar yake zuba daga ƙwayar idanunta yayin da hankalin ta yake matuƙar tashe kafin kice me har idanunta sunyi jajur, tana nan cikin wannan halin ta jiyo dirin motar sa, wani irin tsinkewa zuciyarta, tayi da sauri ta miƙe tsaye tare da zuwa window ta ɗaga labule, a yanayin yanda taga ya fito daga cikin motar tabbas yana zuciye, runtse idanunta tayi cike da tsoro ta sake labulen jikin bango ta koma ta jingina hawaye na ƙara gudu daga idanunta.
DOCTOR kuwa da ƙarfi ya turo ƙofar falon idanunsa jawur, ya shigo ba ko Sallama, a tsakiyar falon ya tsaya cak yana ƙare mata kallo yanda take rakuɓe jikin bango sai famar zubar hawayen munafurci take, a hankali yake takawa inda take yayin da ita kuma zuciyarta take ƙara tsananta bugawa a duk takawar da yayi domin nufo ta, sanda yazo daf da ita har kamar numfashin su na haɗuwa, idanunsa da suka koma kamar gauta ya haɗa da nata yana jefa mata mungun kallo mai cike da zaki gane kurenki, saurin sunkuyar da kanta tayi ƙasa, cike da tsoro,shi kuwa DOCTOR cike da mungunta ya saka hanunsa ya fisgo gashin kanta, runtse idonta tayi cike da azaba ɗago kanta yayi tare da cewa.
” Ɗago kanki ki kalleni baƙar munafuka, uban waye ya baki shawarar ki kai ƙarata wajen Hajja, Hajjan uwata ce ita ko kuma zata hanani na miki abinda naga dama ne, bari kiji abinda baki sani ba, na tsaneki fiye da yadda na tsani mutuwa ta, bazan taɓa ƙara sonki ba a cikin Rayuwata, dan haka ki daina kai ƙarata domin kuwa bazaki ƙara samun wata kulawa daga gareni ba, dan haka kije na……………”
” Ka dakata!!!! Ka dakata!!! Karka aikata babban kuskuren da bazaka taɓa iya gyara sa ba Malam Hassan.”
Daga DOCTOR har Falmata kallon su suka mayar inda sautin muryar ta fito *HABEEB* ne tsaye ya zuba hanunsa cikin aljihu kyakkyawan mutum ne fari sol tamkar bafulatani sai dai KANURI ne shi murmushi HABEEB ya saki tare da cewa.
” Abokina kayi mamakin shigowa ta cikin gidan kane akan lokaci, nazo gyara maka kuskuren kane a karo na farko, kuma na ƙarshe, kana kuskuren rabuwa da ita, ni kuma a lokacin ne zan Aure abata dama tawace ƙaddara yasa ka ƙwace ta, sam bata ma dace da miji irin ka ba damu ta dace waɗanda zamu riritata tamkar ƙawai mu bata kulawa yadda ya dace, domin Falmata matar hutu ce, ka kiyaye idan kuma baka kiyaye ba, ina nan ina jiran fitowar ta, karka manta da har yanzu akwai Soyayyar ta a zuciyar HABEEB.”
Yana gama faɗin haka ya juya ya fice da murmushi ɗauke saman fuskar sa, gagara Magana DOCTOR yayi har HABEEB ya fita daga falon wani irin baƙin ciki ne ya murɗi DOCTOR HABEEB a cikin gidan sa uban waye ya basa izinin shigo masa cikin gida, Okay wato dai har yanzu bai cire Soyayyar matar sa Falmata a cikin ransa ba, ashe har yanzu yana bibiyar ta, cikin haushin ya ƙara damƙe gashin Falmata sanda tayi ƙarar azaba, haɗa kanta yayi da bango, tare da saka ƙafarsa ya mutstsike ƙafar ta, hawayen azaba sune suka gangarowa Falmata, ita kanta ta razana da shigowar HABEEB cikin gidan nan, to wa ya turo sa? sakin ta DOCTOR yayi ba tare daya ƙara furta mata komai ba ya shige Bedroom ɗinsa cikin mungun ɓacin rai, har yana jin kamar jiri, Falmata kuka tasa tana riƙe kanta dake sara mata ga yatsun ƙafarta da take jin kamar zasu fice daga jikinta riƙe ƙafar tayi cikin kukan take furta.”
” Na shiga Uku wai me nayiwa Ubangiji ne yake jarabtar Rayuwata, wani irin laifi na aikata, ya Allah na tuba ka yafe min idan har akwai wani laifin dana maka kake hukuntani dashi, ya Allah ka daidaita tsakanina da mijina, Allah kana gani ina son mijina bazan iya rayuwa ba tare dashi ba, ya Allah ka dawo min hankalin mijina gareni, Allah ka kawo min sauƙi cikin wannan baƙin cikin da nake.”
Ta ƙarasa addu’ar tana kuka mai cin rai.
Shi kuwa HABEEB cike da tausayin Falmata ya fito daga cikin gidan motar sa ya shiga, duban sa ya kai ga Maji dake zaune cikin motar tana jiran fitowar sa tambaya ta jefa masa.
” Ya akayi Allah yasa ba dukanta yayi ba naga ka fito kamar jikinka a sanyaye.”
Ajiyar zuciya HABEEB ya sauƙe tare da cewa.
” Meyasa kika sa na dakatar da Hassan daga sakin Falmata, anya kuwa kin mata adalci, dama haka take shan wahala a gidan Auren ta, da wannan mungun zaman da Falmata take a gidan Auren ta, gaskiya ina ga mutuwar Auren ta shiyafi, tabbas Hassan ya ci amanar Falmata, Soyayyar da ta nuna masa sam bata cancanci sakamakon azabtarwa daga garesa ba, komai tsananin girman laifin da ta aikata masa, amma meyene ya jawo musu wannan zafin ƙiyayyar? Ina ku ji a jiki na kamar zuwan da nayi bai dace ba.”
” Hmmm!!! HABEEB duk wanda yasan rayuwar su a baya abinda zai faɗa kenan wanda kuma bai san rayuwarsu ta baya ba, cewa zaiyi Auren ƙiyayya sukayi, duk abinda kaga DOCTOR yana yiwa Falmata bata ganin laifin sa, sai ma ƙoƙarin da take wajen ganin ta masa biyayya, sanin matsalarsu kuma wannan family essur ne, HABEEB nima dole tasa na sanya ka cikin wannan lamarin, domin samowa Ƙawata farin cikin ta, sanin kanka kaine kaɗai mutumin da DOCTOR yaƙe shayi a cikin samarin da suka nemi Falmata domin kuwa yasan kafi sa komai kuɗi matsayi da kuma iko, hakan yasa yake mungun shakkar ka tare da kishin ka, nasan koda yayi niyyar sakin Falmata, yasan cewa kana nan kana jiranta na tabbata bazaiyi gangancin rabuwa da Ita ba, na GODE daka taimaka min wajen dakatar da DOCTOR.”
” To Allah ya sauwaƙa, nima nayi hakanne kawai domin Soyayyar da nake yiwa Falmata, har yanzu Zuciyata babu macen da take so sama da ita Soyayyar ta a jinina take bazan taɓa daina sonta ba har ƙarshen Rayuwata, sai dai na ɗauki ƙaddarar rashinta a yanda tazo min domin kuwa Ubangiji ya ƙaddara Falmata ba matata bace. yanzu ina kika nufa na sauƙe ki na wuce.”
” Gida zaka mai dani, domin kuwa ina shiga gidan nan yanzu DOCTOR zai fuskanci nine na turo ka, na ƙara jaza mata wata matsalar muje kawai da yamma zan dawo.”
Kaɗa kansa HABEEB yayi tare da jan motar suka bar ƙofar gidan.
Shikuwa DOCTOR Tunda ya shiga Bedroom ɗinsa ya kasa nutsuwa ya manta ma da zagin da Hajja ta masa, kawai yanzu tashin hankalin sa HABEEB daya shigo masa har cikin gida, sannan yake masa barazanar cewa har yanzu yana nan yana jiran matar sa, a fili ya furta, ” cap lallai mace muminar kare ce mai cizo, anya kuwa Falmata basa tare da HABEEB suna Soyayyar bayan fage idan ba haka ba uban waye ya kirasa cikin gidan sa.” Kwalaben da suke shirye kan dressing mirror yasa hanunsa ya watsar dasu ƙasa, hakan bai ishesa ba, sai da yasa hanunsa ya naushi mirrorn da ƙarfi, wani irin mungun yanka glass mirror ya masa tare da tarwatsewa idanunsa sunyi jajur kana ganinsu zaka hango tsantsar kishi a cikin su da ɓacin rai.
DOCTOR SAIF ne ya shigo cikin gidan shima da sauri, Falmata ya fara cin karo da ita a inda take zaune tana famar disgar kuka kamar wacce ranta zai fita, nufota yayi cikin sauri yana cewa.
” Subabanallah!!! Falmata lafiya meya sameki.?”
Bata kai ga basa amsa ba sukaji ƙarar wurgar da abubuwa da ake a cikin Bedroom ɗin Doctor, kusan tare suka nufi ɗakin da DOCTOR SAIF, doctor Saif cike da tsoro ya zaro idonsa yana bin Bedroom ɗin da kallo, ga baki ɗaya yayi kacakaca da kayan ɗakin, harta dressing mirror ma sai da wurgar sa ƙasa hanunsa kuma sai famar tsiyayar jini yake, Falmata hanu tasa a kanta ta ƙara sakin wani sabon kuka, kansa tayi da gudu zata riƙo hanunsa wanda yake zubda jinin ya dakatar da ita yana nunata da yatsa.
” 👉🏻 Karki kuskura hanunki ya taɓani macuciya maciya Amana wacce bata san darajar Aure ba da Auren ki amma kina Soyayya da wani namiji a waje ko kunya bakya ji, shine zaki turo min ƙato ya shigo min har cikin gida ko?, To karki kuskura ki taɓa ni idan kuwa kika taɓa ni sai na miki mungun illa.”
Falmata a razane take kallon DOCTOR tana girgiza masa kai alamar bata da masaniya da shigowar HABEEB cikin gidan, DOCTOR Saif kuwa dariya ce taso ƙwace masa yanda yake hango kishi ƙiri-ƙiri a idanun DOCTOR Amma a hakan yake furta wai ya tsani Falmata bayan gashi yana kishin ta, Falmata ya duba tare da ce mata.
” Waye ne ya shigo cikin gidan nan.?”
Cike da tashin hankali tace.
” HABEEB ne kuma wallahi bani da masaniya akan shigowar sa rabona dashi tun Ranar Aure Na, da yazo ya min murna, ban ƙara sashi a cikin Ido na ba sai yau daya shigo cikin gidan nan.”
Murmushi DOCTOR SAIF yayi, tare da ce mata.
” Okay ki share hawayen ki ki daina wannan kukan kije ki wanke fuskar, karki kanki yayi ciwo, zanyi Magana dashi.”
Falmata fita tayi tana share hawayen ta sai ajiyar zuciya take, DOCTOR Saif cikin Bedroom ɗin ya ƙarasa drowarn doctor ya ƙarasa ya buɗe, first aid box ya ɗauko ya dawo kusa da DOCTOR, zama yayi bakin bed tare da buɗe box ɗin kayan wanke ciwo ya ɗauka tare da kama hanun DOCTOR ya fara wankewa yana cewa.
” Me zai dameka dan HABEEB yazo wajen Falmata, a zatona matar da ake so ita ake kishi, ba matar da aka tsana ba ina tunanin ya fara zuwa zawarci ne, tunda ka kusa sakinta kaga kuwa ai dole shi kuma HABEEB ya fara zuwa kamun ƙafa.”
DOCTOR ƙwace hanunsa yayi daga DOCTOR SAIF cikin masifa da zafin rai yace.
” Inji uban waye yace ina kishin ta, karka kuskura ka ƙara ƙiran kishi tsakanin mu naji zafin keta wa SUNNAR Annabi haddi da yayi ne, tunda duk tsiya dai akwai Aure a tsakanina da ita ko?, sannan kuma bari kaji bazan taɓa ƙyale HABEEB ba, sai na ɗauki hukunci a kansa na keta min haddi da yayi ya shigo min har cikin falo, ƙato dashi ya shigo min falo yana kalle min mata, haka addini yace ka faɗa min.”
Saif bakin sa ya taɓe tare da miƙewa tsaye yace.
” Abokina meye a cikin idanunka idan ba kishi ba, meyasa kaji zafi dan HABEEB ya shigo cikin gidan ka ya kalli matar ka meyasa kaji zafin maganar sa, DOCTOR ka dawo cikin hankalinka domin kuwa kana son matar ka, matar da ake so ita ake kishi, gashi kuma naka idanun sun nuna kishin ka, ka gane cewa matar ka tana da daraja, duk wani abu mai daraja kuma adana sa ake, duk sanda ka sake matar ka ta kufce maka, abune mai matuƙar wahala ta dawo maka, babu yanda ka iya da HABEEB domin kuwa yafi ƙarfin ka, ko shara’a ne bazaka iya dashi ba, dan haka abinda ya kamata kayi shine ka dawo da farin cikin gidan ka ka riƙe matar ka da kyau, sannan ka rage wannan Zafin zuciyar taka, ka kuma cire zargi cikin zuciyarka, shine kawai abinda zaiyi katanga tsakanin matar ka da HABEEB.”
Zama DOCTOR yayi tare da dafe kansa sai ajiyar Zuciya yake sauƙewa idanunsa ya kai kan hoton Abbansa da Aunty Jalila hanunsa yasa ya ɗauki pic ɗin, yana ƙare musu kallo, hawaye ne ya zubo masa daga idanunsa, ɗago kansa yayi ya dubi SAIF yace.
“SAIFUDDEEN taya kake tunanin zan iya gyara alaƙata da Falmata bayan iyayenta sun zalunce mu, sun mai damu marayun Dole, bazan Rayuwar farin ciki da Falmata ba, duk sanda na kyautata mata ji nake Tamkar na kyautatawa iyayen ta, bazan iya ba SAIF.”
” DOCTOR meyasa idanunka suke rufewa kake biyewa zuciyarka take tunzura ka, kake yankewa matar ka hukuncin iyayenta a kanta, dan Allah DOCTOR ka sawa zuciyarka haƙuri ka bawa matar ka farin ciki, kasan Falmata macece ta gari sai son zuciyarka yasa ka yanke mata hukuncin da ba nata ba.”
Shuru DOCTOR yayi jikinsa sosai yayi sanyi yasan dukkan maganganun da DOCTOR SAIF yake faɗa masa gaskiya ne, sai baya jin zai iya bawa Falmata farin ciki saboda yana jin zafin iyayenta…………
*Ku biya domin cigaba da karanta wannan labarin mai matukar tausayi soyayya faɗakarwa tare da ban dariya ga yanda zaki biya kuɗin ki* 👇🏻
*Kuna iya nuna min soyayya ta hanyar siyen littafinan na DOCTOR HASSAN akan Naira 300 kacal,zaku iya biya ta wannan account ɗin 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK ko kuma ku tura katin MTN ta wannan number 08147537180,sannan ku tura shaidar biya a ita ko a 08147537180 Nagode masoya,ina maraba da masu sayan ɗaya ko sari*
Vote
Share
And Comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/2, 9:28 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romance and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 17 to 18*
*_____________________________________*
_________✍🏻 “Zuciyata bazata iya daurewa ɗaukar haƙuri ba, *WUTAR FANSAR* mahaifina itace kawai take ruruwa a cikin zuciyata, SAIF duk sanda na kalli fuskar Falmata ji nake tamkar fuskar mahaifiyar ta na kalla, Sorry bazan iya doguwar rayuwa da Falmata ba, dole ne zan rabu da ita.”
DOCTOR SAIF girgiza kansa yayi cike da haushin DOCTOR, ya rasa wani irin Mutum ne shi sam bashi da fahimta bare kuma ɗaukar shawara, abinda yasa a gaban sa shi kawai yake aikatawa duban sa SAIF yayi yace.
” Shikenan kaje ka yankewa kanka hukunci tunda kaine ka haifi kanka, babu wanda ya isa ya faɗa maka tunda kaine kafi kowa sanin gaskiya, amma ina mai tabbatar maka akwai ranar da zaka zo kana nadama kana neman taimako amma ka rasa samun mai taimaka maka, saboda masu taimakon ka ka watsa musu ƙasa a ido sanda suke taro ka suke nuna maka Hanyar gaskiya, ka sani Ubangiji sai yayiwa wannan yarinyar sakayya abisa cutarwar da kake Mata, DOCTOR anya kuwa saboda matsalar iyayenku kake walaƙanta Falmata, ko dai Saboda bata haihuwa ne kake walaƙanta ta.”
Ɗago kansa DOCTOR yayi da ya kaɗa yayi jajur, ya dubi SAIF tare da girgiza kai yace.
” Karka kai zarginka zuwa ga rashin haihuwar Falmata, domin kuwa bawai kwatakwata bazata taɓa haihuwa bane a rayuwarta matsalace kawai take dashi, kuma muna saka ran zata sami sauƙi kuma koda Falmata bazata haihu a rayuwarta ba ni zan iya zama da ita a haka, saboda kafi kowa sanin yanda nake son FALMATA, sai dai ƙaddara ta shiga tsakanina da Soyayyar ta, matsalar da aka samu nafi son iyayena a kanta Soyayyar su tafi ƙarfi fiye da wanda nake mata, dan Allah Saif mubar wannan maganar haka.”
” Hmmm!!! Ko baka ce dama Dole zan barta tunda ba son gaskiya kake, amma ina son kasan abu wanda kowa yake kallon ka da ita, *TUN CAN DAMA BA SOYAYYAR GASKIYA KAKE MAWA FALMATA BA SHIYASA KA JUYA MATA BAYA A LOKACI GUDA*.”
Ya faɗa masa maganar tare da tashi ya bar Bedroom ɗin.
DOCTOR binsa yayi da kallo cikin sanyin jiki harya fice, kwanciya yayi a bed ɗinsa tare da yin rigingine yana kallon slip muryar HABEEB ne kawai take masa yawo cikin kunnen sa, runtse idanunsa yayi yana jin wata sabuwar tsanar HABEEB cikin ransa *KA ADANA MATARKA DOMIN KUWA HAR YANZU INA SONTA* tsuka yaja still pictures ɗin Aunty Jalila yana hanunsa, rungume shi kaɗai yasan zafin da yake ji na rasa iyayen sa da yayi, tashi yayi yana sauƙe ajiyar zuciya ya ajiye pictures ɗin tare da ƙwalawa Ladiyo kira, cikin sauri kuwa ta shigo da Sallama, nuni ya mata da ta tattara kayan da ya zubar a ɗakin, da to Ladiyo ta amsa sannan shi kuma ya shige falo ya zauna zaman jiranta.
Falmata tunda ta shiga Bedroom ɗinta hawaye ya ɗauke daga idanunta, sai zafi kawai da zuciyarta ke mata ita kanta tana mamakin irin matsanancin Soyayyar da take yiwa DOCTOR Zuciyarta ta kasa hakura dashi, Soyayyar sa ji take tamkar ranta hakan yasa take jin rabuwa dashi tamkar rabuwa da rayuwarta ne, meyasa DOCTOR yake wulaƙanta ta haka, bayan shima bashi da tabbacin iyayenta suna da hanu cikin ɓatar iyayen sa, zama tayi bakin bed ɗin ta zuba tagumi, cike da damuwa, ta daɗe zaune tana cikin tunani kafin ta tashi cikin natsuwa da kuma damuwa ta nufo falo a zaune ta hangesa dama kuwa Bedroom ɗin nasa ta nufa, wajen sa ta taho, ta faɗa jikinsa tare da saka hununta ta ƙanƙamesa, sai kuma tasa kuka.
Kusan suman tsaye DOCTOR yayi jinta a jikinsa, da yayi, ajiyar zuciya ya sauƙe ya kuma kasa yakice ta daga jikinsa domin kuwa rabon dasu haɗa jiki da ita tun randa wannan mummunan lamari na iyayensa ya faru, shuru yayi kawai yana jin sautin kukan ta, cikin muryar kukan tace.
” Bansan wani irin soyayya nake maka ba, ni dai nasan bazan iya jure rasa ka ba, dan Allah kayi hkr, karka rabu dani saboda kuskuren iyayena, Wallahi ban kai ƙararka wajen Hajja ba, ban kuma ce mata komai ba, bansan dalilin da yasa ta maka haka ba, ka yafe min dan Allah karkayi fushi dani mijina.”
Ta ƙarasa maganar tana kwantar da kanta a ƙirjinsa, still shuru, bai ce komai ba, itama shurun tayi tana laɓe a jikinsa, DOCTOR jin wani abu ya fara yawo tun daga tafin ƙafarsa zuwa kansa ya sashi saurin ɓareta daga jikinsa ya tashi da sauri ya bar falon duka, kallo Falmata ta bisa dashi cike da tausayin kanta harya fice, ta daɗe zaune cikin falon kafin ta koma Bedroom ɗinta.
Maji kuwa a ƙofar gidan su HABEEB ya sauƙe ta, murmushi tayi tare da cewa.
” To HABEEB na gode.”
Shima HABEEB murmushi yayi tare da cewa.
” Okay ki gaishe da Mama, sai munyi waya.”
“Zataji” Maji tace tare da shigewa cikin gidan.
Aunty YANA kuwa tun ɗazu zaman jiran ganin Falmata take da takaddar sakinta, amma ina shuru take ji wai Malam yaci shirwa, Yagana da ta shigo ne ta zauna Aunty YANA tace.
” Oh ni YAHANASU wai tun ɗazu fa nake zaune nake jiran naga yarinyar nan Falmata ta shigo min da takaddar sakinta amma shuru babu wani motsi.”
Murmushi Yagana tayi tare da cewa.
” Wai ke tunani kike dama Hassan zai saki Falmata dan kawai wannan rashin mutunci da Hajja ta masa hmmm!!! Kin manta waye Hassan kenan, to wannan dalili yayi kaɗan yasa ya saketa, wai ma Aunty Yana meye ribarki idan Hassan ya saki Falmata meyasa kike son ya saketa.”
Tsuka Aunty YANA taja tare da cewa.
” Ke Yagana baki ga dalilin ba kenan, bakya ganin yanda yake wahalar da rayuwarta kullum cikin baƙin ciki take a gidan ta, wace uwace ranta zaiyi daɗi taga ƴarta wacce ya kamata ace tana taimakon ta cikin wahala babu wannan Uwar komai lalacewar uwa tana son taga ɗanta cikin jin daɗi, duk abinda zanyi domin dawo da hankalin Hassan kan Falmata taƙi ta bani haɗin kai, naje wajen Malamai sun min aiki akansa amma abun yaƙi cinsa na karɓo wanda za’a sa masa yarinyar nan taƙi bani haɗin kai, to ya zanyi idan ba na nemi auren ya mutu, tazo ta sami wani mijin ta aura wanda zata sami kwanciyar hankali.”
Jinjina kanta Yagana tayi tace.
” Tabbas kuwa Falmata bata da farin ciki a gidan Auren ta, kuma itama tana da laifi na shige taurin kai da tausayin wanda baya tausayin ta, ni dai abinda zan faɗa miki, tunda layar nan tana nan, ki ɗauka kije gidan da kanki ki saka ki kuma ja mata Allah ya isa idan ta cire, kinga kuwa idan tana neman albarka ai dole ta barsa.”
” Hmmm!!! Kin kawo shawara mai kyau, zanje da kaina amma ba yanzu ba sai an kwana biyu saboda tsaro.”
” Hakan yafi ya kamata kije kam, bari naje wa Hajja aika gidan Su Maji.”
” Sai kin dawo” Aunty YANA tace.
” FANNA FANNA!!! Hajjo ce mai kwala mata kira amsawa Fanna tayi tare da shigowa ta zauna kusa da Hajjo tace.
” Gani Aunty.”
” Ruwan wankan Umman yayi zafi ne.?”
” Eh yayi zafi daidai wanka.”
” To maza tashi kije ki ɗiba ki sirka ki kai bayin sai kizo ki taimaka min mu kaita.”
To Fanna tace tare da tashi taje ta ɗibi ruwan ta kai sannan ta dawo Hajjo Itace ta tayar da Umma sannan Fanna ta tallafe ta, suka Kaita bayi, fitowa Fanna tayi ta bar Hajjo, itace ta mata wanka tas sannan ta kira Fanna tace ta kawo mata kayan Umma a sip ɗin Umma Fanna ta ɗauko kayan ta kawo Hajjo ta sa mata sannan suka fito da ita suka kwantar, wannan karon idanun Umma a buɗe suke tana bin kowa da kallo sai dai bata Magana, Hajjo hayaƙin magani ta ɗauko ta turare Umma dashi, Fanna kwantar da kanta tayi jikin Umma hawaye ya zubo mata,tace.
” Zaki sami lafiya Umma da yardar Allah, zaki warke ki dawo Kamar da ummana.”
Hajjo ma tausayi Umma ke bata, mata mai kazar-kazar da son ƴan UWA, mata mai kirki tana kwance cikin jinyar da ba’a gane kanta ba, suna nan zaune Hajja ta shigo, Hajjo ce ta gaishe ta, ta amsa fuskar ta a sake duban Umma tayi tace.
” Sannu Yamuram Allah ya baki lafiya, ki tashi ki tsaya akan ya’yan ki, nasan dukkan wannan abinda ke faruwa tsakanin Hassan da fatuma da kina da lafiyarki bazaki bari hakan ta faru, Allah ya yaye miki”
Da ameen hajjo suka amsa, Hajja ta juma zauna kafin ta fita tana cewa Fanna tazo zata aiketa.
Can kuwa gidan DOCTOR cikin dare kowa yayi nisa da bacci amma ita Falmata nata idanun biyu ne ta kasa bacci gashi gobe tana son zuwa school daga nan zata biya gida ta duba Umma, bata san kuma ta yaya zata sanar da DOCTOR ba, ta juma tana Nazari har bacci ya ɗauke ta.
Yayin da shima DOCTOR yake nasa Bedroom ɗin bacci ya gagaresa maganganun Hajja da HABEEB ne kawai suke masa yawo Cikin kunne, bai taɓa jin haushin Hajja irin wannan karon ba, wai shi Hajja take kira banza a banza, hmmm duk abinda aka masa bata gani ba, tafi son ya’yan kawu bukkar akansu, a cikin zuciyarsa ya furta babu komai rayuwa ce, tashi yayi ya shige tollet ya ɗauro alwala fitowa yayi ya tayar da Sallah, duk sujjadar da zaiyi sai ya roƙi Ubangiji daya bayyana masa mahaifinsa da ƴar uwarsa cikin ƙoshin lafiya, bayan ya idar da sallar ma ya juma yana musu addu’a sannan yaji zuciyarsa ta masa sanyi, bed ɗinsa ya hau ya kwanta yana bin gefen da Falmata ta saba kwanciya da kallo, lumshe idanunsa yayi tuno rayuwarsu ta baya mai cike da kwanciyar hankali da Soyayya, yau ɗaya kawai sai da yaji kewarta cikin Bedroom ɗinsa, filo ya jawo ya ƙanƙame tare da rufe idanunsa.
Naso read More ɗin yafi haka yawa amma dai ku shaƙata da wannan ɗin.
Masoya naji daɗin yanda kuka nuna min ƙauna ta hanyar siyan wannan littafin na gode sosai🤝🏻
Ki biya ki karanta cikin kunciyar hankali labari ne mai cike da Soyayya tare da ban tausayi faɗakarwa harma da nishaɗantarwa ki biya kuɗin ki ta wannan hanyar 👇🏻
*Kuna iya nuna min soyayya ta hanyar siyen littafinan na DOCTOR HASSAN akan Naira 300 kacal,zaku iya biya ta wannan account ɗin 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK ko kuma ku tura katin MTN ta wannan number 08147537180,sannan ku tura shaidar biya a ita ko a 08147537180 Nagode masoya,ina maraba da masu sayan ɗaya ko sari*
Vote
Share
And Comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/3, 7:12 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤️ *Love and romantic and funny story* ❤️
*Na*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a duk inda kuke so da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*RIGIJI GABJI TSARƘWAI MAZAƘWAI INA KUKE MASOYA WANNAN SHAHARARREN BOOK ƊIN WATO CONEL UBAIDULLAH TO ALBISHIR YANZU MA DAI GA MOMYN AHLAN ZARAH ABDUL TA SAKE DAWO MUKU DA SABON SALO MAI SABON TAKU GAWURTACCEN SOJA CONEL UBAIDULLAH RETURN MAZA KU GARZAYA KU SAMI UWAR AHLAN DOMIN KUMA A DAMA DAKU KUMA WAƊANDA BAKU KARANTA NA FARKO BA, KU NEMA KU KARANTA KAR A BARKU A BAYA, AKAN FARASHI ƘALILAN MOMYN AHLAN TANA JIRAN MASOYANTA*
Waɗanda suka ce Document ɗin Ruɗanin Zuciya biyu suke so, to ga dama ta samu na gama na kuma haɗa Complete document idan kina so zaki samesa a 200 Naira only 08147537180.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*Book One*
*Page 19 to 20*
*____________________________________*
_______✍🏻Washe gari da safe cikin ikon Allah Falmata ta tashi cikin fara’a domin kuwa haka kawai take jin Damuwar tata ta mata sauƙi, Yau da kanta ta haɗa breakfast, Ladiyo gyaran part ɗin kawai tayi, breakfast ɗin Musa mai gadi ta bawa Ladiyo ta kai masa ita kuma ta shige Bedroom ɗinta, tollet ta shige tayi wanka ta shirya cikin wani koren atamfa wanda aka mata single style sosai atamfar tabi jikinta, ba wani makeup tayi ba sai powder kawai da lipstick da ta shafa, Bedroom ɗin DOCTOR ta shige jin shuru bai fito ba, yana kwance rungume da photo ko tashi baiyi ba da alamu yau baza shi aiki ba, ƙarasawa bakin bed ɗin Falmata tayi ta zauna tana ƙare masa kallo cikin so da ƙauna, ji take tamkar ta kwanta jikin mijinta, sai babu halin hakan saboda gujewa masifar sa, a hankali tasa hanu ta zare photon daga ƙirjinsa ta maida kallon ta zuwa ga photon “JALILA” ta furta a hankali, ajiyesa tayi a gefe tare da tashi ta shige Tollet ɗinsa, wankewa tayi tas tasa air freshener a ciki sannan ta fito daining ta ƙarasa, indomie kawai taci tare da tea ta tashi, Bedroom ɗin ta ta koma ta ɗauki Mayafinta ta saka tare da bag ɗinta, hand out ɗin ta shima ta ɗauka tare da wayarta ta fito, a falo ta tsaya ta rubuta masa a takadda, “NA TAFI SCHOOL SABODA ZAMU FARA TEXT SANNAN ZANBI GIDA NA DUBA JIKIN UMMA.” sanda tazo bakin ged ɗin gidan musa ya taho da sauri yana cewa.
” Ranki ya daɗe Hajiya unguwa zaki fita ne haka da safe.”
Murmushi Falmata tayi tare da cewa.
” Wallahi school zani Musa, ga wannan takaddar idan DOCTOR ya fito dan Allah ka basa bai tashi a bacci ba, ni kuma zanyi let na tsaya.”
Karɓa Musa yayi yana cewa.
” Insha Allah Hajiya zan isar masa a dawo lafiya Allah ya tsare.”
Da ameen Falmata ta amsa tana ficewa, sanda ta kusa nufo titi sannan ta tuna da babu kuɗin adaidaita a hanunta, “Ya Salam” ta furta hanunta tasa a jaka ta ɗauko wayarta numbern Maji ta kira, tana ɗagawa tace.
” Kina makarantar ne ko gida.”?
Daga can Maji tace.
” Ina school yanzun nan na shigo, wani abune.?”
” Ehh na fito ne kuma babu kuɗin adaidaita a hanuna, akwai kuɗi a hanunki ne, idan na ƙaraso sai na karɓa na basa, nayi let ne babu halin na tsaya ko pos na cire kuɗi.”
Murmushi Maji tayi dake zaune gindin wata bishiya ita da Uwani tace.
” Ki hau ki taho akwai kuɗi Amma fa kuyi sauri domin an kusa shiga lecture.”
” Insha Allah yanzu zan ƙaraso.”
Ta ƙarasa maganar tana katse kiran, bata juma tsaye bama kuwa sai ga adaidaita, tare sa tayi ta hau tare da cewa University Of MAIDUGURI zaka sauƙe ni, amma zamu shiga ciki.
Ɗari biyu mai adaidaitan yace mata babu musu ta hau, har cikin jami’ar ya kaita, Maji ta kira a waya tare da faɗa mata inda suke, ba’a juma ba Maji ta ƙaraso tana cewa.
” Nawa ne kuɗin nasa.”
” 200 Naira” Falmata tace, Maji 500 ta basa ya basu sanji sannan suka jera Maji ne ta dubi Falmata tare da cewa.
” Makarantar nan harta fara mantawa dake, nayi zaton ma bazaki zoba.”
” Me zai hanani zuwa Maji, ai tunda nace miki zanzo to zanzo, yanzu inda matsalar take, karatun da aka wuce ni.”
Numfashi Maji ta sauƙe tace.
” Gaskiya akwai matsala, amma ba damuwa akwai Allah, ke dai kawai ki dage ki fahimci darasin gaba.”
” Insha Allah, ina Uwani ne ban ganku tare ba.”
” Wajen ta muka nufa ai yanzu.”
” Ok” tace har suka ƙarasa gindin bishiyar da Maji tabar Uwani, zama sukayi uwani tace.
” Wata sabon gani ke kuma baiwar shikenan sai kika mana hijira kika daina zuwa school.”
Hararar Uwani Falmata tayi tace.
” Shine kuma baki nemeni ba, kiji ko lafiyata kekam Uwani kikayi wasa igiyar zumunci sai ta zargeki.”
Uwani dariya tayi tace.
” Bani da zumunci ko bamu da zumunci ke zumuncin ne dake, ko neman mutane ke kike.”?
Dariya sosai Maji tayi tana cewa.
” To kaji har kun fara faɗan naku kenan daga haɗuwar ku gaisuwar da zaku fara kenan.”
Falmata cewa tayi.
” Oh mune ma kajin kenan, amma dai kin faɗa mana ba suga, KUMA bashi kikaci sai mun rama ko Uwansis”
” Ƙwarai kuwa kowa ai yaci tuwo damu miya yasha, daram zamu rama.”
Dariya Maji tayi tana cewa.
” Oho haɗe min baki kuma zakuyi, shikenan sai dai ku rame ba dai ku rama ba, kinga Falmata tashi mu shiga class time ya cika gara Uwani sai 12 zata shiga lectures ɗin ta.”
Tashi sukayi suka bar Uwani a wajen suka shige department ɗinsu, suna shiga class ɗin Kuma SIR AHMAD ya shigo wanda yake ɗaukar su lecture ɗin Chemistry gaishesa sukayi ya amsa yana kai dubansa ga Falmata, sosai yake kallon ta tamkar zai cinyeta, lura da hakan da Falmata tayi ya sata kawar da kanta gefe tana haɗa fuskar ta tamau, Murmushi Maji tayi yanda taga Falmata ta haɗa fuska daidai kunnen Falmata Maji ta mata raɗa.
” Maza da yawa suna bukatar shi kuma wannan shashashan mijin naki yana wulaƙanta ki.”
Hararar Maji Falmata tayi tare da ce mata.
” Bana son wulaƙanci mijin nawa kike kira shasha, su dai masu bibiyar matan Auren sune shashashu.”
Dariya kawai Maji tayi ta maida hankalin ta ga lectures da ya fara, duk rabin lecture ɗin da Sir Ahmad yake yi hankalinsa yana kan Falmata harya gama ya fita.
Ƙarfe 12 daidai suka fito daga lectures ɗin, a gajiye Falmata ta fito kasancewar ta kwana biyu batayi zama irin na yau ba, waje suka samu suka zauna, Falmata ranta a dagule tace.
” Maji meya kawo HABEEB gidana jiya.?”
Taɓe bakin ta Maji tayi tace.
” Nine na turo sa?”
” Ke kika turosa akan me zaki turo min shi gidana, kinsan yanzu haka kin haddasa matsala.”
Maji cike da mamaki tace.
” Matsala kuma wacce irin matsala, har akwai wata matsala wacce tafi wanda kike ciki a gidan Auren ki.?”
Falmata cikin faɗa tace.
” Hmmm Maji kenan, akwai domin kuwa Allah kaɗai yasan abinda zai faru tsakanin HABEEB da DOCTOR, Tunda yace bazai ƙyale HABEEB ya keta masa haddi, kuma DOCTOR yana da gaskiya HABEEB mahaukaci ne shi da zai shigo gidan matar Aure meye haɗina dashi, nifa nama manta sa a rayuwata, sannan ai kema bai dace ace ki turo sa cikin gida na ba.”
Tunda Falmata ta fara Magana Maji take dubanta sanda ta dasa aya sannan tace.
” To uwata tashi ki dakeni akan sakaran mijinki tunda na saka ransa ya ɓaci, sai wani tayar min jijiyar wuya kike kamar wanda zaki dakeni, akan mutumin da baisan darajar ki ba, shi DOCTOR HASSAN ɗin dokar yake bi, ko shima ba sunnar Annabi yake takawa ba, kinga Malama na turo HABEEB ne domin kuwa shine kawai damar da nake dashi na hana mutuwar Auren ki, tunda nasan gabar dake tsakanin HABEEB da DOCTOR har yanzu tana nan sannan muddun DOCTOR yasan cewa har yanzu HABEEB yana sonki zai kuma iya Auren ki idan DOCTOR ya rabu dake, nasan bazai yarda ya rabu dake ba, ko dan kar HABEEB ya Aure ki, sannan DOCTOR babu abinda ya isa ya yiwa HABEEB, Tunda ranki ya ɓaci na ɓatawa ubanki rai kiyi hkr.”
Maji ta karasa maganar tana tashi cikin ɓacin rai zata bar wajen, Falmata ta kamo hanunta tana cewa.
” Kiyi hkr ƙawata ki zauna.”
” Me zan zauna na miki na zauna kina ɗaga min jijiyar wuya ne saboda mutumin da baisan darajar ki ba.”
” Ki daiyi hkr ƙawata ki zauna ki fahimce ni.”
Zama Maji tayi sannan Falmata tace.
” Kin kasa fahimta ta, Maji, kinsan yanda nake son Doctor ina gudun abinda zai jamin matsala dashi bana son rabuwa dashi, yanzu kamar wanda yake jirana ina kuskura kaɗan zai samu ƙofar da zai ce zai sakeni shiyasa nake razane da zuwan da HABEEB yayi gidana.”
Maji cikin takaici da haushin Falmata tace.
” Zaki rabu dashi sanda ya kashe ki da baƙin ciki, idan aka binne ki, sai naga taya zaki dawo garesa, Falmata wai wani irin makahon so kike yiwa HASSAN meyasa bakya hango aibunsa ne, Falmata anya kuwa akwai zuciya a ƙirjinki, shi namiji girman kai garesa daga sanda ya fahimci Soyayyar da mace take masa yafi wanda yake mata, to daga wannan ranar zai fara takaki saboda yana ganin bazaki iya rabuwa dashi ba, har yanzu Falmata ke ɗalibace a soyayya naga alama ya kamata ki dinga ɓoyewa DOCTOR zalamar Soyayyar ki, ki dinga nuna masa ɓacin ranki domin nemawa kanki yanci, bawai ki tsaya namiji yana cin mutuncin iyayenki da naki ba, wannan ba daidai bane.”
Numfashi Falmata ta sauƙe tare da cewa.
” Maji meyasa bakya son Doctor, tun can baya baki sona dashi, baki taɓa faɗar alkairin sa ba sai dai aibunsa, amma ai kema kinsan DOCTOR yana sona wannan al’amari ne kawai ya kawo matsala a tsakanin mu amma ke kullum kina kama hanuna akan hanyar barin rayuwar DOCTOR.”
Murmushi Maji tayi tace.
” Ba son Doctor bane bana yi, dama tun baya bai dace da rayuwarki ba, makahuwar Soyayyar sane kawai yasa kika kasa fahimtar hakan, sannan ba aibunsa nake faɗa ba, halinsa nake faɗa, nifa Falmata ina kama hanunki akan hanyar gaskiya, domin inganta rayuwar ki, amma ke ƙoƙarin fisgewa kike zuwa baƙar hanya wacce bata da wajen ɓullewa.”
” DOCTOR shine Wanda yafi ko wani namiji dacewa da rayuwata, wannan makahuwar Soyayyar da nake masa ita ake kira Soyayyar gaskiya tunda wahalar da nake sha bata sa na gujesa ba, Maji Hanyar da nake kai itace mai ɓulle min ba hanyar da kike kaini ba.”
Murmushi kawai Maji tayi tana kaɗa kanta cike da tausayin Falmata tace.
” Ai bazaki fahimce ni ba Falmata, amma lokaci zaizo sanda zaki ce na faɗa miki amm…………..”
Ƙarasowar Wata budurwa wajen da Sallama yasa Maji bata ƙarasa maganar da tayi niyya ba amsawa sukayi budurwar tace.
” Sir Ahmad ne yace wai FATUMA ABUBAKAR BUKAR tazo ta samesa a office ɗinsa.”
Kallon Maji Falmata tayi tace ..
” Kije kice bazanzo ba”
Maji cewa tayi.
” Kije kice tana zuwa.”
Juyawa budurwar tayi ta tafi, Falmata zatayi magana Maji ta ɗaga mata hanu.
” Ni ba jahila bace nasan ke matar Aure ce, amma ki sani shi malamin kine bai kuma furta miki yana sonki ba, kuma kin kwana biyu bakya zuwa makaranta dan haka baki san kiran da yake miki ba, kije kiji, ina jiran ki sai kizo mu wuce gida tunda kince gidan ku zaki wuce.”
Falmata bata ce komai ba ta tashi ta nufi office ɗin da Sallama ta shiga amsawa yayi yana gyara zaman glass ɗin idanunsa ya mata nuni da ta zauna.
” Sir gani ance kana kira na.”
Murmushi ya saki tare da cewa.
” Eh ni nayi kiran ki, me yake hanaki zuwa makaranta kwana biyu.”
” Sir bani da lafiya shiyasa.”
” Subabanallah sannu, ai ban sani ba da naje na duba ki.”
Da sauri ta ɗago kanta ta kallesa tare da cewa.
” Sir zan iya tafiya ana jira nane.”
” A’a bamuyi Maganar da yasa na kiraki ba “..
” To sir ina sauraronka sauri nake.”
Murmushi ya saki tare da zare glass ɗin idanunsa yace.
” I love You fatuma, na juma ina sonki, tun sanda na fara ganinki a cikin school ɗin nan Allah ya jarabceni da sonki, kuma Auren ki nake son nayi dan Allah ki yadda ki aureni.”
A razane ta ɗago kai ta kallesa zuciyarta na bugawa dam!!! Dam!!! Dam!!!!
Tirƙashi wai dama AHMAD baisan Falmata tana da Aure bane?
Ku biyoni domin jin amsar ku.
Ku biya ku karanta cikin kwanciyar hankali.
*Kuna iya nuna min soyayya ta hanyar siyen littafinan na DOCTOR HASSAN akan Naira 300 kacal,zaku iya biya ta wannan account ɗin 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK ko kuma ku tura katin MTN ta wannan number 08147537180,sannan ku tura shaidar biya a ita ko a 08147537180 Nagode masoya,ina maraba da masu sayan ɗaya ko sari*
*Dan Allah masu turo min VTU su daina numbobin katin kawai nake buƙata ko transfer to bank account ɗina🤲🏻*
Vote
Share
And Comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/4, 2:43 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤️ *Love and romantic and funny story* ❤️
*Na*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a duk inda kuke so da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
Waɗanda suka ce Document ɗin Ruɗanin Zuciya biyu suke so, to ga dama ta samu na gama na kuma haɗa Complete document idan kina so zaki samesa a 200 Naira only 08147537180.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*Book One*
*Page 21 to 22*
*____________________________________*
_______✍🏻 Falmata kamar sauƙar ruwan zafi taji Maganar sa a ranta ” Wai i love You” duban sa tayi tare da cewa.
” Sorry Sir nifa matar Aure ce.”
Murmushi AHMAD yayi yace
” Nima mijin Aure ne ai, serious da gaske sonki nake fatuma domin kuwa ban taɓa ganin macen da tamin domin na Aura ta ba, sai ke tun sanda na ganki nasan cewa na samu matar Aure.”
Zuwa yanzu Falmata ranta ya fara barazanar ɓaci, miƙewa tayi tsaye cikin ɓacin rai tace.
” Sorry Sir kayi hkr ni ba matar Auren ka bane domin kuwa ina da nawa mijin nima ba wasa nake maka ba, dan Allah karka ƙara kira min soyayya, ina da miji kuna ina sonsa kuma kasan darajar Aure kayi hkr Allah ya baka wata matar Auren wacce ma ta fini.”
Tana gama faɗin haka ta juya ta tafi har tazo bakin ƙofa taji muryar sa yana cewa.
” Idan har da gaske kina da Aure, to mijinki bai iya riƙe mace da daraja ba domin kuwa babu annurin Aure a jikinki, ki faɗa masa ya riƙeki da kyau idan bazai iya ba, ya sakar mana mu zamu iya, karki manta da ina sonki ki riƙe wannan a ranki.”
Sosai Falmata taji zafin maganganun AHMAD tsuka kawai taja tare da ficewa, shi kuwa murmushi ya saki har yanzu zuciyarsa bata yadda matar Aure bace ita, ” amma zanyi bincike a kanki” ya furta yana mai da hankalin sa kan takaddar dake gabansa.
Ranta a ɓace Falmata ta nufo Maji tace ” mu tafi.” Tafiyar sukayi sanda sukayi nisa Maji tace
” Wai ya naga kin fito ranki a ɓace meya faru.”?
Numfashi Falmata ta sauƙe suna tare a daidaita sanda suka hau sannan Falmata tace.
” Mutumin nan bashi da hankali wai cewa yayi yana sona Mtsss.”
” May be bai san kina da Aure bane shiyasa yace yana sonki.”
Murmushi Falmata tayi tare da cewa.
” Da farko na masa wannan uzurin na sanar dashi ina da Aure, amma tsabar mutumin nan tantirin ɗan duniya ne sai bai yarda ba, cemin yayi shima mijin Aure ne kiji ɗan iska fa.”
Dariya maganar ta bawa Maji kafin tace.
” Ikon kuma ya kuka ƙare dashi.”?
” Ya kuwa zamu ƙare banda sanda na MAIMAITA masa da gaske ina da Aure ke kinji baƙar maganar da ya faɗa min, wai harda cewa idan har da gaske ina da Aure to mijina bai iya riƙe mace ba, domin babu annurin Aure a jikina, na sanar da mijina idan bazai iya ba, to ya sakeni su zasu iya, kiji fa wata magana marar daɗi jin sai kace a goshi ake rubuta tambarin Auren.”
Dariya sosai Maji take sanda tayi dariyar ta isheta sannan tace.
” Ikon Allah Shidai Hassan ya shiga Uku da bakin al’umma wallahi baki ya masa yawa da zai gane daya gyara kafin lokaci ya ƙure masa, kinga wanda baisan zamantakewar ki da mijinki bama abinda yace, Allah dai ya kyauta.”
Tsuka Falmata taja cike da jin haushin Maji tace.
” Ya Isa malama mubar zancen nan, naga kina neman shige min hanci da ƙudunduno zaki fara zage min miji dake kin tsanesa.”
Dariya Maji tayi tace.
” Allah ya baki haƙuri Mrs Romio, Ke kuma baki son a zagi habibin ki ba, to Allah ya kawo miki sauƙi cikin lamuran ki ƙawata ya dawo muku da soyayyar ku shikenan abinda kike so kiji nace ko.”
Murmushi Falmata tayi tare da cewa.
” Yauwa abinda ya kamata ki dinga min kenan, ba aibata min miji ba.”
Dariya Maji tayi suka kama wani taɗin duniya har suka iso ƙafar gidan su Maji tare suka sauƙa Maji ta biya kuɗin, Falmata shiga gidan su Maji tayi da niyar gaishe da mamanta kafin ta fito ta wuce gidan su.
Shi kuwa DOCTOR bayan ya tashi daga bacci wanka yayi, kafin ya fito falo da jallabiya a jikin sa, kai tsaye daining ya nufa, tea da ƙwai kawai yasha sannan ya tashi ya dawo tsakiyar falon tv ya kunna ya fara kallon BBC News yafi 1hrs yana falon baiji motsin Falmata ba, kuma bai damu ya duba ta ba, sanda ya ga 12 daidai sannan ya tashi Bedroom ɗinsa ya wuce ya ɗauki kay ɗinsa da wayoyin sa ya fito, Motar sa ya buɗe ya shiga ya tayar Musa mai gadi get ya wangale da sauri, sanda DOCTOR yazo daidai get ɗin ya tsaya tare da cewa.
” Malam Musa, kana lafiya ya mai jikin dai.”
Dariya musa yayi yace.
” Lafiya lau ranka ya daɗe mai jiki da sauƙi, yauwa ga wannan takardar Madam tace a baka ɗazu da safe kafin ta fita.”
Cikin mamaki DOCTOR ya karɓi takaddar sai dai bai nunawa Musa wani abu a fuska ba ya buɗe takaddar karantawa yayi ya ajiye sannan yaja motar sa ya fice, Musa get ɗin ya rufe ya koma ya cigaba da jin rediyo ɗinsa, DOCTOR gidan su ya nufa wajen umman sa, bayan yayi parking ne ya shiga cikin gidan domin kuwa yau babu kowa ƙofar gidan su, Fanna da gudu ta faɗa jikin DOCTOR tace.
” Oyoyo Yayana”
Murmushi DOCTOR yayi tare da shafa kan Fanna yace.
” My dear sister har yanzu baki san kin girma ba ko, ina Hajjo naji gidan shuru.”
Dariya Fanna tayi tace.
” Suna cikin ɗakin Umma malam sani ne yazo yake mata ruƙƙiya harda Kawu Dauda ma.”
” Okay” ya furta tare da cire Fanna daga jikinsa ya shige cikin ɗakin baice komai ba ya zauna a gefe yana kallon yanda Umman sa take wani irin motsi sanda ake mata addu’ar sanda aka gama sannan malam Sani ya miƙawa DOCTOR hanu sukayi musabaha cewa yayi.
” Hassan jiya BELLO ya sanar dani gobe zaku kai mahaifiyar ku wajen MALAM GANA a can BINISHED, gaskiya naji daɗi sosai domin kuwa sahihin malami ne yana aikin sa da gaskiya, kuma ana dace sosai idan anje wajen sa Allah yasa aje a dace, sannan munanan muna yiwa mahaifinku addu’a insha Allah zai bayyana, idan kunje ku sanar da malam Gana maganar ɓacewar mahaifin naku ko Allah zaisa a samu wani taimako daga garesa.
DOCTOR cike da girmamawa yace.
” Insha Allah Malam zamu sanar dashi, kuma a cigaba da mana addu’a kamar yadda kuke mana kullum, na gode sosai mlm”
Kawu Dauda ne yace.
” BINISHED kuma, wajen wani malamin zakuje baku sanar dani ba, maganin da muke anan bai isa ba har sai anje BINISHED, to bazai yuwu ba, babu inda za’aje ai duk inda ya kamata aje anje ba’a samu sauƙi ba dan haka, muyi hkr mu zauna mu cigaba da neman magani a gida ba sai munje wani BINISHED ba.”
Cike da mamaki DOCTOR yake bin Kawu Dauda da kallo, kafin yace.
” Kawu magani fa zamuje nema, meyasa to zaka ce karmu je, ai ba’a gajiya da neman magani, haka zamu zauna muta kallon Umma cikin ciwo, gaskiya Kawu kayi hkr zamuje BINISHED gobe bazan iya jurewa kallon Umma a halin da take ciki ba.”
Mlm Sani ne yace.
” Tabbas wannan yaron yana da gaskiya Dauda ba’a gajiya da neman magani, komai nisan waje indai za’a samu magani to za’a je bare kuma shi wannan malamin mawuyacin abune aje wajen sa ba’a dace ba, sai dai kuma idan cutar mutuwa ce.”
Kawu Dauda cewa yayi.
” Mlm Sani wannan ciwon na YAMURAM wani irin magani ne ba’a nema masa ba, ina ne ba’a jeba, dan haka babu inda za’a je da ita”, ya faɗi maganar kamar wanda hankalin sa yake tashe ga Kuma goshin sa daya tsatstsafo da zufa.
DOCTOR cike da damuwa yace.
” But amma Kawu……….”
Ɗaga masa hanu Kawu Dauda yayi tare da cewa.
” Ni ƙanin mahaifiyar ku ce baku fini sonta ba, kuma dole kubi umarni na, babu inda za’a kaimin ƴar uwa.”
Malam Sani zubawa DOCTOR Ido yayi cike da mamakin yanda ya gigice lokaci guda jin an ambaci za’aje wajen Malam Gana ko meyasa oho, Allah ya kyauta Malam sani yace tare da tashi ya fice.
DOCTOR shuru yayi kasancewar yana yiwa Kawu Dauda biyayya Kamar yadda yake yiwa Umman sa, sai dai hankalin sa yayi matuƙar tashi jin abinda Kawu Dauda yace, sai dai yana ji a cikin zuciyarsa bazai iya haƙura da zuwa BINISHED gobe, Falmata ce tayi sallama ta shigo cikin ɗakin Fanna kauda kanta gefe tayi ganin Falmata, Hajjo dake zaune gefe itace ta amsa mata sallamar, Hajjo ta gaishar cikin sakin fuska ta amsa mata.
” Aunty Hajjo ya jikin……..”
Bata ƙarasa ba DOCTOR ya daka mata tsawa.
” Keeee!!!! Tashi ki fita ki bar gidan nan tunda ba ɓangaren ubanki bane, an baki wani munafurcin ne ki kawo, fita karki kuma shigowa sashin nan ficeee manaaaa!!!!”
Ya ƙarasa maganar cikin tsawa, Falmata kallo tabi DOCTOR dashi cikin zafin zuciya, tashi tayi ranta na ƙuna yayin da idanunta suke zubar da hawaye ta fita daga ɗakin, Hajjo ma sosai ranta ya ɓaci da abinda DOCTOR ya yiwa Falmata cikin ɓacin rai tace.
” Meye kayi haka Hassan, dama ashe da gaske ne abinda yake yawo a cikin unguwa cewa kana wulaƙanta matar ka, matar kace fa ta SUNNAH kake yiwa wannan cin zarafin akan gabarku ta banza wacce zargi kawai kuke baku da tabbas akai, wallahi gaji tsoron Allah ka daina wulaƙanta Aure, ko akwai laifin iyayenta ita meye laifinta, ko laifin iyayenta shine nata laifin, ka dawo hankalin ka, ka ɗauki abinda ya samu iyayenku a matsayin ƙaddarar da Allah ya ɗaura musu, kana Cutar da yarinyar da bataji ba bata gani ba, wallahi idan ka kuskura ka rabu Fatuma bazaka kuma samun mace ta kirki irinta ba, yau naga haukar banza, yanzu kai idan an hukunta ka da laifin iyayenka zakaji daɗi, to karna kuma ji karna gani ka ƙara wulaƙanta wannan yarinyar albarkar.”
Shuru DOCTOR yayi kansa a sunkuye zaiyi Magana cikin zafin rai Hajjo tace.
” Karka cemin, bana son ji domin kuwa duk abinda zai fito daga bakinka akan Falmata shirme ne, ka tashi kaje ka sami Bello ku shirya tafiyar da zamuyi BINISHED gobe, ka barni da Kawu Dauda ni zanji dashi dole gobe zamu tafi.”
Kaɗa KANSA kawai DOCTOR yayi tare da tashi ya ficewa, yau ko kallon part ɗin su Hajja bai ƙalla ba saboda yana jin haushin ta ya bar gidan.
Hajjo rankwashin Fanna tayi tana cewa.
” Wato kema kinbi sahun ɗan uwanki ko, kina biye masa akan zuciyarsa ta banza.”
Tura bakin ta Fanna tayi bata ce komai ba ta yi shuru.
Ita kuwa Falmata sanda ta tsaya ta goge hawayen ta sannan ta shige cikin sashin su, babu Kowa tsakar gidan duk suna cikin ɗaki, ɗakin Mahaifiyarta ta shiga da Sallama Aunty YANA dake zaune ta amsa mata zama Falmata tayi tana duban Aunty YANA tace.
” Ina kwana Mama.”
Aunty YANA amsawa tayi da lafiya tana hararar Falmata juyowa tayi ta fuskancesa tare da cewa.
” Wato Falmata kin raina ni, kin zaɓi sakaran mijinki a kaina ko.”?
” Na raina ki kuma Mama, mena miki.”
Aunty YANA cike da hasala tace.
” Ubanki kika min!!! Nace ubanki kika min dan ubanki har ni zan aiki Yagana da saƙo har gidan ki, ki saka a dawo min dashi kice wai bazaki iya Cutar da mijinki ba kega wacce kika fi kowa tsoron Allah, to aishi zai iya cutar dake, shashashar banza kin zauna namiji sai taka ki yake kamar kare.”
Shuru Falmata tayi bata cewa Aunty YANA komai ba, harta gama faɗanta sanda ta gama sannan Falmata tace.
” Kiyi hkr mama Allah ya huci Zuciyaki.”
Aunty YANA cewa tayi
” Yanzu me kika zoyi.?”
” UMMA na biyo na duba da jikinta.”
” Okay kin shiga ne.?”
” Ehh na shiga, bari ma na shiga wajen Hajja na fito zan tafi .”
” Hajja bata nan ta fita gaisuwar mutuwa ɗazun nan, daga zuwan naki zaki tafi yanzu fa kika shigo.”
” Mama ai dama ba jumawa zanyi ba, ba wuni na tambaya ba, duba jikin Umma kawai na tambaya.”
Taɓe bakin ta Aunty YANA tayi tare da tashi ta buɗe drowern ta, layar nan ta ɗauko tare da miƙawa Falmata, shuru Falmata tayi tana bin layar da kallo, tsawa Aunty YANA ta mata tana cewa.
” Karɓiii!!!! Mana kina kallo na, ki saka a ƙasan katifar mijinki, wannan wulaƙanci da yake miki yazo ƙarshe, Falmata ki fahimce ni, ƙaunar ki tasa na karɓo wannan layar, zuciyata bata jin daɗin abinda mijinki yake miki, bazan cutar da rayuwarki ba, dan Allah Falmata kiyi amfani da wannan layar domin samawa kanki kwanciyar hankali cikin gidan Auren ki.”
Shuru Falmata tayi tare da saka hanu ta karɓi layar cikin mutuwar jiki, tabbas tasan kalaman mahaifiyar ta gaskiya ne, babu uwar da zataji daɗi taga ana wulaƙanta mata ɗan ta a gidan Auren sa, jakarta ta buɗe ta saka layar sannan ta tashi tana cewa………….
*FREE PAGE YA KUSA ZUWA ƘARSHE SAURA 2 PAGE IDAN KINA SON CIGABA DA KARANTA LITTAFIN NAN BIYA KUƊIN KI TA 👇🏻*
*Kuna iya nuna min soyayya ta hanyar siyen littafinan na DOCTOR HASSAN akan Naira 300 kacal,zaku iya biya ta wannan account ɗin 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK ko kuma ku tura katin MTN ta wannan number 08147537180,sannan ku tura shaidar biya a ita ko a 08147537180 Nagode masoya,ina maraba da masu sayan ɗaya ko sari*
Vote
Share
And comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/5, 9:29 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romance and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 23 to 24*
*_____________________________________*
________✍🏻 ” Shikenan zanyi yanda kikace Mama na gode ni zan wuce.”
Murmushi Aunty YANA tayi tare da cewa.
” Yauwa ƴar albarka ko ke fa, raina ɓaci yake idan ina jin labarin abinda yake miki, wallahi muddun kinyi amfani da layar nan dai dai to Tabbas, Hassan zai dawo hanun mu ke ko cewa kikayi ya miki shara wallahi sai yayi, kije ki jarraba Allah yasa mu dace.”
Da to Falmata ta amsa tana cewa.
” Mama ɗari biyar nake so zanyi adaidaita idan akwai kuɗin a hanunki ”
Aunty YANA cewa tayi.
” Oh Allah ya wadaran naka ya lalace, yanzu kuɗin adaidaita ma baki dashi kuma wai a haka mijinki yana da kuɗi, kai Falmata wannan Auren naki sam babu daɗi”
tsuka taja tare da ɗauko 500 ɗin ta bata, ita dai Falmata bata ce komai ba ta karɓa ta fito, da har zata shiga tayiwa Aunty Hajjo Sallama sai kuma ta fasa tuno walaƙanta ta da DOCTOR yayi, fita tayi ba tare da ta koma ba, a daidaita ta tara tace masa Gra zai kaita bayan ta haune sunyi nisa da tafiya, ta buɗe jakarta hanu tasa ta ciro layar da Aunty YANA ta bata, ƙarewa layar kallo take cikin zuciyarta take cewa ( Allah ka tsareni da saɓa maka Allah karka jarabci zuciyata da faɗawa ga hallaka saboda Soyayyar da nake yiwa DOCTOR, ko wannan layar dana karɓa wajen Mama na karɓa ne kawai saboda gujewa ɓacin ranta amma ba dan nayi amfani dashi ba) wurgar da layar tayi tana lumshe idanunta hawaye na gangaro mata, hanu tasa ta goge hawayen tare da nemawa mahaifiyar tata shiriyar Ubangiji, da wannan nazarin mai adaidaita ya sauƙeta a ƙofar gidan ta, kuɗin sa ta basa tare da buga get ɗin Musa ne ya leƙo tare da buɗewa da sauri yana cewa.
” Barka da dawowa ranki shi daɗe, na bawa Oga sakonki ai tun ɗazu ban manta ba.”
Murmushi Falmata tayi tare da cewa.
” To na gode musa, Ladiyo ta kawo maka abincin rana kuwa.?”
Musa yana dariya yace.
” Eh ta kawo min jalop ɗin shinkafa kuma taji kifi ranki shi daɗe ai Ladiyo ba dai iya girki ba alƙur’an rangaɗaɗau take girki kamar kunnen mutum zai cire, idan ba karnayi ƙarya ba sai nace ma ta fiki iya girki.” Sai kuma yayi saurin toshe bakin sa yace ” Oh yi hkr Uwar gidan Oga aradu baki nane ya zarme.”
Dariya Falmata tayi tana tafiya tare da cewa.
” Lallai kace Ladiyo ta karɓi numbern yabo na girki a gidan nan to nima Allah ya sani a danshin ta”
” Sosai ma kuwa dan har Oga yana yabon girkin ta.”
Dariya kawai Falmata tayi ta shige part ɗinta a zatonta doctor gida ya dawo tana shigowa kuma sai taga baya nan Bedroom ɗinta ta shige tayi wanka, three cuttern wando tasa da best sai wata ƙaramar hula faɗawa tayi saman bed yunwa takeji haɗe da bacci, sai dai baccin yafi ci mata jiki, lumshe idanunta tayi bata kuma juma da kwanciyar ba bacci ya sace ta.
Shi kuwa DOCTOR daga, gidan su, Companyn HABEEB ya nufa, kai tsaye, sakatariyar sa ya yiwa Magana kan cewa taje tace wa ubanginta DOCTOR HASSAN ya iso, tashi kuwa tayi taje ta sanar dashi ba’a juma ba, ta fito tare da sanar dashi cewa ya shiga, DOCTOR cike da izza da kuma zafin rai ya shiga, zama yayi ba tare da HABEEB ya basa izini ba, ƙafarsa ya ɗaura ɗaya kan ɗaya fuskar sa na ɗaure tamau, murmushi HABEEB ya saki dake riƙe da biro yana ƙarewa DOCTOR kallo, hanu ya miƙa masa tare da cewa.
” Barka da zuwa masana’antar HABEEB, Likita bokan Turai *DOCTOR HASSAN A MALA*.”
Taɓe bakin sa DOCTOR yayi yana cije leɓensa yace.
” Bana haɗa hanu da kare wanda bai san darajar Aure ba.”
HABEEB yaji zafin kalmar kare da DOCTOR ya kirasa dashi sai dai a maimakon ya nuna masa ɓacin ransa sai murmushi mai sauti da ya saki tare da cewa.
” Ehh ai a wani lokacin gara kare akan jaki wanda shi kullum bai san abu mai mahimmanci daya kamata ya riƙe ba komai wulaƙantawa yake ciki harda abu mai mahimmanci tsabar rashin sanin darajar kai irin na jaki, shi kuwa kare ai yasan alkairi domin kuwa yana riƙe amanar uban gidansa da kuma mutanen da yake tare dasu, harda wanda ya masa alkairi, shi kuwa jaki ko kaɗan baya gane daidai yafi gane yaji duka kafin ya gyara dalilin kenan da yasa karen shigowa gidan wannan jakin domin ya masa bulala ɗaya ko zai dawo cikin hankalin sa.”
Runtse idanunsa DOCTOR yayi yana jin maganar HABEEB tamkar ana caka masa mashi a cikin ƙahon zuciyarsa wato shine ma jakin, cije leɓensa yayi a fusace ya daki teburin dake gaban HABEEB yace.
” Ya Isa!!!!! Haka maci amanar Allah, kai har kana da bakin da zaka gaya min Magana, gargaɗi nazo na maka ka fita a harkar matata idan ba haka ba, wallahi sai na wulaƙanta rayuwarka, kasan halina sarai tamkar yunwar cikin ka.”
Dariya HABEEB yasa har dumple ɗinsa yana lotsawa fararen wushiryarsa suka bayyana, cikin dariyar ya miƙe tsaye tare da cewa.
” Kaga banbancin mai hankali da mahaukaci shi mai hankali duk sanda aka ɓata masa rai ko aka tsokanesa baya nuna fushin sa bare kuma fusatar sa, saɓanin mahaukaci da baya iya jure tsokana, kaga kenan ko a nan ka nuna min halin ka na jakuna, malam Hassan baka iya riƙe Aure ba kaje ka koyi yanda ake kula da mace daga nan sai ka dawo ka min gargaɗin ” kofa HABEEB ya nunawa DOCTOR yace ” fice min daga office kafin nasa security suyi waje dakai a wulaƙance domin kuwa daga ni har kai munsan halin juna, sannan kasa a ranka ko yau nayi niyyar ƙwace Falmata a hanunka, 10 hours sunyi yawa Auren ku ya ƙare, ko ranar da naje gidan ka, naje ne kawai na ganta raina yayi sanyi saboda na juma ban ganta ba kasan dai irin son da nake mata, zaifi maka alkairi kaje ka rungumi matar ka, tunda tana sonka kafin lokaci ya ƙure maka, domin kuwa duk randa kayi sake lokaci ya ƙure maka ni kuma daga ranar nawa lokacin zai fara, tik!!! Tak!! Tik!! Tak!! Ka rabu da ita kenan, dan haka fice min a office.”
Wayyo Allah kuzo kuga ɓacin rai wajen DOCTOR dama Hausawa sunce idan baki yasan mai zai faɗa baisan me za’a mayar masa ba, ga dai DOCTOR shiya fara kiran HABEEB da kare, yazo kuma yafi HABEEB jin haushi, hanu DOCTOR ya ɗaga cike da ɓacin rai zai zabgawa HABEEB mari, kafin hanunsa ya isa fuskar HABEEB tuni HABEEB yasa hanu ya riƙe hanun DOCTOR yana cewa.
” Karka kuskura ka fara wannan babban kuskuren domin kuwa fuskata tafi ƙarfin mari, ko ubanda ya haifeni bai taɓa ba bare kuma kai, ina raga makane fa HASSAN saboda bana son mutunci na ya zube a gaban ma’aikata na, fice min daga office, idan ba haka ba wallahi zan wulaƙanta ka a cikin 1hrs kasan kuma zan iya.”
Wani irin huci DOCTOR yake idanunsa sunyi jawur, nuna HABEEB da yatsa yake yana ja da baya yana huci har yabar office ɗin, tsuka HABEEB yaja yana komawa ya zauna tare da dafe kansa yana jin wata sabuwar Soyayyar Falmata na bijiro masa, innalillahi ya fara furtawa yana koran sheɗan harya samu nutsuwa, aikin sa ya cigaba dayi cike da kwanciyar hankali.
Shi kuwa DOCTOR wani irin dreving yake idanunsa rufe tsabar ɓacin rai ikon Allah shine kawai ya dawo dashi gida parking yayi ya fito cike da ɓacin rai da gudu ya karasa part ɗin nasu, Ladiyo dake zaune tana kallo a falon sai da ta tsorata da ganin yanayin uban gidan nata, Bedroom ɗin Falmata ya shige yana ƙwala mata kira cike da ɓacin rai.
” *FALMATA!! FALMATA!! FALMATA!! FALMATA!!*”
Ita kuwa tayi nisa da baccin ta sam bataji kiransa ba, tsayawa yayi a kanta yana ƙare mata kallo, runtse idanunsa yayi yana jiyo kalaman HABEEB, a fusace ya saka hanunsa ya fisgo ta, da ƙarfi, ai kuwa a firgice ta farka zata danna ihu yasa hanunsa ya toshe mata baki yana saka hanu a bakin sa tare cewa.
” Shiiiiiii!!”
Shuru Falmata tayi tana zaro idanunta cike da tsoro, hanunsa yasa ya ja gashinta cike da mungunta ƙara Falmata tasa tana jin kanta na wani raɗaɗin azaba sake mata bakin yayi still yana riƙe da gashin nata yace.
” Ban taɓa ganin munafukar mace ba irin ki ballagaza wacce bata san mutuncin kanta ba, faɗa min a ina kuke haɗuwa da HABEEB, a ina kuke haɗuwa, wato ke ga jarababbiya ko saboda yanzu na daina haɗa shimfiɗa dake shine bari ki nemi HABEEB kuje ku lalace, kinyi asara wallahi, koda meye ma abun mamaki tunda kinsha nonon tsiya a wajen uwarki ai…………”
Wani irin hankaɗa Falmata ta yiwa DOCTOR HASSAN idanunta sun kaɗa sunyi jajur hawaye ne kawai yake gudu a saman fuskarta tunda DOCTOR yake walaƙanta ta bata taɓa jin zafinsa irin na yau, miƙewa tayi tsaye cike da ɓacin rai cikin tsawa tace.
” Ni ba munafuka bace saboda babu wanda na taɓa munafurta, Zagin iyayena ya isheka haka DOCTOR!!!!! Zan iya jure dukkan wani wulaƙancin ka amma bazan lamunci cin mutuncin iyaye ba, domin kuwa duk tsiya sune suka kawo ni duniya harka ganni ka aura, wato ma zargina kake ina Zina wa’iyazubillah ban taɓa kuma yanzu ma bazanyi ba, da ni jarababbiyar ce da kake faɗi da nayi zina tun sanda ka koya min mu’amala da ɗa namiji ka tafi India ka barni tsawon shekara bakwai da zanyi zina a wannan lokacin ya kamata nayi HABEEB ba mazinaci bane ko a gaban Ubangiji zan masa wannan shaidar, wa mai da baka san da nonon tsiyar nasha ba ka auro Ni, ya isheka DOCTOR cin mutuncin iyaye ya tsaya iya dole ka mutunta iyayena tunda har ka auri yarsu.”
Ta ƙarasa maganar tana kuka mai cin rai tare da jingunuwa jikin bango, DOCTOR Tunda ta fara Maganar ya saki baki yana kallon ta, yarinyar da duk sanda ya ƙuntata mata sai dai ta basa hkr yau itace take mayar masa da magana girgiza kansa yayi yana huci ya tunkaro gabanta hannayensa yasa ya dafe bangon da take jingine ya sunkuyo da kansa har suna jin numfashin juna yace.
” Kece kika fara mayar min Magana ina faɗa kina faɗa, Oh na fuskanta, kinje gida ɗazu ba, wannan uwar taki marar mutunci ta zugoki nace wannan Uwar taki marar mutunci ta zugoki ko.”
Cike da ɓacin rai Falmata ta ɗauke DOCTOR da mari ta tankaɗe sa gefe, riƙe fuskarsa DOCTOR yayi yana jin zuciya na taso masa jajayen idanunsa ya ɗago cikin mungun yanayi ya nuna ta da yatsa yace.
” Ni kika sa hanu kika mara saboda shegiyar Uwar ki, da kyau da kyau Falmata tabbas kin gwada min kin kai bazan saka hanu a jikin ki ba amma zan miki abinda yafi duka zafi dan haka kije na *SAKE KI SAKI ƊAYA*”
Wani dum Falmata taji tare da wani jiri ” *SAKI* ta furta tana kallon DOCTOR cike da tashin hankali sai kuma tasa kuka, lokaci ɗaya kuma tayi shuru tana sauƙe ajiyar zuciya gabansa tazo ta tsaya tare da cewa.
” Ka sake ni kace, ni ka saka DOCTOR Saboda son zuciyarka, saboda kasan ina sonka bazan iya rayuwa babu kai, gaskiyar Maji ne tana faɗa mini bana yarda sai ga zancen ya fito yanzu, dama ku maza haka kuke da zarar kunga ta tana tsananin sonku ku kuma a wannan lokacin baku da abun wulaƙantawa sai ita, meye laifi na DOCTOR dan kawai na soka shine kuskure na, na gode amma ka sani Allah ya isa tsakani na da kai ka cuceni.”
Tana faɗin haka ta juya da sauri ta jawo akwatin ta, tsuka DOCTOR yaja tare da ficewa daga Bedroom ɗin, ita kuwa kayanta ta dinga zubawa a cikin akwatin, sannan ta saka kayanta, da mayafin ta, akwatin ta jawo ta fito hawaye na gudu saman fuskarta, Ladiyo dake zaune ne ta tashi da sauri tana cewa.
” Aunty Lafiya, kika fito kina kuka, ina zaki da akwatin Aunty.”
Cikin muryar kuka Falmata tace.
” Gidan mu zan tafi, Aure ne ya ajiye ni a gidan nan kuma yau Auren ya ƙare, idan akwai wani abu na kuskure daya shiga tsakanin mu a zaman da mukayi ki yafe min.”
Girgiza kanta Ladiyo tayi hawaye na gudu mata itama tace.
” A’a Aunty baki taɓa min laifi ba, sai ma kyauta ta min da kike, Aunty nima tafiya zanyi bazan zauna a gidan nan babu ke ba.
Ta ƙarasa maganar ta na shigewa da gudu Bedroom ɗinta, Falmata share hawayen ta tayi taja akwatin ta ta fice……………
Dan dan dan dan dan dan dan
Akwai ƙura fa cikin wannan labarin ku biyoni mu ninƙaya cikin sa domin jin yacce zata kasance amma ta hanyar 👇🏻
*Kuna iya nuna min soyayya ta hanyar siyen littafinan na DOCTOR HASSAN akan Naira 300 kacal,zaku iya biya ta wannan account ɗin 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK ko kuma ku tura katin MTN ta wannan number 08147537180,sannan ku tura shaidar biya a ita ko a 08147537180 Nagode masoya,ina maraba da masu sayan ɗaya ko sari*
Vote
Share
And comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/6, 3:39 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romance and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 25 to 26*
*_____________________________________*
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 *DOLE NA MUKU GODIYA FANS DOMIN KUWA INA GANIN RUWAN MASOYA A WANNAN BOOK ƊIN I LOVE YOU UMMU NASMAH FAN’S*😘
________✍🏻 Musa mai gadi cike da mamaki yake kallon Falmata da ta fito da akwati idanunta hawaye yana gudu, da sauri musa ya ƙaraso tare da karɓar akwatin hanun nata yace.
” Ranki shi daɗe meyake faruwa, naganki kin fito haka kina hawaye, kuma yanzu kika shiga kina dariya kuma ki fito da akwati ina zaki.”
Falmata hanu tasa ta goge hawayen ta, sannan tayi murmushin dole tace.
” Babu komai Musa zanje gida ne, zan dawo zuwa anjuma, Mama zan kaiwa akwatin.”
Falmata ta faɗa masa hakane kawai dan bata son yawan Magana.
Kaɗa kansa Musa mai gadi yayi cikin rashin yadda yace.
” A’a ranki ya daɗe ba lafiya ba, kuka fa kike.”
” Kaga Musa nace maka babu komai, bani jakata na tafi dan Allah bana son yawan tambaya.”
Ajiyar zuciya Musa ya sauƙe tare da cewa.
” Shikenan kiyi hkr muje na rakaki ki hau adaidaitan”
Akwatin Musa yaja suka fice a ƙofar gidan suka tsaya jiran mai adaidaitan sun ɗan juma kaɗan kafin adaidaitan ya zo, Musa ne ya tare mai adaidaitan, Falmata ce masa tayi ” UNGUWAR BULUNKUTU TSALLAKE zaka kaini amma zaka ɗan jirani na shiga na karɓo maka kuɗinka, Musa cewa yayi.
” Malam nawa ne kuɗin ta da zata biya.”
” Ɗari Uku ne” mai adaidaitan ya faɗa, Musa cike da tausayin Uwar ɗakin nasa ya saka hanu a aljihun sa ya ciro Yan canjin sa, ɗari huɗu ne, ya zare ɗari Uku ya bawa mai adaidaita, sosai Falmata taji daɗin karan da Musa ya mata godiya ta masa sannan ya saka mata akwatin ta cikin adaidaitan hawa tayi Musa yana ɗaga mata hanu mai adaidaita yaja suka tafi, Musa cike da sanyin jiki ya shiga cikin gidan, zama yayi shuru yana tunanin meya fitar da Falmata cikin gidan a wannan yanayin, yana tsaka da wannan tunanin yaga Ladiyo ta fito da gana masgo ɗin ta a kanta, ware idanunsa yayi kansa ya ƙara ɗaurewa ” to ita kuma Ladiyo meya fito da ita da wannan dangwalin.” Sanda ta ƙaraso kusa dashi yace.
” Ke kuma ina zaki da wannan gana masgo ɗin.?”
Ajiye gana masgo ɗin tayi ta zauna a kai sai kuma ta fashe da kuka, cikin kukan tace.
” Ƙauyen mu zan koma, tunda Aunty tabar gidan nan, DOCTOR ya sake ta, ya mata walaƙanci, dan haka nima bazan zauna babu Aunty ba, tafiyata zanyi, na tsani doctor bashi da tausayi da imani, Aunty tana sonsa sosai tana masa biyayya amma baya gani tana haƙuri sosai dashi shine ya sake ta.”
” Innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un allahumma ajirni fil musibati!!!! Lallai Oga ya yiwa kansa babbar asarar dan bazai taɓa samun mace tagari irin Hajiya ba, Mtsss!!! Wannan ƙaddara data faɗawa waɗannan mutanen tayi muni domin kuwa rayuwar su ta baya ba haka take ba, Rayuwa suke mai tsafta da kuma burgewa a wajen ko wani mutum, Allah ya kyauta, kina da gaskiya Ladiyo bai kamata ki zauna a gidan nan ba tunda babu mace a cikin sa, ke zaki iya tafiya, amma ni zan iya zama, Allah dai ya daidaita tsakanin su, yanzu kin sanar da Oga zaki tafi ne.”?
” A’a ban sanar dashi kuma bana son sanar dashi bare kuma na ƙara kallon fuskarsa.”
Musa ce mata yayi.
” Karkiyi haka Ladiyo baki san me Allah ya ƙaddara tsakanin su ba, sai kiga idan Allah ya gyara tsakanin su, ko gobe ma sai ki iya ganin Hajiya ta dawo cikin gidan nan, abinda zakiyi yanzu kije ki sanar dashi cewa zaki tafi ƙauyen ku, sai sanda Hajiya ko wata mace ta dawo cikin gidan nan zaki dawo, kije ki sanar dashi kinji.”
Kaɗa kanta Ladiyo tayi alamun ta gamsu, gana masgon ta ɗauka ta koma ciki.
A kofar gidan nasu mai adaidaitan ya sauƙe ta, akwatin ta ta ja ta shige cikin gidan nasu matan gidan yawancin su suna zaune a tsakar gidan, bunta da akwatin hanunta sukayi da kallo, sallama ta musu tare da gaishe su zata wuce taji muryar Lami uwar gulma tana cewa.
” Mai kantu ya naga ƴar taku da akwati ko dai Hassan ya koreta ne.”
Taɓe bakin ta mai kantu tayi tare da cewa.
” Gata nan dai kam da alamar korar, dan zai aikata tunda ba mutunci garesa ba.”
Lami cike da tsurku tace.
” Hmmm idan anbi ta ɓarawo abi ta mabi sawu, suma fa idan da gaske ne zargin da Hassan yake musu to duk abinda ya yiwa Falmata yayi daidai.”
Tsuka Mai kantu taja tare da cewa.
” Ke kuma lami gulma gareki, to ina ruwan ki, da wannan maganar, ke komai kika gani sai kinyi Magana Mtsss!!”
Ta ƙarasa maganar tare da tashi tabar wajen, lami taɓe bakin ta tayi, tana bin mai kantu da harara.
Falmata shigewar ta Part ɗin nasu Darect ɗakin Hajja ta shige, sallama tayi jikinta a sanyaye, Hajja dake zaune tana lazimi ne tabi Falmata da kallo, ajiye tsarbin Hajja tayi tare da tasowa tazo kusa da Falmata ta dafa ta tare da cewa.
” Fatuma lafiya na ganki da akwati, kuma ga alamun kinyi kuka a idanunki meya faru.?”
Falmata kuka tasa tare da zama ta dafe kanta cikin muryar kuka tace.
” Hajja DOCTOR ya sake ni, yaci amanata Hajja, na shiga Uku na rasa farin ciki na Hajja, bana jin zan iya rayuwa babu DOCTOR Hajja ina sonshi Hajja ina sonshi.”
Kamar sauƙar aradu Hajja taji Maganar saki daga bakin Falmata, zama tayi itama Hajja cike da sanyin jiki ta dafa kafaɗar Falmata tace.
” Dama nasan dole wannan Auren naki zai mutu, alamun haka sun nuna tun sanda Hassan ya juya miki baya, bazaki mutu dan kin rasa Hassan ba, ko mutuwa yayi dole zakiyi haƙuri, Fatuma ki cire Hassan cikin ranki ki manta dashi a rayuwarki ki gina Sabuwar rayuwa karki dinga tuno Soyayyar da, ki dinga tuno walaƙantaki da yayi, ki barsa da Allah na Tabbata zai miki sakayya, Yagana dake kwance ta riƙe haɓa cike da mamaki tace yanzu naji naji muryar bukkar ya shigo jeki kira min shi harma da Yana.”
Tashi Aunty Yagana Tayi tare da amsawa da to ta fice Falmata cikin kukan ta cigaba da cewa.
” Bazan iya manta DOCTOR a cikin rayuwata ba, ina sonshi sosai Hajja koda rayuwata zata cigaba da wanzuwa zata wanzu ne cikin Soyayyar DOCTOR, bazan taɓa iya daina sonshi ba hajja.”
Cike da tausayin ta Hajja ta jawo ta jikinta tare da bubbuga mata bayanta alamun rarrashi, BUKKAR ne yayi sallama shida Aunty YANA suka shigo kusa da Falmatan shima ya zauna yana cewa.
” Lafiya kuwa Hajja yaushe Falmata ta shigo gidan nan kukan me kuma take haka.?”
Hajja amsa ta basa da cewa.
” Hassan ne ya saketa.”
Aunty YANA wani irin farin ciki taji a cikin ranta domin kuwa ta daɗe tana neman DOCTOR ya sakar mata ƴarta, kodan ta huta da baƙin cikin da yake shaƙa mata Baba Bukkar ne yace.
” Shikenan Allah yasa haka shi yafi alkairi, yaron nan Hassan yana min munanan abubuwa akan zargin sa na banza wanda bani da hanu a ciki, ya saketa Hajja domin ya ƙona min rai, amma insha Allah gaskiya zatayi halinta, kiyi hkr Falmata ki cigaba da addu’a Allah ya kawo miki wani mijin wanda ma yafi hassan.”
Da ameen Aunty YANA tace fuskar ta cike fam da farin ciki, Hajja cewa tayi.
” Bukkar daga kai har Yana kar wanda ya yiwa Hassan Magana akan meya sa ya saki Fatuma, kar Kuma ku nuna masa ɓacin ranku nima bazan sanja masa fuska saboda haka ba, Zuru ma ya ishi mai hankali, sannan ke kuma fatuma ki dinga control ɗin kanki duk sanda kika gansa dan Allah ko kallon sa karkiyi.”
Falmata ƙyaɗa kanta tayi alamun taji, Aunty YANA tashi tayi ta fice tana jin zuciyarta wasai, shima Baba Bukkar fita yayi ya rage daga Falmata sai Hajja, kwanciya Falmata tayi a gadon Hajja tayi shuru tana tunani, Hajja kuwa cigaba tayi da lazimin ta tana jin wani irin haushin DOCTOR a cikin ranta.
A cikin mintuna kaɗan Maganar mutuwar Auren Falmata ya karaɗe cikin gidan, koda labari ya iske su Hajjo da AJIRAM da tazo, sosai hankalin su ya tashi barin ma Hajjo har wani jiri take ji, FANNA kuwa farin ciki ma taji, Hajjo tashi tayi ita da AJIRAM suka nufi sashin su Falmata, ɗakin Hajja suka shige da sallama, Hajja ce ta amsa tare da nuna musu wajen zama, zama Hajjo sukayi cikin mutuwar jiki tace.
” Maganar da mukaji a cikin gida gaskiya ne, wai Hassan ya saki Falmata.”
Murmushi Hajja tayi cike da nuna rashin damuwa ta musu nuni da akwatin Falmata tace.
” Ganan Tabbas, amma yaje duniya ce ta isheshi riga da wando, ki duba yarinyar yanda take ajiyar zuciya duk son da take yiwa Hassan, ya cutar da ita sosai sai dai Allah baya barci zai mata sakayya.”
Runtse idanunta Hajjo tayi cikin ɓacin rai tace.
” Abinda Hassan zai aikata kenan wacce irin zuciya ne haka dashi, Tabbas ya cutar da ita Hajja, kuyi hkr dan Allah, zan kirasa yanzu dole sai ya maida Auren nan.”
Murmushi Hajja tayi tare da cewa.
” Allah ya sauwaƙa ai Falmata tabar Auren Hassan kenan har gaban abada, dan haka ku bar wannan maganar mutuwar Auren nan kwatakwata Allah yasa haka shi yafi alkairi, ni kaina idan naso dole sai ya maida Ita amma bazanyi haka saboda zaman Auren su baida wani amfani koda an mayar da Auren Cutar da ita kawai zai dinga yi, dan haka haƙura da wannan Auren shi yafi alkairi.”
Jinjina kanta Hajjo tayi har yanzu ranta a ɓace yake, duban Falmata tayi da tayi shuru ta kasa Magana domin kuwa ita kaɗai tasan abinda take ji a cikin zuciyarta, ƙarasawa Hajjo tayi ta dafa ta tare da cewa.
” Kiyi hkr Falmata, insha Allah Hassan sai yayi kukan rashin ki a rayuwarsa bazai gane kurensa yanzu sai sanda komai ya kufce daga hannun sa hankalinsa ya dawo jikin sa a ranar ne zai gane kuskukuren sa lokacin da baida damar gyarawa Allah ya baki haƙurin rashin sa.”
Hajjo ta faɗi tare da tashi suna ficewa cikin sanyin jiki AJIRAM kasa Magana tayi tsabar kunyar abinda ɗan uwanta ya aikata.
Wunin ranar Falmata tayi shine cikin baƙin ciki da damuwa, ko abincin dare gagara ci tayi, baccin ma kansa rabi da rabi tayi sa, haka ta kwana cikin ƙunar rai da Soyayyar mijinta.
Washe gari da sassafe DOCTOR ya tashi, ya shirya kasancewar yaune zasu je ƙauyen BINISHED, Bello ya kira ya sanar dashi cewa karya ɓata lokaci 11 zasu wuce, falo ya fito yana ɗaura agogon hanunsa, sharaf ya manta da babu mata a cikin gidan ya nufi daining, wayam ya gani babu komai, dafe kansa yayi ya manta da cewa Ladiyo ta tafi gashi ya tashi da yunwa tsuka yaja tare da ciro wayarsa ya dace kawu Dauda kira, ringin ɗaya ya ɗauka, cikin girmamawa DOCTOR ya gaishe sa tare da cewa.
” Kawu mun gama komai, anjuma zamu wuce da UMMA BINISHED.”
Da ƙarfi Kawu Dauda cikin tashin hankali ya furta.
” Whatttt!!!!! Wato ban isa da kai ba kenan, dana hana zuwa BINISHED ɗin wato zaka ce sai kunje to baza’a je ba, idan kuma kuka tafi to kuwa ranku zaiyi mungun ɓaci.”
Cike da ɗaurewar kai DOCTOR yace
” Kawu wai meyasa baka son muje ƙauyen nan ne kam, ka ɗagawa kanka tunda nace maka zamuje BINISHED, wai meye yake faruwa ne, ko akwai wani abune.”
Kawu Dauda saurin dawowa yayi cikin hankalin sa tare da cewa.
” Babu wani abu ni gani nayi munje wajaje da yawa neman maganin nan bamu sami wani nasara ba, shiyasa kawai bana son muje BINISHED ɗin saboda karmu sha wahalar banza.”
DOCTOR cewa yayi.
” Insha Allah Kawu ina ji a jikina zamu sami nasara dan haka zamu tafi anjuma ka mana fatan Nasara.”
” To shikenan Allah ya bada Sa’a.”
Ya faɗa a taƙaice yana kashe kiran, jikinsa kuwa ya jiƙe da gumi sharƙaf duban Jummai matar sa yayi dake gefen sa cikin tashin hankali yace.
” Mun shiga Uku asirin mu yana gaf da tonuwa, idan har muka bar yaron nan yaje BINISHED domin kuwa wannan malamin hatsabibin mutum ne, muddun YAMURAM ta dawo hankalin ta, to fa asirin mu ya tonu, domin kuwa tasan komai taji komai tasan mune muka ɓatar da mijinta da ƴarta, dole musan abinyi kafin su isa ƙauyen nan.”
Jummai a matuƙar har zuƙe ta tashi tace.
” Ƙarya ne asirin mu bazai taɓa tonuwa ba, wannan ƙauyen bazasu isa lafiya, domin dole sai mun dakatar dasu, *YAMURAM BAZATA TAƁA SAMUN LAFIYA BA A HAKA ZATA ZAUNA HAR MUTUWAR TA TA RISKETA* ka kwantar da hankalinka ni nasan abinda zamuyi.
Tir ƙashi wannan shi ake ana zaton wuta a maƙera, to fa ya zata kasance ku biyo ni domin sani👇🏻
*WACCE TAKE DA INTEREST TAKE ƘAUNAR KARATUN WANNAN LITTAFIN TAYI ƘOƘARIN BIYAN KUƊIN TA DOMIN KUWA FREE FAGE YA ƘARE WANDA YA BIYA SHI ZAI SHA KARATU AKWAI WAƊANDA SUKE CEWA 300 YA MUSU YAWA TO DUK MAI SO TAMIN MAGANA RAGI BAZAI GAGARA BA*
*TABBAS NAGA RUWAN MASOYA A WANNAN BOOK ƊIN UMMU NASMAH TANA ƘAUNAR FAN’S ƊINTA SOSAI😘😘🥰🥰*👇🏻
*Kuna iya nuna min soyayya ta hanyar siyen littafinan na DOCTOR HASSAN akan Naira 300 kacal,zaku iya biya ta wannan account ɗin 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK ko kuma ku tura katin MTN ta wannan number 08147537180,sannan ku tura shaidar biya a ita ko a 08147537180 Nagode masoya,ina maraba da masu sayan ɗaya ko sari*
Vote
Share
And comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/7, 5:40 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romance and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 27 to 28*
*_____________________________________*
_______✍🏻Me zakiyi Jammai wannan yaron yanda kika san shaiɗan haka yake taurin kai garesa, mawuyacin abune mu iya dakatar dashi daga wannan tafiyar domin kuwa idan yasa abu a gabansa sai ya kai ga cin Nasara ina mungun jin tsoron yaron”
murmushi Jummai tasa tare da cewa.
” Ka manta da cewa nima shaiɗance mai zaman kanta wallahi na fisa shaiɗanci, kasan dai zan iya aikata duk abinda nake so, ka barsu su tafi, ni kuma zan kira waya abi ta kansu da babbar mota.”
Zaro idonsa Kawu Dauda yayi yace.
” Me kike nufi, kina nufin a kashe su, to ma wai waye zaki saka yayi wannan aikin, ki dai sanja wani tunanin amma banda zancen kisa dan gaskiya akwai rai da yawa a cikin tafiyar Hajjo AJIRAM Bello ga kuma Hassan ga YAMURAM bazai yiwu ba gaskiya a sanja wata mafitar ba dai wannan ta kisa ba.”
Tsuka Jummai taja cikin tsawa tace.
” Ina ruwan ka da rayukan da za’a rasa, badai mutuncin mu muke nema ba, da kuma kuɗaɗen nan su tsira, to ka sani a wajen neman mutunci rai ba a bakin komai yake ba, wallahi sai naga bayan su kafin suga namu, JAMO zan saka ya min wannan aikin, dole mu dakatar dasu.”
Ajiyar zuciya Kawu Dauda ya sauƙe tare da cewa.
” Shikenan ayi hakan Allah ya huci Zuciyarki, ni ma bari na shirya naje muyi sallamar ƙarshe da su, idan sun mutum ma zamu fi samun sukuni wallahi, sai yanzu na hango zancen ki.”
Dariya Jummai tasa tare da cewa.
” Uhumm ko kai fa, shirya kawai kaje kuyi sallama saboda gudun zargi, karka nuna musu tsoro ko damuwa a tattare da kai na zuwan su ƙauyen kuyi komai cikin farin ciki da sakin fuska ka nuna musu kafi kowa son ganin ƴar uwarka ta samu lafiya, yanda bazasu fahimci komai a tattare da kai ba kace nima ina musu Allah ya kiyaye hanya.”
Shewa suka saka, kafin Kawu Dauda ya shige tollet, taɓe bakin ta Jummai tayi tare da furta ” haka kawai muna tsaka da jin daɗin mu, muna cin duniyar mu da tsinke ace za’a dakatar damu, wallahi bazai yiwu ba, duk mutumin da yace zai yanke mana jin daɗin mu wallahi sai naga bayan sa.”
Ita kuwa Falmata da damuwar ta tashi daga bacci, komai cikin sanyin jiki take yinsa, Hajja duk tana kula da yanayin ta, gaishe da Hajjan tayi ta amsa tare da cewa.
” Ga nan abincin karyawar ki, ki ɗauka kici maza, ina zaki naga kin shirya kina ɗauko jaka.”?
Cikin sanyin Murya tace.
” Makaranta zan tafi ina da lectures 11:30 abincin nan kuma DOCTOR ya isheni!!!”
Bakinta Falmata ta riƙe jin ta ambaci sunan DOCTOR a maimakon ta ambaci na Hajja, tana kallon Hajja cike da tsoron masifar ta, Hajja haɗa fuska tayi tamau tare da cewa.
” Wato har yanzu wannan uban yan iskan ne a cikin ranki ko, wai ke Fatuma baki da zuciya ne kam, duk wulaƙancin da Yaron nan ya miki amma yana maƙale a cikin ranki, to Allah ya yaye miki wannan jarrabawar da kike ciki, amma da zaki taimaki kanki ki cire wannan Soyayyar a cikin ranki da yafi miki sauƙi domin kuwa babu ke babu komawa gidan Hassan har abada, tashi kije kici abinci kafin na ɓata miki rai, me kikaci da zakice kin ƙoshi jiya ma haka kika kwana baki ci komai ba, shine yanzu ma zakice bazaki ci abincin ba to baki isa ba Wallahi ko zakici ki amarsa sai kin ci, kuji min ja’irar yarinya dai to Soyayyar taci uwarta Soyayyar banza Soyayyar da ba’a damu da dake ba, Soyayyar shan kwana maza ci abinci kafin raina ya ɓaci.”
Tura bakin ta Falmata tayi tana ƙunƙuni ta tashi ta ɗauko kwanon abinci tasa a gaban ta, Hajja hararar ta tayi tace.
” Ba dole kimin ƙunƙuni ba, tunda ni kin raina ni, aida shi uban naki Hassan ne yace kici da kin ɗauka jikinki yana ɓari kinci, to wallahi bazai yiwu ba, bazaki zauna kamar icce babu cin abinci ba saboda wani katon banza yana can yana ci yana sha yana walwalar sa, ke kuma kin zauna cikin damuwa da rashin kwanciyar hankali, bazai yiwu ba, bazan lamunta ba, ki cinye abincin nan tas ki bani kwanon.”
Falmata dai bata cewa Hajja komai ba sai famar cin dole take yiwa abincin, da ƙyar ta iya cin rabinsa ta ajiye tana duban Hajja dake zaune ta tsareta da idanu, bata ce mata komai ba hakanne yasa ta ɗaukar ruwan tea ɗin tasha kaɗan, wayar ta ta jawo ta dannawa Maji kira, bayan Maji ta ɗaga ne Falmata tace.
” Ƙawata idan kin tashi tafiya school ki biyo min ina gidan mu na nan BULUNKUTU TSALLAKE.”
Cike da mamaki Maji ta duba agogon bangon dake manne cikin Bedroom ɗinta, 10:39 cewa Falmata tayi.
” Falmata lafiya kuwa kike gidan ku wannan lokacin sassafe haka.?”
Numfashi Falmata ta sauƙe tare da cewa.
” Ke dai ƙawata sai kinzo kawai Maganar bata waya bace sai mun haɗu.”
Da shikenan Maji ta amsa tare da kashe kiran.
10:45 daidai DOCTOR ya shigo cikin gidan nasu part ɗin mahaifiyar tasa ya shige Darect, ya samu Hajjo da AJIRAM har sun shirya ta suma sun shirya, murmushi ya saki tare da cewa.
” Hajjo ina kwana har kun shirya kenan bari mu jira Bello to.”
Hararar sa Hajjo tayi cikin ɓacin rai tace.
” Ka kyauta Hassan ka kyauta da kaci amanar ƴar uwarka yarinyar da take maka Soyayyar gaskiya, kuma matar ka mai ƙaunar farin cikin ka, saboda kaga babu idon UMMA shiyasa kake abinda kaga dama, to wallahi ka sani kayi asarar mace ta gari, bazaka taɓa samun Mace mai biyayya da haƙuri irinta ba, kanka ka cuta ba mu ba kai ka sani.”
Ta ƙarasa maganar tana hucin Haushi, tunda ta fara Maganar DOCTOR ya sunkuyar da kansa ƙasa bai ce mata komai ba, tana gama ya juya tare da cewa.
” Bari naje na sanarwa Hajja tafiyar mu.”
Hajjo bata ce masa komai ba harya fice da sallamar sa ya shiga Part ɗin Yagana ce kawai a tsakar gidan, da har zai shige bai kulata ba, sai kuma ya tuno Maganar mahaifinsa da yake cewa ( Hassan duk abinda zai shiga tsakanina da Yan uwana babu ruwan ku a ciki karku raina su koda yankan naman junan mu muke munfi kusa tare kuka ganmu idan kun raina su tamkar kun rainani ne) runtse idanunsa yayi yana sauƙe ajiyar zuciya a dakile yace wa Yagana.
” Ina kwana Aunty Yagana.”
” Lafiya” itama ta amsa masa a taƙaice, DOCTOR shigewa yayi ɗakin Hajja da sallama, amsawa Hajja tayi cikin sakin fuska ba tare da ta sanja masa fuska ba, Falmata jin sallamar DOCTOR sai da taji zuciyarta ta tsinke, gefe kaɗan da Falmata ya zauna yana ƙare mata kallo ta kasan Ido gaishe da Hajja yayi ta amsa fuskarta a sake yace mata.
” Hajja yau zamu tafi da Umma BINISHED wajen mai magani shine nace bari na sanar dake.”
Hajja cewa tayi.
” Masha Allah yayi kyau yanzu zaku tafi kenan.”?
” Eh yanzu zamu tafi Bello kawai muke jira.”
Ya ƙarasa maganar yana duban Falmata da ta tashi zata bar ɗakin, Hajja cewa tayi.
” To Allah yasa aje cikin Nasara, nima ina shigowa yanzu na duba YAMURAM ɗin kafin ku wuce.”
Da to DOCTOR ya amsa tare da yin shiru yaji ko Hajja zata masa zancen sakin Falmata da yayi, amma shuru Hajja bata ce masa komai ba, ya juma zaune kafin ya tashi cikin sanyin jiki domin kuwa Hajja ta dafasa da ruwan sanyi, ita bata ɗaure masa fuska ba kuma bata sake masa fuska ba, babu wasan da suka saba da ita yau, cikin sanyin jiki ya bar ɗakin, koda ya fito Falmata da yana da kuma Yagana suna zaune babu wanda ya kallesa har Aunty YANA dama ita saboda ya sakar mata ƴarta take faɗa dashi, yanzu kuma ya saki yarta bata da wani contract dashi , daf da DOCTOR zai fice daga part ɗin shi kuma Baba bukkar yana shigowa, amma DOCTOR bai basa hanya ba, ya saka kansa, Baba Bukkar ganin yana da niyyar bigesa ya sashi matsawa gefe DOCTOR ya shige, Falmata da take kallon rashin mutunci da DOCTOR ya yiwa mahaifinta ne ya sata runtse idanunta hawaye ya gangaro mata saurin gogewa tayi gudun karsu Aunty YANA su gani, Ranar farko da ta fara jin haushin DOCTOR kenan a cikin RAYUWARTA tashi tayi da sauri tabar wajen jin kuka na neman ƙwace mata, Sarai Baba Bukkar ya ganta amma ya kauda kansa kamar bai gani ba, ya shige ɗakin sa shi kansa yana jin ɓacin rai akan abubuwan da ɗan yayan nasa yake masa, Falmata faɗawa tayi saman gadon Hajja ta saki kuka mai cin rai, Hajja haɓa ta riƙe tana cewa.
” Ikon Allah yanzu kuma me aka miki daga ganin sa shikenan sai ki hau kuka, Oh ikon Allah ni Maryam ina ganin wata shegiyar soyayya shifa yanzu baima nuna ya san Allah yayi ruwan tsoron ki a wajen nan ba, amma ke kin dagawa kanki hankali to wallahi ki cire yaron nan a ranki kafin hawan jini ko ciwon zuciya ya kamaki dan idan mutuwa ma kikayi shi baida asara.”
Shuru Falmata tayi sai kuma sauƙe ajiyar zuciya da takeyi bata kuma tanka Hajja ba, Itama Hajja bata kuma cewa komai ba, ta ɗauki hijabin ta ta shige duba YAMURAM.
Shigarta ta samu har sun fito suna shirin fita waje rike da Umma a hanu gefe guda kuma ga kawu Dauda tsaye kana ganin fuskar sa bazaka ce mungu bane, Hajja cewa tayi.
” Kaddai har kun fito, to Allah ya kaiku lafiya yasa a samu sauƙi, Allah ya baki lafiya YAMURAM”
, da ameeen Hajjo ta amsa har ƙofar gidan Hajja ta rakasu, suka shiga motar DOCTOR harda Fanna, Bello da DOCTOR sune a gaba, Kawu Dauda a dawo lafiya ya musu tare da fatan Nasara, Hajja tana ɗaga musu hanu har suka tafi, ta juya zata koma Cikin gida, sai taga Maji ma zata shiga murmushi Hajja tayi tare da cewa.
” Umhum yanzu kam zamu dinga ganinki ai tunda ƙawarki na gida, ina DANDA kwana biyu bana ganinta bata shigo mana.”
” Tana nan kuma Yan yawon nata ne basu biyo da ita ta nan ba.”
Tare suka shiga suna zance, har ɗakin Hajja, Maji Falmata dake kwance tana sauƙe ajiyar Zuciya tabi da kallo zama tayi saman gadon ta dafa ta tare da cewa.
” Ƙawata wannan yanayin da na ganki a ciki ba lafiya ba, nasan matsalarki bata wuce DOCTOR, meya faru.?”
Tashi Falmata tayi idanunta sunyi jajur ta kama hanun Maji tace.
” Kinsha cemin DOCTOR ba Soyayyar gaskiya yake min ba, ban taɓa yarda da kalamanki ba, a zato na kawai bakya son Doctor ne, ashe abun ba haka yake ba, ke kin hango min abinda ni na kasa hangowa, Maji DOCTOR ya sake ni, bayan ya gama ciwa iyayena mutunci ya zagesu a gabana, ya zargeni da zina da HABEEB, a karshe ya bini da takaddar saki, hakan bai masa ba, yau a gabana DOCTOR yayi niyyar bige mahaifina, sai hanya Baba ya basa, Tabbas yau na tabbar da cewa DOCTOR ba sona yake ba, sai dai kash zuciyata ta kasa wurgar da Soyayyar sa, kullum sonsa ƙaruwa yake a cikin zuciyata, ina son na cire Soyayyar DOCTOR a raina ki faɗa min taya zan cire ta yaya.”
Ajiyar zuciya Maji ta sauƙe cike da tausayin kawar tata tace.
” Hmmm!!! Dama nasan haka zai faru domin babu imani a zuciyar DOCTOR, iya da mungun son kansa da zafin zuciya ta tsiya, ƙawata ki dage da addu’a baki cuci DOCTOR insha Allah Allah zai cire miki Soyayyar sa a ranki, shi kuma yaje kansa ya yiwa asara, akwai maza da yawa wanda suka fishi komai kuma suna sonki dan haka zaki samu wanda ya fisa sonki wanda zai adana miki rayuwarki, ki barsa da Allah insha Allah sai ya miki sakayya, dan tashi ki wanke fuskar ki ki shafa powder mu tafi school time ya kusa.”
Ajiyar zuciya Falmata ta sauƙe tare da tashi ta shige tollet ɗin Hajja dake cikin ɗakin ta wanke fuskar ta, powder da lipstick ta shafa sannan ta dauki bag ɗin ta suka fito, Aunty YANA taje ta yiwa sallama Baba Bukkar ne ya ɗauki 1k ya bata yace tayi transport, karɓa Tayi ta masa godiya sannan suka fice.
Su kuwa su DOCTOR hanya suke ta famar ƙwasa domin kuwa tafiyar 50 minute ne zata kaisu BINISHED, sunyi nisa da tafiya kamar wanda akace DOCTOR ya ɗago kansa yaga doguwar Mota tana nufo kansu gadan-gadan, innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un DOCTOR ya furta a kiɗime tare da duba gefen da zai kaucewa Motar nan ma dai wata motar ya hango, zuciyarsa ne ta tsinke Bello shima cike da tsoro yake bin motar da kallo yace.
” DOCTOR Motar nan fa kanmu take biyowa ka kauce mata mana.”
Su Hajjo kuwa babu abinda suke sai salati Fanna kuka tasa DOCTOR cewa Bello yayi
” Ta ina kake ganin zan kauce masa, ka duba ka gani ko ina na juya ƙarshen karo zamuyi da wata Motar.”
Dafe kansa yayi ba kansa yake ji ba, matan dake cikin motar yake ji, yanzu meye abun yi ta ina zai iya tseratar da rayuwarsu…..?????
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Amsar ku tana page ɗin gaba ta hanyar 👇🏻
*Kuna iya nuna min soyayya ta hanyar siyen littafinan na DOCTOR HASSAN akan Naira 300 kacal,zaku iya biya ta wannan account ɗin 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK ko kuma ku tura katin MTN ta wannan number 08147537180,sannan ku tura shaidar biya a ita ko a 08147537180 Nagode masoya,ina maraba da masu sayan ɗaya ko sari*
*WAƊANDA SUKA CE 300 TA MUSU YAWA SUMIN MAGANA TA PRIVAT RAGI BAZAI GAGARA BA INDAI KINA DA INTEREST AKAN BOOK ƊIN*
Kumin afuwa yau ban samu nayi Editing ba.
vote
Share
And comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*[9/8, 6:04 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
*🩺DOCTOR HASSAN🩺*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻
❤ *Love and romance and funny story* ❤
*Writing by*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah*
Marubuciyar nan taku ta *INDO A BIRNI*
Na sadaukar ga wannan littafin gareku MASOYANA a duk inda kuke ina Alfahari daku a ko yaushe, da wanda na sani da wanda ban sani ba, domin kuwa naji daɗin yanda kuka karɓi wannan book ɗin nawa na Indo a Birni.
*Special Gift to*
*Masoyan Asali waɗanda suka kasance dani a cikin book ɗina na kuɗi wanda ya gabata wato Ruɗanin Zuciya biyu kun sayi wannan book ɗin fiye da zato na Tabbas kun nuna min ƙauna domin kuwa hakan ya gwada min kuna tare dani ako yaushe koda kuɗi ko babu nima dai Ummu Nasmah ina ƙaunar ku*🥰
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*BOOK ONE*
*PAGE 29 to 30*
*_____________________________________*
_______✍🏻Doctor gabaki ɗaya ya kiɗime ya shiga cikin tashin hankali ya rasa ya zaiyi ga Umma da numfashin ta yake neman ɗauke wa, mirrorn motar ya kalla yana ƙarewa bayan sa kallo, babu wata mota a bayan sa hakanne ya sashi ya fara ribas yana ja da baya da sauri, har ya samu ɗan tazara tsakanin sa da waɗannan motocin, layin dake gefen sa DOCTOR yasha kwana ya fasa jejin, wani wawan ribas yaja kafin yayi parking yana sauƙe ajiyar Zuciya, kansa ya kwantar jijin sitiyarin motar yana sauƙe numfashi shi kansa Bello ajiyar zuciya yake sauƙewa, Fanna sai yanzu ta daina kuka, su Hajjo kuwa ko magana sun kasa tsabar sun tsorata, ai kuwa kamar wanda akace DOCTOR ya ɗaga kansa, wannan Motar ya hango ta faso jejin da gudun tsiya ta nufo matar su, idanunsa DOCTOR ya zaro, Motar ya taka da karfi ya figi motar da mungun gudu, cikin jejin suka nufa Allah sarki UMMA numfashin ta sama sama ya fara yana neman ɗauke mata saboda jijjigar motar, Hajjo da AJIRAM kuka suka saka tare da kanƙame Umma suna kiran sunan ta, zuwa yanzu ran DOCTOR ya fara ɓaci, ya fahimci wannan drevern turo sa akayi ya kashesu, kaɗan ya hana motar ta daki tasu DOCTOR, sai Allah ya bawa DOCTOR Sa’a yayi saurin kauce masa, wata babbar bishiya Motar ta buga da ƙarfi, ta tsaya cak, DOCTOR daya kauce ne ya faka motar ya fito da sauri a matuƙar harzuƙe a fusace, sai dai ina wannan drevern doguwar Motar yana hango DOCTOR ya daka tsalle daga cikin motar ya shige cikin dajin da gudu, DOCTOR binsa zaiyi Bello ya riƙesa yana cewa.
” Binsa zakayi kasan meya shirya, idan kuma bashi kaɗai bane fa, kaga da Allah ya kare mu ma mu gode masa kazo mu tafi, Umma tana cikin wani hali, shi kuma ko waye shi yaje shida Ubangiji.”
DOCTOR yana huci ya juya suka shiga cikin Motar ba kowa yake zargi da turowa a ɗauki rayuwarsu ba, sai Baba Bukkar da matarsa, juyawa yayi ya kalli Umma da take famar sauƙe wani wahalallen numfashi wanda yake fita da ƙyar tausayin ta ne ya kamasa, motar yaja da gudu suka fito daga jejin, titi suka hau yayin da DOCTOR yake wani wawan gudu ya samu ya isa da Umma BINISHED da wuri, a cikin lokaci kaɗan kuwa suka dumfaro ƙauyen
*BINISHED*
” AYYARE iye ala gidigo ala gidigo ala gidigo baban goggo ala gidigo ke yarinya zaɓi dogo zaɓi dogo na ɗan wuro dokin iyali alagidigo ita mai wada turmi ta tuno turmi ta tuno zuwa ƙasa ta hau kujera alagidigo budurwar guntu ɗan wadas.!!!!! Ahayye nanaye, cap aradu wata taji kunya, ƙwal uba, yau saurayi haka kamar ɗan tsako abu ɗan yol babu kyan gani sai uban ƙaton kai MERAMA yasin saurayin kin nan bashi da kyan gani sai kace irin aljanu Yan gwaigwai ɗin nan masu rusheshen kayi kamar Rasha, ga wata shegiyar yar sharar sa ta shan iska da baya sanja ta kullum itace a jikin sa kamar ɗan matsiyata, cap wai sunan wata unguwa a Gombe BAGADAZA UNGUWAR SHAN ISKA ”
Ta ƙarasa maganar tana sheƙewa da dariya tana nuna mairama da yatsa, yaran dake wajen suma dariya suka saka har suna riƙe ciki, wani irin haushi ne ya kama mairama idanunta suka ciko da hawaye Muryar ta raurau tace.
” Haba AI’SA wannan wani irin wulaƙanci ne, naga ai Allah shine ya hallici dogo ya hallaci guntu, kuma duk wanda ya raina tsayuwar wata ya hau sama ya gyara, da kike zaginsa ai gara shi akan Kacalla yayanki mai ido ɗaya, cap wannan shine wurƙilina Kacalla baƙi mai ido ɗaya ɗan FEREBUWAYE jikan KAKA gurguwa masifaffiya.”
Ta ƙarasa maganar tana murguɗawa AI’SA baki, ai kuwa take Ai’sa ta cika tam kaɗan ya hana ta fashe, ɗan kwalinta ta cire tasha ɗamara dashi ta sunkuya ta daki ƙasa, tare da cewa.
” Na rantse da wanda ya hallici wannan ƙasar yau babu mai hanani cin Durun uwar ki sai Allah, wani irin wawan duka ta kaiwa Mairama sai kuwa aka tirke da kokuwa, AI’SA cike da kwarewa a faɗa ta jidi ƙafar Mairama ji kuke tim Mairama ta faɗi ƙasa, kanta Ai’sa ta hau ta dinga dukanta danneta tayi ta dubi KARIMA, Tace.
” Karima cika min wannan ɗan iskan bakin nata da ƙasa, karima cike da tsoron Ai’sa ta ɗebi ƙasa ta dinga ɗurawa Mairama sanda suka cika mata bakin ta da ƙasa Ai’sa ta wawwanka mata mari sannan ta tashi a kanta tana riƙe ƙugu tare da.
” Dan ubanki gobe ma ki ƙara zagin halittar ƴan gidan mu kiga yadda zan sanja miki kama, ta ƙarasa maganar tana juyawa ta bar wajen karima bayanta tabi, yaran dake wajen suka dinga yiwa Mairama dariya, haushi ne yasa Mairama saka kuka ta bar wajen da gudu.
Sunyi nisa da tafiya karima ta saka dariya tana duban Ai’sa tare da cewa.
” Gaskiya AI’SA yau kin yiwa Mairama rashin mutunci, Allah ta bani tausayi yanzu bakya tsoron ta faɗawa wannan mahaukacin yayan nata BABA KAWU ya ritsaki a hanya ki shiga Uku”
Tsuka AI’SA taja tare da cewa.
” Mtsss!!!! Ke rabu da shegiya, daga na zagi saurayin ta shikenan sai ta zagi Yan gidan mu, ni Yan gidan su na zaga, ta faɗa masa mana wallahi ina dai dai dashi.”
Hommmmm da sukaji ne yasa su ɗaga kansu wata farar mota ce ƙal mai kyan gani da sheƙi ta ɗauke musu Ido, Karima cike da ƙauyanci take kallon Motar, ita kuwa AI’SA bakin ta ta taɓe sam bata wani yi ƙauyanci ba, kasancewar ta saba ganin irin Motar suna shiga birni sa’i da lokaci, ko gezau Ai’sa batayi ba daga wajen da take tsaye Karima ce ta matsa gefe tare da cewa.
” AI’SA kinga wata moto mai kyan gani, ki matsa mana shigewa zatayi fa.”
” Ke dallah gafara can, na matsa naje ina, waya zo ya sami wani a nan, ko itace kaɗai hanya anan ga nan nan yabi ya wuce mana.”
Ta ƙarasa maganar tana nuni da gefen dake cike da ciyawa, Karima shuru tayi bata kuma cewa komai ba saboda tasan yanzu Ai’sa zata iya zaginta.
DOCTOR Haushi ne ya kamasa ya ƙara danna hommmmm!!! Da ƙarfi amma ina yanda kuka san da kurma yake, cije leɓensa yayi cike da ɓacin rai dama kuwa ran nasa a ɓace yake, Motar ya tayar tare da cewa.
” Zanbi kan yarinyar na taka ta da ubanta, kai duk wanda aka kirasa da ɗan ƙauye Wallahi an cucesa, yanzu idan Banda jakanci da dabbanci irin na baƙauyen mutum kina ganin mota na danna miki homm kiyi kunnen uwar shegu.”
Hajjo ce cikin tsawa tace.
” Kai dakata uban Yan zafin ran tsiya, kai sam baka da haƙuri a rayuwarka, Bello fita kaje ka mata Magana ta kauce ko.?”
Da to Bello ya amsa tare da fita ya nufi wajen Ai’sa, a bayan ta ya tsaya tare da cewa.
” Baiwar Allah, dan Allah ki ɗan matsa gefe kaɗan zamu wuce da mota.”
Tsabar tsiya da Rashin mutunci dake gaban goshin Ai’sa bata juyo ta kalli Bello bama bare kuma ya samu arzikin amsa, ya mata Magana yafi baki biyar bata kulasa ba duban Karima dake gefe yayi yace.
” BAIWAR ita wannan ɗin kurma ce.?”
A fusace Ai’sa ta juyo cikin faɗa tace.
” Ba kurma ba Allah yasa bebiya ce Ni, bazan matsa ba idan duka hanyar dake gefen nan bai isheku wucewa ba, kuta tsayuwa a wajen daga nan har zuwa sanda zan gama tsayuwata.”
Cike da mamaki Bello yake kallon ta, yau yaga ikon Allah, babu ƙira kuma mai zaici gawayi, lallai wannan DOCTOR shine daidai ita, juyawa yayi ba tare da yace komai ba, motar ya buɗe ya shiga tare da cewa.
” Wannan yarinyar bata da mutunci, domin kuwa bazata kauce daga wajen nan ba.”
DOCTOR da yake cike fam da haushinta ne ya buɗe motar ya fice a fusace, yana zuwa wajen yace.
” Ke jakar ƙauye, mahaukaciya ce ke, ko kuma tsabar ƙauyan ci da daƙiƙanci ne yake damunki, ku Yan ƙauye haka kuke sam babu hankali a jikin ku, ki kauce mana a hanya idan ba haka ba, zan takaki da mota kuma na taka banza, wawiya kawai ”
AI’SA runtse idanunta tayi cike da haushin Maganar sa, tunda take babu wanda ya taɓa mata zagin da wannan mutumin ya mata, a fusace ta juyo, zata fara zaginsa kawai sukayi Ido huɗu dashi shima cike da mamaki ya nunata da yatsa yace.
” Dama kece, no wonder zakiyi abinda yafi haka, dama can da haukarki a kanki, kauce ki bamu waje.”
Ƙanƙance idanunta AI’SA tayi na rashin mutunci tace.
” Baran matsa ba jakin Birni, kazo ka takani idan ka fasa takani ka raina Allah daya hallice ka, ni da kai waye daƙiƙin yanzu, da nayi niyyar matsawa amma yanzu bazan matsa ba, kayi uban da zakayi, banza marar lissafi.”
Ta ƙarasa maganar tana riƙe kunkumi, tunda yake a rayuwarsa babu wanda ya taɓa masa zagin da wannan yarinyar ta masa, ransa take ya ƙara ɓaci ya hasala, hanu ya ɗaga da niyyar wanka mata mari, tayi saurin kaucewa tana cewa.
” Dakata jakin Birni karka sauƙe fushin ka a kaina da alamu dai yau, mahaukatan aljanun ka suna kanka wata ƙil ma harda daƙiƙanci ke damunka, bari na baka hanya kafin ka sauƙe haukar a kaina.”
Ta ƙarasa maganar tana kaucewa tare da jan hanun Karima suka bar wajen, DOCTOR Zuciyarsa sai tafasa take yi ta gaya masa maganar da ba’a taɓa faɗa masa ba, dama ashe suma ƙauyawa sun iya baƙar Magana wani irin tsanarta yaji tsanar da bai taɓa yiwa wani ɗan adam shi ba, hmmm ya jima tsaye yana jinjinawa Maganar ta…………………..
Last Free page ne shiyasa na muku typing kaɗan yau ƴar uwa idan kina buƙatar wannan rikitaccen labarin mai ƙunshe da Zazzafar soyayya tausayi rikici ban dariya faɗakarwa tare da gurmi, maza ki garzayo kizo ki biya kuɗinki domin kuwa daga yau Free page ya kare bazaku sake ganinsa ba, sai wanda ya biya kuɗin sa ki biya ta👇🏻
*0006064512 Rashida Usman Jaiz Bank ko kuma mtn card ta wannan number 08147537180 sai ki turo da shaidar biyan ki ta ita number, 300 Naira kacal zaku biya wacce bata da ƙarfin biyan haka tamin Magana ni kuma zan mata sauƙi yadda zata iya biya Ummu Nasmah tana ƙaunar masoyanta domin kuwa taga ruwan masoya a wannan BOOK ƊIN kun saya sosai.*
Kuna iya nuna min Soyayya ta hanyar siyan littafin nan
Vote
Share
And comment
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/10, 11:03 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: Cike da ɓacin rai ya koma cikin motar baice musu komai ba yaja motar tare da kallon Bello da idanunsa da sukayi jajur yace.
” Sai wata hanya zamu bi kuma ya kaimu zuwa gidan.”
Bello kwanar dake gefen daman su ya nuna musa, DOCTOR kan motar ya karya zuwa kwanar, suna tafiya Bello yana nuna masa hanya har suka iso ƙofar gida, mai cike da yara suna karatu harda almajirai, bayan DOCTOR yayi parkin ne suka fito da Bello daga cikin Motar tare da nufar wani kyakkyawan dattijo fari sol fuskar sa cike da haiba yana zaune kan taburma ta kaba, sallama sukayi ya amsa musu yana matsa musu ya nuna musu wajen zama, zama sukayi DOCTOR ya miƙa masa hanu sukayi musabaha shima Bello hanu ya miƙa masa sukayi musabaha Malam Gana yana dariya ya cewa Bello.
” Muhammad Bello ko.?”
Murmushi Bello yayi tare da cewa
” Ehh malam ashe baka manta dani ba.”?
Murmushi malam yayi yace.
” Ina zan manta da kai duk sintirin zuwan da kayi wannan ƙauye.”
Dariya Bello yayi yace.
” Hakane, Malam wannan Ɗan uwana ne sunan sa Hassan likita ne shi, Malam mahaifiyarsa ne bata da lafiya yau kusan shekara ɗaya tana kwance anyi maganin asibiti anyi na gida amma babu wani sanji shiyasa nace muzo wajen ka ko Allah zaisa a dace.”
Murmushi Malam yayi tare da cewa.
” Ayya ayya!!! Sannu yaro kaji, yanzu ina take marar lafiyar kunzo da ita dai ko?”
DOCTOR ne yace.
” Eh Malam munzo da ita tana cikin mota ma yanzu haka.”
Tashi malam yayi tare da cewa.
” Ayya ai sai ku sanar dani da wuri suna cikin motar, ku fito da ita maza a shiga da ita cikin gida.”
Da to suka amsa tare da tashi suka nufi motar leƙawa DOCTOR yayi yace.
” Aunty Hajjo ku fito da UMMA.”
Ya faɗa yana buɗe musu ƙofar Motar, fitowa sukayi riƙe da Umma, malam cike da tausayi ya musu jagora zuwa cikin gidan da sallama suka shiga Mama Ferebuwaye tana zaune a shinfiɗar taburma ta karamno ta amsa tana tashi da sauri ta basu taburmar suka kwantar da Umma a taburmar sannan Ferebuwaye ta shimfida musu wata taburmar tana musu sannu da hanya Fanta dake zaune gefe ne ta gaishe su tana musu sannu da zuwa, malam Gana zama yayi a gefe yana ƙarewa UMMA kallo tare da nazarin ciwon nata, sosai ya ƙare mata kallo kafin ya dubi DOCTOR yace.
” Wannan ciwon nata Asiri ne aka mata, ba ciwon Allah da Annabi bane sannan kuma asiri ne mai wuyar karyawa saboda an mata ture harda aljanu shiyasa take wani kamar na marassa hankali.”
Da sauri DOCTOR ya dubi Malam cike da kiɗima yace.
” Malam duk inda mukaje karɓar magani abinda ake faɗa mana kenan, malam anya kuwa Umma zata sami lafiya.”
Ya ƙarasa maganar cike da raunin murya, murmushi malam ya saki tare da cewa.
” Zata warke bi’izinillah, hanune yayi asirin ai, Kuma hanune zai karya sa, na ɗauka maka alwashi da izinin Allah sai na karya wannan sihirin, karka samu damuwa mahaifiyar ku zata warke kamar bata taɓa wani ciwo ba.”
Jinjina kansa yayi tare da cewa.
” Shikenan Allah ya sa mun gode sosai, to yanzu malam nawa zamu bada kuɗin maganin.”
Murmushi Malam yayi tare da cewa.
” Karka damu da kuɗin magani, bana buƙatar su, bana karbar kuɗin magani ina yine fisabilillah, zan mata magani kyauta fatan dai Allah ya mana jagora ya kuma bata lafiya.”
Da ameen dukkan su suka Amsa DOCTOR yana jinjinawa karamci irin na wannan malami da abun duniya sam bai ruɗe sa ba DOCTOR duban Bello yayi tare da cewa.
” To Bello kai da AJIRAM da Fanna zaku koma gida anjuma, ni da Hajjo zamu zauna, ni ɗin ma ba zama zanyi, gobe zan dawo Hajjo ma kaɗai zatayi jinyarta idan yaso sai adinga zuwa ana dubata.”
Da to suka Amsa, Fanta ne ta taho da ƙwarya a hanunta mai cike da nono wacce tasha fura damammiya ta ajiye musu a gaban su, komawa tayi ta ƙara dawowa da wata ƙwaryar tuwon BURABUSKO NE MIYAR GANYEN YAKUWA ta ajiye sannan ta samu waje ta zauna (Yasin nasan idan akwai kanuri mai karatun book ɗin nan yawunsa ya tsinke 🤣) Malam yace musu Bismillah kuci abinci.
Abincin suka ci shidai DOCTOR furar kawai yasha, saboda ransa a ɓace yake baya jin zai iya cin abinci har yanzu Maganar da yarinyar nan ta faɗa masa ne take masa yawo a kunnen sa, hanu yasa ya toshe kunnen sa tare runtse idanunsa yana jin zafin Maganar.
Da gudu Kuwa ta shigo cikin gidan tana tuntsire dariya har da sunkuyawar ta, ADDABO LUTIYA ne ta biyo ta cikin gidan da gudu itama, ƙara AI’SA ta saka sanda su Hajjo suka tsorata DOCTOR da sauri ya buɗe idanunsa yana duba wajen da ƙarar ta fito, fes ya ɗaura idanunsa akanta cike da tsana yake kallon ta, Malam ma cikin ɓacin rai ya dubeta ita kuwa ɗakin Kaka ta shige tana cewa.
” Na shiga Uku kaka, wannan ɗimemiyar mai ƙirar samudawa zata kashe ni, dan wallahi tana zama a kaina sai dai wata amma ba niba.”
KAKA dake zaune tana ɓarar gyaɗa ne ta rarumo sandar ta, ta miƙe da ƙyar ta fito bakin ƙofa ta tsaya, turus ADDABO ta tsaya tana ajiyar Zuciya kallon ta kaka tayi tace.
” To Uwar marassa kunya, yanzu biyota kikayi har gidan ubanta ki daketa Saboda baki da mutunci, to ai ko mutuwa ma tana Kunyar idon uwar ɗa bare kuma ke, maza fice min daga cikin gidan nan kafin na raɗeki da sandar nan, marar Kunyar wofi ”
ADDABO cike da haushi tana haki tace.
” Wallahi kaka bazan bar nan ba, sai nayiwa Ai’sa shegen duka, uban waye yace ta ce min ADDABO ƳAR LUKUTA MAI SIFFAR KWAƊI Allah bazan yadda ba sai na rama.”
Ta ƙarasa maganar tamkar zata saka kuka, ai kuwa tun kafin kaka tayi magana, AI’SA ta rigata cewa.
“Ubanki ne, tunda sune suka haifeki ƴar lukuta, Kuma na faɗa ADDABO ƳAR LUKUTA MAI SIFFAR KWAƊI, ƙarya nayi ke ba mai siffar kwaɗin bane, kiga fa yanda kike dunƙule kamar kwadon.”
Kaka dariya tasa tare da cewa.
” Shakka babu jikata Ai’sa batayi ƙarya ba, kamarki sak da kwaɗin, dubeki fa tsabar dunƙulewa da kikayi ko wuya baki dashi, zaki kauce min a ƙofar sauro ne ko sai naci uwarki SA’A mai koko.”
DOCTOR Kaka kawai yake bi da kallo mai cike da ɗunbin mamaki, yau yaga ɗaurewa ƙarya gindi, yarinya ta nemo faɗa, ta gudo gida maimakon a hukuntata sai kuma a ɗaure mata gindi Tabbas dole wannan yarinyar tayi rashin kunya.”
Girgiza kansa kawai yayi yana ƙara jin wata irin sabuwar tsanar yarinyar, idanunsa ya ɗan rufe tare da buɗesu yana cigaba da ƙarewa kaka kallo na marar adalci, Malam Gana tashi yayi ya nufesu, sanda yaje ya tsaya a gaban ADDABO cike da kulawa yace.
” ADDABO kiyi hkr kinji duk naji abinda kikace ta miki, kiyi hkr bata kyauta ba, Kuma insha Allah zan hukunta ta, bazata ƙara miki ba kinji.”
ADDABO cike da jin haushi ta jinjinawa Malam kai kafin ta juya ta fita tana ƙananan magana, kaka ce tace.
” Zata sake !!! Nace sai ta sake tsokanar tata, kazo kayi abinda zakayi, har wani zaka hukunta ta, to hukunta ta mu gani, tunda kana gadarar kai ubanta ne, to bari kaji wallahi babu ruwan ka da yarinyar nan, ka fita idanunta ka barta tayi abinda take so haka kawai kunsa yarinya a gaba.”
Malam Gana cike da girmamawa ya cewa mahaifiyar tasa.
” Allah ya huci Zuciyarki AMMA (dake haka yake kiranta dashi), amma AMMA baki ganin abinda *A’ISHA* take a cikin garin nan yayi yawa, ina guje mata bakin duniya ne AMMA kar bakin mutane yayi yawa a kanta bakin mutane guba ne wani bakinsa bashi da kyau, abinda nake so ki fahimta kenan, saboda ita macece wa zai yadda ya aureta da wannan rashin ɗa’ar da take dashi ni kaina uban da na haifeta zan bada shaidar rashin kunyarta dan Allah Amma ki daina biye mata na roƙeki.”
Cike da faɗa kaka tace.
” Ni na auru ai ko tunda har na haifeka, tunda na auru to Itama zata auru domin kuwa na fita faɗa sanda nake kamar ta, Kuma a haka ubanka yake sona Ko ɓacin raina baya so, haka zamuyi faɗan mu, cikin dare ya rarrashe ni, mu shirya, dan haka karka kuskura ka mata mungun baki, juyawa tayi ta kalli Ai’sa tace mata, Ai’sa duk wanda ta miki a cikin garin nan kema ki masa karki raga masa ko ubansa waye ne.”
Wani ɓacin rai Malam Gana yaji a cikin ransa harga Allah baya jin daɗin abinda AI’SA keyi, sannan baya son irin tarbiyyar da kaka take bata, ɗan yaune kawai ka haifesa baka haifi halinsa ba da Ai’sa ta ɗauko sa ko yatsa aka sa mata a baki bazata ciza ba, juyawa yayi ya koma ba tare da yacewa kaka komai ba, amma sam ranshi babu daɗi, kaka komawa tayi cikin ɗakin itama tana zungurin Ai’sa da sandar hanun nata tare da cewa.
” Munafukar Allah, da kika tsokanota da ta riƙeki, ta zaune a ruwan cikin ki da wannan ɗimaɗiman ɗuwaiwan nata, da sai kinyi kashin hanjin ki, gobe na sake jin kin tsokanota kiga yadda zan barki da ita ta jibgeki kamar Allah ne ya aikota”
Bakin ta Ai’sa ta tura cike da rashin mutunci tace.
” Malama daina zunguri na mana, niɗin shegiya ce zan tsaya harta dukeni, kuma wallahi ko gobe na ganta sai na tsokanota.”
Ta ƙarasa maganar cike da tsiwa tana fita, wajen Mama ta wuce tana ganin su Hajjo ko kallon su batayi ba zata wuce, Malam ya kirata.
” Ke AI’SA zonan.”
Tahowa tayi tana tura baki ta tsaya a kansa ba tare data risina ba tace.
” Gani Malam.”
Malam ɗaga kansa yayi ya kalleta cikin ɓacin rai yace.
” Bani maganin nasha, kinji uwata tunda kin tsaya a kaina.”
Bakin ta tura tare da zama tayi shuru Malam Gana faɗa ya hau mata.
” Wai yaushe zakiyi hankali ne kam, sam ke a Duniyar ki baki daraja mutane, Ai’sa ina son ki dawo hankalin ki ki nutsu kisan me kike yi bana son duniyar ta nuna miki kurenki domin kuwa baza kiji daɗi ba, jiyan nan Malam Umaru ya kawo min togaciyar ki kin zagesa, sa’anki ne shi, to wallahi ki kiyayi duniya, ki daina biyewa AMMA tana ɗauraki a turbar da ba itace gaskiya ba, ina miki faɗa ne a matsayina na mahaifinki, sannan kina kallon Mutane bazaki gaishe su ba, sai ki saka kanki ki wuce, to maza ki gaishe su.”
Ƙara turo bakin tayi gaba, kafin ta kalli su Hajjo tace.
” Inda dabtu.”
Ta gaishe su cikin harshen kanuri, amsawa sukayi cike da mamakin yarinyar, juyowa tayi zata ɗagawa su DOCTOR gaisuwa, karaf kuwa suka haɗa Ido dashi, zaro ido tayi tana mamakin meya kawosa gidan su, shi kuwa harara ya wurga mata, tsuka taja tare da cewa.
” Malam ya isheka harara ta, sai wani kallon banza kake min da wasu ƙananun idanunka kamar wanda ka roƙa aka sammaka, an faɗa maka gaishe ka zanyi da kake shirin nuna min IZZA, Mtsss!!!! Marar lissafi kawai.”
🤣 Kuzo kuga baƙin ciki a ZUCIYAR DOCTOR ji yake kamar ya shaƙo wuyanta sai ya kaita lahira kafin ya saketa, yunƙura yayi zai tashi, Bello yayi saurin riƙesa yana girgiza masa kai, alamun ya bari baƙunta sukazo, komawa yayi ya zauna iya jin wani takaici yana hauro masa, Malam Gana cike da haushi ya yunƙura zai jawota ya mata shegen duka, ganin haka da AI’SA tayi ya sata tashi ta fice da gudu, cike da jin haushin abinda ta musu Malam yace.
” Kayi haƙuri Yaro kaji ɗan yaune ka haifesa baka haifi halinsa ba, haka nake fama da Ita, kayi hkr, ka mata addu’ar shiriya.”
Tsabar takaici DOCTOR kasa amsawa Malam yayi, shi dai bai taɓa tsanar mutum ba, irin yanda ya tsani wannan yarinyar.
Awansu biyu Malam ya fara yiwa UMMA magani bayan ya bada ɗaki guda wanda za’a ajiyeta a ciki da la’asar lis DOCTOR ya bawa Bello kay ɗin mota yace su koma gida, gobe da azahar yazo ya ɗauke sa, haka kuwa akayi suka kama hanyar cikin Maiduguri har suka tafi Ai’sa bata dawo cikin gidan ba.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*MAIDUGURI*
“What!!!! Kasan kuwa mai kake faɗa min kana nufin sun tsira karka cemin sun isa cikin ƙauyen nan.!!”
Daga can Jamo yace.
” Ehh sun tsira gaskiya, nayi duk yanda zanyi dan ganin basu kwana a duniya ba, amma abun yafi ƙarfi na, saboda Yaron yana da mungun wayo.”
Tsuka Jummai taja tare da kashe wayar kanta ta dafe zuciyarta sai famar tsinkewa take, a fili ta furta.
” Ina bazai yiwu ba, bazan bari YAMURAM ta dawo cikin hankalinta ba, dole sai ta bar numfashi a duniya dole ne ma, zanje wajen Malam gobe, idan har ya tabbatar min zata sami lafiya ni kuwa sai nasa an bita har cikin ƙauyen an Kaita lahira.”
Ta ƙarasa maganar tana huci, sai kuma taja tsaki tare da kwanciya cikin tashin hankali.
*UNIMAID*
A matuƙar gajiye suka fito daga lectures ɗin Maji ne ta dubi Falmata tare da cewa.
” Muje Capteria yunwa nake ji sosai wallahi, tun abinci safe kinga yanzu har 3:40.”
Juyawa sukayi suka nufi Capteria suna taɗi, waje suka samu suka zauna Maji ta dubi Falmata tace.
” Me za’a kawo miki, ni jalop nake bukata.”?
Numfashi Falmata ta sauƙe tare da cewa.
” Babu abinda zanci ruwa kawai nake buƙata nasha magani.”
Kallon ta Maji tayi tare da cewa.
” Me kikaci da zakice kin ƙoshi, Wai Falmata na lura tun ɗazu lectures ɗin da ake babu rabin hankalin ki a kansa, duk rabi ya tafi ne a tunanin mutumin da baisan darajar ki ba, a rayuwarsa ki dawo hankalin ki, ki manta da wani Hassan a cikin rayuwarki, domin kuwa shi ya juma da mantaki tunda harya sakeki dan haka ki daina ɓata lokacin wajen tunanin mutumin daya manta ki a duniyar sa, yanzu dan baki da hankali ke sai kisha magani ba tare da kinci abinci ba.”
Murmushi mai ciwo Falmata tayi tare da cewa.
” Bazaki taɓa fahimtar irin Soyayyar da nake yiwa DOCTOR bane, da ana iya cire Soyayya da ƙarfi a cikin zuciya dana cire Soyayyar DOCTOR daga cikin raina, sai dai hakan bazai yiwu ba, saboda bani nake da iko da zuciyata ba, ni kaina nasan bana cikin zuciyar DOCTOR, sai dai ina mamakin yanda ni kuma yake maƙale a cikin zuciyata, kullum Soyayyar sa ƙaruwa take a zuciyata maimakon ta ragu, lissafi na yakan ƙauce min a duk sanda na gansa ina son mijina Maji bazan iya doguwar rayuwa babu shiba, taya zanyi DOCTOR ya dawo gareni, ki taya ni neman hanyar da zan koma gidan mijina ƙawata pls.”
Tunda ta fara Maganar maji take kallon ta cike da haushin ta, tsuka taja tare da cewa.
” Wai ke Falmata meyasa shashasha ce ke a cikin Soyayya, meyasa kike ƙaunar mutumin da baya ƙaunar ki, meyasa kike son mutumin daya Raina iyayenki, shin kishin iyayen kine bakya yi, ko kuma kinfi sonsa ne sama da iyayen ki, wallahi Falmata ina jin haushin zuciyarki, da ana bada aron zuciya dana baki aron tawa ko Allah zaisa ki cire Soyayyar wannan ɗan iskan azzalumi wanda bashi da imani bare kuma tausayi, Falmata idan har nine kike tunanin zan share miki hanyar da zaki koma gidan Hassan to ki saka a ranki kin rasa sa kenan har abada, domin kuwa na gwammace na ɗebo ƙayoyi na watsa a hanyar domin ki rasa wajen takawa bare kuma ki shiga.”
A fusace Falmata ta miƙe tsaye cikin ɓacin rai tace.
” Maji ya isa haka ki daina zagin DOCTOR, kina ƙona min zuciyata ne idan kina aibata sa, Maji, wallahi komai tsinin ƙayar dake Hanyar gidan DOCTOR zan juri takata domin ta isar dani har cikin gidan sa, na faɗa miki zuciyata bazata taɓa iya doguwar Rayuwa babu DOCTOR a tare dani ba.”
Kaɗa kanta maji tayi tare da cewa.
” Lallai kina cikin masifa da jarabawa…………………”
Ki biya ki karanta yar uwa, 0006064512 Rashida Usman Jaiz Bank ko kuma mtn card na 300 sannan ki turo shaidar biyan ki, yafi miki sauƙi akan a baki wanda ba gumin kiba
Alƙalamin UMMU NASMAH CE
[9/11, 4:27 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN*
_______✍🏻 ” Meyasa zakice ina cikin masifa bayan kinsan Soyayyar DOCTOR da ita aka halicce Ni, na Tabbata Ubangiji bazai ɗaura min masifa ba, Maji meyasa bakya fahimtar irin Soyayyar da nake yiwa DOCTOR, kece wacce ya kamata kifi kowa yiwa soyayyata uzuri amma kin kasa Numfashi nane DOCTOR taya kike tunanin ɗan Adam zai iya rayuwa babu numfashi.”?
Ta ƙarasa maganar cikin raunin murna, ajiyar zuciya Maji ta sauƙe tare da cewa.
“Lallai kuwa kina hanyar mutuwa idan har Hassan shine numfashin ki, Allah bai halitta miki Soyayyar sa ba, kece dai kika halitta wa kanki, wai ma shin na tambayeki soyayya hauka ce kam.?”
” Ƙwarai kuwa Soyayya hauka ce abu ɗaya suke tafiya dashi, wani lokacin ma gara mahaukaci baya jin zafi a cikin zuciyarsa, dan Allah Maji kiyiwa zuciyata adalci ina son Doctor na fara kasa jure rashin sa, karku bari Soyayyar sa ta kasheni.”
Taɓe bakin ta Maji tayi tace.
” Tabbas idanunki sun makance yayin da kunnuwan ki suka toshe, na Tabbata yanzu bakya ji ba ƙya gani, hanyar da zuciyarki ta ɗauka ita kawai kike bi, hanya mai cike da tarin wahala da ƙalubale, Allah ya fitarki a cikin jarabawar da kika faɗa, ki tashi mu tafi na fasa ma cin abincin.”
Girgiza kanta Falmata tayi tare da runtse idanunta hawaye ne ya gangaro mata ta saka hanu ta gogesu tare da cewa.
” A’a bazan hanaki cikin abincin ki ba saboda damuwa ta, ki zauna kici abinci sai mu tafi karki ƙi cin abinci saboda ni bazan ciba, hakan zai zamo kamar na cutar dake ne.”
” A’a bazan iya ciba saboda kin riga kin cire min sha’awar son cin abincin, bana ƙaunar na ganki cikin damuwa, sai naji nima hankali na yana tashi, ta yaya kike tunanin zan zauna a gaban ki na iya ci na ƙoshi bayan ke cikin ki da yunwa, tashi kawai mu tafi.”
Tashi Falmata tayi suka tafi, har suka fito bakin get babu wanda ya iya cewa ɗan uwansa wani abu a daidaita suka hau, sai yanzu Falmata ta dubi Maji tace.
” Da Soyayya da hauka basu da wani banbanci Maji muddun aka samu saɓani da rashin fahimta cikin Soyayya, SO yakan zautar da mai yinsa ya hanasa bacci ya hanasa ci ya hanasa sha ya kuma hanasa walwala, mafi girman muguntar so shine ya sa maka ciwo, idan akayi rashin dace ma ya kasheka *SO DANGIN MUTUWA* amma idan kikayi dace da masoyin ƙwarai babu abinda ya kai Soyayya daɗi a duniya ji zakiyi duniyar ta miki daɗi, kiji babu komai cikin zuciyarki sai farin ciki da annushuwa, shiyasa ma’abota soyayya suke ƙiranta *ZAƘI DA MAƊACI* sai dai ɗacin nata yafi zaƙin yawa, Maji ina son Doctor sai dai shi baya sona a yanzu, ta wani waje kuma zuciyata ta kasa aminta cewa DOCTOR baya sona, , ya kike tunanin rayuwata zata kasance idan babu DOCTOR a cikin ta, amsa ko ciwo ya kamani ko kuma na mutu, muddun bai dawo cikin rayuwata ba, ke wacce makoma kike hango min anya kuwa ina da hanyar da zata ɓulle min.”?
Shuru Maji tayi tana kallon Falmata cike da tausayin ta, tace.
” Ai ba sai na hango miki makomarki ba, tunda kin riga kin hangowa kanki, sai dai abu ɗaya nake son na sanar dake, idan kin mutu ko kin kwanta ciwo Hassan ba zai fasa Rayuwar sa ba, ƙarshe ma dai Auren sa zaiyi ya manta da an taɓa halittar ki a duniya saboda babu komai tsakanin ku, ma’ana baku haihu tare ba, dan haka ina ƙara faɗa miki ki dawo hankalin ki.”
Shuru Falmata tayi tare da runtse idanunta, ita dai tasan tana son Doctor har yanzu zuciyarta ta kasa yadda cewa DOCTOR baya sonta, ajiyar zuciya ta sauƙe, duk sukayi shuru har mai adaidaitan ya iso ƙofar gidan su Falmata, fita tayi Maji dubanta tayi tace.
” Sai na shigo.”
Da to Falmata ta amsa sannan ta juya zata shiga cikin gidan, HABEEB ta gani tsaye jikin motar sa yasha ɗanyar shadda voyal ya zuba hannayensa cikin aljihu, fuskar sa ɗauke da murmushi ga sanjen daya kwanta luf luf a fuskar tasa gwanin ban sha’awa, haka gashin kansa ma yake sheƙi, Tabbas Allah ya yiwa HABEEB halittar kyau, tamkar bafulatani haka yake, Falmata haɗa fuska tayi tare da ɗaga kanta zata shige tamkar bata gansa ba.
” Ba halinki bane wulaƙanta ɗan Adam, ki juyo ki saurareni tunda nasan kin ganni, idan kuma kika wuce to Tabbas sai na biyoki har cikin gidan kin san dai gidan ba baƙo na bane ko.”
Cak Falmata ta tsaya tana sauraron Maganar sa, ranta ɓace ta juyo tare da cewa.
” Ko ka manta ina da Aure ne, kake ƙoƙarin tsayar dani wai menene hujjar kane ta shiga Rayuwata.”?
Murmushi HABEEB ya saki yace.
” Ya mayar da Auren naki kenan bayan ya sakeki shekaran jiya, kikace meye hujja ta ta shigo Rayuwar ki ko? To da hujja kuwa na shigo rayuwarki tunda ina da labarin sakinki da wannan lusarin mijin naki yayi.”
Ƙanƙance ido Falmata tayi tare da kusanto HABEEB tace.
” Karka ƙara kira min sunan miji da lusari, domin kuwa shiba lusari bane, sannan ka adana hujjar ka domin kuwa daf nake da komawa gidan mijina, ko ka manta banyi iddaba to ka shiga nutsuwar ka, domin kuwa ina son mijina.”
Dariya sosai HABEEB yayi yana karewa Falmata kallo kafin ya ce.
” To Shikenan bari muga zuwa nan da ki gama iddar ko zai maida ki ɗakin naki, sai dai fa ki sani, shifa wannan lusarin mijin naki, Ba wai yana da cikakken hankali bane domin kuwa duk namiji mai cikakken hankali bazai yi kuskuren rabuwa dake ba, Karki manta da cewa har GOBE HABEEB na sonki😉.”
Yana gama faɗin haka ya juya ya shige cikin motar sa yana kanne mata ido shuru Falmata tayi ta jima tana tsaye tana nazarin maganganun HABEEB, tambayar da bata da amsar sa take yiwa kanta, shin meyasa kowa yake faɗar Magana marar daɗi akan DOCTOR, meyasa suka kasa fahimtar DOCTOR mutumin kirki ne.? Rasa amsar tambayar ta yasa ta shigewa cikin gida tana jinjinawa Maganar HABEEB.
” HABEEB wai meyasa ka kasa cire yarinyar nan a zuciyar ka, kana ta dakon Soyayyar banza, ganan Yan mata da yawa ƴaƴan manya suna binka suna cewa sonka suke meyasa bazaka zaɓi ɗaya a ciki ba? ka manta da wannan yarinyar domin kuwa ba sonka take ba.”
Murmushi HABEEB ya saki yana kallon SADIQ yace.
” Bazaka fahimci girman son da nake mata bane shiyasa kake kiran na rabu da ita, a yanzu ina da ƙwarin gwiwwar cewa zan sami FALMATA a matsayin matar Aure na, na Tabbata ƙaddarar Aure na ne ya fito da ita daga gidan DR HASSAN.”
Numfashi SADIQ ya sauƙe yace.
” To ikon Allah, amma kana tunanin iyayen ka zasu yarje maka ka Auri BAZAWARA a matsayin ka na saurayi wanda bai taɓa yin Aure ba.?”
Ya jefa masa tambayar yana duban action ɗin HABEEB mai makon yaga firgita daga fuskar HABEEB sai murmushi ya gani kwance cike da nutsuwa HABEEB ya basa amsa.
” Duk abinda nake so shi iyayena suke so, muddun ba abinda ya kaucewa Shari’a bane, bare kuma sun san girman son da nake yiwa Falmata, bani da matsala da iyayena domin kuwa a kullum sukan fahimce ni, matsala ɗaya ce kawai take gabana yanda zan ƙwace zuciyar Falmata daga hanun Dr Hassan.”
Murmushi SADIQ ya saki tare da cewa.
” Wannan abu ne mai sauƙi, zaka iya ƙwace zuciyarta ta hanyar ƙyautata mata da kuma iyayen ta, domin kuwa ko wani rai yana son mai kyautata masa, sannan ka kasance mai yawan bata kulawa da kuma jure duk wani fushin ta a kanka kar ka bari zuciyarka tayi saurin sarewa Saboda tafi son Dr akanka, ka jure har ka samu cikar burinka, ina Tabbatar maka Abokina idan kayi haka ka gama samun zuciyarta.”
” SADIQ zanbi dukkan shawarar ka, koda kuwa zan zama bawan ta ne, ina sonta Soyayyar da ban taɓa yiwa wata ƴa mace ba, Soyayyar gaskiya nake mata, SADIQ da Allah zai mallaka min Falmata a matsayin matar Aure na, na Tabbata zan bata cikakkiyar kulawar da zata manta da meye damuwa a duniya, ka sani cikin adduar ka Allah ya cika min buri na.”
Dariya SADIQ yayi yana bawa HABEEB hanu suka tafa yace.
” Abokina insha Allah nasara tana tare da kai, yanzu ne zamu nunawa Dr Hassan, ya kuskure daya saki Falmata, tunda ya kasa fahimtar cewa mace kamar Falmata ADANA su ake a waje mai tsafta ba’a sakaci dasu domin kuwa kana tsayawa kallon ruwa ƙwaɗo zai maka ƙafa sai dai ka wayi gari cikin nadama da cizon yatsa.”
Dariya HABEEB yayi suka ci-gaba da taɗi har HABEEB ya sauƙe SADIQ a Companyn sa, sannan shima ya shige nasa Companyn.
***********
” Garin yaya haka ta faru Jummai, ya akayi ya sake har suka kufce masa, amma wannan akwai jakin yaro, yanzu kinsan kuwa girman tashin hankalin da yake tunkaro mu, YAMURAM itace kawai tasan cewa nine na ɓatar da mijinta da ƴarta Saboda JALILA ta sanar da ita ta waya ba tare da na sani ba, sannan ta kamani ido da ido kunne da kunne ina waya cewa a kashe su sannan tasan da dukiyar da muka ƙwata a hanun mijinta muka kai ɗan mu MAHMUD ƙasar waje karatu, me kike tunanin zai faru idan har YAMURAM ta dawo cikin hankalinta.?”
Yana huci cike da tashin hankali yake Maganar Jummai ita kanta a cikin tashin hankalin take amma sai ta dake ta cewa Kawu Dauda.
” Ni kaina ina ciki wannan tashin, amma ina tabbacin YAMURAM bazata taɓa dawowa cikin hankalin ta ba, muddun BOKAYE basu ƙare a duniya ba, idan kuwa abun ya gagara zan iya sawa aje har can garin a kasheta, ko ta halin yaya nayi alƙawarin YAMURAM bazata taɓa samun lafiya, dole a haka zata gama rayuwarta, sannan zan kira AJABO na basa Umarnin kawai a kashe su, dan haka ka kwantar da hankalinka.”
” Hankali na bazai taɓa kwanciya ba muddun banga bayan YAMURAM ba dan haka ki tabbatar kin sama mana mafita.”
Ajiyar zuciya Jummai ta sauƙe tare da tashi ta fita daga cikin ɗakin shima Kawu Dauda ficewa yayi daga gidan gabaki ɗaya.
***************
*BINISHED*
MALAM GANA ne sunkuye akan UMMA sai famar karatu yake mata tare da watsa mata wani ruwan rubutu, yana watsa mata ruwan take wani irin miƙewa tare da razana kamar zata tashi sai kuma ta koma ta kwanta, sanda Malam ya gama addu’ar sannan ya ɗauki wani ƙaramin kasko mai cike da garwashi ya zuba garin magani ɗakin ya turniƙe da hayaƙi, wani irin tari Umma take tare da nannaɗewa tamkar macijiya, DOCTOR dake gefe ne ya runtse idanunsa cike da tausayin Umman nasa, sanda Malam ya gama sannan ya dubi DOCTOR yace.
” Yanzu bacci zai ɗauke ta, insha Allah zata sami sauƙi.”
DOCTOR cewa yayi.
” To Malam Allah ya saka da alkairi.”
Da ameen malam ya amsa tare da ficewa, DOCTOR shuru yayi tare da tare da zuba tagumi, yayi shuru yana tunanin duniya, FAƊO MASA TAYI A RANSA take Zuciyarsa ya tsinke a fili ya furta ” Wani hali take ciki na Tabbata bata cikin kwanciyar hankali” wayarsa ya ciro tare da buɗe gallary ɗinsa picture ɗinta ya buɗe, tana zaune saman kujera tana dariya ya mata picture ɗin, murmushi mai haɗe da ɓacin rai yayi tare da furta ” _*KI GAFARCE NI FALMATA BAN RABU DAKE DON BANA SONKI BA, NA RABU DAKE NE SABODA GIRMAN LAIFIN IYAYEN KI, BAZAN IYA RAYUWA INA ƘASƘANTAR DA IYAYENKI NA TABBATA BAZAKI JI DAƊI BA, BAZAN TAƁA IYA FARANTA MIKI BA, SABODA INA GANIN TAMKAR NA FARANTAWA IYAYENKI NE, NA RUBU DAKE NE SABODA BANA JIN DAƊI A RAINA INA WULAƘANTA KI, GARA NA RABU DAKE A TUNANI NA HAKAN SHINE SAMUN SAUƘI NA DA KUMA KE DALILIN KENAN DA YASA NA RABU DAKE*_ sai dai yanzu na fara jin kewar rabuwa dake, amma zuciyata bazata iya jure zama dake ba, ina sonki kamar yadda kike sona, amma Soyayyar iyayena tafi ƙarfi fiye da Soyayyar da nake miki, *ƘADDARA TA FAƊA TSAKANIN MU DOLE YASA ZAMU HAƘURA DA JUNA SABODA ZUCIYATA CIKE TAKE DA WUTAR FANSAR IYAYENA*”
Ya ƙarasa maganar hawaye na gudu a saman fuskar sa, hanu yasa ya goge tare da kwantar da kansa jikin Umma ya fara magana tamkar Umma tana jinsa.
” Umma na, kece kika cemin nayi dacen mace ta gari, kince ko da wasa karna kuskura na rabu da ita, sai dai kuma abinda baki sani iyayenta mugaye ne suna sukayi silar lalacewar farin cikin mu suka tarwatsa mana family saboda mungun nufin su, Umma na rabu da Falmata Saboda bazan iya rayuwa da jinin BABA BUKKAR, ina son matata Umma na kasa jure haƙurin rasa ta, umma meyasa iyayenta suka kasance azzalumai suka shiga tsakanin mu ki bani Amsa Umma kinyi shuru.”
Ya ƙarasa maganar hawaye na gudu saman idanunsa Yana kuma laɓe jikin Umma da bata san me yake faɗi ba, saboda bata cikin hankalinta………………..
Ki biya kuɗin ki Yar Uwa karki karanta abinda ba gumin ki, ni bazan ja miki Allah ya isa ba, amma idan kinyi daidai kin sani 300 kawai zaki biya ta wannan account ɗin 0006064512 Rashida Usman Jaiz Bank ko katin waya na mtn ta wannan numbern 08147537180 sannan ki turo shaidar biyanki ta ita numbern.
Ummu Nasmah ce ✍🏻
[9/12, 10:39 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 35 to 36*
__________✍🏻 HAJJO dake zaune gefe tana sauraran sambatun DOCTOR ne, cike da tausayin sa ta ce masa.
” Hassan ai ka riga da kayi kuskuren saurin rabuwa da Falmata mace ta gari wacce samun irin ta a yanzu yake matuƙar wahala, Akan me zaka ɗaura laifin wani akan wani, bai kamata ba sabida kuskuren iyayenta , ka hukunta ta da son zuciyarka, yarinyar nan tana sonka Kuma kaima kana sonta meyasa zaka wahalar da zuciyoyin ku, ka duba magana ta Hassan kayi gaggawar maida Auren ka da matar ka, tun kafin lokaci ya ƙure MAKA.”
Girgiza kansa DOCTOR yayi yana goge hawayen fuskarsa yace.
” Aunty Hajjo bazan iya zama da Falmata ba, Saboda idan ina kyautata mata gani nake tamkar iyayenta nake kyautatawa, duk abinda zan faɗa miki ba lallai ki fahimce ni ba, kawai Maganar gaskiya babu Maganar ƙara wani tsakanina da Falmata, zan jurewa zuciyata na cire Soyayyar ta a cikin zuciyata, Allah ya haɗa kowa da rabonsa.”
Taɓe bakinta Hajjo tayi tace.
” To kuwa in dai hakane ƙarya kake baka sonta, muddun kana sonta zaka yiwa rayuwarta uzuri, wannan damuwar daka shiga ta ƙarya ce.”
Ko Kafin DOCTOR yayi magana ta shigo Babu sallama ta faɗo cikin ɗakin bakin ta a ture ta dangwarar da ƙwaryar Abincin da MAMA ta bata ta kawo musu, bata ko kalli inda suke ba, ta juya zata fice, Doctor Kuwa tunda ta shigo ya ɗaga kansa yana binta da kallon tsana da ƙyama harta ajiye abincin zata juya, cikin tsiwa yace mata.
” Ke jakar ƙauye, arna ne mu da zaki shigo mana babu sallama wawiya jahila, marar lissafi.”
Jahila Ai’sa ta maimaita kalmar a cikin ranta, kalmar da tafi tsana kenan a rayuwarta shiyasa ta dage da karatun boko tunda dama akwai makaranta guda ɗaya tak a cikin ƙauyen nasu mai haɗe da primary And secondary school ta government, juyowa tayi ranta a ɓace tace masa.
” Da kai da arne aini duk abu ɗaya nake ɗaukarka, gara ma arne wataƙil na iya masa kara koda gafara dai, ya kamata ka sakar min mara nayi fitsari kana shiga Rayuwata da yawa fa jakin Birni.”
Hajjo da kallon mamaki take bin Ai’sa da ita domin kuwa ita tunda take bata taɓa ganin tacacciyar marar kunya irinta ba girgiza kanta kawai tayi tare da nema mata shiriya wajen Ubangiji.
A matuƙar harzuƙe da ɓacin rai DOCTOR ya miƙe ya yiwo Kanta dan yaga idan ba karya yarinyar nan yayi ba, bazata daina rainasa ba, ganin ya taso ya saka Ai’sa ficewa da gudu tana cewa.
” Kuji gardin banza dai, sai na tsaya ƙaton gardi irinka ya jibgeni.”
Ƙwafa DOCTOR yayi tare da komawa ya zauna cike da munguwar tsanar ta, ya washi yarinyar ji yake tamkar ya kasheta yake ji, yana nan zaune cikin wannan ɓacin rai FANTA ta shigo da Sallama a nutse ta sunkuya ta ajiye kofin da ta shigo dashi tace masa.
” Sannu da hutawa, ya mai jikin.?”
Hajjo ce ta amsa da yauwa.
Ɗago kansa DOCTOR yayi ya kalleta kamar su ɗaya da AI’SA sai dai ita wannan baƙa ce sannan suna da bambancin hali da AI’SA
” Da sauƙi’ ya bata amsa a taƙaice zuciyarsa rabi na ga tunanin Falmata rabi Kuma tana wajen, FANTA cewa tayi.
” Gashi Malam ne yace na kawo maki waɗannan kofin guda biyu yace wannan shayi ne a ciki idan ta farka ki bata akwai magani cikin shayin wannan Kuma ruwan rubutu ne, wai shi kuma fuskarta za’a dinga wanke mata dashi” wani ƙullin leda ta miƙawa Hajjo ta karɓa ta cigaba da cewa.
” Shi wannan Garin maganin a ƙwarya zaki saka ruwa ki rufe ya kwana washe gari da sassafe ki buɗe sai ki zuba garin maganin cikin ruwan yace idan kinsa karki juya ruwan da hanu a nemi kara sai a juya dashi, sannan ki bata tasha.”
Ta ƙarasa maganar da cewa “kin gane bayanin.”
Ɗaga kanta Hajjo tayi tace.
” Ehh na gane, mun gode.”
Tashi Fanta tayi ta fice tare da musu sai da safe, Hajjo ne ta dubi DOCTOR tace.
” Yarinya mai hankali da nutsuwa ba kamar Yar uwarta ba, amm Hassan abinda zan faɗa maka ko, dan Allah ka fita a harkar yarinyar kaga ba kunya gareta ba.”
Tsuka DOCTOR yaja tare da cewa.
” Ai Wallahi Aunty Hajjo bazan bar garin nan ba sai na targaɗa yarinyar nan, sai nayi maganin tashin Kunyar ta, yarin………….”
Ringing ɗin wayarsa shiya hanasa ƙarasa maganar, duba wayar yayi yaga SAIF ɗagawa yayi tare da karawa a kunnen sa yace.
” Abokina ya akayi.”
DOCTOR SAIF cike da ɓacin rai yace.
” Komai ma anyi, yanzu DOCTOR duk yanda na kai ga taroka sai da ka ɓalle, kana tunanin abinda ka aikata shine daidai a gareka.!!!?”
DOCTOR cike da rashin fahimtar Maganar SAIF yace.
” Ban fahimce ka ba, meya faru me kuma nayi.?”
” Yanzu na haɗu da Maji, a unguwar BULUNKUTU AIRPORT, tana kallona ta sanja fuska zata shige, shine na tare ta, take sanar dani cewa ka Saki Falmata, Wallahi wallahi wallahi ka yiwa kanka babbar illar da bazaka fahimci hakan ba, sai nan gaba, sai dai kana dama ɗaya yanzu a hanunka, shine kayi gaggawar mayar da Auren ka, idan ba haka ba kuma hmmm zaka gane kurenka.”
” Mtsss!!! Aikin banza ni nayi zaton ma wani abin nayi, dama akan wannan ƙaramar Maganar ce ka ke wannan sambatun, to ai bari kaji bazan taɓa gane kuskukurena ba akan Falmata tunda ba kuskuren nayi ba, SAIF kafa san yanda nake son Falmata, kuma harna iya rabuwa da ita, ai kaima kasan Abinda ya koro ɓera daga rami Tabbas yafi wuta zafi, dan haka kama daina zancen na dawo da Falmata gida na, har abada bazan taɓa dawo da Ita ba.”
” Hmmm!!! Ƙarya kake Hassan baka son FALMATA domin ka juma kana cutar da ita, kayi mata ƙaryar tana da matsalar mahaifa alhakin family planing kake bata a ɓoye take sha cikin jus, daga karshe ka sanjawa maganin waje ma’ana ka juyesu a wata kwalba, ka koma bata su a matsayin maganin matsalar mahaifa, take shansu a cikin rashin sani, ka faɗa min ina soyayya ga mutumin da yake cutar da rayuwarka, ina tuna maka wannan maganar ne saboda ka hankalta ka dawo cikin hankalinka ka gyara kurakuren ka, kafin Falmata ta juya Soyayyar da take maka daga Soyayya zuwa tsana, shawara na baka wala ka ɗauka wala karka ɗauka, Ruwan kane, amma dai bazaka ce ban faɗa maka gaskiya ba.”
” Ya isa haka SAIF ka daina kiran planing ɗin da na yiwa Falmata a matsayin ƙiyayya, domin kuwa haihuwa ce ban shirya mata ba, yanzu dalilin kenan da yasa na mata planing AMMA ba wai dan bana sonta ba, duk wani namijin da zai so Falmata a baya nane, dan haka ka daina kiran bana sonta, maganar dai saki ne ko, to na saketa kuma bazan taɓa dawo da Ita ba, kuma ka sani ba wai sakin ta da nayi shi yake nufin na ƙyale azzaluman iyayen ta ba, a’a suma ina nan dawowa kansu, yanzu lafiyar Umma nane a gabana tukunna.”
DOCTOR SAIF tsuka yaja tare da taɓe bakin sa ya ce.
” Okay ka cigaba da abinda kake karka fasa amma ka sani akwai ranar ƙin dillanci ranar da hajar mai gari ta ɓata, a ranar zaka tuno da masoyanka na gaskiya waɗanda suke ɗaura ka a kan hanya, yanzu zuciyarka ce take maka mummunan huɗuba wacce zata kaika ta baro ka.”
” Zuciyata bazata taɓa kaini ta baro ni ba SAIF saboda akan daidai take, kune kuka kasa fahimtar haka, ka sani yanda na bar nonon uwata haka na bar Aure da Falmata har abada, abinda yasa ban mata saki Uku ba lokaci guda Saboda Haramun ne, shiyasa, kowa yaje yayi rayuwarsa yayi hakuri da ciwon zuciyarsa, a hankali zata warke har kowa ya manta da yayi Rayuwa da ɗan uwansa………….”
Jiya kunmin korafi cewa na ƙara muku yawan page sai dai bazaku fahimci wahalar typing bane shiyasa, amma kuyi insha Allah zan ƙara muku🥰🥰🥰🥰🥰 INA SONKU MASOYA NA.
*0006064512 Rashida Usman Jaiz Bank 300 only ko mtn card ta wannan layin 08147537180 sannan ki turo shaidar biya ta ita numbern, yafi miki sauƙi akan a turo miki abinda ba gumin ki ba, ki karanta..*
Masu turo Vtu pls ku daina numbobin katin kawai nake buƙata ba vtu ba.
*Ummu Nasmah ce✍🏻*
[9/14, 10:21 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 37 to 38*
________✍🏻 Doctor Saif kashe wayarsa yayi cike da ɓacin ran abokinsa, layin wayar Falmata ya kira, Falmata dake zaune gefen Hajja suna cin dafaffiyar gyaɗa ne ta ji ƙarar wayar ta dubawa tayi taga SAIFUDDEEN hanu tasa cike da nutsuwa ta ɗaga kiran tare da Sallama, amsa sallamar yayi yace.
” Falmata, ashe abinda ya faru tsakanin ki da Abokina kenan har abun ya kaiku ga rabuwa gaskiya banji daɗin wannan lamarin ba rai na ya ɓaci sosai.?”
Kallon Hajja dake gefen ta tayi tare da tashi daga kusa da Hajja gudun masifar Hajja, Cikin ɗakin Hajja tayi tare da zama tace.
” Eh SAIF abokinka yaci amanata ko a mafarki ban taɓa zato ko tsammanin cewa zai juyawa soyayyata baya ba, sai gashi lokaci ɗaya ya cire ni a cikin rayuwarsa, ni ba wannan bane ma yake damuna yanda DOCTOR ya raina iyayena, baya ganin mutuncin su, yana zargin sa akan abinda bayi da tabbacin sun aikata, SAIF koda iyayena sun aikata abinda yake zargin su dashi, ya dace kenan DOCTOR ya juya min baya, ni meye laifi na a ciki, hmmm ba komai duk sanda na yanki jiki na faɗi na mutu shi kuma Ranar sai ya shiryawa rayuwar duniya ya kuma yi walima ya kashe ni ya huta tunda na kasa cire Soyayyar sa a cikin zuciyata, mtss hmmm abin takaicin na kasa ciresa a cikin raina kullum sonsa ƙara ƙarfi yake a cikin zuciyata.”
” Kiyi hkr Falmata ki sawa Zuciyarki hkr ki dage da addu’a insha Allah zaki koma gidan mijinki, shima yana sonki har yanzu, kawai saɓanin tunani aka samu wanda Zafin zuciyarsa tasa ya yanke ɗanyen hukunci kinsan halin DOCTOR inda zuciyarsa ta rufe baya jin dukkan abinda za’a faɗa masa, amma ba wai dan baya sonki ba, dan Allah kiyi hkr ki masa uzuri komai zai wuce nan bada jumawa ba, zanyi ƙoƙarin ganin komai ya daidaita tsakanin ku.”
” Saif a yanzu na fara tunanin DOCTOR baya sona, na fara tunanin ciresa a cikin raina koda kuwa hakan yana nufin mutuwa tace.”
” A’a Falmata karkiyi haka dan Allah ki bani lokaci domin ganin na gyara tsakanin ku, kiyi hkr dan Allah.”
” Shikenan SAIF na gode da kulawar ka gareni ka gaishe da Aunty FAUZA.”
Da zataji ya furta tare da katse wayar, Falmata sosai taji daɗin yanda DOCTOR SAIF ya nuna mata kulawar sa gare ta, waje ta koma wajen Hajja ta zauna a lokacin har Aunty YANA ma ta fito ta zauna, hanu Falmata tasa zata ɗauki gyaɗar, Hajja ta bige mata hanu tace.
” Ajiye min gyaɗa ta marar zuciyar banza yaro yana gwada miki tsana ke kuma sai famar binsa kike a gindi kamar ubanki, to da kika gudu kikayi wayar a ɗaki saboda kar naji to na biki naji duk abinda kuka tattauna, ke dai kinji kunya wallahi marar zuciya wacce bata kishin kanta ke ko ɗan jan ajin nan irin na mata baki da wawiya kawai.”
Tura bakinta Falmata tayi gaba, tace.
” Laɓe fa kika min kenan Hajja kuma kin san ba kyau laɓe, nifa Hajja ina son mijina, kawai kisan yanda za’ayi na koma ɗaki na ni bazan iya rayuwa ba DOCTOR b………..”
Bata ƙarasa maganar ba taji Aunty YANA ta bige bakin ta da ƙarfi, cike da azaba Falmata ta riƙe bakin idanunta na ƙoƙarin ciko da Hawaye, Aunty YANA cewa tayi.
” Wallahi ƙarya kike baki isa ba, muddun ina numfashi bazaki taɓa komawa gidan wannan ɗan iskan Yaron ba, sai dai kuma idan mutuwa nayi, gara ma tun wuri ki fitar dashi a ranki, dan wallahi da ki koma gidan sa gara ace min kin mutu zanfi jin nutsuwa naga gawarki a gabana a kaiki cikin kabarin ki, da ace min cikin gidan Hassan za’a kaiki, ke Falmata kinsan irin rainin da yaron nan yamin kuwa mutumin da yace sai wurgar dani ƙasa koya targaɗa ni mutumin da yake zagin iyaeyenki, shine kike kiran zaki koma wajen sa sam bazai taɓa yiwuwa ba muddun kuwa ina numfashi zanga wa zaki zaɓa Ni Ko shi .”
Falmata Hawaye ne ya ciko mata a idanu cike da tsoron maganganun Aunty YANA, cikin raurau da murya tace.
” Amma wani abinda yake faruwa harda laifin ki meyasa kike zuwa wajen boka ko shima dole zaisa a zargeki, ban taɓa ƙaryata cewa da hanunki wajen faruwar wannan lamari ba sabida kina zuwa wajen bokan tunda nima shaidar kina zuwa ne, ni kaina kinsha kaimin laya da wasu abubuwan na BOKAYE nace miki bazanyi ba, ta ya baza’a zargeki ba ki faɗa min mama.”
Murmushin takaici Aunty YANA tayi, tana girgiza kanta tace.
” Oho fito sarari kice kema kina zargina da ɓatar da Uban mijinki da kuma sawa Uwar mijinki ciwo ki fito ki sanar dani ba sai kinyi kewaye kewaye ba, to buɗe kunnenki kiji da kyau, ni ɗin nan da kika gani ba mace bane mai shiga bokaye sai a sanadin ki, saboda tsantsar wahalar da kike sha a gidan Auren ki yasa na fara zuwa wajen BOKAYE domin samo miki farin ciki, Kuma nan ma ban fara zuwa ba sai da naga wahalar da kike sha tayi yawa, Kuma nabi dukkan wani mataki domin ganin Hassan ya rage miki wasu abubuwan amma hakan bai yiwu ba, sai ma zagi da rashin kunyar da mijinki yake mana nida mahaifinki, hakan yasa na tunzura naje wajen, Ƙawata tace min naje wajen wannan bokan, idan har yayi miki aiki akan Hassan bazai taɓa wulaƙanta ki ba, zaki samu farin ciki, ƙwaɗayin na sama miki jin daɗi a gidan mijinki yasa na amince da shawarar ta, dalilin kenan da na fara shiga boka kuma ban taɓa kai sunan wani ba, ni dai kawai burina farin cikin gidan ki ya dawo, meye laifina neman gyara Aure da ne sunnah ta Annabi ba zuwa nayi a yiwa wani mugunta ba, ga nan Hajja tunda ta fuskanci ina bin bokaye ta kira ni tamin faɗa Ranar da tayi case da Hassan a kanki harta mareshii, tunda tamin faɗa ban kara tunkarar wannan bokan ba, hatta AZUMI da ta sani a wannan hanyar na rabu da ita, Allah Sarki ashe ina can ina wahalar sama miki farin ciki ke kuma kina nan kina min mungun zato, ba damuwa Falmata na gode na fuskanci ke kinfi buƙatar farin cikin ki fiye da farin cikina.”
Aunty YANA ta ƙarasa maganar hawaye na zubo mata, sosai jikin Falmata yayi sanyi tayi shiru ta kasa Magana Hajja ce tace.
” Tabbas gaskiya ne maganar mahaifiyarki, taso shiga cikin hallaka ne saboda sama miki farin ciki a gidan Auren ki, ki sani Fatuma babu wata Uwar da zata ji daɗi ace ƴarta tana cikin damuwa da rashin kwanciyar hankali a gidan ta, dole sai wannan uwar taji babu daɗi a cikin zuciyarta saboda ita uwa tafi buƙatar farin cikin ƴarta fiye da nata farin cikin idan ɗa yana cikin jin daɗi to ita ko tana cikin wahala ne bazata ji zafi ba, ni nan nice na yiwa Yana faɗa, Kuma ta ɗauka ta daina, amma shine ke yanzu kika zaɓi mijinki fiye da farin cikin mahaifiyarki, har kika yarda da shirmen sa na zargin su da yake, dama ashe akwai Soyayyar da zaki yiwa wani mutum daban bayan iyayenki mutumin daya wulaƙanta ki ya wulaƙanta iyayenki shine abin so a wajen ki saboda rashin sanin darajar kanki, to ki sani idan ke kin haukace baki san ciwon kanki ba, to mu bamu haukace ba da hankalin mu, dan haka ni Hajja nace babu ke babu komawa gidan Hassan har abada, kinsan dai idan na yanke hukunci a cikin gidan nan ya yanku ko, dan haka idan zaki cire wannan Soyayyar banzar ki cire idan ba haka ba kuma ki sawa kanki cuta wannan Damuwar kine.”
Shuru Falmata tayi Hawaye na gudu saman fuskar ta, hanun Aunty YANA ta kama cikin kuka tace.
” Kiyi hkr Mama ban fuskance ki bane shiyasa na yanke miki hukunci a bisa rashin sani wallahi Mama ban san DOCTOR yana zagin ku ba, na miki alƙawari Mama zan cire shi a Raina kema ki taimakeni da addu’a, insha Allah duk wani umarninki zanbi , Amma dan Allah Mama karki kuma zuwa wajen boka babu kyau Mama haramun ne zaki ɓata sallarki mama ki ɓata Addinin ki Saboda neman duniya gara ki dage da addu’a sai Ubangiji ya jiɓanci lamuran ki.”
Murmushi Aunty YANA tayi hawaye yana zuba daga idanunta ta rungume ƴarta tace.
” Insha Allah bazan kuma zuwa ba, kuma insha Allah komai naki zai daidaita Allah zai jiɓanci lamuran ki, Allah ya miki albarka.”
Murmushi Hajja tayi ta amsa da ameen Falmata gyaɗar ta ɗauka tare da cewa zan Hajja
“yanzu zan iya cin gyaɗar ko?”
Dariya Hajja tayi tare da cewa.
” Ehh zaki iya ci ja’ira kawai”
Ta ƙarasa maganar tana zungurin goshin Falmata gabaki ɗayan su dariya sukayi har Aunty YANA.
**************
Washe gari da misalin ƙarfe 12 na rana Jummai ce sunkuye take gaban wani ƙaton boka, baƙiƙƙirin mai munin gaske, tace.
” Allah ya taimaki boka na dawo ne akan Maganar ƙanwar mijina wacce ka kwantar mana da ita jinya, yanzu haka boka muna cikin tashin hankali domin………..”
Dakatar da ita bokan yayi tare da cewa.
” Tana BINISHED ko an Kaita wajen wani malami me magani dariya ya sheƙe dashi yace, ke kuma kinzo kine saboda bakya so ta sami lafiya, to zoki gani.”
Ƙwarya ya buɗe mai cike da ruwa shafa ruwan yayi sai kuwa ga hoton UMMAN DOCTOR ya bayyana DOCTOR na gefenta Hajjo zata bata magani, ƙara shafawa yayi sai hoton ya ɓace kallon Jummai yayi data sake baki tana mamaki yace.
” Bazata samu lafiya, zamu lalata duk wani maganin da zai mata, idan ruwane kuma zamu zubar dashi karki damu.”
Ajiyar Zuciya Jummai ta sauƙa tare da cewa.
” Yauwa kota halin ƙaƙa kar a bari ta samu lafiya, kuɗi ta ɗaga ƙwarya ta ajiye masa kuɗin kasancewar tasan dokar bokan tashi tayi ta fita da baya baya karta fice.
Tirƙashi ƙaƙara ƙaƙa akwai lauje Tabbas cikin naɗi, to wai shin menene ainihin tarihin waɗannan FAMILY ku kasance dani a next page domin mu waiwayi baya.
Ki biya kuɗin ki ta wannan 0006064512 Rashida Usman Jaiz Bank ko katin waya mtn card ta wannan numbern 08147537180 Sai ku turo shaidar biya ta ita numbern 300 ne kacal, yafi miki sauƙi fiye da ki karanta abinda ba gumin ki ba.
*ALƘALAMIN UMMU NASMAH CE*✍🏻
[9/14, 10:22 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 39 to 40*
*DOCTOR HASSAN PAID GROUP FAN’S, GASKIYA INA JIN DAƊIN YANDA KUKE TATTAUNAWA AKAN WANNAN BOOK ƊIN, HAKAN YANA ƘARA MIN ƘARFI GWIWWA SOSAI, JI NAKE INA TYPING CIKIN NISHAƊI, ALLAH SARKI HAR KUN TUNO MIN DA FAN’S ƊINA NA INDO A BIRNI, HAKA SUMA SUKE TATTAUNAWA AKAN BOOK ƊIN NAN, FAN’S ƊINA INA SONKU IRIN SON SON NAN 😘😘😘😘😘😘*
*WAIWAYEN BAYA*
*TUSHEN LABARIN*
________✍🏻 *ALHAJI MAI BULUNKUTU TSALLAKE BULAMA BANA WANBAI* amma asalin sunan sa *HASSAN* ne tsoho ne na arziki wanda al’ummar unguwar suke jin daɗin mulkin sa mutum ne mai tausayi da jin ƙan na ƙasa dashi, cikin gidan MAI BULUNKUTU babban gida ne FAMILY HAUSE wanda ya tara ƴan uwa, Part Part ne a cikin gidan, sai dai sashi biyu daga cikin gidan sunfi zumunci shine sashin ƴaƴan *MAI BULUNKUTU, ALHAJI MALA DA KUMA SASHIN BUKKAR* Hajiya MAIRAMA itace matar mai BULUNKUTU ta lalle, tana da yaran ta Uku MALA shine babba sai BUKKAR ya biyo bayan sa sannan Fatuma wacce suke kira da YAGANA Mala da Bukkar zumunci ne mai ƙarfin gaske tsakanin su, mala yana da Mata mai Suna MARYAM wacce ake kira da YAMURAM suna da yara Huɗu ta farko sunanta JALILA sai HASSAN sannan A’ISHA wacce ake kira da AJIRAM sai kuma FATUMA autar Umma wacce ake kira da FANNA, a sashin Bukkar kuwa yana da matar sa ɗaya shima YAHANASU wacce suke kira da YANA suna da yara biyu rak a duniya BALARABE shine babba amma shi baya Maiduguri yana zaune ne cikin garin Abuja wajen ƙanwar Aunty YANA, sai kuma FATUMA wacce suke kira da Falmata, waɗannan Yan uwa suna bala’in son junansu, zumunci ne mai ƙarfi tsakanin su, wanda tsakanin MALA da BUKKAR babu wanda yake son ɓacin ran ɗan uwansa, haka ya kasance tsakanin ƴaƴan su, musamman HASSAN da Falmata wanda shaƙuwa mai ƙarfi take tsakanin su, wacce sam su basu taɓa zaton soyayyace a tsakaninsu, haka kuma tsakanin Hassan da JALILA suma shaƙuwace sosai tsakanin su, sam Jalila bata son ganin ɓacin ran Hassan komai taci sai ta ajiye masa.
” Umma!!! Umma!!! Umma dai kina ina”
Murmushi Aunty JALILA dake zaune gefe tana hura wutar murhu tayi tare da cewa.
” Oh Falmata irin wannan kira haka sai kace wacce ta ci miki bashi ta kasa biya.”
Zama Falmata tayi tana tura baki tace.
” Ƙarar DOCTOR na kawo mata ta shiga tsakanin mu kuma Allah yau bazan yadda ba”
Ta ƙarasa maganar tana haɗa fuska, dariya sosai Aunty JALILA tasa tace
” Oh ni Jalila ina ganin sanabe, mutumin da bai riga ya zama likitan ba shine kike kiran sa Likita, hmmm su malam DOCTOR manya.”
” Kai Aunty Jalila, ai dai kinsan yayana ya kusa zama likita tunda har ya fara karatun sa ni dai ina Umma na.”
” Umma tana ɗaki sallah take amma ina ganin ta idar, ki shiga ki sameta.”
” Aunty me kike dafa mana yunwa nake ji.”
” To acici sarkin ci, shinkafa ce da wake, kuma babu rabonki a ciki.”
” Lalala!!!! SECOND MOTHER karki fara ɗaukar wannan zunubin kin isa ma ki fara girkin da babu rabon mu, rabu da ita my dear na, dole a dafa a bamu muci.”
Aunty JALILA taji muryar Hassan yana wannan Maganar dariya tasa tace.
” Okay wato ma zunubi zanyi, to shikenan na janye na yarda dole na baku kuci fitinannun ƴaƴan Umma.”
Dariya Hassan ya sa tare da kallon Falmata yace.
” My dear ƙanwata, Ina kika shige tun ɗazu nake neman ki cikin gidan nan.”
Tura baki Falmata tayi tace.
” Ni ba ruwana da kai karka sake kulani.?”
Zaro ido Hassan yayi tare da cewa.
” Na shiga Uku an fasa Aure na, laifin me kuma nayi haka my dear yaushe muka fara faɗa dake.”
Dariya Aunty JALILA Tayi tace.
” Oh yau dai naji tsakanin ku, yanzu ma dai Umma ake jira a kai ƙarar ka, ina baza kunnen na naji laifin ka.”
Muryar UMMA sukaji tana cewa.
” Ai kuwa gani ƴata zoki faɗa min, meya faru na ɗauka miki mataki yanzun nan.”
Tahowa Falmata tayi kusa da Umma ta jingina jikin Umma tare da cewa.
” Umma na, kinga ranar asabar kina zaune a falon ki muma muna zaune DOCTOR ya min alƙawarin cewa zai kaini SUDEIS SUPER MARKET ya min siyayya shine ɗazu da safe dana masa magana yace min wai bashi da kuɗi nayi haƙuri.”
Murmushi Umma tayi tare da cewa.
” Ai kuwa bai isa ba ya karya alƙawari, dan kuwa ina wajen yayi wannan alƙawarin, dan haka bai isa karyawa ba, kinga maza jeki ki shirya kizo ku tafi siyayyar.”
Hassan cewa yayi ” Umma banda kuɗi fa…….”
Hanu Umma ta ɗaga masa tare da cewa.
” Maza jeki shirya ƴata ku tafi.”
Tashi Falmata tayi da sauri ta fice tana yiwa DOCTOR gwalo, Umma duban sa tayi tace.
” Kaje cikin wadrob ɗina akwai 20k ka ɗauka kuje ka mata siyayyar, tunda ka mata alƙawari kasan dai haramun ne saɓa alƙawari ko? to daga yau karka sake yiwa wani alƙawarin abinda baka dashi, Saboda zaisa rai idan kuma bai samu ba, bazaiji daɗi ba, kaje ka shirya sai kazo ka kaita.”
Dariya DOCTOR yayi tare da sunkuyawa ya mannawa Umma kiss a goshi yace.
” Thank UMMA na ina sonki.”
Tare da shigewa cikin Bedroom ɗin Umma 20k ɗin ya ɗauka tare da ficewa yana cewa Aunty JALILA.
” Sai kuma asan tayi, ba dai ki jimu da my dear ƙanwata ba”
Dariya Aunty JALILA tayi tace.
” SABODA UMMA tayi belinka ba, da yanzu kuna nan kuna kwasar adashen tsiya.”
” Oho dai sai kuma kiyi.”
Ya ƙarasa maganar yana ficewa, Aunty JALILA duban Umma tayi tace.
” Umma, alaƙar Hassan da Falmata sai nake hango kamar akwai Soyayya a tsakanin su wanda su basu fahimci hakan ba, Umma ko ke kin hango abinda na hango kuwa.?”
Murmushi Umma tayi tare da kaɗa kai tace.
” Gaskiya ban hango ba, nafi dai hango Shaƙuwa ce ta ƴan uwan taka, to ma JALILA Hassan ya isa ya jawo Aure yanzu shi da bashi da komai da wani kuɗin zaiyi Aure ba sana’a yake dashi ba makaranta fa kawai yakeyi, ita kuwa Falmata ko yanzu za’a iya mata Aure ai kuwa kinga ko suna Soyayya Aure bazai yiwu ba saboda bashi da sana’a.”
Numfashi Aunty JALILA ta sauƙe tare da furta.
” To hakane Allah ya sa mu dace.”
Da ameen Umma ta amsa.
Cikin shirin ta tsaf Falmata ta fito da hijab ɗinta a tsaye ta hango DOCTOR yana tsaye ya zuba hanunsa a cikin aljihu murmushi ya saka tare da cewa.
” Wow ƙanwata tayi, kaga farar mace alkebbar mata, Kinga yanda kike haskawa kuwa tamkar farin wata, kinyi kyau my dear ƙanwata.”
Dariya tasa tace DOCTOR na kaima kayi kyau sosai.”
Murmushi yayi tare da cewa” Bismillah muje.”
Fita sukayi suka tari adaidaita, sai sudees Super market, wani makeken shago ne mai cike da kayayyakin mure rayuwa, shiga ciki sukayi fannin takalma suka fara nufa, DOCTOR tsayuwa yayi a gefe tare da cewa.
” Bismillah kije ki zaɓi dukkan takalmin da ya miki.”
Murmushi Falmata ta saka tare da nufar wajen takalman tana dubawa, hanunta ta saka zata ɗauka ɗauki wani toms wanda yayi mungun burgeta sosai ya mata kyau, yayi saurin riga ɗauka, da sauri itama ta juya taga waye ya rigata ɗauka, idanunsu ne suka sarƙe dana juna, dam ƙirjin sa ya buga, Falmata cewa tayi.
” Malam ya haka, takalmin nan fa na riga ganinsa akan me zaka rigani ɗauka.?”
Ta masa tambaya cike da jin haushi.
Murmushi ya saki tare da cewa.
” Akan bai dace da ƙafarki ba, da ƙafar budurwata ya dace dan haka ita ya kamata ta saka bake ba.”
Haɗa fuska Falmata tayi cike da jin haushi tace.
” Saboda ƙafa yafi ƙafa kenan, kaga malam ka bani Takalmi na.”
DOCTOR daya hango Falmata tsaye da wani ya juya baya, ji yayi zuciryasa ta tsinke da sauri ya nufosu cike da ɓacin rai.
” Bazan baki wannan takalmin ba, malama ki zaɓi wani.”
Zatayi magana kenan taji muryar DOCTOR yana cewa.
” Ke da waye kike tsaye, hakane zaɓar takalmin.”
Ya mata Maganar cike da tsawa, juyowa yayi yana sakin murmushi zaiyi Magana sai suka haɗa ido dashi, cike da mamaki DOCTOR yace.
” HABEEB wai dama kaine, yaushe ka shigo ƙasar, mutanen Cairo.”
Murmushi HABEEB ya saki tare da cewa.
” Hassan dama tare kuke tafe da wannan ƴar ƙauyen, na kwana biyu da dawowa mun sami hutu, ya dai har yanzu kana UNIMAID ɗin ne.”
Dariya DOCTOR yayi tare da cewa.
” Eh gamu nan muna ta lallaɓa karatun a haka, ƙanwar tawa kake kira da ƴar ƙauye, to kuwa kaci bashi.”
Falmata cije leɓenta kawai tayi, HABEEB kuwa cewa DOCTOR yayi.
” Ina labarin SAIF.”?
” Saif yana nan, yaje school yau yana da lectures.”
” Ayya, kasan me zai faru, zan yiwa Daddy na Magana, naga akwai Vaccancy da governor ya basa na Mutum huɗu, wanda gomnati ta ɗauki nauyin karatun su, zuwa India, naga kai Science ka karanta, so zaifi dacewa ace a India kayi karatun ka, insha Allah zan karɓi guda biyu a hanun Daddy na baku kaida saif, insha Allah a India zakuyi karatu.”
Wani irin farin ciki DOCTOR yaji tare da rungume HABEEB yana cewa.
” Alhamdulillah!!! HABEEB bansan ta yaya zan fara gode maka, amma dai Tabbas kamin alkairin da bazan taɓa mantawa ba, na gode sosai.”
Falmata ma murmushi tayi tace.
” Ashe dai mutumin kirki ne kai harna fara maka kallon mutum mai son kanka.”
Dariya HABEEB yayi yace.
” Oh kallon da kike min kenan akan wannan takalmi to riƙe kayanki ƴar ƙauye.”
Ya miƙa mata yana sakin murmushi………….
0006064512 Rashida Usman Jaiz Bank, 200 ko mtn card ta Wannan numbern 08147537180 sai ki turo SHAIDAR BIYA ta ita numbern, yafi miki sauƙi da a baki wanda ba guminki ba, ki karanta.
*ALƘALAMIN UMMU NASMAH CE ✍🏻*
[9/17, 4:01 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 43 to 44*
_________✍🏻 ” to fa ni SALAMATU yau ina jin wata rashin kunya, yaushe ka fara soyayya ban sani ba HABEEB har zaka buɗe wannan idanunka na yaran zamani kana cemin ka faɗa Soyayya Mister lover’s.?”
Dariya ya saka yana kallon action ɗin Wasila ta ƙasan idon yace.
” MOMY ke dai ki bari sai mun daidaita tukunna zaki san waye ce, meye a ciki danna sanar da Momy na, ta kusa samun surka, kuma gashi Momy yarinyar macece mai kamun kai wacce tasan mutuncin kanta, ba irin matan nan bane masu maƙalewa maza su lallai sai an sosu yarinya ce mai aji.”
Shuru Momy tayi jikinta yayi sanyi wannan maganar da HABEEB yayi babu shakka tasan da Wasila yake, duban sa tayi tare da cewa.
” Naji to tashi maza ka barmin falo na, kayi tafiyar ka ina buƙatar sakewa nida yarana.”
Itama Wasila sosai jikinta yayi sanyi, HABEEB yana dariya domin kuwa ya fuskanci Momy ta gane da Wasila yake, ya tashi tare da cewa.
” Shikenan Momy na tafi tunda kin koreni a kawo min abinci na.”
MOMY cewa tayi.
” Eh jeka na kore kan”
ajiyar zuciya Wasila ta sake, tana bin HABEEB da kallo harya fice, Momy duban Hajara da take tsume tayi tace.
” Kinga ki saki fuskarki zaifi miki sauƙi, baiyi niyya bane daya saya miki, SUPER MARKET ko anjuma ɗanjuma drever zai kaiki ki sayi takalmin, ki tashi ki ɗauki abincin sa ki kai masa.”
Kafin Hajara tayi Magana wasila ta rigata da cewa.
” Ki bari Momy ni zan kai masa.”
Cike da tausayin ta Momy tace ” shikenan ki ɗauka yana Kitchen.”
Tashi Wasila tayi, ta shiga Kitchen ta ɗauki abincin ta nufi Part ɗin HABEEB da sallama ta shiga amsawa yayi fuskarsa a sake babu yabo babu fallasa, abincin ta ajiye masa tare da zama a kujerar da take Fuskantar sa, fuskarsa ɗauke da murmushi duk da ransa baya son zaman nata a ɓangaren nasa amma sam bai nuna mata a fuskarsa ba, Saboda yasan babu kyau wulaƙanta ɗan Adam, yace.
” Hajiya Wasila akwai labari kenan naga kin zauna.”
Murmushi Wasila ta saki tare da cewa.
” Babu wani labari hira kawai zan tayaka.”
Still murmushi ya sake tare da cewa.
” Ai kuwa kin ƙyauta sai dai kijeki , nima ina shigowa Part ɗin momyn idan na gama, yaushe DATTI zaizo ya ɗauke kine.”
Murmushi itama Wasila tayi tare da cewa.
” Ka gaji da gani nane kake tambayar sanda za’a zo a ɗauke ni.”
Zaro ido HABEEB yayi yace.
” Ni na gaji da ganinki me kika tare min daga tambaya sai cibi ya zama ƙari to Allah ya baki hkr Hajiya.”
” Idan ban tare maka ba na tarewa zuciyarka bisa ga dukkan alamu.”
” Zuciyata kuma, meye haɗinki da zuciyata da har zaki tare mata wani abu.?”
Ya jefa mata tambayar tamkar bai san me take nufi ba, amsa ta basa da cewa.
” Saboda ina sonka, nasan ka fuskanci hakan amma kayi burus dani ka maidani mahaukaciya tamkar baka san me nake nufi ba, nasan ko karen gidan nan yasan ina sonka bare kaikuma da nake yiwa Soyayyar.”
” Soyayya kuma Wasila, wacce irin Soyayya kuma akwai wata Soyayya ce da take tsakanina dake bayan ta ƴan uwan taka.?”
Ɗago kanta tayi ta zuba masa Ido na second biyu kafin tace.
” Soyayya wacce ka sani ta Aure ita nake maka ba Soyayyar ƴan uwan taka ba, Ya HABEEB ina sonka zuciyata ta kamu da Soyayyar ka mai tsanani meyasa ka kasa fuskantar hakan.”
Numfashi HABEEB ya sauƙe mai nauyi cike da tausayin ta yace.
” Tabbas duk mutumin daya nuna maka Soyayya, mutum ne mai daraja a wajen ka, domin kuwa komai tsiya yafi maƙiyinka, na gode da Soyayyar da kike mini, sai dai kash ita Soyayya bata taɓa daɗi idan bata kasance a zuciyoyin mutum biyu ba, dole zuciyar mutum ɗaya zata wahala, kamar dai yanda ya kasance tsakanin zuciyata da taki, ke akwai Soyayya ta a zuciyar ki yayin da ni kuma tawa zuciyar sam babu Soyayyar ki, na riga da na bawa wata soyayyata a yau ɗin nan sorry to say kinyi let, ki rarrashi Zuciyarki ki bata hkr insha Allah zaki sami wanda ya fini, na faɗa miki hakane domin karmu wahalar da kanmu.”
A firgice Wasila ta miƙe tsaye tare da cewa.
” Nayi haƙuri!!!! Nayi haƙuri fa kace, bazan iya haƙura da Soyayyar ka ba Saboda zuciyata ta kamu da ciwon Soyayyar ka, ta ya kake tunanin cire Soyayyar ka a raina abune mai sauƙi, sam bazan iya ba, ina sonka kuma ya zama dole ka soni.”
Ta ƙarasa maganar cike da tsawa hankalinta a matuƙar tashe, shima HABEEB tashi yayi yace.
” Wannan ba maganar tashin hankali bane na sanar dake ne iya gaskiya ta, da take cikin Raina gudun karna yaudari zuciyarki dalilin kenan da yasa na sanar dake gaskiya, Hausawa sukace idan so cuta ne haƙuri ma magani ne, kamar yadda kikace, bazaki iya daina sona ba, haka nima zuciyata bazata iya sonki ba, kinga kuwa Soyayya bazata taɓa yiwuwa ba tsakanin so da rashin so, dole sai ya kasance akwai so da Soyayya, ki rarrashi Zuciyarki ki cire Soyayyata a ranki.”
” Wannan karin magana ce kawai ta Hausawa ina sonka ina sonka ina sonka kuma bazan taɓa daina sonka ba.”
” Hmmm shikenan ni dai na faɗa miki gaskiya ta wannan ruwan kine ki yarda ko karki yarda.”
Hawaye ne suka gangaro daga idonta cikin shashsheƙar kuka tace.
” Wallahi dole sai ka soni dole ka Aure ni, kota halin yayane.”
Murmushi HABEEB ya saki tare da cewa.
” Okay to shikenan ki gwada mu gani ko zan aureki dole, fice ki barmin Part ɗina kafin na tashi na miki abinda bazaki ji daɗin sa ba, tunda na fahimci Zuciyarki shashashar zuciyace.”
” Ba sai ka kore ni ba, da ƙafata zan tafi amma ka sani dole ka Aure ni, bazan taɓa barin wata mace ta raɓeka ba, ka san wannan duk inda kaje dole ka dawo gareni.”
Tana gama faɗin haka ta juya ta fice da gudu tana sakin kuka, tsuka HABEEB yaja tare da furta ” shashasha marar fahimta, ana soyayya dole ne mtsss.”
Wasila da gudu ta haura sama tana kuka a lokacin Momy bata nan ta yi Bedroom ɗinta, bed ta faɗa tare da sakin kuka, Hajara duban ta tayi tare da cewa.
” Lafiya Wasila kika shigo da kuka keda waye haka.?”
” Hajara Ɗan uwanki ya furta min cewa baya sona na cire Soyayyar sa a cikin raina.”
” Kai haba Wasila to sai me, dan baya SONKI shi kaɗai ne namiji a duniya, ki ciresa kawai a ranki.”
Girgiza kanta Wasila tayi tare da furta.
” Hajara baki san menene zafin soyayya ba, shiyasa kike faɗin haka amma ni kaɗai nasan raɗaɗin nake ji a cikin zuciyata, bazan iya cire Soyayyar sa a cikin zuciyata ba.”
” Cap idan haka Soyayya take Allah ya shiga tsakanina da ita, to Allah ya miki mafita.”
Wasila batace komai ba, ta cigaba da kukanta.
Da daddare kowa ya hallara a daining suna cin abinci har Daddy sai dai babu Wasila cikin su, tace ta ƙoshi, HABEEB Daddy ya duba tare da cewa
” Daddy, akwai wasu abokaina waɗanda mukayi primary school dasu, Kuma ina tunanin baka manta su ba, HASSAN MALA BULAMA wanda yake unguwar BULUNKUTU TSALLAKE, da SAIFUDDEEN KHALID.”
Shuru Daddy yayi na ɗan wani lokaci kafin can yace.
” Okay na tuna su, ai harna manta dasu my son.”
” Eh Daddy dama wata alfarma nake nema musu a wajen ka, sunyi karatu ne a fannin Science shine nace mai zai hana a cikin Free education da gomnati ta ba na zuwa Indiya karatu ka basu tunda ɓangaren likitanci suke karanta, kaga India suna da good Education na ɓangaren likitanci, sannan zasufi samun Salary mai kyau wanda zasu taimaki kansa harma da ƴan uwan su.”
Murmushi mai sauti Daddy ya saki cikin so da ƙaunar ɗannasa yace.
” Ka wuce neman alfarma a wajena my son, kuma wannan taimako da za’a musu, basu kaɗai zamu taimaka ba har al’ummar da zasu duba lafiyar su bayan sun kammala karatun, gobe da safe kazo office ka karɓi Vaccancy ka kai musu Allah yayiwa karatun da zasuyi albarka.”
Dariya HABEEB yayi tare da yiwa Daddy godiya Momy ma sosai taji daɗin alkairi da ɗanta yayi, Tabbas ta samu ɗa na gari, mai taimakon al’umma, lallai tayi dacen haihuwa domin kuwa samun mutum irin HABEEB a yanzu abune mai matukar wahala fatanta Allah ya ƙarawa rayuwarsa albarka.
Kuyi hkr dan karku ce kwana biyun nan ina muku typing kaɗan wallahi ina cikin hidima ne shiyasa kumin uzuri dan Allah🤲🏻
Idan kina buƙatar wannan littafin ki nemeni ta wannan numbern 08147537180 yafi sauƙi fiye da ki karanta abinda ba gumin ki ba.
*ALƘALAMIN UMMU NASMAH CE*✍🏻
[9/17, 4:01 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 41 to 42*
Wannan shafin sadaukarwa ne gare ku DOCTOR HASSAN FAN’S ina yinku irin sosai ɗin nan❤️🤝🏻
________✍🏻 Girgiza kanta Falmata tayi tare da cewa.
” A’a bazan karɓa ba, na bar maka ka kaiwa budurwar taka, ni zan zaɓi wani.”
Cike da Zolaya HABEEB yace mata
” Wannan takalmin ya yiwa budurwa ta kaɗan 38 size ne fa ita kuma budurwata 45 size take sawa kinga kuwa ai wannan ya mata kaɗan.”
Ya ƙarasa maganar yana dariya Falmata zaro ido tayi tare da cewa.
” 45 size kace, Wannan wacce Irin ƙaface da, sai kace wacce ta haɗa dangi da Aljanu, amma dai basamudiya ce ko.”
Ba HABEEB harta DOCTOR sai da ya saka dariya yace.
” Kinga my dear ƙanwata karɓi takalmin ki, ki ƙyale HABEEB, tsokanar ki yake, idan kika biyewa HABEEB sai mu wuni a nan.”
Dariya Falmata tayi tare da cewa.
” Oh wato duk wannan ɓata min lokacin da kayi Zolaya ta kake, to ai kuwa dole sai ka sayi wannan takalmin kuma ya kasance shine kyautar farko da zaka yiwa budurwar ka, ka samu budurwa mai size 38 domin kuwa sunfi more Takalmi sannan anfi samun daidan su da wuri.”
Murmushi HABEEB yayi tare da kashe mata ido yace.
” Insha Allah kuwa wannan takalmi shine zai kasance kyautar farko da zan yiwa budurwa ta, duban DOCTOR yayi yace, zan wuce amma insha Allah zuwa gobe zan nemeka.”
Musabaha sukayi da DOCTOR yana masa godiya HABEEB ta tafi tare da ɗagawa Falmata hanu, DOCTOR cewa yayi.
” Kiyi sauri ki ɗauki abinda zaki ɗauka time na tafiya, juyawa Falmata tayi ta cigaba da ɗaukar abinda ya mata sun kai wajen 4 hrs kafin suka nufo wajen payment, Doctor kayan ya miƙa musu, lissafi sukayi 50k DOCTOR cike da razana ya ɗago kansa Domin kuwa 20k kawai hanunsa muryar mutumin sukaji yace,
” Kaine Hassan Mala WANBAI.”
Ɗaga masa kai DOCTOR yayi alamun shine.
” Okay to ba sai kun biya kuɗin ba, an biya wani mutum mai suna HABEEB ya biya muku, 70k mune ma zamu baku canji yanzu.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya saki tare da yiwa Allah godiya, daya tseratar dashi, Tabbas HABEEB yayi belinsa yau, a leda suka zuba musu kayan tare da bawa DOCTOR canjin su 20k, fita sukayi suka tare a daidaita suka hau sunyi nisa da tafiya yaji muryar Falmata tana cewa.
” Wannan abokin naka yana kirki SOSAI na juma banga mutum mai kirki irinsa ba.”
Murmushi DOCTOR ya saki tare da cewa.
” Kaɗan kenan daga cikin kirki Irin na HABEEB mutum ne shi mai sowa ɗan uwansa abinda ya sowa kansa, sannan shi ɗan masu akwai ne Mahaifinsa shine mistern sadarwa na ƙasa gabaki ɗaya wato Nigeria, ALHAJI MAHMUD BAMAI shiyasa kika ga yana wasa da kuɗi yanda ransa yake so, sai dai ta inda yake burgeni ko kaɗan kuɗin mahaifinsa basu damesa ba, shi dai burinsa ya tsaya da ƙafafunsa ma’ana ya nemi na kansa, yasha faɗa mana wannan maganar tun muna primary school.”
Murmushi Falmata ta saki tare da cewa.
” Tabbas wannan abokine na gari, shiyasa Hausawa sukace, yin aboki da mai ture yana daɗi ko ba komai kayi ƙamshi Tabbas duk macen da ta samesa a matsayin mijin Aure ta gama dacewa.”
Murmushi kawai DOCTOR yayi tare da miƙawa Falmata 20k ɗin yace.
” Gashi ki riƙe sanjin.”
Girgiza kanta Falmata tayi tare da cewa.
” A’a ka rike domin kuwa ka fini buƙatar kuɗi, ni iya wannan kayan ma sun isheni.”
DOCTOR zaiyi Magana Falmata ta tare sa tare da cewa.
” Dan Allah karkace komai, ka riƙe su kawai.”
Shuru DOCTOR yayi tare da mayar da kuɗin aljihun sa, koda suka isa da gudu Falmata ta shige sashin su, ɗakin Hajja ta faɗa BULAMA na zaune ta shigo, Hajja hararar ta tayi tare da cewa.
” To gidan rashin nutsuwa, ɗakin arna kika shigo da bazaki mana Sallama ba.”
Ta ƙarasa maganar cikin faɗa Falmata tura baki tayi tare da zuwa kusa da BULAMA ta zauna tace.
” BULAMA kana jin matarka ko, to kace ta fita harkata mena mata haka kawai zata min tsawa dan kawai na shigo ɗakin ta.”
Dariya BULAMA yayi yace.
” To Hajja kinji dai abinda kishiyar ki ke cewa, to kibi a hankali domin kuwa nafi sonta fiye dake, dan haka taka a hankali.”
Gabaki ɗaya dariya suka saka har Hajja, Falmata ledar hanunta ta miƙawa Hajja tace.
” Kinga abinda yayana ya saya min a SUDEIS SUPER MARKET.”
Taɓe bakinta Hajja tayi tace.
” Ikon Allah su masu yaya manya, sunyi kyau Allah ya masa albarka.”
Da ameen BULAMA ya amsa tare da cewa sai kije ki nunawa uwarki ko.”
To Falmata tace tare da ɗaukar ledar ta shige ɗakin Aunty YANA, zama tayi kusa da ita tare da cewa.
” Mama kinga kayan da DOCTOR ya saya min a SUPER MARKET.”
Aunty YANA batayi magana ba Falmata taji muryar DOCTOR dake kwance a ƙaramin gadon Aunty YANA yace.
” HABEEB dai ya saya miki ba dai DOCTOR ba.”
Ya ƙarasa maganar yana sakin murmushi, Falmata cike da mamakin yaushe ya shigo take kallon sa, Aunty YANA ce tace.
” Yau dama HABEEB yana gari, shine bai shigo mana ba, kasan rabona dashi tun kuna primary school, sai kwanaki can na haɗu dashi a Ibrahim communication, amma haɗuwar tayi Shekara shine ma yake sanar dani cewa zai tafi Cairo KARATU, yace insha Allah yana dawowa zaizo mana.”
Dariya DOCTOR yayi yace.
” Yace zai shigo gobe akwai alƙawarin ma da yamin amma dai sai yazo goben idan abun ya tabbata sai kuji.”
Da Allah ya KAIMU Aunty YANA tace, taɗin duniya suka dinga yi, dake DOCTOR haka yake da Aunty YANA tamkar Ɗan da ta haifa.
Shi kuwa HABEEB a matuƙar gajiye ya isa cikin gidan nasu a main Falo ya zauna tare da cewa.
” Wash Momy na gaji sosai.”
Murmushi wata kyakkyawar mata fara sol mai fason goshi, tayi tare da cewa.
” Oh HABEEB sarkin raki, yanzu nan da SUPER MARKET ɗin da kaje ne shikenan harka gaji.”
” Oh Momy waya faɗa miki SUPER MARKET kawai naje, na jewa Daddy aika fa can GIWA BARECK, daga nan na wuce masa har HAUSARI kafin fa na wuce SUPER MARKET ɗin.”
Murmushi Momy ta saka tare da cewa.
” Kuma duka tafiyar ƙafa kayi ko? Kai dai HABEEB wannan son jiki naka yana damuna.”
Dariya kawai HABEEB yayi, Wasila da Hajara ne suka sauƙo daga step ɗin Wasila sai bin HABEEB take da wani shu’umin kallo, HABEEB ya ganta sarai amma ya kawar da kansa gefe yayi a rayuwarsa ya tsani Wasila baya son mace wacce sam bata da kamun kai, amma sai dai sam baya ƙuntata mata, saboda duk yanda mutum yake sonka yafi maƙiyin ka, sai baya sake mata fuska, Hajara ce ta ƙaraso tare da cewa.
” Bros ina takalmin nawa.”
Murmushi ya saki tare da cewa.
” Naje SUPER MARKET amma dai ban sayo miki takalmin ba, saboda banga wanda ya min kyau ba.”
Tura bakinta Hajara tayi tana kallon, takalmin dake gefen sa a cikin leda tace.
” To yaya wannan takalmin fa ba gashi ba.”
” Karki kuskura ki saka ranki a wannan takalmin ba naki bane.”
Ƙunƙuni Hajara ta hauyi tace.
” Momy kinji Bros ko.”
Momy murmushi tayi tace.
” HABEEB!!! Idan ba ita ka sayowa wannan takalmin ba, to wa ka sayawa.?”
Ta jefa masa tambayar, shima HABEEB murmushi ya saki tare da cewa.
” Budurwa ta na sayawa Momy wacce nake matuƙar sonta, shine kyautar farko da zan fara mata, amma fa sai dai bata san ina sonta ba.”
Wasila wani murmushi ta saki ita duk a zaton ta itace wacce yake so ɗin, murmushi Momy ta saki tare da cewa…………………”
Ki biya kuɗin ki yafi miki sauƙi da ki karanta abinda ba naki ba, idan kina buƙata ki neme ni ta wannan numbern 08147537180.
Kuyi hkr yau banyi editing ba saboda bani ishashen time.
*UMMU NASMAH CE✍🏻*
[9/17, 4:01 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 45 to 46*
*Wannan shafin naki ne Aunty na, Aunty HAUWA maman uswan, Allah ya ƙarawa zuri’a albarka ya ƙaro miki tarin farin ciki, a cikin gidan ki🤲🏻*
________ ” UMMA jiya na haɗu da kawu Dauda a kasuwa yake sanar dani cewa na faɗa miki Aunty Yakura bata jin daɗin jikinta sosai.”
” Subabanallah yakura jikin yaƙi daɗi kenan innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un to zan shirya naje gobe da safe yanzu dare yayi da safe insha Allah zanje Allah Ya bata lafiya.”
Da ameen Aunty JALILA ta amsa sunan zaune BABA ya shigo shida DOCTOR, zama sukayi DOCTOR yace.
” Umma sannu da hutawa.”
” Yauwa sannu, yaushe kuka dawo daga SUPER MARKET ɗin, banji ɗuriyar kuba dukkan ku kaida Falmatan.”
” Umma tun ɗazu da la’asar muka dawo, mun shige wajen Aunty YANA ne, kuɗin ya ciro cikin aljihun sa ya miƙawa Umma 20k ɗinta yace, Umma bamuyi amfani da kuɗin naki ba, HABEEB wannan Abokin nawa wanda mukayi primary dashi, shine ya biya mana kuɗin.”
Murmushi Umma ta saki tare da cewa.
” Masha Allah na tuno da Habibu, dama suna garin nan nayi zaton ai sun bar Maiduguri, ka riƙe kuɗin a hanunka zasu maka amfani.”
” Eh suna nan Umma yace ma zaizo gobe da safe idan Allah ya kaimu.”
Baba ne ya saki murmushi tare da cewa.
Wai ni yaushe zaka fara fita kasuwa ne, Hassan nayi nayi da kai kaƙi kasuwancin nan kai lallai sai aikin gomnati ko, kuma ba lallai bane a yanzu ka samu aikin gomnati, idan ka gama karatun tunda ba ɗaurin gindi bane da kai.”
Baba ya ƙarasa maganar cikin faɗa, Umma itama cewa tayi.
” Abinda nake faɗa masa kenan kullum Baban JALILA, amma kunnen ƙashi garesa, yanzu kai ba abun kunya bane a wajen ka, kuɗin da zaka kashe ma sai ka tambaya an baka.”
Haɗa fuska DOCTOR yayi yace.
” Ni Umma kubar Maganar nan kawai, ku min addu’a Allah ya bani aiki idan na gama karatu na, kuma fa Baba kaima ka sani duk wanda ya karanci likitanci to yana da aiki, kawai kumin fatan Nasara cikin karatu na.”
Aunty JALILA ce tace.
” Ƙwarai kuwa Baba, likita da aikinsa yake fitowa kuma Umma ai ɗan abinda kuke basa bazai gagareku ba, na ɗan lokaci kaɗan ne, wata rana shima sai dai ya baku.”
Umma cikin faɗa take cewa Aunty JALILA.
” To uwar marassa son gaskiya, da zarar an taɓo Hassan shikenan sai ki nemo hanyar karesa koda kuwa shine marar gaskiya, Mtsss kega mai ɗan uwa ko.”
Murmushi Baba yayi tare da cewa.
” Jalila kenan Baki san laifin ɗan uwanki, kullum kina cikin karesa, Ubangijin Allah ya ƙara muku son junan ku, Umma ya kalla tare da cewa, GOBE kisa Jalila taje gidan AJIRAM ta dawo min FANNA cikin gidan nan, nifa gidan nan baya min daɗi idan babu Auta na.”
Sallamar kawu Dauda sukaji Aunty JALILA ce ta amsa sallamar, shigowa kawu Dauda yayi ya zauna ya miƙawa Baba hanu sukayi musabaha, Umma ce tace.
” Ya Dauda inda dabtu” ta gaishe sa da harshen kanuri amsawa yayi da.
” Dabtu beji, baki san yakura bata da lafiya bane jikin nata babu daɗi sosai fa.”
” Yanzu JALILA take sanar dani, Insha Allah gobe zanje na dubata, tana gida ne ko asibiti.”?
” Tana gida basu kaita asibiti ba.”
Babane yace
” Allah ya bata lafiya, amma ya kamata su Kaita asibiti sabida ciwon ta kamar bana maganin gida bane.”
” Hakane amma Bana ya hana su Kaita.”
DOCTOR ne ya miƙa masa hanu suka gaisa kafin DOCTOR ya miƙe yace.
” Umma bari naje na kwanta sai da safe.”
Da Allah ya tashe mu lafiya Umma ta amsa, sannan DOCTOR ya fice, Aunty Jalila ma ficewa tayi, ya saura daga Baba sai kawu Dauda da Umma, can Baba ma ya tashi ya basu waje ko zasuyi zancen su na ɗan uwa da ɗan uwa, bayan fitan Baba Umma tace wa Kawu Dauda.
” Ya Dauda naji labarin cewa ka saida min da gonata guda ɗaya ta gado, meyasa zaka saida min ba tare da izini na ba, dan Allah Ya Dauda me kake yi da kuɗin ne kam, ka gama ƙarar da gonakin ka da duk wani abinda ka samu na gadon mahaifin mu, sannan banga abinda kayi da kuɗin ba, komai sun lalace maka, sannan yanzu Kuma ka dawo kan nawa gaskiya bazai yiwu ba, 3million fa ka saida gonar nan, Naira biyar baka kawo min ba, gabaki ɗaya kaje ka hallakar da kuɗin daga wannan ya tsaya haka karka ƙara sai da min kadarata, Idan kuma baka daina ba zan karɓe takadduna daga hanunka na dawo dasu hanun mijina saboda darajar ƴan uwan taka yasa na danƙa maka su.”
Umma ta ƙarasa maganar cikin ɓacin rai, kawu Dauda cike da jin haushi shima yace.
” Lallai Yamuram kin isa yanzu ni kike ɗagawa murya, ko kin manta ina sama dake, saboda kawai na sayar da gonarki gudu ɗaya a cikin Goma, shine kike min faɗa tamkar wata uwata, Yamuram ko kin manta baki da wani ɗan uwan daya wuce ni mu biyu fa rak uwar mu da ubanmu suka haifa a duniya yanzu ashe dama bazaki rufa min asiri ba idan bani dashi, yayi kyau na gode laifi nane dana taɓa kayanki.”
” Ni fa ya Dauda ba abinda nake nufi ba kenan, gani nayi banga wani abu mai mahimmanci wanda kayi da kuɗin ba, shiyasa nayi Magana amma Allah ya baka haƙuri.”
Tsuka Kawu Dauda yayi tare da tashi a zuciye ya fice, Umma a fili ta furta.
” Ikon Allah mutum da haƙƙinsa bai isa yayi magana ba, shikenan sai cibi ya zama ƙari, amma dai wallahi bazan bari ka hallakar min dukiya ba kamar yadda ka hallakar da naka.”
Ta ƙarasa maganar tana tashi ta shige Bedroom ɗinta.
Kawu Dauda ransa a matuƙar ɓace ya shiga cikin gidan nasa, Jummai tana zaune a barandar gidan, zama yayi yana sakin tsaki, Jummai ɗago kanta tayi tace.
” Baban Musa mai yake faruwa ka shigo min cikin gida tamkar wanda akayiwa mutuwa.”?
” Hmmm Jummai wai ni YAMURAM tasa a gaba take min faɗa tamkar zata cinye ni akan kuɗin gonar ta, alhakin ni bani na ci kuɗin gonar nan ba, ko naira biyar baki bani duka kika karɓe kuɗin nan, to wai ma me kikayi da kuɗin da kika sani na saida gonar ta.”
Miƙewa tsaye Jummai tayi tare da kama kunkumin ta cike da masifa tace.
” Eye Lallai Baban Musa, ni kake tuhuma me nayi da kuɗin , yaushe ka samu wannan bakin, to bazan faɗa ba kazo ka matseni sai na faɗa maka, kuma wallahi sisi bazan baka ba a cikin kuɗin nan.”
Ta ƙarisa Maganar tana daka masa harara, cike da tsoro Kawu Dauda yace.
” Allah ya baki haƙuri, dan Allah kiyi hakuri.”
Tsuka taja tare da shigewa cikin ɗaki tana masifa, tashi kawu Dauda yayi yana bata hkr yabi Bayan ta tamkar wata uwarsa.
(Ai kin sihiri kenan, Jummai macece wacce bata da tsoron Allah ko kaɗan, gidan boka kuma ta mai dashi tamkar gidan uwarta, shima kansa kawu Dauda ta shanyesa sai abinda tace yake yi, duk abinda tace yayi baya mata musu haka zai aikata.)
(Kuji tsoron Allah mata, meye ribarki ƴar uwa idan kin yiwa mijinki sihiri shin bakya tsoron lahirar kine, ko kin manta wannan duniyar ba matabbata bane, kuji tsoron Allah matan zamani)
Muna hidimar biki ne, mu haɗu daku next page, i love You MASOYANA😘😘😘😘
Ki biya kuɗin ki yafi miki sauƙi fiye da ki karanta abinda ba gumin ki ba, neme ni ta nan domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180
Ummu Nasmah ce✍🏻
[9/18, 11:42 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 47 to 48*
________✍🏻 Har uwar ɗaka Kawu Dauda yabi Jummai cike da damuwa yake bata haƙuri, ai kuwa Jummai cikin ɗaga Murya tace masa.
” Naji na haƙura amma ka sani daga yau karka kuskura koda wasa ka sake tuhumata, domin kuwa ina nema mana yanda zamu rufawa kanmu ne asiri, wannan kuɗin gonar da kake gani Kabiru na bawa kuɗin yaje ya samu fili mai kyau ya saya mana gini zamuyi, mubar wannan shegen gidan gadon na laka, muma muje mu shiga bulo-da bulo, aha Tunda kai kaje ka hallakar da naka kadarorin a caca duk an cinye ka, to kuma wallahi duk wani buƙatu na daya tashi dole kaje ka kama kadarar wannan shegiyar ƙanwar taka ka sayar ka bani kuɗin haka kuma nan da ƙarshen wata ka nemo 1million ma’ana kaje ka ƙara ɗaukar gonar tata ka sayar ka kawo kuɗin zamu ɗaga gini dole muma A.c nan musha ta muci jar miya muci kaji, ka ji ko baka jiba.”
Kamar wawa haka kawu Dauda yake kaɗawa Jummai kai, kafin yace.
” Naji insha Allah zan kawo miki, ina dai kin huce yanzu bana son ki dinga fushi dani.”
Murmushin makirci Jummai ta saki tare da cewa.
” Yauwa ko kaifa mai gidana ai ban isa fushi da kai ba, kawai bana son abinda kake min ne, bari naje na kawo maka abincin ka.”
Ficewa tayi ta nufi Kitchen ABINCIN kuwa ta kawo masa sai kuma ta zauna suna fira kaɗan kaɗan.
**************
Washe gari da safe, misalin ƙarfe 10 Falmata ta fito cikin shirin makarantar islamiyya da take zuwa huffaz fannin mahaddata, hanunta riƙe da ƙur’aninta sai kuma wayarta Nokia rakani kashi, ɗakin Hajja ta fara shiga ta samu tana lazimi shi kuma Bulama yana kwance akan doguwar kujerar Hajja yana bacci, kusa da Hajja ta ƙarasa tare da gaisheta amsawa Hajja tayi tana cewa.
” Makaranta zaki tafi ne.”?
Kaɗa mata kai Falmata tayi tace.
” Ehh Hajja makaranta zanje ni, wannan tsohon ƙwaraɓaɓɓen mijin naki kam bacci yake kya gaishe sa idan ya farka.”
Murmushi Hajja tayi tare da cewa
” Ai kuwa wannan tsohon yafi waɗannan samarin naku na yanzu, kina kallon tsayayyen namiji mai zati da kwarjini, adalin shugaba, ina zaki haɗa sa da lusari samarin nan naku na zamani.”
Ta ƙarasa maganar tana kallon BULAMA dake baccin sa baima san suna yiba dariya sosai Falmata tasa ta nuna Bulama da yatsa tace.
” Shi wannan ɗinne tsayayyen namiji mai zati 🤣 haba dai Hajja kina kallon abu duk ya kwararraɓe ya fice hayyacin sa, kamar a ɗauka a kaisa juji a yasar, wannan ai sauran ƙasa ne, jira kawai muke ya sheƙe muci gumba da masa ranar sadakar ukun sa muyi rawa mu girgije.”
Ta ƙarasa maganar tana ficewa da gudu bakin ta ɗauke da dariya, Hajja cewa tayi
” Ja’ira da ki tsaya mana kiga yanda zanci mutumci ki, kyayi rawa tunda ɗan iska ne ya mutu.”
Ita dai Falmata tuni ta shige ɗakin Aunty YANA tana zaune tana shan koko da ƙosai kusa da ita Falmata ta zauna tare da saka hanu cikin ƙosan tace.
” Mama kin tashi lafiya.”
” Lafiya lau Falmata, ya kika makara keda zaki tafi 9:30 kene har 10:19 kin san dai bana son wannan lattin da kike ko.”
” Mama maji nake jira tun ɗazu bata ƙaraso ba, amma dai yanzu munyi waya tace gata tahowa, ina Baba Bukkar Mama.”
Taɓe bakinta Aunty YANA tayi tace.
” Yana ƙofar gida suna karin kumallo shida baban Hassan.”
Da to Falmata ta amsa tana kai ƙosai bakinta sallama Maji tayi ta shigo cikin ɗakin Aunty YANA, bata zauna ba ta gaishe da Aunty YANA cikin sauri, Aunty YANA tana murmushi ta amsa tare da cewa.
” Kunyi latti yau, amm maza to Falmata tashi ku tafi, kici ƙosan mana Maji.”
” A’a Mama na ƙoshi, yanzu na karya.”
Falmata tsumman dake gefen Aunty YANA ta ɗauka ta goge hanunta sannan ta ɗauki qur’anin ta, sallama sukayi Aunty YANA, Albarka ta saka musu tare da addu’a suka fita, Falmata ne ta dubi Maji tace.
” Ƙawata zafa mu shiga sashin su DOCTOR na gaishe da Umma sai mu wuce.”
Maji da to ta amsa, suka shiga cikin part ɗin ɗakin Umma rufe da key da alamu yau tayi sammakon fita unguwa, fitowa sukayi, har sunzo zaure Falmata ta doshi ɗakin DOCTOR Maji tsuka taja tare da cewa.
” Haba Falmata wai meye haka ne kam kinfa san munyi let, amma shine kike faman karkata zuwa ɗakin wannan uban ƴan girman kan da zafin zuciya, Allah kika juma tafiyata zanyi sai dai kuma mu haɗu a school.”
” Hmm zan shiga wajen maƙiyin kiba ai dole ki hasala, to kwantar da hankalin ki, yanzu zan fito.”
Ta ƙarasa Maganar tana taɓe bakin ta, Falmata ɗakin ta tura tare da cewa.
” Hi Doctor na”
da murmushi saman fuskarsa ya ɗago ya zuba mata narkakkun idanunsa waɗanda suke kama da na mai bacci, hanunsa riƙe da qur’ani yana karatu murmushi ya saki tare ce mata.
” My dear na, kin tashi lafiya.”
” Lafiya lau Alhamdulillah my dear na, kadai school zaki wuce.”
” Eh school zan shige, naga Umma ɗakinta a rufe da key, har Aunty JALILA ma bata nan.”
Murmushi DOCTOR ya saki yace.
” Umma ta tafi, gidan su unguwar mandagori.”
” To Allah ya dawo da ita lafiya, bari na shige Maji tana jira na.”
Falmata harta juya taji muryar DOCTOR yana mata addu’a.
” *Ina roƙon Allah ya yiwa ƙwaƙwalwar ki Albarka fiye da ƙoƙarin ki,yayi wa rayuwarki albarka fiye da hasken dake cikin rayuwarki yayi miki rahama fiye da tuban ki yaji ƙanki fiye da tunaninki ya ƙara haskaka rayuwarki fiye da hasken ki ya karɓi ibadunki fiye da ƙwazonki, Allah ya miki jalabi da jalabin dake cikin alƙur’ani, Allah ya haskaka miki hanyarki Allah ya yiwa rayuwarki albarka.”
Wani irin lumshe idanunta Falmata tayi tana jin wani farin ciki na shiga ranta, wani irin ƙaunar ɗan uwan nata ne taji ya ƙara tsirga mata a cikin ranta, fuskarta ɗauke da murmushi ta juyo tare da cewa.
” Ameen DOCTOR na, Tabbas yau ka cika zuciyata da farin ciki, zan wuni cikin walwala da farin ciki, ina sonka DOCTOR na, ba iya Soyayyar ƴan uwan taka ba, soyayya nake maka wacce nake fatan na kasance a cikin ƙarƙashin inuwar Auren ka, Allah yasa ban makara ba, wajen bayyana Soyayyata gareka.”
Murmushi shima DOCTOR ya saki zuciyarsa cike da nishaɗi yace.
” Tabbas Soyayyar ki karɓaɓɓiya ce a gareni, Allah ya hallici zuciyata ce saboda ke, ina ƙaunar ki fiye da yanda kike ƙaunata, ki saka a Ranki DOCTOR naki, KUMA zai kasance dake har abada.”
Murmushin farin ciki Falmata ta saka tare da ficewa cikin sauri, dariya DOCTOR yayi yana jin wani irin Soyayyar ta mai ƙarfi tana ƙara bijirowa zuciyarsa, murmushin ya kara saki tare da furta.
” Ashe bani kaɗai nake dakon Soyayyar ta ba, Allah ka cika mana burin mu.”
Tafe suke Falmata sai famar murmushi take, ganin murmushin da Falmata take yayi yawa yasa Maji cewa.
” Ƙawata wai farin cikin me kike haka naga sai sakin murmushi kike yiwa wacce aka yiwa kyautar zuciya.”
Murmushi Falmata ta saki mai sauti tace.
” Kamar kuwa kin sani ƙawata kyautar zuciyar na, samu yau dai na daure na furtawa DOCTOR gaskiyar abinda yake zuciyata ashe bani kaɗai nake sonsa ba, shima akwai ajiyar soyayyata a zuciyarsa, yau ina cikin farin ciki DOCTOR ya amshi soyayyata.”
Ta ƙarasa maganar cike da farin ciki mai yawa, Maji tsuka taja kafin tace.
” Wallahi kin bada mata, meyasa kika kasa haƙuri shi ya furta miki cewa yana sonki da bakin sa, mazan yanzu sune ma su kace suna sonka ya ka ƙare dasu bare kuma kaine ka furta musu, hmmm Falmata duk randa kika fara nunawa namiji cewa kece kike sonsa, wallahi daga baya sai kin fuskanci ƙalubale, zai miki duk abinda yaga dama saboda yana tunanin kina sonsa bazaki iya rabuwa dashi ba, bare kuma namiji Irin Hassan mai Izza da zafin zuciya ga saurin fusata, gaskiya banso ace kece kika fara furta masa soyayya ba , kinyi likin kuma zakice na faɗa miki.”
Numfashi Falmata taja tare da furta.
” Hmmm, DOCTOR ba irin mazan da kike tunani bane, tun ina zanin goyo yake nuna min kulawa da Soyayya, da ƙauna da shaƙuwarsa na taso, yana nuna min kulawa da Soyayya, yau dana furta masa kalmar so bai jaba ya amsa min tare da karɓar soyayyata hanu biyu sannan karki manta DOCTOR fa ɗan uwana ne, taya kike tunanin zai juya min baya, ko kaɗan ina da tabbas akan DOCTOR bazai taɓa juyawa soyayyata baya ba , Kuma na Tabbata zan samu farin ciki mai ɗaurewa a gidan sa har ƙarshen Rayuwata.”
Murmushi Maji ta saki tana duban Falmata duba na baki da hankali kafin tace
” Ba’a shaidar namiji, koda kuwa uwa ɗaya uba ɗaya kuka fito, nikam Falmata banso haɗuwar Soyayyar ki da Hassan ba, domin kuwa hakinku akwai banbanci, ina tsoron ya cutar da Rayuwar ki.”
” Maji kenan, kedai na fuskanci bakya son Doctor na rasa meya tarewa rayuwarki, dan Allah Maji ki barni da abinda nake so, karki zamo silar shiga tsakanina da Soyayyata, dan Allah karki zamo silar hawaye na, ki barni da Soyayyata.”
” Ni ban tsani Hassan sai dai kawai halinsa ne bana so, duk mutum mai saurin fusata da zafin zuciya bashi da daɗin zama, domin kuwa duk kuskuren da zai faru tsakanin ka dashi bazai tsaya bincike ba, hukunci kawai zai yanke cikin zafin rai, ni bazan taɓa zama silar kukan ki ba a rayuwata, sai dai na kasance miki silar dariyar ki, Allah ya tabbatar da alkairin dake cikin Soyayyar Hassan.”
Murmushi Falmata ta saki Daidai lokacin da suka iso cikin makarantar.
***********
Tun ɗazu ya karbo takaddar vacancy daga hanun Daddyn nasa, Darect gidan su DOCTOR ya nufa, a ƙofar gida ya tsaya tare da ciro wayarsa zai kira DOCTOR sai ga su Umma sun dawo daga unguwa, murmushi HABEEB ya saki tare da sunkuyawa ya gaishe da Umma, cikin fara’a Umma tace.
” Ikon Allah wa nake gani kamar Habibu.”
Dariya HABEEB yayi yace.
” Nine Umma.”
Aunty JALILA dariya tayi tare da cewa.
” HABEEB kana duniyar nan, ka manta damu haka ”
Murmushi ya saki tare da cewa.
” Aunty JALILA ai bazan taɓa mantawa dake ba a cikin rayuwata, yanda muka sha goyo da kuma kyautar kuɗin tara a hanunki.”
Dukkan su dariya sukayi Umma tace.
” To mu shiga cikin gidan ko, abokin naka ina ga yana ciki.”
Da to ya amsa tare da sakawa motarsa security suka shiga cikin gidan, Aunty JALILA nunawa HABEEB ɗakin DOCTOR yayi dake cikin sauron gidan, da Sallama HABEEB ya shiga ɗago kansa yayi yana murmushi ya amsa tare da cewa.
” Ka iso kenan.?”
Zama HABEEB yayi bakin katifar DOCTOR yace.
” Ehh gani kuwa, ina Saif ɗin.?”
” Saif yana hanya yanzu zai iso insha Allah, kun gaisa da Umma ne.”
” Ehh mun gaisa tare ma muka shigo da ita, amma zan kara shiga na gaisheta idan muka fita………………….”
Ki biya kuɗin ki kisha karatu cikin nutsuwa yafi miki sauƙi fiye da ki karanta abinda ba gumin ki ba, ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki, 08147537180.
*ALƘALAMIN UMMU NASMAH CE✍🏻*
[9/19, 10:57 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 49 to 50*
_________✍🏻 ” Okay shikenan, bari na sake kiran Saif ɗin naji yana inane haka har yanzu bai ƙaraso ba.”
Ya ƙarasa maganar yana ɗaukar wayarsa HABEEB cewa yayi.
” A’a barshi karka kirasa tunda yace maka ya taho kam, ai sai mu jirasa ko, yauwa HASSAN akwai tambayar da zan maka dan Allah.”
” Okay ina sauraranka.”
Cewar DOCTOR
” Ni kam wai Aunty JALILA har yanzun batayi Aure bane, naga sa’ar Aunty Suwaiban mune ita kuwa yanzu yaranta ma har huɗu.”
Ɗan shuru DOCTOR yayi, kafin cike da damuwa yace.
” Eh batayi Aure ba, har yanzu, ni kaina rashin Auren Aunty JALILA yana sani cikin tashin hankali, babu wanda ya taɓa zuwa yace yana sonta, sai da Baba ya nemo wani ɗan amininsa ya haɗasu har an musu baiko daga baya ya dawo yace ya fasa Auren, ita kanta Aunty kullum cikin damuwa take, hmmm kwanaki cemin tayi ita ta haƙura da Aure ta ciresa cikin ranta, da ina da yanda zanyi dana nemowa Aunty JALILA miji itama tayi Auren nan, ta shiga tarihi.”
Cike da tausayin ƴar uwar tasa ya ƙarasa magana, HABEEB cike da mamaki tare da al’ajabi ya furta.
” What!!!! Hassan da gaske kake min Maganar nan, Aunty JALILA ce ta rasa mijin Aure, kaico lallai maza basu san wanda zasu Aura ba, samun mace irin Aunty JALILA ai abune mai matuƙar wahala.?”
” Ƙwarai kuwa HABEEB Aunty JALILA har yanzu batayi Aure ba.?”
” Innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un allahumma ajirni fil musibati!!!! Yanzu Aunty JALILA ce ta rasa mijin Aure mace mai ilimi tarbiyya tare da cikakken zati, me Aunty JALILA ta ragu dashi tana da kyaun da namiji zai sota tana da tarbiyya, to meta gaza daahi za’a ƙita idan ba jarabawa ta Ubangiji ba kowa da yanda yake zarabtar sa, Tabbas ita kuma tata jarrabawar kenan, Hassan ina son na kawowa Aunty JALILA mijin Aure idan har zata yarda, saboda akwai wani uncle ɗina ƙanin momy na da yace Momy ta sama masa matar Aure, yayi Auren farko bai dace ba, ƙarshe ma dai sun rabu dashi da matar, suna ƴa ɗaya a tsakanin su, zamu tattauna da Momy insha Allah zaizo Wajen ta, sai dai sirri zamuyi da kai dan Allah karka sanar da Aunty JALILA nine na kawo mata miji nafi son yazo mata a shine ya ganta yake so, dan Allah ko Umma karka sanar da wannan maganar pls abokina.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya sauƙe tare da furta, harna rasa da bakin da zan maka godiya HABEEB idan kamin haka Tabbas bazan taɓa mantawa da kai ba a cikin rayuwata.”
Murmushi kawai HABEEB yayi Saif ne ya shigo da Sallama yana dariya tare da cewa HABEEB.
” Shegen gari wato dai ka samu duniya shikenan kuma sai ka manta da abokanka na yarinta.”
Dariya HABEEB ya saki tare da cewa.
” Muka manta da juna dai, Saif kana sha’aninka fa naga sai wani gurun wuya kake, baka jin wahalar karatu fa Malam Saif.”
Dariya Saif ya saki yace.
” Kai Malam ai wahalar karatu mu muke shanta kai kawai idan ana Sallah shuru ake ba’a magana Allah dai kawai ya mana jagora.”
Cikin dariya DOCTOR yace.
” Kaikam ai ka mana tun farko ka ɗauki fannin business ɗinka.”
Murmushi HABEEB ya saki tare d miƙawa DOCTOR takaddar vacancy yace.
” Congratulations zaku cike takaddar nan, insha Allah nan da One month jirgin ku zai ɗaga India idan kun cike sai ku maidawa Daddy dashi office zai saka hanu, Already dama shi gomna yasa nasa hanun.”
Cikin murna da farin ciki, DOCTOR da Saif suke godiya, sosai sukaji daɗin abin alkairi da HABEEB ya musu, HABEEB ne yace.
” Hassan wai ina mutumiyar ne kam, ya kamata fa na ganta kafin na bar gidan nan.”
DOCTOR bai kawo komai a ransa ba yace.
” Ta tafi islamiyya, amma may be kafin ka bar gidan nan zata dawo 1:00 zata kuma naga yanzu 12:30 .”
Murmushi HABEEB ya saki yace.
” Yarinyar tayi hundred pasent , ga hankali da nutsuwa uwa uba sakin fuska gata kuma kyakkyawa.”
Saif dariya yayi tare da cewa.
” Wace yarinyar wai kake Magana ne.”
Kallon DOCTOR HABEEB yayi yace.
” Sorry Hassan menene sunanta dan ban san sunan ba ”
Dariya DOCTOR yayi yace.
” Falmata ake kiranta dashi amma dai Asalin sunan Fatuma.”
Saif ne ya saki dariya mai sauti yace.
” Malam HABEEB ko dai kana ciki ne, naga kamar kana zancen tane da shauƙin Soyayya.”
Dam!!!! Dam!!!! Dam!!! Dam!!!!! Ƙirjin DOCTOR ya buga, cike da tashin hankali yake duban HABEEB yaji amsar da zai bawa SAIF shi kuwa HABEEB murmushi ya saki tare da cewa.
” Bakaji dai mutuwar sarki a bakina ba, ƙanwar DOCTOR ai nima ƙanwata ne.”
Wata irin ɓoyayyiyar ajiyar zuciya DOCTOR ya saki, yana godewa Allah cikin zuciyarsa, sun juma suna hira, har ƙarfe ɗaya sannan HABEEB ya tashi, tare suka shiga wajen Umma HABEEB ya sake gaishe ta DOCTOR ya sanar da ita alkairin da HABEEB ya musu na Vaccancy sosai Umma taji daɗi har sai da tayi hawaye, Aunty JALILA kuwa tafi kowa farin cikin samun cigaban ɗan uwanta.
Sun fito ƙofar gida HABEEB zai shiga mota shi da Saif zai sauƙesa a unguwar su sai shi kuma ya shige, sai ga Falmata da maji sun taho, HABEEB cike da tsokana yace.
” Hi!!! Ƴan mata.”
Falmata da Maji tare suka juyo, murmushi Falmata ta saki tare da kamo hanun Maji suka taho wajen nasu, murmushi Falmata ta saki HABEEB ya cewa Maji.
” Baiwar da ajinki da girmanki kike haɗa hanya da wannan ƴar ƙauyen haba kin bada ƴan Birni.”
Dariya Maji tasa tace.
” Cap amma lallai kaci bashi kuma dole sai mun rama, kana kallon ƙawara fine baby kake kiran ta da village girl, lallai taka zaƙewar tayi yawa amma ba komai akwai Ranar ƙin dillanci.”
Dariya HABEEB yayi yace.
” Ai kuwa bazaku iya ramawa ba sai dai ku rame, ina fine baby ai sai dai village baby, Gaishe ni kafin raina ya ɓaci.”
Gabaki ɗayan su dariya suka saka har DOCTOR Falmata kunkumi ta riƙe tace
” Naƙi na gaishe kam, ƙawata dan Allah dubi wannan baƙin baturen waini yake kira ƴar ƙauye, saboda kawai ya samu ya tafi ƙasar Cairo, to hir ɗinka malam ka dinga daidaita kalaman ka a kaina domin kana tsakiyar gata nane, idan muka so sai mu daka ka anan baka da mai tayaka.”
Dariya HABEEB ya saki yace.
” To shikenan ba komai naji mai gata, samin numbern ki a nan zan wuce sauri nake.”
Girgiza kanta Falmata tayi tace.
” No bazan baka ba, har sai YAYANA ya bani izini.”
Dariya HABEEB yayi tare da duban DOCTOR yace.
” To yayan mu bata izini.”
Dariya DOCTOR ya saki shima yace.
” My dear ƙanwata na baki izni.”
Dariya Falmata ta saki sannan ta basa numbern motar HABEEB da Saif suka shiga, yaja suka tafi Falmata da Maji ma suka shige cikin gida.
**************
Kwana uku da HABEEB ya basu takaddar Vaccancy DOCTOR ya gama cike nasa da Sallama ya shiga ɗakin mahaifiyar tasa, suna zaune ita da Baba, gefen ƙafar Baba doctor ya zauna tare da miƙawa Baba takaddar yace.
” Gashi Baba na gama cikewa duka, yanzu saura a mayar dashi office ɗin Daddyn HABEEB.”
Karɓa Baba yayi yace.
” Masha Allah Allah ya yi albarka, baza kaje kai ɗaya ba, dole tare zamu tafi sai na masa godiya, shima ai zaiji daɗi ai ko.”
Umma ce tace.
” Gaskiya kam hanne ya kamata, saboda jin daɗin kyauta akace godiya, sai kuje tare, na sanar da Dauda ma Maganar tafiya karatun Hassan ɗin nace ya sai da min da gonata ɗaya, sai mu sami abinda zamu basa ya riƙe a hanunsa, tunda ance tafiyar tasu nan da wata ɗaya ne.”
Baba cewa yayi.
” Masha Allah, naji daɗi sosai Yamuram kin ƙyauta wannan abinda kikayi nine ya kamata na masa shi a matsayina na mahaifinsa, ganin bani dashi yasa ke kika masa wallahi naji Allah ya miki albarka.
Shima kansa DOCTOR yaji daɗin hakan Tabbas yasan iyayensa suna sonsa Baba duban DOCTOR yayi yace.
” Ka tashi kaje gidan AJIRAM ka taho min da Fanna sannan ka sanar da ita alkairin daka samu.”
Da to DOCTOR ya amsa sannan ya tashi ya tafi.
Kawu Dauda kuwa zaune yake gaban Jummai yana zayyano mata zancen da Umma ta masa.
” Kai!!!! Kai!!! Ina bazai yiwu ba!!!! Ni za’a rainawa hankali, ɗana bai tafi India ba kai da ka fita samun gadon a matsayin ka na namiji, naka Duk ya hallaka ya bar nata wallahi matar nan asiri ta maka dukiyarka ta kaɗe nata kuma yana nan, shine yanzu zata sayar ta tura ɗanta India, to kuwa wallahi dole nima sai ƊANA MUSA ya tafi India karatu, kuma da dukiyar tata.”
Kawu Dauda ce mata yayi.
” A’a fa Jummai ba da dukiyar ta zata kaisa karatu ba, tace min baban Abokin Hassan ya basa tallafin karatu na gomnati tace wai idan ta sai da gonar zata basa abinda zai riƙe a hanunsa ne saura kuma zata bawa mijinta yayi jari.”
” To karya take maka babu wani jarin da zata bawa mijinta yayi, ƙarya ne, da wannan kuɗin zata fitar da ɗanta karatu, ba dai gona ɗaya tal tace ka sayar ka bata kuɗin ba, na baka izni kaje ka sayar ka bata kuɗin, amma daga yanzu baza’a ƙara bata ko mai ba, daga yau sauran dukiyar ta ya dawo damu zamu sayar da su duka mu kai Musa karatu shima ƙasar waje, saura kuma muyi gini mu ƙaura mubar laka.”
Da sauri kawu Dauda ya ɗago ya kalleta Tare da cewa.
” Taya haka zata kasance mu cinye dukiyar ta, kina tunanin zata yarda ta barmu ne.”
” Dolen ta haƙura ta barmu ko tana so ko bata so zan iya aikata komai akan wannan dukiyar, dan haka ka barni kawai da ita…………………….”
Ki biya kuɗin kisha karatu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali yafi miki sauƙi fiye da ki karanta abinda ba gumin ki ba, ki min magana ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*UMMU NASMAH ce*✍🏻
[9/20, 10:26 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 51 to 52*
___________✍🏻 ” Jummai ina tsoron abinda zai shiga tsakanina da ƴar uwata, bana son mu samu saɓani da ita, tana kawar min da kai akan duk wani abinda zan mata na rashin daɗi, tana sona sosai, ya kamata mubar mata dukiyar ta haka dan Allah Jummai karmu kaita bango.”
Wani irin mungun kallo Jummai take bin Kawu Dauda dashi kanta kawai ta kaɗa tare da ficewa ta bar gurin amma cikin zuciyarta ita kaɗai tasan mungun zaren da take saƙawa, Kawu Dauda tagumi ya rafka cike da damuwa cikin zuciyarsa yana jin baya son abunda Jummai take sakasa yake yiwa ƴar uwarsa sai dai yana kasa ƙin bin umarninta, ya daɗe cikin wannan nazarin Kafin daga baya ya kishingiɗe.
HABEEB a matuƙar gajiye ya shigo cikin Part ɗin Momy a kujera ya zube, babu kowa cikin falon sai Wasila, dubansa tayi ta ƙasan ido tace.
” Sannu da shigowa ”
A daƙile HABEEB ya amsa mata da.
” yauwa sannu.”
Murmushi Wasila ta saki tace.
” Wani abin yakan bani mamaki, yanda ɗan Adam yake gujewa mai sonsa da gaskiya, hmmm!!! Da zuciyarka tana da hangen nesa da kuma lissafi na Tabbata bazata kaucewa Soyayyata ba, domin kuwa ta sani cewa duk duniyar nan babu wanda ya kaini sonka sai dai kash Zuciyarka ta bijirewa alƙibilar ka ta gaskiya ta karkata hanyar da bata da ɓullewa, da zan baka shawara da nace ka umurci zuciyarka da tayi gaggawan dawowa zuwa ga masoyiyarta ta gaskiya domin kuwa hakan ne kawai samun salamar ka.”
Duk Abinda take faɗa HABEEB yana sauraronta cike da mata kallon baki da hankali, sanda ta gama ya saki wata ƙaramar dariya kafin yace.
” Babu abin mamaki domin kuwa hakan tasha faruwa a duniya, babu amfanin tilastawa zuciya son wanda babu shi a cikinta domin kuwa shi so makaho ne, inda yake so nan kawai yake kallo, na godewa Allah da zuciyata bata zamo mai hangen taki zuciyar ba, saboda rayuwata da taki sam ba ɗaya bane bana fatan Ubangiji ya jarabceni da Auren mace Irin ki, hmmm!!! Shin kina tunanin bansan irin mugayen ayyukan da kike aikatawa bane, ko bansan ke fasiƙar ɓoye bace mai fuska biyu ki ɓoye sharrinki ki bayyana alkairin ki, to nasan komai a kanki kallon ki nake tar da waɗannan idanun nawa, dan haka ki daina alaƙanta ni da mace marar daraja da kamun kai irinki uwata gari nake nemawa ya’ya na, ba irin ki ba.”
Wani irin bugawa zuciyar Wasila tayi, ta ya HABEEB yasan tana wannan harkar bayan a boye take yunsu, amma tsabar iya bariki na Wasila sai ta waske tare da cewa.
” Tabbas kayi namujin ƙoƙari wajen bibiyar lamurana, ko banza hakan ya nuna min cewa ka damu dani, na yadda ni karuwace, amma dai kana sane da cewa suma karuwan suna istibira’i a Aure su, dan haka ai kaga KARUWANCI na bai haramta Aure a tsakanin muba, Tabbas ina cikin duhu mai tsanani, Soyayyar kane kawai zata iya sauyani daga baƙi zuwa fari, cigaba da nuna min ƙiyayya kuma shi zaisa na ƙara dulmiya cikin wannan duhun da nake ciki, zan iya sauya wa na tuba na koma ga Ubangiji na muddun ka yadda da Soyayyata, ruwan kane ka ceto ni ko ka barni cikin duhu!!!.”
Ta ƙarasa Maganar cikin sauti mai ƙarfi, murmushi HABEEB ya saki tare da cewa.
” Hmmm!!! Kaji wani kwaɗo wai mutum tsaftacacce ake neman dole sai ya haɗu da ƙazan ta, idan banda toshewar basira irin taki ta ina wannan zai yiwu, hmmm!!! Ai kin mankaro tunda har kika faɗa cikin hallaka Tabbas ke abin ƙyamace a cikin al’umma domin kuwa duk wata darajar ki ta zube kin gama kasa mutuncin ki a tire kin sayar maza da yawa sun kwasa waya sani ma ko kin kwaso wata cutar, taya ma kike tunanin cewa mutum mai kima da daraja zai ɗauki mace Irin ki sharar layi bular kowa, tabbas tuban da badan Allah ba ba tuba bane, shi ake kira da tuban muzuru, malama idan zaki tuba saboda Ubangiji ki tuba, karki tuba saboda wani bawansa ko dan buƙatar ki, ki cireni cikin jagorar tuban ki domin kuwa bani da hurumi a cikin sa, idan har nine wanda zanyi sanadin tuban ki, to kuwa Tabbas zaki mutu cikin baƙin duhun da ko tafin hanunki bazaki taɓa gani, ki tuba dan Allah hakan shine samun tsirarki.”
Wasu hawaye ne masu ɗumin suka zubowa Wasila, cike da ɓacin rai tace.
” Tabbas na fahimci irin girmar ƙiyayyar da kake gwada min, amma kuma ka sani bazan taɓa iya cire Soyayyar ka a raina ba, dole sai ka aureni kota halin yaya.”
Tana gama faɗin haka ta haura sama da gudu tana hawaye, Kusan karo ta kusa yi da Momy dake sauƙowa daga step ɗin, gefe Momy ta matsa mata tana cewa.
” Ke Wasila lafiyar ki kuwa kukan me kike haka.”
Wasila bata kula Momy ba ta haura da gudu, ajiyar zuciya Momy ta sauƙe tare da sauƙowa tana bin HABEEB da kallon tuhuma, zama tayi a ɗaya daga cikin kujerun dake falon tare da jefawa HABEEB tambaya.
” Meya haɗaka da Wasila naga alamun yanzu duk sanda kuka haɗu sai ta wuni cikin damuwa, meyake faruwa a tsakanin ku.”
Zaro ido HABEEB yayi tare da cewa.
” Ni Kuma Momy me zai haɗani da Wasila, nima fa yanzu haka na shigo na sameta tana wannan kukan, tambayar ta nake meya sameta shine fa ta haura sama da gudu ko amsa bata bani ba.”
Taɓe bakinta Momy tayi tace.
” To sabon maƙaryaci ai kai ƙaryar ma baka iya ta ba, kaga baka taɓa min ƙarya ba, karka fara yau.”
” Momy da gaske nake miki ki tambayeta mana kiji, ni Momy yunwa ina abinci na.”
” Yana Part ɗinka an kai maka tun ɗazu.”
” Okay Momy tunda kin kasa samawa Uncle Ɗalladi mata, ni na samo masa kuma Allah Momy macece ta gari wanda kowa zaiyi alfahari da ita idan ya sameta a matsayin mata.”
Dariya Momy ta kwashe dashi tace.
” Ikon Allah, yau ga ɗa da samawa ubansa Mata, to Shikenan ina ne gidan su yarinyar, meye kuma sunanta, zan turasa yaje ya ganta idan ta masa shikenan sai muyi musu fatan alkairi.”
Dariya HABEEB yayi ya tashi da gudu ya rungume Momy kiss ya manna mata a goshi ya koma ya zauna tare da faɗin.
” Thank so much Momy, Auntyn HASSAN maman su ɗaya sunanta JALILA.”
” Okay yayi kyau Allah ya tabbatar da alkairi.”
Da ameen HABEEB ya amsa tare da tashi ya fice zuwa Part ɗinsa, ajiyar zuciya Momy ta sauƙe bayan ficewar ɗannata, ta fuskanci Wasila son HABEEB take tun ba yau ba, sai dai a yanda ta fuskanci HABEEB kwatakwata babu Soyayyar Wasila cikin ransa, hmmm!!!! ” Allah ka zaɓa musu alkairi a cikin lamarin su, idan akwai alkairi tsakanin su ka sawa HABEEB Soyayyar Wasila idan kuma babu Allah ka fitar mata da soyayyarsa a cikin ranta.”
Ta ƙarasa addu’ar tana ɗaukar remote ta kunna sunnah tv.
***********
” DOCTOR na saura wata ɗaya ka tafi India, bana son ka tafi ba tare da gida ansan Soyayyar da ke tsakanin muba, kaga shekara bakwai zakayi ba lallai abarni nayi jiranka har shekara bakwai ba, gara kawai kafin ka tafi a ɗaura mana Aure ni zanyi jiran dawowarka da Auren ka a kaina.”
” Hakane amma ki ɗan saurara kaɗan a gama cuku-cukun tafiyata tukunna idan mun gama insha Allah a cikin sati biyu sai mu taso da Maganar Auren namu.”
” Shikenan Allah Ya kaimu.”
” Ameen ki tashi ki shiga cikin gida, saboda kin juma cikin ɗakina.”
Tashi Falmata tayi zata fice taji DOCTOR ya riƙo hanunta tare da cewa.
” Karki rabu dani komai tsanani komai wahala, dan Allah ki zauna dani, zan riƙe na riritaki tamkar ƙwai, koda wasa bazan taɓa barin hawaye su zuba daga cikin idanunki ba, dan Allah kimin alƙawarin zama har abada tare dani ina son mutuwa ce kawai zata shiga tsakanin mu.”
Cikin sanyin Murya Falmata ba tare da ta juyo ba tace.
” Zan zauna dakai komai tsanani komai wahala, bazan taɓa guje maka ba, ko da mutuwa ce zanyi fatan ta ɗauke mu lokaci ɗaya, a sallace mu tare a binne mu a maƙwaftan juna, ga kabari na ga naka, kamin alƙawarin bazaka taɓa rabuwa dani ba, zakayi haƙuri da duk wani kuskuren da zan maka ina son ka kasance mutum mai uzuri a gareni, ni kuma nayi alƙawarin jure duk wata wahalar da zansha a dalilin ka.”
” Na miki alƙawarin zan zauna dake komai tsanani komai wahala bazan taɓa guje miki ba, zan zauna dake har ƙarshen Rayuwata zan miki uzuri Kamar yadda zanyiwa kaina uzuri ina sonki Falmata ina sonki kece farin ciki na sannan kuma hasken idanuna, kece jagorata a rayuwa, i love You.”
Ya furta tare da sake mata hanu yana sakin murmushi tare da tsantsar shauƙin Soyayya.
” Tabbas nayi dacen samun masoyi wanda zai kasance cikin haska min rayuwata, na Tabbata daga yau nayi bankwana da duk wani duhu a cikin rayuwata domin kuwa Ubangiji ya aiko min da haske mai haska min dukkan wasu lamurana , I love You too.”
Ta ƙarasa maganar tana ficewa fuskar ta cike da annuri murmushi shima ya saki yana jin tamkar ya rungumota jikinsa, Falmata cikin gidan nasu ta shige, a tsakar gida ta samu BULAMA yana zaune, kujera ƴar tsugunne Falmata ta jawo ta zauna kusa da kakan nata.
” BULAMA iska kake shane ina kabar fadar taka.?”
Murmushi Bulama ya saki yana shafa kanta duk cikin jikokinsa yafi jin ƙaunar Falmata yarinya ce mai hankali da nutsuwa gashi kuma ko yaushe takan zuwa ta zauna dashi suyi fira.
” Fatuma yanzu zan fita, ina ɗan shan iska ne, ya naga sai murmushi kike, ko dai akwai labari ne.?”
” Eh BULAMA akwai labari, albishir nazo maka dashi, na sami mijin Aure ya kusa bayyana muku kansa kwanan insha Allah, mutumin kirki ne ɗan Asali wanda yasan darajar manya, Bulama dan Allah idan ya iso gareku ku karɓe sa ku basa aurena dan Allah Bulama kamin wannan gatan ka bani wanda nake so.”
Murmushi BULAMA ya saki yace.
” Mai zai hana mu baki abinda kike so muddun ya cika sharuɗan daya kamata a basa Aure, karki damu idan har kin yadda da ɗabi’un sa.”
” Na yadda da ɗabi’un sa, Bulama.”
Murmushi Bulama yayi tare da tashi yana ƙoƙarin fita waje yace.
” To karki damu nama bashi ke.”
Dariya Falmata ta saka cike da farin ciki ta shige Bedroom ɗin Aunty YANA.
***********
Bayan sati biyu
HABEEB da SAIF ne zaune a cikin motar HABEEB Saif duban HABEEB yayi yace.
” Yaushe zaku koma school ne, naga ka juma sosai a ƙasar nan.?”
” Mun koma ai tun Sati biyu da suka wuce nine kawai ban koma”
Cike da mamaki Saif yace.
” Meya hanaka komawa, bayan kasan yanzu ne first tearm da za’ayi karatu sosai.”
” Mtsss!!! Koda na koma ba lallai na samu nutsuwar karatu ba, saboda ina da tarin damuwa a cikin raina, SAIF na kamu da Soyayya kuma na kasa furtawa wacce nake sonta soyayyata, a gefe guda kuma ga wata masifar da take neman shige min jikina, wallahi wata ƴar uwata ne, ƴar ƙanwar Momy na, ta addabeni wai ita lallai tana sona ni kuwa babu Soyayyar ta ko kaɗan a raina, amma wallahi taƙi bari na, na furta mata bana sonta, amma taƙi yadda ni wallahi tsorona kar wannan abin ya shiga tsakanin zumuncin iyayen mu.”
Kaɗa kansa Saif yayi cike da jinjinawa lamarin kafin Saif yace.
” Tabbas dole ka rasa nutsuwar ka, amma ni shawarar da zan baka shine, na farko ita wannan ƴar uwar taka kayi ƙoƙarin ganin ka fahimtar da ita cikin lumana ku rabu lafiya da ita, karka mata da zafi ka bita da sanyi sai ku rabu lafiya, sannan ita wacce kake ya kamata ka cire shakka cikin ranka kaje ka furta mata Soyayyar ka, kar kayi sake wani ya riga ka shiga zuciyarta.”
” Saif ba wata bace yarinyar da nake so, illa ƙanwar Hassan Falmata, wallahi Saif tun Sanda na fara ganin wannan yarinyar na saka a Raina na samu matar Aure amma ina son na fara neman izinin iyayenta kafin na furta mata Soyayyata hakan shine neman Auren daya halatta a cikin Muslunci, idan sun mata miji kuma zanyi ƙoƙarin ganin na haƙura, saboda haramunne neman Aure a cikin neman Aure, haka kuma idan tana da wanda take so nan ma zan bawa zuciyata hkr, domin kuwa bazan tilasta mata ta soni dole ba, na bakantawa zuciyarta dannawa zuciyar ta faranta, gara na barta da farin cikin ta.”
” Ba’a mijin Aure ba, indai Falmata ne, kuma bana tunanin akwai wanda take tsayuwa dashi, na Tabbata Falmata zata soka domin kuwa kana da kyawawan ɗabi’un da za’a soka, daga nan babu inda zamu tsaya sai wajen BULAMA ka nemi izininsa sannan kaje ka nemi Soyayyar Falmata na Tabbata zaka samu………………….”
Biya kuɗin ki Yar Uwa kafin ki karanta karki karanta min littafi ba tare da kin biya ba, ki neme ni domin biyan kuɗin ki 08147537180
*UMMU NASMAH CE✍🏻*
[9/21, 1:33 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 53 to 54*
________✍🏻 ” Saif wannan maganar taka ta ɗan bani ƙarfin gwiwwa amma sai dai zuciyata tana tsinkewa sai nake ji kamar Falmata tafi ƙarfi na, amma ba damuwa muje na kwatanta.”
Murmushi SAIF ya. Saki tare da cewa.
” Muje Insha Allah kana tare da nasara Abokina, taya Falmata zata fi ƙarfin ka dame ta fika nasaba ko arziki, kaga ka daina shakku muje kawai angon Falmata.”
Shima HABEEB dariya yasa yace.
” Harna zama angon kenan, ɗazu na kira numbern HASSAN baiyi picking ba.”
” May be ko baya kusa da wayar ne, kasan fa shi mutum ne mai barin waya ma ya fice.”
Jan motar HABEEB yayi suka nufi unguwar su DOCTOR, a ƙofar gidan sukayi parking, HABEEB Tunda ya tsaya a ƙofar gidan yaji zuciyarsa tana tsinkewa, amma ya daure duban Saif yayi tare da cewa.
” Saif na sake shawari, bai kamata mu fara zuwa ga iyayenta ba, har sai mun fara jin ra’ayin ta a kaina.”
Girgiza Saif yayi yace.
” No HABEEB wajen iyayenta ya kamata ka fara zuwa domin shine matakin farko na neman Aure a Muslunci, su zasu baka izinin kaje ka nemi Soyayyar ta, daga nan idan kun daidaita fine.”
” Shikenan muje to yanzu wajen Kakan nata zamuje kenan.?”
” Ehh wajen sa zamu may be ma yana cikin fadar sa.”
Ya ƙarasa maganar suna nufar fadar, da Sallama suka shiga yau babu ko sai Baban DOCTOR, da kuma Mahaifin Falmata, murmushi saif ya saki cikin zuciyarsa yana cewa sunzo a dace, zama sukayi tare da kwasan gaisuwa BULAMA ne yace.
” SAIFUDDEEN yau kaine ka kawo min hira kenan.”
Murmushi SAIF ya saki yace.
” Allah yaja da ranka BULAMA, Wannan Abokin nawa shiya kawo ni, baka ganesa ba ko.”
Jinjina kansa Bulama yayi yace.
” Ƙwarai kuwa ban shaidasa ba.”
” Shine wanda mahaifinsa ya bamu scholarship na karatu da zamu tafi ƙasar India.”
Murmushi Baba yayi kasancewar shiya shaida HABEEB BULAMA cewa yayi.
” Masha Allah abu yayi kyau sannu samari Allah ya maka Albarka.”
Murmushi shima HABEEB yayi tare da cewa.
” Ameen na gode.
Ya faɗi tare da yin shuru, Ganin HABEEB yayi shuru yasa Saif cewa.
” BULAMA abokina ya kasa Magana to bari dai na ari bakinsa na ci masa albasa”
Murmushin manya Bulama ya saki tare da cewa.
” Umhum Kai Habibu damo ne sarkin rashin magana ko, to kai kuma SAIFUDDEEN Aku sarkin Magana, ci masa albasar muji.”
Gabaki ɗaya dariya fadar ta ɗauka har su Baba sai da sukayi dariya cikin dariyar Saif yace.
” Bulama HABEEB Falmata ya gani yake so, shine yace bazai fara tsayuwa da ita ba har sai ya nemi izini daga wajen ku.”
Murmushi Bulama ya saki tare da cewa.
” Kaji ja’irar yarinya, ɗazun ta sanar dani cewa mijin da take so ta aura ya kusa zuwa wajena, har take roƙona da idan yazo na bashi Auren ta, ashe kaine.”
Murmushi Baba ya saki tare da cewa.
” Masha Allah Habibu abu yayi kyau ai kai ba mutumin da za’a hana Auren Falmata bane idan har kun daidaita ka turo mana iyayenka kawai.”
Wani murmushin farin ciki, HABEEB ya saki wato ma Falmata ta fuskanci yana sonta, shine har ta sanar da Bulama zaizo murmushi ya saki daidai lokacin da DOCTOR ya shigo fadar, sakamakon ganin takalman su Saif kusa da HABEEB ya zauna, zaiyi Magana kenan yaji muryar Bulama yana faɗin abinda yafi ƙarfin kansa.
” Idan dai nine na baka aure Falmata iyayen ka kawai nake buƙatar gani.”
DOCTOR dam dam ƙirjinsa ya buga a matuƙar har zuƙe yace.
” What!!! Bulama wacce Falmata, wa ka bawa Auren ta.”
Cike da nutsuwa Bulama yace.
” Falmata dai ƙanwar ka, na bawa Habibu Auren ta.”
Miƙewa tsaye DOCTOR yayi cike da ɓacin rai take idanunsa sukayi ja, duban HABEEB yayi yace.
” Dama dalilin kenan da yasa ka bani Vaccancy domin ka siye iyayena, ashe dama ba dan Allah ka bani saboda ka samu Falmata yasa ka bani, to ka buɗe kunnenka da kyau kaji, Falmata ba matar auren ka bace, Falmata matata ce, ni kaɗai ne wanda Falmata take so, dan haka ka fita a harkar ta, zan dawo maka da Vaccancy ka bana so, Falmata tafi min komai a rayuwata, sannan maganar Aunty JAL……………..”
Marin da Baba ya ɗauke sa dashi ne yasa DOCTOR kasa karisa maganar da zaiyi, HABEEB a matuƙar razane tare da mamaki yake bin DOCTOR da kallo cike da kuma mamaki shima SAIF kallon mamakin yake bin DOCTOR dashi Baba Magana ya fara cikin ɓacin rai.
” Uban waye zai baka Aure, me kake dashi meka ajiye wata sana’a kake dashi wanda za’a dauki yarinya a baka, har kake faɗa masa magana mutumin daya maka alkairi kamata yayi ka tausasa kalaman ka a kansa ba ka zafafa ba, bazamu baka Auren Falmata ba shi zamu bawa domin kuwa ya fika hanyar da zai ciyar da ita dan haka ka cire Falmata a cikin ranka babu wanda zai baka Auren ta, idan kai mahaukaci ne mu muna da hankali.”
Bulama ɗagawa Baba hanu yayi tare da cewa SAIF.
” SAIFUDDEEN tashi ka shiga cikin gida ka kira min Falmata.”
Tashi Saif yayi ya shiga cikin gidan, shi kuwa har yanzu kallon mamaki yake bin DOCTOR dashi ko a mafarki bai taɓa zaton Hassan zai faɗa masa magana son ransa ba, Baba Bukar duk abinda ake yana zaune yayi shuru baice komai ba, shi kuwa DOCTOR sai famar ajiyar zuciya yake yana huci ji yake tamkar yaje ya shaƙo wuyan HABEEB, SAIF tare suka shigo da Falmata zama sukayi, BULAMA ya dubi Falmata yace.
” HABEEB yazo min da Maganar yana sonki, shima Hassan ɗan uwanki ya ce kuna Soyayya, shin da gaske ne kina son HASSAN.”?
Falmata Kanta na ƙasa ta ɗagawa Bulama kai alamun ehh.
Shuru Bulama yayi tare da cewa.
” Duk ku tashi kuje zuwa zan nemeku daga baya.”
HABEEB murmushi mai ciwo yayi tare da cewa.
” A’a BULAMA, ba sai an sake zama ba, ai Falmata ta gama yanke hukunci ku barta da zaɓinta, Allah yasa haka shi yafi alkairi.”
yana faɗin haka ya tashi fice da sauri, Saif mungun kallo ya jefawa DOCTOR ya tashi yabi bayan HABEEB, DOCTOR yana huci shima ya fito, har HABEEB zai shiga mota yaji muryar DOCTOR a bayansa yana cewa.
” Ka dakata na ɗauko maka Vaccancy ka, domin kuwa nafi ƙarfin ka siye ni baka da wannan kuɗin, idan na kawo maka Vaccancy ka karna ƙara ganin ka a ƙofar gidan mu.”
Murmushi HABEEB ya saki zuciyarsa na suka ya juyo ya kalli DOCTOR da idanunsa da sukayi ja yace.
” Ban taɓa kyauta da biyan buƙatar kaina, ina yine dan Allah da kuma zaman tare, da tun farko nasan kana Soyayya da Falmata dana danne tawa Soyayyar na bawa zuciyata hkr, ya kamata ka dinga tunani kafin ka furta magana, insha bazaka ƙara gani na a ƙofar gidan nan ba, bare kuma kamin korar kare, Vaccancy na baka shine dan Allah dan Allah bazan karɓa ba, idan baka so ka yaga ka zubar, sannan naji kana son kayi Maganar Aunty JALILA ko, to ka sani bazan fasa niyyar alkairi ba saboda da kai.”
Sosai jikin Falmata yayi sanyi da take tsaye a gefe tana kallon su, ƙarasowa tayi a hankali kusa da HABEEB tsawa DOCTOR ya daka mata yace.
” Uban me zakije kiyi a wajen sa, karki ƙara taku ɗaya idan kuma ƙara hmmm.”
Ya ƙarasa maganar yana ƙaɗa mata, Falmata tsayawa tayi a inda take cikin sanyin muryar ta tace.
” Kayi hkr HABEEB ban kina dan baka cancanta ba, Tabbas ka cancanta a soka mutum ne mai shiga ran duk wanda yayi mu’amala da kai, sai zuciyata ko kaɗan bakai take so ba DOCTOR shine wanda zuciyata take so, bana jin zan iya rayuwa da wani namiji idan ba shiba, kayi hkr insha Allah zaka samu macen da tafini komai, idan rana ta faɗa na Tabbata gobe wata zata fito wacce tafi ta jiya haske .”
Murmushi mai ciwon gaske HABEEB yayi yace.
” Falmata ai rana ta riga ta faɗi.”
Ya ƙarasa maganar yana shigewa cikin motar ya jata da ƙarfi……………”
Kuyi hkr ban samu nayi Editing ba yau.🤲🏻
Ki nemeni domin biyan kuɗin ki, yafi sauƙi akan ki karanta abinda ba halak ɗinki ba 08147537180.
*UMMU NASMAH ce*✍🏻
[9/22, 1:16 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 55 to 56*
_________✍🏻 Saif a zuciye ya juyo yana yiwa DOCTOR mungun kallo cikin ɓacin rai ya fara magana.
” Sai kaji daɗi a zuciyar ka da wulaƙanta mutumin daya maka alkairi, wai har HABEEB kake kora a wannan ƙofar gidan naku na laka wanda ya fito a gidan Ac da Ac, ka bani mamaki ko kaɗan HABEEB bai cancanci wulaƙanci daga gareka ba, mutumin da yake ƙoƙarin ciroka daga rana ya mai dakai inuwa shine kake ƙoƙarin turawa Rana, na rantse da Allah da HABEEB yasan kana Soyayya da Falmata da bazai bayyana soyayyar sa ba, zai dannesa koda kuwa zai masa illa, haka kuma yanzu daka sanar dashi a cikin mutunci da kwanciyar hankali zai haƙura ya janye shine ka sanar dashi cikin baƙar zuciyarka da zafin rai.”
Cike da zuciya DOCTOR yace.
” Oh laifina ma kake kallo dan kawai na faɗi iya gaskiyata karya nayi ba saboda ita ya bani Vaccancy ba, idan kai ya saye ka da wannan banzan takadar ni bai isa ya sayi Soyayyata ba, kuma na faɗa masa karya kuskura ya ƙara tako ƙofar gidan nan tunda ba kofar gidan ubansa bane, juyowa yayi yana nuna Falmata da yatsa yace, ke kuma ko da wasa kika kuskura ya ƙara kiranki ko a waya ne kika ɗaga, ko kuma ya ya tsaida ke a hanya kika sauraresa wallahi zan haƙura na barmishi ke, ki shige ki tafi cikin gida.”
Ya ƙarasa Maganar cikin tsawa , Falmata da sauri ta shige cikin gidan har jikinta yana rawa cike da tsoron sa, SAIF girgiza kansa yayi kafin yace.
” Da kyau uban ƴan masu zuciya, ka kyautawa kanka daga wulaƙanta mutumin daya taimake ka, amma ka sani wannan zafin zuciyar taka ka rage ta idan ba haka ba wata rana sai ta kaika ga danasani, annabin rahama shi kansa ya hanemu da saurin fushi, amma kai shine sana’ar ka, ina tausayin ranar da zata zo maka kana cizon yatsa kana danasanin wannan zafin zuciyar taka.”
” Mtsss wannan Kuma damuwar kane Saif, amma ni dai na sani bazan taɓa dana sani ba, a cikin rayuwata.”
” Haka kace, amma ni dai na sani muddun baka ajiye wannan baƙar zuciyar taka ba, har kuka sai tasa, ka riƙe wannan zaka tunasa koda lokacin bana raye zaka ce SAIF ya faɗa maka ”
Yana gama fadin haka ya juya tare da barin kofar gidan, DOCTOR tsuka yaja cike da ƙunar rai shima ya shige cikin gidan, Part ɗinsu ya nufa ai kuwa ya gwammace bai shiga ba domin kuwa Baba ya samu yana ta masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba.
” Wai yaron nan ni yake so ya raba zumunci da ɗan uwana, idan ba haka ba, ina yake da hanyar Aure, dame zai ciyar da matar wani sana’a yake dashi bayan zaman banza, tun yaushe nake binsa akan yake biyoni kasuwa yaƙi, shine yanzu zaice Aure uban wa zai ɗauki yarinyar ya baka ba sana’a gareka ba, kwana biyu ka saketa ka lalata mana zumunci, to wallahi kayi kaɗan ka shiga tsakanina da ɗan uwana dan ubanka, kasan kana son Auren uban me ya hanaka sana’a ka tara kuɗi, to wallahi ka fita a cikin idona na rufe, idan ba haka ba sai naci maka mutunci shasha marar mutunci.”
Daga Umma har Aunty JALILA shuru sukayi, suna sauraron Baba FANNA dake gefe ta zubawa Baba ido cike da tsoro domin kuwa bata taɓa ganin yana faɗa ba, DOCTOR cewa yayi.
” Amma Baba ina ruwan Aure da sana’a karatu fa nakeyi kuma da zarar na gama dole zan samu aiki babu wanda ya taɓa karatun likita ba tare daya fito da aikin sa ba, kuma in abinci ne, ko a gidan nan Umma zata bata taci, dan Allah Baba karka shiga tsakanina da soyayya ta, ka zame min uba mai adalci wanda zai goyi bayan abinda ɗansa yake so bai kamata ka dinga ƙoƙarin dole sai ka rabamu ba tunda Aure zamuyi ba zina ba, amma sai………”
Ɗaukesa da mari da Momy tayi shiya hanasa ƙarisa Maganar.
” Uban naka kake faɗawa magana yanda ranka yake so ba tare da ka taunata ba, saboda baka da nutsuwa a jikin ka, duk acikin maganganun ubanka wannene yayi ƙarya sana’ar kake dashi koni nan ban goyi bayan a baka auren Falmata ba, yarinyar da bata da tashin kaje can ka dinga cutar ta da wannan baƙar zafin ran naka da idan ka tashi zuciyarka ce take jagorantar hankalinka, fita kabar min gida na shasha ”
Cike da tuƙuƙun baƙin ciki da zafin rai DOCTOR ya fita yana huci, shima baba cike da ɓacin rai shima Baba ya shige ɗakin sa, Aunty JALILA ne ta dubi Umma da ranta yake ɓace tace.
” Umma tun kwanaki na faɗa miki, akwai Soyayya tsakanin Hassan da Falmata, ki musa min, dan Allah Umma ki rarrashi Zuciyar Baba ya barsu suyi tunda suna son junan su, Umma tun Falmata tana zanin goyo Hassan yake kaunar ta, karki manta da wani sa’in har goyon ta yake, meyasa zaku karya musu zuciyoyin su.”
Cike da masifa Umma ta nuna Aunty JALILA da yatsa.
” Kingan ki, ki fita a cikin idona, idan ba haka ba zanci miki mutunci, dake ke duk abinda Hassan zaiyi akan daidai yake a wajenki, abunda muka hango ke bazaki hango sa ba saboda tunaninki bai kan can Hassan da Falmata ba su dace da zaman Aure ba, saboda zafin ran Hassan yafi ƙarfin jikinsa da hankalin sa, bazai iya haƙurin zama da mace ba, shi kuma Aure dole sai da haƙuri komai tsananin Soyayya idan babu hkr bata taɓa ɗaurewa, nina haifi Hassan nafiki sanin waye shi, zafin ransa tun yana jaririnsa yake tare dashi, abin a jininsa yake, wani sa’in ko nono ne ban basa da wuri ba, idan ya zuciya, bazai sha nonon ba, zai cutar Falmata muddun suka samu saɓani, badan bashi da sana’a bane naki a basa Auren Falmata a’a saboda zafin ransa, sana’a ina da kuɗin da zan basa yaja jari dashi ko nawa ne, amma bashi nake tsoro ba zuciyarsa da kuma zumunci.”
” Amma ai Umma naga tunda yana sonta bazai Mata zafin ran………. ”
” Ya isa haka karki kuma cemin komai ban son ji.”
Shuru Aunty JALILA Tayi cike da jin haushi, shi kuwa DOCTOR Tunda ya shiga ɗakinsa ya kwanta yayi shuru, cike da ɓacin rai da tunani, wai shine bashi da sana’a tsuka yaja tare da yin juyi, yana ƙara jin haushin HABEEB da tsanarsa a cikin ransa meyasa ma bai masa shegen duka ba ya barsa ya tafi salin alin, yazo ya jawo masa tashin hankali.
Bulama kuwa, Hajja ya zayyanewa halin da ake ciki, cike da tashin hankali Hajja tace.
” Baban Mala bazai yiwu ba, ban Yadda a haɗa wannan Auren ba, bana son Auren zumunci saboda lalacewar zumunta, bare kuma auren zumuncin ma da Hassan mai baƙar zuciyar tsiya, bazai yiwu ba, tun wuri ka sanar dasu su haƙura da juna ”
” Hajja Mairo nima kaina bana son wannan Auren amma abinda na fahimta yaran nan suna son junansu sosai, shine matsalar, amma gobe da safe zan haɗa su a waje guda domin dakatar dasu.”
” Da kuwa hakan zaifi gara kawai a kawo ƙarshen wannan Soyayyar tasu dan wallahi bazai yiwu ba, kasan halin Hassan ba daɗi garesa Zuciyarsa tafi ƙarfin tunaninsa, itace take juyasa ba tunaninsa ba, bana son muyi la’akari da soyayyar su, nafi so muyi la’akari da cigaban zumuncin mu, kar mu biye musu muzo muna danasani daga baya, saboda shi Aure dole akwai saɓani.”
” Karki damu Hajja Mairo insha komai zai tafi daidai.”
” Shikenan Allah ya mana jagora.”
**************
Cikin mutuwar jiki da sanyin jiki ya shigo cikin gidan, gefen Momy ya zauna tare da ɗaura kansa a kafaɗarsa runtse idanunsa yayi yana jin zafin maganganun Hassan, yayin da Maganganun (kayi hkr HABEEB ban ƙika dan baka cancanta ba, tabbas ka cancanta a soka mutum ne kai mai shiga ran duk wanda ya zauna dakai, sai dai zuciyata ko kaɗan ba kai take so ba, DOCTOR shine wanda ta juma da zaɓa a matsayin masoyi bana jin zan iya rayuwa da wani NAMIJI idan ba shiba kayi hkr insha Allah zaka samu macen da ta fini komai, idan rana ta faɗi yau na Tabbata gobe ma wata zata fito wacce tafi ta yau haske.)
Ajiyar zuciya ya sauƙe hawaye ne suka gangaro daga idanunsa yayi saurin gogewa, Momy duk tana kallon sa, cike da tausayin ɗanta da kuma tashin hankali domin kuwa bata taɓa ganinsa cikin wannan yanayin ba, a hankali ta furta.
” HABEEB lafiya kuwa, meke faruwa da kai.?”
” Babu komai Momy kawai bana jin daɗin jikina.”
” A’a HABEEB bana son ka ɓaci da ƙarya domin kuwa ba ɗabi’ar ka bace, kaga ka sanar dani meyake faruwa da kai, baka da wanda ya wuce ni wanda zaka kaiwa damuwar ka.”
Fitowar Wasila kenan taji suna Maganar saurin komawa tayi ta raɓe a ƙasan benen gudun karsu ganta suyi shuru.”
” MOMY na faɗi a Soyayya wacce nake so Momy bani take so ba wani daban take so, ina cikin tashin hankali Momy bansan ta yanda zan iya cireta daga cikin raina ba, ina sonta sosai.”
Wani irin farin ciki Wasila taji a cikin ranta, Alhamdulillah ta furta cikin zuciyarta, Tabbas yanzu ne HABEEB zai kasance nata.
MOMY cike da tausayin ɗan nata tace……………..
Mu haɗe next page😜😜😜😜😜😜😜
Ki biya ki karanta karki karanta abinda ba gumin ki ba 08147537180 ki neme ni ta wannan numbern.
Akwai sabon BOOK ɗina wanda zan fara sakinsa next week maza ki garzayo ki biya naki, domin kuwa cakwakiyar dake cikin sa yafi na DOCTOR HASSAN na masa take da *AMINAINA KO ITA? farashi ne mai sauƙi Yar uwa.
*UMMU NASMAH CE*✍🏻
[9/23, 10:11 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 57 to 58*
__________✍🏻 Ba’a faɗuwa a Soyayya koda ka faɗi na Tabbata gobe wata zata ɗaga ka, idan yazo da dace ma wacce ta saka ka faɗin sai tazo ta miƙo maka hanu domin ta ɗagaka, karkayi saurin karaya a Soyayya domin kuwa ita idan ta karya maka zuciya sau ɗaya, haka zata barka cikin tsoron Soyayya, HABEEB ka dage da Addu’a insha Allah zuciyarka zatayi sanyi, kayi ƙoƙarin sanyawa zuciyarka hkrn wacce ka rasa hakan shine kaɗai ƙwarin gwiwwar ka.”
” Hakane Momy ina jin a jikina wata rana Falmata zata dawo gareni sai dai ban san yaushe ba, ban san tsawon ranar ba, bana tunanin zan ƙara son wata mace Momy soyayyata ɗaya ce kuma na riga na bawa Falmata ita.”
” Bana son haka HABEEB karka yankewa kanka alaƙar soyayya tun yanzu dan kawai ka faɗi sau ɗaya, kayi ƙoƙarin cire yarinyar nan a ranka tunda ka rasata, kayi ƙoƙarin ka samu wata domin kuwa Aure dole ne a gareka, har yaushe zaka tsaya jiran tsammanin marabbuka wai hausawa sukace malam yaƙi noma dan Zakka, bazan lamunci wannan ba.”
” MOMY ni kaɗai nasan abinda nake ji a cikin zuciyata, bazaki fahimta bane Momy.”
” Na fahimce ka HABEEB, kayi hkr, ka danne zuciyarka kaje ka cigaba da addu’a insha Allah zaka samu sauƙi a cikin zuciyarka, ka tashi kaje ka kwanta ka samu nutsuwa, ka kuma cigaba da ambaton zikirin Ubangiji cikin zuciyarka.”
Da to HABEEB ya amsa tare da miƙewa cikin damuwa kamar zai faɗi yana tangaɗi ya fice daga cikin Part ɗin, Momy da kallon tausayi tabi ɗannata dashi, itama tashi tayi ta shige Bedroom ɗin ta, Wasila murmushi ta saki tare da fitowa wani irin juyi tayi tana sakin dariya, ta furta.
” Ka gama zagayen ka, dole zaka dawo gareni, hmmm lalle yarinyar nan ta taimaki kanta da ta ƙi Soyayyar ka da tayi kuskuren karɓar Soyayyar ka, da kuwa taga tashin hankalin da bata taɓa gani ba a cikin RAYUWARTA, dan HABEEB ƙaddarata ne”
Juyin ta cigaba dayi, tana sakin murmushi, kafin ta fice da sauri ta nufi Part ɗin HABEEB, babu sallama ta faɗa cikin Bedroom ɗinsa yana kwance rigingine yana kallon slim ɗin ɗakin da alamu tunani yake ciki shi baima san ta shigo ba, taɓe bakinta tayi tare da zama bisa kujerar dake tsakiyar falon, ta furta.
” Wannan tunanin bazai kaika ba gara ka daina sa zaifi maka sauƙi, ka ƙyale ƙarya ka kama gaskiya, ko yanzu ya kamata ka fahimci cewa nice ƙaddararka, dan haka ya kamata ka dawo gareni, ko yanzu nasan ka fahimci abinda nake ji a cikin zuciyata tunda kaima kaji.”
Ta ƙarasa maganar tana sakin murmushi duk abinda take faɗa HABEEB yana jinta, bai ce mata komai ba har sai da ta kar ƙarshe tukunna ya tashi ya zauna ya fuskance ta kafin yace.
” Okay, waye ya baki izinin shigowa cikin Bedroom ɗina ba tare da izini na ba.”?
Murmushi still Wasila ta saki tace.
” Nida ɗakin mijina Kuma har sai na nemi izini, ai nafi ƙarfin neman izini.”
” Hmmm duk yanda dai akayi da jaki sai yaci kara, kin ɗauran Auren kenan tunda har na zama mijinki, kinga tashi ki fice min daga cikin ɗaki kafin na wulaƙanta ki, ina kawar miki kai amma naga alamar bakya ganewa, baki san zuru ba, bari kiji ko na rasa matar Aure a duniya bazan taɓa sonki bare kuma ya kaimu da Aure, na faɗa miki ba’a tilastawa zuciya soyayya koda na faɗi a soyayyata, banyi gardama ba, na barta da wanda take so, kuma shima yana sonta, dan haka karkiyi tunanin tilastawa zuciyata dole ta soki domin kuwa bazata sokin ba.”
” Wai wacce Irin ƙiyayya kake gwada minne, me wacce kake son take dashi wanda ni bani dashi, ka faɗa min aibuna, daka tsaneni.”
” Ban tsaneki ba, sai dai halinki shine wanda na tsana, bata fiki da komai ba, sai kamun kai nutsuwa gami da sanin ya kamata, kinga koda kinfita komai ma, ai dai naga shan koko ɗaukar rai ko, abincin wani kuma guban wani, dan Allah bana sonki ba kuma zan soki ba, ki tashi ki fice min daga cikin ɗaki!!!!!!”
Ya ƙarasa Maganar cikin tsawa, Wasila a matuƙar harzuƙe ta miƙe tsaye cikin ɓacin rai tace.
” Bazan fasa faɗa maka dole sai ka aureni ba, ina da hanyoyi da yawa wanda zaisa dole ka Aure ni ko baka so, sai dai hakan bana so, ina so ne muyi Aure na sayayya Amma naga alamar taurin kanka yayi yawa, kana neman dole sai ka tilastani na sa ka Aure ni dole.”
Tana ƙarasa Maganar HABEEB ya miƙewa tare da ɗauketa da tagwayen maruka har uku yace.
” Sa’an ki ne ni da zaki ɗaga min muryar ki, kina faɗa min Magana tamkar kina yi da ɗan cikin ki, ki fita a harkata Wasila , bana son naga ina wulaƙanta mata, dan Allah na roƙeki ki ƙyale rayuwata nasha Iska dan Allah.”
Ya ƙarasa maganar cikin raunin murya da karyewar zuciya sosai ransa yaji babu daɗi na marinta da yayi, Wasila da gudu ta juya ta fice daga Bedroom ɗin nasa, ajiyar zuciya ya sauƙe tare da zama ya riƙe kansa da yake jin yana sara masa kamar zai bar jikinsa, jima yake yanzu zuciyarsa ta fara son Falmata sai dai ina bazai iya mata dole a soyayya ba, dole zai haƙura da soyayyarta koda kuwa hakan zai zamo masa ciwo HABEEB haka ya kasance cikin damuwa shi kaɗai a cikin Bedroom ɗin.
Wasila kuwa kamar mahaukaciya ta dawo a cikin Bedroom ɗinsu, ta rasa inda zata saka ranta ya zatayi HABEEB ya sota, meyasa yake nuna mata tsana, idan harkar bariki, zata daina idan zai yadda ya aureta, why baya sona, mtsss taja tsaki sai kuma ta saki kuka sanda tayi mai isarta sannan ta miƙe tsaye ta hau haɗa kayanta a cikin akwatin ta da tazo dashi cikin gidan gara ma kawai tabar gidan ko idan ta daina ganinsa zata samu nutsuwa, sanda ta haɗa kayan tas sannan ta shige tollet ta wanke fuskar ta, mayafinta ta ɗauka tare da jawo akwatin ta fito, a falo ta samu Momy zaune da alamu yanzu ta fito ita da Hajara suna zaune, Momy cike da mamaki take bin Wasila da kallo harta sauƙo tambaya Momy ta jefa mata tambaya.
” Ina zaki da akwati ke kuma.?”
” MOMY gidan mu zan tafi.”
Ta bata amsa a taƙaice Momy miƙewa tsaye tayi tace.
” What gidan ku, soboda meyasa me aka miki da zaki tashi tafiya lokaci guda.”
” MOMY babu abinda aka min ina son tafiya ne kawai.?”
” To ba yau ba idan ma tafiyar kike so ki bari sai gobe.”
Wasila magiya ta dinga yiwa Momy har ta samu Momy ta barta, Hajara sarai tasan dalilin da yasa Wasila zata tafi sai dai bata sanar da Momy ba tayi shuru abinda, har bakin mota suka rakata, Musa direba shine ya kaita.
****************
Washe gari misalin ƙarfe Goma, Bulama ya haɗa FAMILY MEETING akan su DOCTOR, kowa ya hallara, harta su BABA GANA DA BAMAI, waɗanda suke ya’yan baffanu dasu Baba sai da aka kirasu sai dai babu mata ko ɗaya cikin MEETING ɗin sai Falmata kawai da ya zama dole tana ciki, Falmata tana gefen Baba yayin da Hassan yake zaune kusa da BULAMA, Bulama shine yayi gyaran murya tare da buɗe taron da addu’a, shine ya fara jawabin duk abinda ya faru jiya a fada kafin yace.
” Yara sun haɗa kansu su lallai suna son junansu, dalilin daya sa na tara ku kenan a nan domin sanar daku hukuncin dana yanke, abisa dalilai na kamar haka, na farko Hassan bashi da sana’ar da zai riƙe mata, na biyu Hassan mutum ne mai zafin zuciya da saurin hawa kuma Aure yana buƙatar haƙuri da juriya, shi kuma Hassan ya rasa wannan domin kuwa bashi da haƙuri, sannan kuma karatu shi zai tafi wanda idan ya tafi bazai dawo ba sai yayi Shekara 7 kafin ya dawo, mu Kuma bazamu barta ta kai har wannan shekarun tana jiransa ba, da waɗannan dalilai yasa na yanke hukuncin na yanke alaƙar Aure tsakanin su, babu wannan maganar.”
Cike da tashin hankali Falmata take duban BULAMA idanunta cike da Hawaye, shi kuwa DOCTOR idanunsa sun kaɗa sunyi jajur cike da tashin hankali, danne zuciyarsa yayi yana jiran yaji me su Baba Bukkar zasu ce, Bisa ga tsantsar mamaki sai jin muryar Baba yayi yace.
” Alhamdulillah, dama hukuncin kenan da nake so ka yanke, domin kuwa zuciyar Hassan bazata barsa ya riƙe mace ba, ita kuma mace duk wanda ya zauna da ita dole sai yayi haƙuri, dan haka BULAMA hukuncin ka yayi daidai.”
Kuka mai sauti Falmata tasa, yayin da idanun kowa ya dawo kanta, cike da mamaki, DOCTOR a zuciye ya tashi zaiyi Magana Baba Bukkar ya dakatar dashi da hanunsa, shuru yayi yana huci, tsawa Baba Bukkar ya dakawa Falmata, tayi shuru kafin ya fara magana cike da nutsuwa.
” Bulama wannan hukunci da kuka yanke sam baiyi daidai ba ku fahimce ni, tunda yaran nan suka nuna suna son junan su, abinda yafi sauƙi shine a barsu, saboda dukkan su ya’yan mu ne babu bare a cikin su, sannan Hassan yana gama karatunsa zai fito da aikin sa, yaran zamani ba’a musu tilas a musu Aure shine kawai abinda yafi alkairi saboda hanasu da kuke ƙoƙarin yi kar yaje ya haifar mana da ɗan da bashi da ido, ku dubi idanunsa hakan yana nuna cewa zasu aikata komai domin su mallaki junansu, Tabbas nasan zafin ran Hassan amma ina tabbacin Falmata zata Iya zama dashi tunda tana da hkr dan Allah ku duba Magana ta, ku kuma duba Zamanin da muke ciki, ba irin na da bane da ake yiwa yaro Auren dole.”
Gabaki ɗaya shuru sukayi kafin Bamai yace.
” Tabbas Bulama Maganar Bukkar gaskiya ce, nima nafi son a barsu suyi Auren , idan Maganar ɗakin da zasu zauna ne kafin Allah ya hore masa ai naga ga gidan shi Bukkar wanda ya saya nan baya zai iya basu su zauna kafin Allah ya hore masa yayi nasa.”
Baba zaiyi Magana Bulama ya ɗaga masa hanu yace.
” Na fahimce ku, to naji za’a barsu suyi Auren, to ku faɗa min zamu zuba mata ido ta jirasa har shekara bakwai.”?
Bamai ne yace.
” Ba haka muke nufi muna nufin ayi Auren kafin ya tafi idan yaso sai ta jirasa a cikin gidan nan harya gama karatun sa.”
Shuru Bulama yayi kafin yace.
” Ban gamsu da wannan maganar taku ba dole ina bukatar nazari kafin na yanke hukunci ku tashi kuje zan sake neman ku daga baya.”
Ai kuwa kafin kowa ya tashi DOCTOR ya rigasu a zuciye ya fice yana huci cike da jin haushin kakan nasa, ji yake kamar yace ya haƙura da Auren tunda ba ita kaɗai bane mace a duniya da ake neman walaƙanta sa a kanta kamar wata ƴar gwal.
Jinjina kansa Baba yayi yana binsa da kallo harya fice, dama wannan zuciyar tasa yake tsoro, da baya iya control ɗin ta a ko ina.
Gabaki ɗaya tashi sukayi suka fice daga ɗakin suka bar daga Falmata sai Bulama Falmata kusa da BULAMA ta matso Cikin sanyin jiki tace………………”
Sorry for typing error ban samu nayi Editing ba, kaina ke ciwo.
Masu cewa na ƙara yawan typing kuyi hkr insha Allah zan ƙara muku.
Ki biya kuɗin ki ta kafin ki karanta karki karanta abinda ba gumin ki ba nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya 08147537180
*ALƘALAMIN UMMU NASMAH CE*✍🏻
[9/24, 12:02 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 59 to 60*
_________✍🏻 ” kaifa kamin alƙawarin cewa zaka aura min duk wanda na kawo maka a matsayin mijin Aure na, meye aibu a jikin DOCTOR, ɗan uwana ne fa Bulama, meyasa zaku ƙisa ku so bare, bayan kuma shine wanda nake so.?”
” Saboda halinsa shiyasa muka ƙisa, muna ƙin Hassan ne saboda guje miki wahala amma ke naga alamar bakya fahimtar hakan, Fatuma, dake da Hassan duka jikoki kuke a gareni, nine mutumin daya kamata ace nafi kowa farin ciki da wannan zumunci da kuke so ku haɗa, amma tunda kika ga akasin haka a tare dani to ya kamata ki duba lamarin, danke ne muke ƙin wannan auren da kuma ɓacin zumunci, Hassan ba mutum bane Normal kamar sauran mutane, yana tattare da abubuwa huɗu wanda ba’a son ɗan adam ya haɗasu duka, Zafin Rai Rashin haƙuri da kuma rashin yafiya ga kuma son kansa, taya kike tunanin zaki iya rayuwa ta Aure dashi a haka, ki fuskance mu Fatuma muna sonki ne yasa muke nema muku maslaha.”
” Na fuskance ku Bulama sai dai ka sani DOCTOR bazai min duk abinda kuke zato ba, zamu zauna lafiya, mu kasance abun kwatance da sha’awa, dan Allah Bulama ka barni na auri zaɓin raina, saboda shi nake so zanyi haƙurin zama dashi a duk yanda ya kasance.”
” Bazan iya ba Fatuma, ki haƙura kawai da Hassan Allah ya baki wani mijin na gari, shima Allah ya basa wata matar a can waje, Auren zumunci kam bazamu muku shi ba, tashi ki bani waje.”
” Dan All……….”
Tsawa Bulama ya daka mata daya sata tashi a firgice ta fice cikin tashin hankali, Bulama tsuka yaja yace.
” Yaran Zamani marassa kunya, ta tsaya gabana sai famar magiya take min ita lalle na barta da wanda take so, mu kuma lokacin mu da aka mana Auren da babu wanda yasan wa zai aura sai da akayi auren tukunna muka san juna, ai bamu mutu ba, tunda gashi mun zauna har mun haifi iyayenku, yau naga shegan taka wajen yarinya, Soyayyar banza, zaman lafiya da kwanciyar hankali muke nema ba Soyayyar ku ba.”
Ya ƙarasa maganar cikin sababi, FALMATA kuwa barowar ta wajen BULAMA ɗakin Aunty YANA ta faɗa tana kuka, Aunty YANA dake zaune ita da FANNA ne ya sata duban Falmata a tsorace tana cewa.
“Innalillahi ke meye haka kike min wannan ihun, waye ya mutu da zaki shigo min haka zaki tsinke min zuciyata.”
Jikin Aunty YANA ta faɗa cikin kuka tace.
” Mama ki taimakeni, Bulama yaƙi yadda da Aure na da DOCTOR, WALLAHI Mama ina sonshi, bazan iya rayuwa babu shiba, kice karsu rabamu mama, wallahi aka rabamu dashi bazan yi Aure ba haka zan zauna har abada babu Aure.”
Tsuka Aunty YANA taja tana jin Tamkar ta tsinketa da mari, bakin ta bige tace.
” Amma dai ke Falmata anyi shashashar banza marar kunya, yanzu ke idan Banda lalacewa, shine kike tabkar wannan kukan akan ɗanamjji kamar wanda aka ce miki na mutu, aiko ni na mutu baza kiyi wannan kukan ba, to bari kiji Falmata koni nan bana son Auren ki da Hassan, sai dai idan dole ya zama babu yanda na iya sai na haƙura, saboda Hassan ba tsarin mijin da zaki Aura bane, nasan ke mutum ce mai haƙuri, dole zaki cutu da Auren Hassan, kinga shi idan ya tashi rashin mutuncin sa baya ragawa uban kowa, gashi kuma ba sana’a garesa ba, dan haka ki dakatar da zancen Aure tsakanin ku, kafin ranki ya ɓaci.”
” Na shiga Uku Mama wai ina zan kai kuka na naji daɗi ne, kowa sai yace zan cutu zan cutu, na gaji da jin wannan kalmar, ni ko da yankar naman jikina kullum zai dinga yi, na yadda zan Aure sa a haka, dan haka babu ruwan ku ku barni da abinda nake so.”
Ta ƙarasa maganar tana tura baki hawaye kuma na gudu saman fuskarta, Aunty YANA kallon tsoro tabi Falmata dashi da mamaki tace.
” Ni kike ɗagawa murya saboda ina nemawa rayuwarki maslaha yayi kyau, shige ki wuce ki barmin ɗaki na.”
FANNA dake zaune tana sauraron sune, taji ranta yayi mungun ɓaci da furucin Aunty YANA, akan ɗan uwanta, a zuciye Fanna ta tashi ta riga Falmata ficewa, Aunty YANA ta fahimci Fanna Haushi taji, amma ita ko a jikinta iya gaskiyarta ta faɗa, tsawa ta dakawa Falmata.
” Bazaki tashi ki fice min daga cikin ɗaki bane!!!! Sai na ci ubanki yanzun nan, wawiya marar lissafi ɓace min a ɗaki!!”
Tashi tayi ta fice cikin ɓacin rai ɗakin Hajja ta shige, da Bulama taci karo yana mayarwa Hajja abinda akayi, Falmata tsayawa tayi kansu tana kuka mai cin rai tace.
” Bazan taɓa samun farin ciki ba a rayuwata muddun kuka rabani da DOCTOR, haka kuma bazan taɓa daina kuka da ku ba, saboda kune sanadiyyar rabuwa ta dashi, a ƙarshe kuma zan tattara kayana na bar gidan nan na shiga duniya tunda bakwa ƙauna ta, duk kuma abinda ya sameni kuna da alhaki ciki.”
Tana gama faɗin hakan ta juya ta fice, a jikin igiyar shanya ta figi hijab ɗin ta ta fice daga cikin gidan, Hajja kallon BULAMA tayi tare da cewa.
” Baban Mala, Tunda yarinyar nan ta ambaci shiga duniya, mu zanye domin ko bata shiga duniya ba, zasu iya jawo mana abin kunya, ku barta da Hassan ga fili ga mai doki, jiki magayi, duk abinda ya faru gaba na Tabbata bazata yi kuka damu ba, saboda mun faɗa mata.”
” Hmmm!!! Hakane Maganar ki Hajja Mairo, amma wallahi yaran zamani suna bani mamaki, rashin kunya ya musu yawa, Kuma idan kin lura sam yaron nan bai damu da Fatuma ba sosai, ita tafi damuwa dashi, ai kinga shi zuciya yayi ya tafi ya ƙara waiwaito wani sai ita ya bari da faɗi tashi, Tabbas ina tausayin Fatuma, domin kuwa Soyayya tana daf da kaita ta baro ta, da zanyi tsawon wata ƙila na iya zama mata g
Katangar da zan kare mata wani abun, sai dai ita rayuwa bata da Tabbas, ko na mutu wata matsala ta taso, Hajja Mairo idan kina raye, ki taimaki Fatuma.”
Shuru Hajja tayi kafin ta furta.
” Ba damuwa Baban Mala Allah ya mana nisan kwana, ka sanar dasu za’a musu Auren, sannan ya kamata ace kafin yaron ya tafi India ayi Auren saboda idan har mukace ta jirasa ya dawo daga school , duniya zata zage mu saboda shekara bakwai tayi yawa da ta jirasa, saura sati biyu ya tafi ranar Monday zai tafi ko, to a ɗaura Auren jumma’a ta sama.”
” Ba komai Allah ya kaimu, bari na samu na miƙe bacci nake ji”
Da to Hajja ta Amsa tare da tashi ta shige gyara masa shimfiɗa.
Ita kuwa Falmata gidan su Maji ta nufa da Sallama ta shiga Mama ta samu tana markaɗe a dutse, murmushi ta saki tace amsa sallamar tare da cewa.
” Falmata, kece tafe.”
” Ehh Mama nice, ya aiki tana nan kuwa.”
” Alhamdulillah tana cikin ɗaki ki shiga ki sameta.”
Shigewa Falmata tayi cikin ɗakin Maji ta zauna tare da faɗawa jikin Maji ta saki kuka mai sautin gaske, a razane Maji tace.
” Innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un!!!! Falmata meya faru keda waye.”?
” Maji sunƙi amincewa da Soyayyar mu, sunƙi Maji sunce basu yadda ba na shiga Uku ina cikin tashin hankali.”?
” Mtsss!!!! Aikin banza, ni wallahi Allah ya isa tsakanina dake, kin tsinka min zuciyata a banza nayi zaton wani babban abune ya sameki ashe akan wannan banzan kike wannan ihun kamar wanda uwarki ta mutu.”
Cike da masifa cikin kuka Falmata tace wa maji.
” Kinga Maji bana son wulaƙanci damuwa ta na kawo miki idan bazaki iya mini maganinta ba, ki ƙyale ni, basai kin zagesa ba, sai kawai kice na tashi na bar miki gidan ku.”
Maji ganin ƙawarta ta dau zafi ya sata sassautowa cike da rarrashi tace.
” Ki haƙuri kawata gani da nayi kin shigo cikin ihu ne kamar wanda akayi mutuwa, yanzu meke happining kinsan ni bana son ganinki cikin damuwa ƙawata.”
” Maji sunƙi yadda, sunce bazan Auri DOCTOR ba, sabida wai zan cutu inji su, na rasa meyasa basa sonshi a matsayin su na iyayen sa.”
Murmushi Maji ta saki tare da cewa.
” To su mahaukata ne irinki da zasu amincewa shirmen ki, nifa Falmata banga wani son da Hassan yake miki ba, kece kawai kike haukar sa akan sa, shi bai damu dake ba, sannan tunda iyayenku suka ƙi, akwai dalili ne mai ƙarfi domin kuwa bazasu ƙisa haka kawai ba, sannan ai kema sanin kanki ne Hassan akwai shegen zafin rai ga IZZAR tsiya, ni da tun farko kinbi shawarata da wallahi baki yi nisa cikin Soyayyar sa ba.”
” Ni fa Maji Shawara nazo nema wajenki taya zan mallaki DOCTOR, ba cewa nayi ki bani umarni ba, dan wallahi ina sonsa bazan iya haƙura dashi ba, numfashi nane shi, taya kike tunanin mutum zai iya rayuwa babu numfashi.”?
” Hmmm!!!! Tunda kin sawa kanki wahala ai shikenan, ni dai yanzu shawara ɗaya ce tak dani shine kije ki samu Hajja cikin sanyin rai da kwanciyar hankali, kuyi Magana ta fahimtar juna, ki nuna mata irin sonda kike yiwa Hassan da kuma halin da zaki shiga idan kin rasashi wataƙil ki samu ta amince harta bawa mijinta umarnin a barku kuyi Aure, tunda naga BULAMA yana jin maganar ta, tunda kin nace dole sai shi.”
” Hmmm!! Maji Hajja bazata yadda ba, domin kuwa tana daga cikin waɗanda basa son wannan Auren.”
” Ke dai kawai kije ki jarraba abinda na faɗa miki insha Allah zata amince, naji labarin rashin mutuncin da Hassan ya yiwa HABEEB, kota nan ma ya kamata ki fuskanci waye Hassan Domin ko ƙwarya ta fashe akwai sauran zane sam HABEEB bai kamata ya yiwa HABEEB Rashin mutunci ba, tunda dai komai tsiya ya masa alkairi, kota nan ya kamata ki gane cewa Hassan butulu ne, kuma wallahi kinyi rashin miji na gari tunda kika yadda kika kaucewa HABEEB, HABEEB shine mutumin daya fi dacewa da rayuwarki ba wannan shashan ba.”
” Mtsss!!!! Kai Maji wai meyasa kika tsani doctor ne kam, kamar wanda ya kashe miki wani naki, gaskiya bana jin daɗin wannan tsanar da kike masa.”
Dariya Maji tayi tace.
” Daɗin abun ma ai idan tsanar ce bani kaɗai nake masa ba harda iyayenku, bare kuma ba tsana bace kawai halinsa ne aka tsana, ki dinga dai boye wannan Soyayyar da kike masa Kafin ya fuskanta ya fara fakewa da ita yana takaki.”
” Idan kuma na ƙi na ɓoye fa sai yaya.”
Falmata ta yiwa Maji Maganar cike da gatsali dariya Maji tayi ta bata amsa da.
” Sai jikinki ya faɗa miki, ai kinji kalmar nan ta Malam bahaushe yace jiki magayi, wanda baiji bari kuma ai zaiji hoho.”
” Mtsss!!!! Aikin banza, kawai, sai kuma kiyi insha Allah ni jikina bazai gaya min ba, ni harma na manta da wani HABEEB a cikin wannan Duniyar, ya maganar Assignment ɗin Malam musa na TAHZIF kinyi ne.”
” Banyi ba sai zuwa dare, kekam ai yanzu baki da lokacin yi tunda ana ta Kai ai ba’a ta kaya.”
” Ai kuwa wallahi, bani da hankalin Assignment har sai naga abinda zai turewa buzu naɗi.”
” To Allah yasa kiga alkairi…………….”
Mu haɗu next page🤗
Ki biya kuɗin ki cikin kwanciyar hankali yafi miki sauƙi fiye da ki karanta abinda ba gumin ki ba ki nemi ni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
Love You my FAN’S GASKIYA ina jin daɗin yanda kuke min ruwan sharhi akan BOOK ɗin nan hakan ya nuna min kuna jin daɗin novel ɗin I love You irin sosai ɗin nan🥰
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*[9/25, 11:53 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 61 to 62*
________✍🏻”kinga Malama tashi muje ke ki yiwa Hajja Magana wata ƙil ke taji naki, nikam kinsan mawuyacin abune ta fahimce ni”
” Hmmm!!! Kinga Falmata gwara ma ki kama hanyar ki kiyi tafiyarki yafi miki sauƙi nikam babu inda zani ina nan kwance bisa ƴar katifa ta.”
Haɗa fuskar ta Falmata tayi cike da ɓacin rai tace.
” Haka zaki min Maji saboda na kawo miki damuwa ta ko? Ba komai na gode.”
Falmata ta ƙarasa maganar tana tashi tare da ƙoƙarin ficewa, Maji saurin riƙo hanunta tayi tare da cewa.
” Karki tafi cikin fushi ƙawata, bawai naƙi zuwa miki bane, a’a akwai abinda nake dubawa ne, idan har naje Iyayenki zasu ga kamar nice nake zugaki ki bijire musu, zasu ga baƙi na, ni kuma bazan so hakan ba, ni da idan ta nine ma, Falmata da bazaki gujewa umarnin Iyayenki ba zanfi so ki musu biyayya, babu yanda na iya da zuciyarki ne, bazan iya sanja miki ita ba, kiyi hkr ƙawata.”
Juyowa Falmata tayi Hawaye na zubo mata daga idanunta tace.
” Ni kaina banso kaucewa Umarnin su ba, Maji babu yanda na iya da zuciyata ne, domin kuwa itace bazata iya jure ranshin DOCTOR ba, ban san wani irin Soyayya nake masa ba, sam zuciyata bata iya control ɗin kanta, ba zuciyata tana bugawa ne tare da nasa, da zan iya tanƙwara zuciyata, to wallahi da zanbi umarnin iyayena, sai dai bazan iya juran hakan ba, ku kyautatawa auren mu zato domin na Tabbata Hassan bazai bani kunya ba, Maji na fahimce ki, Tabbas ke ƙawace ta gari wanda dukkan wani mutum zaiso ya sameki a matsayin aminiya, karki damu ƙawata, ke dai ki cigaba da min addu’a Allah ya cika min buri na.”
Cike da tausayin ƙawar tata maji ta amsa da ameen, tashi Maji tayi ta raka Falmata har ƙofar gida kafin suka rabu Maji ta koma cikin gidan ita kuma Falmata ta shige nasu gidan a ƙofar gidan ta samu DOCTOR yana zaune shida Saif suna danna waya suna hira tamkar bashi da wata damuwa, Falmata gefen sa ta tsaya tare da cewa.
” DOCTOR na”
Ɗago kansa yayi a hankali tare da sakin murmushi yace.
” My dear yaushe kika ƙaraso bangan ki ba, sai kuma yayi shuru tare da zuba mata idanu, yace kuka kikayi.?”
Murmushin ƙarfin Hali Falmata tayi tace.
” A’a ba kuka nayi ba, me ka gani.?”
” Haba Dear ni fa ba yaro bane da zaki ɓoye min damuwar ki, kinyi kuka saboda su Bulama suna neman rabamu ko.?”
” DOCTOR hankalina a tashe yake ina tsoron su rabamu, idan suka rabani da kai , da rayuwata suka rabani, baka san rayuwarka rayuwata bane, mtsss, wai meyasa kayi kamar maganar bata dameka.”?
Ta ƙarasa Maganar cikin rau-rau da muryar alamun zata sake wani kukan, DOCTOR murmushi yayi tare da cewa.
” To ya kike so nayi so kike na ɗaga hankali na, kinga nifa bazan iya jure walaƙanci ba, taya dan kawai nace ina sonki sai su tsaya suna neman aibata Ni, mutuwa zanyi idan ban Aure ki ba, yau ko mutuwa ɗayan mu yayi dole zamu hkr, ni fa na yanke hukunci, idan zasu bani ke su bani idan bazasu bani ba shikenan amma wallahi bazan ƙara zuwa na tunkaresu da wannan maganar ba, kuma ko Bulama ya ƙara kiran MEETING wallahi bazan jeba, kema kiyi hkr ki daina sawa kanki damuwa, idan har Allah ya ƙaddara akwai Aure a tsakanin mu, dasu so da karsu so, dole sai mun kasance ma’aurata dan haka kije ki cigaba da addu’a, ki shige cikin gida.”
Saif cike da tausayi yake sauraron su, musamman Falmata yafi jin tausayin ta, Falmata zata sake magana DOCTOR ya kaɗan mata kai alamun karta kuma cewa komai, shigewa Falmata tayi cike da sanyin jiki, SAIF kansa ya dago cike da damuwa yace.
” Hassan, bai kamata ka mata wannan maganar ba, hakan yana nuna tamkar baka damu da ita ba, Hassan idan har kana sonta da gaskiya kamata yayi, ka dinga rarrashinta, ba wai ka dinga karya mata zuciya ba, koni nan yanzu banji daɗin Maganar daka faɗa mata ba Soyayya kulawa take so.”
Ɗago kansa DOCTOR yayi yace.
” Bawai karya mata zuciya nake ba Saif, wallahi ina sonta, sai dai bana jin zan iya jure cin mutunci saboda kawai nace ina sonta shikenan sai ya bawa iyayena damar wulaƙanta Ni, wallahi bazan juri walaƙanci ba, na gwammace na hkr da ita idan yaso suje su bawa duk wanda suke so, tunda since ni ban cancanta ba.”
” Hassan kenan anya kuwa kana sonta da gaske, da kana mata Soyayyar gaskiya, zaka iya jure duk wani wulaƙancin da za’a maka a kanta, kaga abinda iyayenka kenan suke gudu wannan zafin Zuciyar taka, domin kuwa tana rinjayar tunaninka, dan Allah ka rage wannan Zuciyar ka daure ka taka duk wani ƙayar dake kan hanyar Auren ka da Falmata koda kuwa ƙafar ka zata kasa taka ƙasa Saboda wahala, idan kayi wannan shine zai nunawa duniya zaka iya riƙeta, ya kamata ka gyara Soyayyar ka ka daina sako zafin zuciya cikin ta, idan har kana nunawa Soyayya zafin rai, to Tabbas wata rana sai ka samu Abokin takarar da zai kwace Soyayyar ka a wajen ta, muddun kuwa ta saurari wani namiji mai bawa Soyayya kulawa, zata gane cewa kai ba sonta kake, ita macen da ake so, ana riritata ne tamkar ƙwai ya kamata ka san wannan.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya sauƙe tare da cewa.
” GASKIYA ne, SAIF zanyi ƙoƙari naga nabi shawarar ka amma gaskiya iyayena basa kyauta min, saboda bai kamata su nuna min ƙiyayya akan wannan auren ba, iyayena ne fa su, suma sun hanani auren yarsu to waye zai bani Aure.?”
” Ba ƙiyayya suke nuna maka ba Hassan, iyayenka zuciyarka suke tsoro suna gudun abinda zaije ya dawo, ya kamata ka fuskanci iyayenka, sannan kamata yayi duk sanda kuka ƙara wani zama dan Allah ka nuna musu zaka iya riƙe Falmata da kyau, ka jajurce har sai ka samu sun amince maka da Auren Falmata.”
” Shikenan SAIF na gode insha Allah zan gwada na gani ko zan iya, ya Maganar tafiyar ne, next Monday ko.”
” Eh next week insha Allah, jiya munyi waya da HABEEB yake sanar dani cewa jirgin 9:00am zamu bi so Abokina ya kamata ka samu ka saita hanyar Soyayyar ka, domin lokacin ka kaɗan ya rage maka.”
” Mtsss!!! Hmmm!! Lokaci na ƙaɗan kam badamuwa zamu zubawa sarautar Allah Ido insha Allah komai zai tafi dai-dai.”
” Hassan ya kamata kafin mubar ƙasar nan muje gidan su HABEEB mu gaishe da mahaifiyarsa, sannan mu mata godiya saboda wadannan mutanen, sun mana alkairi, kasan fa duk wanda yayi karatu a India da America da kuma Cairo zai samu aiki a kowace ƙasa a cikin duniyar nan suna best Colipication.”
” Mtsss!!! Bazan jeba, kai kaje tunda kayi niya amma ni dai babu inda zani, bazan taka ƙafata a wannan gidan ba, bana buƙatar ƙara ganin fuskar sa a rayuwata.”
” Hmmm!!! Abinda yake cutar ka kenan zuciyarka, tunda kace bazaka ba, nasan ban isa tilastaka dole ba, amma dai nasan duk wani matsayin da zaka taka a duniya da bazar HABEEB ne, hakan kuma bazai taɓa gogewa ba.”
” Hmmm!! Saif gori kenan zaka min, Okay naji meyasa ya ƙi karɓar Vaccancy sa, sanda na dawo masa da abinsa, kaga Malam ya isa ka daina kawo min Maganar HABEEB muddun kana son mu zauna lafiya.”
Murmushi Saif yayi tare da tashi yana cewa.
” Saboda ya bakane dan Allah shiyasa yaƙi karɓa, kwantar da hankalin ka, ni tafiya ma zanyi yanzu.”
Yana gama faɗin haka ya juya ya hau keken sa, ya bar wajen tsuka DOCTOR yaja ya cigaba da danna wayarsa, ita kuwa Falmata sashin Umma ta shiga cike da sanyin jiki, Aunty JALILA Umma Fanna har AJIRAM suna zaune a falon Umma sai hira suke, zama tayi gefen Umma tayi shuru, AUNTY Jalala duban ta tayi tace.
” Falmata lafiya kuwa kika shigo cikin sanyin jiki.”
” Babu komai Aunty.?”
Murmushi Umma tayi domin kuwa duk ta fahimci halin da Falmata take ciki, tashi Umma tayi tare da kama hanun Falmata tace.
” Tashi mu shiga ciki.”
Babu musu Falmata ta miƙe tabi Umma a bakin gado suka zauna Umma ta dubeta tare da cewa.
” Karki ɓoye min damuwar ki Falmata, sanar dani meke damunki, nima mahaifiyarki ce, mai share miki hawaye, dan haka sanar dani matsalarki kinji ƴata.”
Falmata kanta ta sunkuyar tare da yin shuru taƙi sanar da Umma komai murmushi Umma tayi tace.
” Kina cikin damuwa ne saboda munce bazaki Auri, Hassan ba ko.?”
Da sauri Falmata ta ɗago kanta ta kalli Umma, sai kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa, Umma ce ta cigaba da cewa.
” Falmata nine na haifi Hassan a ciki na, nafi ki sanin halinsa mutum ne shi mai zuciyar gaske, yana da ɗaukar zafi akan abu kaɗan, idan har ya zuciya yakan yanke hukunci koda kuwa zaiyi nadama daga baya idan kuma yayi zuciyar baya jin maganar kowa a wannan lokacin koda kuwa nice UWAR dana haifesa bazaiji nawa ba, tsoron zuciyarsa yasa muke tsoron haɗaki Aure dashi bawai dan bama sonku bane.”
Falmata kanta na ƙasa tace.
” Umma ni ina son Doctor a haka zan iya juran zama dasu Umma, Please Umma dan Allah kisa baki Su barmu dan Allah Umma kar a rabamu.”
Shuru Umma tayi cike da tausayin Falmata domin kuwa ta fahimci Soyayyar da take yiwa Hassan yafi wanda shi yake mata, Tabbas akwai matsala hmmm Umma ta sauƙe ajiyar zuciya tace.
” Shikenan naji zan duba lamarin, ki kwantar da hankalin ki, ki saki ranki kinji, insha Allah zanyi iya ƙoƙari na, domin ki samu cikar burinki.”
Ɗan murmushi Falmata tayi tare da rufe fuskarta alamun kunya dariya Umma tayi ta tashi ta fice ta barta a Bedroom ɗin.
Washe gari kuwa da misalin 4 na yamma, Bulama ya ƙara haɗa family MEETING wannan karon harda mata su Umma da Aunty YANA, Baba shine ya fara buɗe taron da addu’a sannan Bulama ya fara magana.
” Nasan yau dukkan ku zakuyi mamaki da hukuncin dana yanke, to ban yanke wannan hukuncin ba sai da na zauna nayi dogon nazari, naga mai zai faru gaba, kafin na yanke hukunci, ba wani hukunci na yanke ba, na yanke hukuncin na yarjewa Hassan da Falmata suyi Aure a tsakanin su, kuma bana son kowa yace komai kawai ku musu addu’a da fatan alkairi, sannan wannan Auren za’ayi shine Jibi ranar juma’a kafin ya tafi India, zata zauna ta jirasa da auran ta harya dawo, dan haka gobe ayi sanarwa a masallaci idan an idar da Sallah cewa jibi akwai daurin Aure, ban Yadda ko wacce mace ta min taron biki a cikin gidan nan ba.”
Shuru kowa yayi dake wajen, Baba sam baiso hukuncin da BULAMA ya yanke ba, Falmata kuwa wani ajiyan zuciya ta sauƙe cike da jin daɗi, haka wajen Hassan ma, shima sosai yaji daɗin wannan hukuncin da BULAMA ya yanke, itama dai Aunty YANA bata so wannan hukunci ba, Baba Bukkar shima yaji daɗi sosai, haka taron ya watse masu farin ciki nayi masu jin haushi da fargaba sunayi……………
Allah ya haɗa mu a next page😝😝😝😝 yasin na gaji da yawa.
Ƴar uwa biya kudin ki, cikin kwanciyar hankali yafi miki sauƙi fiye da ki karanta abinda ba gumin ki ba neme ni ta nan, domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*Alƙalamin RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH Ce)*
[9/26, 11:49 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 61 to 62*
________✍🏻 Falmata sosai take murmushi tare da godewa Ubangiji daya cika mata burin ta, ɗakin aunty Yana ta shige, wayar ta ta ɗauka a bedside drower, cike da farin ciki ta kira Maji bayan maji ta ɗaga ne Falmata cikin dariya tace.
” Ƙawata Albishir, kinsan su Bulama sun amince da Aure na da DOCTOR wallahi yau ina cikin farin ciki marar misaltuwa, ƙawata ranar Juma’a za’a ɗaura mana aura.”
Zaro ido Maji tayi, tace.
” Kai ƙawata da wuri haka, baza’a bari sai ya dawo daga karatun ba, musha biki na kece raini.”
” Hmm ƙawata Bulama yace babu wani biki da za’ayi Aure kawai za’a ɗaura, shi kuma ya tafi India Monday ni hakan ma fa alhamdullahi.”
Dariya Maji tayi cikin zolaya tace.
” Saboda kin samu cikar burin ki, ko, ƙawata na tayaki murna Allah ya sanya alkairi ƙawata Allah yasa gidan zamanki kenan har abada, insha Allah da yamma zanzo mu taka rawa ƙawata kin samu cikar burinki.”
Dariya Falmata tayi tace.
” Allah ya kaimu ƙawata ina jiranki.”
Da ameen Maji ta amsa sannan suka kashe wayar Tana kashewa Aunty Yana tana shigowa cikin ɓacin rai fuskarta a haɗe, ta zauna kan kujera tare da wurgawa Falmata harara, kawar da kanta Falmata tayi daga kallon Aunty Yana domin kuwa ta fuskanci inda hararar Aunty Yana ya dosa, ficewa Falmata zatayi daga cikin ɗakin Aunty Yana ta dakatar da ita ta hanyar cewa.
” Dawo ki zauna munafuka.”
Dawowa Falmata tayi ta zauna kujerar gefe da Aunty Yana tana tura bakin ta, Aunty Yana cewa tayi.
” Hankalin ki, ya kwanta yanzu, kin samu abinda kike so, zan miki addu’a tare da fatan alkairi Allah yasa gidan zamanki ne, sai dai tunda kin nacewa auren Hassan, to kuma dole ki koyawa zuciyarki haƙuri da kuma juriya, ki ji ƙi gani ki gani ki ƙi ji, ki dinga danne fushin ki, a duk sanda kika ga ya fusata, wannan shine kaɗai zaisa ki iya Zama da Hassan, ki tashi kije Allah miki albarka.”
Ajiyar zuciya Falmata ta sauƙe domin kuwa tayi tunanin Aunty Yana, zaginta za tayi, cikin sanyin Murya tace.
” Na gode Mama insha Allah zan kasance kamar yadda kika fahimtar dani.”
Ta ƙarisa maganar tana tashi tare da ficewa yau zuciyarta a wanke take jinsa duk wani damuwarta ta ya goge.
Shi kuwa DOCTOR fitarsa daga Family meeting ɗin, bedroom ɗin Umma ya shige zama yayi yana sakin murmushi Aunty Yana cike da zolaya tace masa.
” Ango kasha ƙamshi, kaga kuwa yanda ka fara haskawa, kana walwalin, angonci.”
Dariya DOCTOR ya saki yana kallon Aunty Yana kafin yace.
” Kai Aunty kema dai ba dai zolaya ba, yaushe na zamo angon, bafa a ɗaura auren ba.”
” Ba’a ɗaura ba, amma dai ankusa ko, kaga Malam Hassan daga yau fa sunan ka ya koma ango, kuma dole ka amsa.”
Kafin DOCTOR ya bata amsa Umma tace.
” Ya isa haka, ka saurareni da kyau Hassan domin kuwa kashedi zan maka.”
Hassan fuskantar Umma yayi, tare da nutsuwa yana sauraron ta, haka Aunty Jalila ma ta maida nata hankalin tana duban Umma.
” Kaga dai yanda yarinyar nan tayi ruwa tayi tsaki, bata hutawa ranta ba, har sai da Bulama ya amince da wannan auren, to wallahi ka riƙe yarinyar nan da amana da gaskiya, idan har ka ci aminarta wallahi Allah bazai barka ba, domin kuwa tana sonka da gaskiya, duk da kaima kana sonta, soyayyar da take maka yafi wanda kai kake mata, dan haka ban yadda ka ɓata mata rai ba, idan ta maka laifi ka hukunta ta, cikin ruwan sanyi bada wannan zafin ran naka ba, wallahi ka ɓata mata rai kamar ni ka ɓatawa rai ne, kuma naji labari kai mai sai na ɓata maka rai, magana ta biyu, ban yadda ka rabu da Falmata duk girman laifin data maka, sai dai kuma idan ta kaucewa shari’a ne shine ya zamo dole ka rabu da ita, amma idan bashi ba, ko bayan raina ka rabu da ita, Ban yafe maka ba, kuma sai mun tsaya da kai a gaban Ubangiji, ka riƙe Falmata da kyau domin ka samu matar rufin asiri, nasan Falmata bazata taɓa ɓata maka ba, kaji dai abinda nace ko.”?
Shuru doctor yayi tare da ɗan cije laɓɓensa na sama yace.
” Umma ina mamaki idan kuna cewa wai Falmata tafi sona fiye da yanda ni nake sonta, wallahi Umma son da nake yiwa Falmata, ko kotansa bata min, kawai ita tana nuna nata soyayyar a fili ne shiyasa kuka fi ganin nata, kuma insha Allah Umma babu abinda zai rabani da Falmata sai dai mutuwa, ki daina shayi a kaina insha Allah duk sai na baku mamaki.”
” Zanso hakan Hassan, Allah ya muku albarka ya sanyawa Rayuwar auren ku albarka ya kuma azurta ku da zuri’a ta gari waɗanda zata taimaki addinin Musulunci.”
Da ameen duka suka amsa har Aunty Jalila, kafin suka koma firarsu ta duniya.
Da daddare Doctor ya kira Falmata a waya yace tazo ta samesa a soron gidan, bai kuma juma da kiranta ba sai gata tazo ta samesa, yana zaune bakin ƙofar ɗakinsa, kujera ta ɗauko ta zauna a gefe, murmushi doctor ya saki tare da cewa.
” Barka da isowa gimbiyar mata tauraruwar Hassan.”
Murmushi ta sa cikin sanyin Murya tace.
” Har kasa naji kaina ya fara hawa gajimare, kaine tauraron rayuwata kuma hasken idanuna jagoran rayuwata, hankali na yanzu ya kwanta saboda nasan na mallaki doctor na.”
Murmushi ya saki tare da cewa.
” Kamar yadda na mallaki Gimbiyata Falmata alkebbar mata, MATATA kinsan dalilin kuwa da yasa na kiraki yanzu.?”
” A’a farin ciki na, ban sani ba, amma dai nasan yanzu zan sani daga bakin Doctor na.”
Cike da zolaya kuwa yace mata.
” Ya kamata kuma ace kinsani domin kuwa zuciyar Hassan taki ce.”
” Zuciyarka tawa ce, sai dai ba lallai nasan ainihin karatun zuciyarba, sanar dani Farin ciki na.”
” Babu abinda yafi daɗi a duniya irin ka samu mace tagari wacce zata soka koda ba ka da komai, ina alfahari dake saboda soyayyar ki ta gaskiya ne a gareni, bani da ko sisi amma a haka kika dage kina sona, hakan ya nuna min zaki iya rayuwa dani, ko a wani hali na tsinci kaina a ciki, sai dai kuma Falmata shin zaki iya haƙurin zama dani kuwa, Falmata ni kaina nasan ina da zafin rai, duk da nasan zanyi iya bakin ƙoƙari na wajen ganin na kawar da zuciyata a kan ki, bazan yadda fushina ya taɓa tasiri a kanki ba, sannan zaki iya jirana har nayi shekara bakwai a wata ƙasa na barki anan.?”
Murmushi Falmata ta saki sannan tace.
” Zan zauna da kai aduk yanda kake, Doctor zan zauna na jiraka koda kuwa shekara dubu zakayi, muddun zaka dawo gareni, to zanyi dakon jiranka har Allah ya dawo da kai lafiya.”
” Tabbas Falmata, kin cika masoyiya ta gari kin samin nutsuwa a jikina, Wanda bazan iya misalta miki shiba, zan ƙara jaddada miki cewa, ina ƙaunar ki, bazan kuma daina sonki ba, har ƙarshen rayuwata.”
” Na gode da soyayyar ka gareni, insha Allah zan kasance mace ta gari mai biyayya a gare ka.”
Dare yayi ki koma cikin gida gobe zamu yi magana, tashi Falmata tayi tare da amsawa da Allah ya kaimu, yana Binta da kallo harta shige, murmushi ya saki shima cikin farin ciki.
***************
Juya spoon ɗin kawai yake a cikin abincin ya kasa kai koda loma ɗaya ne bakin sa, sosai yake cikin damuwa ya kasa jure rashinta a cikin zuciyarsa, bacci ma yanzu gagararsa yake yi, tsuka yaja tare da cije bakinsa, duk abinda yake momy tana kallon sa cike da tausayin ɗanta.
” *HABEEB* ” Ta kira sunan sa a hankali.
Ɗago kansa yayi ya zubawa Umma idanu.
” HABEEB meyasa kwana biyun nan baka cin abinci, tun ɗazu kasa abinci a gabanka amma ko spoon ɗaya baka saka cikin bakin ka ba, sannan na lura kana yawan shiga cikin damuwa, HABEEB kana son sawa kanka ciwo saboda macen da ta maka nisa, HABEEB ka cire damuwa cikin ranka, ka dinga yawan ambaton sunan Ubangijin ka, da kuma zikiri, insha ALLAH zai yaye maka soyayyar ta, kaci abincin ka.”
” Momy bana jin abincin ne a cikin raina, haɗa min tea kawai nasha, sannan momy zan koma CAIRO ranar Monday may be nafi samun nutsuwa a can.”
Kaɗa kanta momy tayi tana miƙo musa tea ɗin tare da cewa.
” Okay ba damuwa Allah ya kaimu Monday, sai ka sanar da Daddyn naka insha Allah zaka samu nutsuwa cikin zuciyarka, Allah zai baka mace ta gari wacce ma tafi ita wanda kake son, sannan munyi magana da kawun ka Musa, yace insha Allah gobe zaije yaga Jalila, idan sun daidaita, shikenan.”
” Okay Momy ba damuwa Allah ya daidaita tsakanin su, bari na tafi wa Daddy aikansa, GIWA BARRECK yace yana jirana a office.”
Ya ƙarasa maganar yana ajiye cup ɗin tea ɗin tare da tashi, Momy Allah ya tsare ta masa, sannan ya ɗauki kay ɗinsa ya fice, Momy da kallo ta bisa tana jin tausayin sa, addu’a take masa a cikin zuciyarta, Allah ya cire masa wannan soyayyar a cikin zuciyarsa……………
Kuyi hkr ban samu nayi editing ba saboda bani da chaji a wayana.
Ki biya kudin ki, cikin kwanciyar hankali yafi miki sauƙi fiye da ki karanta abinda ba guminki ba, ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗi ki 08147537180.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/27, 7:55 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 65 to 66*
Sorry dan page ɗin jiya nayi mistake wajen saka number, 62 to 63 ya kamata na saka sai kuma nasa 61 to 62 kumin afuwa🤲🏻.
___________✍🏻 HABEEB motar sa ya shiga tare da dafe kansa jikin sitiyarin Motar sai kuma ga hawaye shar daga idanunsa suna zubowa, runtse idanunsa yayi yana jin ƙirjinsa yana masa suka, a kullum yakan jefawa kansa tambayar meyasa ya kasa ɓanɓare Soyayyar ta daga cikin ransa duk da ita bata sonsa tama manta dashi a cikin RAYUWARTA amma shi har yanzu tana maƙale a tasa Rayuwar, meke shirin faruwa da rayuwarsa wacce irin Soyayya ce wannan ” Anya kuwa zan iya Auren wata mace kuwa? bana jin zan iya, saboda zuciyata na Falmata ne kaɗai, babu ta yadda zan iya bawa wata gurbi a cikin sa, ya kenan rayuwata zata kasance, innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un, Allah kana kallon matsalar da nake ciki Allah ka tallafi zuciyata ka kawo min agaji cikin Rayuwata.” Ya yiwa kansa tambaya tare da amsa kayan sa , hanunsa ya saka tare da goge hawayen fuskar sa, addu’a yayi tare da jan motar mai gadi ya wangale masa ƙofa, titi ya harba zuciyarsa cike da tunanin Falmata, yayi nisa da tafi yaji ringin ɗin wayarsa, hanunsa yasa ya amsa kiran tare da manna earpice a kunnen sa , a hankali yace.
” SHETIMA, tun ɗazu nake da niyar kiran ka sai kuma ka rigani, ya Cairo.”
Ɗan murmushi SHETIMA ya saki daga can kafin yace.
” Muna lafiya amma dai school ɗin bata min daɗi tunda babu kai a cikin ta, wai dan Allah malam yashe zaka dawo ne, an fara nisa da lecture’s fa.”
” SHETIMA ina hanya insha Allah Monday zan shigo, jiya munyi waya da Malam Murtala yace min wai har Assignment ya bayar, amma dai muna ɗan lectures dashi ta online, so abubuwan zasu zo min da sauƙi, kunyi Magana da AA ne akan Business ɗin nan, saboda ina son zan bada contract a fara ginin Companyn nan, idan zai zauna ya jagoranci Companyn kafin mu gama karatu mu dawo, to idan kuma bazai iya ba, so zan nemi wani kafin na taho, sannan ka sanar dashi cewa, Business ɗin RIƊI zamuyi, idan zai iya fine.”
” Eh munyi Magana dashi ya amince daman kasan ƙarƙashin wani Company yake so kawai ka bada contact ɗin a fara ginin Companyn.”
” Okay ba damuwa zamuyi magana da Daddy sannan kuma, shima A’A ɗin zan sake magana dashi, zan nemeka zuwa dare yanzu ina dreving ne.”
” Okay Allah shi kaimu daren.”
Katse wayar HABEEB yayi, sannan ya cigaba da dreving ɗinsa ya kusa isa Giwa BARECK yaji shigowar text cikin wayarsa, hanu yasa ya ɗago wayar HASSAN ya gani rubuce jikin screen ɗin wayar cike da mamaki yake duban wayar ” Hassan kuma?” Ya furta a zuciyar sa, buɗe text ɗin yaga an rubuta.
” _*Ina gayyatar ka ɗaurin Aure na da Falmata gobe idan Allah 1:30 a masallacin juma’a dake unguwar mu, sannan ina maka godiya da tayani bayyana Soyayyata da kayi, harta kaimu da Aure cikin gaggawa, muah 😘*_ ”
HABEEB wani irin duhu ne yaji ya rufe masa ido da ƙarfi ƙirjinsa ya buga, wani suka zuciyarsa take masa, kaɗan ya hana sitiyarin motar sa ta kufce masa yayi saurin riƙe sa, runtse idanunsa yayi ” shikenan na rasa ta har abada” ya furta tare ƙoƙarin maida hawayen da yake ƙoƙarin cika masa ido, tuno Maganar Momy ya sashi fara ambaton Ubangiji, a hankali kuma sai yaji nutsuwa yana sauƙa a zuciyarsa, harya iso First get ɗin BARECK ɗin.
**************
” Masha Allah ƙawata kice zaki rigani shigewa ciki, Waya ga amarya.”
Dariya Falmata ta saki cikin dariyar tace.
” Badai ZULUM ya kasa ba ai kinga kuwa dole mu rigaki ta inda zaki tabbatar da cewa nawa mijin yafi naki ƘWARI.”
Maji dariya ta saki sosai tace.
” Eyye!!!! To lallai dole HABIBINA ya dage tunda naga, har an fara mana gori.”
Daga bayan ta taji muryar DOCTOR yana cewa.
” Babu wani gori gaskiya ne kawai My dear ta gaya miki ki, Shi dai wannan Sojan naki, kice masa ba a iya filin daga kawai ake nuna jarunta ba, har a fagen soyayya ma, dan haka ya fito ya nuna mana jarumtar sa, kafin ya samu mai tatile masa ƙafa.”
Dariya Maji ta saka tare da cewa.
” Ku dai faɗi komai likitocin kune yanzu, amma dai karku manta akwai ranar Ramako, kun dai san bana barin bashi.”
Murmushi Falmata ta saki tace.
” Ai kuwa sai dai ki rame ba dai ki rama ba, DOCTOR na, barni da ita na isheta riga da wando harda zanin ɗaurawa.”
” Haba dai yarinya ai koshi, wannan mijin naki bai isheni ba, bare kuma ke, naga fa kanku ya fara rawa saboda kawai gobe wai za’a ɗaura muku Aure.”
Dariya DOCTOR yayi yana ficewa yace.
” Munji, kema ki yi zuciya taki naki kan yayi rawar mana.”
Ya ƙarasa maganar yana shigewa Maji murmushi tayi tana duban Falmata tace.
” Ƙawata, wai a ina zaki zauna bayan an ɗaura Auren ne.”?
” Eh to shi dai BULAMA yace, zan zauna na jirasa a nan gidan, a ɗakin kwanana, har Allah ya dawo dashi amma jiya naji Baba Bukkar yace zai basa gidan Alh Adamu na daya saya na nan bayan gidan mu, mu zauna har sanda Allah zai basa yayi nasa muhallin, amma dai yanzu a gida zan zauna sai ya dawo tukunna mu koma can.”
Ajiyar zuciya Maji ta sauƙe tare da cewa.
” Hmmm!!!! Lallai Falmata anyiwa Hassan Auren gata, shi kam ko kaɗan bai san zafin neman Aure ba, to Allah ya sanya alkairi, bari naje Mama na jirana zan karɓa mata aiki, zata fita unguwa, goben na dawo da safe.”
” To shikenan Allah ya kaimu muje na rakaki, har soron gidan Falmata ta raka Maji sannan ta dawo, Bedroom ɗin Aunty YANA ta shiga ta gaishe da AUNTY LADI ƙanwar Aunty da tazo ɗazu sannan ta fita, AUNTY LADI duban AUNTY YANA tayi tace.
” YANA kinsan labarin Auren nan yazo mana a bazata, Aure haka ba zato sannan ace baza muyi biki ba, wannan fa shine Aure na farko da kika fara ɗagawa shikenan sai ayi Aure lami babu wani biki, gaskiya banji daɗin hakan ba.”
” Hmmm!!! Ladi aini kaina banso hakan, babu yanda na iya ne kawai, saboda babu wanda ya isa yaja da hukuncin Bulama.”
” To Allah ya kyauta, yanzu kenan bazaki mata gyara ba, haka zaki bar ta, ta tafi ɗakin mijin tamkar wacce bata da gata.”?
Murmushi Aunty YANA ta saki tace
” Wai wa yace miki ɗakin miji zata ne, Auren nan fa kawai za’a ɗaura sane, bawai zama zatayi da mijin ba, idan an ɗaura juma’a shi kuma Litinin zai tafi India, ba Kuma zai dawo ba, har sai ya gama karatun sa, 7yrs anan fa zata zauna to gyaran me zan mata mutumin da zai shekara 7 ba mijin, na mata idan ya kusa dawowa.”
” Au wai kina nufin ba tare zai tafi da ita aini nayi zaton tare zasu tafi.?”
” A’a ba tare zasu tafi ba, anan zai barta.”
” To amma ai Aunty YANA kinsan dai yaran zamani ne su ko? To wallahi karkisha mamakin kafin ya tafi wani abu ya wakana a tsakanin su, cikin kwana biyun da kike rainawa, tun yaushe zai ɗauke ta da niyar sun fita unguwa, yaje ya maidata cikakkiyar mace kinan wangale da baki.”
Murmushi Aunty YANA ta saki tare da cewa.
” Haba dai Ladi ni ɗin sai na bari hakan ya faru, ai bari kiji na faɗa, Falmata bazata fita koda suron cikin gidan nan bane har sai Hassan yabar ƙasar nan, ke na taƙaita miki zance, ɗakin nan zata dawo da kwana tunda dama shi Bukkar ba’a nan yake kwana ba.”
“Sai dai kuma hakan ba”
Sun juma suna hara da Aunty Ladi har akayi kiran magarib, sannan suka tashi sallah.
Da daddare Saif ya shigo cikin gidan wajen DOCTOR a ɗakin sa ya samesa, kusa dashi Saif ya zauna tare da cewa.
” Congratulation Abokina, kawai sai kake sanar dani komai ya daidaita, gaskiya Abokina na tayaka murna Allah ya samu a dashin ka, dan kayi dacen mace ta gari, kace gobe ey warhaka mun juma da angoncewa, da ita zamu shige India ne.”
” Abokina waye zai biya mata kuɗin jirgin kasan gomnati sit ɗina kawai ta bayar, anan zan barta harsai na dawo.”
Zaro ido Saif yayi yace.
” What!!!! 7years fa zakayi kana tunanin zata iya haƙurin jiranka har wannan shekarun, dutse ne ita aka faɗa maka bata da sha’awa.”
” Ko tana da sha’awa, ya zan mata to, kasan dai bazan bar karatu na, dan kawai na zauna da ita ba, dole naje nayi karatu domin kuwa shine rufin asirin mu daga ni har ita, kama daina wannan maganar dole zata hkr.”
” Hmmm, to hakane amma dai lamarin akwai Abin dubawa, kasan fa yawancin mata sunfi namiji sha’awa, ni tausayin ta kawai nake ji, domin nasan zata cutu.”
” Babu wani cutuwar da zatayi Malam shiyasa ma bazanyi kuskuren saninta mace ba, yanzu har sai na dawo saboda karna koya mata abinda bazata jura ba.”
” Good Abokina, idan kayi hakan shine daidai abin zaizo da sauƙi, nayi zaton a hanu kake ne ai bazaka iya hkr ba, har sai ka ɗanɗani zumar kafin mu tafi shiyasa nayi wannan maganar.”
Kafi kowa sanin zan iya tunda ina iya danne jarabata bana kaiwa matan banza, an faɗa maka ni irinka ne, SAIF kaji tsoron Allah ka daina lalata yaran mutane, wai ana cewa abokin ɗan iska ɗan iska ne ko, to wallahi ni ba ɗan iska bane.”
Dariya ce ta ƙwacewa Saif Sanda yayi mai isarsa Kafin yace.
” Naji ni ɗan iska ne, amma dai kasan kwana biyun nan na gyara halina ko, Allah da gaske na tuba, amma dai taba kam bazan iya daina shanta ba.”
” Hmmm!!! Akwai taba babbar illa ce ga rayuwarka, zaifi maka sauƙi duka ka gyara.”
Dariya Saif yayi ba tare da yace masa komai ba, sai wani zancen ya ɗauko masa daban.
Kuyi hkr banyi editing ba yau.
Ki biya kuɗin ki ta wannan numbern 08147537180 zan faɗa miki yadda zaki biya, karki karanta min LITTAFI idan kinsan baki biya.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/28, 11:07 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 67 to 68*
__________✍🏻 Rana bata ƙarya sai dai uwar ɗiya taji kunya, yau take juma’a ranar ɗaurin auren Falmata da Hassan, Hassan da babbar rigarsa ya fito, bayansa SAIF ne, shima yasha babbar riga, su Baba kuwa tuni sun juma a masallacin, DOCTOR part ɗin Umma suka shiga, tana zaune cikin yaranta AJIRAM JALILA Fanna, sai UMMAHANI ADDAR Umma wacce suke uwa ɗaya, suna ta hira, kusa da Umma ya sunkuya, idanunsa ya ɗago tare da zubasu ga Umma, cikin shauƙi da sanyin murya yace.
” Umma yau Ranar farin ciki ne a gareni, ranar da bazan taɓa mantawa da ita ba, ki samin albarka Umma, domin na fita cikin Nasara ina ji a jikina, nida Falmata mutuwa ce kawai zata raba mu.”
Murmushi Umma ta saki cike da ƙaunar ɗan nata, domin kuwa a duk cikin ƴaƴan ta, tafi jinsa a cikin ranta ko dan shi kaɗai take dashi namiji ne, cewa tayi.
” Kullum da Albarka ta kake tafe Hassan, Ubangiji ya albarkaci Rayuwar ka, ya tsare maka gaban ka da bayan ka, mahassada da kuma maƙiya ya kau da idanunsu a kanka, Allah yasa wannan Auren idan an ɗaurasa sai mutuwa ne zai rabaku, ka tashi kaje ɗana lokaci na ƙaratowa Allah ya albarkaci Auren nan ya haskawa Rayuwar ku.”
Gabaki ɗaya falon da ameen suka amsa cike da sha’awa Saif yake binsu da kallo rayuwar Umma da ƴaƴan ta yana basa sha’awa sosai, shi kam ya rasa wannan gatan, tun yana ɗan shekara Biyu ya rasa iyayensa duka biyu daga uwa har uba, hawayen dake ƙoƙarin sauƙo masa yayi saurin saka hanu ya tare su, Umma duban ta ta kai garesa tare da saka hanu a kansa tace
” SAIFUDDEEN Allah ya maka Albarka, kaima ya fito maka da taka matar Auren ta gari, Allah ya jiƙan iyayenka.”
Da ameen suka amsa har DOCTOR, UMMAHANI cikin murmushi itama ta masa addu’a, Aunty JALILA kuwa tashi tayi ta zo daf da ƙanin nata, hanunta riƙe da turare, fesawa DOCTOR ta hau yi sosai a jikin sa kota ina, tana dariya, sanda kwalbar turaren ya kusa rabi kafin ta ajiye turaren.
” Ɗan uwana, ina tayaka farin ciki yau domin kuwa rana ce wacce zaka samu farin cikin rayuwarka Kuma mace ta gari, Ubangiji Allah ya albarkaci Auren nan ya samu cikin danshin ku.”
” Ameen Aunty na, sai dai har yanzu ina da sauran cikar burina a rayuwa, ina son naga Auren ki Aunty JALILA.”
Hawaye ne ya zubo daga idanunta bata goge ba, tace.
” Ka cire Aure na a cikin, cikar burinka domin kuwa abune marar Tabbas, a yanzu yaci ace ina da Aure harda kusan yara uku, sai dai ƙaddara ta hanani Aure, jarabawa ta kenan Hassan, na Rashin mijin Aure, wata ƙila bana daga cikin matan zasuyi aure a duni…………”
Saurin toshe mata baki DOCTOR yayi yana kaɗa mata kai cike da damuwa yace.
” Karki yanke tsammani da rahamar Ubangiji Aunty JALILA, domin kuwa bai hallici ko wace mace ba, sai da ya ƙaddara mata mijin Auren ta, sai dai jinkiri yasa muga nisan lokacin Aure yana tafiya ne da ajali idan lokacin sa yayi dole sai anyi, mutane sune suke kasa Fuskantar hakan, amma nasan insha Allah, zaki sami mijin Aure jinkirin ki zaizamo alkairi.”
Kafin JALILA tayi Magana Umma ta riga cewa.
” Hassan, ku shige maza ku tafi, time na ƙurewa.”
DOCTOR bai kuma cewa komai ba suka shige da Saif zuciyarsa cike da tausayin ƴar uwar tasa wanda yake jinta tamkar uwar da ta haifesa, Umma cike da tausayin Jalila ta dubeta tace.
” JALILA, bana hanaki furta mugayen kalamai ba akan wannan jarrabawar taki ta rashin miji, ni na haufeki JALILA nafiki jin zafin rashin Auren ki, amma ya muka iya da ƙaddarar Ubangiji, lokacin kine baiyi ba JALILA, da zarar lokacin ki ya cika, Allah zai fito miki da mijinki kiyi Auren ki, harma mu manta da kinyi jinkiri, addu’a shine abinda ya kamata kiyi ba mugayen kalamai ba, daga yau wannan ya zamo shine na ƙarshe da zanji wani kalma marar daɗi a bakin ki.”
Hawayen Aunty JALILA ta goge tare da cewa Umma.
” Insha Allah Umma bazan sake ba.?
Can kuwa wajen ɗaurin auren cike yake da mutane, DOCTOR da SAIF harma da wasu daga cikin abokan sa, suna zaune gefe guda, ana ɗaura auren wasu kasancewar akwai layi a gaban su sai an ɗaura Aure biyar kafin nasu sune na shida, Bayan angama ɗaura nasu ne sannan aka kira su BULAMA dai-dai lokacin Kuma HABEEB ya na ƙarasowa da motar sa, duk da HABEEB yana jin zuciyarsa na tsinkewa, ga wani suka da take masa, sai dai hakan ya daurewa Zuciyarsa yayi ya hallaci ɗaurin auren, shigowa yayi ya zauna gefen DOCTOR, BABA BUKKAR shine ya bada sadakin DOCTOR dubu 30,000 lakadan, Baba kuwa shine ya bada Auren Falmata, bayan an gama ɗaurin auren ne, HABEEB cike da murmushi ya miƙawa DOCTOR hanu tare da cewa.
” Congratulation 🤝🏻 Hassan na tayaka murna ka samu mace ta gari sai dai shawara, ka riƙe ta da kyau, domin kuwa ka samu matar rufin asiri.”
Murmushi DOCTOR shima yayi tare da cewa.
” Na gode, koda baka faɗa ba, nasan na samu matar rufin asiri, naji daɗi daka amshi gayyata duk da ka faɗi amma ka daure har kazo.”
Ya ƙarasa maganar yana sakin murmushi cike da gatsali, shima kuwa HABEEB ɗin murmushi yayi tare da cewa.
” Ai shi HABEEB duk wanda ya gayyace shi sai yazo, koda kuwa maƙiyinsa ne, faɗuwa ba ita take nufin rashin nasara ba, wani yakan faɗi kusan sau goma amma tashi ɗaya yake samun nasarar data zarce wanda bai taɓa faɗuwa ba, ya kamata ka daina saurin cika baki, idan kaga baka san me yake gaba ba.”
Yana faɗin haka ya juya tare da nufar su Baba, sosai DOCTOR yaji haushin Maganar HABEEB sai dai yaƙi basa damar mayar masa da amsa ya juya abinsa, HABEEB cike da girmamawa ya gaishe da su Bulama, dubu ɗari ya basu gudumawa duk da daƙyar Bulama ya karɓa albarka sosai ya sawa HABEEB.
” Allah ya maka Albarka Habibu, ban taɓa tunanin zaka hallaci wannan auren ba, saboda ba ka samu Falmata, sai gashi ka bani mamaki, lallai kai mutum ne na gari.”
” Bulama ai kun zama iyayena koda ban Auri Falmata ba, zan shige saboda ana jirana.”
Murmushi Bulama ya saki yace.
” Shikenan Allah ya maka Albarka, mun gode.”
Baba ma Albarka ya masa, cikin farin ciki, HABEEB juyawa yayi ya shige cikin motar sa, Saif saurin ƙarasawa jikin motar yayi, turus ya tsaya yana duban HABEEB cike da tausayi, domin kuwa kifa kansa HABEEB yayi ya saki kuka mai cin rai Tabbas yau yasan ya rasa Falmata, ya rasa farin cikin sa, cikin sanyin jiki SAIF ya kira sunan sa.
” HABEEB!!!”
Ɗago kansa yayi a hankali idanunsa sunyi jajur.
” Nasan yanda kake son Falmata HABEEB, Amma meyasa ka kasa cireta a Zuciyarka, duk da kasan baka cikin zuciyar Falmata.?”
” SAIF nima nayiwa kaina wannan tambayar, sai dai na kasa samun amsar tambaya ta abinda na sani kawai shine itace macen dana fara so a cikin rayuwata, nasan na rasata kuma dole na haƙura, sai dai ka sani harna mutu Soyayyar Falmata yana cikin zuciyata.”
Yana gama faɗin hakan ya ja motar sa ya bar wajen, cike da alheni Saif ya dawo wajen DOCTOR, cikin farin ciki suka watse daga wajen ɗaurin auren.
Yau Falmata tana cikin farin cikin da bata taɓa tsintar kanta ciki ba, haƙoran ta, sun kasa ruhuwa dariya kawai take yi, Maji murmushi ta saki tace.
” Oh ƙawata ban taɓa ganinki cikin farin ciki irin na yau ba, gaskiya kina cikin farin ciki, ina roƙon Ubangiji daya albarkaci Auren ki, Allah ya tabbatar miki da farin cikin da kike ciki har ƙarshen rayuwarki ZULUM yana hanya gobe may be asa ranar Aure idan ya zo daman kinsan dawowarsa ake jira.”
Murmushi Falmata ta saka tace.
” Maji Tabbas ina cikin farin ciki ko yau na mutu na godewa Allah domin kuwa naga cikar burina, na samu abinda nafi so a cikin RAYUWATA, Ƙawata kice gobe kema kina tare da habibin ki.”
” Insha Allah gobe muna tare.”
AUNTY Yagana ce ta shigo cikin ɗakin tare da cewa.
” Ke Falmata ki tashi kizo, Bulama na kiran ki, suna ɗakin Hajja.”
Da to Falmata ta amsa ta cewa Maji fa taje ta dawo, ɗakin Hajja ta nufa zama tayi kanta a ƙasa, bata juma da shigowa ba shima DOCTOR ya shigo kusa da Falmata ya zauna, tare da ɗan mangarinta kaɗan, ɗago kai tayi, ya kanne mata ido😉 murmushi Falmata tayi tare da mai da kanta ƙasa, muryar Hajja sukaji.
” To Alhamdulillah!!! Yau dai Allah ya tabbatar da wannan auren, hakan ya nuna mana Tabbas akwai ƙaddarar Aure a tsakanin yaran nan, to ina son kowa ya manta da cewa mun nuna rashin so a wannan auren, amatsayin mu na iyaye addu’a zamu musu Allah ya tabbatar da zaman lafiya mai ɗaurewa a tsakanin su, sannan kai Hassan abinda nake so da kai, kaji tsoron Allah ka riƙe yarinyar nan da kyau, idan ka wulaƙanta ta, wallahi sai Allah ya mata sakayya domin kuwa ta nuna maka ƙauna, sannan ina son ka rage wannan Zafin rannaka, dan Allah Hassan ka riƙe Fatuma tsakanin ka da Allah, koda bayan ranmu dan Allah karka bari rayuwarta ta shiga cikin matsala.”
Ɗago kansa DOCTOR yayi ya kalli Hajja yace.
” Ki daina shakku a kaina Hajja, ina son Falmata fiye da yanda kuke zato, Falmata igiyar Rayuwata ne, tsinketa a jikina tamkar tsinkewar Rayuwata ne, taya kike zaton zan sake wannan igiyar rayuwata ta tarwatse, bazan taɓa rabuwa da ita ba.”
Murmushi Bulama ya saki tare da cewa.
” Alhamdulillah naji daɗin wannan maganar taka, Hassan, Allah ya muku albarka, sannan kema Fatuma kibi mijin ki sau da ƙafa iy nayi bari na bari, ki masa biyayya, domin kuwa yanzu aljannar ki tana ƙarƙashin ƙafarsa , koda wasa kar ki yadda muji kin ɓata masa rai ko kin masa abinda ba daidai ba, idan har muka samu wannan labarin to wallahi ranki sai yayi mungun ɓaci.”
Girgiza kanta Falmata tayi alamun taji, Hajja cewa tayi idan su Baba suna da abinda zasu faɗi, Umma ce tace.
” Duk abinda ya kamata mu faɗi kun faɗa hajja sai dai Magana ɗaya da zan maɗa, wanda maimaita masa shi zanyi yanzu, ku zama shaida Hajja, ban yadda Hassan ya rabu Falmata ba, muddun ba saɓawa Shari’a tayi ba, idan kuma har ya rabu da ita ba da haƙƙinta ban, ban yafe masa ko da na mutu zanci gaba da ja masa Allah ya isa ina cikin kabari na, ku zamo min shaida ban yadda ya hukunta ta cikin fushi.”
Baba cewa yayi.
” Tabbas ina bayanki YAMURAM, nima kaina bazan iya yafe maka ba, muddun ka wulaƙanta min ita.”
Ajiyar zuciya Hajja ta saki tare da cewa.
” Insha Allah hakan ma bazai faru tsakanin su ba, Allah ya muku albarka, YANA ke baki da abinda zaku faɗi ne keda Bukkar kunyi shuru.”
Yana cewa tayi.
” Babu wani abinda zance Hajja duk abinda zan faɗa kun faɗa, Allah ya albarkaci Auren shine kawai abinda zance.”
Shina Baba Bukkar cewa yayi.
” Alhamdulillah, Falmata, nasan ke macece mai haƙuri, to ina son ki ƙara haƙuri akan wanda kike dashi, domin kuwa shi Aure dole sai da hkr, saboda zakiga daɗi za kuma kiga rashin daɗi, harshe da haƙori ma suna saɓawa, bare kuma ku, dan haka ki kasance mace mai tsananin hkr shine ribar Aure, duk macen da bata da hkr to mawuyacin abune ta iya zaman Aure, ki zamo mace mai rufawa mijinki asiri, kiyi hkr da babun sa, ki kasance mace mai tsaftace muhallinta da kuma jikinta, idan kika kasance a yanda na suffato miki Tabbas zaki zauna lafiya da mijinki.”
” Insha Allah Baba kamar yanda ka faɗa min haka zan kasance, bazaku taɓa samun matsala daga gare ni ba.”
Bulama cike da farin ciki shima yace.
” Magana ta karshe itace, Fatuma zata zauna a tare damu har Allah ya dawo dakai, idan ka dawo sai a mata jere a nan gidan Bukkar na baya ku zauna kafin Allah ya baka naka muhallin.”
Murmushi DOCTOR ya saki tare da yiwa iyayen nasa godiya, umarni BULAMA ya bawa kowa akan ya tafi DOCTOR shine ya fara fita sai Falmata ta fita itama.
Da daddare har bayan isha’i kafin Saif ya tafi, itama Maji tafiyar tayi, tana yiwa ƙawartata addu’a da fatan alkairi, haka kowa ya watse cikin farin ciki………………..
Wannan littafin na kuɗi ne, idan kin gansa a waje ma na sata ne gara ki biya kuɗin ki, ki karanta guminki, yafi ki karanta abinda ba haƙƙinki ba, ki neme ni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/29, 10:41 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 69 to 70*
_________✍🏻 washe gari kuwa da safe Falmata cikin farin ciki ta tashi yanzu bata da wata damuwa ko tunani tunda ta samu abinda take so, Kamar kullum yanda ta saba haka tayi ɗakin Aunty YANA ta shiga ta gaishe ta sannan tayi ɗakin Hajja ta shiga, ita kaɗai ta samu zaune a falon kusa da ita ta zauna tare da cewa.
” Hajja ina kwana”
Murmushi Hajja ta saki tana dubanta cike da tsokana tace.
” Amarsu ta ango kinsha ƙamshi sai walwal kike kina ɗauke mana ido, ja’ira da kika nace sai da kika samesa kika huta, to ai gaki gashi sai ki jiƙasa kisha ƙarshen So.”
Dariya Falmata tayi tace.
” Wannan kuma ai yanzu keya dama idan ma kina jin haushi ne ke baki samesa ba, kishi ya murɗoki.”
Dariya sosai Hajja tayi kafin tace.
” Allah kiyashe ne zaɓen tumun dare, ina zan kai wannan Uban Yan zuciyar tsiyar, ai sai ke da kika ga zaki iya na bar miki kuje can ku ƙarata.”
Dariya Falmata ta saki ba tare data tanka Hajja ba domin kuwa ta fahimci tsokana Hajja take ji dashi, Hajja cikin serious tace.
” Kinje kin gaishe da surukar taki YAMURAM kuwa?”
” A’a Hajja banje ba.”
” To maza tashi kije ki gaishe ta, daga yau duk wani wayewar gari zakije ki gaishe ta, dole ya zamo miki, idan kin ganta da wani aiki ma ki karɓa mata ki mata wannan shine ɗa’a, domin kuwa yanzu uwar mijinki ne, idan kin fito kuma shima mijin naki kije ki gaishe sa.”
Da to Falmata ta amsa tare da tashi ta fice daga ɗakin Hajja ta nufi Part ɗin Umma, da Sallama ta shiga Fanna kawai ta samu a tsakar gidan tana wanke wanke.
” AUNTY Falmata ina kwana.”
Fanna ta gaishe ta, tana murmushi Falmata ta amsa da lafiya tare da cewa.
” Umma tana ciki kuwa.?”
” Eh tana ciki, yanzu ma ta shiga.”
Ɗakin Falmata ta shige tare da Sallama, Umma dake zaune ta saka tv gaba tana kallon sunnah tv ta amsa tare da sakin murmushi, karo na farko da Falmata ta fara jin nauyin Umma, kusa da Umma taje zata zauna a ƙasa Umma tayi saurin cewa.
” Kul kika zauna a ƙasa, zoki zauna nan kusa dani, yaushe na dawo surikarki ban sani ba, to karma ki kuskura ki ɗaukeni a suruka, ni uwa nake gareki ba surka ba dawo nan kusa dani ki zauna.”
Murmushi kawai Falmata tayi tare da zama kusa da Umman saman kujera, gaishe ta tayi cikin sakin fuska Umma ta amsa Falmata ta ɗan juma a wajen Umma, kafin ta tafi, soron gidan ta shige ɗakin DOCTOR, hanunta ta saka ta tura ƙofar da yake kare bakin ta ɗauke da Sallama, yana kwance hanunsa riƙe da waya ya amsa mata sallamar bai ɗago kansa ba yace.
” My dear, shigo mana kika tsaya daga bakin ƙofa ko kin manta nan ɗakin mijinki ne.”
Murmushi Falmata tayi tare da shigowa, a gefen katifar tasa ta zauna tare da cewa.
” Oh DOCTOR na, kai dai baka gajiya da danna waya, ko yaushe idanunka suna kan waya.”
Ɗan Murmushi DOCTOR ya saki, tare da mirginowa, hanunsa yasa ba tare da Falmata ta ankara ba, ya fisgo ta, ta faɗa ƙirginsa, jifa yayi da wayar gefe tare da saka hanunsa duka biyu ya kana west ɗinta, zuba mata idanu yayi yana sakin murmushi, yayin da ita kuma Falmata zuciyarta ta tsinke, karo na farko kenan da ta fara haɗa jiki da namiji tsikar jikinta ne ya zuba, gashi kuma ta kasa haɗa ido dashi, idon nata suna rufe, breaz ɗin ta ya zubawa idanu da suka ɗan leƙo masa ta cikin riga lips ɗin sa ya lashe yana haɗiyar yawu, tare da ɗan cije leɓen sa na sama a hankali yace.
” Ki buɗe idanunki ki kalle ni my dear, babu kunya a tsakanin mu yanzu, mijinki ne Ni, dan haka ki cire duk wata kunya ki fuskance ni.”
Kasa buɗe idanun nata tayi, ita dai yau kam tana jin kunyarsa, ganin dai da gaske bazata buɗe ba ya sashi sakin murmushi tare da sakin west ɗin nata, zura hanunsa yayi cikin rigarta, wani zubawa tsikar jikinta yayi jin hanunsa a rigarta, yana shafa breaz ɗin ta a hankali, shima wata irin sha’awar tane ya bijiro masa, idanunta na rufe cikin sanyin muryar ta mai cike da tsoro tace.
” Stop DOCTOR pls.”
Murmushi ya saki cikin hanzari kuwa ya haɗe bakinsa da nata, bayan ya cire hanunsa daga rigar tata, ƙoƙarin ƙwace kanta take amma ta kasa, tunda DOCTOR ya fara tsotsan lips ɗin ta taji wani daɗi tamkar karya daina, ƙara runtse idanunta tayi, tare da saka hanunta ta ƙanƙamesa, hanunta da DOCTOR yaji a jikinsa ya sashi gane ta fara amsar saƙon sa, harshen ta ya capka ya fara mata wani irin hot kiss mai rikitarwa, sanda yaga ta gama sake masa jikinta, har kamar tana neman ficewa a hayyacin ta, gudun karya zarme ya sashi zare bakinsa daga nata a hankali yana sauƙe ajiyar zuciya, Falmata da duk jikinta ya gama mutuwa ne ta narke masa a jikinsa, dubanta yayi tare da sakin murmushi gashin ta ya shafa cikin kunnenta mata raɗa yace.
” Haka ake gaishe da miji, good morning my dear.”
Ya ƙarisa Maganar tare da hura mata iska a kunnenta, kunya ce ta Kama Falmata ta ƙara rufe idanunta tana laɓewa a ƙirjinsa tare da sakin murmushi, ta kuma kasa Magana still murmushi ya ƙara saki yace.
” Ko dai matar tawa ta zama kurma ce, Please my dear buɗe idanunki ki kalleni mana ko zanji sanyi.”
A hankali ta buɗe idanun nata ta zubasu a idanun DOCTOR tana kuma kwance a ƙirjinsa, lakace mata hanci yayi yace.
” Ko ke fa, nafi samun nutsuwa idan kina kallo na, amarya ta, bani labari mai daɗi.”
” A wajen ka ya kamata na samu labari DOCTOR na, zuciyata tana tsinkewa, a duk sanda na tuno zaka tafi ka barni harna tsawon wasu shekaru, ina tsoron karkaje ka gano wacce ta fini acan ta ƙwace min kai, ta warware min igiyar dana juma ina tuƙawa a kanka.”
Murmushi DOCTOR yayi tare da mirginowa da ita suka fuskanci juna idanunsa ya saka cikin nata, yace.
” Igiyar ki tayi tuƙuwar da babu wata macen da ta isa ta waresa koda kuwa hurul aini ne, mace ce ta dabam ke a gareni, rayuwata ne fa ke, taya kike tunani akwai wacce ta isa rabani da rayuwata, Hassan naki ne, ke kaɗai ba tare da kishiya ba ki saka wannan a ranki, ki kwantar da hankalin ki koda shekara dubu zanyi bana tare da ke, zan tsare miki kaina, babu wanda ta isa shiga cikin rayuwarki domin kuwa rayuwata taki ce.”
Murmushin jin daɗi Falmata tasa cike da ƙaunar mijin nata tace.
” Zanfi kowa farin ciki da alfaharin cewa, nafi ko mace sa’ar miji, idan har ka tsare min kanka daga wasu sheɗanun mata, Tabbas ina sonka, Soyayyar da bazan iya jure rashin ta ba, DOCTOR na, kana sona Kuwa Kamar yanda nake nake sonka.”?
Ɗan dariya DOCTOR ya saki yana ƙara kallonta yace.
” Soyayyar da nake miki, tafi ƙarfi fiye da wanda ke kike min, naki kawai kika san Zafin sa, amma ni nasan duk duniya babu wata macen da zanso sama dake, ina ƙaunar ki.”
Murmushin Falmata ta saki cike da jin daɗi, sun juma da DOCTOR cikin ɗakin suna hira, kafin Falmata ta fito cike da farin ciki.
Kwana biyu da ɗaurin auren Falmata da Hassan kullum cikin farin ciki suke tattare dashi domin kuwa suna bawa junansu kulawa, a cikin kwana biyun nan DOCTOR kullum sai yayi romance da Falmata sai dai bai taɓa kuskuren shigarta ba, suna dai samun nutsuwa da juna a haka.
Yau Monday itace Ranar da DOCTOR zasu tafi India, da sassafe ya shiga wajen Umma, kusa da ita ya zauna Baba ma yana zaune, gaishe su yayi cike da girmamawa yace.
” Baba Umma, jirgin 9:30am zamu hau yau.”
Baba ne yace.
” Masha Allah abu yayi kyau, Allah ya kaiku lafiya ya baku nasara cikin abinda kukaje nema ya rabaku da sharrin maƙiya, kai kuma Hassan ka maida hankalin ka, kayi abinda ya kai ka, domin ka samu abinda kaje nema, a duk inda ka kasance karka manta da cewa kana da mata, Allah ya maka Albarka ya baka Sa’a cikin karatun ka.”
Da ameen Umma ta amsa tare da cewa.
” Ka dage ka zamo mutum mai ƙoƙarin karatu, Hassan ina son ka zamo wani abu a rayuwa, karka biyewa abokan banza dan Allah Hassan ka dage ka zamo zakaran gwaji cikin makarantar Allah ya maka Albarka ya baka nasara ya tsare maka gaban ka da bayanka.”
Da ameen doctor ya amsa tare da cewa.
” Insha Allah bazan baku kunya ba, zanyi abinda ya kaini, kuma insha Allah zan fito da sakamako mai kyau na gode sosai, ku cigaba da min addu’a.”
Murmushi Umma ta saki tare da ɗauko kuɗin da Kawu Dauda ya kawo mata a kunshe cikin leda ta miƙa masa tace.
” Ga wannan dubu ɗari shida ne, ka riƙe su a hanunka saboda buƙatun yau da gobe, idan sun ƙare ka sanar dani Insha Allah zan turo maka wasu.”
DOCTOR cike da ƙaunar mahaifiyar tasa yasa hanu ya karɓa yana jin tausayin ta da ƙaunar ta, a cikin ransa, kafin ya tashi ya fito, Aunty JALILA ya samu tsaye bakin ƙofa cike da ƙaunar ɗan uwan nata itama ta miƙo masa leda mai cike da donut da cake har da cincin, tace.
” Allah ya kaika lafiya ya baka Nasara insha Allah sai ka zamo likitan da sunan sa zai amsa a cikin MAIDUGURI.”
Yana murmushi ya karɓa sun juma suna hira da Aunty Jalila, FANNA ma maƙale masa tayi, da ƙyar ya ɓanɓareta daga jikinsa, sannan ya shige cikin gidan, sanda yayi sallama da kowa sun juma da Bulama yana masa fatan alkairi, da nasiha, kafin ya dawo ɗakin sa, ƙofar ya tura, cike da mamaki yake dubanta da take kwance rufda ciki sai famar sharɓar kuka take, ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ajiye kayan daya shigo dasu, bakin katifar ya zauna tare da saka hanu ya ɗago ta, biyo hanunsa tayi ta taso tare da faɗawa jikin sa sai kuma ta ƙara sakin kukan.
” Kukan me kike, mutuwa zanyi idan na tafi ne.?”
Da sauri ta ɗago jajayen idanunta ta kallesa, ɗaga mata kai yayi yace.
” To mesa zakiyi kuka, ko kinfi so na zauna ba karatun ne,.?”
Girgiza masa kai tayi tace.
” A’a amma zuciyata bata jin daɗin bari na da zakayi, jikina ya saba da naka jikin zan shiga cikin damuwa idan babu kai a kusa dani.”
Murmushi ya saki tare da ɗago kanta ya tallafe da hanunsa, harshen sa ya zura a cikin bakin ta, wani irin hot kiss suke yiwa junan su, yayin da ɗayan hanunsa yake ciki rigarta yana murza nipples ɗinta cike da salo, a wannan lokaci, kaɗan ne ya hana DOCTOR maida Falmata cikakkiyar Mace, sake juna sukayi suna sauƙe numfashi, DOCTOR da idanunsa da suka koma jajur yake cewa.
” Ki kwantar hankalinki shekara bakwai kamar kwana bakwai ne da yardar Allah, insha Allah zan kasance dake kullum a ta waya, zan kuma dinga ziyartan mafarkin ki, kimin Addu’a fatan Nasara damuwar ki tana ɗaga min hankali.”
” Shikenan DOCTOR ubangi Allah ya baka Nasara ya tsare min kai, dan Allah DOCTOR karka kalli ko wace mace a matsayin mace dan Allah.”
Murmushi ya saki tare da kama kumatun ta, yana kuma sakin murmushi.
” Insha Allah kece kaɗai a cikin zuciyar Hassan.”
Nocking ɗin ƙofar sukaji, da sauri Falmata ta tashi daga jikin Hassan ta koma saman kujera, Bello ne ya shigo, murmushi DOCTOR ya saki yace.
” Kardai har time ya cika.”
Dariya Bello yayi yace ƙwarai kuwa 9:12 yanzu ya kamata mu fita, tunda shi Saif yanzu haka yana can filin jirgin, tashi DOCTOR yayi tare da ɗaukar cut ɗinsa ya saka akwatin ya nunawa Bello ɗauka Bello yayi yana cewa Falmata ” ranki shi daɗe” tare da jan akwatin ya fice dashi, Falmata taahi tayi ta rungume DOCTOR, Kafin ta sake sa, hijab ɗin ta ta ɗauka ta saka tare da ɗaukar ledar tasa ta fito dashi shi kuma ya shige cikin gida, sallama da su Umma tare suka fito da Aunty JALILA da Baba Bukkar sai Bulama sune suka masa Rakiya filin jirgin harda Falmata ciki.
A filin jirgin sun sami SAIF suna zaune da HABEEB shima iya jiran jirgin Cairo, harda Daddyn sa, wajen dukkan su suka nufo, kasancewar wajen ake zama jiran tashin jirgin, DOCTOR cike da girmamawa ya gaishe da Daddyn HABEEB, ransa ɓace ya miƙawa HABEEB hanu sukayi musabaha, daya san zai sami HABEEB a nan da bai bari Falmata ta biyo su ba, shi kuwa HABEEB murmushi yayi ganin yanayin DOCTOR, yaso ya yiwa Falmata murnar Auren ta amma sai ya fasa, tare da kawar da kansa gefe, itama kanta Falmata taso ta gaishe da HABEEB sai dai ganin yanayin DOCTOR yasa ta fasa, Daddyn nasa kawai ta gaishe, jirgin Cairo shine ya fara tashi, HABEEB yana kallon Falmata cike da so da ƙauna ya shige, cikin jirgin, haka HABEEB ya bar ƙasar cike da Soyayyar Falmata, basu jima da tashi ba, suma DOCTOR aka kira nasu jirgin, sallama sukayi da iyayen sa, shida Saif suka shige cikin jirgin, suna ɗaga musu hanu, DOCTOR idanunsa yana kan matar sa, Falmata idanunta cikowa yayi da Hawaye, tana ji tana gani jirgin su ya ɗaga, haka suka juyo gida cike da kewarsa Falmata kuwa babu daɗi taji amma haka ya zamo mata dole tayi hkr.
Haka rayuwa ta dinga tafiya, Falmata kullum sai sunyi waya da DOCTOR safe da kuma dare, yau wata huɗu da tafiyar DOCTOR, aka saka ranar auren Maji da ZULUM wata Uku, kacal Falmata sosai ta taya ƙawarta murna, Falmata tare da Maji suka dinga hidimar hada-hadan Auren, lokaci kuwa babu wuya take lokacin Auren yazo saura sati ɗaya kacal inda za’a kai Maji unguwar BULUNKUTU AIRPORT, Ranar Alhamis akayi walima Falmata itace kan gaba a hidimar bikin, sai dai bata bawa ko wani NAMIJI fuskar mata magana ba.haka akayi hidimar bikin aka watse cikin farin ciki aka kai amarya gidan ta dake BULUNKUTU AIRPORT……………….”
Kuyi hkr yau na muku a gurguje saboda naga kun matsu mu dawo cikin labari shiyasa na ɗan muku a gurguje.
Wannan littafin na kuɗi ne, idan kin gansa a waje ma ɗauko sa aka yi, ki biya kuɗin ki ki karanta yafi alkairi fiye da ki karanta Abinda ba gumin ki ba ki neme ni ta nan domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[9/30, 10:46 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 71 to 72*
_______✍🏻 Falmata tunda ta shiga kaɗaicin rashin DOCTOR na waɗannan watannin, sai taji tana da sha’awar ta cigaba da karatun ta, zaman gidan ya isheta, tunda aka ɗaura mata Aure da DOCTOR shikenan ake mata kulle a cikin gidan babu inda take samu taje duk anbi an takura ta, ita kaɗai take wannan tunanin yayin da take kwance a ɗakin ta, wayarta ta jawo a hankali ta danna masa kira, harta yanke bai ɗaga ba, sai can kuma taga kiran sa ya shigo mata, ɗagawa tayi ta kara wayar a kunnen ta cikin sanyin Murya tace.
” Aminci Allah ya tabbata a gareka tauraro na DOCTOR na.”
Murmushi DOCTOR ya saki ya lumshe idanunsa, yana jin wani sanyi da yaji muryar ta ta doki kunnensa, yana zaune harabar school ɗin nasu shida Saif da wani ba’indiyen Mutum mai suna sanskar sai Hema dake zaune gefen Saif.
” Ya akayi hasken rayuwar Hassan, tauraruwar mata da fatan kina cikin halin lafiya my dear.”
Ɗan dariya Falmata ta saki mai sauti cike da farin ciki tace.
” Muddun kana cikin halin lafiya, babu makawa nima ina halin lafiya, domin kuwa bugun zuciyata ne kai kaga kuwa dole idan cutu sai kaji sautin a ƙirjin ka, DOCTOR na, alfarma na kira na roƙa ko Allah zaisa na samu.”
Murmushi ya saki yana kallon Saif dake bawa Sanskar lbrn Falmata yace.
” Faɗi ko wacce irin alfarma ce, haske na, Ni kuwa insha Allah zan cika miki ita muddun batafi ƙarfi na ba.”
” DOCTOR na, MAKARANTA nake so na koma University, na gaji da zaman gidan ina son na cigaba da karatu.”
Ɗan shuru yayi, yana nazarin Maganar ta, kafin yace.
” University Falmata!!! Wacce makaranta kuma zaki cigaba da ita, ni gaskiya da anawa ra’ayin ne, zance ki hkr da wani karatu, kawai ki rungumi Auren ki, sai dai bazan danne miki ƴancin ki ba, kina da right ɗin da zaki nemi ilimi a matsayin ki na mace, zan barki ki cigaba da karatu, amma sai na dawo hankalina zaifi kwanciya da hakan, yanzu ina cikin school idan na koma hostel zan kira ki.”
Ran Falmata baiso wannan hukuncin da DOCTOR ya yanke ba, a son ranta ya barta tayi karatun domin kuwa yanzu ne take buƙatar sa da take cikin kewa, bata son jayayya dashi yasa tace masa.
” Shikenan Allah ya dawo da kai lafiya ta furta ina son zanje gidan Maji gobe da safe na wuni .”
” Yawo dai kike son fita Dear, to Allah ya kaiki lafiya ki gaisheta ko”
Da zataji Falmata ta furta tare da katse wayar, juyi tayi daga katifar tana sakin murmushi.
***************
Malam na dawo ne game da Maganar Da mukayi na ƙanwar mij……..”
Dakatar da ita yayi tare da cewa.
” Na sani ba sai kin faɗa ba, kin dawo ne game da ƙanwar mijinki ko, da kuma mijinki daya fara miki tawaye.”
Kaɗa kanta tayi alamun eh, sannan ta ƙara da cewa.
” Malam ina son a ƙara dawo min da mijina tafin hanuna, sannan itama ƙanwar tasa a rufe min bakinta ta manta da dukiyar ta, da yake wajen mijina, a kawar da hankalin kowa daga kan wannan dukiyar.”
Dariya bokan ya bushe dashi irin na marassa imani yace.
” Wannan abune mai matuƙar wahalar gaske rufewa wannan matar baki domin kuwa macece mai ibadar gaske dan haka ba ƙaramin aiki zamuyi akanta ba, aikinta zanyi shi amma ba yanzu ba, saboda sai mun samata tashin hankalin da zamu sa ta shagaltar da ibadar ta, a wannan lokacin ne zamu yi aiki a kanta, shi kuma mijinki, aikin sa mai sauƙi ne, ga wannan kwalbar kije ki saka a ƙarƙashin gadon da yake kwana karki kuskura wannan kwalbar ta fashe, ga wannan ƙwai ɗin da layar nan shi kuma zaki nemi tulu ki saka a ciki harda allura, sai ki tonu rami a cikin gidan ki, ki binne, yanda kika binne wannan tulun kin binne bakinsa da kuma gardamar sa gareki kenan, bazai taɓa miki musu akan duk wani umarninki ba, ita kuma zan nemeki idan buƙatar aikin nata ya taso, ajiye min numbern wayarki anan.”
Cike da jin daɗi Jummai ta saka numbern ta a wayar bokan, ajiye masa kuɗin da zai kai 40k tayi a karkashin shimfiɗar sa, sannan ta ɗauki abubuwan daya bata tana murmushi tare da ja da baya harta fice, dariya bokan ya bushe dashi.
Kamar yadda bokan ya umarce ta Jummai haka tayi tun a hanya ta sayi tulun ta, bayan ta gama binnewa ne, sai kuma ta zari hijab ɗinta ta nufi gidan Umma.
Da sallama kuwa ta shiga, Umma dake zaune tsakar gida ita da JALILA sukaji sallamar ta, JALILA da gudu ta tashi ta faɗa jikinta tana cewa.
” Oyoyo Aunty Jummai!!!”
Dariya Jummai tasa tace.
” JALILA aini fushi nake dake, na zamo miki kura baki zuwa gida na ko.”?
Dariya Jalila tayi Umma ce tace.
” Mu shiga daga ciki Jummai.”
Cikin falon Umma suka shiga suka zauna cike da sakin fuska Umma suka gaisa da Jummai, Jummai ne tace wa Umma.
” Hassan kuma an girma, naso ai zuwa Ranar ɗaurin auren sai Baban Musa yace min babu taro shiyasa banzo ba, to naso kuma nazo bayan bikin na miki murna nan ma Allah baiyi ba, sai yanzu, Allah ya sanya alkairi.”
Dariya Umma tayi tace.
” Lah babu komai fa Jummai, komai ai sai Allah ya nufa, jiya ai Musa yazo da yamma ya gaishe ni, ya labarin Yakumbo.”
Yakumbo tana nan lafiya, kinsan kwanan nan ƴan boko Haram sun shiga cikin BANKI sun musu ɓarna sosai, harda jikanta magidan ci shima abin ya rutsa dashi sun kashe sa, yankan rago suka masa, abin dai babu daɗin jin.”
” Innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un allahumma ajirni fil musibati, Oh ko yaushe wannan masifar ta ƴan boko Haram zata ƙare a Nigeria, abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, Allah ya mana maganin wannan musibar ita kuma Yakumbo Allah ya bata hkrn rashin sa, hmmmm!!! Allah ya jiƙansa.”
Da ameen Jummai ta amsa, dai-dai lokacin Falmata ta shigo cikin falon bakin ta ɗauke da Sallama, Jummai ita ta amsa sallamar, kusa da Aunty JALILA ta zauna tace.
” AUNTY JALILA, Ga can wani yaro a tsakar gida yazo wai wani yana sallama dake a waje.”
Cike da mamaki Aunty JALILA tace.
” Wani kuma waye to.?”
Umma ce tace.
” Ki tashi kije ki duba ko waye ne ma ai zaki gani idan kinje.”
Tashi Aunty JALILA tayi ta ɗauki mayafinta ta fito cike da mamakin waye yake kiranta.”
Falmata kuwa cike da ladabi ta gaishe da Jummai, amsawa tayi cikin fara’a tana cewa.
” Amarya, anyi biki lafiya.”?
” Lafiya Alhamdulillah” Falmata ta amsa tare da cewa Umma, ” zanje gidan Maji, tunda aka yi biki banje ba.”
A Dawo lafiya Umma ta mata sannan Falmata ta fice.
Can kuwa ƙofar gida, Jalila ce tsaye jikin wata farar mota, tare da wani babban mutum, fuskar sa cike da haiba.
” Za kiyi mamakin ganina ko, kuma baki sanni ba.”?
Ɗaga masa kai JALILA tayi alamun eh, ba tare da tayi Magana ba.
” Sunana Alhaji Ibrahim Dake ni cikakken ɗan nan MAIDUGURI ne, ina unguwar GIWA BARECK da zama nayi Aure harda yara biyu, amma Allah ya yiwa matata rasuwa na ganki ne, naga kinmin kuma ina sonki shine aka min kwatancen gidan ku, Allah yasa na miki a mijin Aure.?”
Shuru Aunty JALILA Tayi kafin tace.
” Ta waje na babu damuwa, sai dai idan har da Aure kake sona zaka iya zuwa gurin iyayena duk yanda kukayi dasu dai-dai ni a waje na ”
Shikenan babu damuwa insha Allah zanyi Magana dasu gobe idan Allah ya kaimu, wayarsa ya miƙa mata, ki samin numbern ki anan duk yanda mukayi zakiji ni insha Allah, amma karki manta da ina da yara biyu kuma idan Allah ya tabbatar da Aure tsakanin mu, zaki zauna ne tare dasu.”
Miƙa masa wayar Aunty JALILA tayi bayan tasa masa numbern, ” Babu Allah ya tabbatar da alkairi ni zan shiga ciki.”
Kuɗi ya miƙa mata yace ” ga wannan ko.”
” A’a na gode ka barsa.”
Murmushi Alh Ibrahim ya saki tare da cewa.
” Kin san dai haramun ne mai da hanun kyauta baya ko,? Kyauta na miki dan Allah ki karɓa.”
Hanu tasa ta karɓa tare da masa godiya ta shige cikin gida.
*************
Wata huɗu da Maganar Alh Ibrahim da Jalila, komai ya kankama domin kuwa Bulama sunyi bincike sosai a kansa mutumin kirki ne, sannan kuma ƙani ne ga Momy mahaifiyar HABEEB, su Bulama sunsa ranar Aure wata biyu kacal, sosai kowa yayi murna da wannan Aure na Jalila da kowa ya ke muradin gani, barin ma DOCTOR da yafi kowa son ganin Auren Yar Uwar tasa, sai dai kash bashi nan za’ayi Auren, Umma taso ta ƙara sayar da Filin ta, saboda Auren Baba yaƙi yace shine zai mata komai, Umma dole ta haƙura ta barsa.
A cikin wannan watan kuwa akayi auren Jalila, aka kaita gidan ta, ya’yan mijin nata ma yara ne masu tarbiyya sam basa raina ta, yanzu Rayuwa ta yiwa Umma daɗi, kwanciyar hankali ya ƙara zuwa mata, shima DOCTOR cikin kwanciyar hankali yake karatun sa, ko wani jarabawa shine wanda yake zuwa first class sosai malam suke ji dashi a cikin makarantar, ya samu numbern yabo sosai, a wajen HABEEB kuwa har yanzu ya kasa daina tunanin Falmata ji yake a jikinsa kamar zata dawo garesa sai dai bashi da tabbacin saƙar zucinsa.
Rayuwa tana tafiya musu cikin nutsuwa ba tare da gaggawa ba, Falmata kullum tana maƙale da DOCTOR a waya, Soyayya ce mai ƙarfi ta shiga jikinsu, yayin da ɗaya yake jin bazai taɓa iya rayuwa babu ɗaya ba.
Maji ma cike da kwanciyar hankali take a cikin gidan ta, yayin da take ɗauke da tsohon ciki, haka kuma Aure bai rabata da aminiyarta ba, sukan kawowa juna ziyara a kai akai watan Maji goma da Aure ta haihu ɗan babu rai sosai maji taji zafin rashin ɗanta amma dole tasa ta hkr ta dangana.
**************
Rayuwa tana gudu yayin da shekaru suke shuɗewa, a kwana a tashi babu wuya a wajen Ubangiji, yau shekarar DOCTOR Bakwai da tafiya India kuma a yau suke saka tsamanin dawowar sa, sosai Falmata take cikin farin ciki da dawowar mijinta…………..
Ki biya kuɗin ki yafi dacewa fiye da ki karanta abinda ba gumin ki ba, ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[10/3, 8:03 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 73 to 74*
This page Deducted to *DOCTOR HASSAN PAID GROUP* sonso nake muku ƴan uwa 😘
________✍🏻 Bello shine ya ɗauki Falmata da Umma a mota sukaje tarbar DOCTOR SOSAI Falmata tayi kyau cikin wata koriyar atamfa mai ratsin baƙi tasha ɗinkin doguwar riga fuskarta yane da baƙin mayafi sosai tayi kyau duk da fuskar ta ba makeup, karo na farko data yafa gyale kenan, sun ɗan juma zaune a wajen suna jiran isowar jirgin su DOCTOR, sai can jirgin ya sauƙa Falmata cike da nishaɗi ta zubawa jirgin ido, tana duba ta ina DOCTOR zai fito, mutane sai famar sauƙowa suke a cikin jirgin, cike da nutsuwa yake sauƙowa, zuba masa idanu Falmata tayi cike da ƙauna, sosai yayi kyau har ƙiba ya ɗan yi, fuskar sa cike da saje ya kewaye masa fuska, gashin kansa ya kwanta luf gwanin ban sha’awa har haske ya ƙara, miƙewa tsaye Falmata tayi ta fara takawa cike da nutsuwa, tana nufar sa, murmushi suka sakarwa juna, sanda suka haɗa ido, Umma idanu ta zuba musu tana kallon ikon Allah sai yanzu ta ƙara tabbatar da cewa yaran nan suna son junansu, sanda ya sauƙa daga step ɗin jirgin Falmata ta ƙarasa da gudu ta faɗa jikinsa tana sakin ajiyar zuciya mai sauti, hanunsa yasa ya riƙe bayan ta, yana jin wata nutsuwa na sauƙa masa a jikinsa, a kunne ta raɗa masa.
” Welcome DOCTOR na, yau ina cikin farin ciki da dawowar ka.”
Murmushi shima ya saki tare da manna mata kiss a goshin ta cewa yayi a hankali.
” Nafi Kowa jin daɗin dawowata domin kuwa nayi missing ɗinki sosai matata, ina ga dai kin manta da Umma tana wajen nan ko.?”
Saurin sake DOCTOR tayi, cike da kunya domin kuwa zumuɗi da jin daɗin ganin mujin nata ya sata mancewa da Umma tana wajen, murmushi ta saki tare da sunkuyar da kanta, murmushi DOCTOR ya saki shima tare da kama hanunta, suka nufo Umma, Umma murmushi take musu tana jin ƙaunar su na ratsata, Sanda DOCTOR ya ƙaraso wajen mahaifiyar tasa ne ya saki Falmata tare da rungume Umma, yana dariya.
” Naji daɗin ganinki Umma na, sosai nake kewarki, Umma ina Aunty JALILA bata zo tarba ta ba.”
Murmushi Umma ta saki tare da ɗago sa daga jinkita tace.
” Barka da dawowa ɗana, yanzu ba lokacin amsa tambaya bane, muje gida ka huta tukunna sai na amsa maka tambayar ka, Umma kallon Falmata tayi da kanta ke ƙasa wai ita a dole kunya murmushi ta saki tace, Oh wai ke yanzu kunya ta, kike ji, kinga ƴata, daina wannan kunyar keda yayan ki, kuzo muje gida, Oh ina Saif ne kam ban gansa ba tare da kai.?
Murmushi DOCTOR ya yi yana shafa kan Fanna dake maƙale jikinsa yace.
” Umma ai tun jiya Saif ya shigo ƙasar nan, nima sun ɗan dakatar dani ne dalilin dayasa kenan ya rigani dawowa kar dai baizo miki ba?.”
” Kajika da wani zancen, ya dawo jiya ya zo min ko hutawa baiyi ba, kaga muje gida ka samu ka huta.”
Cewar Umma, Bello akwatin DOCTOR ya jawo, suka shige cikin motar, suka nufi gida.
A falon Umma DOCTOR ya sauƙa yayin da mutanen gidan sai famar shigo masa sannu da dawowa suke, yayin da yake amsawa cike da farin ciki, Hajja cike da tsokana ta shigo tana dariya ta zauna kusa dashi tare saka hanu ta daki kansa.
.
” Kai kai!!! Hassan anya kuwa karatu ka tafi kaga kuwa yanda ka dawo Wani ƙato, ƙiba fa kayi, malam kai da ya kamata ka rame sai kuma ka dawo jibgege, kai ina da sake ban yarda da wannan ƙibar ba.”
Dariya DOCTOR yayi tare da faɗawa jikin Hajja ya kwanta yana cewa.
” Ban rame ba, sai kizo ki ramar dani ai, kuji min tsohuwa da saka ido.”
Hajja cike da dariya tace na saka idon, harna kai wannan matar taka saka Ido sauƙa min a jiki karda ka karya ni, ta ƙarasa Maganar tana nuna Falmata.”
Harara Falmata ta sakar mata, tare da miƙewa tsaye tana ƙoƙarin fita ta cewa Hajja.
” Ni dai nafi ƙarfin ki nida mijina sai dai kije ki rungumi wannan tsohon.”
Ta ƙarasa maganar tare da ficewa Umma dariya tayi tace,
” Kinci uwaki Hajja kike tsigalewa uwar tamu.”
Daga wajen tace.
” Umma ai ku ta haifa mukam bata haife muba.”
Dariya Hajja tayi cike da ƙaunar jikokin nata, sai a lokacin DOCTOR ya dubi Hajja yace.
” Hajja ina Bulama.”?
” Yana can kwance cikin ɗaki zazzaɓi ke damunsa tun jiya.”
” Subabanallah DOCTOR ya furta tare da cewa.
” Hajja an kaisa asibiti kuwa.”?
” An kaisa sun masa allura tare da magani suka basa.”
” Okay Allah ya basa lafiya zan shigo na dubasa yanzu insha Allah.”
Ya ƙarisa Maganar yana tashi daga jikin Hajja, Hajja ta juma zaune kafin ta fice, ya saura daga shi sai Umma da AJIRAM sai Fanna, Falmata ce ta shigo hanunta ɗauke da, tire jere da kuloli ta ajiye gaban DOCTOR ficewa tayi daga cikin falon domin basu lokaci su gana da mahaifiyarsa, Fanna itace ta sunkuya ta zuba masa abinci, sauƙowa yayi ƙasa tare da kalmashe ƙafar sa ya jawo abincin, tuwo ne miyar ɗanyen kuɓewa best food ɗinsa kenan idanunsa ya lumshe, ko baa faɗa ba yasan wannan girkin Falmata ne tayi sa, ruwan wanke hanu ya jawo ya wanke hanunsa, abincin ya ja gabansa da Bismillah ya fara ci cike da jin dadin abincin, domin kuwa sosai yayi missing ɗin abinsu na Nigeria, sosai DOCTOR yaci abincin kafin yayi hamdala yana godewa Ubangijin sa, Umma cikin murmushi tace.
” Wannan shine kura ta gamu da abincin ta nama ai kuwa sai wawa, a ƙaro ko ka ƙoshi.?”
Murmushi ya saki yace.
” Umma nayi missing ɗin abincin ne fa sosai kinga kuwa ai dole naci na ƙoshi, na ƙoshi ma Alhamdulillah!!, Umma Baba baya nan ne naji shuru.”
” Eh yaje Gombe, tun jiya amma may be ya dawo nan da kwana uku.”
” Okay Allah ya dawo dashi lafiya, Umma bafa dawowa nayi Nigeria duka ba, zan koma next week, sun ɗauke ni aiki a can India sai dai gaskiya Umma naƙi yadda nayi aiki a ƙasarsu nafi son nazo na hidimtawa ƙasata Nigeria, amma sun roƙeni da nayi aiki dasu na shekara ɗaya kawai, kuma na amsa aikin, next week zan koma, sun bani gidan da zan zauna harna gama shekara ɗaya da zanyi da kuma motar hawa, shine nake son na koma da Falmata, sannan Umma asibitin da suke buƙatar nayi aiki dasu sun bani kyautar kuɗi har Naira Miliyan 6.”
Shuru Umma tayi kafin tace.
” Da a son raina ne da gaskiya bazaka koma India ba, gara ka nemi aiki a Nan gida Nigeria, amma tunda ka musu alƙawarin komawa, ka koma Allah yasa kan alherin ka zakaje, sai maganar tafiya da matar ka wannan hukuncin ba’a hanuna yake ba, yana hanun iyayenka maza duk abinda suka yanke akai mu mata a wajen mu daidai ne, yanzu wannan kuɗin me zakayi dasu.”
Amsa ya bata take da cewa.
” Asibiti zan bayar a gina min kafun na dawo zan nemi manyan likitoci harma da nurse domin mu raya asibitin, tunda ina da lasin ɗin da zan iya buɗe asibiti na, na kaina Umma, kinga da zarar na dawo kuma, duk abinda na samu sai muyi odan kayan aiki dasu, hakan zaifi min samun kudi sosai fiye da nayi aiki a ƙarƙashin wani, Maganar muhallin da zan zauna kuma shima insha Allah, zanyi sa, tunda yanzu Baba Bukkar ya bamu wajen zama.”
Cike da gamsuwa Umma ta gyaɗa kanta alamun ta gane, fatan alheri ta masa, sannan ya ƙara tambayar ta Aunty JALILA.
” JALILA tana gidan ta, kasan cikin ta ya tsufa, tafiyar tana bata wuya, gashi dama kasan tana da matsalar ƙafa.”
Murmushi DOCTOR ya saki cike da farin ciki, wai yau AUNTY JALILAN sane tayi Aure harda ciki, lallai ne duk abinda yayi farko zaiyi ƙarshe, cike da annuri yace.
” Umma, insha Allah zan kawo karshen matsalar ƙafar Aunty JALILA, bari naje nayi wanka zan ɗanyi bacci idan na tashi zanje gidan nata.”
Ya ƙarasa maganar yana tashi, Kaɗa masa kai Umma tayi tace a fito lafiya, ɗakinsa na zaure ya shige, wanka yayi ya saka tree cutter da best kwanciya yayi bai juma da kwanciyar ba kuwa bacci ya kwashe sa.
Falmata kuwa AUNTY YANA ta sata cikin ɗaki, sai ɗure ɗure take mata, turaren wuta gaf-gaf na tsugunno ma, dabam na musamman tasa aka mata shi, harda haɗin wankan lalle, wani ruwan gora da Aunty YANA ta bawa Falmata tasha mai shegen bauri sai famar haɗa rai da yamutsa fuska Falmata take sha, Aunty YANA tsawa ta daka mata tace.
” Kifa shanye Falmata bana son shashancin banza!!! Dan ubanki meye abin taɓe fuska a wannan.”
Tura bakinta Falmata tayi, bata ce komai ba, har ta shanye, nuni Aunty YANA ta mata da tollet tace.
” Ki tashi ki shiga, akwai ruwan lallai a cikin baho ki shiga ki zauna a ciki na 30 minute, idan kin gama karki tashi kimin Magana zan kawo miki kasko ki tsugunna.”
Da to Falmata ta Amsa tana shigewa cikin tollet ɗin, duk abinda Aunty YANA ta umurce ta haka tayi, sanda ta fito gabaki ɗayan ta ƙamshi take rusunanne mai daɗin shaƙa, domin kuwa shi kanshi lallen data shiga da kuma wanka dashi, turaruka ne kala-kala masu daɗi shaƙa, zama tayi tana fuskantar Aunty YANA, Aunty YANA ce mata tayi.
” Ki ɗauki haɗin zumar nan ki shanye duka karki barmin ko kaɗan.”
Tura bakinta Falmata tayi tana cewa.
” Na shiga Uku Mama nikam ki bari sai anjuma, yanzu fa nasha bauri kuma nazo sha zaƙi yanzu, kusan sati biyu fa Mama, kina bani waɗannan abubuwan.”
Haɗa rai Aunty YANA tayi cikin faɗa tace.
” Kinci UBANKI nace kinci UBANKI!!!! Bana son Iskanci wallahi, ki ɗauka kishanye kafin na ɓata miki rai.”
Tana tura bakin ta Falmata ta ɗauka, ta kai zumar kenan bakin ta, taji ringin ɗin wayarta, ajiye zumar tayi ta ɗaga wayar HANNA ƙanwar Maji ce tace.
” AUNTY Falmata, Mijin Aunty Maji ya rasu yanzu aka sanar damu boko haram sun kashe sa.”
” Innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un allahumma ajirni fil musibati!!!! Yanzu ina Maji take, tana halin lafiya.”
” A’a Aunty Falmata tun ɗazu take suma fa, mun rasa ya zamuyi.”
” Ina zuwa yanzu” Falmata ta furta tare da kashe wayar tace.
” Mama mijin Maji ne ya rasu, Boko Haram, zan tafi wajen ta bansan Wani hali take ciki ba.”
Salati Aunty YANA ta ɗauka cike da tausayawa Maji domin kuwa mutuwar miji akwai zafi, cike da alhini tace.
” Ki tambayi mijinki tukunna Kafin ki tafi, Allah ya jiƙansa da rahama yasa mutuwa hutu ce a garesa, wannan masifar ta Boko Haram ta addabemu.”
Falmata ficewa tayi da mayafin ta a hanu cike da tashin hankali, ta faɗa ɗakin DOCTOR yana kwance sai baccin sa yake cikin kwanciyar hankali faɗawa tayi jikinsa ta saki kuka mai sauti na tausayin Maji, DOCTOR kamar a mafarki yake jin sautin kukan nata, jin abin yaƙi ƙarewa ya sashi buɗe idanunsa a hankali, sai kuma ya waresu fes a kanta cike da tsoro yana duban yanda ta dunƙule a jikin sa sai shan kukanta take a hankali cikin tashin hankali ya ambaci sunan ta.
” *FALMATA*”
Idanunta da suka sauya kala zuwa red ta ɗago ta dubesa dasu hawaye na ƙara gudu mata.
” Ke da waye, me aka miki.?”
Ya jefa mata tambayar cikin sarƙewar murya tace.
” DOCTOR Maji mijinta ya rasu, tana can cikin tashin hankali bansan wani hali take ciki ba, ji nake a zuciyata ya zanyi idan akace min ka mutu, ina kwatanta Zafin da zanji idan har na rasaka, na Tabbata itama maji irin wannan Zafin take ji tana sonshi kamar yanda nake sonka, gashi yanzu ya tafi ya barta, sun kashe mata shi, shin sai yaushe ne al’ummar Borno zasu daina tsoro da zullumin rayukansu, yaushe sojojin ƙasar mu zasu sami kwanciyar hankali, amsar ɗaya ce, bamu san lokacin ba, ina tausayin aminiyata DOCTOR, na Tabbata yau tana cikin tashin hankalin da bazan iya misilta maka shiba, ka barni naje gareta.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya sauƙe cikin sanyin jiki da tausayin Maji, miƙewa yayi ya zauna tare da jawo Falmata jikinsa ya mannata da ƙirjinsa wani laushi yaji fatar ta ta masa tare da wani ƙamshi mai daɗin shaƙa lumshe idanunsa yayi ya buɗesu cike da nutsuwa yace.
” Komai Soyayya da shaƙuwar zuciya biyu, dole sai mutuwa ta shiga tsakani, kota ɗauke ɗaya tabar ɗaya ko kuma ta ɗauke su duka lokaci guda, amma babu wanda mutuwa zata ƙyale, Falmata duk yanda zaki so masoyinki karki saka a ranki cewa bazaku taɓa rabuwa ba, akwai ƙaddara akwai kuma mutuwa, dole ne sai sun shiga tsakani, kuka ko damuwa bashi ne abinda ake yiwa masoyi ba, bayan an rabu dashi, addu’a da kuma sadaka shine babbar Soyayyar da zaki cigaba da masa bayan kin rasashi, mutuwar masoyi bashi bane yake nuna ƙarshen Rayuwar masoyiya ba, dole zata rayu koda kuwa zata kasance da ciwon sonsa, ki masa gata bayan sa da addu’a da sadaka, ki riƙe wannan a ranki, sannan ke yanzu kina nufin a haka zakije mata, kina kuka tana kuka babu mai rarrashin kowa a cikin ku, ke ya kamata ki danne damuwarki ki rarrashi ƙawarki, saboda yanzu zuciyarta rarrashi take buƙata, gatan da zaki mata shine ki ɓoye wannan damuwar taki, ki Kuma share hawayenki, sai kije kiyi ƙoƙarin share mata nata Hawayen dan Allah karki karya mata zuciya idan har kinsan bazaki iya rarrashinta ba, Please karki jeki.”
Shuru Falmata tayi tana laɓe a ƙirjinsa sai famar sauƙe ajiyar zuciya take, ta kuma kasa Magana domin kuwa maganganun DOCTOR sun kashe mata jiki, ita a nata ra’ayin ta rayu dashi har ƙarshen rayuwarta, sai kuma gashi shi yana sanar da ita cewa dole sai ɗaya ya tafi yabar ɗaya, ita zata fi so koda mutuwa zata shiga tsakanin su, zatafi so ta fara ɗaukar ta, kafin shi, bata son ganin ranar da ƙaddara zata rabasu da numfashin su, domin kuwa itace ranar da zatafi ko wacce rana muni a rayuwarta, a hankali ta furta masa.
” Zan adana Hawaye na, domin ganin na rarrashi Maji, sai dai fuskata bazata taɓa ɓoye tausayi da kuma alhinin rashin da tayi ba, Zan bata kulawar data kamata ƴar uwa ta jini ta bawa ƴar uwar ta, domin kuwa tsakanina da Maji ya shige ƙawance ko aminta, jini ɗaya nake ɗaukar ta, kamin na tafi gareta.”
Kanta DOCTOR ya shafa tare da manna mata kiss a dokin wuyan ta, hanunsa yasa ya jawo Briefcase ɗinsa, kuɗin Nigeria ya ɗauko 3k ya ware tafin hanunta ya danƙa mata tare da cewa.
” Na miki izini kije Allah ya jiƙansa, ki sanar dani lokacin jana’izar sa, ko ta waya ne insha zanzo.”
Hawayen ta ta goge tare da kaɗa masa kai alamun to, sannan ta tashi ta tafi, cike da ƙauna ya bita da kallo harta fice, tashi yayi ya shige tollet wanka yayi, ya fito shafe shafen sa, yayi kasancewar shi mutum ne mai son gyaran jiki da ƙamshi tamkar mace, cikin Black jeans da Yellow riga ya shirya, ya fito da niyyar zuwa gidan Aunty JALILA, sashin Hajja ya nufa, kafin ya shiga wajen Hajja sai da ya shiga falon Aunty YANA da Sallama amsawa tayi tana masa maraba, ƙarasowa yayi ya zauna yana cewa.
” AUNTY sannu da hutawa mun sameku lafiya.”
Murmushi Aunty YANA tayi tace.
” Alhamdulillah mutanen India kunje can kun ɓace abunku, ya karatun an gama cikin Nasara, abu yayi kyau sosai Allah ya sanya alkairi.”
Murmushi DOCTOR yayi tare da cewa.
” Ameen AUNTY, bari na shiga na duba Bulama da jiki, ya labarin Ibrahim yazo kuwa.”
” Ibrahim baizo ba, amma dai yace insha Allah ya na hanya.”
“Allah ya kawo sa Aunty”
Doctor yana ficewa, ɗakin Hajja ya shiga shuru yaji falon nata babu kowa da alamu tana ɗakin Bulama fitowa yayi ya shige ɗakin Bulama, tana nan kuwa zaune harda Baba Bukkar Bulama sai famar jan numfashi yake da ƙyar, kusa dashi DOCTOR ya zauna yana cewa sannu Bulama, kai kawai ya ɗaga masa numshin dake fito masa da ƙyar shiyake hanasa Magana, duban Baba Bukkar yayi ya gaishe sa, amsawa Baba Bukkar yayi cike da fara’a yace.
” Ɗazu ai da YAHANASU take sanar dani dawowarka, naso shigowa sai kuma Allah baiyi ba, bana gusawa kusa da Bulama, saboda baya jin daɗi SOSAI.”
Kaɗa kansa DOCTOR yayi yana ɗan gwale idon Bulama, yace.
” Ayya ba komai Baba Amma ya kamata Bulama a kaisa asibitin kustin, zazzaɓin fa da alamu ya fara ƙona masa jini, ayi gaggawar kaisa kafin rai yazo yana ɓaci.”
” Hakane Hassan, yanzu ka tashi kaje ka ɗauko mana mai adaidaita, sai mu tafi asibitin.”
Cike da nutsuwa DOCTOR yace.
” Baba ai akwai motar gida naga, me zai hana a kira BELLO sai yazo aje asibitin.”
” To shikenan kirasa.”
Cewar Baba Bukkar, Doctor wayarsa ya ɗaga tare cewa Bello yazo yanzu za’a kai Bulama asibiti, bayan ya gama wayar ne ya dubi Baba Bukkar yace.
” Baba na masa magana yana zuwa yanzu, ni yanzu zanje na duba Aunty JALILA bata jin daɗin ƙafar ta itama, daga can zanzo asibitin na sameku.”
A dawo lafiya Baba Bukkar ya masa sannan DOCTOR ya fita yana yiwa Bulama sannu, bai juma da fita ba kuwa Bello yazo suka wuce asibitin.
*GIWA BARECK*
DOCTOR bai sha wahala ba wajen gane gidan Aunty JALILA kasancewar, mijinta babban mutum ne wanda kowa ya sanshi, bakin makeken get ɗin ya tsaya tare da ƙwanƙwasawa mai gadi ne police ya buɗe, tsayawa yayi tare da ƙare masa kallo yace.
” Wajen wa kazo ka.”
Amsa DOCTOR ya basa da cewa.
” Wajen Jalila nazo matar gidan.”
Mai gadin gidan cewa yayi.
” Okay to kayi haƙuri amma gaskiya nan ba’a shiga sai da ambada sanarwar cewa zaka zo, ni kuma ba’a bani izinin zuwanka ba.”
Murmushi DOCTOR ya saki tare da cewa.
” Ba komai officer, jeka kawai.”
Shigewa ciki yayi shi kuma DOCTOR ya zaro wayarsa, numbern AUNTY JALILA ya kira sam baiso tasan da zuwan sa ba, yafi so yayi mata suprice, muryar ta yaji ta cikin wayar tana cewa ” ƙanina nayi laifi tuba nake ”
Dariya DOCTOR ya saki yace.
” Tunda baki zoba aini gani a ƙofar gidan ki, Hajiya JALILA an hanani shiga gidan manyan mutane”
Cike da mamaki Aunty JALILA tace.
” Dan Allah da gaske kake ko kuma wasa kake min.?”
” Serious AUNTY Wallahi ina ƙofar gidan ki.”
Katse wayar Aunty JALILA Tayi tana duban HABEEB dake zaune tace.
” Abokinka ne mutanen India wai yana waje an hanasa shigowa, dan Allah taimaka kaje ya buɗe masa get ya shigo, murmushi HABEEB ya saki tare da ɗaga Salma dake kwance jikinsa tana bacci ya kwantar da ita a kujerar, ya tashi tare da fitowa, a wajen mai gadin ya tsaya cike da Zolaya yace.
” Officer yau fa ka tabka babban laifi taya zaka hana ɗan masu gida shigowa, gidan su, Lallai yau Aunty zataci tararka, ka hana ɗan lelenta shigowa.”
Ya ƙarasa maganar cike da dariya officer cewa yayi.
” To ai ban sanshi bane, shiyasa da gaske dangin kune.”
” Ƙanin Aunty ne uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, ita yake bi, kuma ɗan lelenta ne, daga yau karka kuma hanasa shigowa GIDAN NAN bashi da shamaki da gidan.”
” Insha Allah bazan sake ba.”
Officer ya faɗa yana tashi ya buɗe ƙofar, DOCTOR dake tsaye ne yaga buɗewar get ɗin umarni ya masa daya shigo.
Shigowar yayi, HABEEB dake tsaye ne ya saki murmushi tare da cewa.
” Welcome DOCTOR HASSAN.”
Yana miƙa masa hanu suyi musabaha, kau da kansa gefe DOCTOR yayi tare da shigewa yana jawa HABEEB tsaki, murmushi HABEEB ya saki yana kallon rashin hankali da raini irin na DOCTOR, sam bashi da hali mai kyau ko kaɗan……………………
Kuyi hkr da wannan insha Allah gobe zaku sami read more kamar na yau..
Wannan littafin na kuɗi ne karki karanta min idan baki biyu ba, ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[10/3, 8:04 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 75 to 76*
_________✍🏻Girgiza kansa kawai HABEEB yayi tare da ficewa daga cikin gidan gabaki ɗaya domin kuwa bazai iya komawa cikin gidan ba, Hassan yana masa kallon banza zuciyarsa bazata daurewa hakan ba ya rasa wani irin baƙar gaba Hassan yake masa yau ko wani ɗan uwan sa ya kashe masa iyakaci kenan, balle kuma akan mace hmmmm!!! Ya sauƙe ajiyar zuciya tare da ficewa, mai gadi kuwa cike da ɗaurewar kai yake duban su, idan ba saɓanin fahimta yayi ba, sai ya ga kamar wannan bakon gaba yake da Oga HABEEB sunan daya ke kiran sa dashi kenan, ajiyar zuciya ya sauƙe ganin bashi da amsar tambayar sa, shi kuwa DOCTOR cike da ɓacin ran ganin HABEEB ya shiga falon Aunty JALILA da yasan zai haɗu da HABEEB da baizo ba, tana zaune tana yanke farcenta ya shigo da Sallama, dariya tayi cikin farin ciki tace.
” Oyoyo ƙanina, ka rigani zuwa, amma dai ni naso zuwa maka sannu da zuwa kafin kai kawai saurin zuwa kayi.”
Dariya DOCTOR yayi yana zama gefen da Salma ke kwance yace.
” Ke dai kawai kinga nazo ne, kunya ta isheki shiyasa zaki kare kanki, Umma ta faɗa min ƙafarki ke ciwo, AUNTY nayi farin ciki sosai yau da na ganki a cikin gidan ki na Aure gashi har na kawo miki ziyara ina zaune ɗakin ki, hmmm ko yanzu na godewa Ubangiji ya gama cika min burina, gashi yau har saka rai ake da ganin zuwan ɗanki ko ƴarki duniya, Allah ya sauƙeki lafiya AUNTY.”
Murmushi Aunty JALILA tayi tana jin ƙaunar ɗan uwanta yana ratsata, cike da nishaɗi tace.
” Nima KULLUM nakan godewa Allah, daya min ni’ima ta Aure wanda a baya na fidda rai da samunsa, gashi yanzu jinkiri ya zamo min alkairi, Tabbas ba macen da zatayi jinkiri bai zamo mata alkairi ba, na samu miji na gari mai kula da iyalansa haka ma danginsa mutanen ƙwarai musamman Momy mahaifiyar HABEEB, ta riƙeni tamkar ƴar da ta haifa a cikin ta yaran mijina sun ɗauke ni tamkar mahaifiyar su, basa min raini kuma basa son ɓacin raina, bani da damuwa yanzu ina cikin fari.”
” Alhamdulillah!!! Naji daɗin jin wannan labarin, Tabbas kowa ya ganki yasan kina cikin kwanciyar hankali, sai fatan Allah ya sauƙeki lafiya.”
Da ameen AUNTY JALILA ta amsa tare da tambayar sa.
” Wai ina HABEEB ne ban gansa ba, ka barsa gun officer ko nasan shi idan ya haɗu da officer sun dinga calikanci kenan.”?
Girgiza kansa DOCTOR yayi tare da cewa.
” No ya fita, bansan ina yaje ba gaskiya.”
Yayi Maganar yana haɗe ransa.
” Ya tafi kuma, ko dai ka masa hali, kaga Hassan, abinda kake fa baya dacewa, SAIF ya sanar dani duk wani abinda yake faruwa tsakanin ka da HABEEB akan Falmata, HABEEB ba mutum bane wanda ya cancanci wulaƙanci daga gareka, mutum ne wanda ya kamata ka riƙesa riko na mutunci, domin kuwa HABEEB mutum ne shi mai alkairi da kuma daraja ɗan adam mutumin da baya ƙyamar talaka, ko yaya kake zai zauna dakai, dan Allah karka zamo mutum mai saka alkairi da sharri, komai tsiyar HABEEB, kaikam ya taimakeka ya maka rana, ba gori nake maka ba, gaskiya nake faɗa maka, domin kuwa duk wani matsayi da zaka taka a duniya shine silar hakan, koda kuwa shugaban ƙasa ka zamo, ka janye gaba tsakanin ku domin kuwa sam hakan ba daidai bane, akan mace kake wannan gabar kuma kaine kayi Nasarar auren ta, to meyasa bazaka manta komai ba, ku dawo Kamar da, ina faɗa maka gaskiya ne fa a matsayina na ƴar uwar ka Hassan wacce bazan so na barka cikin ɓata ba, dan Allah ka rage wannan Zuciyar ta ka HABEEB bai kamaci wulaƙanci ba.”
” Hmmm!!! Aunty kenan, wai meyasa mutane suke min gori ne akan wannan Hanyar karatun da HABEEB yamin na tafiya India, wannan karatun fa Allah ya ƙaddara sai nayi shi, koda taimakon HABEEB ko ba taimakon sa dole sai nayi tunda Ubangiji ya hukunta hakan, sannan wannan kuɗin karatun fa, ba kuɗin ubansa bane kudi ne na gwamnati, haƙƙin mune, akan me za’a dinga min gori, ko dole ne sai nayi aminta dashi, ubanane shi waye shi, kowa yayi harkar sa mana, nace bana ƙaunar sa dole ne sai na sosa ko ana tilastawa zuciya sosai ne.”
Girgiza kanta Aunty JALILA tayi cike da jin haushin bak’ar zuciyar ɗan uwan nata tace.
” Ba a tilastawa zuciya sosai amma ana tilastawa zuciya hallaci, bakaji karin maganar nan ta Hausawa ba, *ANA BARIN HALAK KO DAN KUNYA* meyasa kai zuciyarka ta kasa yiwa HABEEB uzuri, tana neman mayar dakai butulu, koda kuɗin gomnati ne, ai dai shine ya maka hanya ko? Idan bai maka Hanyar ba, a ina zaka samu haƙƙin naka da kake ambaton sa, ka dawo hankalin ka, ka fara gane mai sonka, domin kuwa ba kowa bane yake zama maƙiyi, domin kuwa HABEEB ba ƙaramin masoyinka bane, amma bak’ar zuciyar ka ta hana ka gane hakan me ka ɗauki Soyayya gaba, idan har haka taka Soyayyar take to Wallahi zuciyarka bata maka adalci ba, bai kamata Soyayya ko kishi ya rufe maka idanu daga ganin gaskiya ba, ka gyara kaje ka nemi HABEEB ku daidaita na Tabbata shi baya fushi da kai, Hassan yau na faɗa maka gaskiya koda kuwa zakaji haushi na.”
Tunda ta fara Maganar yake kallon ta harta kai ƙarshe Kafin ya miƙe yana taɓe baki yace.
” AUNTY ki gafarce ni, AMMA bazan taɓa shiryawa da HABEEB ba, saboda ni ina hango abinda ku kuka kasa gani, har yanzu ina kallon Soyayyar matata a cikin idanunsa, zuciyata bazata taɓa aminta dashi ba, dan haka ku daina danganta zuciyata da wannan matsalar, idan kuma laifin zuciyartawa ne, to tayi a daidai, domin kuwa tana kishin abinda take so ne, amma ki sani har abada bazan taɓa jin haushin ki ba, koda kuwa rufeni kikayi da duka, kin kai kimin faɗa ne shiyasa kika min, na tafi dama ba zama nazo yi ba.”
Ya ƙarasa maganar yana juyawa zai bar falon, Magana Aunty JALILA take masa, amma bai saurareta ba, saboda ya hau dokin zuciya yana tsoron ya tsaya zuciyarsa ta kasa jure Maganganun ta, har ya faɗa mata abinda bai dace ba, gara kawai ya tafi abinsa numfashi Aunty JALILA ta sauƙe tare da furta.
” Ikon Allah, wai mutum Zuciyarsa harta rinjayi tunanin sa, Allah ka yayewa ɗan uwana wannan Zuciyar tasa, ta ƙarasa maganar tana cigaba da yanke farcenta.
Can kuwa gidan mutuwar, Maji tana jikin Falmata har yanzu bata daina zubar da Hawaye ba, hankalinta har yanzu yana tashe Falmata cike da raunin murya tace.
” Maji dan Allah ki daina kukan nan, ko kin manta cewa, dukkan mai rai mamaci ne, Allah Shida kansa yace ” KULLU NAFSIN ZA’IƘATUR MAUT” to meyasa zaki kasa haƙura da hukuncin Ubangiji, addu’a da sadaka shine gata da zaki masa bayan babu numfashin sa, domin kuwa zai iskesa har makwancinsa sa, kinga kenan kina nan kina aika masa Soyayyar ki yana kwance cikin kabarin sa, dan Allah ki daina kukan nan haka Maji babu kyau yiwa mamaci kuka.”
. Sharce majinar da ta zo mata Maji tayi, tayi shuru tana sauƙe ajiyar zuciya ba tare da tayi Magana ba, sai ajiyar zuciya kawai da take famar sauƙewa, Mama mahaifiyar Maji Falmata ta kalla tare da ce mata.
” Mama yaushe ne za’ayi sallar jana’iza zan sanar da DOCTOR ne.”
Mama cewa tayi.
” Sunce sai zuwa yamma ko gobe saboda sai anyi cike cike kafin a kawo su amma dai basu saka lokaci ba.”
Kaɗa kanta Falmata tayi, ita kuwa Maji shuru tayi sai ambaton sunan Ubangiji take, a hankali take jin damuwar na ɗan mata sauƙi.
Tunda aka yi mutuwar Falmata bata koma gida ba, sai da akayi sadakar uku, Aunty YANA da Umma tare sukaje suka yiwa Maji ta’aziya Umma sosai ta yiwa maji nasiha tare da nuna mata girman haƙuri, shima DOCTOR tare sukaje da SAIF suka musu ta’aziya.
Bulama shima kwanan sa Uku a asibiti amma jikin nasa babu sauƙi, su kansu likitocin sun kasa gane abinda yake damunsa, sun san yana da hawan jini amma ba shine Abinda yafi damunsa ba, Baba ko da ya dawo daga Gombe sosai yasha kuka yanda yaga halin da mahaifin nasa yake ciki, DOCTOR da yaso ya fasa tafiya da Falmata ya je da Bulama can India a duba lafiyar sa, amma Bulama yaƙi yadda yace shi a barshi a masa jinya a kasarsa babu yanda suka iya dole suka haƙura suka barsa.
AUNTY YANA kuwa musamman ta ɗauki Aunty Ladi take yiwa Falmata gyaran jiki, kasancewar Aunty Ladi SOSAI ta iya gyaran jiki, ɗure ɗure kuwa sosai take mata, a cikin kwana Biyar Falmata tayi wani irin haske na ban mamaki, fatarta kuwa tamkar fulawa haka ta zama tsabar santsi, ƙamshi kuwa duk inda ta gifta sai anji sa, AUNTY YANA sosai ta saka mata Ido da zuwa ɗakin DOCTOR, rabonta da ɗakin tun sanda taje ta sanar dashi mutuwar mijin Maji, bata sake komawa ba, sakamakon warning ɗin da Aunty YANA ta mata sai dai su gaisa idan sun haɗu a ɗakin Umma ko ɗakin Hajja, DOCTOR SOSAI ransa ya ɓaci da tsakani da Aunty YANA ta musu sai dai bashi da halin Magana yasa shi haƙura Dole.
Falmata komawarta gidan Maji sau uku a cikin sati biyu, Alhamdulillah yanzu Maji ta ɗan sake har tana walwala da mutane.
Aunty LADI gyaran sati Uku ta yiwa Falmata, amma kuma ta gyaru, tayi kyau sosai jikinta gwanin ban sha’awa.
***************
Zaune yake gaban Baba Bukkar da Baba cikin fada DOCTOR ne yace.
” Baba jibi zan koma India, sai dai ina sone zamu tafi da Falmata, shekara ɗaya kawai zamuyi mu dawo.”
Cike da nutsuwa Baba yace.
” Allah ya kaimu, mahaifiyarka ai ta sanar dani rashin lafiyar Bulama yasa ban samu na zauna da kai ba mun tattauna, zaka iya tafiya da ita, matarka ce ai kana da iko da ita, amma Hassan da zan baka shawara da nace gidan da suka baka ka sai dashi tunda bawai Rayuwa zakayi a can ba, ka aiko da kuɗin nan gida Nigeria, akwai fili na a New GRA na mallaka maka shi, sai a tada gini kaga kafin ka dawo an kammala komai ina tunanin hakan zaifi, can kuma sai ka kama haya.”
Shuru DOCTOR yayi yana nazarin Maganar Mahaifin nasa, Tabbas hakan zaifi domin kuwa idan ya sayar da gidan ya aiko kuɗin zai masa ginin da yake so, duban Baba yayi yace.
” Hakan yayi Baba insha Allah zan turo da kuɗin idan na koma, za muyi magana da Saif yayi Magana da Usman art ya turo min zanen gida sai na zaɓa na tura masa hakan yayi Baba.”
Baba Bukkar ne yace.
” Alhamdulillah!!! Masha Allah hakan ma babban arziki ne ka mallaki gidan ka na kanka, shine arziki, Maganar Falmata Kuma, ku tafi Allah shi muku albarka, zanyi Magana da Yana sai ta shirya ta zuwa jibin ku wuce.”
Godiya DOCTOR ya yiwa iyayen nasa, tare da tashi ya fito cikin farin ciki.
Hakan kuwa Baba Bukkar ya sanar da Aunty YANA da Hajja Maganar tafiyar su DOCTOR, babu wanda ya hana sai ma fatan alkairi da suka musu.
Ranar Lahadi da yamma ana gobe zasu tafi, DOCTOR ya shigo shida Saif hanunsu riƙe da manyan akwati biyu sai karami a hanun wani yaro, a ɗakin Umma suka ajiye, zama DOCTOR yayi ya cewa Umma dake kallon akwatin.
” Buɗe mana Umma ki gani”
Hanu Umma tasa ta buɗe akwatin farko cike yake da atampopi dukkan su kuma an ɗinka su, sai turame uku wanda ba’a ɗinka ba, cire ukun yayi ya ajiye a gefe, Umma rufe akwatin tayi ta sake buɗe na biyu, wasu arnan sleeping dress ne da kuma dogin riguna sai riga sket da kuma wanduna, sai set ɗin bireziya da hijab, sun kai kala hamsin, shima Umma rufesa tayi ta buɗe ƙaramin kayan makeup ne cike fal, dubansa Umma tayi tace.
” Waɗannan na menene.?”
” Umma Falmata na sayawa, na bawa Babawo ya dinke mata atampopi, saboda ba’a mata kayan lefe ba, kuma kinga zamu tafi India, bazai yiwu ta tafi ba ta da wasu kaya ba, wadannan atampopi kuma naki ne guda uku na sayan miki.”
Murmushi Umma ta sauƙe tare da cewa.
” Masha Allah, ka kyauta, Allah ya maka Albarka bari su Fanna su shigo sai su kaiwa Yana ko.”
Da to DOCTOR ya amsa sannan saif ya gaisa da Umma sun juma a wajen umman kafin ya tafi gidan Aunty JALILA mata sallama.
Itama Falmata ranar a gidan maji ta wuni sai magarib ta dawo koda ta dawo taga kayan da DOCTOR ya kawo mata sosai taji daɗin kayan.
Washegari da misalin karfe goma jirgin su DOCTOR ya ɗaga zuwa India shida matarsa.
Kuyi hkr ban samu nayi Editing ba, yau🤗🤗🤗🤗🤗
KI biya kuɗin ki ki karanta halak ɗinki yar uwa, karki na sata, ni bazan ja miki Allah ya isa ba, amma dai kinsan hukuncin wanda yaci haƙƙin wani ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*Alƙalamin RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[10/5, 10:22 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 77 to 78*
__________✍🏻 Tunda suka sauƙa a filin airport dake cikin garin Mumbai Falmata ta fara ware Ido tana kalle kalle, ikon Allah wai itace cikin ƙasar India mutanen da take ganin su cikin tv yau kuma gata gasu, tana kallon su, DOCTOR ne ya riƙo kunkumin ta, ganin tana neman shigewa cikin jama’a ta ɓace masa, gefe guda ya matsa da ita, tare da neman kujera suka zauna, ajiyar zuciya ya sauƙe yana duban wani mutum dake ajiye musu akwatin su a gefe, kallon sa Falmata tayi tana sakin murmushi tace.
” DOCTOR na ya muka zauna a nan kuma.?”
Murmushi ya saki cike da Zolaya yace mata.
” Saboda naga kamar baki gaji da kalle kallen bane ƴar ƙauyen Nigeria.”
Dariya Falmata tasa sosai har tana kwanciya kafaɗarsa ta maida masa amsa da cewa.
” Ai kuwa dole nayi ƙauyanci tunda nazo ƙasar da ban santa ba, Serious Doctor na, me muka tsaya yi anan.”
Murmushi ya saki yace.
” Motar da zata zo ta ɗauke mu muke jira.”
Kaɗa kanta Falmata tayi tana lumshe idanunta, basu juma ba kuwa motar ta zota, cike da fara’a kyakkyawan mutumin ya ƙaraso wajen su yana ƙarewa Falmata kallo, shima DOCTOR murmushi yayi tare da miƙa masa hanu.
” Welcome Hassan.”
Mutumin ya furta, murmushi DOCTOR ya saki yace.
” Thank Sanskar, nuni ya masa da Falmata yace she is my wife.”
” Murmushi Sanskar yayi tare da cewa.
” Wow Beautiful women, Black Beauty”
Ya faɗi yana ɗaga mata hanu,duka dariya sukayi, wannan mutumin Sanskar ya kira ya jidi akwatin nasu ya kai Motar suka shiga, tafiya suke Falmata tana karewa ƙasar kallo ta glass ɗin motar, wani makeken gida suka nufa, Darect kuwa aka wangale musu get ɗin, suka shige ciki, bayan sunyi parking ne, suka fito, DOCTOR shida kansa yake ƙarewa gidan kallo mai gadin ne ya fito da sauri ya jidi akwatin ya shigar dashi cikin falon, ciki suka shige har Sanskar falo ne mai kyawun gaske wanda ya tsaru da kayan more rayuwa babu abinda babu ciki, zama sukayi dukansu a kujerun falon, cikin harshen turanci Sanskar ya yiwa Falmata magana.
” Hi Madam, ki duba komai ya miki ko akwai abinda kike buƙata wanda babu a cikin gidan nan.”
DOCTOR kallon Falmata yayi yaji mai zatace, cikin harshen turanci kuwa ta basa amsa da cewa.
” No ba sai na duba ba, komai ma yayi daga ganin tsarin falon.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya sauƙe sosai yaji daɗin amsar da Falmata ta bawa Sanskar, yayi zaton zata ce da akwai abinda bai yiba amma bisa mamakinsa sai yaga ta nuna godiyar ta bisa abinda ta tarar, kaɗa kansa Sanskar yayi cike da gamsuwa, ya sanar dasu cewe akwai abinci a daining table, sannan ya tafi, bayan ya tafi ne Doctor ya kalli falmata cike da murmushi yace.
” My dear naji daɗi da kika nuna masa karamci baki nuna masa zalama ba.”
Ya ƙarasa maganar yana kanne mata ido, murmushi Falmata tayi tare da cewa.
” To ma meye baiyi ba, a cikin falon nan, komai yayi gaskiya duk wanda ya shirya wannan falon tabbas yasan designing.”
” To yanzu bari na ɗauki akwatin nan na shigar dashi ciki, muje kiga bedrom ɗinki ko.”
Tashi falmata tayi tana murmushi ta ɗauki ƙaramin akwatin suka haura sama, bedroom ne mai kyawun gaske, gado da durowa sai dressing mirro da kuma kujera ɗaya, a ciki sai tollet, mai kyau da tsari babu abinda babu cikin tollet ɗin.
” Komai yayi doctor na, bedroom ɗin So Beautiful colour.”
Dariya doctor ya saki tare da cewa.
” Masha Allah sarkin son Pink colour, to yanzu sai kiyi wanka ki gyara abubuwan da bai miki daidaiba, nima bari na shiga wannan bedroom din dake gefenki, na watsa ruwa, idan kin gama ki sameni a daining ko.”
Ɗaga masa kai falmata tayi alamun to sannan ya fice, falmata bata shiga wankan ba, sai da ta ɗan yiwa bedroom ɗin gyara, sannan ta shige wankan fitowa kuwa tayi ɗaure da towel ta tsane ruwan jikinta, cikin wasu riga da sket na kanti ruwan maroun kanta hula ta saka masa fari, sannan ta feshe jikinta da turare da humra, wani shu’umin ƙamshi ne ke tashi a jikinta, sannan ta fito, ƙarar tv da taji shine ya sanar da ita yana ƙasa, ai kuwa gangarowa tayi, tun kafin ta iso ƙamshinta ta sanar dashi zuwan ta, juyowa yayi yana kallon cike da so da ƙauna, sosai ta masa kyau cikin riga da sket ɗin alama ya mata da tazo garesa da hanunsa, ƙafarta ta maƙale tare da nufar daining tana cewa.
” Yunwa nakeji naga alama kai bakaji.”
Murmushi ya saki cikin sauri ya biyota daining ɗin, kafin ta zauna yayi saurin zama yana jawota kan cinyarsa murmushi falmata ta saki, tare da cewa.
” Oh Doctor, yunwa fa nake ji.”
Murmushi ya saki tare da ce mata.
” No my dear bazaki iya cin abincin ƙasar nan ba, fa, sai dai kisha tea da bread 🍞 amma banda abincin su kam, koni da na shekara bakwai har yanzu ban iya ciba bare kuma ke, ki dai sha tea kafin na fita na mana siyayyan kayan abinci ko.”
Ya ƙarasa maganar yana shinshina wuyan ta.
” Ai kuwa sai naci, dan kai ka kasa, sai kace nima bazan iya ba, bari kaga.”
Ta ƙarasa maganar tana miƙewa daga jikinsa, murmushin mugunta Doctor ya saki tare da zuba mata ido tana jawo kular harda ɗauko plet, farar shinkafa sai, ta saka cikin plet ɗin sai ta jawo ƙaramar kular ta buɗe, wata irin miyace mai wuyar kwatance, ita dai gata koriya ba kuma koriya, ba, kallon miyar tayi ta kalli Doctor daya zuba mata idanu, hararar sa tayi tare da ɗiban miyar ta zuba saman shinkafar shi dai doctor murmushi kawai ya saki, zama tayi tare da bismilillah ta kai loma ɗaya bakin ta, ai kuwa bata iya haɗiyesa ba ta furzar dashi, da sauri, take bakinta ya gauraye mata da wani irin ƙamshi marar daɗi dariya doctor ta saki da sauri ya jawo cup tare da miƙa mata ruwa karɓa tayi ta sha cikin hanzari kafin ta ajiye cup ɗin tana ajiyar zuciya, Dariya Doctor ya sheke dashi tana turo mata plet din abincin yace.
” Bismillah my dear cigaba daci bana son ki kwana da yunwa.”
Cikin sanyin murya tace.
” Wallahi bazan ciba, gara nasha tea.”
Ta ƙarasa maganar tana jawo plast ruwan tea ta haɗa mai kauri tasha, harta gama Doctor dariya yake mata.
” Haba dai Doctor yanzu bazaka daina min dariyar nan ba.”?
Ta ƙarisa maganar cikin marairaicewar murya.
” Na daina ya furta, yana duban a gogon hanunsa da ya nuna 6:15pm alamun magaruba ta kawo kai, tea ɗin shima ta basa yasha, yana ƙoƙarin tashi ya tafi massalaci yaji ringin ɗin wayarsa, UMMA ya gani a rubuce murmushi yayi tare da ɗaga wayar.
” Salamu alaikum Ummana.”
Ajiyar zuciya Umma ta sauƙe tace.
” Wa’alaiku mussalam, Hassan kun sauƙa lafiya ?.”
” Umma lafiya muka sauƙa ya jikin bulama.’?
” Da sauƙi” umma tace
Tare da cewa ” ina Falmata.”
Dubanta yayi da take kurɓar tea yace.
” Gata nan tana shan tea na bata wayar ne.?”
” Aa ka gaisheta kawai, ku huta gajiya.” ta ƙarisa maganar tana katse kiran, kallon falmata yayi yace.
” Umma tana gaishe ki, zan tafi sallah, sannan bazan dawo ba sai ƙarfe 9:30pm sabida xanje wajen mai gida na *DOCTOR SALIM KHAN* zamu tattauna dashi game da aikin daya kawo ni.”
” Shikenan a dawo lafiya, amma Doctor na, ina tsoron zama ni kaɗai.”
” Tsoro kuma my dear, me zai sameki bayan ga mai gadi da ma’aikatan gidan, babu abinda zai sameki, ki kunna tv kafin na dawo.”
Kaɗa masa kai tayi alamun to, sannan ya fice, tashi itama tayi ta haura bedroom dinta alwala tayi, tare da tayar da sallah, ta juma tana adduoi kafin ta baɗe sallayar ta kwanta shuru tana tunanin maji wayarta ta ɗago da niyar kiran majin sai taji babu kuɗi cikin wayar, ajiyewa tayi, tare da jan tsuka cikin jin haushi.
Doctor kusan 9:45pm ya dawo cikin gidan, shuru yaji falon ba kowa, sama ya haura hanunsa riƙe da goran fresh milk , bai shiga bedroom din falmata ba, ya shige nasa, zama yayi bakin bed ɗinsa tare da zaro ƙwayar planing ƙanana mai yellow da kuma jajaye, guda biyu ya ɓallo tare da buɗe murfin fresh milk ya watsa su ciki, rufe gorar yayi tare da ajiyewa ya tashi ya nemi waje ya adana su inda babu mai ganinsu, 15 minute ya dawo ya ɗauki gorar tare da jijjigata sanda ya tabbatar maganin ya narke sannan ya saka goran a frich , tollet ya shige yayi wanka cikin wata blue ɗin rigar bacci ya saka bayan ya gama feshe jikinsa da turare, bedroom ɗin falmata ya nufa cike da murmushi tana kwance rufda ciki bacci harya kwasheta, tana sake da wata ƙaramar rigar bacci iya gwiwwa duk ta tattare ta dawo cinyar ta rigar mai sharashara, ce pink color duk jikinta kana hango sa, ajiyar zuciya ya sauƙe tare da zama bakin bed din yana ƙare mata kallo, sosai ta masa kyau cikin kayan baccin ƙirjinta ya zubawa ido da suke tsaye ƙyam cike da sha’awar su, ɗan kwantowa yayi ya fuskanci fuskarta, murmushi ya saki tare da manna bata kiss a goshin ta, hanunsa yasa ya ɗan daki fuskarta kadan, yana hura mata iska a kunnen ta, a hankali ta buɗe idanunta ta zubasu a fuskarsa murmushi ya sakar mata yace.
” My dear bacci Kuma, baki jirani na dawo ba, tashi mu tafi Bedroom ɗina, baccin zaifi miki daɗi a can.”
Lumshe idanunta tayi dake cike da bacci jikinta duk a mace yake, ƙara rufe idanunta tayi zata maida bacci, murmushi DOCTOR yayi ya miƙe tsaye tare da saka hanunsa ya ɗago ta caɗak kamar ƴar baby buɗe idanunta tayi tace.
” DOCTOR BACCI, ka barni nayi na gaji.”
A kunnenta ya raɗa mata.
” Yau bakici ta bacci ba, domin kuwa yau ranar da zaki farantawa mijinki rai ne.”
Cike da rashin fahimtar inda zancen nasa ya nufa, ta ƙara narkewa a jikinsa, Bedroom ɗinsa ya shige da ita a bed ɗinsa ya ajiye ta, tare da dago ta, ta ZAUNA, murmushi ya saki yana kallon yanda ta taɓe fuska ita a dole ya hanata bacci.
DOCTOR bai bar Falmata ba, sai da ya sata sukayi nafila raka’a biyu ya ɗaga ta suka zauna bakin bed sannan yaje ya buɗe frich ya ɗauko fresh milk ɗin da cup ya tsiyaya mata zama yayi ya jawota ƙirjinsa.
” My Dear, naga baccin nan bazai barki ba, hingo maza shanye.”
Ita kuwa Falmata sarkin son fresh milk, da sauri ta karɓa tana ware idanunta murmushi DOCTOR ya saki dama kuwa yasan tana sonsa sosai, shiyasa yayi amfani da shi, karɓa tayi ta shanye tas ta ajiye masa cup ɗin, sannan ta faɗa jikin sa cike da kasala, shima DOCTOR zamewa yayi suka kwanta a bed ɗin, tana lumshe masa idanunta, murmushi ya saki tare zaro harshen sa, ya lashi lips ɗin ta lumshe idanunta tayi cike da jin daɗi domin kuwa tayi missing ɗin rommance ɗinta da yake yi tsawon shekaru bakwai, bakin ta buɗe masa, shi kuwa cikin hanzari ya capki leɓenta, tare da birkito ta jikinsa, wani irin hot kiss yake mata tare da zuƙar harshen ta, Falmata rufe idanunta tayi cike da jin kanta bisa gajimare, a hankali ya zame bakinsa daga nata a hankali, hanunsa ya saka ya ɓalle boturan rigar ta, manyan nonon ta dake tsaye ƙyam ya saka bakinsa yana lasar kan nonon da harshen sa, a hankali hanunsa ɗaya kuma yana matsa mata ɗaya nonon, wani irin miƙar daɗi Falmata tayi, har tana wani gurnani, sosai DOCTOR yake romance ɗin Falmata, birkice masa tayi cikin jin daɗi ta rasa wata duniyar take, Falmata bata fara dawowa cikin hankalinta ba, sai da ta fara jin raɗaɗi a ƙasanta, sannan ta fara ƙoƙarin turesa daga jikinta amma ina ta kasa, domin kuwa DOCTOR yayi nisa baya jin kira, azaba iya azaba Falmata tasha a hanun DOCTOR, SOSAI tayi kuka har sai da muryar ta, ta dashe, DOCTOR Sanda ya sami nutsuwa sannan ya gangara gefe yana lumshe idanunsa cike da nutsuwa wani irin ƙaunar Falmata ne ya ƙara shiga ransa, Tabbas ta basa jin daɗi da farin cikin da bai taɓa cin karo dashi ba, a duniya, Tabbas Falmata macece mai cikakkiyar ni’ima juyowa yayi yana kallon ta da har yanzu tana shashsheƙar kuka, mirginawa yayi yasa hanu zai jawo ta jikinsa ya rarrasheta, da sauri ta bige hanunsa cike da tsoron sa, domin kuwa yanzu ta fara jin tsoron sa, numfashi DOCTOR ya saki cikin sanyin murya yace.
” Mtsss My dear, I am sorry kina jin zafi na, ko meyasa zakiji zafi na, bayan kinsan komai game da Aure, kinfa je islamiyya kuma kinsan hukuncin macen da take gudun mijinta a shinfiɗa ko, SORRY ki daina kuka kinji farin ciki na.”
Ya ƙarasa Maganar tare da jawo ta, jikinsa ya ƙanƙameta yana jin ƙaunarta, kamar ya haɗiye ta, dakyar ya samu tayi shuru tana ajiye zuciya, a hankali ya zameta daga jikinsa sannan ya tashi tollet ya shige yayi wankan tsarki sannan ya ɗauro alwala saboda baya kwanciya shi sai da alwala, ruwan zafi mai ɗumin gaske ya haɗa a bowel na wanka Tare da saka Dettol cikin ruwan, sannan ya fito, yazo ya dawo bed ɗin, ɗagata yayi cak ya nufi tollet ɗin da ita, a cikin bowel ɗin ya ajiye ta, ɗan ƙara ta saki zata tashi, ya mayar da ita ciki tare da Girgiza mata kai yana riƙe da ita cije bakinta tayi cike da azaba, tun tana jin zafin ruwan har ta dawo ta tana jin ruwan yana mata daɗi lumshe idanunta tayi a ciki, ganin tayi lamo cikin ruwan ya tabbatar masa da cewa taji daɗin ruwan sakinta yayi tare da cewa tayi wanka, ya fito ya barta cikin tollet ɗin, koda ya fito yaye zanin gadon yayi domin kuwa ya ɗan ɓaci da jini kaɗan, wani ya shimfiɗa sannan ya fita da ɗayan.
Falmata ta juma cikin bowel ɗin ƙasan zuciyarta tana jawa DOCTOR Allah ya isa, sannan ta tashi da ƙyar tayi wankan janaba, towel taja ta ɗaura a jikinta sai dai yanzu taji raɗaɗin da ɗan sauƙi, amma dai da ƙyar take taka ƙafarta kam, a haka ta fito tana cije baki, bakin bed ɗinsa ta ZAUNA, tana haɗa fuska, murmushi DOCTOR dake kwance ya saki, tare da tashi ya ɗauko magani da ruwan tea mai kauri ya miƙa mata, azababbiyar yunwar da take ji yasata karɓa tasha tare da maganin, kwanciyar ta, tayi da towel ɗin a jikinta ta duƙunƙune tana jin sanyi, take zazzaɓi mai zafi ya hauta, ganin rawar sanyin da takeyi yasa DOCTOR saurin jawota ya mannata da ƙirjinsa, bargo yaja ya rufesu dashi, daren ranar daƙyar bacci ya kwashe Falmata, cike da nutsuwa shima DOCTOR yake baccin……………….
Yaufa sai kunyi hkr dani banyi editing ba saboda bani da caji🤗
*SHIN KINA SON KIGA NI’IMAR KI TA ZARCE WANDA KIKE DASHI TO YI WANNAN HAƊIN KI GWADA*👇🏻
*NI’IMA*
_Zaki iya samun ruwan kwakwa da madara peak da zuma sai garin ridi ki hadasu guri daya ki gaurayashi sosai sai ki ajiyeshi kinasha wannan ga ni’ima ga karawa mace yawan sha awar namiji_
ƳAR UWATA KASANCE MAI YAWAN SALLAR DARE.👇🏻
*SALLAN DARE (QIYAMULLAILI)*
🔷 *ME AKE KARANTAWA ACIKIN SHAFA’I DA WUTIRI??*
Kamar yadda ya gabata abaya cikin hadisin Ubayyu bin Ka’ab Allah ya ƙara masa yarda cewa manzon Allah ya kasance yana karanata Surah Al’ala araka’ar farko, ya karanta surah Alkafirun araka’a ta biyu, araka’a ta uku kuma ya karanta surah Ikhlas”.
سنن النسائي ١/٣٧٢
Waɗannan surori su akeso mutum ya karanta acikin sallan shafa’i da witiri, Sannan mutum zai iya ƙarawa da surah Falaq da Surah An-Nas araka’a ta uku kamar yadda yazo ahadisin Abdullahi bin Juraij yace Na tambayi Nana Aisha gameda witirin manzon Allah, sai tace “Yana karanta Surah Al’ala da Surah Alkafirun araka’a ta uku kuma sai ya karanta surah Ikhlas da falaq da kuma Surah An-Nas”
سنن الترمذي ٤٦٢
🔷 *HUKUNCIN YIN AL-QUNITI ACIKIN WUTIRI*
Azance mafi inganci cikin zantukan malamai shine yin Addu’ar qunuti acikin witiri mustahabbine ba wajibi ba, dalili kuwa shine an samu wani lokaci manzon Allah ya kanyi wutiri batare da kuma yayi qunuti ba, wanda hakan ke nuna cewa ba wajibi bace, domin da yin qunuti wajibine da manzon Allah ya lizimceshi.
Hakanan an samu wasu sahabbai da tabi’ai basa yin qunuti, wasu kuma ba kullum sukeyi ba, wasu kuma sai acikin watan ramadhan sukeyi wasu kuma an samu suna lizimtar yinsa kullum, duka wadannan sabanin aiki na sahabbai da tabi’ai din yana nuna cewa yin qunuti mustahabbine domin da wajibine da basu barsa ba.
مجموع الفتاوى ٢٢/٢٧١
🔹 *SHIN KULLUM AKEYIN QUNUTI??*
Malamai sunyi saɓani akan shin kullum ne akeyin qunuti ko ba kullum ba,
Wasu daga cikin malamai sun tafi akan cewa kullum ne akeyin qunuti cikin kwanakin shekara, sannan za’ayi ne kafin ayi ruku’u, cikin malaman da suke da wannan ra’ayi akwai Sufyanus Sauri da Ibnu Mubarak dama Ahlul Kufa, juma shine ra’ayin Sahabi Ibnu Mas’ud Allah ya ƙara musu yarda.
Wasu malaman kuma suna ganin ba kullum akeyin qunuti ba, anayine kawai acikin watan ramadhan nanma idan tayi tsakiya, sannan kuma anayine bayan ɗagowa daga ruku’u, wannan shine ra’ayin shafi’iya kuma shi aka ruwaito daga Sahabi Aliyu bin Abi Dalib Allah ya ƙara masa yarda.
Adarasi na gaba zamu tashi akan gurbin da akeyin Alqunuti da siffar yadda ya akeyinsa in sha Allah.
KI biya kuɗin ki ki karanta halak ɗinki yar uwa, karki na sata, ni bazan ja miki Allah ya isa ba, amma dai kinsan hukuncin wanda yaci haƙƙin wani ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[10/5, 10:22 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 79 to 80*
________✍🏻 Da asubar fari DOCTOR ya farka, duban Falmata da ta maƙale a jikinsa tana bacci ta tsuke ɗan ƙaramin bakinta, murmushi ya saki tare zameta daga jikinsa a hankali, filo ya samata, sannan ya tashi tollet ya shiga ya ɗauro alwala masallaci ya tafi, ba tare da ya tashi Falmata ba, ganin har yanzu aɗan kwai zazzaɓi a jikinta, bai dawo ba sai da gari ya ɗan fara haske, Bedroom ɗinsa ya koma har yanzu Falmata bacci take, hawa bed ɗin yayi tare da janye filon daya kareta dashi, ya ƙanƙame matar sa, shima baccin ya koma cike da nutsuwa.
Misalin ƙarfe 11:00am agogon India Falmata ta buɗe idanunta a hankali, a fuskar DOCTOR da yake bacci ta sauƙe su, sai abinda ya faru daren jiya ya faɗo mata, hararar sa tayi tare da maida kallon ta, ga hannun sa dake riƙe da kunkumin ta, hanunta tasa ta cire hanunsa daga jikinta, a hankali ta sauƙo da ƙafafuwan ta, ƙasa daga ita sai towel ɗaure a ƙirjinta, ta miƙe tsaye, a hankali take takawa cike da tsoro domin kuwa har yanzu tana ɗan jin zogi a ƙasanta, harta fice daga Bedroom ɗinsa ta shiga nata, tollet ɗin ta ta shige tare da ƙara gasa jikinta da ruwan zafi, ta ɗauro alwala ta fito Sallah tayi sannan ta sake komawa ta kwanta taso gyara gidan ta, sai dai yanda take jin jikinta yana mata ciwo bazata iya ba, gashi har yanzu tana jin zazzaɓin, bata juma da kwanciyar ba kuwa bacci ya sace ta.
DOCTOR daya tashi wayam yaga wajen babu Falmata hakanne ya tabbatar masa da cewa ta fita, wanka yayi ya shirya cikin three cuttern wando da kuma best, yau bazai fita ko ina ba, yafi so ya zauna da matar sa ya kula da ita, Bedroom ɗinta ya shiga tana bacci har yanzu, fitowa yayi falo yana ƙare wa falon kallo, JENIFER wacce take aiki cikin gidan ta gyara falon tas sai ƙamshi sir freshener mai daɗin shaƙa yake, Kitchen ya nufa still Jenifer ya gani tana ƙoƙarin kunna gas da alamu breakfast take da niyar musu.
” HI Sister.”
DOCTOR ya faɗi yana shigowa cikin Kitchen ɗin, juyowa Jenifer tayi cikin girmamawa tace.
” Good morning Sir.”
” Morning” ya furta tare da cewa ” SORRY ki bar dafa abincin, daga yau na ɗauke miki Madam tafi son tayi girki da kanta ki dinga dafa muku naku kawai a Kitchen ɗin tsakar gida.”
Girgiza kanta Jenifer tayi alamun gamsuwa sannan ta fice, ƙarasowa DOCTOR yayi ya ɗaga plast ɗin yaji cike yake dam Da ruwan zafi, shuru yayi yana tunanin yanda zaiyi gashi shi bai iya girki ba, bare ya dafa musu, ko yabar Jenifer kuma ta dafa ba iya cin abincin ƙasar za tayi ba, rashin makamar yi ya sashi kashe gas ɗin tare da ɗaukar plast ɗin ya kai daining da cup, bread da madara duka suna daining ɗin, komawa cikin falon yayi ya zauna ɗaya daga cikin kujerun ya kunna tv BBC News ya kunna, Falmata kuwa da dogon wando ta fito wanda yasha jikinta sai wata ƙaramar top, kanta sanye da hula, yanzu kwata kwata bata jin zogin sai idan tazo fitsari, falon ta sauƙo tunda ta hangosa ta tura baki, Kitchen zata shige cikin sauri domin sama musu abinda zasuci, muryar sane ya dakatar da ita daga shiga Kitchen ɗin.
” Karki shiga Kitchen yanzu ki bare sai da Rana.”
Taɓe baki tayi tare da dawowa ta zauna a kujera, ya daƙile tace.
” Good morning Doctor” wai ita a dole fushi take dashi, dariya ce taso ƙwacewa DOCTOR yayi saurin dannewa kujerar da take ya dawo ba tare daya amsa mata gaisuwar ta, ya hau zolayarta.
” Umma Mama Hajja!!! Kuzo zai kashe ni, wayyo Baba zai kashe ni, DOCTOR zafi ƙasa na wayyo Mama, ai dai Su Mama kam sunyi nisa basa jiyoki”
Ya ƙarasa maganar cikin dariya yana jan kumatun ta, ya cigaba da cewa ” Oh da kuma har sakin jikin daɗi ake min, yanzu kuma naga sai wani haɗe miin fuska ake, ai dai gani nayi sweet ɗin da mutum yake so na basa, kamata yayi a min godiya ba wai a haɗe min fuska ba, yanzu ma dai akwai zagaye na biyu wancan na farko ne Malama idan ma zaki ware ki ware.”
Falmata cika tayi fam cikin haushin Maganar tasa ta miƙe a fusace zata bar wajen, DOCTOR yana dariya ya fisgo hanunta ta faɗa jikinsa riƙeta yayi gam yana cewa.
” Haba sarauniya ta, nifa wasa nake miki, sorry ki daina haɗe min ranki, sam bana jin daɗi idan na ganki cikin damuwa, bai kamata ranki ya ɓaci ba akan wannan abun kinsan dai ko wacce mace sai ta fuskanci wannan Ranar muddun kuwa ta kawo budurcinta gidan mijinta, wannan zafin da kikaji na yaune kaɗai gobe ko anyi bazai miki zafi ba, dan Allah ki daina fushi dani, idan ba so kike na shiga cikin wani hali ba.”
Kwantar da kanta ƙirjinsa tayi, ba tare da tace komai ba.
“Kinyi shuru ko baki daina fushi dani ba ne.”
” Na daina ” ta furta tana sunkuyar da kanta ƙasa alamun kunya, murmushi yayi yace.
” To ki daina jin kunyata kinsan dai babu kunya tsakanin mu, tunda babu daren da jemage bai gani ba”
Dariya Falmata tayi tare da ɗan dukan ƙirjinsa, murmushi ya saki yace.
” To tashi mu je muyi breakfast da ruwan tea, dan kinsan ba iya girki nayi ba, tea kawai na dafa muje musha da hkr.”
” Ai da kabari ko ƙwai na soya mana, tea ai bazai riƙe mutum ba.”
Murmushi kawai doctor yayi yace.
” A’a bazaki shiga kitchen ba, yanzu ki bari kawai musha tea ɗin Allah ya sa masa albarka.”
Da ameen Falmata ta amsa tare da tashi suka wuce daining table, Falmata itace ta haɗa tea ɗin ta miƙa masa, haka suka sha tea ɗin da bread, bayan sun gama suka dawo falon, Falmata tana maƙale jikin Doctor, a wunin Ranar Falmata sai da suka dawo daidai da Doctor duk wani fushin ta manta dashi cikin farin ciki da walwala suka wuni.
Satin Doctor ɗaya a India ya fara zuwa asibitin, Shida na safe yake fita, bazai dawo ba shida na yamma, Falmata sosai take kewar wuni ita kaɗai sai dai Jenifer tana ɗan shigo Mata suna hira, kayan abinci kuwa ya jibge musu a store da kanta Falmata take girkinta na ƙasar mu Nigeria , Rayuwarsu suke da mijinta cike da jin daɗi sai dai abinda Falmata bata sani Doctor kullum sai ya sa mata fill na planing, a cikin Fresh milk bata taɓa sani ba.
Yau asabar baida aiki yana gida, yana zaune a falo wayarsa tayi ringine Saif ya gani ɗaga wayar yayi yana murmushi yace.
” Shegen gari ya akayi ne kwana biyu shuru, ɗazu kuma na kira baka ɗaga ba.”
Daga can Saif yace.
” Kai dai bari kasan na fara aiki a Custing, so time ɗin sai a hankali, ɗazu ina dreving ka kira, ya Madam Falmata.”
” Falmata tana lafiya, oh kace ka zamo babban ma’aikaci, aikin sai a hankali, am sorry wani ɗan nauyi nake so na ɗaura maka, maganar ginin asibiti na, da za’a fara, dan Allah ina so ka kula da aikin sannan za’a fara min ginin gidana A New GRA Fili Umma wanda ta mallaka min shima munyi magana da Wani mai zane so na mishi bayanin tsarin ginin da nake so, har ma ya turo min, so na bashi numbern ka, zai kira ka sai ku jagoranci ginin, zan turo maka kuɗaɗen ta account ɗinka Allah yasa ban ɗaura maka wahala ba.”
Falmata ta fito daga kitchen, ta faɗa jikin sa tana ɗaga masa girarta, murmushi ya mata Saif ne yace.
” Babban mutum kenan, ni kuwa wani wahala zaka bani, babu abinda bazan iya maka ba a rayuwata, ba damuwa zan saurari kiran sa, sai ka turo kuɗin.”
” To shikenan abokina na gode, ka gaishe da Aunty.”
Da zataji yace tare da katse wayar duban Falmata dake kwance a jikinsa yayi yana shafa kanta yace.
” My dear ya dai, kin gaji ko?”
Girgiza masa kai Falmata tayi cike da shagwaɓa tace.
” Ni so nake mu fita ganin gari, tunda mukazo ina zaune cikin gida, ni dai ka shirya mu tafi cikin gari zuwa anjuma idan na gama girki.”
Murmushi Doctor yayi, yana dariya yace.
” Oh yanzu akan wannan kawai kike ɓata ranki, to kwantar da hankalin ki, gama girkin mu tafi shikenan My dear.”
Cike da dariya Falmata ta tashi da sauri ta shige cikin kitchen ɗin, tana sauri ta gama girkin ta shirya………………..
Yauma dai kamar jiya ban samu nayi editing ba🤗 Sorry for typing error.
KI biya kuɗin ki ki karanta halak ɗinki yar uwa, karki na sata, ni bazan ja miki Allah ya isa ba, amma dai kinsan hukuncin wanda yaci haƙƙin wani ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*ƘARAWA KANKI NI’IMA ƳAR UWATA DOMIN GAMSAR DA MAI GIDA*👇🏻
*Ki samu sassaken baure ki zuba masa ruwa ki dora akan wuta idan ya tafasa zakiga ruwan ya canja kala saiki sauke sannan ki tace ruwan dama kin daka kanun fari saiki zuba garin sannan ki zuba zuma kadan saiki saka bazar kwaila sannan ki mayar dashi kan wuta idan ya tafasa zakiji yana kamshi saiki saukeshi sannan ki ajiyeshi kina shansa sau2 a rana*
🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗
*Ki yanka rake kanana kanana kamar alawar yara sai ki saka a tukunya da ruwa ki jefa kanumfari bada yawa ba fa da yar cittar ki itama ba mai yawa ba sannan ki bare dabinon ki cire kwallon ki jefar kwallon saiki dakashi ya zama gari saiki zuba aciki sai ki dora kan wuta ya dahu sosai sai ki sauke ki matse rake ki cire sannan ki tace ruwan sai kuma ki maida kan wuta ki saka mazalkwaila a ciki sai ta narke sai ki sauke kisa a fridge yayi sanyi kisha*
*MU KULA DA KITCHEN ƳAN UWA NA*
*🥛KUNUN WAKEN SUYA DA ALKAMA🥛*
INGREDIENTS
Alkama
Waken suya
shinkafar tuwo
Gyaɗa
Sugar
Madara
*YANDA ZAKI HAƊA*
Dafarko zaki haɗa waken suya da alkama amma ita gyaɗar sai an soyata sama sama asa idan aka niɗa sai a tankaɗe idan zakiyi sha saiki ɗora ruwa a tukunya idan ya tafasa saiki dama wannan garin kamar niƙa saiki zuba kina juyawa kar yayi gudaji yana dahuwa saiki sauke idan ya huce ki zuba a Kofi ki saka madara da sugar kisha wasu kuma basa saka madara wasu kuma suna saka hulba idan sunasan ƙarin nono kenan kuma yana sa ƙiba zaki iya bawa yaroma yana saka ƙiba.
*KIYAYE HARSHE FALALA CE MAI GIRMA ƳAR UWATA* 👇🏻
Ibnul Qayyim Allah ya masa rahama yake cewa “Abun mamaki zakaga mutum yana masa sauki ya kiyaye kansa daga cin haramun, zalunci, zina, shan giya, kallace kallacen haramun dama wasun wadannan laifukan amma kuma yana mai wahala agareshi ya iya kiyaye *harshensa*, ta yarda har zakaga mutum ana nunashi ana cewa yanada addini, zuhudu da kuma yawan ibada amma sai ka sameshi yana furta wasu kalmoni da zasu janyo masa fushin Allah batare da ya saniba, kalma daya daga cikin irin maganan da yake ta isa ta jefashi wuta gwargwadon Nisan dake tsakanin gabar da yamma”.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[10/7, 9:43 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 81 to 82*
_________✍🏻Cikin 40 minute ta gama girkin ta, farar shinkafa da dankali sai miya kawai ta dafa musu, sai juice ɗin abarba da ta haɗa a daining ta jera abincin, lokacin da ta gama DOCTOR baya cikin falon ya shiga cikin Bedroom ɗinsa, itama Bedroom ɗinta ta shige tayi wanka, bata juma ba, ta fito cikin shirin ta, baƙar doguwar riga ta fito, babu ɗankwali a kanta, tayi Bedroom ɗinsa, yana ƙoƙarin ɗaura takalmin ƙafarsa ta shigo murmushi ta saki tana ƙarewa mijin nata kallo cike da Soyayya, sosai ya mata kyau cikin manyan kayan, shadda yasa riga da wando mai ruwan Ash color, tasha aiki, sunkuyawa tayi ta karɓi igiyar ta hau ɗaure masa takalmin, bayan ta gama ne ta, ɗauko turare a dressing mirrorn sa, ta feshe masa jikinsa da turaren, cike da ƙauna yake kallon ta, harta gama hularsa ta saka masa a kansa tare da gyara masa zaman hular, rungumesa tayi tana dariya tace.
” Kayi kyau sosai DOCTOR na, anya kuwa bazamu fasa fitar nan ba, kar muje wata ba’indiya ta ƙwace min kai, na shiga Uku.”
Dariya DOCTOR yayi tare da kamo hanunta suka fito yana cewa.
” Kina tunanin har akwai wacce isarta ya kai ta ƙwace miki Ni, babu wannan macen a duniya yanzu duk wata mace bayan ke kallon NAMIJI nake mata, DOCTOR naki ne ke kaɗai, sam yafi ƙarfin haɗaki da wata, ke kaɗai ce hasken da nake gani domin duba hanyata, kece murmushin DOCTOR, UWA Uba kuma numfashin sa, taya kike tunanin zanyi wasa da Rayuwata, ke kaɗai ce daga ke babu ƙari my dear Hankalinki ya kwanta”
Murmushi Falmata kawai ta saki tare da Girgiza kanta tace masa.
” Hmmm!!! Karka sa naji kaina ya fara girma nasa a raina dani kaɗai zakayi rayuwa har ma kasa na fara jin nafi ko wacce mace Sa’an samun miji a duniya, bayan nasan ku maza baku da tabbas akan mace, zaku nunawa mace so kamar ku haɗiye ta, amma da zarar kun hango wata wacce ta fita kyau zaku fara juyawa ta gida baya, dalilin kenan da yasa ban taɓa sawa a raina cewa zan zauna ni kaɗai a gidan mijina ba, na dai san ina kishin ka, amma bani da ikon hanaka kawo wata, ko wannan maganar da nayi yanzu kawai wasa ne.”
Murmushi kawai DOCTOR yayi tare da sakar mata hanu yana zama a daining ɗin ya bata amsa da cewa.
” Ba ko wani NAMIJI bane ya kasance a yanda kika lissafo yanzu, domin kuwa kowa da nashi tsarin ko ki yarda dani ko karki yadda dani ni dai nasan dake kaɗai zan iya rayuwa bazan taɓa yiwa Soyayyar ki kishiya ba, koda ace kin rigani mutuwa bazan taɓa miki kishiya bayanki ba, zan zauna haka ba
mata har nima tawa mutuwar ta riskeni.”
Murmushi Falmata ta sauƙe tare da ajiye mishi plat ɗin abincin a gaban sa, nata taja gabanta ita ma, tare da duban DOCTOR cike da murmushi da kuma son kawar da maganar tace.
” Ban ƙaryata maganarka ba, sai dai na jinjinata, kuma Tabbas bazan saka a raina cewa nice kaɗai zakayi rayuwa da kai ba, domin kuwa shi Aure ƙaddara ce, yana zuwa makane koda baka shirya masa ba, hmmm!!! idan har Allah ya kira maka auren mata sama da ɗaya to kuwa dole sai kayi shi, Kaci abinci kawai DOCTOR na, mu samu mu fita da wuri.”
Ta ƙarasa Maganar tana kai lomar abinci bakinta, murmushi DOCTOR yayi shima tare da cewa.
” Zaki tabbatar idan kika gani, domin kuwa bana faɗar abinda bazan iya ba.”
Yayi Maganar shima yana cin abincin, dariya kawai Falmata tayi ba tare da tace masa komai ba, abincin suka ci-gaba da ci bayan sun gama ne, DOCTOR ya dubi Falmata tare da cewa.
” Masha Allah abinci yayi daɗi my dear, tunda kinga na cinye duka wanda kika samin duk da yawan san nan.”
Murmushi Falmata ta saki tace.
” Kai dai kawai dama kai ciccika rumbu ne Malam karka wani fake da daɗin abinci ka ɓoye yawan cinka malam acici!!!.”
Cike da Zolaya ta ƙarasa maganar, Falmata sosai take jin daɗin Rayuwa da DOCTOR, mutum ne shi mai sauƙin kai da daɗin zama tare da kyautatawa wanda yake tare dashi, mutum bazai fuskanci haka ba, har sai ya zauna dashi, Tabbas Mutum ne mai Zafin rai da kuma faɗa amma sai idan harka tsokane sa, wani sa’in yana da sauƙin kai amma idan zuciyarsa ta tashi harya zarce kuturu masifa, amma dai yana da daɗin zama sosai wannan zafin ran shine kaɗai matsalarsa, DOCTOR murmushi kawai yayi tare da cewa.
” Wannan Maganar taki ba yanzu zan rama ba, amma dai kinci bashi kuma dole sai kin biya domin kuwa hausawa sunce cin tuwon kishiya ramako ne, ki samu ki tashi kije ki dauko mayafinki mu fice, naga kin tsaya sai zuba kike kamar kurna.”
Tashi Falmata tayi tana dariya ta haura sama tana cewa.
“Ai banga kishiyar ba bare kuma ta rama, sai dai kai ka rama, Muna zuba kuma zakace ba ina zuba ba, gyara zancen malam.”
Ta ƙarisa Maganar tana shigewa Bedroom ɗinta, murmushi ya saki tare lumshe idanunsa, Falmata bata wani juma da shiga ba ta fito fuskarta yane da mayafin abayar sosai tayi masa kyau, hanunta riƙe da ƙaramar jaka, tashi yayi tare da riƙo kunkumin ta suka fito matarsa Suka shiga yaja suka tafi.
Wunin ranar sosai DOCTOR yayi yawo da Falmata ta zaga gari, har Hospital ɗin da yake aiki sai da ya kai Falmata, sosai asibitin ya yi mata kyau domin kuwa tunda take a rayuwarta bata taɓa ganin asibiti mai kyawun wannan ba, babbane sosai gashi a tsare, bayan sun fito daga Hospital ɗin, makay suka shige su kayi sayayya sannan suka dawo gida.
Falmata a matuƙar gajiye ta zube a ɗaya daga cikin kujerun falon, DOCTOR shine ya shigo da kayan a gefe ya ajiye tare da zama kusa da ita yana sauƙin ajiyar zuciya, ƴar ƙaramar ledar dake hanunsa ya miƙa mata, Falmata hanu tasa ta karɓa tana duban sa tace.
” Menene Wannan DOCTOR na.?”
Ta masa tambayar tana kallon ledar cike da nutsuwa yace mata.
” Bakya buƙatar tambayata tunda abin yana hanunki kina iya buɗewa kiga ko menene ƴar ƙaramar kyauta ce na miki.”
” Kyauta kuma?” Falmata ta furta cikin zuciyarta, gyara zaman ta tayi tare da buɗe ledar, waya ce infinix hot 9 mai bala’in kyau ruwan jibi, dariya Falmata ta saka cike da jin daɗi tace.
” DOCTOR na, Wannan wayar kana nufin tawa CE, wayyo daɗi, thank so much DOCTOR na, Allah ya ƙara arziki mai albarka, ina ka samu kuɗi haka DOCTOR.?”
Murmushi yayi cike da jin daɗi domin kuwa shi mutum ne, mai son a yaba masa da kuma gode masa idan har yayi kyauta, amsa ya mayar mata da cewa.
” Ameen my dear, Wannan gidan da muke ciki, Doctor Salman Khan ya mallaka min shi kyauta tare da wannan motar da nake hawa still kafin na koma Nigeria ya bani 6 million, ganin da nayi ni ba zama zanyi mai ɗaurewa a nan ba, yasa na sayarwa Sanskar da gidan Naira miliyan goma harma ya turo min kuɗin ta account ɗina jiya, sai dai ya barni na zauna na tsawon lokacin da zan gama wannan aikin na shekara ɗaya mu koma gida, a cikin su na saya miki wayar, sauran kuɗin kuma na turawa Saif za’a min ginin gida na da Kuma asibiti.”
Ajiyar zuciya Falmata ta sauƙe tana ƙara juya wayar a hannun ta, tace.
” Masha Allah, Allah ya yi albarka, ban taɓa tunanin zan riƙe wannan wayar ba, Amma DOCTOR kuɗi ne haka dashi da zaiyi irin wannan kyauta mai yawan gaske wanda ko a cikin ƴan uwan ka ba kowa bane zai iya maka shi .”
Murmushi mai sauti DOCTOR yayi tare da cewa.
” Kinsan wanda zaiyi irin wannan kyautar, ba ƙaramin mai kuɗi bane, sannan hayata ya ɗauka na tsawon shekara ɗaya, babban likita ne acikin ƙasar India babu jihar da ba’a sanshi, yana da rashe reshe na asibitin sa a cikin dukkanin jihar dake cikin ƙasar sannan kuma yana Business sosai, shiyasa duk makarantar da yaje taron yaye likitoci, muddun idanunsa suka kyalla kan mai ƙoƙarin makarantar baya taɓa yadda, ya barsa, sai yayi duk yanda zaiyi dan ganin ya jawo sa jikinsa domin yayi aiki a karkashin sa, da na yadda da yanzu anan zan zauna domin nayi aiki, kuma zan samu kuɗi fiye da tunanin ki, sai dai sam babu hakan a raina nafi buƙatar na bautawa ƙasata fiye da kuɗin da zan samu.”
Jinjina kanta Falmata tayi cike da gamsuwa, ƙara masa godiya tayi sannan ta tashi taje ta saka wayar a caji, da la’asar lis Falmata ta cire wayar a caji tare da sáka sim card ɗinta, Maji ta fara kira cike da zumuɗi, ringin ɗaya Maji ta ɗaga tare da cewa.
” Ƙawata kin ɓata a India ɓat bama jin labarin ki.”
Dariya Falmata tayi tace.
” Kai ƙawata Ni na isa ɓacewa na manta dake, kinsan nayi babbar waya, ɗazun nan DOCTOR ya bani ita.”
Dariya Maji tasa cikin taya ƙawar tata murna tace.
” Masha Allah ƙawata kice yanzu zamu haɗe a WHATSAPP kenan, na tayaki murna.”
” Na gode ƙawata, am kin koma gida ne, ko har yanzu kina gidan ki tare da Amma.?”
” Na koma gida Falmata, bazan iya zama a gidan ba, nakam tunanin ZULUM har bacci ya nemi gagarata, gara kawai na dawo gidan mu, zanfi samun sauƙin raɗaɗin da nakeji a raina.”
Jinjina kanta Falmata tayi tace.
” Hakane gara da kika dawo gida, Allah ya jiƙan ZULUM, yasa ya huta, ƙawata Allah ya baki wani mijin wanda ma yafi ZULUM.”
” Hmmm!!! Nikam Aure ba yanzu ba, kar kuɗin ki ya ƙare, zamu haɗu a WHATSAPP Anjuma.”
Ta ƙarisa Maganar tana katse wayar ba tare da ta tsaya taji me Falmata zatace mata ba, Maganar aure ne yanzu kwatakwata bata so a ƙara mata shi.
Falmata ajiyan zuciya tayi tare da ajiyar wayar a gefen ta.
******************
Akwana a tashi babu wuya Falmata tun suna ƙirga kwanakin suka dawo ƙirga watanni, gashi yanzu har Allah ya nufa sun cika shekara ɗaya a ƙasar India, Saif kuwa tuni ya sanar dashi cewa an gama masa ginin gidan sa, da kuma asibitin, har funiture’s ansa a cikin gidan nasa.
yau wuni sukayi da DOCTOR suna siyayyar tsaraba na komawa gida, domin kuwa gobe suke saka ran zasu tafi, Acikin Shekara ɗayan da DOCTOR yayi ba ƙananan kuɗi ya samu ba, Shi kanshi uban gidan nasa baiso DOCTOR ya barsa ba, domin mutum ne wanda yasan aikinsa ƙwararrene a fannin fata, yana da jajurcewa, shi kansa yasan yanzu yayi rashin Jajirtaccen likita, bayan sun gama sayayyar ne da suka dawo gida.
Da daddare Falmata ta gama haɗa kayan ta, Bedroom ɗin DOCTOR ta shiga, yana ta famar haɗa nasa kayan Falmata tazo, ta fara tayasa bayan sun gama ne Falmata ta zauna gefen bed ɗin, DOCTOR zama yayi tare da cewa.
” Wannan motar fa na bawa Sanskar kyautar ta, saboda ya mana hidima ya kuma zauna damu bisa Amana a matsayinsa na Christen.”
Jikin DOCTOR Falmata ta faɗa tana saka hanunta tare da shafa gashin dake kwance a ƙirjinsa tace.
” Hakan yayi, Allah ya biyaka.”
Jin hanunta na yawo a kirjinsa ya sa tsikar jikinsa zubawa, sha’awarsa take ta fara tasowa, saurin capko bakinta yayi suka fara kissing ɗin juna, cike da ƙauna suke rommance ɗin juna, yayin da kiɗan ya sanja musu salo, sune basu sami nutsuwa ba, har sai da suka gamsar da junansu, tare sukayi wanka sannan suka fito dukkansu ɗaure da towel, Falmata ƙaramar rigar baccin ta, ta mayar shima DOCTOR rigar baccin nasa yasa, suka kwanta cike da nutsuwa.
Washegari da misalin ƙarfe 11 jirgin su DOCTOR ya ɗaga zuwa Nigeria, Falmata cike da farin ciki take zata dawo ƙasar ta.
Alhamdulillah sun sauƙa lafiya, Falmata da DOCTOR cike da nutsuwa suke saukowa daga jirgin, Maji murmushi take saki yayin da ta hango Aminiyarta, sosai taga tayi fresh tayi kyau, Falmata bata hango Maji har sai da suka sauƙo, Umma Aunty YANA Baba Bello Maji duka suna tsaye jiran sauƙarsu, Falmata cike da farin ciki da gudu ta faɗa jikin Maji tana dariya, itama majin dariya ta saka tana cewa.
” Welcome ƙawata.”
” Thanks ƙawallita, i miss You so MUCH.”
Umma ce tayi dariya tace.
” Ikon Allah wato kin manta ma damu Maji kawai idanunki suka hango.”
Dariya Falmata tayi ta saki Maji ta faɗa jikin Umma tana cewa.
” Umma na ganku mana, amma dai idanuna sunfi hango min Ƙawata.”
Dukkan su dariya sukayi har DOCTOR, Umma tace.
” To ai shikenan sai muje gida ko.?”
“Sannu Baba.” Falmata ta furta tana kallon Baba.”
Murmushi baba yayi ya amsa da sannu da hanya.
Bello shine ya kai akwatin su cikin mota, sannan suka shiga dukkan su, suka nufi gida………..
KI biya kuɗin ki ki karanta halak ɗinki yar uwa, karki na sata, ni bazan ja miki Allah ya isa ba, amma dai kinsan hukuncin wanda yaci haƙƙin wani ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*KULA DA JIKIN KI ƳAR UWATA DOMIN KUWA BABU ABIN KUNYA IRIN ACE MIJINKI YANA JIN KINA WARI.*
WARIN JIKI
Warin jiki na daya daga cikin abubuwan da ke janyo tsana a tsakanin jama’a, musamman lokacin zafi, idan aka hada gumi ko aka yi yawo a rana sai warin jiki ya rika tashi. Akan samu warin jiki ne saboda yanayin gari ko an haifi mutum da shi ko kuma ta irin abincin da ake ci. Kamar masu yawan cin tafarnuwa daga sun motsa sai an ji warinta.
Hanyoyi mafiya sauki da za ki bi don magance warin jikin:
♦ Turare: Yawan fesa turare na jiki ko na hammata ko na tufafi na magance warin jiki. Amma ki sani yawan amfani da turaren jiki da ko na hammata na sanya kuraje fesowa.
♦ Sabulu da ruwa: Hanya mafi inganci wajen magance wannan matsalar ita ce, amfani da tsaftataccen ruwa da sabulu, don yin wanka kamar sau uku a rana, kuma ki dage wajen wanke lungun da ke janyo wari kamar hammata da sauransu.
♦ Wankakken tufafi: Kada ki manta duk yadda mutum ya kai ga wanka idan tufafin da yake sanyawa masu datti ne, to lallai ba zai rabu da wari ba. Don haka ana son ki rika sanya tufafi mai tsabta musamman wanda ake sanyawa a ciki, kamar dan kamfai da rigar mama da sauransu.
♦ Amfani da sinadarin alam: Idan warin jikinki ya kasance mai tsanani ne, to sai ki rika sanya sinadarin alam a ruwan wankanki kafin ki yi wanka, hakan zai magance miki warin jiki.
♦ Zuma: Bayan kin yi wanka za ki zuba kamar cokali daya na zuma a ruwan dumi, sannan ki watsa a jiki, hakan na rage warin jiki.
♦ Shan ruwa: Domin rage warin jiki, za ki iya shan kofin ruwa daya da sassafe kafin ki ci wani abu..
♦ Amfani da ruwan Rose: Za ki iya diga ruwan rose water a cikin ruwa kafin ki yi wanka, hakan na rage warin jiki da kuma kara wa jikin kamshi.
*KITCHEN*
*KUNUN AYA MAI KWAKWA*
ingredients:
1⃣Aya
2⃣Sugar
3⃣Kwakwa
4⃣flavour
5⃣Madara
6⃣Dabino
Yadda zakiyi.
Da farko zaki wanke ayarki ki fitar da datin ta saiki jiqata tayi taushi ki kawo dabino ki bare shima ki sa shi a ruwa, saiki barsu su jiqu idn suka jiqu saiki zubar da ruwan ki kawo citta da sauran kayan qamshi ki zuba ki yanka kwawarki ki qanana ki zuba ki saka dabinon saiki bada a kai miki niqa idn aka dawo niqa saiki tace ki fitar da dusar saiki kawo sugar da flavour dinki mai qamshin kwawa ki zuba saiki kawo qanqara ki jefa saiki dan rufe .ki koma ki goga ragowar kwawarki a abun goga kubewa qanana saiki watse a ciki ki kawo madarar ki ta ruwa ki zuba saiki juya, kisa a gdn sanyi kunun ayarki na kwawa ya kammala asha dadi lpy😋
*Alƙalamin RASHEEDAT USMAN ✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*
[10/10, 10:23 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 82 to 83*
_________✍🏻 Cikin falon Umma dukkan su suka sauƙa, Falmata na zaune gefen Maji sai famar sakin murmushi take, ruwa mai sanyi da Umma ta kawo musu Falmata tasha, suna nan zaune sai famar hira ake ana dariya Aunty JALILA ta shigo da goyon ɗanta namiji a bayanta, Ashfat ƴar mijinta ne a bayanta riƙe da basket mai ɗauke da kula a ciki, ajiyewa tayi a gefe cike da dariya Aunty JALILA ta ZAUNA kusa da ɗan uwan nata, goyon ta since ta ajiye masa a cinyarsa tace.
” Oyoyo ɗan uwana yau dai Allah ya nufa ka dawo gabaki ɗaya kuma zamu ɗana ka, ga nan takwaranka, Junior.”
Murmushi DOCTOR ya saki yana ƙarewa yaron kallo wanda zai kai 7month a duniya.
” Masha Allah, Junior Allah ya albarkaci rayuwarka, Aunty na gode da takwara, ina alfahari dake a Duniyar nan Aunty har wani zaku ɗana Ni sai kace wata mota.”
Murmushi Aunty JALILA Tayi tana maida hankalin ta kan Falmata tace.
” Sannu da dawowa ƴar ƙanwata Falmata, kinga yanda kikayi kyau kuwa sosai fa, har wani haske kika ƙara meye sirrin ne, kodai ɗana ne yake kan hanya na fara tarun kayan suna tun yanzu.”
Dariya Falmata tasa tare da rufe idanunta tana dariya alamun kunya ta Girgiza mata kai alamun a’a, dariya Aunty JALILA tayi tace.
” Oh kunyar Umma kikeji kenan, shikenan ai idan tayi wari zamuji.”
Murmushi DOCTOR ya saki yana yiwa Junior wasa, Maji a hankali ta raɗawa Falmata cewa.
” Nima fa tun kallon farko dana miki a airport na fara zargin kin harbu, ciki ne dake Hajiya.”
Murmushi kawai Falmata tayi tace.
” To kuwa kin min kallon tsoro Malama, domin kuwa yanzu haka bana Sallah ɗazu da safe kafin mu taso al’adana yazo min.”
Cike da mamaki maji ta kama hanun Falmata suka shige Bedroom ɗin Umma duban ta maji tayi tace.
” Baki da ciki Falmata, Shekara guda da mijinki ya sanki ƴa mace amma ace har zuwa yanzu babu alamun ciki a tare dake, koda planning kike Falmata, karfa ki cuci rayuwarki, koda zakiyi planing ki bari tukunna ki samu ki haifi yaranki koda biyu ne, karkije garin neman kiba ki sami rama.”
” Hmm!!! Ban gane inda maganarki ta ƙunsa ba, planing kuma ni, a’a babu wani planing ɗin da nakeyi wallahi, asali ma ban taɓa gwadawa ba nifa yanzu ko zaki yanka ni basan kalar ƙwayar planing ba, kawai dai Allah ne bai kawo min haihuwa ba.”
Numfashi Maji ta sauƙe tare da furta
“Alhamdulillah, to Allah ya kawo rabo mai albarka, tashi mu koma falon ƴan sannu da zuwa suna zuwa kar aga baki nan.”
Tashi tayi suka koma falon, Falmata bata wani juma cikin falon Umma ba, ta gudu sashin su wajen Aunty YANA, anan tayi wanka taci abinci itace bata samu kanta ba sai dare ta samu nutsuwa, Aunty YANA da suke zaune tare ne tace.
” Bakiga Hajja ba, kuma baki tambaye ta, ba.?”
” Mama ban samu nutsuwa bane sai yanzu Kuma dama FANNA ta sanar dani cewa tana asibiti wajen BULAMA, insha Allah gobe zamuje da safe.”
Da Allah ya KAIMU Aunty YANA tace, tana tashi, wasu magungunan mata ta ɗauko ta kawowa Falmata, tare da mata bayanin yadda zatayi amfani dasu, karɓa Falmata tayi tare da yiwa Aunty YANA godiya.
Washegari da safe Falmata tayi wanka cikin wasu riga da siket na atamfa mai ruwan blue ɗinkin barno style, ɗakin AUNTY YANA ta shiga Baba Bukkar ta samu zaune yana breakfast, gefen sa ta zauna tare da cewa.
” Baba an tashi lafiya.”
Cike da ƙauna ya dubi ƴar tasa ya amsa mata.
” Lafiya Alhamdulillah, kun dawo lafiya, jiya bamu hadu kafin na dawo daga asibiti kun yi bacci, Bulama yace lallai yau kuje asibiti ku samesa keda Hassan, yanzu ma Hassan ɗin ya fita a nan na sanar dashi yace ma ya shirya ke yake jira.”
” To Baba dama anjuma zamuje ai dashi DOCTOR, Tunda ya shirya bari kawai nayi breakfast sai naje mu tafi.”
Tayi Maganar tana saka hanu cikin abincin Baba Bukkar, tare sukaci abincin cike daso da ƙauna irin na ɗa da Uba, Aunty YANA ce ta fito daga Bedroom ɗinta, zama itama tayi, Falmata ɗaga kanta tayi tare da gaishe da ita, bayan sun gama breakfast ɗin ne Falmata tashi ta fita zuwa SASHIN Umma, a falo ta sameta kwance sai FANNA dake zaune.
” Ina kwana Umma”
Falmata ta furta.
Cike da murmushi Umma ta amsa da lafiya tana cewa.
” Harkin tashi, yanzu Hassan ya shigo yake sanar min zaku asibiti, ko.”
” Eh Umma zamuje yanzu.”
” To a dawo lafiya” Umma ta furta tashi Falmata tayi ta fita, kusan karo sukaci da DOCTOR dake ƙoƙarin shiga, murmushi ya sakar mata tare da cewa kamar kuwa kinsan ke zan shiga nema, kinga ɗauko jakarki kizo ki sameni ina waje a cikin motar Bello sauri dan Allah zamuyi ɗan biye-biye ne.”
Murmushi Falmata tayi tare da shigewa da ɗan ta ɗauko mayafinta da kuma jaka, a motar ta samesa gaba ya buɗe mata ta shiga yana murmushi yaja motar tare dace mata.
” My Dear kinyi kyau sosai, wannan atamfar ta ƙarbi jikinki, yau fa da daddare zamu koma gidan mu, naso ma a ɗanyi walima, sai kuma na fasa tunda akwai walimar buɗe asibiti na ma, anyi odan magunguna gobe za’a kawo su, sai dai akwai waɗanda ba’a samu ba, kuɗin bai kai ba, zan yiwa Umma Magana ko zata sayar da filinta guda uku da suka saura sai ta bani kuɗin na haɗa, idan yaso daga baya na biyata sannan nayi sanarwar cewa zan ɗauki ma’aikata, sai dai abun farin cikin shine na samu ƙwararrun likitoci, guda goma, insha Allah idan mun fara aiki dasu, asibitin zai samu karɓuwa sosai wani sati zamu fara aiki insha Ranar Lahadi zamuyi walima Monday a fara aiki.”
Falmata murmushi tayi tana wasa da zoben hanunta tace.
” Masha Allah naji daɗin wannan labarin Ubangiji yasa ku fara wannan aikin cikin Nasara, ko yanzu Alhamdulillah Allah ya maka arziki na rufin asiri, Tabbas HABEEB mutum ne wanda ya cancanci girmamawa, domin kuwa duk wani daukaka daka samu yanzu sanadinsa ne.”
Haɗe ransa DOCTOR yayi jin ta ambaci sunan HABEEB, cikin tsawa yace mata.
” Ƙarya kike ba HABEEB ne sanadin samun ɗaukaka ta, Ubangiji shine ya ɗaukakani ba wani katon banza, karki kuskura na sake jin sunan HABEEB a bakin ki muddun kuwa kina neman zaman lafiya dani.”
Cike da mamaki Falmata take duban DOCTOR kishi take hangowa tsantsar sa a idanunsa.
” Allah ya huci Zuciyarka insha Allah bazan sake ba, kayi hkr bansan baka son jin sunan sa ba, da ban ambato ba.”
Bai kulata ba, cike da Zafin rai ya cigaba da dreving ɗin, Falmata ta basa hkr kusan sau uku amma yayi banza da ita dole yasa tayi shuru har suka shiga cikin asibitin, Darect ɗakin da Bulama yake suka nufa da Sallama suka shiga Hajja ne ta amsa tana murmushi gwanin sha’awa take kallon jikokin nata domin kuwa duk wanda ya kalli Falmata zaiga alamun jin daɗi a tattare da ita DOCTOR wani irin tsinkewa zuciyarsa tayi yanda yaga BULAMA yana kwance rai a hanun Allah, duk ya rame ga robar fitsari da aka saka masa cike da sanyin jiki ya zauna kusa da Hajja yana cewa.
” Hajja Bulama ne yake kwance haka, Hajja meyasa baki sanar dani, da nasa an ɗauko sa zuwa India, koda baya so amma fa Hajja kiga Bulama kamar bashi ba.”
Numfashi Hajja ta sauƙe tare da cewa.
” Ya muka yi jarabawa ce, kuma likitocin suna kula dashi sosai kasan sauƙi yana wajen Ubangiji, tun jiya yake ambato ku, lallai sai dai kuzo ya ganku.”
Share hawayen daya gangaro mata Falmata tayi ta matsa kusa dashi tare da kama hanunsa, a hankali ya buɗe idanunsa da kyar muryar sa ƙasa-ƙasa wanda sai ka nutsu sosai kaji yake cewa.
” Kira min Hassan Fatuma, kirasa kuzo kinji Fatuma.”
Kuka ne ya kusa ƙwace mata duban DOCTOR Tayi tace.
” DOCTOR Bulama kazo.”
Tashi yayi cike da kasala ya zo ya zauna kusa da kan Bulama.
” Sannu Bulama.” Ya furta idanunsa yana ruwa, kama hanunsa Bulama yayi ya haɗa dana Falmata a hankali cikin haki yace.
” Tunda na kwanta nake roƙon Ubangiji karya ɗau raina har sai kun dawo na ganku, Hassan ka riƙe Fatuma kamar yadda na haɗa hanunku, karka yadda ka rabu da ita, matar rufin asiri ce, dan Allah Hassan karka bari ƙaddara ta shiga tsakanin ku, ka riƙeta da kyau ka min zaka riƙe Falmata bisa gaskiya da Amana.”
Hawayen sa DOCTOR ya goge Yana kaɗa kansa tare da cewa.
” na maka Bulama babu wata ƙaddara da ta isa shiga tsakanina da Falmata, insha Allah itace matata har a lahira.”
Kaɗa kansa Bulama yayi tare da maida duban sa wajen Falmata.
” Fatuma ki kula da mijinki ki masa biyayya, karki saɓa Umarnin sa, duk abinda ya saki masa mijinki ne kuma yayanki, bana son ki raina sa, ina sone kuyi rayuwa mai tsafta mai cike da farin ciki, dan Allah Fatuma karki zamo irin mata waɗanda basu ganin darajar mijinsu, Allah ya muku albarka.”
Da ameen suka amsa cike da tausayi Hajja ma idanunta hawayen yake, domin kuwa duk wani alamu da mamaci yake nunawa haka Bulama yake nuna mata itace kawai ta fahimci hakan, DOCTOR sun juma sosai kafin suka tafi, kafin su koma gida sai da DOCTOR ya kaita taga asibitin nasa, sannan suka dawo abin mamaki suna shiga sukaji ana ihu, da sauri suka karisa ciki, AUNTY YANA ce take wannan kukan sauran matan gida kuma suna tsaye sunyi carko carko, cike da tashin hankali DOCTOR ya jawo Fanna yana cewa.
” Me yake faruwa a cikin gidan nan.?”
” Yaya BULAMA ne ya rasu yanzu Hajja ta kira ta ke faɗa su Baba Bukkar da Umma duk sun tafi.”
Kusan suman tsaye DOCTOR yayi tare da furta BULAMA kuma, mutumin da muka baro wajen sa ɗazu innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un………..
Kuyi hkr da wannan insha Allah gobe zaku sami read more da ɗan yawa masu son a Dawo labari to albishir insha Allah saura 3 page kacal mu dawo labari.
KI biya kuɗin ki kafin ki karanta, karki karanta min LITTAFI ba tare da kin biya ba, idan kikayi haka, Tabbas keda Allah nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180
*KITCHEN*
*MU GYARA DOMIN IYALAN MU DA MAI GIDAN MU TUKUNYAR KI SIRRIN KI*
1-Gawda amfani da maggi star dan samun danɗano mai daɗi
2-Rage yawan gishiri a miya yana taimaka mana wajan rage cututtuka da hawan jini gishirin da aka saka a sulale ya wadatar a miya sai dai a kara maggi.
3-ki samu roba mai kyau ki jiƙa kanwa dan amfani yau da kullum ba sai kina zuba garinta tana ɓata abinci”¿ saboda kanwa bata rabuwa da kasa
4-idan zaki soya manja bayan kin zuba albasa tai laushi karki barta ta ƙone sai ki ɗiga kanwa a ciki yana bada danɗano mai daɗi
5-soya albasa da citta da garlic sama-sama suyi laushi kafin kiyi sauce ko stew, suna bada kamshi a girki.
6-ba lallai kullum sai kiyi jar miya ba,dunga bada sauyi dan iyalanki,zaki iya yin yar sauce,albasa,garlic citta,koran tattasai ,attaruhu,tumatur,
Zaki iya zaɓar yau kiyi amfani da wannan gobe ki sake wata saffur ,yau kinyi da carrot,ko cabbage ko alayyahu.ko kuma ki dan chopping potatoes dinki dasu albasa da carrot attaruhu ki haɗa sauce,barin aci da couscous ko rice duk dai abin da kike so.
7-wake da shinkafa ba lallai sai kullum kinyi da mai da yaji ba ko da miya,zaki iya soya manja kiyi chopping albasa da attaruhu ki soya sai maggi da kayan kamshi.
Ko kuma kisa gasashan kifi titus ki ɓare kisa aciki idan kina bukatar local maggi wato daddawa itama kisa kaɗan sai alayyahu !
Zaki iya ci da wake da shinkafa ko doya
8-idan kika markaɗa garlic tare da mai sai ki samu roba ko kwalba ki zuba,amma ba’a saka ruwa zata daɗe kina amfani da ita batare data lalace ba,ko garlic da black pepper da mai,ana ajiyewa ya jima bai komai ba.
9-idan lokacin ganye yazo kamar calary ko Parcely ko curry leaves ko mint ko lemon grass ,ki yanka ki shanya awaje marar rana awa kaɗan ya bushe sai ki samu mazubi mai kyau ki adana dan amfanin gaba.
10-masara idan aka surfa sai ajiƙa ta kwana bayan kin shanyata ta bushe sai ki haɗa da rogo ki kai niƙa
“ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(UMMU NASMAH Ce)*
[10/10, 10:23 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 84 to 85*
__________✍🏻 Falmata jingunuwa tayi a jikin gini sai kuma kuka ya ƙwace mata durƙushewa tayi da gwiwwar ta, maganganun daya musu ɗazu ne kawai suke yawo a ƙwaƙwalwar ta, Tabbas ɗan adam ba komai bane, in yau kaine gobe ba kai bane Bulama ya rasu innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un!!! Ta furta cike da tashin hankali, DOCTOR saurin ficewa yayi daga cikin ya nufi asibiti, sosai gidan ya hargitse da tashin hankalin mutuwar Bulama, bama gidan ba har unguwar sai da ta amsa, mai unguwa mai adalci sun rasa shi, shin waye zai iya kwatanta adalci da Bulama ke yiwa talakawan sa, yawancin maganar da ƴan unguwar keyi tare da alhini.
Tun kafin a dawo da Bulama gidan ya cika da mutane masu kuka nayi masu addu’a na yi, Aunty YANA sosai idanunta yayi jajur tsabar taci kuka ta ƙoshi, Falmata kuwa tana jingine da jikin maji tayi shuru sai ajiyar zuciya kawai da take yi, Umma da Hajja tare suka dawo, kina kallon idanun Umma zaki tabbar da taci kuka, sai abin mamaki Hajja ta bawa kowa mamaki sosai tayi jarumta, bata masa kuka ba, sai addu’oi kawai dake fita daga bakin ta, kasancewar ta mace mai addini, A falon ta Hajja ta zauna ta cigaba da jan carbin ta, duk wanda yazo ya gaishe ta, sai dai ta ɗaga masa kai, ƙarfe 2 na rana aka dawo da Bulama, tsoffin unguwar sune suka masa wanka tare da sutura, yaransa kuwa babu wanda bai shiga ya masa addu’a ba, shi kansa DOCTOR ya juma a kansa yana masa addu’a, Hajja itace ta karshen shiga, ta tsugunna akan gawar tasa addu’a ta masa sosai kafin tace.
” A zamana da kai baka taɓa cutar dani ba, ka kasance mutum mai ibada da kyautatawa na ƙasa dakai, ina rokon Ubangiji yasa halinka na gari ya bika, Ubangiji ya kawo haske da salama cikin kabarin ka, Tabbas a hanu mukazo kuma a hanu zamu koma, Allah ya maka rahama, ya haskaka maka makwancinka.”
Ta ƙarisa Maganar hawaye na gudu saman fuskarta, a hankali ta tashi tare da ficewa tana masa kallon bankwana ba’a juma ba, kuwa aka kaisa makwancinsa sai fatan Allah ya kai haske cikin kabarin sa.
A ƙofar gidan aka kafa rumfuna na zama makoki, Baba Sosai mutuwar ta shiga jikin sa mutane Kuwa da suka hallaci wannan jana’iza Allah yayi yawa dasu, DOCTOR suna tare da Saif tunda akayi mutuwar, shima HABEEB ya halarci wannan ɗaurin auren, a cikin gidan kuwa suma cike suke.
Kwana uku da mutuwar akayi sadakar Uku da kuma bakwai suka haɗa kasancewar haka al’adar Kanuri take sukan haɗa sadakar Uku da ta bakwai a tare, kowa ya watse babu wanda ya rage, haka kowa ya ɗauki haƙurin rashin BULAMA, Hajja sosai tayi jarumta, ta cigaba da zaman takabarta.
Randa Bulama ya cika kwana bakwai da rasuwa da daddare AUNTY Yagana da Maji sai Inno matar Ibrahim ɗan baffan Baba sai AUNTY JALILA da AJIRAM sune suka raka Falmata gidan ta dake cikin unguwar New GRA unguwa ce mai kyau ta masu kuɗi, tun daga get ɗin gidan zaka tabbatar da DOCTOR ba ƙaramin kuɗi ya kashe ba, bare kuma idan ka shiga cikin gidan Part biyu ne, kuma duka benene, sosai falon Falmata yayi kyau sosai duk da Hassan shine yayi furniture ɗin amma ya saka mata Best color ɗinta pinch da ratsin fari haka cikin falon ya kasance, daga cikin Bedroom ɗin ma haka ne komai pinch, su AUNTY Yagana basu juma ba suka koma cike da saka musu albarka.
Bayan sun watse ne Falmata take ƙarewa gidan kallo sosai ya mata kyau harma yafi gidan da suka zauna a India tsaruwa, har Kitchen sai da ta duba, sannan ta dawo cikin Bedroom ɗin ta, tollet ta shige tayi wanka sannan ta fito ɗaure da towel, dressing mirror ta tsaya ta hau mulke jikinta da mai, ƴar powder ta shafa fuskarta da lips tick sannan ta ɗauki humra mai shu’umin kanshi ta shafe lungu da saƙo na jikinta, maroun ɗin sleeping dress ta ɗauko tare da zirasa a jikinta, zama tayi bakin mirror tana sakin murmushi tare da zaro wayar ta ta buɗe data, chart take hankali kwance ita da Maji, ƙarar buɗe ƙofar Bedroom ɗin dake gefen nata taji, hakan shine ya tabbatar mata da DOCTOR ne ya shigo, murmushi kawai ta saki ba tare da ta tashi ba.
Shi kuwa DOCTOR wayarsa ya ajiye a dressing mirror, yana sauƙe ajiyar zuciya, towel ya ɗauka dake ratayi jikin bed ɗinsa kayan jikinsa ya cire tare da ɗaura towel ɗin tollet ya shige bai juma ya fito ɗaure da towel ɗin, ya rataya ɗaya kuma a wuyansa yana goge jikinsa ac ya kunna saboda yana ɗan jin zafi, sannan ya mulke jikinsa da lottion, turare ya feshe jikinsa dashi sannan ya ɗauko riga da wando na bacci na maza fari tas ya sanyawa jikinsa, wayar sa ya zaro da niyar kiran Falmata sai kuwa yaji an turo ƙofar Bedroom ɗin Falmata ce kuwa ta shigo fuskarta ɗauke da murmushi gefen sa ta zauna tare da furta.
” Sannu da dawowa, yau ka ɗan juma a waje.?”
Murmushi yayi tare da cewa.
” Wallahi kedai bari, mun tsaya nida Saif ne muna tattaunawa game da sauran kayan aikin da zamu zuba a Hospital ɗin nan, kinsan babu Kudi yanzu a hanuna, da Umma naso tambaya sai kuma akayi wannan rasuwar shiyasa na dakatar da komai, so yanzu kuma ina kunyar tambayar ta gaskiya, saboda tasha hidima a kaina ina cikin tension.”
Ya ƙarasa Maganar yana huro iska daga bakin sa, Falmata gyara zaman ta tayi cike da kulawa tace masa.
” DOCTOR na, babu kunya tsakaninka da Umma mahaifiyarka ne fa, babu abinda bazata iya maka ba a duniya muddun tana da halin haka, dan haka banga wani abin kunya kawai ka tambaye ta na Tabbata zata baka.”
” Hmmm!!! Zata bani my dear amma sai nake gani kamar zan shiga haƙƙin ƴan uwana, zasu ga Kamar ina yiwa mahaifiyar mu wayo, bana son suji haushi na my dear.”
” Kaga DOCTOR, babu mai jin haushin ka cikin ƴan uwanka Domin kuwa suma masu maka ne idan har suna dashi, kawai kaje ka tambayi Umma dan Allah karka cuci kanka.”
” Hmmm!!!! Shikenan ba damuwa gobe zanje muyi Magana da ita, ɗazu na juma a gidan ana ƙoƙarin yanke hukuncin wanda zai gaji sarautar Bulama tsakanin Baba Bukkar da Baba, mutanen unguwa sunfi son Baba yayi sarautar, amma kuma Baba Bukkar shima yana son yayi, Baba kuwa yace baya son Sarautar to yanzu sunce gobe zasu yanke hukunci.”
Murmushi Falmata tayi tare da cewa.
” Oh Babana, ai dama Baba shine ya dace da yayi sarautar tunda shine babba, to Allah ya zaɓar da abinda yafi alkairi, DOCTOR na gidan nan fa yayi kyau sosai komai Normal har kitchen.”
Murmushi DOCTOR ya saki tare da jawo ta jikinsa yana cewa.
” Ai daman nasan dole zai miki kyau, wai ni na tambayeki mana, kawarki kam ta sallamar da Aure ne.”
” Hmmm!!! Ni kaina yanzu lamarin Maji ya fara bani tsoro, kwatakwata bata son Maganar Aure yanzu kana fara mata zata ɓata ranta, sai dai kawai mu bita da addu’a.”
” Amma ai hakan sam bai dace ba, ko ta manta da mutuncin mace ɗakin mijinta, zan sameta mu tattauna zancen, zanyi ƙoƙarin fahimtar da ita”
Cike da farin ciki Falmata ta rungumesa tana dariya tace.
” Wow Idan kamin haka zanyi farin ciki sosai domin kuwa ina son naga Maji a ɗakin mijinta.”
Murmushi DOCTOR ya saki cike da so da ƙauna ya shafa kanta tare da cewa
” Insha nasan zata gamsu da hujjata.”
Ya ƙarisa Maganar yana ƙanƙame matar sa, sun juma suna hira kafin bacci ya ɗauke Falmata blanket ya ja musu.
Washegari da safe Falmata tunda ta tashi sallar asuba bata maida bacci ba sai da ta gyara gidan ta tas sannan ta ɗaura musu breakfast, farar doya ta soya tare da sous ɗin tumatur da albarsa, sai tea data haɗa masu, sannan ta koma Bedroom ɗinta, wanka tayi ta shirya cikin riga da wando na kanta wanda suka matse jikinta, sosai suka mata kyau, a falo ta zauna kallo har 11 DOCTOR ya sauƙo cikin gajeren wando da best, zama yayi yana rungumota jikinsa tare da manna mata kiss.
” Good morning my dear love.”
Murmushi Falmata tayi ta amsa masa da
” morning Doctor na, breakfast is ready.”
” Sorry na manta ban sanar dake cewa akwai mai gaji ba, wanda kullum zaki dinga basa abinci dare da rana, sunansa Musa, sannan muyi Magana da Aunty JALILA tace akwai wata mai aikinta Ladiyo zata turo mana ita take tayaki aiki domin kuwa aikin gidan ya miki yawa ke ɗaya.”
Cike da farin ciki Falmata take masa godiya tashi tayi ta shige cikin Kitchen sai gata da kula cike da abincin ta miƙawa DOCTOR tace.
” Gashi ka kaiwa musa mai gadin sai ka dawo muyi breakfast ɗin.”
Karɓa DOCTOR yayi yana murmushi tare da tashi yace.
” Ai dole na tunda kin mayar dani ɗan aikenki, mijin tace.”
Dariya sosai Falmata ta saki tare da cewa.
” Kuma dole kaje ba, ko kuma na yanke maka *ƊANYEN HUKUNCI*”
Dariya DOCTOR yasa tare da ficewa kaiwa musa nasa breakfast ɗin, a zaune ya sami Musa yana famar jin rediyo zama yayi kusa dashi ya ajiye kular a ƙasa yana cewa.
” Sarkin masu jin rediyo ba, to ga breakfast ɗinka.”
Dariya Musa mai gadi yayi tare da cewa.
” Barka da fitowa Oga, an tashi lafiya, Oga ai Nigeria ce sai da jin labarai, har Hajiya ta fara girkin kenan, bari na wanko hanuna nazo na kwashi gara.”
Ya ƙarasa maganar cike da nishaɗi Girgiza kansa DOCTOR yayi yana murmushi, ya miƙe yana cewa ” a kwashi gara lafiya mlm Musa nima na shige.”
Ya ƙarisa Maganar yana tafiya, shima musa dariya yayi ya dauki buta da sauri ya wanke hanunsa kular ya buɗe yaga doya da sous mai yawan gaske wanda zaici har ya bari, murmushi yayi tare da furta ” da alama matar gidan nan zatayi kirki wannan abinci mai yawa haka ko a gidana iya wanda za’a bani kenan.”
Ya ƙarisa Maganar yana kai doyar bakinsa lumshe idanunsa yayi yana jin daɗin abincin yana sawa Falmata albarka.
DOCTOR kuwa a daining ya sami Falmata har tayi seving ɗin sa, plet ɗin ya jawo ya fara cin abincin a nutse, Falmata loma ɗaya tayi ta ajiye cibin sunan DOCTOR ta kira a hankali, idanunsa ya ɗaga ya zuba mata ba tare daya amsa ba, cike da raunin murya tace.
” DOCTOR kwanan nan marata tana yawan min ciwo ga kuma jinin al’ada na ya fara min wasa, jiya har sai da na tsorata.”
Ajiyar zuciya DOCTOR ya saki tare da cewa
” Tun yaushe ya fara miki.”?
Yau fa wajen wata Uku Kenan, shine nace ko zaka bani izini gobe naje asibiti.”
Girgiza mata kai DOCTOR yayi domin kuwa sarai ya gane abinda yake sawa jininta yake mata wasa wannan kwayar planing da take shane amma tsabar iya bariki na DOCTOR sai yace.
” ki bari gobe zamuje asibitin Fasaha sai na dubaki da kaina, idan yaso sai ki hau adaidaita ki dawo gida.”
Kaɗa kanta Falmata tayi alamun to sannan sukaci gaba da breakfast ɗin bayan sun gama DOCTOR bedroom ɗinsa yayi bai juma ba ya fito cikin shirin fita, hunging ɗin Falmata yayi tare da ficewa, FAMILY HAUSE ɗin su ya wuce, yauma a cike yaga fadar da alamun har sun shiga MEETING ɗin, fadar ya fara shiga tare da neman waje ya zauna ganin sai famar musu ake, mutanen unguwa sun dage da lallai sai dai a bawa Baba shugabancin su, yayin da shi kuma Baba Bukkar yake so a basa, ganin da Baba Bukkar yayi Yan unguwar sunfi son Baba ya sashi saka baki wajen a bawa Baba Sarautar, amma sam ransa baiso ba, shima kansa Baba baiso ba aka basa, a haka taron ya watse akan satin sama za’a naɗa Baba, shi dai DOCTOR part ɗin Umma ya shige Bayan yabar fadan, a waje ya sameta, shima yaja kujera ya zauna yana gaishe da Umma cike da fara’a ta amsa tana tambayar sa Falmata, sun ɗan juma suna hirar rayuwa kafin DOCTOR ya sosa kansa yana cewa.
” Umma dama nazo ne wajenki game da Maganar asibiti na, Umma kinsan an gama komai har ankawo wasu kayan aiki an zuba gashi next week nake son ayi walimar buɗe sa, to sai kuma kayan aikin basu gama kammaluwa ba, har yanzu akwai abubuwan da babu gashi babu kuɗi a hanuna shine nace Umma ko zaki taimakeni ki sayar da sauran filinki ki bani kuɗin n kawo sauran kayan insha Allah zan biyaki a hankali.”
Murmushi Umma tayi tana kallon sa kafin tace.
” Meyasa baka sanar dani tun farko ba, ai da na sayar na baka kuɗaɗen, amma yanzu ma bata ɓaci ba, bare na gama girki sai na saka hijab ɗina naje na samu kawun ka Dauda, sai ya sayar da duka biyun ya bamu kuɗin ina ga ai zasu isheka, ka kuma daina zancen zaka biya Ni, bazaka taɓa iya biyana abinda nake maka ba, addua kawai nake buƙata a wajen ka.”
Cike da jin daɗi DOCTOR ya yiwa Umma godiya kafin ya tafi.
Umma kuwa tana gama ayyukan ta da yamma lis taje gidan Kawu Dauda, Jummai matarsa kawai ta samu tsakar gida wajen bishiyar maina tana shan iska, zama Umma tayi, tana gaishe da Jummai, amsawa tayi ƙasa ƙasa tare da cewa.
” Yau kece cikin gidan namu kenan, ta ƙarin hkrn Bulama, yanzu nake jin Baban Musa yake cewa wai Baban Hassan aka bawa sarauta, gaskiya abu yayi daɗi Allah ya sanya alkairi.”
” Ameen mmn Musa, Yaya Dauda yana nan kuwa nazo wajensa ne.”
” Eh yana nan yana ɗaki bari na miki Magana dashi.”
Ta ƙarisa Maganar tana tashi tayi ɗakin nata, sun ɗan juma kafin suka fito tare Kawu Dauda zama yayi kusa da ƴar uwar tasa, Umma cike da girmamawa ta gaishe shi ya amsa yana cewa.
” Lafiya kuwa Yamuram yanzu fa na baro ƙofar gidan ku.”?.
Umma murmushi tayi tare da cewa.
” Lafiya lau babu komai, dama nazo ne game da sauran filina da suke wajen ku, dama saura Uku ne, to sai kuma kace min kana gini a ɗayan shine nace to na bar maka shi kyauta sauran biyun kuma ina son ka sayar min su duka, zan bawa Hassan kuɗin ne ya ƙara a asibitin sa, kuɗin hanunsa basu kai ba, shine zan cika masa.”
Dam dam gaban Jummai ya buga filayen da ta gama saka ran cewa sun gama zama nata shine yanzu za’a mata baƙin ciki ina bazai taɓa yiwuwa ba, zatayi magana sai taji kawo Dauda ya fara.
” Wai YAMURAM baki da hankali ne, shikenan ke dukiyarki akan Hassan zata ƙare, to bazai yiwu ba, bazaki sai da gadonki akansa ba, yasan da Asibitin nasa yaje ya shera BABBAN gida bene har biyu kamar gidan gwamna, sannan kazo kace uwarka ta sayar da kadararta ta baka kuɗi, to bazan bayarba yaje ya nema a wani waje amma bazaki ƙare a kansa ba.”
Umma cike da mamaki take duban Kawu Dauda, meye laifi idan ta taimaki ɗanta waye zai taimaka masa idan ita ta kasa taimakon sa, dan waye ta ajiye kadarar domin ta rufawa ƴaƴan ta asiri ne, SOSAI ran Umma ya ɓaci sai ta danne ɓacin ranta tace.
” Amma a tunanina yaya Dauda zan iya rasa komai saboda rufin asirin Hassan, wannan dukiyar tawa ce, dan haka idan bazaka sayar min ba, ka bani takadduna zan bawa MIJINA ya sayar min bance dole sai ka sayar min ba fili suna gamborin gala, kuma mijina yana da ƙafar da zaije ya sayar min.”
Cikin faɗa kawu Dauda yace.
” Bazan bayar ba kizo ki ƙwata idan kina da karfi karfa kimin Rashin kunya YAMURAM, ki shige ki tafi ki bani waje bana son shashancin banza.”
Murmushi Umma ta saki tana dubansa, a yanzu ta fara gajiya da mulkin mallaka da Kawu Dauda yake mata akan dukiyarta dan haka yau ta gaji dole ya bata takadduna.”
” Ya isheni haka Yaya Dauda, ka bani takadduna tun muna cikin girma da arziki, nayi niyyar taimakon ɗana kuma bazan fasa ba, koda kuwa zan rasa komai shiya tashi, ka bani takadduna idan ba haka ba, hukuma ce zata rabani dakai, saboda naga alamun kamar so kake na bar maka dukiyata ka cinye.”
Dariya Jummai tayi, ba tare da tace komai ba ta shige Bedroom ɗinta, bata juma ba, ta fito hanunta riƙe da takaddun ta miƙawa Umma tace.
” Allah ya baki haƙuri ga takaddun ki, haƙƙinki ne ai tunda kika nema kuma ai dole a baki, Baban Musa bai kyauta ba kiyi hkr yaushe ne zaki sayar da Filin.”
Umma hanu tasa ta ƙarbi takaddunta tace ” gobe idan Allah ya kaimu da safe Baban Hassan zaije ya saka a kasuwa.” Tayi maganar tare da ficewa a zuciye, Kawu Dauda duban Jummai yayi yace.
” Kinsan me kikayi kuwa, takaddun nan fa da kika saka a ranki shi kika bata.”
” Na sani Baban Musa, zagon ƙasa na mata, kuma wallahi sai filin nan sun dawo hanuna, sai Musa ya fita ƙasar waje karatu shima da wannan dukiyar, duk wanda yaci tuwo dani miya yasha, badai gobe ne shi mijin nata zai tafi sayar mata da filin ba, kaji kaji mai zai faru lokaci yayi da zamuga bayan YAMURAM ka saka Ido kawai kayi kallo dani suke zancen nida su shege ka fasa.”
DARIYA Kawu Dauda yayi tare da cewa.
” Na sani bakya Magana baki aiwatar ba, nima a yanzu ina buƙatar ganin ɗana yayi karatu domin kuwa akwai riba, ki duba kiga yanda wannan yaron Hassan yake neman yin kuɗi, duk abinda zakiyi ina bayan ki, sannan idan kina naiman taimako na, a shirye nake.”
Tare suka saka dariya cike da mugunta da kuma mungun nufin su………….
Sorry for typing error not editing.
Karki KARANTA min LITTAFI ba tare da kin biya ba, ki biya kuɗin ki kafin ki karanta, neme ni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki, 08147537180.
*MU SHIGA KITCHEN MATA*
*Dambun Kwai*
Ingredients
Kwai
Nama
Curry
Maggi
Gishiri
Albsa
Tarugu
*procedure*
Zaki tafasa namanki da citta da albasa magggi gishiri inyatafasu saiki sauke kizuba shi aturmi kidakashi yayi kamar zakiyi dambun nama saiki juyeshi awurimaifadi saiki zuba jajjage aciki saiki fasa kwai biyar
Kiyanka albasa kixuba curry saiki zuba maggi da gishiri kadan saiki jujjuyashi saiki. Daura mai inyayizafi saikizuba naman dakikahada inyasoyu zakiji kamshi saiki sauke
*Butter yam*
Ingredients
Doya
Butter cokali8
Albasa1
Kwai:3
Curry cokali 1
Gishiri
Mai na suya.
METHOD
Ki fere doya ki yanka ki dauraye ki dafa ta sai ki marmasata sosai ki zuba butter ki sa maggi gishiri curry sai ki lailayata dogaye kamar girman spring rols ki sata a furji ko gurin mai sanyi tayi awa daya sai ki kada kwai ki dora mai a wuta yayi safi saiki dinga tsoma doyarki. Acikin ruwan kwai kina sawa a mai kina soyawa idanyayi ruwan kasa sai a tsame.
*PINEAPPLE,MANGO, PAW_PAW AND BANANA JUICE*
1 Pineapple
2 Banana
3 paw paw
4 mango
Da farko zaki wanke mango dinki sai ki, fere bayan sa, sai ki zuba masa ruwa ki dora akan tukunya ya dahu, idan ya dahu sai ki saukeshi, sai ki yanka banana dinki tare da sauran kayan kanana, sai ki markad’asu, amma ki markad’a yadda zaiyi laushi, shima sai ki kawo wannan mango din shima ki markad’a bayan ki gama sai ki kawo kankara ki saka a ciki,zaki iya bud’a baki dashi
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN*✍🏻
*(UMMU NASMAH CE)*
[10/10, 10:23 PM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 86 to 89*
__________✍🏻 Umma cike da ɓacin rai ta shigo cikin gidan nata, zama tayi ranta a ɓace Baba dake zaune ne ya dubeta tare da cewa.
” Lafiya kuwa Yamuram, naga kin shigo haka cikin ɓacin rai meke faruwa.”
” Baban Hassan, wai yau ni, Yaya Dauda zai wulaƙanta akan dukiyata, har yana neman zagina dan kawai zan karɓi kayana bafa taimako naje nema wajen sa ba bare kuma ya wulaƙanta ni.”
” Subabanallah, Daudan meya haɗaku haka.”
” Baban Hassan, kasan dai akwai gado na a wajen sa, gidaje ma biyu na gada duka ya hallakar dasu ko kai ban sanarwa ba, nayi shuru nabar maganar a ciki na, ko yarana ban sanarwa ba, gudun fitina, sannan still cikin filayen da nake dasu biyar ya hallaka biyu suma na barsa nayi shuru, ɗaya kuma na sayar na bawa Hassan kuɗin sanda zai tafi India, wai shine yanzu naje nace ya sayar min da sauran guda biyun zan bawa Hassan zai saka cikin asibitin sa, shine zai ce min wai bazan ƙare akan yarana ba, kai kaji fa wata Maganar da bata da daɗi, yau ko faɗuwa nayi na mutu bashi da gadona yaran nawa dai sune zasu gajeni, na karɓo takaddun filaye na, gasu nan zan baka, gobe kuje da kai da Hassan da JALILA ka samin fili a kasuwa, JALILA kuma abinda yasa zakaje da ita saboda akwai mai bada maganin ciwon ƙafa a wajen sai ta karɓa, gashi kuma tana da mota kaga zaku sami sauƙin tafiya.”
Numfashi Baba yaja yana duban Umma yace.
” Amma banji daɗin abinda kikayi ba, ai tsakanin ƴan uwa da ɗan uwa sai Allah, idan ya huce zuwa gobe ko jibi kije ki basa hkr, insha Allah gobe kuma zamuje a sai da filin.”
Da to Umma ta amsa amma dai cikin ranta tana jin haushin Kawu Dauda, Baba ne yace.
” Ɗazu mun shiga MEETING an yanke shawarar cewa nine zan karɓi sarautar Bulama, sai dai gaskiya banso hakan ba, domin kuwa shi Bukkar mutum ne mai son SARAUTA tun sanda muke yara, mtsss, amma ba yanda na iya dana bar masa sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi.”
” Haka ne tunda al’umma ne suka zaɓeka Allah yasa hakan shi yafi alkairi, amm kira min Hassan a wayar ka.”
Ciro wayar Baba yayi tare da neman numbern Hassan, bayan ya ɗaga ne ya miƙawa Umma karɓa tayi tana cewa.
” Ganan takardun filin nan na karɓo gobe idan Allah ya kaimu kazo kuje da Baban ka kuje ku sai da filin, zakuje harda JALILA saboda zata karɓi maganin ƙafarta acan.”
Shuru Hassan yayi sai kuma yace.
” Umma bazai yiwu aje dani ba, saboda akwai abubuwan da zanyi cikin asibitin gobe, Baban ma kawai idan yaje ya wadatar, saboda zamu tantance likitocin da zasu yi aiki a asibitin ne gobe.”
” To shikenan babu damuwa Allah ya taimaka, akwai wasu kuɗi a hanuna dubu ɗari, sai kazo ka karɓesu ka fara dasu kafin muga abinda Allah zaiyi.”
Cike da ƙaunar mahaifiyar tasa DOCTOR ya mata godiya, domin kuwa babu wanda zaiyi faɗi tashi domin ganin cigaban ka, sai iyayen ka.”
Katse wayar yayi yana duban Falmata dake kwance a doguwar kujerar falon, yace.
” Hajiya ya akayi ne kikayi shuru kamar wanda ruwa ya cinyeta.”
Ɗan murmushi Falmata tayi tana cewa.
” Kai dai bari wallahi bana jin daɗin marata ne, kuma nace maka muje asibiti har yanzu Kamin shuru, ga wasa da jinina yake min.”
” Zamuje gobe idan Allah ya kaimu, bari naje na watsa ruwa zafi nake ji.”
” Okay sai ka fito.”
Tashi DOCTOR yayi ya haura sama ita kuwa Falmata shuru tayi tana jin Damuwar wasan da jini ke mata, ta rasa wa zai faɗa mata ma’anar hakan ga yawan ciwon mara da ada bata yinsa, rashin amsar tambayar ta ya sata sakin ajiyar zuciya ta tashi ta shige Kitchen.
*****************
Jummai kuwa yau magaruba a wajen bokan ta ya mata tsugunne take gaban sa tana sanar dashi dukkan abinda ke faruwa tare da ɗaurawa da.
” Sannan abinda na yanke shine zansa a tare a hanya, a kwace takaddun sannan aje a ɓoye su inda babu mai ganinsu har sai mun gama cika burin mu.”
Dariya marar daɗin sauraro bokan yayi mai haɗe da amo yace.
” Idan kika saka akayi haka to Tabbas mun samu Hanyar da asirin mu zaiyi aiki akan ta, idan kinsa an ɗauke su, ki kirata kice tazo wajen ita ɗaya idan har tazo, kinga wannan kwalbar ki fasata ki juye ruwan a jikinta, da zarar ta koma gida, shikenan zata kwanta jinya zata dinga yin abu tamkar mahaukaciya, bazata ƙara sanin waye a kanta ba, bare ta nemi tona muku asiri, amma fa dole ki sata komawa gida da wuri idan ba haka ba, a wajen zata faɗi miki, ki riƙe wannan kwalbar da kyau, samun maganin karya wannan asirin yana da matukar wahala sannan zan turo aljanu kan ƴarta Ƙaramar nasan Bukkar yana son SARAUTA to zansa Fanna ta faɗi ta bada shedar cewa su Bukkar ne sukayi asiri suka ɓatar da da Mala sannan suka kwantar da Yamuram jinya, saboda na kawar musu da zargin da suke muku.”
Cike da farin ciki da kuma mamaki Jummai tace
” Boka ina kasan wannan maganar sarautar da kuma sunan su.”?
Tayi tambayar cike da mamaki, dariya ya bushe dashi sannan ya daki wani ruwa dake cikin ƙwarya a gabansa, take kuwa photo Bukkar ya bayyana da kuma Fanna, yana dariyar yace.”
“Ki daina mamaki akan aiki na, domin kuwa ni ba karamin hatsabibi bane, karɓi kwalbar nan ki tashi ki tafi la’ananniya!!!”.
Ya mata Maganar cikin tsawa yana haɗa fuskarsa, ai kuwa da sauri Jummai ta ajiye masa kuɗi tare da ɗaukar kwalbar ta fita ta baya baya.”
**************
Da daddare Falmata na kwance jikin DOCTOR, ya dubeta tare da cewa.
” Kin san me zai faru tashi ki ɗauko hijabin ki, muje Asibitin Lawan na dubaki, saboda gobe akwai abubuwan da zanyi sosai mawuyacin abune na samu lokaci.”
Tashi Falmata tayi tana murmushi ta amsa da to, sama ta haura bata juma ba kuma sai gata ta fito sanye da hijabi, tashi yayi ya kama hanunta suka fita adaidaita suka hau har cikin Asibiti, Saif ya samu yana zaune a OFFICE ɗin DOCTOR Lawan, dariya DOCTOR yayi yana miƙa masa hanu suka tafa yace.
” Kaji shegen gari yau kuma nan ka ɓullo.”
Dariya shima SAIF yayi yace.
” Dafa gidan ka nayi niyyar zuwa sai kuma na fasa na gangaro nan, to ya akayi na ganka da Madam ko dai kunzo fara awu ne.”
Dariya DOCTOR yayi yace.
” Kaji banza idan awu ne sai kuma muzo yanzu, ina DOCTOR Lawan ɗin.”
Murmushi SAIF yayi yace wa Falmata.
” To Madam Hassan, ya kk, jiya ai na kira numbern ki bakiyi picking call ɗina ba, dama cewa zanyi ki dafa abinci mai daɗin gaske ina hanya.”
Dariya Falmata tasa tace.
” Ai kuwa da kazo da ka samu abinci mai daɗi, banga kiran ba, sai daga baya, na kuma nemi layin naka sai yaƙi tafiya.”
DOCTOR ne yace.
” Kai dallah Uban ƴan kwaɗayi, baka bani amsar tambaya ta ba, ina DOCTOR Lawan ɗin.?”
” Kai DOCTOR Lawan fa Tunda yaga na shigo ya fita ya barni da aikin da ba nawa ba, kaje kawai kayi abinda ya kawo ka, dan bana tunanin zai dawo yanzu.”
Taɓe bakin sa DOCTOR yayi tare da ɗan sunkuyawa ya ajiye wata ƙaramar kwalba mai cike da ƙananun magani ya cewa Falmata muje ko tashi tayi tabi bayan sa tunda ya fita Saif yabi kwalbar daya ajiye da kallo, kasa hkr yayi ya saka hanu tare da ɗago kwalbar buɗewa yayi tare da zaro idanunsa a fili ya furta.
” Ƙwayoyin planing kardai ace waɗannan mutanen planing suke lallai kuwa da sun cika cikakkun marassa hankali”
Ajiyar zuciya ya sauƙe yana jinjina kansa, jumawa kaɗan kuwa sai DOCTOR ya shigo shi kaɗai cikin sauri zai ɗauki kwalbar daya ajiye bisa mamakin sa wayam babu ita inda ya ajiye, cike da mamaki ya dubi SAIF yace.
” SAIF na ajiye wata kwalba anan ban ganta ba, waye ya shigo.”
Numfashi Saif ya sauƙe tare da ɗauko kwalbar yace.
” Gata nan, naga kwayar planing cike cikinta, amma amatsayin ka na cikakken likita, kasan illar da wannan kwayar da take ɗauke daahi ko, wallahi kun bani mamaki daga kai har Falmata, tsarin Iyali tun yanzu bazaku bari koda yara biyu bane ku haifa idan yaso ku fara planing ɗin, zan samu Falmata zan mata Magana naji meye hujjarta na neman cutar da kanta, domin kuwa planing kafin haihuwa kasan yana jawowa mahaifa ta samu matsala wanda ko da gaba ta samu ciki, lalacewa cikin zai dinga yi, idan akayi rashin dace ma, sai a rasa haihuwar gabaki ɗaya duk kasan da wannan amma ka bari takeyi, idan bazaka iya hanata ba, ni zan hanata na mata bayanin illolinsa tun kafin ya mata yawa.”
A matuƙar fusace DOCTOR yace.
” Enough Malam, babu ruwan ka cikin wannan lamarin ban aika ka kaje ka faɗa mata domin kuwa bata san ina mata wannan planing ɗin, dan haka babu ruwan ka, haihuwa ce yanzu ban shirya mata, saboda nima ta kaina nake, ban gama ɗaukar buƙatun kaina ba tukunna bare kuma na ɗauki nata dana yara, yanzu haka Umma ce zata saida filin ta, domin na samu na ƙarisa abinda babu a cikin asibiti na, Taya kake tunanin zan tara iyali a haka, babu ruwan ka, ka kau da idonka cikin wannan lamarin.”
Tashi tsaye DOCTOR SAIF yayi yana yiwa DOCTOR kallon mutum mai son kansa, yace.
” Bata san kana mata planing, saboda ba kai zaka cutu, kana ganin duk sanda ka shiryawa haihuwa koda ita bazata haihu ba, zaka auro wata matar tazo ta haifa maka yara, ita kuma Falmata ka cuceta, wallahi kaji tsoron Allah ka dakata haka kabar yarinyar nan ta haifi Wanda zasu mata addu’a koda bayan mutuwar tace, bakayi talaucin da har zai sa ka kasa riƙe gidan ka ba, wannan kawai son zuciyarka ne, ka gyara idan ba haka ba, wallahi zan sanar da Falmata cutarwar da kake mata.”
“Hmmm!!! Jeka sanar da ita tunda burinka ka kenan ka shiga tsakanin mu, to jeka ka faɗa maka, duk yanda zaka so Falmata baya nane tunda ƴar uwata ce kuma matata, to kai meye case ɗinka a ciki, ka daina min haka bana son muzo muna samun saɓani da kai.”
” Wannan ba soyayya kake mata ba, zalunci sunan sa, Tabbas nasan ƴar uwar kane kuma bazan shiga tsakanin ku ba, amma ka sani, duk randa ta gane kana bata fill, sai tafi kowa tsanarka, kashi ma sai ya fika darajar a idanunta.”
” A’a ƙarya kake Falmata bazata taɓa tsanata ba, Soyayyar da take min dole zaisa tamin uzuri.”
Ya ƙarisa Maganar tare da ɗaukar kwalbar ya sata a aljihun sa ya fice, a zaune ya samu Falmata, yace ta tashi su tafi, koda suka koma gida a falo suka zauna, DOCTOR ya dubi Falmata tare da cewa.
” Mahaifarki ne ta samu matsala, shine yake kawo miki wannan ciwon marar da kuma wasa da jinin da yake miki.”
Ya faɗi maganar ne kawai domin kuwa karya yake mata so kawai yake yayi amfani da wannan damar wajen bata ƙwayar planing ɗin ta hanyar sanja mata kwalba domin ta cigaba da amfani dashi kanta.
A matuƙar tsorace Falmata tace.
” Na shiga Uku, DOCTOR bazan haihu ba kenan.”
” A’a ba haka nake nufi ba, zaki haihu nan da lokaci kaɗan, hanunsa yasa cikin aljihu ya ɗauko wannan kwalbar ya miƙa mata, wannan shine maganinki idan kika cigaba da amfani dashi, zaki sami sauƙi, kullum shabiyu na rana zaki na sha, karki kauce lokaci koda kuwa da minti biyar ne, zaki sami lafiya da yardar Allah.”
Kaɗa kanta Falmata tayi cikin tashin hankali ta karɓi kwalbar………………
Kuyi hkr da wannan, sannan kwanan nan bana samun damar muku editing so sorry my lovely FAN’S.
Ki biya kuɗin ki kafin ki karanta karki karanta min LITTAFI baki biya ba, ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻*
*(Ummu Nasmah ce)*
[10/12, 9:57 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 90 to 91*
_________✍🏻 Washe gari da sassafe DOCTOR ya fito cikin shirin sa ko karyawa bai tsaya yayi ba, saboda yana son yaje suyi sallama da Baba kafin ya wuce, Ɗakin Falmata ya leƙa tana kwance tana bacci abinta cikin kwanciyar hankali, murmushi kawai ya saki yaja mata ƙofar ya fita a binsa, koda yazo ƙofar gidan nasu motar Aunty JALILA tana nan alamun harta sammako cike da murmushi ya shiga cikin gidan, da Sallama, AUNTY JALILA itace ta amsa tana sakin murmushi, kusa da ita ya zauna yana cewa.
” AUNTY har kin ƙaraso, ina Junior na ganki ke kaɗai kaddai har yayi girman da zaki fara barinsa.”?
Murmushi Aunty JALILA tayi tace.
” Na barsa a gidan su wajen yayunsa, tunda yana cin abinci kuma yana shan kunu ai kaga nima sai na huta.”
Murmushi ya saki tare da cewa.
” Okay tafiyar zata miki daɗi kenan, ina kwana Aunty bamu gaisa ba muka tsaya zance.”
” Lafiya Alhamdulillah, naji Umma tace zamu tafi tare da kaine, yanzu kuma Fanna tace min wai ka fasa zuwa meyasa.?”
Numfashi ya sauƙe yace.
” AUNTY, abubuwa sun min yawa, yanzu haka yau 10am ɗin nan zamu tantance ma’aikata, ga kuma tashin hankali na sauran kayan da ban samu na ƙarisa sawa a cikin asibitin ba, gashi on Monday za’a fara aiki cikin asibitin sauran kayan yanzu haka an kawo su suna hanu, kawai baza’a bani bane sai na basu kuɗin.”
Murmushi Aunty JALILA ta saki tare da cewa.
” Yanzu nawa ne kuɗin da zaka kai musu, su baka kayan.?”
” Dubu ɗari takwas fa Aunty, shine ai duk na shiga cikin tashin hankali kuɗin suna da yawa sosai.”
” Dubu ɗari takwas ne suke da yawa, kaga akwai kuɗin Ahmad ƙanin mai gidana daya tura min ajiyarsu ta account ɗina, so yanzu bari na ara maka sai ka kai musu su baka kayan, idan yaso aka sayar da Filin sai a bani na maida masa kuɗin sa, bani account numbern ka na maka transfer ɗin su yanzu.”
Wani irin farin ciki DOCTOR yaji tare da jin ƙaunar Yar Uwar tasa ta ƙara ninkuwa a cikin zuciyarsa cike da farin ciki yake mata godiya, account numbern ya bata take kuwa ta masa transfer ɗin.
” AUNTY wai ina Umma ne kam ban ganta ba.”?
” Ta shiga ɗakin Baba yanzu zasu fito.”
Jinjina kansa yayi sannan suka ci-gaba da hira da Aunty JALILA har su Umma suka fito DOCTOR Baba ya gaishe.
” Baba an tashi lafiya.”
Murmushi Baba ya saki yana karewa DOCTOR kallo, haka kawai yake jin jikinsa ya mutu da tafiyar wani irin sanyin jiki yake ji mai cike da kasala, kara duban DOCTOR yayi yace.
” Lafiya lau Hassan ya iyalin naka.”
” Tana lafiya Baba, da tare zamu taho sai kuma bata jin daɗin abinda yasa bamu taho tare ba.”
” Ayya Allah ya bata lafiya, mu zamu wuce sai Allah yayi dawowar mu lafiya, ke JALILA tashi mu tafi.”
Umma ce tace.
” A dawo lafiya Allah ya tsare ya kaiku lafiya, JALILA ki masa bayanin duk yanda ƙafar ke damunki ko, kinga wannan cikin da kikayi kinsha wahalar ƙafar.”
” Insha Allah Umma zan sanar masa.”
A dawo lafiya DOCTOR ya musu har wajen mota ya rakasu sanda suka tafi sannan ya koma cikin gidan.
Sanda ya karya a wajen Umma sannan ya sanar da ita Aunty JALILA ta ranta masa kuɗi zaije yanzu ya basu kuɗin ya karɓo kayan.
Umma sosai itama taji daɗin yanda JALILA take ƙaunar ɗan uwan nata, sun ɗan juma da Umma Kafin ya tafi.
**************
Falmata kuwa koda ta tashi wayam ta gani babu DOCTOR hakan ya nuna mata cewa yayi sammako ya fice, wanka tayi sannan ta fito zata shiga Kitchen bisa mamakin ta har Ladiyo da tazo jiya ta gama breakfast ɗin tana famar mopping ɗin falon cike da farin ciki Falmata tace.
” Kai Ladiyo irin wannan aiki haka baki gajiya ne, kinyi breakfast kuma yanzu kizo kina mopping, kawo na miki mopping ɗin sai ki huta ko tunda kinyi girki.”
Ta mata maganar cike da kyautatawa tare da tausayi, Ladiyo murmushi tayi cikin sanyin murya tace.
” A’a Aunty ki bari zanyi, ke dai ki huta, ni ai na saba da waɗannan ayyukan.”
Ɗan dariya Falmata tayi tace.
” No Ladiyo ni bazan barki ba, aiki ya miki yawa, ba ƴar aiki na ɗauke ki ba, ƙanwata ta jini na ɗauke ki, kinga kuwa ai bazan bari wahala ya miki yawa ba, dan haka ki dinga min kallon yayarki da kuka fito uwa ɗaya uba ɗaya, ba matsayin wacce kike wa aiki ba, bani kije kiyi wanka ki kwanta ki samu nutsuwa sai ki fito kiyi breakfast nasan baki maida baccin asuba ba.”
Miƙa mata abin mopping ɗin Ladiyo tayi, cike da jin daɗi ruwan idanunta suna ƙoƙarin zubar da Hawaye na jin daɗi tayi aiki a gida Uku, bata taɓa gamuwa da uwar ɗaki mai kirkin Aunty Falmata ba, duk da Aunty JALILA ta kwatanta mata adalci da kauna amma Tabbas Falmata tafi ƙaunar ta, Bedroom ɗin ta ta shige cike da jin daɗi, Falmata mopping ɗin tayi, sanda ta gama ta kira numbern mijin nata three miss call bai ɗaga ba, dole ta hkr ta barsa, breakfast ɗinta tayi sannan ta dawo tsakiyar falon ta cigaba da kallo sha biyu dai-dai ta ɗauko maganin ta cikin hanzari tasha, sannan suka ci-gaba da hirarsu da Ladiyo tamkar ƙawaye.
Shi kuwa DOCTOR tuni harya biya kuɗin kaya sun kawo masa tare da DOCTOR SAIF da waɗanda suka kawo kayan suka shigar dashi cikin store, sannan suka fara gabatar da interview ɗin, cike da nutsuwa.
Da misalin ƙarfe sha biyu na rana Umma tana zaune taji kiran wayar ta, ɗaga wayar tayi taga JALILA, ajiyar zuciya ta sauƙe tare da ɗaga kiran tana cewa.
” Ya akayi JALILA, har kun isa ne.”
Wata Irin ƙatuwar murya marar daɗin ji Umma taji ya doki kunnen ta cikin tsawa.
” Ba JALILA bace keee tsohuwar banza!!!! Ƴarki da mijinki mun sace su suna wajen mu, idan kuma har kina so mu sake su kizo yanzu da dubu ɗari, cikin ƙauyen KUKAWA, kuma karki sanar da kowa bare kuma ɗan sanda idan har kika sanar musu to wallahi gawarsu zaki samu daga nan harki karaso muna da mai bibiyar ki idan kinzo ki kira wannan numbern.”
Cike da tashin hankali Umma ta miƙe tsaye tana furta innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un!!! Cikin tashin hankali ta zari hijabin ta ta fice ba tare da kowa ya sani ba, da ƙyar ma ta samu motar Ɗan Birni wanda daga shi mashin kawai zata hau ya shigar da ita KUKAWA, tunda suka shiga motar take Allah Allah su isa, domin kuwa ita kaɗai tasan mungun tashin hankali da take ciki, ƙarfe ɗaya suka shiga ɗan Birni sannan ta hau mashin zuwa KUKAWA tashin hankali da take ciki har ya sata mantawa da ambaton Allah, basu yi wata doguwar tafiya ba, kuwa suka shiga cikin kukawa Umma tsayawa tayi gefe tare da kiran layin Jalila sai da ta kira sau biyar ba’ayi picking call ɗin ba, sosai Umma ta shiga cikin tashin hankali tsoronta ɗaya karsu cutar dasu, hanunta na ɓari ta ƙara kiran wayar, cikin Sa’a akayi picking ɗin cike da tsawa yace.”
” Ki juya bayanki zaki ga wata farar mota ki biyota, a inda tayi parking wannan gidan zaki shiga.”
Cike da hanzari Umma ta juya bayan ta, tashin motar ta gani, cikin sauri mai haɗe da gudu take dumfarar motar, yayin da drever yake sauri cike da mugunta ganin da Umma tayi zai ɓace mata ya sata binsa da gudu, wani madaidaicin layi ya shiga Itama ta bisa, a kofar wani ƙaramin gida yayi parking, ba tare da ya fito ba, cikin sauri Umma ta shige cikin gidan a tsakar gidan taga Baba da JALILA ɗaure a cikin rana, an manne musu baki da gam, cike da tashin hankali Umma ta nufesu da gudu sai dai kafin ta ƙarisa taji an daki kanta da wata kwalba wani irin wari taji sakamakon ruwan dake bin jikinta tamkar ruwan kwata, a hankali take bin jikinta da ruwan ke bi da kallo, kafin ta juyo da sauri, Jummai dake saurin komawa kar Umma ta ganta ne suka haɗa ido biyu da Umma, cike da ruɗani tare da tsantsar mamaki Umma ke bin Jummai da kallo, ” me muka mata wanda yasa zata mana wannan mummunan aikin, meyasa meye tsakanina da ita ban taɓa tashin hankali da ita ba, meyasa tamin haka” Umma ta furta cikin zuciyarta cike da tashin hankali, da hanu ta nuna Jummai tace.
” Jummai me…………”
Dakatar da ita Jummai tayi cikin tsawa tace.
” Baki da lokacin tambayata, ki ajiye kuɗin da kika kawo ƴarki da mijinki zasu dawo gobe idan kuma kika mana taurin kai wallahi yanzu zansa a kashe su a gabanki sannan kema na kashe ki.”
Cike da tsoro Umma jikinta na rawa ta ajiye kuɗin ta fito da sauri tana hawaye, Aunty JALILA hawaye ke gudu a fuskarta tana ƙarewa UMMA kallon tausayi yayin da take jifan Jummai da mungun kallo na tsana, Tabbas yau an tozarta mata mahaifiyarta a gabanta, ta ɗauki alƙawarin cewa, insha Allah idan ta kuɓuta daga wannan gidan sai ta nunawa Jummai kuskuren ta.”
Baba kuwa babu abinda yake sai ambaton Allah cikin zuciyarsa, Jummai bata so Umma ta ganta ba, amma sai dai bata jin tsoron hakan domin kuwa ta sani nan da awa uku bakin Umma bazai ƙara Magana a duniya ba, dariya ta sheƙe dashi tare da duban jamo tace.
” A sanja musu wajen zama saboda tsaro.”
Ta ƙarisa Maganar tare da ficewa da kuɗaɗen da Baba ya sai da filin a hanunta wanda Umma kuma ta kawo sai ta bar musu.
Umma kuwa harta iso gida Hawaye ne ke tsere saman fuskarta, babu kowa tsakar gidan hakanne ya bata damar shigewa ba tare da Kowa ya ganta ba, a bakin bed ɗin ta ta zauna tare da sakin kuka mai cin rai wayarta ta ɗaga zata kira DOCTOR domin sanar dashi abinda ke faruwa, jiri ya fara kwasarta komai na ɗakin ya fara koma mata bibbiyu, sake wayar tayi a ƙasa tana zubewa ƙasa itama, tun sanda Umma ta zuɓe ƙasa bata sake sanin ina take ba, ita dai gata nan kamar mahaukaciya kamar kuma macacciya.
Shi kuwa DOCTOR aikin sa kawai yake na tantance ma’aikatan da zasuyi aiki ƙarƙashin sa, ko kaɗan baida masaniyar abinda ke faruwa da ƴan uwan sa, sai misalin biyar na yamma sannan suka tashi tare da sanar dasu cewa, za’a sanar da duk wanda ya samu nasarar aiki da Asibitin ta email address ɗinsa, haka kowa y watse ana farin ciki da raha, bayan fitowar DOCTOR ne ya tari a daidaita, ya shiga tare da ciro wayarsa yana kiran numbern JALILA yaji ko sun dawo switch off yaji, cike da mamaki yace kodai cajinta ya ƙare ne, layin Baba ya kira nan ma switch off, tsuka yaja dai dai lokacin da mai adaidaitan ya sauƙe sa ƙofar gidan nasu, kuɗin sa ya basa sannan ya shiga cikin gidan babu kowa Part ɗin Umma shuru ba kowa falon nata ya shige yana ” Umma Umma” shuru dai still yaji, zama yayi cikin falon yana jiranta may be, ko ta shiga tollet ne, har aka fara kiran magaruba nan shuru, cike da mamaki ya nufi Bedroom ɗinta, mai zai gani Umma ce kwance bakinta sai famar fitar da wani irin kumfa yake, cike da tashin hankali yayi kanta da gudu yana jijjigata tare da kiran sunanta.
” Umma!!! Umma!!! Umma!! Ki tashi Umma meya sameki Umma!!!?”
Shurun da yaji bata Magana sai ido kawai da take zuba masa tamkar bata taɓa ganinsa, fita DOCTOR yayi da gudu ya faɗa ɗakin Hajja yana cewa.
” Hajja!! Hajja!!! Umma na Umma na Hajja!!!”
A tsorace Hajja da AUNTY YANA ke zaune suka miƙe Hajja tana cewa.
” Subabanallah!!! Meya samu YAMURAM ɗin, ka shigo haka a ɗimauce.”
Yana haki yace.
” Tana ɗakin ta Umma zata mutu, kije karta mutu.”
Sosai ya gigice a matsayin sa na likita gabaki ɗaya ƙwaƙwalwar sa ta toshe, Aunty YANA da Hajja da gudu suka nufi sashin Umma, Bedroom ɗinta suka shiga yanda DOCTOR ya barta haka sukazo suka sameta, cike da tashin hankali suma suke jijjigata, Hajja duban sa tayi tace.
” Ka nemo adaidaita muje asibiti.”
Da sauri ya fice, ya dawo da Adaidaitan, shine ya ɗauko Umma a hanunsa ya sata cikin adaidaitan, Hajja da AUNTY YANA suka shiga, shima ya zauna gaban adaidaitan, asibitin Kustin suka nufa, take kuwa aka shige da ita emargency tunda aka shiga da ita cikin tashin hankali suke, Aunty YANA Baba Bukkar ta kira a waya, ba’a juma ba kuwa shima sai gashi ya zo, cikin minti talatin zancen ya karaɗe family, Kawu Dauda da Jummai ma sunzo asibitin Jummai harda kukan munafurci take yi, AJIRAM da Fanna Harda Hajjo duk sunzo su, suna tsaye suna jiran fitowar likitocin, sunan tsaye Falmata da Ladiyo suma sukazo cikin tashin hankali, kusan awan likitocin uku suka fito duk sun haɗa gumi, cikin tashin hankali sukayi kansa suna tambaya.
” DOCTOR ya jikin nata, ta farfaɗo DOCTOR.”
Likitan cike da sanyin jiki yace.
” I am sorry to say, gaskiya, duk wani binciken da zamuyi munyi sa, lafiyar ta ƙalau bamuga wani abinda ke damunta ba, bare musan wani irin magani zamu mata, gaskiya wannan lamarin ya ruɗa mu sosai, shawara ɗaya zan baku kuje ku nema mata maganin gargajiya na gida, ciwon ta bana asibiti bane.”
Cike da tashin hankali kowa ke kallon kowa Tabbas kowa yana cikin tashin hankali, amma shi DOCTOR HASSAN cikin zuciyarsa bai yadda ba, a daren sanda sukaje asibiti biyar duk amsa ɗaya ake basu su dawo suyi na gida, haka dole suka haƙura suka komo gida, hankalin su bai ƙara tashi ba, sai da sukaji su Baba da Aunty JALILA Basu dawo ba sannan duk layin su a kashe, cikin matsanancin tashin hankali suka kwana hatta Falmata a gidan ta kwana washe gari da safe Baba Bukkar yace DOCTOR ya tafi yaje gamborin gala ya dubo su Baba shi kuma zasu kai Umma wajen wani mai magani.
Haka kuwa akayi suka tafi da Umma shi kuma ya tafi neman su ba, mutumin daya sayi filin ne ya tabbatar masa da cewa Tabbas sunzo har sun sai da musu da filin sun juya gida, cike da matsanaciyar tashin hankali HASSAN ya dawo ya samu su Umma ma sun dawo.
Kusan kwana Biyar jikin Umma babu wani sauƙi sai ma wani irin abu take kamar mai ciwon hauka, ga su Baba anyi neman duniyar nan babu labarin su, DOCTOR da AJIRAM sosai sukayi kuka har suka godewa Allah duk wani mai magani da sukaji sai sun kai Umma babu wani sauƙi, hakanne yasa DOCTOR samun malam sani yake zuwa kullum yake mawa Umma addu’a sannan yake musu roƙon Allah ya bayyana musu Baba da Aunty JALILA, kawu Dauda KULLUM yana gidan Hanyar duba Umma bazaka taɓa tunanin cewa yana da hanu cikin tashin hankali su ba, AUNTY YANA da AJIRAM kusan kullum suke yiwa Umma, ta dawo tamkar yarinya komai sai an mata, bata taɓa ƙyamar Umma ba Aunty YANA harta tsarki take yiwa Umma da hanunta.
Yau da sassafe DOCTOR yana kwance ya saka kansa a cinyar Falmata, kana kallon fuskarsa zaka tabbatar da cewa yana cikin damuwa cike da tausayin halin da yake ciki Falmata tace.
” Mijina dan Allah ka daina saka kanka cikin damuwa, ka cigaba da yi musu addu’a insha Allah Umma zata sami lafiya, Baba kuma Allah zai bayyana su.”
” Hankali na bazai taɓa kwanciya har sai Allah ya bayyana min su Aunty Jalila Naga Umma na ta sami lafiya, hakan shine kawai kwanciyar hankali na.”
” Amma damuwar zata iya sa maka ciwo ai, ni dai da zakaji shawari na, daka rage yawan Damuwar.”
Kafin ya bata amsa Saif ya shigo da Sallama Falmata ce ta amsa, zama yayi yana fuskantar DOCTOR yace.
” Naga alamar kamar ka jingine komai a rayuwarka saboda ƙaddara ta faɗa maka, wannan ba shi bane halin Mumini na ƙwarai yakan karɓi ƙaddara a duk yanda tazo masa, duk yanda zaka damu bazaka taɓa sanja ƙaddara ba, haka kuma bazaka iya bawa Umma lafiya ba, ko ka dawo da su AUNTY JALILA, jiya munyi walimar buɗe asibitin ka ba tare da izinin ka ba, saboda nasan ba lallai ka yadda ayi walimar ba, zaka iya cewa ka dakatar komai harsai Umma ta sami lafiya, on Monday za’a fara aiki office ɗinka na jiran ka, idan ma baka zoba zamu fara aiki mukam, daga gidan ku nake yanzu Aunty AJIRAM tace kazo yanzu Fanna tana kwance ba lafiya.”
A matuƙar razane ya miƙe tare da cewa.
” Itama still innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un allahumma ajirni fil musibati!!!”
Ya furta tare da ficewa da sauri, Saif tashi yayi yabi bayan sa, Falmata cike da tashin hankali itama ta haura ta ɗauki hijabin ta, tabi bayan su.
Shigarsa da sauri yayi kan Fanna dake kwance tana muƙurƙuso sai wani irin gurnanin aljanu take, hanu Aunty YANA tasa zata ɗago ta, ta bige hanunta da karfi tana cewa.
” Karki yadda ki taɓani munafuka, ba kune keda Baba Bukkar ba kuka yiwa Umma asiri ba, ta kwanta jinya kuka ɓatar dasu Baba SABODA kawai Baba Bukkar ya yi sarauta, sune suka musu asiri sune sune.!!!”
Da ƙarfi cike da wani irin murya mai amon gaske take wannan maganar idanunta duk sun jujjuya, gabaki ɗaya waɗanda suke wajen mai da dubansu sukayi ga Aunty YANA da Baba Bukkar, suma cike da mamaki tare da tashin hankali suke bin Fanna da kallo, DOCTOR gagara magana yayi, har MLM SANI ya iso ya fara yiwa Fanna ruƙiyya, still dai abu ɗaya take faɗa, da ƙyar suka samu aljanun suka bar jikinta, DOCTOR cike da tsana yake nufo Baba Bukkar, ya shaƙo wuyan sa idanunsa sunyi jajur yana cewa.
” Saboda banzar sarauta zaku hallaka min iyayena, meye Baba bai maka ba a duniya, yau Babu mai hana ban kashe ka ba a cikin gidan nan.”
Sosai Baba Bukkar yake neman fita a hayyacin sa sakamakon shaƙar da DOCTOR ya masa Saif da Kawu Dauda da ƙyar suka kwace Baba a hanunsa, nuna sa yayi da yatsa yace.
” Na tsaneku na tsaneku dakai da dukkan wani abu daya fito daga jikinka, kuma wallahi kayi gaggawar fito min da mahaifina da ƴar uwata, sannan kuje ku karya asirin da kukayi, idan ba haka ba bazan taɓa barin kuba sai na zamo barazana ga rayuwarku, baƙin macuci azzalumi wallahi Abubakar na tsaneka.”
Wani irin kuka mai sauti Falmata ta saki cike da tashin hankali, Baba Bukkar gagara magana yayi, kawai yana kallon su, shi kuma yaushe yayiwa ɗan uwan sa asiri, son zuciyarsa bai kai haka Hawaye ne ya zubo daga idanunsa, MLM SANI gyaran murya yayi yana cewa.
” Subabanallah!!! Haba Hassan yada hankalin ka, kake wannan irin jahilci, yanzu kai sai ka yadda da maganar aljani maƙaryaci, suna irin haka domin su haɗa, karkayi hukunci ba tare daka tabbatar ba.”
Tsuka kawai yaja tare da ficewa cikin ɓacin rai da tsanar Aunty YANA da Baba Bukkar, shi dai kam ya yadda da Maganar Fanna, Falmata kuka take sosai tare da shiga cikin ruɗani da gudu itama ta juya ta fice.
A hankali ta shigo cikin falon nata, yana zaune ya haɗa kai da gwiwwa, kusa dashi ta zauna tare da dafa ƙafar sa tace.
” DOCTOR.”
Bata kai ƙarshe ba ya hankaɗa ta da ƙarfi yana nunata da yatsa.
” Karki ƙara taɓa jikina, na tsaneki kamar yadda na tsani azzaluman iyayen ki, karki kuskura ki ƙara shiga cikin harkata a cikin gidan nan.”
Cike da tashin hankali Falmata ta ce.
” Meyasa zaka hukuntani da laifin iyayena meyasa.”
Tsuka yaja ba tare daya kulata ba, ya tashi yabar wajen, Falmata ƙasa ta sulale tana sakin kuka mai cin rai.
Wannan shine mussababin tsanar da DOCTOR ke yiwa Falmata da iyayenta, har na tsawon shekara guda, a cikin wannan halin Hajja ta bada umarnin a naɗa Baba Bukkar SARAUTA duk da itama tana cikin ruɗanin shin da gaske ya aikata abinda ake zargin sa dashi, yayin da Umma kuma sukaci gaba da nema mata magani amma har yau babu wani sauƙi haka kuma su Baba ma babu labarin su, a haka DOCTOR ya CIGABA da zuwa asibitin sa, a cikin wannan shekarar Allah ya ɗaukaka asibitin, sosai asibitin ke kawo masa kuɗi, harya sayi mota biyu, yana Kuma cigaba da nemawa Umma MAGANI.
Wannan shine dalilin gabar.
Mu tara daku gobe domin komawa Cikin labari.
Ki biya kuɗin ki kafin ki karanta karki karanta min LITTAFI baki biya kuɗin ki ba ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki.
08147537180.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(UMMU NASMAH Ce)*
[10/15, 10:12 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 92 to 93*
*Mu koma labari yanzu aka fara kafcen masoyana DOCTOR HASSAN FAN’S ina ƙaunar ku irin sosai ɗin nan⛹🏽♀️⛹🏽♀️*
_______✍🏻 Yau Falmata sassafe ta tashi tayi duk wani aikin da zata yiwa AUNTY YANA, har breakfast itace tayi, sannan tayi wanka kasancewar ƙarfe takwas take da lecture’s, breakfast ɗinta Tayi sannan ta shiga ta gaishe da Aunty YANA da Baba Bukkar ɗakin Hajja ta shiga tare da zama kusa da Hajja tana cewa.
” Ina kwana Hajja.”
Da lafiya Hajja ta amsa tana duban Falmata cike da tsokana tace.
” Wanka haka da sassafe ko dai har kin fara samo mana jawarawan ne, tun kafin ki gama idda, harda wani shafa man leɓe, lallai zawarcinki akwai kallo.”
Murmushi kawai Falmata tayi tace.
” Kai Hajja sai kace wacce naci uban kwalliya, to maida gulmar ki, ni makaranta zani, kuɗi ma nake so a wajen ki Hajja, dubu Uku ina son zan sayi handout, sannan akwai ƙaramar buƙatar da nake so zanyi da dubu ɗaya.”
Dariya Hajja tayi tana tashi ta nufi Uwar ɗakar ta, tare da cewa.
” Bari na duba miki, ai ba’a rasa nono a ruga.”
Kaɗa Kanta Falmata tayi alamun to, Hajja bata juma ba, ta fito hanunta riƙe da kuɗin ta miƙawa Falmata tana cewa.
” To Allah ya tsare a dawo lafiya, ga wannan ɗari biyu idan kin dawo ki tsaya wajen saminu ki saya min gwarango da goro sai ki dawo min dashi.”
Amsa Falmata tayi tare da ficewa, a tsakar gida ta tarar da temple ɗin matan gidan cike, gaishe su tayi ba tare da ta tsaya ba ta fice abinta kasancewar bata cika shiga harkar su ba, a ƙofar gidan su Maji suka ci karo da ita ta fito, cike da murmushi Maji tace.
” Tab bana ka taɓa ƙawata kinyi abin kirki kin fito da wuri baki samu mun kusa makaraba, muje kinsan yau lectures ɗin mutumin kine dr Ahmad, karya rigamu shiga ya hanu shiga.”
Taɓe bakinta Falmata tayi tana cewa.
” Muje ni lectures ɗinsa baya ɗaga min hankali, domin kuwa haushin sa nake ji, na tsani mutumin daya cika kallon mata mtsss dan Allah ki daina min zancen sa.”
” Hmmm ke Kuma daman Falmata, zancen wani NAMIJI kike so, idan ba na wannan ɗan iskan maha’incin tsohon mijin naki marar gaskiya da rashin riƙon Amana ba.”
Falmata bata tankawa Maji ba domin kuwa taga alamun neman magana take, sai ma gaba da tayi ta barta tsaye, ƴar dariya Maji tayi sannan tabi bayan ta, suka tsaya bakin titi jiran adaidaita sahu, baƙar mota ne ta tsaya a gabansu tasha tintak glass, Falmata cike da masifa tace.
” Mtsss kai kiji wani shiga haƙƙin ɗan adam, haka kawai kayi parking a gaban mutane suna tsaye.”
Ta ƙarisa Maganar tana ƙoƙarin matsawa daga wajen bata yi taku biyu ba HABEEB ya zuge Glass ɗin motar yace.
” Assalamu alaikum Amincin Allah ya tabbata a gareki Falmata sa’ar mata.”
Jin muryar sa yasa Falmata ko juyowa bata yiba ta matsa gefe a binta, Maji ne tace.
” Malam HABEEB dama kaine ka tsaya bamu ganeka ba, ya aiki.”
Murmushi HABEEB ya saki yana kallon Falmata ya cewa Maji.
” Nine WALLAHI tare kuke kenan, ƙawarki kamar wacce take jin haushi na, bansan laifin dana mata ba, Ni kuwa gashi Allah ya ɗaura min jarabawar sonta.”
Murmushi Maji tayi tace.
” Babu wani laifi daka mata kasan halin mutumiyar juju gareta, kuma tana ganin bata gama iddaba, bazata saurari kowa ba, karka damu.”
Numfashi HABEEB ya saki tare da furta.
” Well, ina zaku ne da sassafe haka.”
” School zamu je.”
Falmata ta basa amsa.
” Okay ku shigo na rage muku hanya ko tunda ta hanyar school ɗin naku zan shige.”
” Okay to bari nayiwa mutumiyar Magana.”
Ta ƙarisa Maganar tana nufar Falmata, tsayawa tayi gabanta tace.
” Kizo muje HABEEB ya sauƙe mu.”
Harara Falmata ta jefawa Maji tace.
” Saboda bamu da kuɗin mota ko? To bazan shiga motar sa ba, sai ki dakata mu tari a daidaita ko, mu wuce tunda dama bashi ke kaimu ba?”
” Haba Falmata haba dan Allah, wannan ai bai kyautu ba, ya za’ayi mutum da mutuncin sa, ya tsaya ya miki magana kiƙi kulasa, sannan yanzu yace ya rage mana hanya kinƙi, anya kuwa kin masa adalci, dan Allah kizo muje ya sauƙe mu.”
Kunkuminta Falmata ta riƙe tana taɓe fuska.
” Innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un!!! To meye haɗina dashi da har dole sai na masa adalci, baƙar Magana na faɗa masa, ko zaginsa nayi, ko ance dole sai na sauraresa? Nifa ba yarinya bace, ki daina tilasta ni dan Allah, motar sa ne nace bazan hauba, ko ana dole ne, dan Allah ki ƙyale ni.”
” Bazan ƙyaleki ba Falmata dole na faɗa miki gaskiya, Please kizo muje mu shiga dan Allah ya KAIMU.”
” Wallahi Maji bazan shiga motar sa ba, yau kam, kinji na ratse, idan zaki hau kije ki hau ban hanaki ba, zamu haɗu a makaranta, amma ni dai bazan hau ba, ki daina ƙoƙarin haɗani da wani NAMIJI domin kuwa akwai idda a kaina kinsan kuma hakan haramun ne.”
Shuru Maji tayi cikin damuwa ta dawo wajen HABEEB tace masa.
” Dan Allah HABEEB kayi hkr wallahi taƙi yadda muzo mu hau, tace akwai idda a kanta I am sorry kaje kawai.”
Ɗan murmushi mai ciwo HABEEB yayi tare da kaɗa kansa yace.
” Ba damuwa na gode Maji, hanu yasa cikin aljihun sa ya zaro dubu goma ya bata yace, ga wannan kuyi adaidaita.”
Maji jikinta a sanyaye ta karɓi kuɗin sannan HABEEB yaja motar sa ya bar wajen su kuma suka tare adaidaita Maji tsabar haushi bata kula Falmata ba, har suka isa cikin makaranta, sunci Sa’a kuwa Malam Ahmad bai shiga ba, Kusan takwas da rabi Malam Umar ya shigo, ya sanar dasu cewa yau Malam Ahmad bazai samu zuwa ba, su jira lectures na gaba sannan ya fita.
” Maji ranta a ɓace ta ciro wayar ta, ta hau game ba tare da ko kalli inda Falmata take ba, domin kuwa yau haushin ta take ji, Falmata ganin yanda Maji ta haɗa fuska ya sata cewa.
” Maji wai me yake faruwa ne kam naga ranki a ɓace tun muna cikin nafef na fahimci hakan.?”
Maji bata ɗaga kai ba tace.
” Idonki ne kawai yake ganin haka, kuma ai kinsan ba ko yaushe mutum yake cikin nishaɗi ba.”
” A’a Maji ba haka muka fito ba, fa daga gida kina cikin sakin fuska muka fito tun haɗuwar mu, da HABEEB naga yanayin ki ya sauya, ko dai kina jin haushi nane akan HABEEB.”
Murmushi Maji ta saki tare da ɗago kai ta kalli Falmata tace.
” Saboda me zanji haushin ki, akan HABEEB?”
” Saboda na nuna bana sonsa, ina tunanin hakan ne ya sa fuskarki ta sauya.”
Murmushi Maji tayi tare da Girgiza kanta tace.
” Hmmm!!! To meyasa zanji haushi bayan bani da ikon tursasa makauniyar zuciyarki taso wanda bata so, ke dai kawai tsarguwa kikayi, ni yanzu na sanya miki ido ne, kije kibi Umarnin zuciyarki tunda har yanzu kin kasa yin hankali bana tunanin zakiyi hankali koda nan gaba dan haka kije kiyi abinda kikaga yafi miki sauƙi a rayuwarki tsakanina dake ido koda shawarace na daina baki, kije ki cigaba da son wanda baya ganin mutuncin ki, tunda zurki marar lissafi ne da tunani.”
Falmata cike da raunin murya tace.
” Har kullum baki fuskanta ta, kin kasa gane cewa laifin zuciyata ne, ba laifi na ba, ita DOCTOR kawai shine wanda take sannan bata tunanin zata iya haɗa Soyayyar sa dana wani, ki fahimce ni bazan iya Soyayya da wani NAMIJI ba, ba’a iya tilastawa zuciya taso abinda bata so.”
Murmushi Maji tayi ta bata amsa da cewa.
” Hmmm!!! Ki daina ɗaurawa zuciyarki abinda ba laifinta ba, domin kuwa ana tilastawa zuciya taso abinda yake alkairi a gare ta, abinda ba alkairi ba kuma dole ta haƙura dashi tabi abinda yafi alkairi a wajen ka, Allah da kansa acikin littafin sa mai tsarki cikin suratul Baqara yake cewa : kutiba alaikumul ƙitalu wa huwa kurhun lakum, wa asa antakrahu shai’an wa huwa kairun lakum, wa asa an tuhibbu shai’an wahuwa sharrun lakum, wallahu ya’alamu wa antum la ta’alamun : an wajabta yaƙi a kanku, gashi kuwa kuna ƙinsa, sau da yawa kukan ƙi wani abu, alhaki kuwa shi alkairi ne a gareku, sau da yawa kuma kukan so abu, alhali kuwa shi sharri ne a gareku, Allah yasan abinda ku baku sani ba.
Misalin Soyayyar da kike yiwa Hassan, wanda babu alkairi a cikin sa, Falmata, duk Soyayyar da akace an ginata bisa ga turbar da iyaye basa so, to wannan Soyayyar dole sai ta samu nakasu a tare da ita, dalili kuwa shine kin saɓawa iyayenki, saɓawa iyaye kuwa babban laifi ne mai girma a wajen Ubangiji, na Tabbata da tun farko da iyayenki suka baki umarnin ki rabu da Hassan, da kin musu biyayya da yanzu bakya cikin wannan mawuyacin halin da kike ciki, abinda Babba ya hango yaro ko ya hau tsauni bazai taɓa hangowa ba, gashi yanzu kin fara ganin raahin bin umarnin iyaye, meyasa bazaki haƙura da. Hassan ba, ki jira alkairin ki, domin kuwa na lura sam babu alkairi tsakanin ki da wannan ɗan tashan wanda baisan darajar manya ba, ki farka daga nannauyan baccin da kike Falmata, ki rabu da wannan ɗan tashan, ki daina tunani da zuciyarki kiyi tunani da ƙwaƙwalwar ki, domin itace kawai zata faɗa miki gaskiya, ita Zuciyarki bazata taɓa gaya miki gaskiya ba, ko yaushe nuni zata miki da abinda tafi ƙawatuwa dashi, musamman irin taki zuciyar da take makahuwa wacce babu abinda take gani, sai Soyayyar mutumin da bai dace da rayuwarki ba ki lissafa da hankalin ki, ki gani, nasan lissafin ki zai sanar dake zuciyarki kaiki take ta baroki inda fitowa take miki wahala.?”
” Ban san ya zan fahimtar dake irin son da nake yiwa DOCTOR ba, rabani dashi wallahi rabani da rayuwata ne, bazan iya ciresa a raina ba, Saboda ba nine na halittawa zuciyata Soyayyar sa ba, kiyiwa Soyayya adalci Maji ki daina alaƙanta ta da tilastawa, domin kuwa ita ba’a iya tilasta mata Soyayya ciro ce daga Ubangiji wanda babu wani mahaluƙin da zai iya tuge wannan tsiron sai ubangin daya dasa shi, ki sani muddun zuciyata tana bugawa da soyayyar DOCTOR, ƙwaƙwalwa ta, bazata taɓa tunani ba, domin kuwa zuciyata ta toshe duk wani hanyar tunanin ta, babu abinda take nuna mata sai Soyayyar DOCTOR, haka zalika, bani da wani lissafi idan ba nasa ba, ina lissafa rayuwata dashi, dan haka zuciyata tayi nisan da bazaki taɓa sauya mata ra’ayin ta ba, Maji ina cikin tsoro da fargaba domin kuwa na yiwa iyayena alƙawarin da bazan iya cika musu ba, tausayin Mama yasa na ɗauki wannan alƙawarin, yanzu ya zanyi bazan iya cika musu alƙawarin dana ɗauka ba.”
Ta ƙarisa Maganar muryar ta, tamkar za tayi kuka.
Bakinta Maji ta cije cike da tausayin Falmata, ita tsoron ta, kar Soyayyar Hassan yasa ta haukace, domin abubuwan da take yi kama da yanayin kalamanta akansa ya fara mata kama da irin na mahaukata juyowa tayi tace.
” Tabbas kin fara fita cikin hayyacin ki, Soyayyar Hassan tana neman tarwatsa miki Rayuwa, bansan taya zan iya ceto rayuwar ki ba, daga ƙubuta daga sharrin wannan azzalumi Hassan, duk wata hanyar daya kamata nabi domin ceto ki nabi Amma bakya barina harna ɓulle sai kin datse Ni, kina iya karyawa iyayenki alƙawarin da kika musu, domin kuwa riƙarki takai wannan, kina iya yin duk abinda kikaga daidaine a rayuwarki ni kuwa zan samiki ido bazan ƙara baki wata shawara ba, domin kuwa koda na baki bata miki amfani.”
Zaro ido waje Falmata tayi, cikin damuwa da kuma jin rashin daɗin kalaman ƙawarta tace.
” Na saɓawa alƙawarin su fa kikace Maji, taya zan saɓa musu bayan nasan hakan babbar matsala ce a gareni, Alƙawari abune mai girman gaske, kinsan alƙawarin dana musu kuwa, ki daina min kallon mahaukaciya mana wallahi da hankali na, idan ban faɗa miki damuwata ba waye zan faɗawa, kece wacce nake iya kawowa matsalata sannan ki kawo min mafita ba tare da kowa ya sani ba, bani da ƴar uwa mace, kece nake ɗauka a matsayin ƴar uwata wacce muka fito ciki ɗaya, sannan kice karna kuma kawo miki damuwata, koda bazaki saurareni ba, ni zan faɗa miki Matsala ta hmmm.”
” Ƙarya kike Falmata baki ɗauke ni matsayin wacce kike ɗaukar shawarin ta ba, domin kuwa da hakane da yanzu kin rabu da wannan ɗan tashan Hassan kin gina Sabuwar rayuwa mai cike da jin daɗi, amma ke zuciyarki wahala take hango miki a matsayin jin daɗi nasan alƙawarin da kika ɗaukarwa Mama bazai wuce na kin rabu da Hassan bane, nasan ko nace ki saɓa musu ko karki saɓa musu, a ƙarshen dai dole saɓa musu zakiyi, saboda hankalinki ya riga ya daɗe da barin gangar jikinki da zuciya kawai kike amfani, na riga na gama sauraronki, zanje nayi breakfast Maganar wannan ɗan iskan azzalumin ya isheni haka.”
MAJI ta ƙarisa Maganar tare da tashi tana ɗaukar bag ɗin ta ta fice tabar Falmata cike da jin haushin ta.
Ajiyar zuciya Falmata ta sauƙe cike da damuwa, ta rasa meyasa kowa ya tsani DOCTOR babu mai sonsa kowa aibunsa yake faɗa, yayin da ita kuma bata ganin wannan aibun nasa, ƙwafa kawai tayi tare da tashi tabi bayan Falmata, a kaftariya ta sameta har an kawo mata indomie, zama Falmata tayi ba tare da tacewa Maji komai ba, haka itama Maji bata kulata ba.
Wunin ranar haka sukayi shi a makarantar babu walwala domin kuwa Maji yanzu ta fara jin haushin Falmata akan Hassan.
****************
*BINISHED*
Yau tunda safe DOCTOR ya shirya zai dawo cikin gari, Aunty Hajjo dake zaune kusa da Umma ya duba tare da cewa.
” Aunty ni zan koma cikin gari saboda nasan akwai aiki SOSAI a asibiti yana jira na, so bazan dawo ba sai jibi, ki kula da Umma sosai, sannan ki kula da maganinta, ga wannan 20k ne may be zaku nemi wani abun.”
Karɓa Hajjo tayi tace.
” Shikenan Allah ya kaika lafiya insha Allah zan kula da Umma kuma zata samu lafiya da yardar Allah, ka gaishe da gida.”
Da zasuji DOCTOR ya amsa tare da sunkuyawa ya yiwa Umma addu’a sannan ya fice, a ƙofar gida ya samu Malam Gana yana zaune cikin ɗaliban sa, gefe kaɗan dashi ya zauna cikin girmamawa ya gaishe da Malam tare da cewa.
” Malam ina son zan koma gida yanzu, saboda akwai aiki dayawa cikin asibiti na, Malam ganan Umma a wajenka, duk abinda ake buƙata a mata shi, fatana Allah ya bata lafiya.”
Nisawa Malam yayi cike da kulawa yace masa.
” ya kamata ka koma kan aikinka insha Allah mahaifiyarka zata samu lafiya, ka dage da addu’a muma muna nan muna magani tare da haɗawa da addu’a Allah ya maka Albarka, motar haya kenan zaka hau naga Muhammad Bello ya tafi da motar da kuka zo da ita.”
” Eh Malam Motar haya zan hau bari na tashi na tafi kar Rana ya min malam ga wannan dubu hamsin ne, zaka rage cefenen gida dashi.”
” Gaskiya ne Allah ya kaika lafiya, amma wannan kuɗin ka barsu na gode.”
” Malam daka karɓa, bazanji daɗi ba idan har ka dawo min da kyautar dana maka.”
Murmushin manya Malam ya saki tare da amsa yana saka masa albarka, tashi DOCTOR yayi tare da tafiya yayi nisa da tafiya yaji an doki kafaɗarsa da ƙarfi, a matuƙar har zuƙe ya ɗago idanunsa.
” Kayi haƙuri dan………”
Haɗa idanun da sukayi ya hanata ƙarasawa sai ma haɗa fuska da tayi tamau, ganinsa tsuka taja tare da ƙoƙarin shigewa tana jefa masa kallon banza, cikin tsanarta da jin haushin ta, yasa hanu ya fisgota da ƙarfi ya dawo da ita baya yana cewa.
” Jakar ina ne ke wawiya, mahaukaciya ce ke, da zaki bigeni, kin ɗebo gudu tamkar wata dabba wawiya.”
Runtse idanunta Ai’sa tayi tana jin zafin maganarsa muddun ta barsa ya cuceta wallahi cikin tsiwa da rashin kunya tace.
” Ba’a jaka ɗaya sai biyu, kenan kaima jakinne, akwai ma wani wawan daya wuceka ne da zaka tsaya kana sa’insa da ƙanwar bayan ka, kuma wallahi daga yau karka kuskura ka ƙara cemin mahaukaciya domin kuwa na fika hankali, aikin banza Mtsss.”
Ta ƙarisa Maganar tana jan tsaki, tare da juyawa tabar wajen tana jan tsaki, gagara tanka mata DOCTOR yayi tunda yake a rayuwarsa babu yarinyar data taɓa masa abinda wannan yarinyar take masa, sosai RANSA ya ɓaci idanunsa har ja sukayi, amma kuma ya ɗauki alwashin cewa sai ya koya mata hankali duk randa suka kuma haɗuwa dashi sai tayi danasanin saninsa a rayuwarta………………..”
Ki biya kuɗin ki kafin ki karanta karki karanta min LITTAFI baki biyu ba, ki nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
*Alƙalamin Rasheedat Usman*✍🏻
*(UMMU NASMAH Ce)*
[10/16, 10:50 AM] TYPING DOCTOR HASSAN💊💊💊: *DR HSN 94 to 95*
MASOYANA na gode sosai da addu’oin ku gareni, jiki Alhamdulillah da sauƙi.
___________✍🏻 Cike da haushin AI’SA DOCTOR ya fita wajen garin, ya hau motar da zata kaisa cikin Mai Duguri, ƙarfe 12 na rana ya shigo, cikin gidan sa ya nufa, a ƙofar gidan ya tsaya tare da ƙwanƙwasa ƙofar, Musa mai gadi ne ya leƙo tare da buɗewa da sauri yana cewa.
” Barka da dawowa Oga.”
” Yauwa Musa barka, ya fama da gida.”
” Gani nan dai Oga ina ta zaune cikin kaɗaici ko abinci yanzu sai na fita na saya, ada kuma sai dai kawai Madam tasa a kawo min, zaman gidan babu daɗi Oga dan Allah a taimaka a dawo mana da Madam.”
Numfashi DOCTOR ya sauƙe, yana jin wani zafi a zuciyarsa jin Musa ya ambaci sunan Falmata a cikin kwana biyun shima kansa yakan yawaita tunaninta sai dai tsanar da yayiwa iyayenta bazai bari ya ƙara sauraranta ba, numfashi kawai ya sauƙe ba tare daya juyo ya kalli Musa mai gadi ba, ya shige cikin part ɗinsa, Girgiza kansa Musa yayi cike da tausayin ogan nasa, falon duk ƙura ba Kamar yanda ya saba shigowa ya samesa tas cikin ƙamshi da tsafta ba, sanda Falmata take cikin gidan sosai ransa ya ɓaci domin kuwa a rayuwarsa ya tsani ƙazanta, babu yanda ya iya dole tasa ya shige Bedroom ɗinsa nan ma dai ƙuran ya samu, tsuka yaja ba tare daya huta ba ya hau gyara Bedroom ɗin, bayan ya gama ne ya dawo falon nan ma ya gyara, amma duk da haka baiga ya masa tas kamar na Falmata ba, a matuƙar gajiye ya shige Bedroom ɗinsa tollet ya faɗa yayi wanka tare da dawowa ya ɗauki wayarsa ya kira SAIF akan ya sayo masa abinci a restaurant ya kawo masa yana gidan sa, kashe wayar yayi three cutter da best yasa sannan ya faɗa saman bed ɗinsa a matuƙar gajiye bai juma ba kuwa bacci ya ɗauke sa.
Saif bai shigo gidan ba sai wajen 2:30 ya tabbatar da mutumin ya tashi daga bacci, tun a falon shima SAIF ya fara ganin sauyin rashin mace cikin, cikin zuciyarsa ya furta “Tabbas Hassan yayi rashin mace mai tsafta” Bedroom ɗin DOCTOR ya shiga, shimfiɗar bed ɗin kawai ya kalla ya sheƙe da dariya, shimfiɗan duk yayi kwana kwana , cikin rashin fahimta DOCTOR yake kallon sa, cike da fara jin haushin dariyar da baisan tame bane yace.
” Kai Malam dariyar uban me kake yi.?”
Still dai Saif yana dariyar ya zauna tare da nuna masa bed ɗin, yace.
” Haba malam DOCTOR ka duba ka ga wannan shimfiɗar ta ƴan daudu da kayi, wallahi rashin mace ma dai baiyi ba, wai mutumin da yake zuwa ya samu abinci Iri iri a cikin gidan sa saiya zaɓi wanda yake so, wai yau shine da cin abincin kasuwa, kaɗan ma ka fara gani.”
Tsuka DOCTOR yaja tare da cewa.
” Mtsss aikin banza, dama wannan ƙaramin abun kake yiwa dariya, dake kai abin dariya baya baka wuya, a gajiye nake shiyasa nayi shimfiɗar gadon haka, abincin kasuwa kuma kaima aishi kake ci meya hanaka Auren kai a girka maka, ai dai gara ni na kwatanta Auren ko, kai fa da har yanzu ka gagara fitar da mace ɗaya, Saif shifa mai bunu a gindi baya kwalalar gobara dallah bani abinci na.”
Ya ƙarisa Maganar tare da wafcar ledar a hanunsa, bakin sa SAIF ya taɓe ba tare daya furta komai ba, sai ma kwanciyar sa da yayi, sai da DOCTOR ya gama cin abincin sannan yaji muryar Saif yana cewa.
” Idan ka huta ka shirya zamuje wajen Falmata.”
” Falmata kuma”? DOCTOR ya furta cikin zuciyarsa sannan ya juya yana kallon SAIF yace.
” Muje mu mata uban meye.”
Tashi Saif yayi ya zauna, yana fuskantar DOCTOR cike da nutsuwa yace.
” So nake muje ka bata haƙuri, sannan ka maida Auren ku, Saboda ka mata laifi ya kamata zuwa yanzu ka fahimci kuskuren ka, ina jiye maka tsoron kaƙi maida Auren ku da Falmata, har ta gama idda, wallahi ka yarda ta gama idda baka dawo da ita ba, to Wallahi zaka rasata domin kuwa kasan akwai masu harinta, bana son kayiwa kanka asarar mace ta gari, samun mace irin Falmata abune da yake matuƙar wahala a yanzu, ya kamata kayi tunani da kyau ka manta abinda ya faru tsakanin ku da iyayenta, domin kuwa ita bata da laifi, har abada bazan daina faɗa maka gaskiya akan Falmata ba a matsayina na abokin ka.”
Wani mungun kallo DOCTOR ya jefawa Saif tare da cewa.
” Kaga SAIF na ce maka ka daina ɗago min zancen Falmata, domin kuwa ba ita bace a gabana, nasha faɗa maka cewa nida Falmata har abada bazamu sake zaman Aure ba, iyayenta sun haramta hakan a garemu, bana son muke yawan maimaita Magana guda ɗaya da kai, ni yanzu haka daka ganni jira nake jikin Umma ya ɗan samu sauƙi, zan maka Baba Bukkar a kotu, ya fito min da mahaifina, Falmata kuwa a yanzu ko ɗaura min ita akayi a wuya zan yageta da ƙarfi na yasar, tunda can ma ƙaddara yasa na Aure ta, amma ai ni ba ajint………….”
” Dakata dallah malam, wannan maganar banza kake yi, kotu fa kace, yanzu kai sai ka iya zuwa ka tsaya da baffan ka ƙanin mahaifinka a kotu, wannan ma ai abun kunya ne, da tonawa halin da gidan ku yake asiri, wallahi karka kuskura ka fara duk rashin hankalin zuciyarka, Falmata kuwa insha Allah daga yau na daina maka zancen ta, amma ka sani duk abinda ya biyo baya ina so ka tuna da kalamaina koda kuwa na mutu, domin ina da tabbacin sai kayi danasanin wannan cin amanar daka mata, ko Allah ma baya kama wani da laifin wani, sai kai ɗan adam, zaka mata hukunci akan abinda bata da hanu a cikin sa, wallahi kaci amanar soyayya ka zalunci Falmata kuma wallahi Allah sai ya saka mata .”
” Hankali na ras yake a jikina haka kuma zuciyata a cikin nutsuwar ta take, kotu kuwa babu wanda ya isa hanani makasa a cikin ta duk duniyar nan sai ubangin daya halicce Ni, sannan kuma babu abinda zai biyo baya sai alkairi.”
Tsuka SAIF yaja tare da tashi ya fice a fusace, kafaɗarsa DOCTOR ya ɗaga alamun wannan damuwarki ne, tashi yayi ya shirya cikin wandon jeans da farar t-shirt kay ɗin motar sa ya ɗauka tare da nufar family Hause ɗin nasu zaije ya duba ko Fanna tana nan sannan ya gaishe da Hajja, daga nan ya shige gidan Baba Dauda.
Sanda ya fito dubu biyar ya bawa Musa kyauta kafin ya fice, a ƙofar gidan nasu yayi parking tare da fitowa yana sawa motar kay, Baba Bukkar dake zaune ƙofar gidan ne Shida wasu mutane biyu, DOCTOR ya shige yana jefa masa mungun kallo, shi dai Baba Bukkar kau da kansa gefe yayi Tamkar bai gansa ba, gudun karya masa rashin kunya cikin mutane, part ɗin Umma ya fara shiga shuru ɗakin Umma a rufe da alamun babu kowa, cikin zuciyarsa ya furta may be gidan AJIRAM take, fitowa yayi ya faɗa part ɗin Hajja, kusan karo suka kusa ci da Aunty YANA amma tsabar tantiranci da bariki irin na DOCTOR bai matsa mata ba, sai itace ta kauce masa, Maji runtse idanunta tayi cikin tsana da jin haushin DOCTOR, Falmata dama ta shiga tollet, Bedroom ɗin Hajja ya nufa, Aunty YANA ta kaɗa kanta cike da takaici ta shige abinta, Maji cike da ɓacin rai ta miƙe a fusace tasha gaban DOCTOR dake ƙoƙarin shiga cikin tsantsar ɓacin rai tace masa.
” Marar mutunci marar hankali, wanda baisan mutuncin na gaba dashi ba Butulu, wallahi ko a ƙasar kafurai ban taɓa ganin tantirin marar mutunci irinka ba, idan banda rashin sanin darajar manya, har kaine zaka nemi bige kafaɗar Mama har ka manta sanda take maka rana, kake zuwa ka kwanta akan gadon ta, ka kawo mata damuwarka ta magance maka, amma dake Butulu ne kai harka manta, wallahi Hassan yau da Allah yasa ka bigi Mama, wallahi da yau sai ka kwana a cell, mayaudari maha’inci,.”
Ta ƙarisa Maganar cike da ƙunar rai, ji take tamkar tasa bindiga ta harbesa, ta tsanesa bata son ganinsa a rayuwarta, shima DOCTOR a zuciye ya ɗago hanu zai zabgawa Maji mari tayi saurin riƙe hanunsa tana Girgiza masa kai tare da cewa.
” Fuskata tafi ƙarfin ƙazamin hanu irin Naka mai cike da tarin zunubai ya taɓa fuskata, idan banda zuciyarka ta banza ce, da mace zaka yi faɗa mtsss kana kuskuren saka hanu jikina wallahi sai na ajiye maka mummunan tarifin da bazaka taɓa mantawa daahi ba.”
Hanunsa ya fisge yana ƙoƙarin shaƙota Hajja ta fito da sauri tana cewa.
” Hayaniyar me nake jiyowa ne haka, kun dameni ina sallah.”
Ta ƙarisa Maganar tare da fitowa ta tsaya a gaban Maji, hakanne yasa DOCTOR sauƙe hanunsa ƙasa yana jin zafin Maji bai taɓa jin tsanarta ba sai yau Tabbas da badan Hajjo ta fito ba, wallahi sai ya kusa karyata Maji, yarinyar tayi mungun raina sa, nunasa Maji tayi da hanu tace.
” Gashi gabanki ki tambayesa Rashin ɗa’ar da yayi, wallahi Hajja wannan da badan ansan asalinsa ba, sai ace bai fito daga gidan mutunci da ɗa’a ba, sai dai kash albasa ce batayi halin ruwa ba”
Hanu yasa ya ɗauke Maji da mari zai sake, Hajja tayi saurin riƙe hanunsa tana nuna sa da yatsa tace.
” Bana son shashancin banza, kana da hankali kuwa ubanta ne kai da zaka saka hanu a jikinta, kaji min ɗan banza, to Wallahi karka kuskura ka sake saka hanu a jikinta” juyowa tayi ta dubi Maji da ta riƙe fuskarta tace mata, ” kiyi hkr Maji insha Allah hakan bazai kuma faruwa ba, kije ɗakin yana.”
Cije bakinta Maji tayi cike da ƙunar rai tabar wajen, Hajja kuwa cikin ɓacin rai ta nuna masa hanya.
” Fice min daga cikin gida, bana son na ƙara ganin wannan fuskarta ka, a sashin nan, tunda har abada bazaka taɓa hankali ba.”
” Amma Hajja fa kina ji yarinyar nan Magana take faɗa min munana marar sa daɗi sannan sai nayi shuru ta zageni yarinya ƙarama.”
Cikin faɗa hajja tace.
” A ina naji ta zageka, banji ba, ko ma naji banji ba, domin kuwa duk abinda ta faɗa a kanka gaskiya ne ta faɗa, shige kabar nan.”
” Hajja amma………”
Cikin tsawa mai sauti Hajja tace.
” Ka wuce kabar nan nace maka!!!!!!!!! Idan ba haka ba, zan maka rashin mutunci, ɗan iska marar hankali wanda baisan alkairi ba.”
Tsabar ɓacin rai DOCTOR har wani duhu yake gani, sai yau ya tabbatar da Hajja bata ƙaunar sa, lallai, basu da kowa yanzu cikin gidan nan, juyawa yayi da sauri ya fice, daidai lokacin da Falmata ta fito daga tollet kenan, duk abinda ke faruwa tana sauraronsu, sai dai tafi jin haushin Maji domin kuwa itace tasa Hajja take yiwa DOCTOR ihu a kayi, ina ruwan ta yanzu fa taga alamar Maji tana neman shige mata hanci da ƙudunduno dole ne sai ta taka mata burki, bayan DOCTOR tabi da sauri, a zaure ta iskesa zai fita tayi saurin tare gabansa tana cewa.
” Dan Allah kayi haƙuri da abinda Maji ta maka, banji daɗi ba, kuma insha Allah bazata sake ba, sannan DOCTOR kayi hkr ka maidani ɗakina wallahi ina sonka kaine Rayuwata, ka rufa min asiri ka maidani ɗakina.”
Tayi Maganar cike da raurau ɗin murya, tsuka DOCTOR yaja yana watsawa Falmata kallon banza ya nuna ta da yatsa yace.
” Kauce ki bani waje na shige shashar banza, wai ke mayya ce, ko dole ne sai nayi rayuwa dake, nace bana sonki ko ana dole ne, koda ma dana aureki, tsabar jarabar nacin tsiya ce irin taki da kika kai mari kika kai gauro, kikayi tsayuwar daka har iyayen mu suka liƙa min ke dole, idan banda haka ai kinsan nafi ƙarfin ajinki, kaddara tasa na Auri Irin tsiya irin ki, SHIYASA nake godewa Allah daya sa ban haɗa zuri’a dake ba, sannan ga saƙo ki bawa waɗannan ƴan iskan iyayen naki matsafa cewa su fito min da mahaifi na, idan ba haka ba, wallahi nine ajalinsu.”
Ya ƙarisa Maganar tare da hanƙaɗa ta gefe sanda ta gwaru da jikin kango take kuwa goshin ta ya fashe jini ya fara biyu fuskarta…………….
Tirƙashi wannan wacce irin ƙaddarar Soyayya ce, take bin Falmata, shin waɗannan maganganun da DOCTOR ya faɗa mata zaisa ta zuciya ta haƙura dashi, ko kuwa har yanzu zuciyarta bata karaya da soyayyarsa ba.
shin Falmata zata iya dakatar da Maji daga ɗaukar mataki akan DOCTOR kuwa.
Umma zata sami lafiya harta tona asirin Jummai.
Shin Falmata zata so HABEEB kuwa, ya labarin Wasila tana nan ko kuwa tayi Aure idan har tana nan shin zata bari HABEEB ya Auri Falmata kuwa.
Shin koda DOCTOR ya amince zau dawo da Falmata gidan sa, Anya kuwa iyayenta zasu yarda.
Mu tara daku a cikin BOOK Two, anan na kawo ƙarshen Book One.
Ki biya kuɗin ki ki karanta cikin aminci da a baki labari gara ki bayar, nemeni ta wannan numbern domin sanin yanda zaki biya kuɗin ki 08147537180.
WANNAN BONUS NA BAKU, DOMIN SAMUN COMPLETE KIYI ƘOƘARIN BIYAN KUƊIN KI, DAN ALLAH IDAN BAKI SHIRYA BA, KARKI BIYO NI KI BARI SAI KIN SHIRYA, NA ROƘE KI.
*ALƘALAMIN RASHEEDAT USMAN✍🏻*
*(UMMU NASMAH CE)*