K’ADDARA CE CHAPTER 2
Blanket tajawo talullu6e jikinta.
Daidai lokacin su Abbah suka turo k’ofar d’akin suka shigo dasauri abbah yanufi wajenta hankalinsa a tashe, idanuwanta a lumshe suke hawaye yagani suna gangarowa daga idanuwanta,
Bakin abbah yana kyarma yace Amina kiyi hak’uri laifi na ne ni najamiki wannan mummunar k’addarar.
Bud’e idanuwanta tayi tace a’a abbana kar kace haka K’ADDARA CE kawai kadaina d’aura laifin a kanka domin na san abbah na ba zai ta6a aikata abunda ba daidai bane, kakwantar da hankalinka abbana nasan koma minene yafaru laifin nasune ba na abbana ba.
Dafa kanta yayi yana hawaye yace Allah yayi miki albarkar Amina.
Murmushi tayi tace Ameen Abbana,
Ammah jikinki akwai zazza6i bari asamo miki magani,
Juyowa yayi yakalli ummah da tunda suka shigo tana tsaye batace komai ba yace zainab dan Allah kije d’akina kid’auko mata paracetamol tasha,
Kallon Abbah tayi tace wlh Alhaji ban iya zuwa ni kad’ai tsoro nakeji, jin haka yasa abbah yatafi.
Kusa da Amina tadawo fuskarta a d’aure tace sannu kitashi kid’an watsa ruwa ko kinji dad’in jikinki, kunya Amina taji domin ta gano abinda ummah take nufi,
Dasauri taruntse idonta tace ummah na yi wanka ai, yamutsa fuska ummah tayi tace Allah yasauke,
Daidai lokacin Abbah yashigo d’akin hannunsa rik’e da magani da ruwa tashi kisha maganin kinji mamana,
Ahankali tatashi zaune ba tare da ta bud’e idonta ba, maganin takar6a tasha daidai lokacin aka fara kiran sallah, komawa tayi takwanta ganin haka yasa su abbah suka fita daga d’akin.
Tana jin fitarsu tatashi tana tafiya ahankali tashiga toilet alwallah tayi tazo tasa hijab tayi raka’atan fijir da tagama karatun alk’ur’ani tazauna tayi har aka kabbara sallah sannan tatashi tayi sallar asuba,
Gado takoma takwanta saboda wani irin bacci da takeji bata dad’e da kwanciyaba bacci yad’auketa.
**** **** **** ****
Tunda suka dawo suka sauke babban yaro gida suka wuce club danshi cewa yayi ba zai je ba.
A tsaye yake a wajen gidan sai saffa da marwa kawai yakeyi a wajen da ka ganshi ka san hankalinsa a tashe yake akan abinda ya aikata,
Tunaninsa na kullum yafad’o masa a rai, nan danan idanuwansa suka kad’a sukayi jawur.
hawayene suka fara fita daga idonsa, d’aga murya yayi yace innalillahi wa inna’ilaihir raji’un wannan wace kalar KADDARA CE Allah kakawo min mafita.
K’addarace taraboni daga gida, K’addarace tahadani da wad’annan mutanen har nayi wannan aika-aikar Allah kakawomin mafita a cikin K’ADDARA TA (na chubado mhmd) kuka yakeyi sosai kamar k’aramin yaro
WANENE BABBAN YARO
***** ***** ***** *****
Fahad umar shine cikakken sunansa suna zaune a garin kaduna a tudun wada.
Alh umar shahararren d’an kasuwane yana shigo da kaya daga k’asashe dadama shima wani lokacin yana fita da kayan Nigeria wasu k’asashen da suke buk’atarsu.
Yana da mata d’aya Hajiya Hafsat ‘yar jihar yola ce, da ‘ya’ya ukku khadeeja ce babbah tana da shekara 5 sannan aka haifi fahad dayake bi mata,
Saida fahad yakai shekara goma sannan aka haifi yar autarsu Fatima sun taso cikin gata gasu kyawawa sosai kasancewar mahaifiyarsu bafullatana ce ta usuli mahaifinsu kuma barumayene.
STORY CONTINUES BELOW

Sun taso cikin tarbiya kasancewar iyayensu tsaye suke wajen kula da yaran nasu.
Tunda khadeeja tagama secondary school dinta aka yi mata aure da wani d’an chairman din garin.
Fahad kuma aka fiddashi k’asar U.S.A domin yin karatun doctor,
kasancewar fahad bai da buri a rayuwarsa da yawuce yaga ya zama likita.
Bayan wasu shekaru Alh umar yak’ara aure ya auri wata customer dinsa bazawara mai suna hindatu.
suna zaman lafiya da mummy kasancewar mummy batada hayaniya sosai kuma tana da hak’uri kuma hindatu tana binta sau da k’afa.
hindatu bata ta6a haihuwa ko 6atan wata ba shekara biyar kenan da aurenta da Alh umar.
Bayan shekara biyar Fahad yakammala karatunsa yadawo gida anyi murna sosai da dawowarsa, lokacin khadeeja ‘ya’yanta biyu.
Lokacin ita kuma fateema tagama secondary school dinta a wata private school.
Tunda hindatu tad’aura ido akansa taji tana sonsa sosai kasancewarta tana bin maza, tunda fahad yaji matsayinta a gidan bai bin takanta domin ba ta gabansa harkarsa kawai yakeyi,
Ahaka har yasamu aiki a wani babban asibiti federal da yake garin kaduna.
Ammah ita sai ta tsiri shishshige masa ko unguwa zataje daddy takeyi ma magana yasa Fahad yakaita,
Insuna tafiya tayi ta jansa da hira ammah ba ya biye mata saidai tayi ta surutunta tagaji tayi shuru.
Daga nan sai ta tsiri zuwa d’akinsa domin suyi hira abinci ma ba ta bari yana cin na ‘yan aiki ita take girka masa,
Mummy tana jin dadi sosai ganin yadda hindatu take ji da yaranta.
Kunsan in akace mutum d’an duniya ne toh sai ahankali ahaka tasamu tajawo hankalin fahad yafara kulata, har d’akinta take jansa domin suyi hira daga nan shak’uwa tashiga tsakaninsu sosai komi yasamo wajenta yake zuwa domin yana ji da Auntyn tashi sosai.
Ranar wata asabar ne kasancewar ba aiki fahad ne zaune d’akinsa yana kallon labarai,
Wayarsace tayi ringing jawota yayi yaduba sunan da yagani ya bayyana jikin screen din yasa yayi murmushi tare da d’aga wayar hello my lovely Aunty,
Daga d’ayan 6angaren akace my son pls kazo d’akina ga wasu takardu nan katayani cikesu wlh tun d’azun nakeyi na gaji.
Shuru yayi batare da ya ce komai ba, hello fahad,
Toh Aunty ganinan zuwa, kashe wayar yayi bai jira jin abinda zata ceba.
Murmushi tayi ta wullar da wayar saman gado tace yau dai burina zai cika akan fahad mafarkina zai zama gaske.
Fridge tabud’e tad’auko jug din kunun ayar da ta had’a kasancewar ta san fahad yanason kunun aya sosai.
Wasu k’wayoyin magani guda biyu tazuba tamotse su tamaida cikin fridge d’in tana murmushin mugunta.
Daidai lokacin akayi knocking din k’ofar.
Dasauri takoma saman gado tazauna,
Yes shigo mana my son.
Turo k’ofar yayi yashigo, bakin gadon tanuna mai inda takardun suke tace pls have a sit mana banason wannan la6e-la6en da kakeyi in kashigo d’akin nan,
Yauwa ka ga takardun nan.
Zama yayi bakin gadon tare da d’aukar takaddun yana dubawa na wasu filayene murmushi yayi yace Aunty fili zaki siya ne,
Eh wlh shiyasa nakeson kaduba min kaga wane zai fi dacewa insiya.
Cigaba yayi daduba takardun daidai lokacin tatashi taje tabud’e fridge din tad’auko jug din da cup.
Gabanshi tazo ta aje mashi tare da d’aukar cup din tacika da kunun aya tace my son ga fa kunun aya d’azu nayi shi,
Kar6a yayi yana murmushi yace thanks my lovely Aunty itama murmushin tayi.
Fara sha yayi yana lumshe ido saboda dad’in da kunun ayar yayi tas yashanye shi sannan ya aje cup d’in.
Hammah yafari tare da lumshe ido yabude ahankali yace Aunty bari inje d’aki bacci nakeji kallonsa tayi tace toh.
mik’ewa yaso yayi ammah ya kasa duk kasala yakeji sai hammah kawai da yakeyi.
Kakwanta nan mana my son.
saman gadon ya ida kwanciya ba ayi minti biyar ba bacci mai nauyi yad’aukesa.
Ganin haka yasa hindatu tafara murna domin burinta ya kusan cika, kayan jikinta tacire tatsaya daga ita sai bra da pant.
Saman gadon tanufa rigar jikin fahad tacire tare da kwanciya saman k’irjinsa wayarta tajawo tadinga yi masu pics .
Har saida tagaji dan kanta sannan tadaina, murmushi tayi tare da gyara kwanciyarta a jikinsa a haka itama bacci yad’auketa.
K’arfe takwas din dare daddy yadawo daga kasuwa yagama shirinsa yana zaune shuru hindatu bata kawo mai abincin sa ba,
Tashi yayi yafito daga d’akinsa part din hindatu yanufa.
Daidai lokacin fahad yafarka daga bacci ahankali yabud’e idonsa,
Jin mutum a jikinsa yasa yamaida kallonsa akanta hankalinsa a tashe dasauri yatureta daga jikinsa yana salati.
Farkawa tayi itama. Mezangani haka meyake faruwa dani ne inji fahad,
Dasauri yasafko daga saman gadon itama safkowa tayi tana murmushi.
Ja yake da baya tana binsa yace Aunty miye haka mi kike shirin aikatawa da haka har yakai jikin bango idanuwansa yaruntse yana ta addu’o’i.
Saida tazo daf dashi har suna jin numfashin juna sannan tace fahad na dad’e ina sonka tun lokacin da nafara ganinka sonka yashiga raina da tunaninka nake kwana dashi nake tashi dan haka yau nakeso kabiya min buk’atata.
Dasauri yabud’e idonsa yace Aunty kinsan hakan baida kyau fa mahaifi na fa kike aure, koma ba hakaba ai haramun ne dan Allah kiyi hak’uri kikyaleni duk abinda kikeso zan baki.
Murmushi tayi tace fahad kai kad’ai nakeso kuma kai kad’ai nake sha’awa idan kayarda kabiya min buk’atata zan baka komi kake buk’ata idan kuma kak’i toh,
Pics din da tad’aukesu tanuna mai tace wlh zan nuna ma Alhaji da mummynka kuma ince ka dad’e kana bibiyata.
Hankalinsa a tashe yake kallonta ya rasa ya zaiyi da rayuwarsa duk tsoro yakamashi,
Ganin haka yasa tayi murmushi tace in ka amince bismillah inko baka aminceba toh kaima ka san sauran.
Kallon tsana yabita dashi yace wlh ba zan aikata ba saida kiyi abinda zakiyi Allah yana tare dani,
Bani waje inwuce rik’esa tayi tace wlh fahad baka isaba sai ka biyamin buk’ata ta Zaka fita daga d’akin nan,
K’ok’ari yake yak’wace daga rik’on da tayi mashi daidai lokacin aka bud’e k’ofa aka shigo.
Dukkansu suka maida kallonsu wajen mai shigowar abbah ne yashigo yana cewa hindatu wai bakisan na..
Maganarce tamak’ale a bakinsa ganin abinda idonsa yagane masa………