JUYIN RAYUWA CHAPTER B
..Sosai jikin Zainabu ya kama 6ari! Sabo da tsananin tsoron abunda zai faru , gashi yau mahaifin ta mai tare matan baya gida.+
Tsawa! Laitana ta sake dakawa Zainabu, “bakya jinane?” , Ko ba dake nake magana bah?”.
Zainabu cikin rawan murya! tace “daman tulunne ya fashe….
“Kan uban nan ya meye ?”.
“Fashewa yayi Zaibanu ta maimaita zancen .
“Kika fasa dai dan ubanki , kuma wallahi biyana zakiyi shegiya bak’ar muna fuka wanda batason ci gabana, karuwancin da kike yi ake zagina bai isheki ba sai kin had’a da bak’ar muguntan baki kin cutar dani , wallahi biya zakiyi bakya min sana’an komai dan haka bazan d’au asara ba , ki fita ki nemon kud’in siyan tulu , saboda bak’ar muguntan kije birni ki ringa yin aikatau ki samo kud’i ma kunk’i keda mahaifin ki ,dake duk muguntan ne a ranku , wai ke y’ar boko sai kici bokon ai , boko ko karuwanci ohoo! ga yawon bokon naki ai yanda ya jama gidan nan bak’in jini Kuluwa ko zuwa neman auren ta ba’ayi sanadin bokon naki ance gidan karuwai ne….
Zainabu ta bu6e baki zatayi magana , Lantana ta jifo mata wani k’aton dutsi tas kake ji ya sauk’a a fiskan Zainabu , ihu! tasa tare da ficewa a gidan , kafin kace meye wannan jini ya jik’a hijab d’in nata gaba d’aya , kid’imewa Zainabu tayi tama rasa meye zata yi Sam , rik’e gun kawai tayi tare da ci gaba da kukan ta…
Ahmed ne ya fito daga nasu gidan , ganin zainabu cikin wani yana yi yasa shi zuwa inda take cikin sauri , “subhalallahi zainab…
Dak’er ta d’aga Kai ta dubeshi sannan ta mayar sabo da jinin da yakai zuba , hanun ta ya rik’o tare da shigar ta gidan su , ina Larai ce ta d’ibo ruba aka wankewa zainabu gun ciwon suna mata addu ‘an Allah ya kawo mata k’arshen wannan lamarin dan ba sabon abune agunsu ba daman sun saba gani.
Inna Larai ne ta tanbayi Zainabu abunda ya faru , bayan ta fad’a mata ne ta bata wani tulun tare da zuba mata ruwa aciki , zainabu d’auka tayi sannan tayi godiya tabar gidan…
Asanyaye Ahmed yake bin zainabu da kallo idan sa fal gawaye , bayason ganin yarinyan cikin damuwa iya matuk’ar sonta kuma yana da niyyan auren ta insha Allah.
Inna Larai ce ta juyo ta dubi D’an nata da duk yanayin sa ya Sanja , “Ahmed ta Kira sunan sa.
Ahankali ya juyo yana dubanta , ba tare da ya amsa bah.
“Agaskiya lokaci yayi da zaka fidda yarinyan nan cikin damuwa , kaga dai ta kammala karatun nata ko.
“A’a Inna bata gamaba futu tazo saidai a wannan shekaran zata yi paper .
STORY CONTINUES BELOW

“Da saura kenan?”.
“Eh Inna akwai saura…
“Naji duk da hakan dai zan baka shawara , kaga koda ta gaman ai baka da yanda zaka yi kuyi aure tunda ba kud’i , mezai hana ka tafi birni kaya sana’a muga me Allah zaiyi ,Amma kai ya kagani?”.
“Ba komai Inna zanyi shawara mugani , can birnin ne inba kasan wani ba wuya kawai zakasha kuma kinga ban ta6a yunk’urin zuwa ba ina rayuwa na a inda Allah ya ajiye ni , sana din zuwa na birnin kaduna ma sabo da kaiwa zainab ziyara ne a can makarantan nasu kema kinsan haka Inna…
“Na sani Amma yanzu dole zaka je neman kud’i can , dan ko baka da yanda za kayi ka auri yarinyan nan tunda baka da wata sana ar kirki in banda saida rake kuma jarin nawa ma yake gaba d’aya….
“Allah dai yasa mu dace kawai Inna.
“Amin ta amsa .
Ahmed ficewa yayi a gidan zuciyar sa d’auke da tinani kala kala nayan da zai samu ya auri zainab a halin yanzu….
*Waye Ahmed*?”
Ahmed shine mutun na farko da zainabu ta saki jiki da shi a cikin maza , yana bata kulawa tun tana k’arama akwai shak’uwa mai k’arfi a tsakanin su , bayan ta girma kuma abun ya juye da Soo , suna matuk’ar son junan su , Ahmed ya raini zainabu tun tana k’arama sakamakon lnna Larai da take shiga har wajen Lantana ta d’auko zainabu , duk yanda Lantana taso hana faruwan hakan ta kasa , tana jin haushin kulawan da zainabu take samu daga wannan bayin Allah saidai bayanda ta iya , Ahmed yana d’awai niya da zainabu tun tana k’arama , yana dai mata Soo , K’auna ga kuma tausayi, hakan yasa malam Garba bawa Ahmed auren zainabu tunda jumawa lokaci kawai ake jira…
Shima Ahmed maraya ne , bashida uba Allah ya yiwa mahaifin sa rasuwa tun yana k’arami da mahaifiyar sa ya bud’i ido tun yana k’arami haka suka rayu da mahaifiyar sa cikin rufin asiri yana kuma kyautata mata sosai….
Kuluwa ne tare da Delu suke tafe suna tattaunawa akan lamarin aure da ya kasa yiwuwa musu , duk k’annensu ma sunyi aure sun haifu bare kuma sa an ninsu, tun abun baya damun su harya fara damun su , koda samari basayi bare ma susa ran zasuyi auren , “hmmm! Kina ga anya ba asiri aka mana bah?”, Cewar Kuluwa.
“Toh ni kam lamarin nan ya isheni , Allah ya gani inason nayi aure dan abun sha awa yake bani cewar Delu.
Hmmm! “Keh nifa inason yi ko dan sha awan da take damuna , na gaji da zaman gidan mu gashi duk samarin k’auyen nan tsoron mu suke ji , kai mata da maza duk suna shakkan mu taya zasu zoo beman auran mu tab ai abune mai wuya , nidai na fara tinanin komawa birni kozan samu miji kinga anan duk gulman mu akeyi saboda girman mu, ba gara waccan shegiyar ba ta 6uge da boko kuma koda ta gama ga miji a hanu shiysa ba a wani zancen ta tunda bata zama a k’auyen nan…
“Hakane kam nifa inason zuwa birnin nan kodan nahau mota , keh nifa nayi dana sanin rashin yin bokon nan yanzu ba gashi ba ita zainabu ta zama y’ar gaye , muko ki dubi jikin mu fah…
“Dallah meye abun sha awa a karuwan ci ?” , Wallahi bata burge ni Sam , inason zuwa birni Amma ba yawon karuwan ci irin na shegiyar nan bah…
“Hakane mu yita addu’ah dai kawai , yanzu na dage da sallah ai..
“Keh Nima na fara ai cewar Kuluwa, saidai bansan meye ake fad’i ba idan an sunkuya ko an kifuu…
Delu dariya tasa! Tab nikam dai na iya.
“Laaaah toh koya min cewar Kuluwa.
“Toh kinga idan kinyi sunkuyo , sai kice murgiw murgiw , sakkar sakkar , idan kinje kifuwa kuma sai kice d’adu na mud’al , shikenan fah.
“Ai ko dai na gode , zanna yi…
Sallama sukayi kowa ya kama gabansa .
Bayan komawan zainabu gida takai ruwa Baba Lantana bata wani damu da ciwon da tajiwa zainabu bah saima wani tilin wanki data tara mata akan tayi , bayan da ta iya dole ta kwashi kayan ta nufi rafi wanki…
Kamar daga sama taji muryan masoyin bata wato Ahmed , kirarin nan da yake mata a koda yaushe yanzun ma shi ya shiga mata.
Doguwa fara kyakkyawa , zuciya fara mai farar aniya mata a gidan Ahmed Allah ya cika mana burinmu ga zarah ga wata ba abunda zai rabamu sai mutuwa, daman k’awar ki Safina ce tacemin ta ganki zaki wanki shiysa nazo nan , ga wannan zoben sayo miki nayi , maza kawo hanun ki muga.
Ba musu ta mik’a hanunta yasa mata zoben , godiya sosai ta shiga masa , shiya tayata wanke har suka gama sannan ya rako ta har gida ya wuce inda zaije….
Bayan kwana biyu zainabu ta had’a kayan ta takoma skull, cikin farin ciki dan bata wani shan wuya acan komai ana mata dan ko zuwa skull d’in scholarship ne ta samu sabo da k’ok’arinta , duk da cewa zainab tana da k’awaye wayayyu yaran masu kud’i , kuma suna jida ita saidai hakan baisa ta juyawa saurayin ta Ahmed baya bah…
*Sultana* d’aki ta koma taci gaba da kukan ta ga ba wanda zata bawa labari taji sanyi , wayan tane ya shiga k’ara ganin Sultan ke k’ira yasa ta d’auka da sauri tare da sake mar kuka , cikin tashin hankali yake tanbayan ko lafiya me ya faru?”…
Sultana bata 6oyemar komai ba cikin abunda ke faruwa , shima ya shiga damuwa cikin k’ank’anin lakaci ya mata transfer d’in 50 k , saida yayi ta rarrashin ta sannan sukayi sallama ya katse wayan…
Washe gari Daddy kamar an tsikare sa ya farka a bacci , bawan da ya fad’o masa aran sa sai Sultana , wayan sa ya jawo ya Kira ta saidai har tayi ringing ta gama ba a d’auka ba , sake Kira yayi a karo na biyu a sanyaye Sultana ta d’au wayan tare da samar kuka , cikin tashin hankali yake tanbayan ta abunda ya faru dan shi abunda yayi kamar ma baya cikin haiyacinsa , saida ta k’ara tinamar ya shiga damuwa ya kuma ce mata gobe zai dawo insha Allah, suna gama wayan ne be tsaya bata lokaci ba ya mata transfer na 500 k…
Mamy ya Kira ya hau masifa wai Sultana ba lafiya har kwana biyu amma a rasa mai kaita asibiti wallahi idan sukayi wasa zai zama a bakin auren su…
Yana kashewa ya kira momy , nan ma masifan yayi dai .
Momy bata yi shiru ba itama tahau dokin zuciya ta ringa ramawa , bai tsaya 6ata lokaci ba yace ya sake ta , sannan ya katse wayan .
Bai iya Kiran momy faty bakam dan tsoron ta yake ji….momy cikin tashin hankali ta nufi d’akin momy dan ta rasa ma meyake mata dad’i , zaune ta samu mamy tana ninke kaya cikin sauri ta k’ariso d’akin tare da cewa “ke ma ya sake kin neh?”.+
Cikin rashin fahinta mamy ke bin momy da kallo , ” momyn yara bangane me kike nufi bah.
“Ba komai Alhaji ne ya sake ni , nad’au ka kema sakin naki yayi da naga kina tattara kaya.
“Subhalallahi innalillahi saki fa kike ceh?” .
“Eh saki na yayi , sabo da y’ar gold babu lafiya ba’a kaita asibiti ba , yace na kaita nace mar bazan Kai bah , wallahi mamy yara abunne da bak’in ciki bafa musan bata da lafiya tunda ba shigowa gunmu take ba , sannan ko da zamu bugi juna da Sultana akan hanya baza ta ko d’aga Kai ta dubemu ba bare ma ayi zancen girmamawa ko bada hak’uri , bata ganin mu da mutunci muda yaran mu duk ta hana amana komai , kuma duk mun hak’ara mun zauna muna hak’uri shine yau kuma ya k’aramin da saki…
“Tab toh ai wallahi tare zamu tafi nima banga ta zama bah.
“A’a baza ayi haka bah , ki zauna tunda ke bai sake ki bah, idan kika tafi zaki sake jefa yaran namu cikin tashin hankali ki zauna Allah na tare damu kuma zai kawo mana mafita…
“Yanzu namarin Alhaji har yakai haka?” , Allah yasan me yarinyan nan ta fad’a mar , daga yara mai kamar tayau na sake cire Sultana cikin jerin yaran da na haifa , ba’ana na yafe ta babu ita babu ni banyarda tazo inda nake bah ni ba Uwar ta bane , nayi dana sanin haifuwan ta dama cikin zubewa yayi….
Da sauri momy ta rufewa mamy baki , tare da cewa” baki da hankali ne ?” , Ko kin haukace ne kefa kika haifi Sultana kawai ki mata addu ‘ah , Allah ya shirya mana ita.
Tana kaiwa nan bata jira meye mamy zata k’ara cewa bah ta fice daga d’akin .
Ko da su Husna suka dawo daga skull haka suka tarar da wannan mummunan labarin sunsha kuka ba yanda suka iya dole suka yi shiru , sunku ma sake jin tsanan Sultana a cikin ransu baka d’anbah.
Bayan Sultana taji shigowan alert , ya mutsa fiska tayi tare da jawo wayan ta taduba , ganin daddy d’in ta ne ya turo kud’i yasa tajan tsaki ta sannan a zahiri ta furta “aikin banza in danma ka goge laifinka ne kaban kud’i masu yawa haka Sam baka burgeni bah , tunda har million ka bawa agola a gabana ni kuma ka hanan ko naira .
Daddy dctr ya kira akan yaje gida ya duba Sultana, ana wani d’au lokaci ba kuwa dctr yazo gidan , kai tsaye yaje site d’in momy faty dan ancemar acan ne Sultana take , koda yaje momy faty cewa tayi ai zainab ce bbu lafiya ba Sultana bah , dole ya duba zainab d’in da kuma yace a Kira Sultana Sam tace ya bari kawai karya da damu , ba yanda ya iya dole ya tafi Amma ba hakan yaso ba dan shi kanta yanason ganin yarinyan dan kuwa yana son tah, bayan ya fita ne yayi waya ya shaida wa Alhaji abunda ya furu , hankalin daddy ya tashi baiji dad’i bah ya kuma yanke shawaran dawowa gidan zuwa gobe tunda duk gidan bbu mai kulamar da y’ar tasa…
STORY CONTINUES BELOW

Washe gari da sassafe daddy ya sauk’a a kano ba tare da yayi shawara da kowa bah , d’akin Sultana ya fara nufa saidai ya jima yana nocking amma shiru ba ‘a bud’e ba , parlor ya koma ya zauna yana jiran tashin d’iyar tasa daga bacci , wayan sa ya zaro ya shiga Kiran number d’in ta amma a kashe , text ya tura mata akan idan ta farka ta sauk’o zasu je hospital…
9:am Sultana ta farka sai a lokacin tayi sallan asuba , wayan ta tafara kunna text d’in daddy d’in ta shiya fara shigowa ,da sauri ta shiga ta duba mik’ewa tayi dan tayi missing daddyn nata tanason ganin sa kaya tasa cikin sauri sannan ta nufi parlor zaune ta sameshi yana duba wasu takaddu yana ganin ta ya ajiye da sauri yana binta da kallo sannu ya shiga jera mata ganin duk ta rame lokaci d’aya , Sultana sake narkewa tayi tana ci gaba da kuka daddy ya jima yana rarrashin ta kafin tayi shiru , asibitin suka je aka dubata sosai harda k’arin ruwa aka mata , acan daddy ya barta shi ya dawo gida domin nema mata abunda zata ci , Sam momy faty bata san Alhaji ya dawo gidan ba sai data gansa kamar daga sama duk rud’ewa tayi tana tanbayan sa ko lafiya ya dawoo yau sannan dawowa babu sanar wa🤔.
Bai tsaya kulata ba ya nufi site din masu aiki domin gabatar da abunda ya kawo sa , ba’a wani d’au lokaci ba aka had’amar duk kan abunda yace…
Parlon ya dawo fiskan nan a had’e babu alamar wasa ko dariya momy faty ya kalla da take ta faman lalla6a Zainab akan taci abinci , harara ya watsa mata tare da cewa maza kije gidan ku ki futa saina nemeki…
“What me kace ?” akan meye zanje gidan mu ?” Wani laifin nama ko yaya ?”.
“Bansani ba , karku ma na dawo na sameki a cikin gidan nan , daman ai na auro ki sabo da kulawa da Sultana tunda baza ki iya ba ai saiki tafi gidan ku , wallahi idan yarinyan nan ta mutu kema dole ki bak’unci lahira Bari kiji…
Yana kaiwa nan yasa kai ya fice daga gidan, 6angaren mamy yaje ya shaida mata Sultana tana asibiti tazo suje , amma ga mamakin sa sai cewa tayi baza taba dan tacire Sultana a jerin yaran tah, dole ya tafi yabar mamy dan bazai iya d’aukan mataki a kanta ba sabo da itace sanadin zuwan Sultana duniya….
Kwanan Sultana d’aya a hospital aka sallameta ta dawo gida , sosai daddy yake lalla6a Sultana harta ware sosai .
Yauma kaman kullun daddy yasa Sultana a gaba yana ta faman lalla6ata akan tayi hak’uri taci gaba da skull , amma Sam tak’i , ko daya takura mata ma akan dole zatayin cewa tayi sam ita aure zata yi .
Zaro ido waje! daddy yayi tare da cewa aure fa kikace” .
“Yes daddy aure zanyi…
Sam bazan miki aure ba kinyi k’arama…
Mik’ewa Sultana tayi tare da cewa idan baka min aure ba zaka ga abunda idon ka bazai Soo gani ba ina fatan baza kayi danasanin hakan bah…tana kaiwa nan tasa kai tabar d’akin.
Daddy ya shiga tashin hankali sosai idon sa yayi jah , babu abunda jikin sa yake yi sai 6ari , shi Sultana take fad’awa wannan kalla shine sakamakon son da yake mata ?” Kawai sai yaji hawaye na zuba mar…
Haka ciwon Kai mai tsanani ya rufe shi saboda jinin sa da hau , dctr ya kira ya dubasa sannan ya basa magani ya kuma ce ya rage damuwa saboda jinin yahau sosai .
Daddy abokin sa ya Kira domin su tattauna akan matsalan Sultana , bai 6oyewa Alhaji Jameel komai ba akan matsalan da yake ciki yana basa labarin yana hawaye kaman wani k’aramin yaroo.
Gyaran murya Alhaji Jameel yayi sannan ya fara magana, “wannan shi ake kira illan gata , daman kullun ina cema kabar nuna mata mummunan so irin wannan Amma bakaji , yanzu ina ranan irin wannan lamari baka isa kasa yaro ba ko ka hanasa Allah dai yasa mu dace , tunda har ta bu6i baki tace aure take so ina ga amatan kawai zaifi , akwai yaron wajena zan turo sa yazo suga juna sai muga mai Allah zaiyi…
“Toh shikenan aikuwa naji dad’in hakan Kai ko bataso Allah indai tamar bashi zanyi yafi ta lalace ai ko ya ka gani?”.
A’a mudai bi komai a hankali kasan d’an yau ba a iya masa, hakane sallama suka yi sannan ya wuce gida.
Momy faty tun bayan tafiyan ta bata zauna ba , gun malamai kala kala ta ringa zuwa ita dai kawai ta samu ta koma gidan ta sannan ta mallake mijin shine burinta , bata wani damu da kud’in da take cirewa ba indai buk’ata zata biya ai shikenan , takuma shirya tsaf yanda zata yiwa Sultana shigo shigo ba zurfi…
Daddy bai sake bi takan Sultana ba , bai kuma bata labarin zata yi bak’o ba saida yanma tayi bak’o ya zo gidan sannan daddy ya shiga da kansa yace tayi maza ta fito ana jiran ta…
Cikin rashin fahinta Sultana kebin daddy da kallo , sannan tace “ni kuma?”.
“Eh keh , daddy ya bata amsa a takaice.
Sultana ganin daddy babu alaman wasa a tattare dashi yasa ta mik’ewa tana turo baki ta fito parlor , zaune ta samu Al’ameen tun kafin ta iso yake ta faman doka murmushi harta k’ariso gun.
Waje Sultana ta samu ta zauna d’an nesa dashi , sannan ta maida hankalin ta kan tv taci gaba da kallo , d’aya daga cikin masu aikin gidan ne ta shigo d’auke da tire Wanda aka shak’e sa da kayan ciye ciye , cikin rashin fahinta Sultana ta dubi murja tace “wannan fah?”.
“Daman cewa akayi na kawo nan wai kina da bak’o .
Tsawa! Sultana ta bugawa murja , maza d’auki ki 6acemin anan banzaye marasa tinani ko ina bak’on ohooo…
Da sauri murja tabar parlor din jikin ta har 6ari yake.
Al’ameen ya dubi Sultana yace “toh fah , ikon Allah ke baiwar Allah mai yayi zafi haka?”.
Da sauri Sultana ta sa gyalen ta ta toshe hanci tare da cewa ubanka ne yayi zafi , Wawa jaki k’azamin banza…………..Cikin mamaki Al’ameen ya kebin Sultana da kallo dan yama rasa abun cewa, “ahankali ya furta ashe baki da tarbiya?”.+
“Yes banda shi kasan ubanka baimin ba , tak’arasa maganan tana mik’ewa zata bar parlon.
Tsaki kawai Al’ameen yaja dan mahaukaciya yad’au ki Sultana , tabbas mai hankali bazai yi hakan bah , kansa ya fara tanbaya shin mai daddy yake nufi?” , Mahaukaciya zai aura mar ?” , a’a wallahi sam bazai yiwuba ya bawa kansa amsa.
Bayan fitan Al’ameen gudu kawai yake yi da mota dan baik’ima ya gansa a gida bah , yakoci sa’a mahaifin nasa na gida , Alhaji jameel ganin D’an nasa ya sashi gyara zama sannan yace “Baba nah iso nan mana , harka dawa da wuri haka?”, Ina fatan dai babu wata matsala dan banason abun ya d’au lokaci , daman nima nafison kayi auren kodan naga jikoki na tun ina raye….
Al’ameen tsumewa yayi ya 6ata rai bai koma ce komai bah , saida Alhaji Jameel ya sake magana “wai baka jinane kayi shiru?”.
“Ina jinka daddy abun cewan ne bbu.
“Kamar yaya babu ?” .
“Toh daddy tsakani da Allah dai ya za’ayi ka turani gun mahaukaciya , kuma kace ita zan aura?” .
“Daddy ido ya zaro mahaukaciya kuma?” , Kaci gidan ku, ingo naka…
Al’ameen bai wani damu ba ya ci gaba da magana , Daddy ya zaka tura ni wajen da za’a raina ni babu abunda nafi tsana kamar raini , amma yau k’aramar yarinya ta bu6e baki ta zageni , wallahi da bankai zuciya nesa ba da saina 6allata , aikin banza mtsw yaje tsaki…
Alhaji Jameel yasan halin d’an sa sosai kuma yasan bazai mata k’arya ba hakan yasa shi yarda da abunda d’an nasa yace mar , dan inda bata marba ne dazai fad’a, “ohk ba damuwa zanyi magana da mahaifin nata karka damu…
Al’ameen bai k’ara cewa komai ba ya mik’e yabar parlon, daman yana da wanda yake so kawai yaje ne sabo da tsananin biyayya irin nasa.
Sultana tana mik’ewa d’aki ta fad’a , cikin tsananin 6acin rai , tanbayoyi ta ringa jera wa kanta wanda babu amsa, waye wannan kuma?” , Mezai mata?” Me daddy ya turo sa yi?” Ko auren dole zai mata neh?”, Waje ta nema ta zauna tama rasa abunda yake mata d’aki…
Daddy ne yayi sallama ya shigo d’akin , Amina ya kira sunan ta , cikin sauri Sultana ta d’aga Kai tana duban Daddy , cikin ranta tasake furta kalman sa Amina ?” , dan tunda take da daddy bai ta6a kiran sunan ba saidai cikin kuskure , tsawa! ya buga mata bakya jinane ?”, ya kikayi da bak’on me kuma kika mar?”.
Sultana ganin bbu wasa a fiskan mahaifin nata yasa ta fara kame kame uhm! Uhm! “daman…
“Daman meye ?” , Ya sake daka mata tsawa .
STORY CONTINUES BELOW

Shiru yayi kuma ni bansa Shiba , dan namar magana ya min tsawa , shine na cemar k’azami…
Hmmm! Kawai daddy ya furta tare da barin d’akin ,idan yayi wasa Sultana zata kashe shi, kwana biyu bai sake bi ta kanta ba domin kuwa Alhaji Jameel ya cemar yaron Sam yak’i yace mar ya fasa saboda yarinyan ta zagesa , daddy bai wani damu ba ya shiga bin bayan Sultana wai suyi hak’uri ai yarinta ne yake damun Sultana , Sam Alhaji Jameel yace wannan ba yarinta bane amma tunda yabi bayan d’iyar sa shi bazai yiwa d’ansa dole bah , haka dai suka rabu baran baran cikin fishi tunda kowa ya nuna d’ansa yake Soo…
Daddy ya dawo da momy faty , awannn karon ma tasake jan Sultana a jiki tare da bata mugayen shawara akan mahaifin nata , ita ko Sultana sarkin hauka duk abunda momy faty ta sata yi takeyi rashin kunya kuwa ya ninka na da , duk gidan bata ganin mutuncin kowa idan ka cire daddy duk da cewa yanzu ya rage nuna mata wannan mummunan so din , tsakanin ta da mamy kuwa sai ido domin Sultana gaba take da Uwar tata , cikin wannan yana yi akayi bikin su Ummul’kairi da Husna , daddy bai musu wani abun kirki bah amma yaya Nura yayi rawar gani dan ya musu komai kasan cewan ya samu aiki yanzu…
Abu kaman wasa daddy saita yayi wa Sultana miji sau biyar amma taki yarda da ko d’aya , cikin taimako irinna zugin momy faty…
Yau dai daddy yana da babban bak’o wani abokin kasuwan cinsa ne zaizoo da iyalan sa , da ganin yanda daddy yake 6ari kasan wannan bak’o mai mahinmanci ne agun daddy, Sultana yasa a gaba yana tsara mata abunda yake son tayi wai ta jawo masa hankalin Ashwan idan tayi hakan ta gama mar komai dan had’a jini da Alhaji Hussan ba k’aramin abu bane , Alhaji Hussan ficaccene anan gida Nigeria da kuma k’asashen waje yana da kud’i sosai sannan yana mugun son d’ansa Ashwan kuma shi kansa yaron akwai canji a hanunsa zaiso Sultana ta aure sa dan bayason yakai ta inda zata sha wuya sannan koda wasa bazai bawa talaka bah, duk maganan da yake yiwa Sultana jinsa kawai take yi amma bawai yana shiga kunneta bane dan ita Sultan shine za6in ta kuma farin cikin ta , cikin k’osawa da zancen tace “ohk daddy naji….
Itama momy faty a nata 6angaren zainab tasa a gaba ta ringa tsara mata yanda zata yi idan bok’on yazo saboda tasamu shiga…
Sultana d’aki ta koma tayi kwanciyan ta har dare babu labarin ta , koda bak’in sukazo Sultana bata fito ba ita kuwa momy faty hakan bak’aramin dad’i ya mata ba dan ita burinta bai wuce Ashwan yace Zainab tamar bah.
Ganin shirun yayi yawa daddy ya sa zainab taje Kiran Sultana , koda taje ma Sultana bacci take yi zainab bata ko kira sunan Sultana ba ta juya ta koma ta shaida wa daddy Sultana na bacci take yi…
“Bacci kuma ?” Daddy ya tanbaya .
“Eh daddy bacci take yi…
Daddy kasa hak’uri yayi dole saida yaje d’akin ya taso ta , alokacin ne tayi wanka sannan ta fito cikin wani doguwar riga sai d’an kwali rik’e a hanunta , Sultana sai da ta bisu ta k’are musu kallo sannan ta k’arisa parlon ta nemi guri ta zauna , koda wasa Sultana bata yi tinanin gaida kowa ba a cikin bak’in , daddy kunya kamar zai nitse k’asa , itakan momy faty taji dad’in hakan ba kadan bah…
Ashwan ne ya dubi Sultana tare da cewa “hy .
Itama Sultana hy din kawai tace mar tana gyara zama agun .
Alhaji Hussain ne ya dubi daddy “wannan itace Sultana ko ?” .
“Eh itace , yayi maganan yana kauda Kai sabo da kunyan abunda Sultana tayi…
Daddy wayansa ya d’auka sannan ya turawa Sultana sak’an cewa ta gaida bak’in , wannan na hanun ta tana dannawa aak’on ya shigo, Baki Sultana ta tura gaba sannan takai dubanta gun bak’in ta gaida su…
Daddy cikin wayan cewa yace “ai wannan sakarci ne akan meye zaki zauna da ciwo ?” gashi yanzu dare yayi dole saida gobe doctor ya dubaki…
Alhaji Hussain ne ya dubi daddy “eyyrh bata ji dad’i bane?” .
“Eh Wallahi ba lafiya kuma tayi zaman ta a d’aki bata fad’a ba.
Allah ya bata lafiya duk suka amsa da amin…
Sultana ganin sa’arta yasa ta saki jiki suna d’an hira , daga k’arshe ma suka wuce nata d’akin tare da Safna tunda ta fahinci itama Safna ar’zafin kaine irin tah…
Ashwan baiji dad’in barin Sultana wajen ba dan shikan yarinyan ta burgesa.
Zainab kan taji dad’in hakan haka ta ringa yiwa Ashwan rawan Kai tana jansa da hira , shikuma duk haushi take bashi mah , wayansa ya d’auko ya turawa Safna text akan ta San yanda zata yi ta karbi number d’in Sultana…
Koda su Safna suka zo tafiya Sultana wasu d’an kunne da sarka masu shegen kyau ta bawa Safna , ta kuma mata al’k’awarin zata zoo gidan su itama , d’an zuwan da Safna tayi amma har Sultana ta bata labarin Sultan ta kuma ce mata za suyi aure kwanan nan , sunyi exchange phone number ta raka su hargun mota sannan ta dawo ciki…
Ashwan ya nunawa iyayen nasa zalaman sa a fili akan Sultana tun kafin suje gida, Ita kam mahaifiyar sa Hajiya Sadiya bata wani murna ba dan iya d’an zuwan sunnan ta fahinci yarinyan bata da cikakken tarbiya , sannan koda suka shiga d’aki ta sake samun wasu labarai game da Sultana k’arya da gaskiya agun momy faty , saidai sam bata gane dabaran momy faty ba itama zainab takeson shigarwa wajen..
Shikan Alhaji Hussain yayi murna sosai dajin labarin daga bakin d’anka , yayi da Sadiya ta ja tsaki ta bugawa Ashwan tsawa akan ya rufe mata baki ta isheta…
Bayan isan su gida Ashwan bai yi sake da kar6an number bah , a daren ya kira Sultana yafi 10 miscalls sam tak’i d’agawa a k’arshe tasa shi a black list , wata number ya sanja yaci gaba da kira sam tak’i d’auka text ya mata ya shaida mata akan shine Ashwan brother d’in Safna da suka zo gidan su , ganin haka yasa Sultana d’aukan wayan cikin gadara manyan ashar ta ringa bugawa Ashwan yana jinta duk yanda ta k’arewa iyayen sa zagi koda ta gama godiya yayi tare da ajiye wayan , yana kuma jin sonta na k’ara shiga cikin ransa sam baiji haushin zagin da tamar bah , duk da kuma girman Kai irin nasa da raina mutane shima hakan yake baya ganin mutuncin kowa bashi da kunya ga kuma bin mata akwanta dake ak’arshe aci mutuncin ki bbu yanda kika iya uwa uba shaye shaye wannan shi yafi komai muni mah….
Ashwan baya sallan asuba sai 9:am , amma yau da asuba sai ga Ashwan a masallaci , abun ya masifan bawa Daddyn sa mamaki ta yanda harya kasa 6oye mamakin sa har saida ya tanbaya ko lafiya cikin jin kunya Ashwan yayi murmushi ya sosa k’eya tare da cewa “wallahi daddy maganan yarinyan nan ne da mukaje gidan su daman…
“Ya akayi toh son?”.
“Daman so nake kayi magana da wori nidai nagani inaso…
“Yanzu Son ko kunya na baka ji?”.
“Gaskiya akan wannan lamarin bazan jiba daddy…
Hmmm! Kawai daddyn yace “ba komai za muyi magana da mahaifin nata , karka damu….
Yauwa na gode daddy nah , bari naje na kwanta…
“Ohk na bari…
Dariya! Ashwan yayi sannan ya wuce…
Washe gari daddy ya kira Sultana akan zancen Ashwan zaune ta same shi a parlon yana ta faman doka murmushi!…
Waje Sultana ta samu ta zauna ta nata faman cika tana batsewa , gani daddy…
Momy faty datasan dalilin kiran itama harara ta watsawa Sultana ta gefe , dan haushin ta take ji taso ace zainab yake so ba Sultana bah…
“Yauwa Mama nah , kinsan meysa na Kira ki?”.
“Noo kawai Sultana ta furta , sannan taci gaba da chat din da take yi wanda ya d’auke mata hankali…
“Yauwa d’iyar arziki dama akan zancen Ashwan ne Dan wajen Alhaji Hussain yace nan duniya ke yake so ni kuma nace na bashi….
“What ?” , Sultana ta furta tare da mik’ewa zunbur daga zaman da take yi zuwa tsayuwa…………”Haba Daddy ai wasa ma kakeyi nasan bazakayi hakan ba , saidai in so kake mu k’ona gidan nida wannan wawan yaron , tab nice zan auri wannan jakin?” , Kawai saita kwashe da dariya.+
Alhaji Musa wanda tinin ransa ya gama 6aci game da furucin Sultana , tsawa ya daka mata “keh….agabana kike fad’in wannan zancen saboda baki da kunya?”, Sam ni ba sa’an ki bane kuma dole ki auri Ashwan domin shine za6ina , badai kince bazakiyi karatu ba aure zakiyi toh ga miji na samo , kuma nan ba jimawa zan aura mar tunda yana so , banason shashanci ai nina haifeki ba kece kika haifeni ba suna kikaci kawai….
Duk wannan abunda Daddy yake yi d’in ba har cikin ransa bane , yayi hakan ne dan ya samu Sultana ta yarta ta auri Ashwan domin yana hango mata hutu acan yasan yaron zai rik’e ta amana, kuma daga ni yana da hankali, uwa uba zumuncin su zai k’ara k’arfi da Alhaji Hussain , kuma ta hakan ne zai samun daman sake shiga jikin sa har yakai ga samun kwangilan da yake nema agunsa na mak’udan kud’i…
Ni kuma araina nace Daddy ai wannan shirme ne , son da ka nunawa Sultana ya zama na banza tunda naiman kud’i zakayi da ita , shiysa idon ka ya rufe kake shirin aurar ta babu bincike…
Sultana ganin Daddyn ta cikin matsanan cin fishi yasa ta tsorita tare da sakin ihu!, Wajen momy faty ta nufa da gudu!, “Momy faty ki taimaka min please Daddy auren dole zaimin wallahi banaso Dan Allah ki bashi hak’uri , wallahi ni na tsani wannan wawan bazan iya zama dashi matsayin miji ba , Daddy yabar Sona , shikenan na shiga uku wayyoo Allah nah please please help me out…ta Kai k’arshen maganan tana shashshek’an kuka!..
Momy faty zuciyan ta a wanke tas , sa boda tsananin farin ciki na abunda idonta yake ganin , ta kuma ji dad’in hakan sosai sannan wannan wata dama ne ta samu na zuga Sultana akan ta bujirewa Daddy , kuma ta shirya tsaf domin bawa Sultana duk wani gudun mawa na yanda zata shiga tsakanin ta da mahaifin nata, “haba Sultana kibar kuka insha Allah komai zaizo da sauk’i mahaifin ki bazai cutar dake ba yana tsananin sonki ki daina kuka zanyi magana tashi kinji Koo , maza tashi kije d’aki gashi har jikin ki yayi zafi bari na samo magani shiga , momy faty cikin ranta cewa tayi shegiya wama zai baki Ashwan d’in har kike wani kuka akansa , ai saidai ki hangosa a nesa….
Daddy parlon ya bari ya nufi d’akin sa domin kuwa idan akwai abunda yafi d’agamar hankali to bai wuce kukan Sultana bah .
Itama Sultana nata d’akin ta nufa cikin kuka da tashin hankali marar misaltuwa.
Momy faty cikin farin cikin ta Kira Zainab domin su tattauna akan lamarin , dole kuma su koma gun malam da wuri tunda ya fara cewa auren da wuri za’a yisa….
STORY CONTINUES BELOW

Sultana cikin tashin hankali ta d’auki wayan ta tare da key din motan ta parlon ta fito kamar wata firgicacciya tana ta faman kuka , momy faty ko ido bata d’aga ta dubi inda Sultana take ba , bare kuma tace ina zata je aranta ma cewa tayi Allah yasa gidan zata bari ta gudu kowa ya futa…
Sultana haraban gidan nasu ta nufa tana matsar k’walla , su kansu ma’aikatan gidan abun ya basu mamaki y’ar gaban goshi yau tana kuka mai yayi tsanani haka?” , Cikin 6arin jiki suka fara kwasan gaisuwa saidai yaukm bata su tayi ba , mota ta shige ba tare da tabi ta kansu bah , mai gadin ganin tana kuka yaso yayi gardama wajen bud’e mata gate d’in saidai tsawan da Sultana ta doka mar yasa shi bud’ewa babu shiri , a 360 ta fice a gidan gudu takeyi sosai kuma tana ci gaba da kukan ta , tinanin abunda yake faruwa take yi , tsakiyan titi taja ta tsaya tare da d’ara kanta bisa stearine motan tana kuka , haka mutane suka ringa kaucewa suna bata hanya dan a tinanin su motan ne ta 6aci , cikin lokacin kad’an ta had’a goslw agun , gandin abun yayi yawa ne wani ya fito daga nasa motan yazo wajen motan Sultana domin duba mata meye matsalan , glass motan yayi nocking! , firgit Sultana ta dawo daga duniyan tinanin da takeyi Sam ta manta akan titi take , tada motan tayi taci gaba da tafiya , gidan su k’awar ta Zahra ta nufa , takoci sa’a ba kowa a parlon Kai tsaye ta wuce d’akin Zahra kwance ta sameta tana faman bacci , Sultana na kuka ta fad’a kan Zahra, tare da cewa “K’awata na shiga uku wayyo Allah na Daddy aure zaimin kuma bada Sultan bah wallahi saidai na gudu Amma indai kikaga ban auri Sultan ba saidai in mutuwa nayi…
Zahra cikin rashin fahinta ta fara goge idon ta , domin a tinanin ta ai bacci take yi , ahankali ta furta “Sultana nah?”.
Itama Sultana jajayen idon ta ta d’ago tana duban Zahra ba tare da ta amsa bah , “maza kiyi shiru fad’amin abunda yake faruwa domin ban gane bah…
Sultana bata 6oyewa Zahra komai bah cikin abunda yake faruwa , duk ta kwashe labari ta bawa Zahra, ajiyan zuciya Zahra tayi lallai yau ake yinta wallahi nama rasa me zance , gaskiya daga ke har sultan kunyi gangancin rashin fad’an soyayyan ku a gida Abu tun muna yara , ta’ina za’a fara rabaku yanzu gaskiya rabakuma ganganci ne , ni dai a nawa shawaran inaga ki tattara kawai ki bar k’asan nan ki tafi skull d’in kinga sai a fasa yin auren ai.
“What naje skull fa kikace ?”.
“Eh haka nace akwai matsala neh?”.
“Akwai wallahi babba ma , Sultana ta furta tana duban Zahra.
“Meye shi?”.
Hmmm! “Kedai Zahra ayi shiru kawai , Amma bazan iya karatun ba aure nake soo amma da sultan , nagaji wallahi bazan iya ba kullun cikina ciwo bazan kashe kaina ba feelings yana damuwa gara dai nayi auren ba wani skull aikin wahala ba zanyi bah , ai ko islam da nace bazan yiba ambarni bare boko aure zanyi da Sultan kuma sauran 1month ya dawo , shinake adanawa kaina tsawon lokaci da tini na lalace tunda ni ba dutsi bace aha…
Zahra sake baki kawai tayi tana duban Sultana , tasan halin k’awarta tun suna yara duk abunda yake ranta bata 6oyewa dan ita Sultana bata tsoron kowah..
Sun jima suna tattaunawa kafin Sultana ta wuce gida.
Kwana uku kenan Sultana bata wani walwala agidan bata magana bare shiga harkan wani , shima Daddy gaisuwa ce kawai take had’asu , momy faty kan kullun tana cikin zuga Sultana akan ta auri za6in ta karta biye mahaifin ta , aure zama ne na har abada ba’a fatan idan kayi kafito Dan haka karta sake ta fabati ayi wannan auren , tunda yana sonta dole zai hak’ura ya bata Wanda take so , tunda yace ita aure zata yi ba skull bah…
A 6angaren Sultan kuwa tunda Sultana ta bashi labarin abunda ke faruwa ya shiga tashin hankali da kuma jinya mai tsanani , sultan ya gama karatunsa wani abu kawai yake jira zai dawo next month , amma saboda rashin lafiyan da yake yi mai tsanani yasa aka Kira iyayen sa a waya aka shaida musu ciwon d’ansu dole sukaje bashiri….
Gidan su Ashwan kan shirin biki akeyi sosai saidai Ashwan ya 6oyewa iyayen sa irin k’iyayyan da Sultana take mar , ida sun sani koda wasa ba zasu Bari ayi wannan auren ba , ita kam Safna tasan komai , tunda yanzu haka Sultana tabar kulata tace itama muna fukace ta kuma Sam duk irin cin mutunci da Sultana ke yiwa d’an uwan ta , Ashwan yana zuwa gidan su Sultana bai fasa ba saidai kullun cin mutunci kala dabn zai gani agun Sultana , amma yana hak’uri ne harta shigo sannan yayi maganin ta .
Hajiya Safiya ido tasa sannan ta ci gaba da bin malamai akan tasamu afasa auren nan , tafison Ashwan ya auri Zainab d’iyar Hajiya faty , shikuma ya kafe kamar wani maye…
Itama Momy faty ba zaman tayi ba , tana ta faman bin malamai…
Hajiya Maryam kam tana cikin gidan Amma ba ‘abunda tasani akan zancen auren Sultana shima Alhajin bai fad’a mata ba.
*K’auye*
Zainabu kam ta kammala secondary d’in ta cikin nasara , saidai bata ma tinanin zata yi gaba tasan ta kaga karatu yanzu kam , ta k’ara kyau da gogewa tankar ba y’ar k’auye bah , dan madai tana shan wuya sosai a gidan nasu…
Malam mahaifin Zainabu da kansa ya nemi Ahmad saurayin d’iyarsa zainabu akan zancen auren su , ya rok’a akan Adan k’aramar lokaci , malam yace ba matsala amma bayaso aja lokaci kafin auren duk abunda yake dashi yazo ayi haka karyace zai daurawa kansa abunda Allah bai dira mar bah , dan yasan halin d’iyarsa zata iya hak’urin zama a ko wani yanayi….
Ahmed bayan yaje gida sunyi magana da mahaifiyar sa ya yanke shawaran shiga birni yayi sana ‘a domin samo kud’in auren zainabu…
Washe gari ya kama zai tafi birni zainabu ce rik’e da kayansa da ke cikin laidan viva tana rakashi , sai faman kuka takeyi yana bata hak’uri…
“Haba zainab tawa kibar kukan nan haka ya isa , insha Allah bazai jima ba da naso kud’in nan zandawo muyi aure.
Zainabu Kai ta d’aga tana dubansa tare da cewa ni wallahi tsoron yan matan birnin nan nake yi , da sunga saurayi mai kyau shikenan sai suce so , ta k’arisa maganan tana juyamar baya.
Gaban ta yasha yana dariya “haba Zainab ikon Allah , soyayyan mu a cikin jini take wallahi ina sonki kaman raina na kuma fiki dokin zuwan wannan rana Allah dai ya nuna mana.
Zainabu wacce tinin hawaye sun wanke fiskanta kuka take sosai , Ahmed sunkuyawa yayi yana lashewa….
*pls kuyi hak’uri dani bana muku typing kullun wlhy skull yake 6oyeni but zanyi iya kokari nah… Insha Allah*🤦🏼♀🤦🏼♀🤦🏼♀
…….Baki bud’e Zainabu take bin Ahmad da kallo cike da kunya , ” toh Zainab zantafi sai Allah ya dawo dani kimin addu’ah…+
“Shikenan Allah ya kaika lafiya , ina maka fatan alkairi ka rik’emin amana sannan ka kula da kanka zanyi missing d’in ka.
“Bake kad’ai ba , Nima zanyi missing d’in ki , amma ba yanda na iya sai hak’uri tunda kud’in auren ki zanje nema.
“Haka ne , Allah ya kare min kai aduk inda kake, ta k’arisa maganan tare da juyamar baya tana share hawayen ta.
Jikin Ahmad a sanyaye ya fara tafiya , ba tare da ya sake dubanta bah , saidai tafiya kawai yakeyi amma yanajin cikin ransa bbu dad’i tare dajin matsanancin tausayin ta , haryayi nisa ya juya yana dubanta ba tare da tasani ba har ta 6ace mar , sannan ya juya yaci gaba da tafiyan sa.
Itama zainabu a nata 6angaren tana tafe tana kuka!, cikin tashin hankali , gani take kawai kamar sun rabu kenan bazai dawo bah…
*Kaduna*
Sultana ta shiga tashin hankali bana wasa ba, saboda ko ta nemi Sultan bata samun layin sa , duk tabi ta rame saboda damuwa , momy faty ke rarrashin ta kullun akan ta k’ara hak’uri tasan dole zai dawo din kamar yadda ya fad’a , haka dai Sultana tadau dangana badan ranta yaso ba, sai dai Sam zuwa yanzu ta daina ko da gaisheda daddy bare wata magana ta shiga tsakanin su , idan ma tagan sa saija hanya takeyi tare da had’a fiska , rashin kunya takemar sosai amma yayi kamar ma besan tanayi bah , saima ci gaba da shirye shirye aketa faman yi.
Ana biki sauran sati biyu ne Daddy ya shiga 6angaren Mamy , tayi mamakin ganinsa sosai tunda yanzu Sam yabar zuwa inda take , kawai dai tana zaman y’ay’a ne a gidan shima saboda gudun idan tabar gidan yaran baza suji dad’i ba , duk da cewa a yanzu duk suna gidan mazajen su , amma ta zauna kodan yaran su tsira da mutuncin su kar wataran a musu gorin babu iyayen su a gidan .
Daddy ya fahinci duniyar tinanin da ta shiga , hakan ne ya sashi yin gyaran murya sannan ya fara magana , “kinyi mamakin ganina ko ?”.
“Dole nayi Mamy ta bashi amsa a takaice.
“Toh ba abun mamaki bane , auren d’iyar kice ya taso hakkin kine dole nazo na sanar miki, duk da cewa kin cireta cikin Jerin yaran ki tunda jimawa , hakan bazai hana fad’a miki bah…
Mamy har cikin ranta taji babu dad’i , ace d’iyar cikin ta amma sai dai da biki yazo take jin labari , amma bakomai duniya ce , kuma daman yarinyan ma bata ganin ta da mutunci, “Allah ya Sanya alkairi ta furta a tak’aice tare da mik’ewa tabar gun.
Daddy sai da ya tsaya Jim kamar me tinanin wani abu , sannan ya furta “Amin tare da barin falon, yana jin wani irn bugun zuciya, Sam baiji dad’in halin ko in kula da ta nuna ba akan lamarin…
Gidan su Ashwan sun kawo lefen su na gani na fad’a , kud’in k’asan akwati kawai sai da akasa 1m , kawai cikin akwati kuwa fad’an suma 6ata lokaci ne saidai ayi shiru , momy faty tare da k’awayen ta biyu sune suka kar6i kayan , ba tare da sanin mamy bah ,momy faty ta shiga damuwa sosai da ganin kayan dan tana gudun ya su6ucewa zainab d’in ta , nandai K’awayen suka ringa bata muguwar shawara ta yanda za’a 6ullowa lamarin dan ganin Zainab ce ta auri Ashwan ba Sultana bah.
Sultana ta shiga tashin hankali sosai a nata 6angaren , duk tabi ta fige kamar wanda tayi wata doguwar jinya, tana mugun son Sultan kamar ranta batason ta rasa shi.
Anshirya zuwa Dubai domin sayan kayan d’akin Sultana , saidai itakan uwar gaiyan fir taki zuwa , fatan ta shine Daddy ya mutu a hanya domin samu ta auri za6in ranta.
Daddy da momy Faty 4dsys sukayi suka juyo gida Nigeria , anyi siyayya bana wasa ba , naira tayi kuka , duk wannan siyayyan Momy faty ta yi shine saboda farin cikin ta zainab , dan tasa a ranta duk kayan na zainab zasu zamu, gyaran jiki kuma musanman zainab taba gidan suwa wani gida dabn ana mata gyaran acan , yayin da itakan amarya Sultana babu abunda aka bata domin ta gyaran jikin ta dashi , bare kuma ta samu matsayin a mata , duk shirin da momy faty take yi tanayin sane saboda zainab shiysa ma ta dage dayin gaiyata.
1week to biki , Sultan ya dawo bayan jinyan ciwon zuciya da yayi fama dashi , ko da suka iso airport , tare da iyayen nasa sun samu tinin driver ya iso domin d’aukan su , amma Sam Sultan yak’i shiga mota, Number d’in Sultana ya fara kira , kamar bazata d’auka ba sai kuma taja tsaki kami da daga wayan ta kara a kunnan ta.
“Hello who calling me?”.
Daga d’ayan 6angaren aka sauk’e ajiyan zuciya , sannan yace “Sultan atakaice.
Wani uban tsalle Sultana tasa gami da sakin ihu! , Da gaske?”.
“Uhm! , Kizo yanzu ina jiran ki , gani a airport , ke nakeso ki kaini gida….
“My , are you sure?”.
“Yes dear.
Cikin farin ciki marar misaltuwa tace” ban 20 minutes , gani zuwa…….Cikin zumud’i Sultana ta fad’a bathroom, bata wani d’au lokaci ba , ta fito d’aure da towel tana goge jikin tah, mai ta shafa sannan ta feshe jikin ta da tirare, doguwar riga ta zira a jikin ta , jim tad’an tsaya kome ta tina ohoo,, tsaki tad’an jah, tad’au gyalen ta tare da key d’in mota ta fice daga d’akin.+
Parlor ta nufa cikin sauri , Daddy ne yayi magana cikin sanyin murya , ba tare daya kira sunan taba yace” ina zakije?”
Cikin sauri! Sultana ta juya inda taji anyi maganan , dan bata masan akwai mutane a parlorn ba , ido suka had’a da Daddy , fiskan sa babu yabo babu fallasa , shiru tad’an yi na wani lakaci tana tinanin abunda zata cemar….
Tsawa Daddy ya buga mata, ” bada ke nake magana bah?” .
Take idon Sultana ya ciko da hawaye! tana shirin yin kuka.
Momy Faty cikin farin ciki , tare da kirsa ta matso sosai kusa da Daddy, “haba honey banason kana d’aga hankalin ka akan abunda baikai ya kawo ba , yanzu meye abun fad’a anan?” , ta k’arisa maganan tana shafan gefen fiskan sa.
“Bakya ganin ina mata magana ta manna min hauka ne?”.
“Ai hak’uri zaka yi , kasan Sultana yarinya ce, sannan y’ar soo.
Sultana wani bak’in cikine taji ya tokare mata wuya , yayin da hawayen takaici ya shiga bin kuncinta.
Ganin hakan yasa Momy faty tayi wani fari da ido sannan tace honey ka barta taje kaji..
“Shikenan gimbiya , taci albarkacin ki.
“Murmushin jin dad’i tayi , sannan tace godiya nake ranka shi dade.
Sannan ta watsawa harara sannan tace shikenan kije , amma karki jima.
Sultana dak’er ta iya jan k’afar ta tabar wajen , badan tanason taje taga farin cikin taba , tabbas data hak’ura, yanzu ita Daddy ya kema wannan cin mutun cin me tamar haka yabar sonsa , wasu hawaye masu zafine suka zubo mata! , ahankali tasa hanun ta ta shiga sharewa.
Asanyaye ta k’arisa jikin motan , tana k’ok’arin mud’ewa , wayan tane ya shiga k’ara da sauri ta d’aga danko bata dubaba tasan waye neh.
Tana d’agawa bata jira taji abunda zaice bah , asanyaye ta fara magana , “kaji shiru ko?”.
STORY CONTINUES BELOW

“Eh , ina ta jira gashi Abbah Ummy duk suna tsaye suna jirana , ga driver ya iso tun d’azu , nace musu wani abokina nake jira kuma shiru kuma.
“Am sorry gani zuwa yanzu ta k’arisa maganan tana mai share hawayen da suka zubo mata akan face d’in tah.
Da sauri! ta shiga motan tabar gidan a 360 , dan gudun kar taje ta samu ya tafi , kuma gashi alk’awari suka yiwa juna akan duk randa ya dawo kafin yaje gida saita ganshi harma sun faran tawa juna rai kafin yaje gida…
Bata wani 6ata lokaci ba ta isa cikin kaduna international airport,
tana daga cikin motan tafara bin gun da kallon ko zata hango sa , saidai bata ganshi ba dole ta fito daga motan ta fara takawa a hankali tana Waige waige , ji tayi an rugumeta wani irin razana tayi saidai jin daddad’an k’anshin turaren sa yasa ta gane ko waye, wani irin k’aran farin ciki tasa tare da juyowa da sauri ta k’ank’amesa tana murna .
Sultana bata kawo komai a ranta ba , ta k’ara shigewa jikin sa tana mar wani irin kiss , take hankalin mutane ya fara dawowa kansu , yayin da Ummy da Abban Sultan suka sake baki suna ganin ikon Allah , wannan wani irin rashin kunya ne agun yarinyan nan?” , badai akan ta yake ta faman ciwo ba , ina akwai sake bazai yiwu ba wannan ta zamo surkuwarta mai mutunci take so gaskiya ba wannan yarinyan marar ta ido bah.
Sultana kan tini Soo ya rufe mata ido bbu abunda take fahinta , ta manta ma da yace bashi kad’ai bane har dasu Mum dinsa.
Ahankali ya rad’a kata , “Baby sake ni , kinsan akwai su Ummy karsu hango mu .
A razane! ta sake sa tana ja da baya cikin jin kunya , Sultana cikin ranta ta fara addu’ah Allah yasa dai su Ummy basu hango taba, ji tayi baza ta iya binsa wajen iyayen basa ba saboda kunya.
Ko yaje gun Mom d’in sa had’e giran sama da na k’asa tayi tana dubansa , tare da cewa” yamaka kyau, abunda ka koyo a can d’in kenan?”.
Nanfa Sultan ya shiga sosa k’eya dan ya gane ta gansu, cikin jin kunya yace” wallahi Ummy munyi missing juna ne shikarun da yawa tun tana k’arama fa na tafi , gashi yanzu harta girma.
“Dallah ne rufemin Baki, marar kunyan banza.
D’an dariya! yayi kawai ba tare da yace komai bah.
Duk wannan abunda suke d’in Abban nasa bece komai har suka gama , sannan ya dubesu yace” mu wuce ko ?”
Sultan ne ya matsa jikin Abbah sosai ya rad’a mar a hankali”pls Abba nah da Sultana zamu wuce musanman tazo d’auka nah.
“A’a Son , mu wuce gida ba wani ishashshen lafiya ne da kaiba .
Langa6ar da Kai yayi jikin mahaifin nasa , karmar zaiyi kuka! Yace Abba ka tausayamin ka barni kafin Ummy taji , nasn idan taji wlhy ba barina zatayi na jeba…
“Son bason yawan rigima fa kana jina ko .
“Ohk ka barni naje?”.
“Kaje amma ina zata kaika?”.
“Girkin ta nakeson cine…
“Shikenan Abban ya furta , tabbas yasan D’an sa tino yana cikin wani yanayi , yanason yarinyan gashi ance ammata miji da saiya nema mar auren ta amma yanzun ma bata 6aci ba zaije yaji yanda za’ayi , ko zasu tausayawa yaron albarkacin wannan ciwon a bashi auren yarinyan , juyawa yayi yana duban yaron nasa tare da tausayamar , dan ya lura da irin son da sukewa junan su gaba d’aya.
Ummy tinin ta shige mota tana jiran ahigowan su , Abbah ne ya shiga sannan yacewa driver su tafi , Ummy ta jefa mar tanbaya tana dubansa “ina shi Sultan din yake?”.
“Sunshige ya bata amsa atakaice.
Ta bud’e maki zata sake magana , Abbah ya d’aga mata hanu alaman bayason damuwa , ba yanda ta iya dole tayi shiru tana tattauna lamarin a cikin ranta , anya zata yarda D’an ta ya auri yarinyan da bata da tarbiya kuwa?”, San tasake cewa toh idan baki yarda ba ya zakiyi tunda yana sonta gashi har ciwon zuciya ya samu saboda ita , kai kodake ma ai yanzu kam anyiwa yarinyan mijin , can tasake cewa Kai kuma ai anyiwa yarinyan miji runtse ido tayi tana tinanin wani irin halin Dan nata zai k”ara shiga , bata son yarinyan Amma tanason farin cikin d’anta.
A 6angaren Sultana kuwa gudu take yi sosai , dan gani takeyi zata k’arar da time din nata a hanya kafin ta isa .
Sultan ne ganin hanyan da ta d’auka yasa shi juyowa ya dubeta tare da cewa “Baby ina muka nufa?”.
“Sa ido kayi kallo ta bashi amsa.
Shiru Sultan yayi bek’ara cewa komai bah , dan duk ya sururuce akan Sultanan sah, ta k’ara wani kyau ta girma ga fari tayi wani cika na ban mamaki , so kawai yake ya jishi a jikin ta…
Sultana bata tsaya ko ina ba sai wani lafiyayyen hotel daya gaji da had’uwa,Emerald suit malali kaduna , aharaban hotel din ta yi parking sannan ta kashe mota , kallon sa tayi tanata faman doka murmushi tace” my tashi mu wuce..
Zagayowa tayi ta bud’e masa motan sannan ta rufe motan da key suka nufi cikin haraban hotel din……….kai tsaye wajen biyan kud’i sukaje , saida suka cika wani form , sannan aka basu number d’in room din da zasu zauna , d’aya daga cikin security ne ya shige gaba da key a hanunsa , saida ya kaisu har d’akin sannan ya saka key a jikin d’akin sannan ya juya cikin rusunawa….+
Har suka shiga d’akin hannun su na rik’e a cikin na juna , bakin gado suka zauna suna duban juna , Sultana ne ta dubi Sultan tare da zuba masa dara daran idanunta tana k’aremar kallo mai cike da sha’awa wanda ya ringa d’awai niya da ita tsayin lokaci, ahankali ta furta “my very own tashi wanka zakayi bamuda time….
Sultan runtse ido yayi saboda yanda yaji saukan muryanta cikin dodon kunnan sa , tabbas yayi rashin Sultana kuma yana cike d kewar ta na tsayin lokaci, bayajin zai iya rayuwa babu ita , yana sonta so mai tsanani yana k’aunarta , sannan yana tsananin sha’awar tah….
Sultana mik’ewa tayi ta wuce cikin bathroom d’in ta ciro towel ta ajiye bakin gadon sannan ta fara ragemar kayan jikin sa…
Sultan wani irin shocking yaji a duk cikin jikin sa har saida ya runtse ido, fari da ido Sultana tayi hadi da murmushi dimple din da yak’awata face d’in nata kyau tinin ya fara lotsawa tankar zaka ajiye abu cikin ramin ya zauna , bayan ta gama cire riganne ta k’orawa chest d’in sa ido tana k’arewa gun kallo saboda wasu kwancacun gashi daya kwanta a saman k’irjin nasa , haka kawai taji tana sha’awan kai hanunta gun , batayi shawara da kowa ba ta fad’a saman ciyan sa tashiga murza gun , sultan da tuni k’wayar idon sa ya sanja ya koma launin jah , sakamakon da dayake fari tas, sake jawota yayi ya gyara mata zama , sannan ya shiga kissing dinta ta ko ina…
Sultana jin joystick dinsa yana faman zungurarta yasa ta lumshe ita, cikin zuciyarta ta furta dole na baka kaina ayau ko zanji zafi zandaure na jima ina maka tana din kaina babu abunda nakeso sama dakai , bazan yi gangancin kaiwa wani banza budurci naba kai dindai zanbawa , saboda ina sonka , banta6a son wani irin kwatan kwacin son da nakema bah, ahankali ta fara k’ok’arin k’wace kanta daga iron da ya mata , shikan Sultan sai faman sake matseta yake a jikin sa, dak’yar tasamu tad’an zauna sannan ta rad’amar magana cikin kunne “pls my kafarayin wanka , da cin abinci , kafin kamai , tana kaiwa nan ta mik’e ba tare da tajira jin me zaice bah…
Wayan da aka tanadar dokin costumers ta nufa , number din da taga anyi saving da maintenance shi tashiga Kira , bugu d’aya na biyu aka d’auka tare da tambayan ko suna buk’atan wani abune , take ta fad’in kalan abincin da tasan Sultan yanaso sosai sannan ta ajiye wayan , ta juyo tana duban sa sai faman k’are mata kallo yake yi yana lasan lips dinsa cike da matsanan ciyar sha’awan ta wanda lokaci d’aya ta haifar masa ciwon ciki mai tsanani , rumtse idonsa yayi da k’arfi kamar me tinanin wani abu….
Cikin 5minutes ma’aikacin hotel din ya iso d’auke da abinci kamar yadda Sultana ta buk’ata , tanajin nocking ta mik’e zuwa bakin kofan ta kar6i tire din sannan ta dawo ciki , ta ajiye sannan ta dawo inda Sultan yake…
“Tashi kayi wanka ko abincin zaka fara ci ?” tayi maganan tana dubansa.
Siririyar muryansa ta doki cikin kunnan ta,”Baby ke nake buk’ata a halin yanzu ba abunda kika lissafoba…
Murmushi! Sultana tayi ba tare da tace komai bah , saidai a cikin ranta cewa tayi “na fika buk’atan hakan ai, a zahira kuma kama hanun sa tayi zuwa inda abincin yake , zama sukayi ta ringa bashi a baki shima yana bata har suka koshi.
Nanfa ya juya yana duban ta sannan yayi magana a hankali” Baby tashi muje ki tayan wankan .
Sultana kaman daman jira take ai kuwa zunbur ta mik’e suka nufi bathroom d’in rungume da juna….
Shi da kansa ya cire mata kayan jikin ta , sukaci gaba da wanka cikin shower din .
Sultana da kanta tayi masa wanka sannan sukaci gaba da wasa a cikin ruwan , haka suka ringa romancing juna ruwa na ci gaba da dukan su harna tsawan lokaci.
Ganin tsayuwan bazai kaisu ba yasa Sultan d’aukan Sultana cad’ak har zuwa kan gadoo…
Daga Sultan har Sultana sun fita a haiyacin su , babu abunda Sultana keyi sai k’ara mannewa a jikin sa tana faman shagwa6a, tare da d’ora kanta saman chest dinsa tana faman murzamar kan niple dinsa , hanun ta daya yana kan joystick dinsa tana faman shafamar kamar tasamu wani abun wasa…
Babu abunda Sultan keyi sai maida wani irin nunfashi , saman breast dinta ya kama ya shiga tsotsa kamar ya samu sweet , yayin da hanun sa d’aya yake k’asan maranta yana wasa da vagina dinta , ahankali harya kai yatsansa cikin hussy dinta yaci gaba da juyawa tare da kalon reaction d’in ta ganin tanajin dad’in abunne yasa shi ci gaba dayi , yajima yana yi sannan yakai bakinsa cikin Qh din yana faman tsotsa kamar wani tsohon maye….
Ba abunda Sultana keyi sai ihun dad’i , juyawa tayi cikin dabara suka had’a fuskansu guri guda , sannan suka ci gaba da tsotse bakin junan su cikin wani irin shauk’in juna wanda su kansu bazasu iya misaltashi bah…
A kasalance ya d’ago kanta yake rad’a mata ,”pls Baby nayi sex dake?” , Wallahi nayi alk’awarin bazan gujeki ba mutuwace zata rabamu…
Itama Sultana cikin wani irin yanayi ta fara magana , “nayarda saboda inasonka saboda Kai najima ina adana kaina dan kawai na baka wannan farin cikin…
Cikin wani irin jin dad’i sultan yaci gaba da kissing d’in ta aduk illahirin jikin tah, cikin dabara Sultan ya d’ago Sultana sosai tare dasa pillow a k’asan k’ugunta , sannan ya fara k’ok’arin jefa joystick dinsa cikin duniyarta, yajima yana Abu daya kafin yayi nasarar shiga jikin ta ya fara juyawa , take ya birkice saboda yanda sultan yaji tankar asa gura cikin rijiyar da take cike ana k’ok’arin d’ibo ruwa….
Itakam Sultana a nata 6angare tun bayan da ya tsaga jikin ta ya shiga daganan labari ya sanja , Dan wani irin zafi taji yana ratsa jikin ta wanda bata ta6a jin irinsa ba duk hak’urin ta abun yaci tira, ihu ta saki tare da bashi hak’uri tana had’ashi da Allah akan yayi hak’uri ya barta , haka ta ringa ihu tana neman d’au ki , “pls Sultan ka barni wallahi zafi nake ji Dan Allah ka zare bazan iya ba akwai zafi waiyoo Allah nah…….Haka dai Sultana ta ringa sanbatu , saidai Sam Sultan bemasan tanayi bah.+
Hankalinsa kwance ya ringa hak’arsa kaman Allah ne ya aiko sa, Sam baya cikin haiyacin sa bare ma yasan Sultana na kuka, wani irin d’adine yake ratsasa wanda baisan kalan saba, duk wata sha’awan da ta ringa d’awainiya dashi tsayin lokaci ayau saida ya magance sa ,domin kuwa yakai 10 round yayi…
Sultana tun tana iya kuka harta kasa ta6uka komai , domin kuwa Sultan bacin wasa ya mata bah, zan iya cewa gaskiya ta ciwu ba kadan bah , kodan baisan zafin ta bane ohhoo🤣, sai nakega kaman inda ya biya sadiki zai mata a hankali ko nace zai tausaya mata.
Sultan saida ya tabbatar yayi realising ya zubar da duk wani sperm daya jima yana haddasamar ciwon ciki sannan ya sauk’a a kanta ya fad’a gefe yana faman sauk’e ajiyar zuciya.
Sultana bata iya k’wakkwaran motsi , tajima tana matsar k’walla , kafin daga baya bacci ya d’auketa.
Sultan bayan ya koma normal ya tashi daga inda yake kwance ya dawo jikin Sultana ya kwanta kamar zai shige jikin ta saboda irin rungumar da ya mata , shima baccin yayi cikin farin ciki marar misaltuwa tare da addu’an Allah ya mallakamar Sultana a matsayin matar sa.
Bata fi 1hour ba ta farka daga baccin , ahankali ta fara bed’e ido tana tina abunda ya faru a hankali, dubansa tayi tana k’arewa kyakkyawan fiskansa kallo d’an murmushi tayi sannan ta fara k’ok’arin zare jikin ta da nashi saidai ya rik’eta sosai kamar wanda za’a k’wace mar ita , ahankali ta shiga romancing dinsa tare da had’e bakin su waje guda tana tsotsa , sai faman tafiyan tsutsa takemar ajikin sa, ahankali ya fara bud’e ,wani sabon farin ciki ne ya rufe Sultan , kissing d’in ta ya shiga yi a duk kikin ta.
Sultana langa6ar da Kai tayi ajikin sa ahankali ta furta ” my sake ni bathroom zanshiga , ta k’arisa maganan kaman zatayi kuka.
Shima Sultan cikin kwaikwayon maganan ta ya furta”to ai tare zamuje nima can zani .
“Ohk kawai ta furta nata k’ok’arin mik’ewa, shima mik’ewan yayi yana k’ok’arin sauk’a a gadon , Sultana tana taka k’afan ta tasaki wani k’ara saboda azaban da taji , da sauri Sultan ya k’ariso inda take yana dobanta.
“Baby sannu kinajin zafi neh?”.
Kai kawai ta shiga d’agamar! alaman tanaji.
“Ohk jirani zauna kafin nazoo.
Babu musu tanemi waje ta zauna cikin dauriya.
Ba’a wani d’au lokaci ba ya dawo d’akin , bathroom ya fara shiga ya ajiye abunda ke hannu sa sannan ya dawo cikin d’akin , d’aukan ta yayi tankar wata jaririya yakai bathroom din , cikin bathtub ya ajiye ta , heater ya kunna ya hada ruwan zafi da sanyi gu daya wani garin injection ya zuba a cikin ruwan , ahankali yake ratsa Sultana cikin dauriya taci gaba da zama a ciki, harzuwa wani lokaci duk wani zafin da takeji neman sa tayi ta rasa , saida ruwan yayi sanyi sannan aka bud’e ya fita , Sultan ya rad’a mata a hankali “baby sauran wankan tsarki…
“Ni ni nidai ban iyaba…😫, ta K’arisa maganan kaman zata yi kuka…
Sultan zaro ido! yayi waje, baki iyaba kuma?” , Yayi maganan cikin jin mamaki.
Duk yanda ya d’auka wasa takeyi dole ya ajiye domin kuwa Sam bata iyan ba da gaske, dole ya koya mata sannan shima yayi nasa, suka fitoo.
****
Daga Ummy har Abban Sultan sun shiga damuwa na rashin dawowan sa , ga kuma duk layu kansa a rufe, duk abun duniya ya bi ya ishesu duk da cewa Sultan ba k’aramin yaro bane da hankalin sa , tun suna damuwa har suka daina suna ganin iya gudun ruwan sah…
Sultana sai dare sukabar hotel , saida Sultana takai Sultan gidan su kafin itama ta wuce nasu gidan , da alk’awarin zasu had’u gobe da yamma.
Ko da Sultana ta isa gida mama faty kawai ta samu a parlour , babu ko sallama ta nufi hanyan d’akin tah , harta kusan shigewa Mama Faty ta dakatar da ita ta hanyan kiran sunanta.
“Keh Sultana meyafaru da tafiyan ku?”.
Sultana bataji ko d’ar bah ta juyo ta watsawa Mama Faty harara sannan ta juya zataci gaba da tafiya .
Tsawa! momy faty ta doka mata , “Keh bada ke nake bah?”, Sweet heart kana ina?”.
Daddy ne ya fito da sauri yana zare ido kamar wani zautacce, “lafiya honey naji kinata faman d’aga murya, kuma kisan banason damuwan ki ba wani ishashshen lafiya ne da keba….
” Ni da y’arka ne , kullun rashin kunyan ta k’ara gaba yake yi , harni zan mata magana ta shareni , har tayi wannna girman ?” , tunda ni ta fi k’arfina kai sai ka tanbaye ta daga ina take , dan naga tafiyan ta kamar ta sadu da d’a namiji gaskiya amma ka tanbaye ta , tunda ni ta mayarni banza, ta k’arisa maganan tana fashewa da kuka…
Cikin zagin nama Daddy yayi kan Sultana “keh daga ina kike dan ubanki?” , haushin shirun da tayi , da kuma tashin hankalin kukan rabin ransa keyi ko muce uwar sama, yasa shi kaiwa Sultana duka babu ji ba gani ya yaringa dukan Sultana har saida ya gaji dan kansa sannan ya barta , Momy Faty ta shiga farin ciki marar misaltuwa haka ta ringa shagwa6e mar yana rarrashin ta, a k’arshe tacemar ai mamy ce ke zuga Sultana..
Cikin 6acin rai Daddy yayi 6angaren mamy yana fuci.
“Maryam ,Maryam ,kina inane?”.
“Gani lafiya kuwa?”.
“Bansani ba , asirin kine ya tonu, saboda kina zigamin yarinya tana raina min mata toh wallahi bazan lamunta ba , dan haka kije na sake ki…..
*K’auye*
Tun bayan tafiyan Ahmad , zainaba ta shiga tsaka man wuya , ga kuma mahaifin ta ya kwanta jinya babu ko kud’in kaisa asibiti Baba Lantana tace bata dashi , baya ko magana sai an D’aga sai an kwantar duk wani d’awai niyarsa Zainaba keyi , karatun da tayi a birni baisa ta sanja halaiyarta ba.
Baba Lantana tuwon siyarwa ta shiga yi na dare zainaba ke siyarwa ,randa tayi kwantai kuwa babu zaman lafiya girmanta bazai hana ta lakad’a mata duka ba har yau , duk abun duniya yama zainaba yawa ,gashi haryau bata yi waya da Ahmad ko lafiya yake waya sani kullun tana cikin kuka.
Kuluwa kuwa a nata 6angaren abudai babu dad’in ji dan saurayi tayi wanda take matuk’ar Soo ya kuwa bata mata rayuwa a halin yanzu har shaye shaye take yi , duk yanda baba Lantana take 6oye lamarin dole saida ya fito kawa ya shaida , ance ya fito ya aure ta kuma yak’i acewarsa bai shirya aure bah, wannan ba a wani dau lokaci ba saiga ciki wannan shine sanadin kwanciyn mahaifin su jinya saboda bakin ciki…