K’ADDARA CE CHAPTER 5

 K’ADDARA CE CHAPTER 5

Kallonta Hajiya maimuna tayi tace ni sunana Hajiya maimuna ni nakeda wannan resturent d’in na meenat resturent,

Na sa mashi suna meenat saboda sunan d’iyata ne ita kad’ai gareni mace sauran biyun duk mazane ina sonta sosai,+

Murmushi Amina tayi tace Allah sarki Allah yaraya su.

Ameen am kince kinason yin aiki a gidannan ko?

Eh hajiya in zan samu wlh inaso.

Eh zan d’aukeki aiki saboda ina tausayin rayuwarki dan haka girki ne sai serving d’in customers idan sunzo, salary zan dinga biyanki 3k per month tunda a nan gidan zaki zauna, ina bada 5k ga wad’anda suke zaune gidan mazajensu indai zaki zauna lafiya damu toh masha Allah muna maraba da ke banson tashin hankali ko da daga ganinki kamar ba zakiyi rigima ba,

Murmushin jin dad’i Amina tayi tace insha Allahu hajiya ba zaku sameni da matsala ba zan zauna daku tsakani ga Allah.

Toh shikenan kin kyauta saidai har ynz ban san sunanki ba,

Sunana Amini d’iyata kuma Ameerah

Woww nice name ashe namesake d’in daughter d’ina ce inji hajiya Amina tana murmushi.

Eh Hajiya.

Toh kije ga d’aki chan kusa da na babah salame zansa agyara maki sai kizauna ke da d’iyarki saboda zaki fi jin dad’in zama ke kad’ai.

Sannan sauran ayyukan zansa sukoya maki yadda suke tafiyar dashi

Toh Hajiya nagode sosai Allah yasaka da alkhairi, Allah yak’ara girma.

Ameen zaki iya tafiya.

Godia tak’ara yi ma hajiya sannan tafito tanufi resturent wajensu inna salame suna gwada mata yadda suke tafiyar da komai daga nan suka cigaba da serving d’in customers, tana goye da Ameerah Sallah ce kawai take tadasu daga wajen sai kuma cin abinci,

Tana jin dad’i sosai domin hakan yana d’ebe mata kewa,

Sai wajen taran dare sannan aka rufe resturent d’in sauran matan da ba kwana suke gidanba suka tafi gidan mazajensu, su kuma suka shiga gida,

‘Dakin da aka gyara mata d’an k’arami kusa da d’akin baba salame shi tanufa ledace a shimfid’e a d’akin sai ‘yar k’aramar katifa sai toilet daga ciki,

Kwantar da Ameerah tayi tashiga tayi wanka sannan tashirya takwanta.

Tunda sukayi sallar asuba suka fara gudanar da aikin girki kowa da abinda yake yi ba su suka gamaba sai wajen k’arfe goma,

Wanka tayi tashirya, tashirya d’iyarta  tayi  breakfast suka gaisa da hajiya sannan suka nufi restaurant domin gudanar da aiki.

Haka rayuwar Amina tacigaba da tafiya a gidan hajiya maimuna tana jin dad’in zama dasu, su ma suna jin dad’inta domin bata da k’yuyar aiki kuma tana ba kowa girmansa a matsayinta na k’aramarsu duk abinda taga ya dace shi takeyi ba ta shiga harkar kowa rayuwarta kawai take,

STORY CONTINUES BELOW

Duk abinda take buk’ata tana siye da kud’in da suka rage a wajenta, tana kula da d’iyarta sosai.

Ta samu kwanciyar hankali sosai a gidan domin batada matsala da kowa, saidai a kullum tunanin mutumin da yasa ta a cikin matsalar nan da burin sake ganinsa take domin ko kad’an ba ta jin haushinsa saboda yadda takejinsa a ranta, sau dayawa ta sha ta6oye a d’akinta tasha kukanta domin tasamu sauk’i a zuciyarta, wani lokacin har addu’ar shiriya take mashi da fatan dawowa gareta, itama kanta tana mamakin yadda yashiga ranta lokaci guda koda ta san k’addara ce tahad’a ta dashi ya mata nisa ammah ya zamo wata tsoka a cikin jinin jikinta.

*****   *****   *****  ******

A chan 6angaren fahad karatunsa yake hankali kwance saidai wani lokacin idan yazauna tunanin abinda ya aikata yana damunsa musamman fuskar yarinyar da take kuka a lokacin da yai mata aika-aikar tayi ta mashi gizo duk sai yaji yana jin haushin rayuwar da yayi a lokacin da abinda ya aikata,

Gashi gidansu bai fad’a ma kowa kalar rayuwar da yayiba saboda kar hankalinsu yatashi.

Yauma kamar kullum bayan sun fito daga lecture direct gidan da suka kama haya suka nufa shi da abokansa biyu, kowa room d’insa yanufa,

Wanka yayi yagabatar da sallah sannan yajawo wayarsa yakira mummynsa,

Fatima ce da salma zaune a main parlor suna kallo k’arar wayar mummy ce dake kusa da ita takatse mata kallo, hannu takai tad’auko wayar ganin wanda yake kira yasa tasaki murmushi dasauri tayi picking d’in call d’in tare da yin sallama,

A chan 6angaren aka amsa mata,

Cikin girmama tagaishe da yayan nata,

Murmushi yayi ya amsa tare da cewa my little sis ya kk?

Hmm yaya fahad kenan kaida ka mance da ni ko irin kace bari kakira k’anwarka ammah shuru ni fushi ma nake,

Ayyah am sowie my little sis wlh kina a raina a kowane lokaci kawai dai ina busy ne dat’s y kwana biyu baki jina.

Allah sarki yayana nima na yi tunanin hakan, toh y study,

Alhmdllh my little sis, ya naku dafatan dai kina maida hankali sosai baki wasa ko.

Eh wlh yaya ina maida hankali.

Fira suke sosai itada yayan nata

Kallonta takai wajen salma da tunda tafara wayar tatsareta da ido,

Murmushi tayi tace yaya fahad ga salma kugaisa,

Jim yayi sannan yace wacece salma kuma?

Cikin shagwa6a tace haba yaya har ka manceta salma fa d’iyar Aunty maijidda da take yola.

Ta6e baki yayi sannan yace oh ynz nagane zuwa tayi ne?

Ka mance na fad’amaka itama ta samu admission a school d’inmu shine take zaune a nan gida,

Oh god i forgot wlh am so sowie.

Dariya tayi tace yayana ko dai ka fara tsufane duka yaushe mukayi maganar ammah har ka mance.

Murmushi yayi yace ai da alamar hakan my dear sis.

Toh yaya gata kugaisa, wayar tamik’a ma salma a tsorace ta amshi wayar  a hankali tayi sallama,

Amsa mata yayi ciki-ciki shima,

Gaisawa sukayi sama-sama sannan yai mata nasiha akan tadage tayi karatun da yakawota banda wasa,

Godiya tayi masa, sannan sukayi sallama.

Mik’awa fatima wayar tayi yace My little sis mummy ba ta kusa ne?

Ayya yaya tana room d’inta a nan parlor ta mance wayar,  i think ma yanzu haka ta yi bacci sbd tun d’azu naji tana cewa bacci zatayi.

Ohk badamuwa my little sis i will call her letter, gud bye

Nan sukayi sallama suka aje wayar,

Kallon salma tayi da har yanzu bata daina kallonta ba, murmushi tasakar mata tace ya dai sister?

Itama murmushin tayi tace kawai dai kuna burgeni nima sai inji daman ni ke da bro kamar ke.

Hmm toh kema ai kinada Aunty mariya,

Ai ita macece duka fa mu biyune, ni inason inga ina da yaya namiji.

Ammah irinsu yaya fahad sai ahankali ni wlh wani lokacin har tsoro yake bani yanayin yadda yake d’aurewa kwata-kwata shi ba ya son wasa bai sakin fuska kuma bai shiga harkar kowa.

Kai my sis yanzu duk yayan nawa yake haka?

Eh mana kema ai kinsan halinsa.

Dariya sukayi sannan suka cigaba da kallonsu.

Fahad tunda suka gama wayar da little sis d’insa kiran friends d’insa yayi yace nifa yunwa nakeji kuzo muje musamo abinda zamuci daga chan sai muwuce library domin inason yin research kan wani abu da ban ganeba.

Had’ad’d’an restaurant suka tafi shi da abokansa biyu ‘yan nigeria sukayi order d’in abinci sukaci sannan suka wuce library,

Bayan sungama gida suka dawo kasancewar magrib ta gabata alwallah sukayi sukai sallah sannan suka zauna hira sai bayan sallar isha’i sannan kowa yakama gabansa domin suyi karatu.

Wajen k’arfe goman dare yagama karatun wanka yayi yashirya sannan yakwanta bacci.

Tunanin da yasaba yi yafad’o mashi a rai nan hankalinsa yafara tashi hawayene suka zuba daga idonsa yace innalillahi wa’inna ilaihiraji’un ya zanyi da wannan k’addarar dole inje insamu mutanen nen inbasu hak’uri ko nasamu sauk’in abinda nakeji a raina,

Shi dai a tunaninsa ya san tausayin yarinyar yakeji saboda bai kyauta mataba.

Zumbur yatashi zaune daga kwancen da yake yace innalillahi wa’inna’ilaihiraji’un auren da aka d’aura mana fa tabbas na san ban saketaba a lokacin ya akai hakan tafaru,

Dafe kansa yayi yace Wannan wace kalar k’addara ce tasameni me yake faruwa dani gaskiya dole inkoma innemi afuwarta da ta iyayenta sannan insauwak’e mata aurena da yake a kanta saboda hakan shine kawai mafita kusan shekara da wata hud’u kenan,

To kuma yaushe hakan za ta faru ni da ban Nigeria oh god,

Ammah dole insamo mafita domin very soon nakeson zuwa Nigeria ko dan saboda wad’annan bayin Allahn.

Allah gani gareka.

Kwanciya yayi yana ta tunanin yadda zai 6ullo ma lamarin daga k’arshe saida  yaga ya samo mafita sannan yayi bacci.

Bayan kwana biyu fahad yagama shirye-shiryensa visarsa tafito  yashigo Nigeria ta flight  yasafka kaduna ammah bai kira kowaba daga gidansu yafad’a masu zai zo saboda ya fi son sai ya dawo daga inda zai je sannan zai wuce gida,  domin idan yafara safka gida zai sha wuya kafin iyayensa su amince da tafiyarsa,  kuma yace masu ina zaije alhalin ba ya son susan halin da ake ciki dan kada hankalinsu yatashi,+
Direct  flight d’in katsina yayi booking yabi cikin yan mintina kad’an suka iso garin katsina, mai adaidaita sahu yasamu yace tashar motar mashi za a kai shi,
Ya yi sa’a motar mutum biyu take jira a tashi,
Shiga yayi yaga za’a 6ata masa tym yace atafi zai biya kud’in mutum d’ayan da babu.
Bayan minti talatin suka isa mashi kallon garin kawai yake yadda cikin shekara da watanni ya d’an canza masa.
Murna yakeyi domin zai gamu da su ogah burinsa ina su ma sushiryu sudaina abinda suke,
Da zaiji dad’i sosai zai iya d’aukar nauyin komai nasu indai za su shiryu.
Hotel yasamu mai tsada yakama d’aki bayan ya yi sallah ya ci abinci ya nutsu yafito yasamu mai adai-daita yafad’a mashi inda zai kaishi.
Tafiya sukayi mai nisa sannan sukazo wajen dajin yasafka yabiya mai adaidaita sannan yanutsa ciki.
Tafiya kawai yake dakyar yake gane hanya domin dajin duk ya canza ga manyan ciyawu da suka fito kamar ankwana biyu ba a bi hanyar ba,
ahaka har ya iso gidan, gabansane yafad’i ganin yadda gidan yakoma bango har ya fad’i direct cikin gidan yanufa jikinsa duk ya yi sanyi,
Gidan duk ya yi k’ura ga yana, hankalinsa yak’ara tashi ganin kamar anshekara ba a Shiga gidan ba,
Lek’a ko ina yayi sak’o da lungu yaga babu alamar mutane na rayuwa a wajen d’akunan duk yana.
Hankalinsa a tashe yace toh ina suka je ko dai sun bar nan d’in sun canza waje ko kuma sun shiryu sunkoma ma iyayensu suma tambayar kansa kawai yake ammah ya rasa amsar tambayar,
Yace ni yanzu ya zanyi su da nazo surakani gidansu yarinyar inbasu hak’uri tunda ban gane gidan, ko sunan anguwar ban saniba tunda a mota mukaje ranar kuma cikin darene to wai ya ma haka ta kasance,  dafe kansa yayi yace wai mi yake faruwa da ni ne wannan wace kalar k’addara ce!
‘Daga murya yayi yace ina kuka shigane cha6o, kwaro, cinnaka kuna ina kuzo gani nazo gareku dan Allah kufito wai mi yake faruwane.
Sai da yak’ara bincike gidan sannan yak’ara tabbatar da tabbas sunbar gidan murmushi yayi yace ina ma ace zan ganku kun shiryu ku ma.
Dafe kansa yayi hankalinsa a tashe yace toh ni ynz ina zan gano gidansu yarinyar nan.
Fitowa yayi daga dajin ganin rana ta fad’i yanufi hotel d’in da yakama,
STORY CONTINUES BELOW
Wanka yayi sannan yayi alwallah yatafi masallaci bai baro masallaci ba sai bayan ya yi sallar isha’i
Daganan sai yashiga gari yana bincika ko Allah ya sa yagamu da ko mutum d’ayane daga cikinsu ogah ko kuma yagamu da yarinyar ko mahaifinta.
Haka yayi ta wahala yana yawo sai wajen goman dare yakoma hotel d’in.
wanka yayi sannan yayi shirin bacci.
Saida yadad’e yana juyi akan gadon da tunani barkatai sannan bacci 6arawo yasaceshi.
Tunda yayi sallar asuba yakoma bacci ba shi yafarka ba sai wajen 11am,
Wanka yayi yashirya yakira aka kawo mashi breakfast yayi sannan yakama hanyar cikin gari domin har a lokacin yana sa ran k’ara ganin ko mutum d’ayane daga cikinsu haka yayi ta yawo sau biyu yana komawa gidan da sukayi rayuwa a ciki ammah ko giftawar mutum bai ganiba saida yaji ya gaji sosai sannan yakoma masaukinsa.
Ko da yayi sallar isha’i yabazama nemansu yau ma kamar jiya sai wajen 10pm yakoma masaukinsa hankalinsa a tashe domin baiyi nasarar ganin ko mai kama da su ba,
Kasa cin komai yayi a lokacin saboda bak’in cikin rashin ganin kowa daga cikinsu, gashi gobe yakeso yawuce gida domin yaga danginsa daga chan yakoma school,
A ranar baiyi baccin kirki ba duk yadda hankalinsa yayi dubu toh ya tashi,
Juyi kawai yake idanuwansa kad’awa sukayi sukai jawur cikin d’aga murya yace shikenan ni kuma tawa k’addarar kenan meyasa hakan takasance da ni wannan wace kalar rayuwace.
Ya ubangiji ka fi kowa sanin halin da nake ciki,  gareka na dogara ya Allah kakawo min d’auki a cikin rayuwata.
Sai wajen k’arfe biyun dare sannan bacci yad’aukesa.
Tunda yayi sallar asuba bai koma bacci ba yana saman darduma karatun alkur’ani yayi saida yaga gari ya yi haske sannan yayi addu’a yakoma bacci.
Chan cikin baccinsa yajiyo ringing d’in wayansa ahankali yabud’e idonsa tare da jawo wayar, ganin Wanda yake kiransa yasa yayi picking dasauri tare da tashi daga kwancen da yake.
Dasallama Yad’aga wayar yace mummy ina kwana?
Daga chan 6angaren ta amsa masa tare da murmushi tace ya kk my son?
Lafiya lou mummy
Hmm shine kwana biyu ba a ko nemanmu,
Sry mummy wlh ina ta son inkiraku.
Hmm haba my son ashe zaka iya yin kwanakin nan ba tare da kaji lafiyar mu ba.
Please mummy pardon me insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba.
Bakomai my son ai ba fushi nayi ba, Allah yayi maka albarka.
Ya naji muryarka haka kamar bakada lafiya?
Lafiyana lau mummy kawai bacci ne nake, 
Mummy yau zan baki surprise,
Name kuma my son,
Hmm kuduba hanya yau ina nan tafe.
Hmm bana son wannan zaulayar taka kaida tun tuni muke fama da kai kazo ammah kak’i kuma baka fad’a mana zaka zo ba sai yanzu.
Dariya yayi yace mummy wlh am serious insha Allah nan da 3 hours ina gida.
Kai my son gaskiya na ji dad’i sosai Allah yakawo mana kai lafiya bari infad’a ma su fatima daman suna ta tsogumin rashin zuwanka,
Murmushi yayi yace Allah sarki my lil sis ai yau za ta ganni.
Fira sukayi sosai da mummyn tasa daga k’arshe sukayi sallama kowa yana murna.
Komawa yayi saman gadon ya lumshe idonsa zuciyarsa babu dad’i domin ko wayar da yake da mummy saida yadaure ya6oye damuwarsa dan kar tagano yana cikin matsala hankalinta yatashi.
Ahankali yabud’e idonsa yasafkesu akan agwaggon da take jikin bango,
Zare ido yayi dasauri yayi wuf yatashi tare da cewa 12:30 kuma?  Ko dai batada saiti clock d’in, 
Wayarsa yajawo yaduba sannan yak’ara tabbatar da hakane.
Wanka yayi yashirya cikin farar shadda ya yi kyau sosai.
Breakfast yayi yad’auki kayansa sannan yafito yaje reception ya basu key d’in room d’in sannan yabiya kud’in da ake binsa yakama hanyar katsina.
Basu dad’eba suka iso katsina.
Booking yayi yabi jirgin k’arfe biyu cikin ‘yan mintina kad’an suka iso garin kaduna.
Tun kan su ida isowa yakira driver d’in gidansu yasanar da shi yazo yad’aukesa bai kira su mummy ba saboda ba ya so suzargi wani abu idan sukaga daga garin da yafito.
Suna isowa yatadda sa yana jiransa zuwa yayi suka gaisa yayi mashi sannu da zuwa sannan yakar6i jakarsa suka kama hanyar gida.
Lokacin da suka isa gidan farinciki fal acikin ransa dasallama yashiga.
fatima da salma ne a tsakar gidan duk sunyi ado gwanin kyau kular abincine suka d’auko zasu nufi main parlour dashi, ganinsa yasa fatima tasaki k’ara tare da aje kular k’asa tanufi wajensa dagudu tana oyoyooo yayana,
Jikinsa tafad’a suka rungume juna suna murna sannan tad’ago daga jikinsa tace u ar highly wlcm back my big bro.
Murmushi yayi tare da jawo dogon hancinta yace thanks my lil sis,  ya kuke?
Lafiya lou yayana daman kana hanya shine baka fad’a manaba domin muzo mud’auko ka.
Daidai lokacin salma ta iso wajen tana murmushi tace yaya fahad sannu da hanya dafatan andawo lafiya.
Kallonta shima yayi yana murmushi yace lafiya lou,  salma Ko?
Eh nice.
Daidai lokacin mummy tafito daga d’aki tace wai hayaniyar me nakeji haka a gidan.
Curus tayi tatsaya tace my son daman kaine kadawo? Mu muna ta shirin zuwa tarboka ashe kai har ka iso.
Wajen mummynsa yanufa tare da rungumeta yace sorry mummy malam idi nakira shi yad’auko ni dafatan na sameku lafiya.
Murmushi tayi tace lfy lou my son mushiga daga ciki.
A ranar sunsha murna har yaya khairat saida tazo gidan ita da yaranta biyu.
Dady saboda murna baije ko ina ba nan aka baje main parlour ana ta firah cikin raha da jin dad’i cike da k’aunar junansu.
****    *****     *****    ****
Amina ce cikin restaurant d’in suna ta serving d’in mutane daidai lokacin wasu mutane biyu suka shigo suka zauna wajensu Amina tanufa tana tafiyarta a nutse,
Tunda ta tafo d’aya daga cikinsu yakafeta da ido har ta iso.
Sallama tayi masu sannan tace me za a kawo maku,
‘Daya yace tuwon shinkafa miyar ku6ewa d’anya yakeso,  kallon d’ayan yayi da yatsareta da ido murmushi yayi yace Alh faruk kai kuma fa me za a kawo maka.
Shuru yayi na d’an lokaci Amina har tagaji da tsayuwar da take gashi duk ya tsareta da idanuwansa d’ago kai tayi takallesa.
Murmushi yasakar mata yace komai kikaga ya dace da ni kikawo min zanci.
Kallon mamaki tayi mashi tace a’a mu nan mutum shi yake za6ar abinda yakeson ci.
Toh ni kuma na baki za6i duk abinda kika kawo min zanci.
Amina tayi-tayi yaza6a ammah yak’i yace takawo mashi koma minene zai ci.
Ganin zai 6ata mata lokaci yasa tawuce tazuba mashi waina da miya takawo mashi.
Murmushi yayi yace woww thanks kamar kinsan favourite food d’ina ne kika kawo min.
Murmushi kawai tayi ba tare da ta ce komai ba tajuwa za ta wuce yace am bakiji ba ‘yanmata.
Ahankali tajuyo tasafke idonta a saman kyakkyawar fuskar mutumin, murmushi yasakarmata a karo na biyu yace saura drinks da ruwa.
Ba tare da ta tanka mashiba tawuce tad’auko masu takawo.
Murmushi yayi yace thanks ‘yanmata ko zan iya sanin sunanki?
Shuru tayi takyalesa kamar bata ji abinda yace ba, saida yak’ara maimaita mata
‘Dago kai tayi zata mashi masifa kawai sai tafasa ganin babban mutumine tunda ak’allah zai kai 42yrs bai dace tayi mashi hakaba tunda ya girmeta.
Ba tare da ta tanka mashiba tawuce tayi tafiyarta.
Binta yayi da kallo yana murmushi domin shi ji yake yarinyar ta burgesa saboda akwai hankali da nutsuwa.
Abokin ne yakallesa yace Alh faruk wai miyake faruwane tunda kaga wannan yarinyar duk ka bi ka chanza me kake nufi da hakan ne?
Kallonsa Alh faruk yayi yace Alh Abdul ba zaka gane bane wlh yarinyarce ta kwanta min a rai.
Ba dai kana nufin sonta kake ba?
Nima dai ban saniba ammah gaskiya kusan hakane,  mugama cin abincin sai muyi maganar.
Bayan sun gama cin abinci suka kirata taxo tak’ar6i kud’in.
Fuskarta a d’aure ta iso inda suke murmushi Alh faruk yasakarmata yace ‘yanmata nawane kud’in.
Dubu da dari biyar tace a gadarance.
Five thousand yad’auko yamik’o mata,
Kallonsa tayi tace kud’in ai sunyi yawa.
Murmushi yayi yace bakomai ai dad’in abincinma ya ci ace ya fi haka kikar6a kawai.
Gaskiya ba zan kar6a ba saidai kabani dai-dai wanda nace.
Ni kuma haka nayi niyya indai ba so kike mukwana a nan ba toh ki kar6a.
Hannu tasa takar6a tare da juyawa za ta tafi yace am ‘yanmata baki ji ba.
Juyowa tayi tare da k’ara tsuke fuska tace ya akayi?
Bakomai ammah dan girman Allah kifad’a min sunanki.
gaskiya kayi hak’uri ba zaka samuba, 
Bata jira jin abinda zai ce ba tayi tafiyarta.
Har ya tashi zai bi ta Alh Abdul yayi saurin rik’eshi yace haba kabarta mana saikace za ta guje mana, yarinyarce da alama kamar za a sha wuya kafin ashawo kanta,
Jan numfashi yayi yace toh yanzu Alh Abdul ya kake ganin za a yi domin ni dai wlh yarinyar ta kwanta min a rai ina sonta.
yanzu dai tashi mutafi gobe inmundawo sai muyi mata magana idan tak’i bamu had’in kai sai mubi ta wajen shugabarsu.
Alh faruk ya yarda da shawarar abokin nasa dan haka yatashi suka tafi.
Amina da tabaro wajensu Ameerah ta amsa daga wajen gwaggo salame da ta tashi daga bacci sai kuka take.
STORY CONTINUES BELOW
Cikin gida takoma tashayar da ita tasamu tayi sallar la’asar sannan ta rungume abunta tadawo restaurant d’in suka cigaba da sana’ar su.
wajen k’arfe tara suka rufe restaurant d’in suka kwashe komai suka koma cikin gida saida suka gyara komai sannan kowa yanufi d’akinsa.
Amina tana shiga d’aki tasafke Ameerah da take goye tana bacci lalla6awa tayi ta ajeta sannan tacire kayanta tanufi toilet domin tawatsa ruwa.
Bayan ta fito ta yi shirin bacci addu’a tayi takwanta,
kogin tunanin da tasaba tafad’a domin ya zamemata kamar farilla ne ba ta iya bacci ba tare da ta yi tunaninsa ba, itama kanta har tausayin kanta take yadda akayi lokaci guda tafad’a tarkon k’aunar Wanda baisan tana yi ba.
Hawaye ne suka zubo daga idanuwanta a fili tace ya kamata indaina tunanin Wanda baisan ina yi ba,  maybe ma ya mance da rayuwata a duniyar bare ta d’iyarsa da baisan da itaba.
Shin waima idan Ameerah tagirma me zan ce mata? Tunowa tayi da abbanta da hidimar da yake mata ita da d’iyarta batare da ya gajiba fashewa tayi da kuka tace Allah sarki abbanah Allah yajik’anka da kana nan da ba zan shiga wannan k’uncin rayuwar ba,
Saida tayi kuka mai isarta sannan ta lallashi kanta takwanta tayi bacci.
Tunda sukayi sallar asuba suka fara aiki domin hakan ya zame masu jiki.
Ko da suka gama aikin ruwan zafin wanka tad’aura tayi dan kar Amirah tatashi, sannan tad’auki Ameerah tayi mata.
Bayan sungama sukayi breakfast suka nufi d’akin hajiya suka mik’a gaisuwa sannan suka wuce wajen sana’arsu.
Yauma kamar jiya wajen k’arfe ukku suka shigo restaurant d’in raba ido suka farayi har saida suka hango Amina da take kai ma wasu abinci.
Ko da tagama bata lura da suba takoma wajen zamansu Kasancewar Hajiya maimuna ta fito itama yau ita take kar6ar kud’i  zaune take tana had’a kud’i tace Amina ga fa wasu customers chan ba a kaimasu abinci ba kitambayosu kiji me suke buk’ata.
Amina kallonta takai wajen wad’anda akace su ma ita suke kallo tabbas ta ganesu na jiyane.
Shuru tayi kamar kar taje ganin hajiya ce dakanta tayi mata magana yasa tatashi tanufi wajensu dan gudun 6acin ran hajiya, fuskarta a d’aure.
Sallama tayi masu tare da tambayar me za a kawo madu.
Yauma gogan tunda ta taso yatsareta da idonsa tana ganin haka tak’ara tufke fuska,
Abokin ne yayi gyaran murya yace kikawo mana fried-rice,
Ku dukanka?
Alh faruk yace idan kika zubo min ita nima ai zan ci tunda daga hannunki tafito ‘yanmata,
Ko kallon inda yake batayiba tawuce taje tazubo masu takawo sannan takoma tad’auko masu lemu,
Alh Abdul yace Yauwa sannu mungode dan Allah idan ba zaki damuba munason magana da ke.
K’ara tsuke fuska tayi tace gaskiya kuyi hak’uri banda lokaci.
Haba minti biyar fa ya isa dan Allah inji Alh faruk kamar zaiyi kuka.
Ammah ai kunga aiki nakeyi,
Eh munsan da haka taimaka mana za kiyi ai.
Ba tare da ta kallesuba tace kuyi hak’uri ana jirana.
Wucewa tayi takoma wajen zamansu duk yadda zata d’ago kai sai ta ga mutumin yana kallonta.
Ganin haka yasa tatashi tace ma hajiya bari tashiga gida tadawo.
Tunda suka gama cin abincin sukaga shuru bata fitoba.
Alh Abdul ne yakalli Alh faruk yace inaga fa mutunniyar guduwa fa tayi dan kar mudameta.
Numfashi Alh faruk yaja yace nima abinda nake tunani kenan,
Yauwa ga shawara muje muyi magana kawai da shugabar tasu kamar Zaifi.
Tashi sukayi suka nufi inda hajiya take zaune sukayi mata sallama.
Cikin sakin fuska ta amsa masu.
Sukace sungama cin abincin nawa za mu biya plate d’in fried-rice biyu sai maltina itama biyu.
Ohk,  1,500 zaku biya,
Alh Faruk yaciro check yarubuta mata 50,000 yamik’a mata,
Hannunta yana kyarma takar6a tace Alhajin Allah wannan kuma na minene ranka yadad’e.
Kallon juna sukayi su biyun sukayi murmushi ganin alamun samun nasara.
Sannan Alh Abdul yace hajiya tun jiya da mukazo cin abinci abokina yaga d’aya daga cikin ma’aikatanki yaji yana sonta shine mukaga kamar ba zata aminceba sai mukayo ta wajenki.
Wace daga ciki kenan.
Kwatanta mata ita sukayi,
Hajiya tagane Amina suke nufi tace gaskiya kuban lokaci zamuyi magana da ita.
Toh ba matsala hajiya kamar yaushe yadace mudawo.
Eh to zuwa jibi.
Toh Allah yakaimu nan sukayi mata godia suka tafi.
Hajiya sai murna take ganin irin kud’in da aka fara sakar mata lokaci guda.
*****     *****     ****    ***
A chan 6angaren salma tunda fahad yadawo hankalinta yatashi domin ya shiga ranta sosai ji take ina ma ya amince da ita suyi aure ko da baya sonta itadai tana sonshi a ranar kasa baccin kirki tayi sai tunaninsa kawai take.
Gaskiya ya kamata infara shiga sabgar guy d’in nan ko da ba kulani yake ba na san wata rana shima zai fara sona,
Tashi tayi zaune daga kwancen da take tace toh ya zan 6ulloma al’amarin? Saida tadad’e tana tunani sannan tayi murmushi tace yaya fahad ina sonka kuma kaima dole kasoni.
Komawa tayi takwanta ahankali har bacci yad’auketa,
Tun da safe da tatashi wanka tayi tatsaya gaban dressing mirror tana tsantsara kwalliya kamar wadda zataje gasar sarauniyar kyau itama kanta saida tayaba da kyaun da tayi.
Material ne maikyau maroon colour tasaka tana cikin d’aura kallabi fatima tashigo d’akin kallonta tayi tace wow sis kinyi kyau sosai wlh ina zakije ne haka?
Murmushin jin dad’i salma tayi tace babu inda zanje my sis.
toh wannan kwalliya haka kamar zakije gasar sarauniyar kyau? Kifito muyi breakfast inji su mummy muna a dining
Ohk, am coming.
Saida tagama murza d’aurin kallabinta tak’ara duban kanta a mirror sannan tafeshe jikinta da turare.
Tafiya take cikin takunta tanufo dining sallama tayi sannan tagaishe da su mummy.
Mummy tayi murmushi tace masha Allah my daughter kinyi kyau sosai,
Fatima tayi dariya tace kamar wata amarya.
Kallonta takai inda yake zaune abincinsa kawai yakeci tunda tafito ko inda take bai kallaba,

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *