HASKE CHAPTER 23

HASKE







CHAPTER 23









Magana yakeso yayi amma ya rasa abinda zai ce. Duk ilahirin jikinsa sai tsuma yakeyi,
idansa banda zallan bacin rai baka ganin komai. Kamar bai taba dariya ba tunda ya sauko
duniya, idan ka Kalle hannun sa zakaga yana rawa da kansa. Wani makoko mai dan karin
zafi yaji daga kirjinsa zuwa makoshin sa. Tunani kala kala ke rikito mashi. A cikin abinda ya
iyatantancewa baiwuce; a
‘Ke wace irin mai kunnen kashi ne?
‘Na rantse kin bala’in raina ni’
‘Yanzu idan na soma dukan ki sai ace na zalunce ki?
‘Na sake ki saki daya, idan yaso kije ki aure Laila saiku raina cikin tare’
Sune abinda yazo mashi, amma bai ce komai ba. Binta ya cigaba da mugayen kallo, har
bargonta takejin kallon da dukwani sansa nata. Zaka ga tsanarta ya soma dasuwa cikin
idansa. a
Numfashin 5a har lokacin bai daidaita ba, ita kuma bata bar girgiza kai alamarta tuba.
Daya gama kallonta sai yayi kwafa ya tafi. Keydinsa ya dauka saiya fita. Ta bala’in yin
mamaki yadda bai hukunta ta ba, sai kuma wani zuciyaryace ‘Akwai wani hukunci dayafi
kallon rashin arzikin daya maki?Yanuna you’re as uselessas the P in Psychology’. Zaman
dirshan tayi, saialokacinhawaye wandayazamemata sana’a suka fara binfuskanta. n
Wayar dake kasa ta dauka, babu abinda ya faru dashi, abinka da IPhone X inbuilt battery,
balle ta saka mashi screen guard da rigar waya watau pouch. Ta dayan bangaren har Laila
ta dauka wayar tana ‘Hello! Hello!!’ bataji ance komai ba. Tsaki tayi tareda cewa ‘Almura
kin fa isheni’ a fili saita kashe wayan wanda a lokacin Hasketa dauka kenan kuma taji tsab.
Saidaibazataiyatantancecewakoda itaakeyibakowani Chandaban gefen Laila. a
Kan Haske ya soma bala’in sara, ga kuma yunwa yana addabanta, rabon ta dataci wani
abincin kirki tun suna dasawa da Badman. Adafe taje dinning ta dauki doughnut daya da
kyarta ci kamar magani saita sha ruwa tana zare ido kamartaci wani mugun abu. Ba komai
bane illa tsabaragen tashin hankali yasa ta rasa appetite. Yanzuta soma tausayin kanta
saboda tana tsaka mai wuya.
Three seaterta koma domin ta kwanta, yanzu tama soma ganin jiri, tunani take yanzu
matsayin ta a wajen Bilal. Bazatajure irin kallon daya bita dashi ba. Dama ya zage ta ko
wani abu, yafi mata akan shirun dayayi. Abin yw bakanta mata rai. Yanzubatasan me yake
tunani ba, komai yanzu ya sake chabewa. Gashi babu Besty da zata kira ta bata shawara ko
zatajidamadama. a
Tana ganin kamartunjiya da yau kap bata shiga da kafar dama ba, duk rnetayi yana
barewa da ita. Anya ba Laifi wani dangin su yayi ba alhaki yake antayo mata? Kokuma
bakin Ammi yake tasiri a rayuwar ta? Tunda ta tashi take wahala yanzu kuma auren ta
shima ansoma.Bakuma takira Lailabayanzu suna magana Bilal yashigo kamarguguwa. a
Shi yanzu ya daina mamaki da tausayin ta, yafl danganta abin da tsabaragen iya shege.
Idan bashi ke zaune da ita ba bazai taba yarda akwai irin mutanen a doron kasa ba. Sam
batada wayo, duk iliminta da kaifin tunani Laila tafi, da badin mugayen halayyar Laila ba
da tsabaragen bakin ciki, tafl Haske sau dubu. Haske batada maraba da mutanen farko
masu tsabaragen taurin kai da kaflya.
Saboda idan Laila ce 3 maimakon Haske ranarfarko zata gane halinta ta fatattake mutum
amma banda sweetie dinsa, koda yake baiyi tsammani yanzu ko she isstill hissweetheart
ba. Varinyar batada wayyo abinda ya sani kenan. Idan bata gaggauta canza hali ba suna
dabdarabuwa. a
Yanada kyau namiji ya zauna da mace saboda halinta, kuma da basirarta domin cigaban
gidan baki daya, yanzu a haka ne zata raina yaransa? Ita ma bata wuce a raine taba tareda
koya mata karatun gane makiya, hakurin sayanadabdagazawa. Wannan kenan! a
an
Awanni ya soma komawa kwanaki, babu jituwa tsakanin Haskeda Bilal. Bayadawowa sai
bayan Isha, yadda ta dafa abinci haka zata kwashe abinta ko bin wajen batayi. A waje yake
karyawa da kuma Dinner, idan yaso shan shayi kuma da kansa zaije kitchen yasa ruwan zafl
a cup, idan ya shanyeya dauraye ya ajiye.
Baya ma fitowa sai ta tafl aiki balle ta dame shi, idan kuma ya dawo cikin dare zai ganta
zaune a falo, bayan sallama baya ce mata komai. Ita cetake masa magana ta gaida shi,
Shima baiwuce Sannudazuwa, inawuni’ II
‘Lau’ yake amsa mata fuska a murtuke saiyawuce dakinsa, yadda yake mam rawar kai a
farkon auren su bata taba tunanin zai iyafushi haka ba, abinda Laila ta fada mata akan
mugayen halinsa ya sake bayyana. Laila isalways right, abin yana mata yanayi da Bilal irin
mugayen maxajen nanne masu raba matansu da duniya saboda sujidadin mata wayo
bamaiganewa. a
Shi kam yaje wajen Banan sau biyu inda tayita murna, basuyi hira ba banda danna IPad
dinsa dayayi gaba daya, bayan minti talatin yaceyake tafiya. Bataji haushi ba tasan wata
rana zasuraba gado.
Tunda auren zai yiwu, kawai fatan Banan ta rinka jin maganar sayake. idan tayi zai bata
duniya. A hankali mai kunnen kashi Hasketana salance mashi. Koda yace zai mata magana
yana ganinta haushin ta zai dawo masa fil. Anyi lefe akwati seti daya mai hudu da kit. Ansa
komai daidai gwargwado saura kaiwa.
Yanzu kusan kwana uku wayan Laila baya shiga, kawai faduwar gaba take samu na rashin
dalili. Tana tsoron kada yan bashi sunyi mata wani mugun abu. Gashi babu dama ta biya
wajenta domin taduba, itamatananeman sulhudamijinta. a
Text kam yafi ashirin na, ‘Babe where are you? ‘Call me back’ ‘l m worried’ ‘Gabana yana
fadi’ wanda duktake tura ma Laila. Har su Facebook da WhatsApp message makil ta tura
kuma bai shiga ba.
lta kuma Laila gidanta yanzu ya hargitse, Saifya fada niyyar sa na kara aure kuma ginin
dayake yi anan matarzata zauna. Koajikin Sameera, lokacin auren Laila ne taji wani iri
amma yanzu ya auro mata dubu. Ta dawo daga rakiyar maza.
Anan hankalin Laila ya tashi, tana kokarin ta kore Haske daga gidan Bilal, sai ta kore
Sameera yanzu kuma yana maganar auro wata. Fitina take masa kuma ta nuna rashin
amincewa karara. Dariya ya bita dashi sannan yace, “Toh uwata, ai dole ki hanani na
hanu….Ahhhlallai” II
Kamar yadda sukayi ma Sameera yana waya a gabanta haka wannan karan yake ma
Laila, gwara ita Sameera night call ne baya kashe ko sisi dinsa, wannan kam ana lsha suna
falo yake saka katin dubu daya. A gaban Laila ya kankare yana fito tareda karkada kafa.
Sannan yakira Bukola. a
lta Bukola tace bai dace ba tunda sun hadu ranar, shi kam yace yana kewarta yasa ya
kirata. Hakasuketa magana yanababbaka dariya. u
Dayake Laila ta dade bata saka relaxer ba, gashin kanta ya soma karyewa yana tauri. Saita
aika aka siyan mata kumfan lux domin tasaka, shine kadai abinda zata iya siya. Batada
kudin Ozone balle Mega growth. Abinka da rashin sabo haka ta babbake kai kamarwanda
aljanu sukayi wa aski.Gaciwoduk taji a fatar kanta, zugiyake mata kamar ana tsikarin ta a
tafin kafarta.Tanazaunetana danzaburezabure shineSaifyasoma wayar iskancin sa. 9
Aikam Laila tayi zuciya taje ta hgo wayar ta rada da kasa tana haki. Zafln kishin sa ke
mata ruri kamar ganNashi. Ji take kamar an soka mata takobi a kirji. Numfashi takeyi
kamar wanda tayi gudun fanfalaki, bazata iya raba shi da kowace mace ba, ko ganin
Sameera datake yi ji take kamar ta shake ta ko ta saka mata piya-piya, saita saka hannu a
kugu tana jijiga taredajiran mai Zai biyo baya.
“Daga ni bazaka kara aure ba! Karyan iskanci kake yi Shege ka fasa! You’re Mine alone….
MINEEE! ” tace cikin tsiwa.
Kwada mata mari yayi saiya tureta, dayake ya fita iskanci saiya dauki wayanta ya Flto da
sim din ya karya, sannan ya dauki ya saka Sim dinsa ciki. masifa ta soma wai bata yarda ba,
kici-kici ta fara tana kokarin kokawa dashi, anan ya sake zabga mata mari na ganin taurari,
shafa wajen ta rinka yi tana ganin kamar ya tsaga mata fuska saboda zafl.
Bata dandara ba ta sake nufan inda yake tareda dunkula hannu tana watsa mashi ashar,
aikam ya chapke saiya tureta. Wayan DVDYafinciko ya soma antaya mata, nan ya daketa
sanranshi. Banda kuka maitsuma rai bata komai, tayi dana sanin takalar sada fada data
barshi da Allah. Sannan yace ta gyara mashi nashi tukun saiya bata nata wayan, toh
sanadiyarrashin jinLailadaHaskebataji bakenan. n
Ranar garin akwai lumshi, babu rana mai gasajiki, iska yana kadawa yadda ya dace. Kowa
yana harkan gabansaa garin Kaduna,yanofIssuntafl yan kasuwa suma ana ciniki tareda
gode ma ni’imar da Allah ya basu.
Shago dan madaidaci ne, anyi fentin wajen da ruwan kwai da zuma, sannan kuma an
saka plaster of paris(POP) a matsayin Ceiling. 3D tiles ne a kasa na katon shark ya bude
baki kamar zai hadiyeka.Daga bangerendake adjacentda kofa, madubi ne tun daga sama
bangon. Sannan ga makeken tabur gaban wajen. lnda ya kunsa kayan make-up kala kala,
Zaron, classic, Kylie, Fenty, KKWda sauran su.
Kujeru stool yan kanti guda uku sai cushion guda daya. Sannan akwai AC daga chan kurya
yana kwarara sanyi. Gefensa kuma durowa ne showglass. A cikin akwai turare English and
Arabian, kayan kwalliya da brushes na siyarwa.
Nan ba ko’ina bane illa ‘Fijr Glam’ shagon da Daddy ya bude mata na kwalliya tunda ta
iya. Balle bayan ta arba’in ta soma flta taje make up school inda ta kara kwarewa. Duk da
cikin shegenetanabukatan tallafl,kuma kullumabatabaitaso ha. a
Gwara ta tashi ta nema da kanta, anyi karamin budewa inda ta gayyace mutanejiya suka
zo akayi masu free make up, kawai hoto zasuyi suyi tagging dinta a Instagram.
Ammi Hadiza anyi amai an lashe, yanzu ta koma gidan Hajia Binta da zama, haka taje
tana masu kuka wiwi wai sharri akayi mata. Kawai ana mata bakin ciki ne. Dan munafunci a
kasa ta zauna tana roko. Mommy kallon ta tayi saboda su Maimuna sun gani a Social media
ga video sanda ake ingiza keyarta admin block.
Amma kuma hannun ka baya rubewa ka yanke ka yar, ta yarda ta dawo gidan da zama.
Sannan tayi rna mijinta magana akan Yama Zailani magana, koba komai ta koma tayi
zaman yaranta.
Fafur Zailani yaki aminta, sabodayanzuya somaneman aure. Kanwar matar abokinsace
mai suna Fadeela. Ta aure soja an mashi transfer Maiduguri inda aka kashe shi, yanzu haka
tanada yarabiyumarayu.
Yaaminta da halinta kuma yanaso ya aureta nan bada dadewa ba, babban yarta shekarar
su daya da Aneesa. Zasu tashi tare kenan tunda yacetazo da yaran.
Bakasan wa zaijikan ka ba nan gaba. Ga Fadeela tafqHadiza kyau da gogewa, tanada
karatun arabi da boko. A university of Madina tayi karatu bakinta ya zauna da larabci kamar
jikan King Fahad. Koda Mommy taji zancen tayi ma Zailani murna amma Kuma ya zatayi da
Hadiza? Shikenan zatayi ta zama dasu dindindin. Anan ta yanke shawara bayan kwana biyu
zatacemata takoma Zaria gidan gadonsutazaunatunda yana nan. u
Da Ammi, Mommy, Maimuna, Amina da YarDubai Yasmin aka je wajen bude shagon.
Yasmin itace babbar yar Mommy kuma shekararta ashirin. Yargayu ce na ajin farko kuma
ta gaji kyan gidan. Batada wuyan sabo kuma tanada fara’a and she isvery bold. Kartake
ganin kowa duk abinka tana karantar yanayin ka. Anyi mata kwalliyarVampire da cat eyes,
inda tayi tagging mutane da yawa daga ciki har Haisam. Dama tun f1lazal tana sansa, shine
dai yake basarwa.
Yanzu haka bayan kwana biyu takan mashi maganajefijefi a whatsapp. Sannan tana
yawan tagging dinsa a funny video na Instagram ko Kraks ko lasisiko Bushkiddo. Mommy
tayi abinci takeaway na bama baki. Kuma anyi gayya sosai, kowa ya yaba da yadda Fijr keyi.
Very professional kuma sukadauki alwashin zasu dawo.
Hafsee kamaryadda ake kiranta anyi mata Cradle a shagon domin barcin ta, sannan kuma
tanada kayan wasa. Yanzu zama ya nuna sosai har tana dabo ta kama abu ko mutum ta
mike tsaye.
Kowa yazo wajen banda Haske, abin ya dan sosa ran Fijr saboda yanda taga suna dasawa
kwana biyu har whatsapp sukeyi jefl jeR Ta kirata a waya anan Haske tace aiki yayi mata
yawakuma batajindadinjikinta. 
Ita kuma bataso ta kure hakurin Bilal yasa take tsantsan dashi kar ta kwance igiyar auren
ta dake yawo. Sai dai ta tura ma kawayen ta yan secondary da university invkation kuma
dayawa anyi mata kara anje.
Kashe garin ranar bayan ta dawo daga aiki, tana kitchen tana jollof rice da busharshen
Kifi. Bilal baya cin abinta kuma bata fasa dafa mashi. Zata yi kokarin shan kansa, Mai gadi
ta ke kaima abincin inda yake binta da addu’a.
Dayake Fijr takan je mata, musamman sanda take make up school baida nisa da gidan,
anan take zuwa sallah idan taga dama. Sun fahimcejuna da Mallam Musasosai,yana san
yadda take barkwanci. Rana dai dai ne baya rabata da masu napep.
Kullum maganar canji ake yi, kokuma yabi da ita ta dogon hanya inda zata zage shi tas
la ada waje. ‘Hajia Fijr Dodo maganin dodanni. A ganki a kyale ki bindi a bayan surika’
Mallam Musa keyawan cewa mata kuma ta kan bashi dari biyu lada. Yau da wuri tabar
shagonta sabodatanasotabiya wajen Hasketayi mata yajiki. a
Customer biyu ta samu inda taji dadi sosai, sauran lokacin sai tayi tutorial din nude make
up tareda tagging mutane da yawa.
Hafsee tana sagale a kafadarta tana barci, saijakarta a hannu daya, sallama tayi kusan
sau uku kafin Haske taji. Dafara ta tarbe ta.
“Maman Hafsee kece tafe .7”
“Wallahi kuwa Anty Haske, nazo ganin jikinki” yanzu Anty take ce mata tunda suka shirya.
Zama Fijrtayi a 3 seatertareda kwantar da Hafsee.
“Aida bakiwahala ba, naji saukiyanzu….Barina kawo maku ruwa”
Kitchen Haske ta koma ta dauko Fanta da ruwa, a gaban Fijrta ajiye. Saita koma lokacin
abincin ya kusa gama nuna, rage gudun gastayi sannan ta koma falo ta zauna, kallon juna
sukayi ana murmushi jefijef’l tareda kallon TV a tsakani.
Fijrta soma magana tana dariya, “Bansan ko kin samu labari ba amma Ammi tayi sata
kuma an fatattake ta” kwarewa ta soma yi saboda mugunta. Zaro ido Haske tayi tareda
dafa kirji, gabanta ya fadi kuma bataga abin dariya ba. Koda yanzu tasan Ammi ba mum
dinta bane bataji dadin yadda abin ya faru ba.
Innalillahi! Kin tabbata ita ce ba sharri bane? “
“Wallahi ita ce Saita watsa ma Haske hararar wasa. Sannan sai ta cigaba da dariya. Kora
ruwa tayi saboda makonshinta yanata dishewa.
“Na rantse abin da bala’in dariya, ai nayi missing naso ina wajen na babbaka dariya da
kyau… WaisaigaAmmi anazareidoanaroko… Yihuhuhu ammaNajidadi” u
ke a ina kika gani?
“lnstagram duniya duk sun gani… Sai tace wai sharri ne… Da ina wajen kadan ba saina
zuga su sun rike mata damtse ba sun rinka fincikarta sunarflzga sannan a mika ma yan
sanda” saita sake barkewa da dariya, “Wayyo cikina !Wayyo Cikinal! Wayyo cikina!!!” tayita
nanatawasabidadariyaryayi yawa. u
“Allahdai ya kiyaye, amma abu baiyi dadin jiba!”
“Kamar ya Anty? An nayi bala’in jin dadi… Sai gaAmmi… Sai ga… Ammi an gwalalo idanu
ana wallahi tallahi…. Konijiya haka nayita kaffa kaffa da kayana a shago ina binta da ido
kamtasampeminkaya”tace taredasarkewacikin dariya. a
“Yanzu ina Ammi?”
Aina gaya maki Ammi an fatattake ta, korar kare fa sukayi mata… Taje wajen Daddy
shima yayi matan fuska, Maman suYasmin ta sake daukar ta a karo na biyu”
“Ehen Yasminta dawo hutu ma shekaran jiya” Fijr ta kara.
“lkon Allah ! Na tausaya ma Ammi wallahi, ka rasawajen aiki da gida babu dadi”
“Anty kenan ke dai Kincika abu! Ai ni Maman suYasminbata burgeni ba. Wai asheAmmi
dukan tashi ki sha gishiritayi ma Maimuna ta kuma zage su sanda ta tw dinnan… Haba sai
kace ba yar halas ba… Ai wanda zai dake Hafseeyanzu yayi booking permanent bed space
aasibiti,sainatsiyayarmashi dajinijikinsatabaki dahanci” a
Abin bana dariya bane, amma yadda Fijr ke cijewa da nuna hannaye yasa Haske
murmusawa. Batajin dadin yadda tsautsayi ya debe Ammi tayi wannan mugun abu ba. Ba
ita ba harjikoki ta bata masu suna. Abu daya yanzu yake cinta, tanaso ta roke Fijralfarma
akan taje gidan Laila ta duba ko laWa.
“Na saka maki abinci?”
“Eh kadan
Lukacin da Hasketa koma abincin ya nuna, ta saka ma Bilal nashi saita kai Dinning.
Sannan ta saka masu nasu kowa da plate dinsa. Fijrtace a kawo mata barkono duk da ya
jin cikin abincin, ita dama haka take saita kara yaji. Tafl sotana cin abinci tana ganin azaba,
tayita atishawa tana zare ido,jin kanta take kamaryar ruwa. A kasa Hasketa zauna wannan
karan sabidayafl bata balance, sunacisaita somamagana. a
“Kin tuna Laila kawata?”
“Shegiyar ba, ai ta daku wajena rannan!” ta kwashe da dariya.
“Me tayi maki?”
“Almurantazotana mana maganar waye wayeakan ki…Banmatsayanasaurareta hana
dakashegiya,Ammi na kallokuma bata hana ba”
Anan zuciyarHaskeyayi fes,gashidai zanceya nuna Laila bataaiki da Ammi kamar yadda
Bilalyace.Ammi cemuguwaita kadai. lta kuma Fijr batasakeganin Lailaa gidanba, balle
ta dangantasutarehar DaddyyasakeAmmi.
“Damana kwana biyubanganta ba,gakuma Cikinnanya sakanigabashine nake
tunanin ko zaki gidanta ki dubata” tace 3 dan tsorace.
ShiruFijrtayi,juya idotakeyi a doletana tunani saidaga bisani ta somamagana, Anty
kiyihakuri amma wallahibazaniyazuwaba”
“Meyasa?”
“Wallahibana ta’ammali da munafukai.Kuma ni un muna yarajinina bai hadu da ita ba.
Karnajegidantana kasancontrollingkainana dake shegiyayariska,gwara nesanesa.Ban
iyafuska biyu ba,idan inayinka nek0banayinka… Notwofaced” p
Nisa Haske tayi tana kallon Fijr, akwai kuruciya da ita, bata san mutum ba tana binsa da
ashardan Kawai jinin su bai hadu ba. Wannan ba halin musulmin kwarai bane, balle tana
mace zata sha wuya gidan miji idan bata canza hali ba, “Ki daina irin haka! Yanzu kin
zalunce ta batayi maki komai ba Kin zage ta. Babu kyau haka” (ace ranta a bala’in bace.
Murguda baki Fijrtayi tareda wulla idanu, koma menene bata san Laila kuma bazata
gidanta ba.
“Nidai Anty kiyi hankali da ita” tace kasa kasa. Hafsee ne ta tashi a inda Haske ta mike
cikin azama taje wajenta. Daukarta tayi yayin da suka soma murmushi tunda sun saba.
“Hello Ma Chérie(My dear) tace, ita kuma Hafsee wawulan bakinta mai hakora mitsatsa
guda 3 ta nuna tareda kokarin kaihannugashin Haskezatafizga.
Ba Fijr tabar gidan ba sai da tayi sallan Magrib sannan Haske tasa Driver ya mayar da ita,
kuma ta bashi kudi ya siyan ma Hafsee katan din Bobo a hanya.
tn
Idanazaharyayi an somahada hada ana ciniki kenanhar bayanla’asar.A lokacinsuke
riba tareda maida kudin su. Da kyar ka samu tabur empty harna tsawon minti talatin kafin
wani ya hau.
Abinci mai rai da laflya yaci a shagon Hajia Mujibat, yanzu anan yake cin late lunch san
ransa, nama sunkuma sunkuma kamar dai yadda yaga ana ma Baban Tunde lokacin. Kuma
babu ko sisin shi har idan ya basar yace baza shi ba Bukola tayita zuciya. Gashi idan yace
‘Aminat’ ‘YesSir’take cewa.Daidai yaddayake sonsu. p
Ranar yakaita gida bayan aiki saita dakatar dashi, wai tanaso taje gidansa ta gaida
matansa. Balle ma sun kusa fara zama gida daya. Yanzuginin har roof ansa aluminium zinc
da kofa da Plaster of Paris.
Abin da ya rage daga tiles sai susink da wiring sannan kuma fenti. ‘kululu’ cikinsa ya
soma, Nisayayi saboda Bukolatana tambayar abinda yafl karfin sa, dama Sameera kawai
ne dayayarda amma kumaLailayariskaceajin farko.DafashiBukola tayi é kafada,
“Please gobe naje na gaida my seniorAunties” tace kamar zatayi kuka.
“Okay babu damuwa” yaceyana share gumi.
Bayan ya koma gida dakin Sameera yake ranar, gobe sanda Bukolazata yana dakin Laila.
Dubara yafado mashi akan ya yaudare suyace matar abokin sanetazo gari za ayi zumunci.
Sadiya da Abul Khair duk sunyi barci, wutan Laila ma 3 kashesanda yaje wanda ya nuna
hana kwanta, ita kuma ranarta wuni da yunwa. Kawai sai Sameera ta aika mata abinci mai
bala’in dadi, balle bata tsammani nan taci tayi gyatsa ta kwanta. Mubina da Sameera ake
falo, tashar FOXLife keaiki yayinda take kallon ‘Second Chance’ fllm din Turkey na Murat
da Deniz.
Mubina taje ta gaida shiharya dagata sama, Sameera kuma daga zaune ta gaida shi. Ta
riga ta saka pyjamas masu kyau silk wanda ta siya kwanaki a kasuwar barci. Tayi kyau
abinta sai basarwa takeyi. Shima yayita saxarkallonta saboda tayi ne. A kosheyake amma
kuma yasan Sameera ta iya kayan kwalam kuma tana saka nama. Gwara yaci rabon sa duk
dababukosisin sa.
“Keh! ajiye min abincikafln na flto daga bayi” taku ukuyayisaiyajuya,”Kaninshi zanyi
(Kanin wanka)” Saiya wuce hanyar bayi, banka tusa yayi mai uban wari da kara gwararap
yayin da zai shiga,anan yashafe kusan awa daya kamar yaje haihuwa. wari ya rinka
sirirowa mata kamar na mattacen shanu. Dasauri Sameera ta dauko burnerta jona a
socket tareda sakaturaren wuta, a hakan ma warin yana kokarin ya yi overpowering
kamshin. Mamaki takeyi anya Saifyanada lmya kuwa ko za’a kai shiquarantine? (inda ake
kebemasucutakada wasusukama) p
Sanda ya flto yaji turaren wuta, tura baki yayi tareda watsa mata harara. shi a ganin sa
raini ne idan ya shiga bayi a wani saka turaren wuta. Kowa dai yana babban harka, daga
sarki har mallam, meye abin damuwa ciki?
Zama yayi akan one seater ya wurga kafa daya akan hannun kujerar yayi babakere, nishi
ya soma yi ga zufa kamarwanda yayi faskare, ‘Dan kara min fanka’ yace saiya rufe ido
Sannan ya soma magana wayyo Allah amman naji dadi yau kaiii sai ya rera 
fito, dama haka yake idan yagama kashi kuma ka sake mashi fuska zai cezai kwatanta
maka kalar kashin sa.
Tuwan alkama tayi mai bala’in danko, kana gutsura wani laushi zakaji mara misaltuwa.
Sai miyan karkashi da busarshen kifl manya yan Maiduguri da stock fish da ganda. Anan ya
sakegodemaAllahdabaiyi kauran baki bayacebazaiciba.
Juice din garin kuka tayi wanda yasha lemun tsami, ga kuma bala’in sanyi. Laila ta mance
yaushe rabon data saka kaya cikin fridge din. Yanzu batada sana’a bata komai. Yadda
abinci gagaranta yake yasa ma take yawan zuwan gidan Haske.
Kashegari daya koma dakin Laila saiyasanar da ita matar abokinsa zatazo. Da asuban
fari yaje kasuwa ya siya kaza da kayan cefane harda su curry da thyme bai mance ba.
Sannan ya siyakayan salad da salad cream da kuma kwai. Sai tiyan zobo, sigada flovour.
Da kansa ya share gidan ya wanke bayin su, ita Laila tana kitchen, wannan Karon tun
daga tafashe ta soma ci. Bazata bari ya shammace taba. Dayazo rabawa yaga ba cinya
daya, fifike da wuya abin yayi masa ciwo. Tamke gira tayi tana jiran yayi magana su soma
zagezage. Yanzuta bala’in raina shi, bata shayin cewa zataci uwarsa koda tasan zaijibge
tane, bakinta baya mutuwa ashartake masa kala kala. Ta mance yaushe rabon data kira shi
Destiny.
Bai cekomai ba, yasan tana takalar sa ne, kafln suna cikin dambe Bukola tayi ram dasu
yaji kunya. Jollof tayi wanda yasha karas da peas,saitayi peppered mai dankarin dadi.
Yasoya barma Bukolacinya daya amma yadda yake sheki da kamshi ya kasa hakura, haka
yaci yana lashe baki.
Lailataji matar aboki zatazo, wannan dai purple lace din na lefenta wanda shi kadai ne
abin arziki ta dauko tasa, sannan ta zabga makeup tareda saka purple eyeshadow. Jan baki
ta rambada tau purple kamar magajiyar karuwai. Sannan ta saka dan kunne dogo fashion
har tsawon wuyanta wanda ake kira ‘Jahannama ga pasinja’. Har salon taflya ta canza tana
karkada jiki kamar balbela.
Saif rigayasa na polo mai layi layi brown, saiarmy wando da hula hana sallah(Facing
Cap) saboda Bukola tace tafi san yana saka kananan kaya, wai yana fito da asalin yanayin
kyawawan idansa. Sai dai matsalar sa daya bai iyasawa yayi kyau ba, disaster yakeyi koda
yaushe. Kamaryanzu baida maraba da kwanan Amala da miyan ganye. Gashiya mulka
vaselineafuska cikinrashin sani, fuskan sashekiyakeyi kamar danwake. u
Wajen 12:30 Bukola ta isalayin, shineyaje ya dauko ta 3 busstop. Tana ganin yadda yake
washe baki gashi ya hada kala, ciwon kai taji amma kuma tasan dan Adam tara yake,
wannan shine abinda bai iya ba.
Yanayin gidan ya burge ta, komai yayi mata daidai. Dakin Laila ya fara kaita, nuna Laila
yayi yana murmushi saiya ce
“Wannan ita ce Laila my second”
“Ina wuni Anty?” saita rinsina alamar girmamawa.
“Lafiya lauya aiki?”tacetareda daga kafada ita a dole matar gida. Bukola zata girma Laila
da wajen shekara 2.
“Sunan ta Aminat Bukola”
“Bukky ma ya isa Anty” tace cikin murmushi. Kallon Bukky yayi dake tsaye, Zauna
mana… Bismillah”
Zama Bukola tayi tana kare ma gidan kallo a kaikace, a lokacin Laila taje kawo mata
abinci. 
Abin yayi mata dadi yadda Laila ta tarbe ta duk tasan wacece ita. Yanuna abu daya ne
watau Laila tanada dattako. Shi ma Saif ya zuba abincin yana daga gefe yana ci, Laila ma
Haka. Dakin bakajin karar komai sai kachau kachau na cokula.
Bayan sun gama sai Bukola ta bukaci tanaso tayi Sallah sai taje wajen Sameera, abin ya
burge Saif ainun. Cikin suukun ita ce wanda ta tuna da sallah. Bayan ta shiga bayi shima
sai ya wuce masjid. Fargaba fal ransayasan yan unguwa zasuyi ta mamaki, banda ramadan
baya sallah ajam’i. Kunyayaji sosaiakan haka.
Bawaibayasallahbane,kawai baisanyitaredamutane,A gidayakeabinsa.Yasoyatsaya
a bakin gateyaki zuwa,da acehe isfive yearsyounger tsabzaiyi haka sannan yasakakasa
goshin sakamaryayi sujjada.
Wani abin, kai kake gani, gaisuwa na mutunci aka bishi dashi a masjid. Babu wanda Yama
lura baya zuwa, kowa hidumar gabansa yakeyi. Abin yayi masa dadi sosai kuma ya dauki
alwashin idan ya aure Bukolazai rinka zuwakaf1n kuma ta gane.
Bukola ta bala’in burge Laila, daga kayanta wanda lace necobalt blue da gyale baby pink
mai laushin gaske zuwajakarta na Dior. Har kofardakinta taje domin taga irin takalmin
datazo dashi, Vinci ne mai heels. Gashi sarkan zinare ke makale a kunnenta da wuya, kuma
gazobuna uku duk na zinare.
Bayan Saifya dawo lokacin har Bukolata idar, Laila batayi ba tanajiran idan Bukolata tafi
saitayi. Dankwalin ta na ture Kaga tsiya ya bata wahala kafin ta same shi haka. Murmushi
Bukolatayi saitace, “Muje muga suAbul”
“Okay tashi” saiya mayar mata murmushi. Bayan sun tafi Lailatayi maza ta cinye sauran
naman da Bukolata rage kafin Saifya rigata.
Yana gaba tana baya tiryan tiryan har suka isa, sallama yayi tareda murmushi abinda bai
saba ba. Ita ma Bukolatayi suka shiga. Sameera ta flto daga kitchen inda Bukolata
dukursa har kasatana gaida ta.
“Ina wuni Anty, mun sameku laHa?”
“Lafiya lau, ya hanya?”tace cikin zallan fara’a
“Alhamdulillahi,yasuSadiya?”
Kallon kan kujera Sameera tayi inda Sadiya ke wasa da yar baby abinta, “Gafa Sadiya ana
wasa” sai sukayi murmushi. “Kin tsaya bakin kofa shigaciki… Pleasesi down”
A lokacinSaifya dadeda zamaabinsa,Bukolata zaunatareda Sadiyatana matawasa,
Sameera kallon su Abul Khair tayi tana masu magana da ido, murmushi sukayi suna sosa
keya.
“AL… Ina wuni Anty”
“Lafiya lau. Kana zuwa school?”
“Eh”
“Very good” saitabudejakarta ta daukochocolateBounty guda shida ta basubir biyu. Da
girmamawasuka amsa, a tareAbulda Mubinasuka ceThankyou.
Kitchen Sameera ta koma, pancake dlnta mai dankarin dadi tayi. Gashiyayi fluffy ya
kumbura sosaigakuma kauriga laushi. Saitayi decoratingplatedin da Syrupna cin
pancake da kuma soyayyar kwai a gefe da sausage.
Ba Saif kadai ba harta Bukola abin yayi mata kyau, amma kuma Saifyayi mamakin
meyasa ba’a kawo mashiba. Ranshi yayi mugun bacimiyanshiyasomatsinkewaamma ga
Bukoladoleyadake, saidaisaida yagayamaSameeramagana. a
“Bakuwakawaiaka sani yaubandamiji” yafada yana murmushi.
“Ai bansan kanasan irin kayan nanba, saboda yanayin cefane” tace tana dariya. Shiya
gane me take nufl, watau iya kudinka iya shagalin ka, ita kuma Bukola ta za a saboda bai
taba siyan kala ingredients dinba Sameera batayi tunanin yana ci ba.
Fakonidon Bukolayayi yana harararSameera,irin kallonbari bakuwata tafi naciubanki.
Waita hakan zatatsoratata sakamashi,mirsisi tayi ta zaunagefen Bukolatama somajanta
da hira.
“Yasunanki?”Tauna abincin bakintaBukolatayi da saurisauri tanasota amsa.
“Bukola”
“Allah sarki ni sunana Sameera”
“Okay Anty nagene” 9
Komai na Sameerayamburgeta akan Laila, daga yanayindakin kasan Sameeratafita
daban. Colors dinta yaf’lmatured daga labule zuwa kujeru. Sannan makeup din Sameera
yafi kyau, simple riga da skirt tasa wanda ya bayyana surarta, atampha ne Chivangy.
Fuskanta babu wani make-up, lip gloss ne da kwalli sai dan kunnen zinare amma banda
sarka, k0 sadiya da mubina shike makale kunnen su. Ga fatarta baki amma yana sheki,
anan Bukola ta aminta da black beauty sun hadu. Yautaga wanda ta tw da imaninta.
Bakar macebugun Allahbakyakodewa, a haukiazamekihaumutum kizaunadaram. 
Tasta cinye pancakes din, kwan neta rage, Saif ya hadiye miyau yafi sau saba’in. Tsuma
yakeyi yana jiran Bukola ta tafl, zai nuna ma Sameera asalin dan iskayake, zai nuna mata
cewa bata iya bariki ba.
Kusan minti arba’in tayi a dakin saitatashizatatat1,anantafito da wani trinket box, sarka
da yan kunne ke ciki. Ta mika ma Sameera.
“Antygashi ba yawa” da fara’a Sameera ta karba, abin yayi mata kyau. Dama tanada bikin
wata yar yarta sai tayi amfani dashi lta ma asheta saka turaren wuta, sagem, mahallabiya
da kasko cikin leda.
“Nagode sosaiBukola, nima gawannan ki tafl da shi har kasa Bukolata duka kafln ta
karba. Abin yana bama Sameera dariya, tasan ta girme ta amma girmamawa yayi yawa.
Har kofa Sameera ta rakata saita tsaya anan ta jira ta shigadakin Laila suyisallama tukun,
a kwance ta iskeLaila a kujera.
“Anty zan tam ga wannan babu yawa” ita ma ta bata sarka amma kala daban dana
Sameera, Shima yanada kyau ainun.
Da azama ta karba ta soma budewa, a gabanta ta soma juyawa tana murmushi. Taji dadin
sa sosaitunda yafi duka na lefen ta.
“Amma na gode kamar kinsan ina neman sarka da yan kunne”
“Allahsarki Anty kuma zai maki kyau
“Sosai… Thank you so much Bukola” Laila tace.
Bukola taji dadin irin karamcin da sukayi mata, abu daya ya sake nunawa. Saif mutumin
arziki ne wanda ya iya rike gidan 53 da kyau. Sake satar kallon ginin ta tayi, dadi ya sake
mamaye tasosai,ji takeyikamar tajanyo agogoayiaurenalready. 0
Su uku, da Sameera da Laila sai Saifsuke mara mata baya. Harta kusan kaiwa gate sai ta
juya ta fara magana.
“Agaskiya Naji dadin zuwana nan gidan. Kun karrama ni fiye da tunani na. Allah ya saka
da alheri”
“Ai ba komai wallahi” Sameera tace
“Uhmm”Lailataamsa
Nisa tayi tareda dogon ajiyar zuciya, “Gaskiya Naji dadin yadda kuka hade kanku, kun
bambamta da sauran matan Hausawa. Yasainaso nima ku karbe ni hannu biyu”
Zufa ya karyo ma Saif, ‘Anzo wajen! Karya ta kare wai mallam ya kashe boka’ yace tareda
cirehularHana seller53domin yaji dama dama. o
“Mene?” Laila tace, Sameera nan take ta gane wanda Saif zai aura ne.
“Ina nan idan nima na shigoinaso mu hada kanmu baki daya banda wariya”
“Tashin duniyartsuntsaye!”Laila tace tareda fatali da kallabin ta, nan take masifa ya
turnuke ta. Annurin fuskanta ya bace kishin Saif ya soma dawainiya da ita.
” Jar uba! “
ta sake magana tana girgiza kai. Bukola bata san meyasa take haka ba, ai
tasan da zuwarta kuma tasan waye ita.
YoSaifdan lskanci shine ka kawo min kishiya har cikin daki dan raini? taga sirri na taga
komai. Wallahi bazai yiwu ba, wai Asha fate ranar sallah. Saina nuna maku ku kananan yan
iska ne”
“Ke kuma kin tabo tsuliyar dodo tunda kika ce mijina zaki so, bazaki sake samun zaman
[aflyaba.Aurenshizaizamemaki bakincanji a rayuwa,saikingwammace kidadakaratu!
“Kebansanrashinkunya, diban albarkadinki da fltsara ya tsaya kainakarkije wajen
Bukola saboda ita mace ce mai Class”
“BaClassbata zamamaischoolko University, yausainaci ubanci”saita KalleBukola Ko
agirman jiki Bukolatafita,Laila batafi lomadayadarabi bawajenta. u
“Saif baka gaya masu asalin Wacece niba halan?” Bukolatace tana kallon sa, sosakai ya
hauyi baicekomai.Yarinka fnkifiki da idanu. Rantaya bala’in baciyadda akatozartata.
“Kasanyadda bana sankarya,bana sanalakada masukarya. Shinekayimin kuma kayi
masu. What kind of life is this? A haka zan aure ka babu aminci?”
“Babe kiyi hakuri,Lailaismentallydisturbedyasabangaya ba, Kalleyaddatake zareido
verybarbaric,dab take da akaita mental asylum”Sameera taji dadinabinharda murmushi
kadan. u
“Yanzu zannunamaku hauka, idan yasosaia kaini turu a sakania mari(chains)”
“Ba abinda zakiyi, gwara ki wuce kaHn ranki ya baci”
“Saina nuna ma tsohuwar karuwar nan bata iya bariki ba, shegiya yar iska kin zo neman
gindin lama wajen kishiya. Kin girme ni nesa ba kusa kina ce mun Anty, makira kawai”
“PleaseAnty Lailaki dainazagina,banaso.Mutunci nazomuyikuma nagama.Sai
anjima”
Hanyar gate ta nufa ta ta& “Sai anjima Allah ya kiyaye” Sameera tace, juyawa tayi ta Kalle
ta tayi murmushi, ba tace komai ba sai dai taji dadin yadda bata cin mata fuska ba. Laila
zatabi sahun Bukola sai Saifyasha gabanta.
“Wallahi kika matsa sai nayi maki dukan kawo ceto”
“Ahayye nanaye an zage karuwar ka shine ranka ke baci, toh kayi kadan Saifullahi kake
kome? Dane zaka dakan amma yanzu sai dai mu dakejuna. Shege ka fasa!” Yadda take
girgiza kai zaka sha wani karfin kirki gareta. Yanzu yana bala in dana sanin auren ta. Batada
tarbiya ko kadan pretendingtakeyi kafin aurensu amma yanzu asalin halinta ya flto.
“Dan Allah Kuyi hakuri,…. Laila please ki koma daki bai dace ba”
Har Laila zatayi mata rashin kunya saita tuna kwana biyu ita take bata abinci, bata zageta
ba amma ta bita da mugayen kallo. Da sauri Saifyabi bayan Bukola domin ya bata hakuri.
lta kuma tana flta ta samuNapep ta hau, “Tudun Nufawa zaka kaini”bayanta tana shiga
Saifyagani, yanakiranta tacemamaiNapepsutafl.Wannankenan! u
an
Kamshin turaren sa wajen kala biyar da yayi amfani dashi ketashi, daga OUD, YesSaint
Laurent, Dior, Ellie Saab da Issey Miyake. Fuskan sa makale yake da tabaran sa baki na
Fendi, sanye yake cikin kananan kayan buga polo, farar riga sol na Balmain da wando kalar
zuma, sai hular base ball na Guccisannan takalmin Yeezy boots dinsa da helmet ajiye a
gefen sa. Polo stick dinsa Shima yana gefe, yau za ayi wani gasa na masu buga polo wanda
yake soyayi. Daga nan ya sake introducing kansa ga masu so su canza dollars ko pounds
yayi sabbin customers.
lta kuma Haske ta dauki alwashin yau sai sunyi magana, ko aiki bataje ba ta kira wai
batada latiya. Ayau tana sotasan matsayin ta wajen sa. Soyayyar sa addabanta yake yi,
tana bukatar sayanzu, tanaso taga murmushin sa, tanaso tayi masa hidima suna wasa da
dariya. Tanason yadda yake zuba mata shagwaba, she missesthem so much. Hawaye ta
soma sabida bataso tayi losing dinsa.
Kamshin turare yaji na Chanel No 5 da wasu na larabawa wanda take ta’ammali dasu. A
da chan zai dago yayi mata murmushi tareda janyo ta kusa dashi. Yanzu kam kememe yayi
yana danna waya, yana jiran goma da rabi yayi saiya fita yaje Fifth Chukker dake Maraba
Jos, shahararen gidan polo na Kaduna da Nijeriya baki daya.
Sanye take cikin multi colored chiffon gown wanda bai kamata ba, saita tamke gashin
kanta yanayin ponytailda kuma kadanta gaba indaya kawatamatafuska.A2 seaterda
yake zaune inda itama ta zauna, bai hanata bai kuma Kalle ta ba, TVyake kallo da waya a
tsakani. Ta kusan minti goma sha biyar batace komai ba banda kallon fuskansa, shikam ko
ajin kin sa. Yasaba ana kallon sasanda yake saurayi haka mata zasu bishi da ldanu 3
events kamar Mayu.
Hannunsa ta kama, a hankali ya kalleta sai kuma ya sake kauda kai. Murzawa takeyi tana
wasa da azurfan wajen mai ratsan baki. A hankali ta rinka matsawa gefen sa harya zamanta
babu wani spacetsakanin su watau tadin ‘no gab’ , kafarta ta daura guda daya akan jikinsa
saitarakuba dashi.Vandasuke sunajinnumfashin juna. F
Cikin karamin murya ta soma magana, “Baby dan Allah kayi hakuri, Wallahi bazan kara
ba. Katausaya min zuciyana yana barazanar fashewa… Pleaseam sorry”
‘Dama ya fashe tunda kunnen kashi gareki’ yace cikin ransa. A mi kuma yayi fuska.
Hawaye ta soma yi, kadan kadan sai gudun famfo,jinsa yayi ya soma damshi wanda ya
tabbatar mashi da cewa kuka takeyi, yaji tausayinta kadan, koba komai domin abinda ke
cikin ta.
Da Huskyvoice dinsa ya soma magana a hankali kamar bai so yayi, “Meyasa bakya jin
magana Shamsiyya?” da sauri ta dago ta Kalle shi, taji dadin yadda ya amsa ta. Ta mance
yaushe rabon da yayi mata magana, zakaga murna a fuskar ta.
Ta tsane aki mata magana, abin yana takura mata. Tafi san kayi mata fada bawai ka barta
da halinta ba. Share hawaye tayi da hannu daya.
“Wallahi na tuba, dan Allah baby kayi hak uri bazan sake ba”
Kallonta yayi cikin ido, ga rama kadan ta soma. Saiya tausaya mata kuma, hannunsa
yakai wajen fuskanta yana share mata hawaye.
“Shamsiyya na tsane wannan hawayen, amma bakyajin magana. Meyasa bazaki natsu
muji dadin soyayya ba? Meyasa bazaki bude idanun ki kiga komai kamar kowa? I love you
amma kina bani wahala, nida gidana banda iko… Kin kyauta kenan?”
Da Kai ta girgiza kai tana kuka, tanaso su daidaita. Kawai ya fadi bukatar sazatayi. Janta
yayi jinkinsa inda ta kwanta sosai, sai ya soma bugun bayanta alamar kulawa.
Pleaseki dainagardama dani dawasu halida bansan kidashiba, banasanzamanrashin
mutunci.I am trying to change,don’t unleashthe Badman in me”
“Okay In sha Allah zan kiyaye”
“Nagode Sweet
Daga nan suka shirya, watsa majuna kalamai sukayi na masoya harda saka mashi abinci
na dankali da kwai sai Sap din Acha. Da kanta tayi feeding dinsa, yadda yake murmushi
abin yafaranta mata rai. Tasamu natsuwa sosaifIye da yadda ta tsinta kanta a da chan.
RANAR KIN DILLANCI
Dama anceakwai ranar kin dillanci,ranar da babbanrigar Mai gari ta bata. Komai zakayi
kayi shi madaici, saboda kar kazo kayi dana sani daga baya. An kawo lefen Banan, daga
yan tarba harda kalan dangi Ammi. Ta matsa ma Hajia Zainab akan suje domin ayi komai a
idonta. Balleyanzuduniya yasanba ita ta haifa Shamsiyyaba karara take nuna tsanar.
Bayan an watse take sheda ma Banan ai lefen bai kai rabin na Haske ba, kuma ita harda
mota aka bata. Anan ranBanan ta soma ci zanyatsarantayayi mummunan bacita soma
neman hanyarmarda Haske kafin auren. Dariya Ammi tayi tana karkada kafa, “Dama
yarinya kallon ki kawai nike yi, amma rne za’ayi da kishiya?Ai tuntuni nace ayi mai gaba
daya amma kin tsaya sanya”
“Duk abinda za’a hada da boka Allah ya amfana” Banan tace a hankali, harara Ammi ta
watsa mata tareda zaginta cikin ranta. Anan kuma Ammi ta sheda ma Banan an saketa
kuma ta rasa aikin ta, idan ta taimaka mata aka kulla makirci zata saka Bilal ya kama mata
haya ya kuma bata dan kudin domin ta rinkajuyawa.
“Toh yanzu me kike so ayi?
“Akira Lailadukan musaia hadakamdomin a dake karfe” a
Ranar Litinin plandin zaiyi aiki. Taresukashiga motar Banan har gidan Laila. Saif baya
gida domin yayi ma Hajia mujebat bayani data gamsu, aurensa yanzu cikin sati uku kenan
rana daya dana Bilal. Yanzu tun safe yake fita baya dawowa sai dare ana hada hada komai
kar a makara. ita tana tsakar daki tana kwance daga underwear babu riga taja shi har
saman kirjinta. Babu wuta ta bude window kumata daga labulenfalo sabidaiska ya shigo
mata.
Bataji sallamadinsu basaidai ta gansu kanta kerere,da saurita mike ta fara washe baki.
“Saka kayanki yi maza” Ammi tace. Da sauri ta shiga uwar daka ta zumbula dogon riga ta
flto, zama tayi akan kujera tana kallon su.
“Look!Bawani bata lokaci, yanzu idan kikayi abinda muka ce komaizai zo mana da
sauki. Kowa zai samu abinda yake so a wuce wajen, kuma kema zaki ci 20k” Banan tace
cikin yatsina fuska.
“Koma me kuke so a shirye nake in yi” ita bawai dan kudin take yi ba duk da tana san
kudin ammakokyautanezatayi. 
“Zaki gidan Bilal ne zan maki bayani daga nan”
Shiru Laila tayi sabida Bilal ya hanata zuwa gidansa yace zai karya ta idan ya ganta, yanzu
kuma suna so su tura ta, sai dai kuma gaba take kallo. Idan aka samu nasara ita ce zata fi
kowa murna.
“Shikenan a shirye nake Allah ya bamu sa’a, in sha Allah zamu samu nasara wannan
karan. Dukbakin cikin tanda saimunciwaina”tacetaredareroflto. n
Saita wuce daki domin tasa kaya da kyau, wannan purple lace din ta dauko tunda yafi
armashi. Yama chukurkude amma hakatasa. Banan tayi tsaki yafl a kirga sabodagidanbai
mata ba, kawai danta kama dole ne.
Haske tun bakwai da rabi ta tafl aiki, Bilal kawai ke gida yana kara barci. Dama shi sai
wajen tara k0 goma yake flta. Wata rana ma har sha daya idan baida wani abin yi. Ta tafi
suna murmushi dan ya tashi sunyi breakfast tare kuma har mota ya rakata. A kofar gidan
suka ajiye Laila, dayake Bilal yasan tana tsoron sa baiyi tunanin gayama mai gadi cewa
kada ya yarda ya barta ba.
Tun tana hanya ta kira Haske wai tana hanyar gidanta, anan hankalinta ya tashi tana
kokarin hanata amma Laila ta kashe taki sauraro. Sake kira Haske tayi amma yaki shiga,
yau tasan idan Bilal yayi ido hudu da Laila saiya kusan kasheta da duka kuma bazata so
haka ba.
Nan ta tashi tana tafiya dakyar duk a birkice. Yau tata ya semeta bata san abinda Bilal
zaima Laila ba, gwara taje ta kashe wutan.
Gaban Laila duka uku uku yakeyi, ta kawo kanta makisa. Bata san me zai faru da ha ha
idan Haske bata dawo ba. Kawai fatan ta ace Haske tana mata soyayya da kowa ke
tsammani. Falo ta shiga bata ga kowa ba, anan ta zare mayafinta ta ajiye.
A hankali gabanta yana fadi ta nufa hanyar dakin Bilal, kofa ba’a gama rufewa ba. Tana
shigabata ganshi a ciki ba amma taji karar ruwa alamar yana bayi, abin yazo mata daidai
wai mai ido daya ya leka shantu. Gabanta bai daina faduwa ba saidai tanata addu’a samun
nasara.
Cire kayan jikinta tayi tana barkawa kamar tayi kokawa da wani, tanayi tana bakin ciki
saboda shi kadai ne wanda yafi armashi. Amma kuma idan ta samu nasara yafl kamn riga a
wajen ta. Daga ita sai breziya da pant ta tsaya tana jiran ya futo.
Bilal bai kawo komai ransa ba, yasan shi kadai ne gidan. Sanye ya fito da boxers sai towel
a wuya yana goge jikinsa. Gabansa yayi mugun faduwa daya ga yanayin ta. Cikin fushi ya
soma magana.
“Dan ubanki iskancin kaina kuma zaki dawo? Ni sa’anki ne?” daidai lokacin Haske ta
shiga falon tana sallama. Aikam Laila ta tsandara ihu.
“Wayyona shiga uku Bilalkayi hakuri na tuba, bazansakezuwa ba. Ni matar aure ce”
Saitaje ta chakume shitana makalkale mashiwuya, kokarin tureta yake mamaki fal ransa
za’a kulla mashi sharriidansa biyu. Da sauri Hasketayi hanyar dakin tana kwala kira.
“Laila! Lailau Laila!!!”
Sakerike Bilaltaye harda sargafo mashi kafa, shi kuma yana dukanta amma taki sakinsa.
Anan Hasketa shigacikin dakin.
“Innalillahi wa inna ilayhi rajiun” saitafasheda kuka.Anan Lailata sake shita rugabayan
Hasketana nishi. Kukaitama tasoma namunafunci. 
“Haske nagode da kika zo kika cece ni, wallahi yau da sai ya keta min haddi da aure na….
Innalillahi banyi tsammani haka halin mijinki yake bayan na dauke shi kamar danuwana”
“Sweet wallahi karki yarda da ita, sharri ne. Na rantse maki da Allah ban nemata da
komai” tsuma yakeyi duk hankalin sa a tashe. Hannu ta daga mashi dom’m yayi mata shiru,
tasan me ta gani, gyalen jikinta tasa ajikin Laila saita Kalle shi da tsana.
“Mayaudari! Makaryaci! Macuci! Mazinaci’. Azzalumi! Allah ya isa tsakanina dakai Bilal. I
cursed the day i met you wallahi. Nayi dana sanin haduwa da kai. Kuma Allah bazai barka
ba saiya bin min hakki na. I promise you zakayi dana sani haduwa dani.Yadda ka shayar
dani bakin cikin ka saina rama. Zaka gwammace kida da karatu Bilal Bello Kamfani “
Girgiza kai yakeyi, bai ma san yadda zai soma kare kansa ba, yasan me ta gani amma
kuma ba haka abin yake ba. Meyasa bazata bashi darna ya kare kansa ba? Meyasa bata
yarda dashi ba? Meyasa! Meyasal!
Wallahi Shamsiyya sharri ne, ban neme taba… Haba mana… Kalle fah abin… Me zanyi da
Laila for heaven sake… Na gaya maki rabamu take so tayi tuntuni… Karki yarda da ita… I
love you so much” saiya naushi iska tareda shafa kansa dake gumi.
“Rufe min baki, kai har ka isa kayi zancen so bayan abinda kayi. Kaci amanar soyayya
kuma ka bata mashi suna. Idan haka so yake banaso na alakanta kaina dashi.. I hate you
Bilal kuma ko gawana bazai sake zama dakai ba. Yauzan bar maka gidan ka”
Da sauri ya karasa wajenta yanaso ya rike mata hannu, matsawa baya tayi tana share
hawaye. Bilal ya cuceta ba kadan ba, dama Laila yakeso shine yake wani cika yana
batsewa. Dayake tanada kawar arziki bata basa kanta ba, da wata ce haka zaa ci amanar ta
a bayanidantalKallonLailatayi wanda take rawardaritareda kuka,anan tausayintaya
sakemamayeta.Amma yauzata nunaitayarHalasce,aurentadaBilalyakare. a
JanyehannunLailatayisukabardakin,dakinta ta komata Mikamatan wasukayasaiita
kuma ta soma hada nata. Anan murna ya rinka mamaye Laila. Aikinta yayi kyau ainun. Bilal
saka kayansa yayi da sauri, abin yayi masa zuwan bazata wai zai rasa Haske farad daya.
Yashiga dakinta yaga tana hada kaya, rike mata hannu yaje yi saita sharara mashi mashi.
“Karka kuskura ka tabani Bilal, banso na kara jin maganar da zakayi. Nasan me nagani
kuma na gane zaman mu. Idan aka bani labari zan musanta because i thought you love me,
amma ganin ka yau ya tabbatar mun da baka taba sona ba. Daga kawata tazo wajena saika
mata fyade, kai wani irin dabba ne? Matar aure ce fah? Bakada imani ne kome? Wallahi
Bilal sai kayi dana sanin abinda kaso yi, bayan ka sake ni sai mun maka ka kotu for sexual
harassment. Sai mun wulakanta ka cikin Kaduna, zaka gane cewa kudinka baida wata
amfani” kukatasakefashewadashi. ¢
Dafa wajen marin yayi yana haki, idansa yayi ja sosai, idan yace zai rama zai sakejagula
al’amarin. Cikin fushi ne kuma idan ta kwantar da hankalin ta zata gane komai. Laila ne ta
sake fashewa da kuka kamar ana kashe ta harda tari.
“Dan Allah Besty kiyi hakuri, ki yafe mashi. Karki kashe auren ki a kaina. It’s not worth it!
Mu gode ma Allah baici zarafina ba yadda yaso” saita sake barkewa. Cizan lebe Haske tayi
bakin cikin Bilal yana Cizan ta. Batasan me zatayi masa ta huta ba,jibe yadda yasa yar
mutane ta susuce sabida selfish interest dinsa.
“No Laila karki karaya, yadda yaso wulakanta ki saina rama maki. You’re the sisteri never
had. I won’t trade you for anything, ki yi shiru please zanyi maganin komai” saita Kalle inda
Bilal yake tsaye tsuru tsuru yana ganin ikon Allah. Yadda Laila tayi abin was so perfect.
Saiyasomatunanianyabashiyanemetaba?Dukwanda yagani haka zaidaukaal’amarin. 
“Fita ka bamu waje, yanzu zamu tafi. Bazan sake zama da fasiki ba… Wallahi Tallahi” da
hannu ta nuna masa hanyar kofa.
Sum sum ya bar dakin da gidan baki daya, gidansu Daddy Zailani ya wuce kai tsaye
domin ya roke alfarma. Sai yanzu ya gane kalar san dayake mata. Bazai iya rabuwa da ita
ba. Ta gama fushin ta harda duka duk ya yarda amma karta kaurace mashi.
Yana mota yana tuki hawaye masu zafin suka soma malala masa, bai hanasu ba. Ya
mance yaushe rabon da yayi kuka. Yanada taurin rai da juriya. Ba abu kadan zaisa ya karaya
ba,amma wannan fadan yanaganin yafl karfin sa,da wuyayasamunasara.
Zafl kirjinsa ke masa yana gudu da karfin gaske. Yasaba jin kaidin mace amma yau ya gani
da idansa. Bin Laila yayi da tsinuwa, duka ko yan sanda bazai fanshe mashi abinda tayi ba.
Allah ne gatan sa, shine zai kwatar mashi hakki. Yana horn gaban kofar gidan Mallam
Adamu yace Daddy baya nan.
Anan Bilal ya sake shiga cikin tashin hankali, yanzu ina zashi ya nema ceto. Sai ya tuna da
Hajia Binta. Anan ya tuka mota yaje gidan, bayan ya shiga ciki yayi parking. Yana fitowa sai
ya ganta itama zata shiga mota. Anan ya duka ya soma kuka, abinda yaga ya dace da
wannan rana kenan.
Kallon sa Mommy tayi tana nazari me yayi 22mkodai Shamsiyya ta mutu ne? Amma da
mutuwa ne zaiyi magana maimakon shirun.
“Muje ciki?”
Haka ya bita tiryan tiryan har cikin falon Mommy. Bai iya zama kujera ba kamar ba Bilal
ba. Kasaya zauna fuskan yana kallon kasa. Hawayeyakeyi haryanzu. Komaiya cunkushe
mashi,fadan nan yafl karfin sa.An rigaanyi mashi sharri, baiyi tsammani Lailazataga
annabi ba.
“Meya faru kake kuka haka kamar anyi maka mutuwa” bai ce komai ba tukun, share
hawaye yayi yana kokarin gyara muryan sa domin magana ya fito. Wai shi yake kuka akan
mace,duniyajuyijuyi. Anan ya labarta ma Mommy komai abinda ya wakana, sannan ya
gaya mata yadda Laila ta keta kokarin raba su da Ammi.
Ta yarda dana Ammi amma tanata shakkun na Laila, yadda take kiran Shamsiyya Besty
tana nuna mata sokarara abin akwai tambaya.
Su Haske sun kwashe kaya da zatayi amfani dashi na kwana biyu kafln ta aika babban
mota yazo ya tzm da sauran. Laila ta taya ta ja akwatuna uku sannan suka bama mai gadi
makulli. HaushinBilalkaruwa yakeyi mata, yanzu babu burbushin sansa saitsabaragen
kinsa dake mata yawo.
Gidansu ta koma, babu kowa a gidan sai Lantana. Fijr ta tafl aiki Aneesa ana makaranta.
Dakinta nada takai kayanta tareda taimakon Laila. Tana bala’in ganin kokarin Laila yadda
take iya motsi. Da kanta taje kitchen ta hada mata ruwan shayi daya sha kayan kamshi,
citta, na’a na’a, kanin fari da sauran su. Sannan ta soya mata kwai guda uku tunda taga
biredi a ajiye.
Dama Laila bata karya ba, nan ta zauna taci tayi nat. Haske gefe ta kwanta tana hawaye.
Batasan abinda zatayi ba, komai ya cunkushe mata. Kanta ya daina aiki, Kawai abinda ta
sani shine ta gama auren Bilal koda shine autan maza. Gwara tayita zama haka amma
bazasu sake zama inuwa daya ba.
Mommy tace mashi ya tafi zatayi ma Shamsiyya magana, tanaso taji komai tukun. Haka
gwiwa babu karfl ya tafl, gidansu na iyayen sayaje dakinsa na da. Kwanciya yayi akan kafet
yana tunani. Zuciyar sadaci yake tareda makoshinsa.Sannanjikinsa sai kyarma ya ke duk
tsigan jikinsa ya tashi. Yanzu kuma hawaye ya kaurace masa balle yaji sauki.
Shamsiyya ta koya mashi yadda zai sota tsakani da Allah, ta koya mashi yadda rayuwar sa
zatafl dadi idan tana ciki. Yanzu kuma tana so ta guje shi. Meyasa bata yarda dashi ne?
Why? Why? Why? Yaketa tambayar kansa.
Amma baida amsar tambaya kuma baida tudun dafawa, kawai yanzu yana roko da fatan
kar’a tilasta mashi akan ya saketa. Idan aka ce mashi haka rayuwa zai mashi kunci da
bala’in baki. Kuma an zalunce shi.
Sai daga baya Ammi suka lura cewa Laila batada waya balle su kirata suji update. Sun
kosa kunnensuya yayi maraba da labari mai dadin gaske. Haka sukarinka kai mari suna
kai gwauro cikin daki. Sun kasa sukuni balle su zauna. Hankalin su ya bala’in tashi, idan
basu samu nasara ba wannan karan kashen su zai bala’in bushewa.
Ammi ne tace suje gidan su tambaya a gate k0 Laila ta fita, aikam haka sukayi. Anan
Mallam Musa yace ta fita tareda Haske. Anan sukayi murna tunda abin ya nuna Haske ta
yarda. Ammi bata koma gida ba shagon Fijr ta yada zango. Kafan ace harda ita cikin zancen
Zailani yaki mayar da ita.
on.
Falon Hajia Binta karfe hudu da rabi na yamma ranar….
A kalla an kai mutane goma ne 3 zaune, Daddy Zailani a waya ya samu mummunan labari
inda ya dawo daga taflyar sa na Katsina. Sai Engr Muktar, Alhaji Bello, Hajia Lubna, Ammi,
Yayar Bilal Anty Jalila da Mijinta, sai Haske, Laila da Bilal.
An hallara ana so aji zancen abinda ya faru, Haske ne ta soma magana. Anan ta zayyana
masu yadda Bilal ke nuna bai san Laila ashe fuska biyu ne. Yana ganinta ita kadai ya far
mata. Kuka takeyi tana zayyana masu yadda ta gansa babu kaya kuma ya yaga ma Laila
nata duk da yasan tanada auren ta.
Anan Laila ta fashe da sabon kuka, yadda takeyi kowa zai tausaya mata. Banda dai kuka
bata ce komai ba tana shesheka.
Ammi ta soma kwashe mashi albarka inda Zailani ya dakatar da ita. Kotayi shiru Kota bar
wajen. Baban Bilal kunya ya soma dawainiya dashi, idan kasazai budeya hadiyeshiyafi
mashi sauki akan mugun abinda dansa yayi masa. Takaici yake sosai meya kai Bilal
wannan danyen aikin. F
Shima Bilal ya soma rantsuwa yana karyata zancen, yadda suke fuskokin su yasan babu
wanda ya gasgata shi musamman mahaifinsa. Ashe yasan yana kai yanmata gidansa idan
baya nan kawaiishiruyayi baitaba magana ba, amma kuma yayi ma matar aure fyade a
cikin gidan aurensa bazai dauka ba. Gyara murya yayi saiya soma magana.
“Shamsiyya nasan kinada hakuri, kowa ya sheda da wannan. Shine tambarin ki. Amma
idan Kinga an zalunce ki inaso ki fadi. Karki ji tsoro babu abinda zai faru dake. Bazan so kiyi
aurenwahala ba ko inda mental statedinki zaiyi tangarda”
“Ehki fada mana rnekike sodaga gare mu iyayenki?”DaddyZailaniyace
Hawaye Haske takeyi tana wasa da yatsan ta, bataso ta nuna rashin da’a tace a saketa
gatsal amma zaman gidan Bilal bazata iya ba. Saita barke da kuka kowa yana kallonta, Bilal
kuma ya sunkuyar da kai yana hawaye. Yauya tashi kwance gado daya da ita gashi yanzu
za a rabasu. Kasa kasa ta soma magana.
“Daga Allah da manzan sa sai ku iyaye nake bi. A nawa tunanin nasan bana maku musu,
baku taba tambaya wani abu daga gareni na kasa maku ba. Please ina neman alfarma ku
mar dani daga gidan shi…. Wallahi bazan samu wani natsuwa muddin ina cikin gidan ba”
“Anya kinsan abinda kike fadi kuwa, bakya soa baki lokacikiyi nazari?”Mommy tace.
Ranta yaki aminta da yanda abinya faru,tafl gasgata makirci ne na makiya. DasauriAmmi
ta chapke tana masifa.
“Tunanin me kuma? Wato ta sake zuwa ta kama shi kenan! Yarinya tace bataso ana dole”
anan Haske taji wani sanyi a ranta. A rana na farko Ammi ta nuna ita uwa ce gareta kuma
tana kokarin kwatan mata yanci.
“Kawai naga abin yayi sauri ne” Mommy tace
“Yata yanzu zaki guje mu?” Hajia Lubna tace sabida harga Allah tana san shamsiyya.
Kuma indai zance aka hada da Laila tasan karya ne amma babu halin magana kaf’lnAlhaji
Belloya saba mata akan tursasa auren Banan. Kukan Haskeya saketsananta dataga basu
so su taimaka mata. Meyasa suke mata haka? Sai kace ba mata ba? Yazasuyi idan sune
sukaga mazajen su babu kaya zasuyi raping kawayen su? Babu wani mahaluki dayake
ganin kwatankwacin tashin hankali irin nata. Bayan cin amana akwai rainin wayo a cfkin
lamarin.
“Nifa bazan sake matana ba” yace kasa kasa, kowa sai ya maida hankali akan sa. Hawaye
ya shareyana kalIon kasa kamaryadda yayi tun farko.
“Saika saketa! Tunda ba’a aure dole” Ammi tace cikin masifa.
“Mu zuba!”ya mayar mata. Zatayi magana saiAlhaji Belloya chapke.
“Bilal idan kayarda ni na haife ka, ina soka tausaya ma yarinya ka sallameta”
“A’a baza ayi haka ba!” Zailani yace
“Aikam baiyi kyau ba” Engr Yace
“Aa karmu zalunceyarinya. Bamu zamu zauna mata dashi ba. Ba’a dole a aure, wannan
kawai ne abinda zai kawo mata kwanciyar hankali. Aiba duka za’a yanke ba. Daya zaiyi idan
sunada rabo zasukoma tare”Alhaji Belloyamayar
“Amma abinda kejikinta fah? Ta kusan haihuwa” Mommy tace cikin damuwa.
“Ni fa bazan sake matata ba!” saiya fashe da kuka.
“DanAllah Kuyi hakuri duka, Naji ni mai laifi ne. Kuyafe min ku barni da ita” saiyatashi
yakoma gaban Haske yaduka, harde hannunsa yayialamarroko “DanAllahkiyafemin, na
dauka duk wani laifl da kika daura min. Maybe subconsciouslylaifi nane. Amma kiyi hakuri
muje gida mu raine babyn mu. I promiseto be a better husband,wanda zakiyi alfahari
dashi, bazansake bata maki rai ba.Abinda kike sozan maki…. Pleaseshamsiyya karki rabu
dani…l need…”
Kai dalla rufe ma mutane baki…. Tace batayi Kanata bata mana lokaci” Ammi tace cikin
tsiwa. Bilal ya dago idansa jajaye ya sauke akan nata, magana yakeyi kamar baiso yayi
saboda gajiya.
Kiyi hakuri Ammi kema ki yafe min, k0 me nayi maki ko shamsiyya tayi maki kiyihakuri ki
bar mu tare. Dan san Annabi ki daina kokarin rabamu. Wallahi harga Allah ina santa kuma
bazan bata mata rai da gangan ba”
Mommy ta goge hawaye dake kokarin mo mata, Bilalya bata tausayi. Bata taba ganinsa a
haka ba kuma ba komai bane illa soyayyadake dawainiya dashi. Kodayayi abinda Haske
tace tanaso ta yafe mashi, tana kyautata zaton bazai kara ba. Asalin nadama yakeyi.
“Haske karki kashe aurenki a kaina, na yafe ma Bilal Laila ace cikin kuka. Hannun xa
Hasketa rike tareda matsawa irin karta damu tasan me akeyi. Wannan shine nasararsu.
Alhaji Bello ya soma magana, kanaji kasan babu wasa. “Bilal bansan taurin kai. Na
umurce ka akan ka sawwake mata, idan yaso daga baya ayi sulhu. ldan ba haka ba zan
dauki mataki akan ka”
“Abba kayi hakuri Dan Allah” saiya fashe da kuka
“l’m warning you, karna kara magana”
RanBilal yanakuna, dama yankeharshen saakayi da aceyafada mummunanabinnan.
Runtse idoyayi, “Nasake kisakidaya” a
“lnnalillahi wa inna ilayhi rajiun” Mommy tace tareda Umma.
Mikewa tsaye yayi ya Kal|e Laila, “Bazan yafe maki ha, Allah saiya kwatan min hakki na”
yace saiya barfalon a sittin. Mommy ta fashe da kuka saita kashita wuce daki, Umma kuma
tasomahawaye. DaddyZailaniranshibaisoba.Masu murnadagaHaske, Ammi daLaila. a
n.
A parking lot Haske taga kamar Laila da Ammi sun tafa, amma kuma ta mayar da abin gizo
ne. Bazaiyiwu hakan ta faru ba.
Suna shiga motar Haske zasu koma gidan iyayenta. Laila dake kuka kamar wanda zata
mututawashefuska. Radiotakunna inda akasakawakar Rihanna What’s MyName. 9
Nanta soma rerowa baiti baiti tana rangaji, duniyayayi mata fes. Hakonta ya cinma
ruwa, Haskean bar gidan Bilal. Batataba tsammani akwai newsdayafiwannan dadinjiba.
Tasotanadawaya tatura socialmediakowayasani. a
Desukaisagidansunadaki, murnar dake fuskanta baya boyuwa. Tohdama Ammi

ta

bata karamar Nokiadaga wajen Banansabodata somaamfani dashi.
Hasketa shiga kitchendomin ta kawo masuabinci kaf lnta mayar da Lailagida, ta sakaa
tray ta dawo saitaji abinda yafl katfln kunnen ta. Shewa Laila keyi tana magana
” Haba Bestyai na iyadrama, yadda na rinka kuka ina turjewa dole ta rude.Anan ta nace
saiya saketa” 9
“Yanzu kina nufin Bilal baida mata ni kadai zan zauna?”
“Sosai ma kuwa, bar shegiya ita a dole tayi abin arziki. Zataci ubanta”
“Hehehe! Amma Laila bakida kyau! Aji tsoron ki saboda na Sara maki!”
“Haba me nayi? Yiwa kai ne! Yanzu tunda ta kaso aurenta banida sauran matsala, ko
ganina bazata sake ba donni bana hulda da zaurawa” sai suka fashe da dariya su biyu.
Anan Haske ta shiga idonta fal da hawaye.
Jikinta ya soma rawa, a tsorace Laila ta sake wayan amma dayake Nokia ne baiyi komai
ba. Bataso dataji yanzu ba ko a haka, muryanta yana rawa sosai.
“Laiiillllaa! Da gaske ne abinda Naji? Bilal was right! Sharri kikayi masa?” tajera mata
tambaya murya yanasarkewa. p
‘a tsaya kiji…” tace a tsorace. Sai kuma ta dake. Wulla idanu tayi tareda yatsina fuska.
Dankwalin kanta ta tura saman goshi ta chugalo shi.
“Ehen sai me? An rabaki da mijinki kiyi kutumar uban da zakiyi” tace.
Anan komai ya so ma zuwan ma Haske. Yadda komai ke tame sai yanzu ta gani akwai
alamar tambaya a ciki.Abubuwa da dama yanzuta fahimci cewaba alheri Laila ke nufanta
dashi. II
Jikinta ya cigaba da rawa, gabanta ya sake mummunan fadi data tuna cewa ta kashe
auren ta. Fuskan Bilal take gani yadda yake hawaye tareda daukar laifin da baiyi duk akan
ta hakura karta gujeshi. Yaddaya dageakan nuna mata asalinkalan Laila, asheshinemai
santa ba Laila ba. How could be be so naive and stupid? Harda marin satayi akan Laila
ashe ita ce babbanjaka.
Maganar Lailataji yana dukan mata dodon kunne, “Bari nagaya maki shamsiyya”
Ikon Allah! Yaushamsiyya ma!” ace saita ajiye tray akan bedsidedrawer. Harara Lailata
bita dashi, kana gani kasan da gaske ne.
“shamsiyya tunda nake bawai kina burge niba ne, Kin flye nuna natsuwa da kamala. Ga
tsabaragen wulakanci wai aceduk wanda nake sosunasanki. Kinsan lrin sandanayi ma
Badman tun daga lnstagram amma yana ganinki ya rude, ko nan Saif inace ke ya fara nema
kikayi mashi fuska. Am always second a gefen ki banida wani daraja”
“Shine zaki rabani da Bilal?Haba Laila mijina fah! “
tace hawayen yana bin mata fuska.
“Bani na raba ku ba, tsabaragen taurin kanki ya raba ku. Tunda na lura kejaka ce sai
mukayi amfanidadaman daAmmi daBanan” a
Kallonta Haske tayi tanaso ta tambaya da hada hannunta cikin auro ma Bilal mata, amma
kuma ta kasa.Yanzukomai Bilalyake fadi ya zama daidai. MeyasaLailatayi haka?Wannan
wani irin rayuwa ne? Idan beta santa ai ba a kawance dole? Why fake a miserable life tana
zaunedaitaammabata jindadi. p
Dana sanin abinda tayi ma Bilal ta soma, yanzu ta ina zata shawo kansa bayan yadda taci
zaram sa harda mari. Zatayi magana sai kanta ya soma juyawa mata, ciwo yake mata tun
safe take fama dashi, a hankali ta fara lumshe ido saita ta fara layi, anan ta zube
summammiya. 9
Da Sauri Lailata bude purse dinta raga 7k ta kwashe, saita bude akwati ta dauki leshi
guda biyu domin rage zafi, sannan kuma da dan kunnen gold din kunnen ta sai tayi waje a
sittin. a
Fijr an dawo ana bala’i da mai napep akan canji, saiga Laila ta Fire a hargitse kamar bible
din Hausa. Anan tabi titi a guje Fijr na mata magana bata amsa ba. Barin ma mai napep tayi
dari biyar tashigacikin gidan. P
AsheLantana taga fitan Laila,itama taje dakin da gudu. A kasa taga Haskekwance a kasa
babu alamar rai ajikinta.
“Anty! Anty!! Anty!!!” Lantanake fadi tana kuka tareda girgiza shamsiyyawanda bata
motsi.
Fijrda ta mance rabon datayi salati idan abu ya faru banda kwarara ihu k0 ashar, flrfito da
idanu tayi gabanta sai tsinkewa yake “Innalillahi wa inna ilayhi rajiun!” ta soma nanatawa.
Laila tazamaajalin Haskekamar yaddataketsammani. Wannankenan! 

Hmm ya abin yake ne laila tayi babban butulci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *