Hausa novels
GANGAR JIKINSA NA AURA
Chapter 11
Wayar ce ta sake yin kara tasa
hannu ta dauka taji
Habib ne. Ya ce “Ina Haisam din?
Ta ce “Ya fice, ya
ce “Ranki ya dade kema har da
laifinki tun rannan
Baba ya kiraki har gida ya ce kiyi
murda-murda
kisa a koreshi daga
makarantarki zai biya ki ko
nawa ne. Kika ce bazai yu ba,
wannan yaron ko
kashe shi za ayi bazai bar
makarantar nan ba.
Wanne irin lallashine ba’ayi
masa a gida ba yaki ya
bar koyarwar, Principal ta nisa
ta ce “Habib tunda
kaji nace bazan iya sawa a kori
Haisam ba to babu
yadda zanyi saboda wannan
makarantar ta gwamnatin
taraiya ce daga can kololuwa
aka dauki
Haisam haka kuma korarsa sai
daga can Abuja.
Dana bincika ma babban
director na federal shine
ya dauke shi aiki Alh. Sabi’u
Auwal abokin
babanku ne ko? To babu kuwa
yadda za ayi na
hada baki dashi a kori Haisam
daga makarantar nan. Habib ya
ce “Zanzo makarantar watakila
nan
da sati biyu, idan na dawo dawo
daga tafiya dole
ne ma ya bar makarantar don
yaga anayi masa
sakwa-sakwa ya dauka tsoronsa
ake yi. Don ni
banga uwar da yake samu ba a
makarantar. A
haka dai suka yi sallama suka
ajiye kan wayoyi.
BAYAN SATI
Ashe ba Sahabi ba kadai akwai
Malamai da yawa da
suke son Hannah, sai yanzu
suka dinga baiyana.
Ranar talata data zagayo Haisam
da sauran Malamai
Uncle Sahabi da Uncle Yusif suna
zaune a gindin
bishiya da prep din yamma sai
Uncle Yusif ya aika wata yarinya
ya ce taje S.S. 1A ta kira masa
Hannah
Abubakar. Haisam na zaune
yana tunanin lafiya
yake kiran Hannah. Hannah ta
karaso tazo ta
durkusa ta gaishe su, Uncle
Yusif bai amsa ba ya ce
“Hannah yau zan nuna miki
karshen taurin kai,
girman kai da ji da kai. Don haka
kije ki karyi bulala katuwa mai
kauri dai-dai tsawanki ki kawo
min.
Haisam na zaune yana kallonsu
Hannah ta tashi
jikinta a sanyaye ta nufi dawa,
can ba da dadewa ta
taho dauke da wata zabgegiyar
bulala. Ta zo ta
durkusa ta mikawa Uncle Yusif
ya ce tayi Kneel
down ta daga hannu ya kuwa
tashi ya fara zabgawa Hannah
wannan reshen. Haisam ya kau
da kai gefe kawai yayi shiru,
Yusif yayi mata bulala
kamar sau takwas sannan ya ce
“Kinsan me kika yi
min? Cikin shesshekar kuka
Hannah ta ce “Ban sani
ba, ya sake daddagewa ya sakar
mata wani dukan,
ya ce “Kin tuna yanzu? Cikin
gigicewa Hannah ta ce “Na tuna,
ya ce “To me kika min? Ta ce
“Jiya daka
aiko kace inzo in sameka a
lambu banzo ba. Ya ce
“Yauwa ashe dai kin gane to yau
sai na lahira ya fiki
jin dadi don kin samu ma ana
sonki, ke din me da
zaki yimin wulakanci? Sahabi ya
tashi ya karbi
reshen nan ya zazzabga mata
sau biyar da karfi kuwa ya ce
“Tashi saura ki ki zuwa nan
gaba idan
muka aika kiranki da prep. Tana
tafe tana rusa
kuka ta tafi ajinsu. Sahabi yana
cewa “Bari muga
zata zo da prep din daren
kuwa? Idan bata zo ba
wallahi double din wannan
zamu yi mata. Haisam
yayi tsaki ya mike ya nufi ajin su
Hannah, zuciyarsa cike da
tsananin bakin ciki da tausayin
Hannah.
Yaje ajin ya tambaya aka ce
Hannah bata shigo ba.
Nan da nan hankalinsa ya sake
tashi yayi waje da
sauri yana dube-duben ko daji
ta tafi ta zauna tana
kuka, yazo wucewa ta ajijuwan
*yan aji shida yaji
nishi kamar wata tana tsallen
kwado ya leka ta wundo da
sauri yaga ashe S.S.3 A sun taru
kusan
dukkanninsu suna azabtar da
Hannah ta jike
sharkab saboda gwale-gwale da
duka. Juwairiyya
ce rike da dorina a hannunta
tana biye da Hannah
tana tsallen kwado tana fyada
mata. A fusace
Haisam ya daka musu tsawa duk
suka waigo wasu suka ruga
ajijuwansu suka zazzauna. Ya
hango
wani masinja ya kirashi ya ce
yaje daji ya karyo
masa manya-manyan reshinan
bishiyar maina ya
kawo masa. Ya zagaya cikin
ajijuwan ya ce
dukkaninsu su firfito waje bai
rage kowa ba duk
S.S3 din. Sun dauka abun da
wasa ne suna tafe suna
rangwada suna tauna cingam,
Juwairiyya
kenan suka firfito waje daga
ajijuwan ya ce su fara
tsallen kwado suma, yaje cikin
ajin ya tarar da
Hannah sharkab tayi gumi ga
sawun bulala nan
duk jikinta lambar. Yasa hannu
ya tasheta tsaye ya
ce ta daure ta tafi daki ta
kwanta. Tana tafe tana layi tana
rike bango ta nufi hostel.
Suna tsallen kwadon a duk
yadda suka ga dama a
zatonsu zai ce su koma aji su
zauna suka hango
masinja dauke da himilin bulali
kai kace jakuna za’a
daka tafka-tafka da su. A fusace
Haisam ya karbi
bulala nan ya fara taf-tafka
musu ita ta ko ina, ji kake
rududu suna tsallen kwado
suna yi yana
binsu duk wcce ta fadi kota
tsaya a baya yana tafka
mata. Wani dogon waje ya nuna
ya ce har can zasu
kai kuma su juyo. Haka suka
dinga yi suje su juyo
har sai da ya tabbatar kowacce
ta jigata hawayen
ma ya kasa fitowa sannan ya ce
su biyo layi kowacce ta zo ta
kwanta flate sannan ya
shassharba mata reshen nan
sau goma sha biyu.
Bayan jikinsu yayi kaca-kaca ya
farfashe, kuka
wiwi dan kwalayensu a hannu
ga kafa ta sage
babu damar tafiya, Juwairiyya
tafi kowa shan wuya
duka yayi mata kamar Allah ne
Ya aiko shi ko kirgawa ma baya
yi da bulalai suka kakkarye yasa
kafa ya dinga ball da ita daman
yana ciki da ita.
Kuka wiwi suke suna bashi
hakuri daga yau baza
su sake ba. Sannan Haisam ya
kyalesu anan a
kwance wasu a durkushe.
Tunda Haisam ya zo
makarantar nan bai taba zagin
wata ba balle duka yau sai ga
Haisam ya canja fuska babu
digon
rahama murtik da ita kamar zai
kashe su haka yayi
susu ligi-ligi dukan da babu
Malamin daya taba
yin irinsa a makarantar ko
displine master baya yin
irin wannan duka. Labari ya kai
gidan principal, a
gigice ta fito ta taho a bakin
ofishinta ta gamu da Haisam. Ta
dube shi sai taga ya canja gaba
daya sai
ta shiga tsoron tayi masa
magana. Can ta ce
“Haisam wanne irin duka
kayiwa S.S3 yau, me suka
yi maka? Ya juyo a fusace ya ce
“Ki tambayi kanki
da kanki daman na fada rannan
tunda baza ki iya
daukar mataki ba akan abun da
su Juwairiyya suka yiwa Hannah ba
to ni na dau fansa, kuma zan iya
yin
haka akan kowa duk wanda
yake marmarin
takurawa Hannah a makarantar
nan.
Principal ta rike baki kawai
tana kallon Haisam, ya wuce ya
barta anan a tsaye ya nufi
gidansa. Yana jiyo
Malaman da suke zazzaune a
wajen suna cewa “Ai kuwa
yarinyar nan sai zaman
makarantar nan ya
gagareta don sai mun zane ta
itama. Nan dai
principal ta hau fadace-fadace
tana cewa “Dole ne
na kira meeting da manyan *yan
federal akan abun
da Haisam yake min a
makaranta.
Magaruba tayi Uncle Yusif da
Uncle Sahabi suka nufi
gidajensu ta jikin gidan Haisam
suka zo wucewa
yana jin abunda suke fada wai
da prep din dare
zasu kira Hannah suyi mata
dukan tsiya. Shima
Haisam din yaji idan da dadi. A
haka suka rabu
kowanne ya nufi gidansa.
Haisam na idar da sallar
magariba yayi shigar wata riga
mai gajeren hannu damammiya
(body hook) ya dora wata suit
aka ya
fita ya nufi gidan sahabi. Ya
kwankwasa kofa,
Sahabi ya zo ya bude fuskar
Haisam ce ya gani a
murtike ta bashi tsoro. Ya ja da
baya da sauri.
Haisam yasa hannu biyu da karfi
ya angaza shi ya
tafi taga-taga ya fada kan
kujerar da ke falon. Haisam ya
shigo cikin falon ya mayar da
kofar ya
datse. Sahabi yayi tsuru-tsuru a
zaune Haisam ya
karaso inda yake zaune yasa
kafarsa daya ya taka
kujerar da Sahabi ke zaune ya
duko dai-dai fuskar
Sahabi suna kallon-kallo. Sahabi
yatsune fuska
ya ce “Meye haka Haisam lafiya
ko ka zama dan ta adda ne kazo
har gidana ka angajeni. Ya
yunkura
zai tashi yaji Haisam ya turashi
karshen kujera,
wannan karon hannu yasa ya
danki wuyan Sahabi.
Sai ido kuru-kuru an shake shi
kai ka ce mujiya ce
ta fada rami. Haisam yasa hannu
a aljihu ya ciro
wata *yar karamar wuka ya
bude ta tana walkiya ya
shinshinawa Sahabi a hancinsa
ya ce “Ka kula da
abun da nake so na fada maka,
idan ka kiyaye ka
kubuta idan kuwa kaki to
kaiconka kaga wannan
wuka zan iya lumata a cikinka
ko na yanka ta a
wuyanka ka fadi ka mutu ko? To
ina da niyyar
aikata haka in har ka kuskura ka
sake takurawa Hannah a
makarantar nan. Zan iya kashe
ko waye
ba kai kadai ba don haka ka
kiyaye. Sannan
Haisam ya sake shi ya mayar da
wukarsa aljihu ya
juya ya bude kofa ya fita yabar
Sahabi nan zaune
yana tunani kamar a mafarki
yau yaji kanshin
mutuwa baro-baro, yana fadin
“Lallai Haisam da gaske yake zai
iya kisa a kan yarinyar nan fa. A
bayyane.
Haisam na fita gidan Uncle Yusif
ya shiga
kasancewar duk yawancin
Malaman samari ne
babu mata a gidan. Daya taba
kofar yaji a bude sai
kawai yasa kai. Kicibus suka yi
Yusif ya fito daga wanka daure
da dan tawul a jikinsa. Yayi
mamaki
daya ga Haisam a tsakiyar
falonsa ko sallama bai ji
ba, murtik Haisam yake babu
walwala, shima sai ji
yayi an tunkudeshi kan kujera
yayi masa gargadi,
kamar yadda ya yiwa Sahabi ya
fito ya barshi nan
zaune yana mamaki. Saboda
tsabagen tsorata su Yusif ko
fitowa basu sake yi ba sai da
safe,
ballantana su je su daki Hannah
da daddare kamar
yadda suka shirya yi. Haisam
tunda ya shiga gida
bai sake fitowa ba sai washe
gari da misalin sha
daya na rana yana da lesson a
S.S 2B zai yi musu
Geography. Yana doso ofishin
principal ya hango motar Yaya
Habib yana cikin ofishin
principal, kuma
yasan yau za’a yi tane kawai
donshi babu mai
rabashi da makarantar nan. Ya
karaso da sauri ya
nufi ofishin principal tun daga
kan baranda yake
jiyo kukan Hannah ya shigo a
fusace gami da yaye
labulan kofar bazar. Ya tarar da
Hannah a durkushe ga jakar
kayanta nan a gabanta, principal
tana
rubuta mata takardar kora
(dismisal letter) takardar
kora daga makaranta kwata-
kwata ga Yaya Habib
a zaune yana cewa “Ai idan yaga
tabar makarantar
zai bari shima dole. A gigice
Haisam ya karaso ya
kalli Yaya Habib ya kalli principal
yaga da gaske suke sunsha
kunu. Hannah na kuka kamar
ranta
zai fita tana magiya don Allah
suyi hakuri. Haisam
ya tabbata muddin principal ta
gama rubuta
dismisal letter nan tasa aka yo
typing dinta ta buga
stamp aikin gama ya gama ko
gaban wa aka je
baza a dawo da Hannah
makaranta ba, kuma duk sharrin
data yi mata a jiki ya zauna babu
gogewa,
sai hankalinsa ya tashi matuka.
Nan da nan ya hau magiya yana
rokar principal
kada ta kori Hannah shi ya yarda
duk abunda suka
ce yayi zai yi zai ma bar
makarantar amma a bar
Hannah tayi karatu. Yaya Habib
ya kalleshi a wulakance ya ce
“Wa zai sake yadda da
alkawarinka? Kai da baka cika
alkawari tun yaushe
kake cewa zaka bar makarantar
nan. Haisam ya
juya ya dubi principal ya ce
“Madam don Allah kada
ki rubuta disimal letter nan ni
zan bar makarantar
ku bar Hannah tayi karatu,
principal ta harareshi ta ce
“Bazai yuwu ba kai da ka kusa
kashe *ya*yan
mutane akan wannan yarinyar
nayi maka magana
ka nuna ko nima zaka iya yimin
haka idan na daki
Hannah kaga gara kai da ita duk
ku tafi kafin
dukan ya dawo kaina. Wasikar
kora ai na riga na
gama rubutawa typing kawai
za’ayi. Ta danna kararrawa
masinja daya ya shigo ta ce
dashi
“Maman Joy tana nan a
ofishinta, a bude yake? Ya
ce “Eh yanzun nan ta shiga. Ta
ce “Ka kai mata
takardar nan ta bugota yanzu ta
baka ka kawo
min. Tana mikawa masinja
Haisam yasa hannu zai
fisge sai Yaya Habib yayi sauri ya
fisge ya ce “Ni kazo ka kwata a
wajena tunda ka zama marar
kunya. Haisam ya fusata ya
dakawa masinja tsawa
ya ce ya fice daga ofishin nan.
Sum-sum ya fita.
Kukan da Hannah take ya sake
tsananta taga an
fara rigima a kanta.
Haisam ya wawuro wata adda a
bayan kyauran ofishin irin ta
yankan ciyawa ya dora a kan
kirjin
Yaya Habib. Wanda mamaki ya
hana Yaya Habib yin
motsi daga kan kujerar da yake
zaune. Haisam ya
ce “Hakika zan iya kashe duk
wanda yake kokarin
jefa Hannah a cikin tashin
hankali da wahala a
rayuwarta. Ban dauka zan
sameka kana daya daga cikin
irin wadannan mutane ba,
amma duk da haka
ba zan karya alkawarina ba. Kai
Yayana ne Uwa
daya Uba daya da irin soyayyar
da Mahaifanmu
suke mana, ka duba kuma irin
soyayyar da muke
yiwa junanmu don haka bana
so na zama ajalinka.
Ba kuma zan bar makarantar
nan ba har sai na cika burina
dana kudira akan Hannah.
Hannun Haisam
rike da adda akan kirjin Yaya
Habib karkarwa yake duk
jikinsa yake hawaye ne yake
shatatowa daga
idanuwan Haisam gaba ki dayan
sai ya canja, Yaya
Habib ya tabbata Haisam yakai
kololuwar bacin rai
don shi yasan yadda bacin ran
Haisam yake abun babu kyau. Da
wuya dai yayi fushi abu da yawa
bai
cika bacin rai ba sai an kai shi
bango idan ya hau to
kowa sai ya tsorata kuma mai
lallashinsa ya sauko
sai an sha wuya kuma idan
ransa ya baci zai iya yin
duk abunda ya ce zaiyi. Hannah
ta kwala kara ta ce
“Yaya Haisam kada ka kashe dan
Uwanka a kaina na yarda ni zan
bar makarantar. Dan Allah Yaya
Haisam, dan Allah kayi hakuri.
Wani zazzafan
hawaye ne ya ci gaba da
zubowa daga idanuwan
Haisam a tsaye yake kawai ya
kurawa Yaya Habib
ido rike da wannan adda a
wuyan yaya Habib.
Principal kuwa tuni ta daka
tsalle tayi lungu tana jiran taga
yadda Haisam zaiyi da Yaya
Habib sannan
ya dawo kanta. A fusace Yaya
Habib ya yunkura zai
tashi Haisam yasa Hannu ya
turashi kan kujerar ya
koma ya zauna. Haisam ya ce
“Bani takardar
hannunka. Yaya Habib ya ce
“Son Hannah kake? Ya
sake fada cikin tsawa ya ce
“Tambayarka nake sonta kake
shi yasa ka kasa barin
makarantar?
Haisam ya ce “Burina inga
Hannah tana cikin farin
ciki a rayuwarta kuma in kwatar
mata *yancinta
kamar kowacce yarinya tunda
ita ba baiwa bace.
Gatan Hannah Allah, sai kuma ni
a duk duniyar nan.
Cikin sanyin jiki Habib ya
mikawa Haisam takardar a
sanyaye sannan Haisam ya
dauke addar daga kan
kirjinsa, ya wurga bayan kyaure
ya dauki jakar
kayan Hannah yaja hannunta
suka fice. Habib da
principal suka bishi da kallo.
Suna fita principal tayi
ajiyar zuciya don da kyar
numfashinta yake fita
saboda tsabar ta tsorata ta
tabbatar yadda Haisam ya
harzuka yau zai iya kashe
Yayansa balle
kuma ita. Bayan wani lokaci mai
tsaho suna zaune shiru
babu wanda ya iya magana
suna tunani kawai.
Yaya Habib ya nisa ya kalli
principal ya ce “Madam
yaron nan da gaske yake don
haka kada a kaishi
bango ya zo ya kashe wani a
dinga kai kawo a kotu, ina
ganin a kyalesu kawai don Allah
a daina
dukan yarinyar balle har ya
harzuka yayi kisa
domin Haisam zai iya aikata
hakan tunda ya furta
yana da zuciya sosai, amma fa
sai an kaishi bango
dan bai taba cewa zai yi kisa ba
sai yau akan
yarinyar nan, zanje in sanarwa
da Mahaifinmu. Ya mike ya fita,
principal kuwa dakyar take iya
magana saboda tsoron Haisam
tana ganin zai iya
binta gida cikin dare ya kashe
ta. Daga karshe ta
yankewa kanta shawara gwara
taje ta sami Haisam
ta bashi hakuri suyi sulhu. Ta
kuma yi masa
alkawari baza ta sake yadda
kowa ya takurawa Hannah ba.
Haka kuwa tayi ta sami Haisam
har gida
cikin lumana suka zauna ta
bashi hakuri suka yi
sulhu. Tana fita Haisam ya
tuntsire da dariya dadi ya
lullubeshi ya ce “Haisam!
Hannah!!.
Kwanci tashi su Hannah sun
shiga aji shida (S.S.3)
sune manya. Cikin ikon Allah da
hukuncin Allah Hannah tazo tafi
kusan duk *yan makarantar
kokari saboda tun tana zuwa ta
takwas ta fara
zuwa ta biyar daga nan ta
kwacewa Pamella Matin
position dinta ya zamana Rauda
ta daya, Nusaiba ta
biyu ita take zuwa ta uku.
Tafia tayi tafiya sai ga Hannah
tazo ta daya a ajinsu wani lokaci
Rauda ta kwace kayanta idan
Nusaiba ma ta hargitso sai ta zo
ta
kwace itama, haka dai ake ta
fafatawa. Amma
yanzu da suka shiga aji shida
har Malamai ma fadi
suke Hannah tafi su Rauda
kokartawa don sau da
yawa ko tambaya aka yi a aji
Hannah ce take
amsawa sau tari. Sannan a class
work da Assignment tafi kowa
ci, an basu mukamai daban-
daban. Hannah Abubakar Imam
itace shugabar dalibai (Head
girl) Nusaiba mataimakiyarta.
Rauda
kuwa dake tayi kaurin suna a
wajen iya rawa da wasanni
(Games) harma ake mata lakabi
da Janet Jacson sai aka bata
social prefect da games prefect
mukamai biyu aka hada mata
kuma tayi murna matuka da
wannan mukamin nata. Duk
ranar social
night har koyawa yara rawar
disco kala-kala take
yi. Hannah ma ta dace da
mukamin saboda ana son
Head girl ta zamana mai kokari,
wacce ta iya turanci
sosai, mai gaskiya, ladabi da
biyayya, mai kamun kanta ba
ballagaza ba, mai aji da tausayi
da adalci.
To duk wadannan Hannah ta
hada su don haka
nema da aka tace aka zabeta.
Domin a yanzu
Hannah ko Hausa bata cika yi ba
turanci ya kama
bakinta sosai Haisam har
mamakinta yake idan yaji
tana zuba turanci. Tana da jan
aji Hannah ba kasafai ta fiye
shiga cikin *yan mate dinsu ba
suna
hayaniya. Gata da tausayi
musamman ga yara *yan
kananan aji, babu ruwanta da
cin zali kuma bata
yarda kawayenta suci zalin yara
a gabantaba, tunda
ita ce shugabar dalibai tana da
ikon ta hana sauran
prefect. Wannan halaye na
Hannah ya sake fito mata da
kyakkyawar surarta. Hannah ta
sake gogewa abun
har baya misaltuwa ta yi kyau
kai kace ba *yar
Africa bace. Yaya Haisam yasan
irin mayukan da
kayan sawar da suka dace da
jikin Hannah.
Tsadaddun riga da wando da
riga da siket kala- kala Yaya
Haisam yake hadawa Hannah sai
dai
kawai idan ta dawo hutu ta
tarar ya aje mata a
gidan Uwar biyu, daman tun ba
yauba baya ga
Mahaifinta babu wani da take
ganin girmansa a
duniya irin Haisam. Amma da
yake Haisam mai
wasa da dariya ne da dalibai
suna wasa da dariyarsu a aji
kamar yadda ya saba yi musu
tun a
aji daya.
A garin su Hannah kuwa
Hannah har gizo take yi
musu, gani suke kawai baturiya
ce ta zo tace ita ce
Hannah, duk ranar da Hannah
zata dawo gida hutu
samari har tsayawa suke a
hanyar da zata wuce suna
kallonta, mata kuma ta katanga
suke lekowa.
Ana cewa Hannah ce fa *yar
Malam Habu a garin turawa take
karatu. Hannah sai tayi
murmushi
kawai ta wuce.
A gidan su kuwa Iya Abu da
*ya*yanta daina
magana suka yiwa Hannah
sunga wannan ci gaba na
Hannah daga Allah yake, babu
irin asirin da
basu yi mata ba akan a korota
daga makarantar ko
kuma ma ta haukace amma
baici ba. Hannah tana
dawowa da duk kayayyakin
amfani wadanda zata
yi amfani dashi har hutu ya kare,
ko ta bawa su Iya
Abu da *ya*yanta sai suce basa
so. Sai tayi hutunta kakaf ta bar
gidan Iya Abu ba ta bata abincin
da
suke dafawa ba. Ita kuwa
Hannah daman tafi son
haka domin ita yanzu ta saba da
cin mai maiko a
makaranta, tuwon dawa miyar
kuka sai su Iya Abu.
Madara da biskit ne abincinta a
lufge a jakarta a
dakinta. Sabulun wanka dana
wanki masu kamshi take amfani
dasu ita da Mahaifinta. Ta bashi
yayi
wanka ta wanke masa kayansa.
Malam Habu yana
jin dadi sosai da wannan abu da
Hannah take yi
masa. Yasan dole idan Hannah
ta zo zata kawo
masa kudi da abun duniya, ga
dinkuna da take
kawo masa tace inji Haisam.
Silifas dan madina dana gayu
yanzu Malam Habu yake sawa,
tsaf-tsaf dashi
na kashewa ya daina gagararsa.
Hmm! ***ajiyar zuciya da
lumshe ido** wannan wasan