KANDALA CHAPTER 13 THEND QARSHE

KANDALA






CHAPTER 13 THE END QARSHE







Murmushi tayi tafara kokarin rufe fuskarta.. +

” shafa cikin yafariyi yana kissing dinta ina sonki ina kaunarki you know that i miss you dear Please karki hanani…

” jikinta ne ya mutu cikin hawaye ta toshe bakinta…

” ke daina kuka dear wannan kukan naki yakan tabamin zuciya komai Allah ya rubuta zai faru to sai yafaru, dan haka ki daina kuka domin kuwa Allah ya riga ya rubuta hakan zai faru agarek’i kuma ki godewa Allah my wife i love u so much dear…

” Bakomai mijina Allah ubangiji ya barmu tare…

” Hawayen fuskarta yasa hannunsa ya goge..

” A hankali tace kamar sallama nakeji yaya..

” Koma wanene ya koma ina jin dumin jikin naki zaizo ya rabamu

” murmushi tayi tare da jindadin maganar tasa sannan ta fuskance shi bari naje na duba kaga anata sallama…

” shiru yayi sannan ya saketa da alamun baiji dadin maganga nun nata ba….

” hijjabin kan bed din ta dauka sannan ta fita zuwa palour sadik tagane…
” ina yini Anty aisha?

     ” lafiya lou sadik yasu umman ka?

        ” Suna nan kalou gashi tace in kawo miki wai sai tazo…

     ” Toh kace Nagode, kitchen ta nufa tana budewa taga farfeson kifi ne da couscous sai zobo, murmushi tayi tace Allah sarki makotan kirki…

     ” Dak’inta ta huce Alwala tayi sannan tayi sallah wata green din body hug ta dakko ta saka tayi mata kyau sai ta fesa turare….

     ” cikin rashin jindadin rabuwarsa da kande ya miki yasa jallabiyar sa sannan ya fita zuwa masallaci…

    ” Tana fitowa ta jera abinci a dinning sannab ta kunna kallo tana zaune wayanta yafara ringing dauka tayi tace hello anty…

     ” yauwa kande dama nakira nakara tuna miki dacewa duk abunda yafaru yafaru fa abunda ya huce ya huce ki dauke abunda yafaru abisa Alkhairi kuma ki daina damun kanki kokuma yawan tunani ki nunawa mijinki kulawa da soyayya….

    ” Tohm Antu inshaa Allah, please inason mai kitso da kunshi…

     ” Gobe zantawo miki da mai kunshin Amma kitson nayimiki….

     ” Sukayi sallama, Haruna yana shigowa yaganta zaune tana kallo tayi bala’in kyau gawane kamshi da ya kaure ko’ina….

     ” sannu da zuwa yaya ina fatan anyi mana addu’a…

    ” Nayi miki Addua Allah yakawo yan biyu sau biyar…

    ” bata rai tayi ta kau da fuskarta!

     ” cikin murmushi yakaraso kujerar datake zaune ya riki hannun ta sannan yace ina kaunar ki Aisha kau da fuskar ki da fushin ki sai naga kamar baki yafemin abunda yafaru ba…

    ” Hannunta ta saka tana kokarin rufe masa baki, sannan ta kwanta Akirjen sa Ne Ba haka nake nufi ba….

    ” Amma kinsan yadda nakeson ‘ya’ya ko?

     ” Dagowa tayi tana kallon idon sa dake kokarin komawa red, Cikin kissa tace bafa kace abinci ba?

     ” Mikewa yayi yana murmushi yace kaddai kice mumy ce tabayar Aka kawo?

    ” maman sadik ce ta bayar…

    ” zubawa yayi sannan ya dawo kusa da’ita yace oya open your mouth…

     ” Shagwabe masa tayi tace nifa kai nakeso kace…

      ” Ni kuma sai kin koshi sannan zan iya sakawa acikin bakina, oya bude mana…

     ” budewa tayi cike da sauken kaunarsa ya zuba mata har sai datace ta koshi….

    ●●●●●

        Firdausi ke zagaye acikin palour dinta Aliyu yana shigowa tace sweety farida tana asubuti fa….

     ” subhnlhi to shirya muje Allah ya raba lafiya…

    ” tunda sukaje asubutin su mumy goggo inna ummi duk sun cika asubutin hamza in banda murna babu abunda yakeyi…

    ” Dady ne tace gatanan kamar ku daya…

     ” Mumy tace wallahi da kande yake kama yaron nan…

    ” hamza bai kula da hakan ba sai da yakara zuba mai ido…

    ” goggo tace shiru ma basu karaso ba kafin goggo ta rufe bakinta sai Taji anyi sallama…

    ” Haruna ne ke ruki da hannunta tasaka black abaya da jaka sai powder da lipstick sunyi kyau sosai…..Durkusawa sukayi har kasa sannan suka gaishe su, kande mikewa tayi tace bana baby boy din naganshi ya hamza… +

     ” Kallonta kawai yakeyi yadda tayi wane kyau ga kiba…

      ” Lah ya hamza hanani zakayi toh mai jego dashi zan tafi, aka saka dariya kande sai wasa takeyi masa…

    ” firdausi tace kuma bakiga yadda yayi miki kyau ba kamar babyn ki, wama yasane ko kema kin kusa…

     ”  Ai kuwa kinga kamar tamu, shikenan Nasamu d’a…

      ” ya Ali ne yace sai kiyi kokaro kema ki samu naki ai…

     ” Shiru tayi tana kallon yaya da hankalin sa gaba daya yana kallon ta…

     ” Tashi mu tafi Esha kinga inada tafiya gobe…

    ” Please kabarni sai nabi su mumy…

     ” cikin sanyin murya yace toh, Har yafita tace au bari na bashi wayarsa…

      ” Tana fita ta ganshi ya saka kansa akan sitiyari, bude motar tayi tace yaya lafiya…

        ” bai kalleta ba, balle ya dago kansa…

  ” Hannun ta tace yaya please kayimin magana banson…

     ” bakyason bacin rai na Amma kikeyin abunda zaki batamin, yaushe zaki gane rashinki akusa dani yafe komai masifa…

    ” Kayi hakuri mijina bazan kuma ba Naga gobe zakayi tafiya ne…

     ” kallon ta yayi sannan yaja motarsa bai tsaya ko’ina ba sai cikin gidansu yana shiga ya huce dak’insa wanka yayi ya kwanta…

    ” Oh ne kande duk dan yaga hamza yana ta kallona shine ya bata fuskarsa, banda abin yayana shi kadai nakeso kuma dashi zanyi rayuwa murmushi tayi tace Nasan matsalarka ai, wanka takarayi sannan ta saka kayan bacci tashafa humra sannan ta nufi dakinsa….

     ” Tana kwanciya ya juya mata baya, Murmushi tayi kawai ta kwanta..

     ” Kamshin turare ne ya ishesa yana jiyowa yaga tana hawaye rungumeta yayi yana shakar kamshinta please karki ce zaki rabu dani please matatah…

    ” yana yake kissing dinta shi yafe bata tausayi Nan yafara aika Mata sako Nan tafara yimasa respondn ina tuni ya gigece yana ambatar sunan ta cike da kauna bai rabu da’ita ba sai 3…

    ” Al’adarta ce bata taba barin janaba wanka tayi sannan taje ta kwanta tare da Addu’o’i kallonta kawai yakeyi sannan yajata kusa dashi…

   Da safe tana tashi ta hada musu break fast sanadiyar zafin da taje garin nayi yasa tasaka wata gajeriyar riga mai hannun vest sai skirt…

    ” Kinga yanzu flight zai tashi i need to go..

     ” Wallahi banson tafiyarka Amma sai kace abinci Allah zaka tafi…

     ” murmushi yayi sannan ya kai bakinsa nata kusan 3minute sannan yace Ganawa abincin…

     ” Ne Ne Ne kayita gogen lipstick dina???

     ” Ai danne akasaka dan haka Na koshi yanzu kikular min da kanki kiyimin Addu’a please ki kula da babyna….

    ” To tace sannan ta huce zuwa kitchen..

    ●●●●●●

    Yusrah bantaba tunanin zaki shiryu ba har ki koma haka…

    “Alhamdulilahi da ubangiji ya hadani da mahaifiya tagare, a kullum kinayi min fada dangani da rayuwar Nan ba ma tabbaciya bace, Ada ba rayuwa   Nakeyi ba sai yanzu Tsoron Allah ya kara mamaye min zuciyata, babu Abunda zance miki sai dai Allah yabiyaki ummata Ni kuma Allah ya yafemin…

    ” Allah yakara shiryamin ke..Ameen ummata please umma inaso kije kano ki bawa kande hakuri akan abunda nayi mata domin ina tsoron hakkin ta akaina… +

    ” Bakomai shirya mu tafi…

    ” Wayar yusurah ce tafara ringing bata dauka ba har sau uku..

     ” wanene yake kiranki kika k’i dauka?

       ” Wallahi umma babana kullum maganar sa naturo masa kudi…

      ” Amma karki manta mahaifin kine sai ki dauka…

    ” hello dady ina yini?

            ” Are you stupid how many times nakira baki dauka ba million 1 Nakeso..

     ” kuka yusrah ta saka sannan tace Wallahi kaje tsoron Allah ya kai mahaifina, kowanne uba nagare yana fatan ‘yarsa ta kasance agidan ta, Amma kai ka bambanta kullum hanyar dazan samo maka kudi kakebi; wallahi ubangiji Sai ya tambayi ka dangane da tarbiyata….

    ” uwarki sai dai takaiki ta baro ki, hanyar da zakije dadi nake nemar miki…

     ” Jindadi na bazai huce Na kasance cikin ambaton Allah da aikata aiki nagare bin maza son abun duniya duk ba na muminai bani ba, farkon mu mukasani bamusan karshen mu ba duk jindadin da zamu samu ba zai huce na dan lokaci ba, fitar rai, kabare,alkiyama, wuta duk gaskiya ne, kayi hakuri mahaifina banida kudin da zan turo maka…

     ” har cikin ran umma taje dadi sosai da sosai Addua taketayi Allah yakara tsaremun yusrah, ticket suka siya zuka tawo….

   ●●●●●

      Tun karfe 12 mai kunshe tazo anty ce tayi mata kitso ba karamin kyau tayi ba sannan akayi mata ja da baki, sai gurin karfe 4 suka gama aka gyara gida Anty tace ki markada ayar nan kisa mata zuma kiyita sha har dabinon zaki hada…

     ” Wallahi anty wannan zogalen dana sha har naji canji..

    ” Sallamar yaya Abbas sukaje, ohhh Abbas tun kafin kazama wane ka yanke zumunci ko?

    ” kande ce suka gaisa tace munata jiran antyta mu..

    ” antyn ku tana tafi nan da 3days za’akai kudi…

    ” wacece?

      ” kafin ya fada mata yusra da ummanta suka shigo…

    ” kirjen kande ne ya buga can ta daure tace sannun ku…

    ” gaisawa sukayi da umma sannan tayi ta bawa kande hakuri ..

    ” yusrah da Abbas sai kallon juna sukeyi har kasa abbas ya gaida umma…

   ” cikin hawaye yusrah tace Nasan cewa idan aka fasa kwalba ba lallai a iya hadeta kamar da ba….

    ” Murmushi kande tayi tace wane sa’in takan hadu in ankaita gurin wanda ya k’erata…

    ” Nan anty tace ai babu komai Allah ya yafi mana baki daya…

    ” Bayan sun tafi abbas yake fadin Ai ita yakeso…

    ” Kande ce tace toh Allah ya sanya Alheri..

    ” Sukace Amin…

●●●●●

    Wayyo madam ki taimaka mine kada na mutu dubi yadda nakoma bazan iya fasa dutsen nan ba….

     ” bulala ta zuba mata sannan ta watsa mata ruwan zafi, Ne zakicewa na tausaya miki to in baki bini a hankali ba kashe ki zanyi…

    ” kukan datakeyi acikin gidan yaren shi yafe tsorata wata mata…

    ” Lallai muneebah kin shuka tsiya dubeki yanzu babu kudin babu kyan babu gatan, wallahi jaba ma tafiki kyan gane…

     ” Ai wallahu bazan kyaleta ba daga ita har haruna…

     ” kice baki sadu dabah??

     ” ai sai na kashesu tukunna yanzu nasan tana da ciki so nakeyi in kin fita kisa A zubar mata…

     ” ke dai anyi shaidaniya to ne natuba nabi Allah kallon banza ma bazan karayiwa wane ba Ballantana nasamu zunubi, mugayen Aiyukan danayi kullum addu’a nakeyi Allah ya yafemin, tunda ke kinzama mai bakar zuciya to sai kiyitayi banza matar shedan…

     ” Kafin takarasa magana taga madam ta watso mata ruwa. Fitsarin gurin kije kiyi wanken sokawe…

     ” Da rarrafe muneebah ta fita…


     ●●●●●●

   Kande tana zaune cikin wata rigar bacci tana kokarin fita ta rufe gida sai taje sallamar haruna..
  
     ” cikin mamaki tace yaya kaine?

      ” Murmushi yayi sannan yace nine nafasa sati dayan…

      ” Amma hakan bazai jawo tangarda ga sana’arka ba?

     ” Kusa da’ita ya dawo hannunta yakurawa ido yadda sukayi kyau, cikin murya mai cike da Nauyi yace Wallahi bazan iya nisa dake ba sai dai mutafi tare…

    ” kamar yaya?

          ” Hannunsa yasaka akamakam.fuskarta ina masifar kaunarki esha i cant live without you tunda na tafi nake tunanin ki… +

     ” Wane tausayin mijinta taje tace toh tashi kayi wanka sai Na hada maka tea..

    ” bayan sun gama komai kwanciya tayi abisa kirjensa tana kokarin yin bacci, baisan lokacin da yafara sarrafata ba, da asuba suna sallah yace mata ya siyar mata mota…

    ” Rungumeshi tayi tana tsalle Godiya nakeyi mijina A hankali takai masa sumbata bakinsa…

      ” Dariya yayi yace kinga ki daina tsokanata kuma kina hanani…

     ” mek’iwa tayi tana zagaye kujeru yana binta!

     ”  washhh gaskiya ka wahalar dani…cak ya dauketa har kan gado ya kunna mata Ac sannan yajata jikinsa yana rada mata wasu kalmomi da suke sakata dariya…

    ” Yana ganin tayi bacci ya huce yayi wanka….Yana ganin tayi bacci ya huce yayi wanka Bayan ya shirya bai tsaya ko’ina ba sai office dinsa, murmushi yake ta famanyi shi kadai cikin zuciyarsa yana ta fadin indai Allah yabaka mace ta gare to sai godiya, bayaji aikin ransa zai ‘iya rabuwa da kande.. +

     Mukhtar Ne yaturo kofar office din fuskarshi cike da fara’a ya zauna yace maza ashe kazo?

    ” Eh! Na karaso saboda kayan nan Na Alhaji auwalu kaga Har na kasafta su zamu samu ribar million2…

     ” Amma fa mun wadi sosai..

     ” Bamu wadi ba domin akwai kayan da zasuzo Nan gaba kuma munada riba sosai da sosai…

    ” Toh Allah ya samana albarka! Wato arayuwa indai zakayi hakuri kayi imani da Allah to sai warware maka matsalar ka! Tabbas muneebah shidaniya ce sosai ka dubi yadda ta kullah makirci kala kala..

    ” wallahi kam mukhtar in banda muna addu’a da shikenan, tace riba akan mu Mutum ai abun tsorone shiyasa kullum muke Addu’a Allah ya saukaka mana duk wata kaddara dazata samemu…

     ” Wallahi hakane bari Na tafi zuwa ga kasuwa zan hada kan kudin nan…

    ” Toh sai munyi waya Nema gida zanje yanzu…

    ●●●●●

  Hamza ke rike da baby boy sai wasa yakeyi masa firdausi ce taje dama itace…

     ” goggo ce tace farida tashi ruwan ya hadu…

    ” hamza ne ya riketa ta karasa toilet din sannan yaje ya dakko musu kaya…

     ” hahaha yaya hamza ka kasa tafiya office fa…

   ” firdausi ko naje bazan iya zama ba tunanin maman boy da boy zan tayi…

     ” Lallai soyayya! Su ummi sun tawo ko?

      ” Eh sun tawo i think yanzu zakigansu…

     ” Allah ya kawosu lafiya bari Na dura muku abincin…

  ●●●●●●

     Mumy ce tace Dady yanaga kayan jajirai kala biyu?

     ” Eh kinsan kande ta kusa haihuwa itama  kuma wannan kayan sautu nabayar shiyasa…

     ” Mumy ce tace ohh hakane fa Ne namanta ma…

     ” Mama farida tana jinsu tace dady yau dai zamuje ko tunda sun koma gida…

     ” eh toh kuje yau din inyaso bazaku kara zuwa ba sai ran suna…

    ” ita dai mumy batace komai…

     ●●●●

         Bulalar da aka zuba mata ita yasaka ta firgecewa da mikewa wayooo wayooo…

    ” madam ce tace au dama kinada hutu cikin gidan yari? ..

      ” Please ki rangwanta mini ki dubi yadda kafata kurje yafito har wari takeyi…

    ” Kara zan bada mata bulalar tayi sannan tayi saurin shigewa toilet din tafara kwashe kashin dake kasa Tun tana Amai har ta daina…

    ” Su kansu shaidanun gidan birsin din tausayin muneebah sukeyi duk kyanta yanzu ko kallonta kayi sai ka kusa amai wasu kuraje da baki gashinta duk ya dankare…

    ” wata matace tasamu muneebah tace ke kuwa baiwar Allah mekika aikata rayuwar ki tayi haka?

     ” Muneebah ce ta fashi da kuka ki dubi yadda kyau na da matsayina suka dushashi To wallahi indai nafirta daga gidan yarin nan sai na kashe su….

      ” Lallai kin kuyamun darasi dumin da zuciyata bata russuna ba Amma yadda naga kin koma nasan dan adam ba abakin komai yake ba kudin naki babu kyan babu takama, To baiwar Allah kisane Wutar Allah da ta ke lahira, Mai radadi ce da azaba,Kar ka manta kana da zama mai tsayi yana jiran ka a kabari, kuma baka da abokin zama a wannan lokacin face ayyukan da ka gabatar a rayuwarka kafin mutuwa…..Indai burinki ki cutar da wane to kuwa kina cikin wahala bakara ma domin hakk’in dan Adam yafi karfin wasa…

    ” Kafin tayi magana madam ta watso mata ruwan fitsare da gudu ta dauke fatanya tayi ban dake…

    ” Kuka matar tafashi dashi tare dashi tare da Allah ya saukaka musu dan tsarkin mulkin sa yasa suyi mai kyau aduniya…

●●●●●

   To abbas yaushe gobe za’akai kudin auren naka za’asaka wata 5 kaga sai ahada dana su sumayya da Maryam…

   ” Tohm dady Nagode zan shiga mu gaisa da mama farida..

   ” Madallah..ohh ne farida Abbas ka gujemu daga karatu shikenan.. +

    ” ke dai bari kinsan harkar karatun sai addua shine natsaya nasamu aiki a abujan…

    ” Ashe kuma yau za’akai kudi toh Allah yasa abokiyar arzukin kace yakuma kaudar muku da fitina kuma ka dage da Addu’a domin yanzu kana ganin baka cuce wane ba wane yana can yana kokarin samun hanyar dazai cuceka….

   ” Hakane wallahi Allah yayi mana jagora ne natafi…

    ” Da ka tsaya nakarasa Abincin mana!

    ” Ai zanje gidan farida ne..

  ●●●●●●

       Alhamdulilah! Yau burina ya cika zakiyi aure yusrah gashi Allah ya hadaki da miji nagare dan Asali mai mutunci!

     ” wallahi umma Abbas yanada hankali sosai da sosai..

     ” Nagane Ai yanzu sai mufara shirye shiryen kayan dakin ki duk da baffa yace shi zaiyi..
  
     ” Rungume ta yusrah tayi tace ummata Allah ya barmu tare…

    ●●●●●

Tunda kande ta tashi ta gyara gida sannan ta hau dafa Abinci sai data dafa kala hudu friedrice, pepper chicken da kunu da hadin salad duk ta zuba acikin flask sannan ta zuba musu nasu dana baba mai gadi, bayan tayi sallar la’asar ta zauna tanata Azkar sai data gama tass sannan ta dakko kur’ani tana karanta suratul daha tana gamawa tayi wanka tasaka wane blue less din da matafi white ta fito palour kenan taje sallamar haruna..

   ” Tsayawa yayi yana kallonta ga cikin nan yafito sosai tayi masifaffan kyau cikin murya mai kama da dishashewa yace wannan kwalliyar fa…

    ” Murmushi tayi ta zauna akusa dashi tace takace mijina…

    ” serious?

        ” kumatunsa ta taba tace yes!

        ” Amma kinyi kyau sweety i can’t explain irin son da nakeyi miki….  
   
    ” murmushi tayi tana kokarin mik’ewa…

  ” ki dingayi ahankali kada ki illatar mun da baby na!

     ” Ne to ai yana wahalar dani kaje Nauyi kuwa?

     ” To kozaki dawo dashi cikina? ” murmushi tayi tace kafiya zolaya…

    ” Shiru yayi Nadan mintuna….

      ” Lafiya yaya kayi shiru Ne banson ganin ka cikin wane yanayi ahankali ta kwanta akirjensa…

    ” My esha gane nakeyi kamar bakyasona!..

      ” Azabure tatashi bana sonka fa kace??

    ” Har yanzu bakya nunamin soyayya gani nakeyi kamar nikadai nake kidana da rawata….

     ” Hannun sa ta dauka ta dora akan kirjenta cikin dashsheyar murya tace da’ace kana ganin Abunda kicikin nan da baka yanke mun hukunci ba! A hankali ta rungumeshi tace son danakeyi maka bazai misaltu ba bana tunanin iya zama da kowanne d’a Namiji Aduniya in bakaiba…

    ” ba karamin jindadin maganganun ta yayi ba murmushi yayi yace oya kiss me…

     ” Sai da ta danyi diriss can kuma zuciyarta tace wannan ne zai nuna masa ina sonsa…

     ” A hankali tayi kiss din lips dinsa..

      ” cike da zolaya yace ba kiss ba kissing dina zakiyi…Shagwabe masa tafarayi ne wallahi yaya Allah kuwa bazan… +

      ” wane mugun feeling yaje yadda take magana! To bari na hakura daman….

       ” Kafin ya karasa tasaka bakinta Anasa sai da ta tabbatar ya fita hayyacinsa sannan ta sakeshi, Da sauri ta mik’e tayi dak’inta….

     ” Kamar ya bita sai kuma yafasa ya huce dak’insa….

   ” Tana shigowa cikin dakinta abayan kofarta ta jingina tana mai da numfashi Lallai tana kaunar haruna she can’t live without him…

   ” wayar hannun tace ta fara ringing tana dauka yace kawomin tea…

     ” yana zaune ya kunna fanka yana murmushi ta mika masa har zata tashi yace to ina zakije?

     ” Kasan fa…

           ” kafin takarasa yafara sarrafata duk yafita hayyacinsa sai kusan 5:30 ya rabu da’ita tayi wanka ta shirya cikin atamphar ta batik…

     ” ina zakine?

          ” Gidan farida yaya tun safe ya kamata ace naje…

     ” okay dakko key din motarki dakkowa sukayi yace yau ke zaki tuk’amu…

     ” Zadai kaje ko yaya?

            ” A’a zan sauka acan akwai abubuwan da zanyi if nagama zanyi miki waya saiki biyo….

      ” wallahi ne kunya nakeji aci ne nake driving dink’a..

       ” Wannan shine kauna my esha!..

  ●●●●●●

Tana isa gidan tasa masu aiki suka shiga da kayan flask din ita kuma ta riko manyan ledoji guda biyu tanayin sallama taga mumy, anty harda ummi ga goggo, dasu sumayya da maryam….

    ” ina yinin ku ya mai jego Allah yaraya mana baby boy yasa mai Albarka ne…

     ” Ameen suka ce farida tace Allah kande bakida da kirki sai yanzu zakizo tun safe nake jiranki…

    ” kusa da’ita ta dawo tace Am sorry sister kinsan halin yaya wallahi bai dawo ba sai 4…

     ” Ummi ce taketa kallonta yadda tayi kyau ga cikin yafito tace kande kice kema kin kusa sauka?

    ” murmushi tayi sai mumy ce tace ko yau ko gobe…

     ” mamafarida tace toh Allah yaraba lafiya!…

     ” Amare ya abujan?

       ” bakiga yadda kikayi kyau ba kande menene sirrin….

    ” cikin zolaya tace banda zage bari na leka gurin goggo, mama farida ma binta tayi sallama tayi ta zauna kusa da’ita…

    ” in ba nema ke zaki zauna min ba!

     ” kinji ja’irar ‘ya kin tabajin inda uwa ta zaunawa ‘ya…

    ” Dariya sukasa ita da Anty…

    ” Ya maigidan naki?

            ” yana nan lafiya! 
” amma dai yakamata ki tawo tun dazu kande…

    ” goggo wallahi ya haruna bayason na dinga fita yanzu ma bakiga da yadda ya barni ba!…

      ” anty tace ai da gaskiyar sa menene amfanin yawan fitar azo ana cewa kace kokuma kayi wane Abun kibi mijinki da Abunda yakeso….

     ” tohm my mama farida! Amma goggo please kice nayi wankan jego a kauye…

    ” Goggo ce tace dama ki daina wannan zancen domin iyah habu tayi masa yace shi bayason matarsa taje ko’ina….

    ” Bata rai tayi tace amma kuma ku nada iko ai dani! ….

    ” Anty ce tace Amma dai Ai yafemu iko da ke dan haka kima bar zancen, Shi yakawo ki yanzu?

     ” A’a ninazo da kaina ta bude jakarta tace ga mukullin mota ta ya siyamin….

    ” cikin murna mama farida tafara tubuli…

     ” Mashaa Allah, Allah yakara arzuki ai da kin fada tuntuni da munyi masa godiya….” Duk’ansu suka fita ganin motar tayi kyau sosai gata ash…

     ” Sai da kande ta danga canjin fuska atattare dasu…

    ” mumy tace lallai haruna Arzukin gaba yakeyi motar 10million ai kuwa yayi kokari..

     ” sumayya tace matar ya haruna zokije suka shiga wane Dak’i firdausi ke faman bacci sumayya tana shiga tace toh uwar bacci sai ki  tashi magariba ta kusa…

     ” please kande i need ur help gurin bani tip na zaman aure…

    ” Ga kakanin ki da iyaye ai sai sunfi baki…

    ” Ke fa kinfiya zolaya wallahi..

Ita rayuwar aure kisa ka hakuri acikin ta! Ki kyautatawa mijinki ki kuma zauna da abokiyar zamanki saboda Allah kada kisa azuciyar ki zaki cutar da’ita kisa aranki zama zakuyi na Ammana wallahi bazaki kasance kina tsaida sallah kina sadaka kina kyautatawa bayin Allah kina bin mijinki kina addu’a kina karatun Alkur’ani face Allah ya kareki daga dukkan mai sharri.. 

   ” hakane kuwa!

   ” idan Kuma Kin dauka Boka ko Mugayen Malamai Sune Masu Share Miki Kukanki Ananne Kikayi Asara Kan Asara….

Dafarko Kinyi Asarar Imaninki Dukka, Kin Zubda Qimarki a Idon Al’umma Kinyi Asarar Dukiyar ki ,Kuna Abun Dakike Nema Bazaki samu ba Imma Kisamu Na Lokacine Qalilan Sannan a karshen Rayuwar ki Sai Kin
Kunyata Sai Kowa Yagane Ke Me Zuwa Gun bokace Sai kin wulakanta. ….

  Kiyi Bin cike a Unguwarku Kiga Yaya Qarshen Mata Masu Zuwa Gidan Bokaye yake…..???

  Zakiga Sunyi Mummunan cikawa sannan kuma Ki mutu Kisami Allah Kina Kafura ta asali Kinyi Asarar Ibadarki Ta Dukkanin Rayuwarki Abanza Akan Rudin Zuciyarki Kawi dan mallake Miji Kawai……

   ” wallahi abunda kika fada gaskiya ne Allah ya hanimu ya gyara mana zuciya…

    ” Ameen bari naje nayi sallah, tunda sukayi isha’i suketa hira sai karfe 9 sannan ta koma gida…

   ●●●●●

   Yau wata biyar kenan muneebah rayuwa ta canja mata kafarta ta rube an kaita asubuti sun yanke mata duka biyun tana zaune tanata kuka wata nurse ta shigo dak’in baiwar Allah kanakin ki sun cika zaki iya tafiya muna wanda zamu kwantar a asubitin…

     ” To ina zani bani da kafa fa bani da kowa wallahi natsane kaina…

      ” Ga wani keken gurgaye can wane bawan Allah yabaki kuma kije kinemi maganin domin kinada brain cancer…

    ” wayyo nashiga uku tafiya takeyi acikin keken sai ta samu wata ‘yar bukka tana tsaya taga mai abinci please ki bane Abincin Nan Nace…

    ” kunga yar iskar mataa kije kiyi bara kisamo kudi sai kisiya…

    ” Ne nafi karfin bara sai dai ke wallahi…

     ” hahaha toh Ai duniyar batayi miki zafi ba shiyasa in duniyar ta gujeki da kanki zakije kiyi barar ki samo….

     ” Kuka tafashi dashi tace sai narama haruna sai na rama kande…

    ●●●●●●

      Kande dake faman salati sai nishi takeyi tana karatun Alkur’ani bayan ta gama tana kokarin shiga kitchen Sai ga haruna…

    ” me zakije kiyi akitchen?

     ” abinci zan dora maka ya mijina kada ka dawo bandafa maka ba sai kuma ta cije baki…

     ” Daina kuka my esha riketa yayi ya kaita kan kujera Amma fada takeyi kace Abinci kace Abinci???

      ” wane tausayin ta da sabon kaunarta yaje ya lullubesa, Allah ya sauke ki lafiya bari na kawomiki yogurt….

     ” yana mikomata ta cillar da yogurt din mijina ko bayan raina ka kyautatawa mara ka kyautata masa…

     ” Ki daina fadin haka DanAllah bazaki tafi ki barni ba…

   ” mutuwa dole ce! Kada ka manta da hadisin nan! An karbo daga Sahl bn Sa’ad Allah ya qara yarda a gareshi daga Manzon Allah SAW yace:
*Ni da wanda yake daukan nauyin maraya acikin aljannah kamar haka*
Sai ya kwatanta da ‘yan yatsunsa guda biyu manuniya da ta/na tsakiya…Bukhary..

*Wato Maraya shi ne wanda mahaifinsa ya rasu kafin ya balaga, sannan daukar nauyin maraya wajen abinci da abin sha da sutura da ilimi da lafiya da dai sauransu duk suna cikin daukar nauyin maraya, kuma abune mai daraja ta yadda bãwa zai maqwabci Manzon Allah SAW cikin aljannah*

    ” key din motarsa ya dakko riketa yayi sai asubuti idanuwansa sai zubda hawaye yakeyi suna isa akayi dak’in haihuwa da’ita shikuma ya tawo daukar kayan jarirai ya dakko kudi… +

      ” A hanya ya tuna da maganar kande da take cewa  Tabbas zama da mutane abu ne mai matukar wahala koda kuwa kana nufin su da alheri sai ka samu wasu suna nufin ka da sharri, Amma idan ka yi hakuri ka mayar da al’amuranka ga Allah sai wata rana ka huta a Aljanna….ya kara tuna wata kalmar datace Allah yabaka arzuki mijina kayi amfani dashi ta hanya mai kyau kada kazama wanda Alumma zasuyi Allah ya wadaran arzukin ka, kabada zakkah kayi sadaka ka taimakawa marayu, Dan Allah kada ka hulakanta takalawa, ka kyautatawa miskinai ka ziyarci asubuti kaga halin da marasa lafiya suke ciki ka taimaka masu da Abunda Allah ya hore maka kakuma godewa Allah abisa lafiyar da yabaka domin duk cutarka akwai wanda yafika…Yayen da ya toshe mata baki tacere hannunsa tace ka ziyarci makabarta domin hakan zaisa ka tuna da mutuwa kada ka shagalta da duniya domin mutuwa dole ce azaba ma haka! Ka sasanta tsakanin mutane biyu kayiwa yan uwa musulmai addu’a ta gare ka fadi Alheri, ya mijina kadinga taba azumin nafula kana yawaita karatun Al’kurani duk da nasan kanayi ka kara dagewa….

    Bai san lokacin da hawaye ya wanke masa fuskar sa jikinsa Amuce ya karasa asubutin yana shiga zuciyarsa tana bugawa Addu’a yake tayi…

     ” Wata nurse ce tafito tana barka congrat matarka ta haihu twins mace da namiji…

     ” Alhamdulilahi Ala kulli hal♡ bai san lokacin da yayi sujjadar shukru ba yayi hanyan dak’in akace shirya su akeyi ya dan dakata…

     ” wayarsa ya dakko yanata kiran yan uwa murna suke kafin kace me asubuti ya cika da family suna zaune aka kawo macen sannan aka kawo namijin…

     ” Daukarsu yayi yayi musu kiran sallah ya basu zamzam da zuma…

     ” firsaudi tana dauka ta hau yi musu addu’a…

     ” Hankalin sa kuma yakoma kan kande can kuma ya tuna da maganar ta lokacin da tace yaya haruna idan Allah yayi maka wata ni’imar to kayita godiya agareshi hakan zaisa yakara maka wata…

     ” fitowa tayi sanyi da doguran rigar atampha sai sannu da barka likitocin suke mata su ummi suna zuzuta kyan ‘yayan, mumy tace ai ne za’abawa…

   ” kande dai jinsu takeyi kawai haruna ya hado mata tea tasha sannan ya bata magungunan…

    ” Kallonsa kawai takeyi yadda yake ta rawar jiki akanta! A hankali yace Allah yayi miki albarka kingama yimin komai matatah ya rike hannunta ina kaunar ki……..

     ” murmushi tayi itama cike da jindadi azkar tafarayi sannan ta dan kwanta!….

    ” farida ce tace oh mum twins yauma sai anyi azkar din…

     ” murmushi tayi tana kwance tace ako da yaushe mu kasance masu ambaton Allah!…

     ” Dady yace Allah yayi miki Albarka ya dauke namijin……Dady yace Allah yayi miki Albarka ya dauke namijin yayi masa Addu’a Sannan ya dauki macen ma yayi mata, Wai yaran nan dawa suke kama? +

   ” mumy ce tace da Abi suke kama kai irin idonka ne dasu..

     ” Akasaka dariya! Firdausi tace dady ko abar maka sune?

      ” mumy ce tace Ne nadau namijin ita antynku sai ta dau macen…

    ” Aikam har kun kasafta..

       ” haruna kuwa yakasa magana sai murmushi yakeyi yana kallonsu…

       ” kande data dan kishin gida tana jinsu ga bacci a idonta ta kasa, mikewa tayi taje toilet ta chanja pad ta dawo…

     ” mumy tace sannu mejigo har kuwa kin wada….

     ” murmushi tayi tana kallon mijinta da babu wayanda yake kallah sai ‘ya’yan nasu…

     ” Doctor ne ya shigo nan yace su danyi waje ta dan huta zai dubata ne….

      ” haruna ne ya karbi twins din ya zauna kusa da’ita..

     ” likitane yace mum twins ina problem?

      ” No Am well!

          ” To Allah yaraya by 4 zamu sallame ki, kibawa twins din abinci…

      ” Gyara zamanta tayi haruna ne yafara saka mata macen akan cinyarta sannan yasa hannunsa yana kokarin fito da nonon hannun sa ta riki….

     ” yaya menene haka? Please kabari mana! Azuciyar ta kuwa tasan halin mijinta inyaga dukiyar fulanin ta yanzu zai rikice….

      ” jikinsa yaje wane yar Amma dai kinsan banaso ki wahala ko?

     ” murmushi tayi cikin kissa tace ina sonka mijina!…

      ” To bari naje nayi sallah nadawo…

       ” Anty ce ta shigo kinga yadda kukayi kyau ke da ‘ya’yanki?…

      ” ke Anty Allah nasha wahala dan nayi tunanin mutuwa zanyi…

     ” Anty ce tayi murmushi tace toh ne ina nasanta?

     ” Nayi miki Addu’a sosai da sosai Allah kema zai baki…

     ” wallahi nasan zakiyi min kande, ga twins dinki mashaa Allah kamar ‘yayan larabawa….

     ” Ai da yaya suke kama anty kawai dai baku gani bani….

    ” hakane kuma wazai zauna miki toh?

      ” Nefa ko naje kauye kokuma Na biki gida, Allah nafiso naje kauye….

     ” Anty dai shiru tayi domin sunyi zancen da haruna yace babu inda matarsa zataje….

    ” Haruna ne yayi sallama ya shigo yace yanzu zasu sallame mu sai gida…

    ” Nan da nan idon kande ya ciko da kwallah sai kuka!..

    ” My menene ko bakyajin dadi ne please ki gayamin, gaba dayansa ya rikice hannunsa yasa yana goge hawayen…

     ” Abty ce tayi dariya a zuciyarta lallai kande ansan kissa…

   ” Nifa kauye zaka kaine sai nayi Arba’in…

     ” kirjensa yaje ya wane buga! Dan Allah kiyi zamanki agida Allah banason matata tayi nisa dani please….

      ” Allah ne bazan yarda ba gwara naji gurin iya habu please yaya Dan Allah….

        ” Amma kinsan banaso ko Amma in zai kawo farin ciki gareki tohm zan kaiki…

     ” yauwa yayana ta kwanto ajikinsa namijin ya dauka yana kallonsa can ba sai hawaye ba sauri yayi ya goge dan kar sugane…

   ” A hankali kande tace yaya? ” Yana dagowa taga idonsa yayi jajir lafiya? bakomai bacci nakeji… +

     ” wane iri taje ajikin ta tace Allah ba bacci kakeji ba wane Abun ne Aranka…

     ” Mikewa yayi yana kokarin fita kande tace Anty to muje tare mana?

     ” Ina Ai dady bazai yarda nayi nisa dashi ba wallahi…

    ” To basai ki lallabeshi ba…

      ” Na kuma ai bazan iya tafiya nabar mijina ba gwara na zauna na faranta masa…

    ” Haruna ne ya jiyo ya kalle kande sannan ya fita…

    ” ke dai doluwa ce mijinki bayaso sai ki hakura kada kije kisaka shi awane halin kuma kullum aci yana zirya a kauye haba kande ina tunanin naki?

    ” Toh anty nafasa zan bashi hakuri…

      ” yauwa namiji ko baya tarairayar ki ta rarrayar sa akeyi ballanta kuma yanayi…

      ” Shigowa yayi ya dauke jakarta da kayan shayi ko kallonta baiyi ba yafita….

     ” Tashi muje ki bashi hakuri….

      ” mayafin ta tasaka Anty ta dau macen suka fito su dady sunata zolayarta….

      ” motarsu suka shiga anty ta tsaya kafin su sasanta…

       ” wasa kande ta ke tayiwa baby boy din abun sha’awa a hankali ta sumbace shi…

      ” wane dadi haruna yaje Amma sai ya tuna  nisa zasuyi dashi…

     ” yaya yanaje kayi shiru?

    ” A hankali yace banason rabuwa dake esha…

  ” Kayi hakuri mijina babu inda zanje so ka kwantar da hankalin ka ina tare dakai….
    
    ” Murmushi yayi yace da gaske?

     ” kiss yayi mata yace yauwa har naji dadi…

     ” Daga nan suka rankaya sai gidan kande…

●●●●●

    Ke gurguwa karki kara zama a inuwar damuke zaune in bahaka ba kasheki zamuyi mu hutu….

    ” muneebah ce ta fashi da kuka tace anya kuwa kunada imani bakuga a halin danake ciki ba??

    ” Daya daga cikinsu ne ya wanka mata mari kaga gurguwar banza in bamu yanka ki ba…..

     ” Hakan dataje yasa tayi saurin barin gurin cikin sauri da keken guragunta ta buge wata mota mai motan ne yafito….

     ” ke wacce irin jaka ce dabba banza jahila zaki bugar min mota…

     ” kai dai ba haifafe baniba baka tausayi na…

     ” Afusace yazo ya hankada ta ta wadi sannan yace wai ke yar iska to ga karshin imani nan kinga sai ki rama banza kawai…..

     ” Allah ya’isa azzalumi zaka hadu da daidai kai…

       ” zalunci wayasan abunda kikaye ke???

      ” yana tafiya ta dinga kiran mutane domin su durata kan keken Amma kowa yazo sai yace Allah ya kiyaye ya dauketa wata ma banza sukeyi mata!. …

    ” cikin kuka tace lallai ma mutanen nan inba kara nakai kande da haruna ba bazan taba fanshewa ba….

   ●●●●●

        Kinyi kyau yusrah ya kur’anin kina dai ta biyawa ko?

     ” Eh Abbas dazuma ummata ta karamin, kuma tace nagaida ka!

     ” Ina Amsawa, haka nakeso kizama cikin nutsuwa hankali da kuma tsoron Allah wallahi yanzu har kyau kika kara…

    ” Babu Abunda zance sai dai godiya da Allah da kuma neman yafiya domin Allah yaso ne da rahama daya hadani da miji nagare mai kauna ta mai kuma addini…

    ” Murmushi Abbas yayi yace yanzu mekike bukata na biki???

     ” Ne fa ko dinner baza’ayi ba kamu da yini kawai nake bukata….

    ” Toh mashaa Allah sai ki turomin da text din Abunda kike bukata…

     ” Tohm, yauwa kande ta haihu kuwa?

     ” lah namanta ban gayamiki ba eh ta haihu…

    ” cikin fara’a tace me ta haifa?? Please

      ”  twins namiji da mace..wow Allahu Akbar Amma gaskiya naji dadi when zaka kaine nayi mata barka? +

      ” sai dai zuwa gobe in Allah ya kaimu…

     ” yau my abbas bari na shiga na dura girke..

     ” okay bye..

   ●●●●

   Tunda suka isa cikin gidan aketa hira Sumayya ce keta faman fadin gaskiya ummi ki dauke baby girl mutafi da’ita Abuja…

    ” cikin zolaya kande tace abi zanbawa baku ba…

     ” Toh ai duk daya mukeyi abi ai bazai kula da’ita ba kamar ne…

     ” Anty ce tayi dariya tace Ai ne na riga ku sai kuyi hakuri anriga An bani…

   ” in baso kukeyi yaya ya biku gidanku ba kudaina kasa masa ‘ya’ya cewar firdausi…

     ” kande ce tace kin sanar da mamie anty?

    ” eh! Nagaya musu har nafeesa ma..

     ” yauwa bari nayi wanka firdausi dura muka girke mana!…

     ” kinga ne mijina jirana yakeyi tafiyata zanyi…

    ” mumy tace to rasa kunya uwar miji tashi ki dura mata manah!…

     ” aa mumy kyaleta bazan iya bani shiyasa bari ina zuwa…

    ” Tana shiga dak’i ta dau wayarta hello yaya?

    ” Naam sweethart kina lafiya ganinan karasowa…

    ” Dama su mumy ne zasu tafi please inason….

     ” Dan yarasulillahi matata kidaina zancen zaki bisu why kika ki fahimta ta ne kinaso nashiga wane hali ne ya zanyi da kaunarki da ta ‘ya’yana???

   ” Haba mijina farin cikinka da kaunarka shine burina Allah nafasa katawo musu da kaza da yogurt…

    ” wane dadi yaji sannan yace Nama siyo musu…

    ” yauwa yaya Allah yasaka da Alheri mijina…

    ” sumbata yayi mata ta wayar sannan ya kashe…

   ” Tunda tafito taje babu hayaniya bayan ta saka doguwar rigarta ya ‘yan kati tafito taga iya habu azaune sauri tayi ta karaso ta rungumeta ‘yar tsohowa ta aida nayi fushi Allah bazaki tafi ba…

    ” Barka barka dubi kamar baki kika haihu ba sannu ‘yata Allah yakara lafiya yayi musu Albarka…

   ” Ameen iya habu ina kika bar habun?

   ” habu makaranta nabarshi gidan kawonsa…

     ” kande ce ta kara rungumeta Allah naji dadin zuwanki…..

     ” *ke dai tadabance*kiyi hankali kada ki danne yayan naki…

    ” haruna ne ya shigo nan ya gaidata…

    ” ina ka shiga tun dazu kabarsu su kadai har tara dare?

   ” Na kai su mumy ne da ajiye firdausi agida…

      ” Adai dinga kulawa ana kuma adalci…

       ” inshaa Allahu ke kuma tashi kibasu nono su sha…

     ” Tohm ina zuwa iya bari naje na bashi abinci kitchen ta huce ta kaima masa yana zaune, yaya tashi kayi wanka manah…

     ” kin hadamin ruwa?

           ” eh tun dazu please katashi kayimana….

      ” kafin ya fito ta dakko masa jallabiya sannan ta koma dak’in iyah habu sannan ta basu abincin su…

       ” Toh sai ki kwanta ki huta kwantar da ‘ya’yan naki bari ne na sauka kasa..

    ” A’a iya zai ishemu fa kada ki sauka kiyi kwanciyar ki…

     ” Tohm sai ki tofa masu Addua..

    ” haruna ne ya shigo ya zauna kan kujera..

         ” kallonsu kawai yakeyi har kun kwanta?

      ” Eh mun kwanta ko kana bukatar ayi maka wane abunne?

     ” A’a

           ” iya habu ce tace sai ka tashi kaje ka kwanta kabarsu ku huta suma…

     ” mikewa yayi jikinsu babu kwari yafita yaba shiga daki yace anyi ba ayi ba inason naji duminsu amma iya ta hana ai shikenan addu’a yayi ya kwanta!..

    
     Da safe sun shirya zasu tafi asubuti ya rufeta da fada wannan wane irin abune kinsan kece burin rayuwa ta ki dinga nisanta ne da ‘ya’yana?kinsan irin farin cikin danakije I’dan naganki ko naji muryarki? ?? In kin gujeni so ai bai kamata ki nisanta ne da ‘ya’yana ba…..

     ” idon tani ya ciko da kwallah sannan tace kayi hakuri yaya..

     ” banza yayi mata har suka isa asubutin adawowa taga wata mata akan keke tanata bara yaya please tsaya nabata sadaka please…

     ” tsaya yayi sannan yace ke Almajira tawo ki karba…

      ” dagowa tayi tace banda kafa sai kuma tayi diriss haruna shi baima ganeta ba yace oya kai mata ki dawo..

    ” kande ce ta karba ta bata nan muneebah ta hau yimata godiya tana dagowa tace kande??

    ” kadai muneebah ce? ” haruna shi kansa sai da kirjensa ya buga yace innalillahi wainna ilahirraji’una muneebah… +

    ” kuka tafashi dashi tace muneebah takarasa kusa daita….

    ” kada ki karaso ku kuk’a saka ne acikin halin nan Allah ya’isa..

     ” mamaki kande tayi wato har yanzu batayi nadama ba…

   ” haruna ne yace shiga mota mu tafi kema kirasa rasa wacce zaki bawa sadaka sai Wannan…

    ” haba yaya bakaga halin danake take ciki ba??

    ” Sharrin datayi a bulus kike tunanin tayi…

” kamanta hadisin Abi Huraira Allah ya qara yarda a gareshi yace: Manzon Allah SAW yace: (( Duk wanda yayi sadaka da kwatan-kwacin dabino daya wanda ya samoshi ta hanya tsafta-tacciya, kuma da ma babu abin da ke hawa zuwa wajen Allah sai tsaftatacce, to Allah SWT zai karbeshi da damansa, sannan ya raine ta ga ma’abocinta/wanda yayi sadakar, tamkar yadda dayanku yake rainon qaramar dabba har sai – sadakar – ta kai tamkar – babban – dutse, bukhari….

” haruna ne yace me ake nufi da Fuluwwa?

” kande ce tace dabba qarama da ake shãyarwa….

” kuma yaya sadaka na da muhimmanci a addini, sannan Allah SWT baya karbar duk wata sadaka sai wacce take an samota daga arziqi na halal !!! Idan dan Adam ya mutu/ko yazo dab da mutuwa farkon dãnasanin da zaiyi shi ne: Inama a dan qaramin lokaci kadan don in samu inyi SADAKA….

   ” Toh nagode, suna isa ya ajiyesu ya huce office…

   Tana shiga taga ‘yan barka…

●●●●

     Kai Alhaji haruna meke damunki Ne nadadi  a tsaye Amma bakasan inayi ba??

     ” A’a Aminina ai ban kula ba ai inada cikin matsala!

      ” wacce kuma matsala? ” kai ingaya maka wane mugun feeling din matata nakeyi gashi babu hali…

     ” Ai saboda irin wannan nace ka kara aure!…

     ” ideas dinka baiyi ba!

      ” to kadinga azumi!…” yauwa yanzu naji magana zanyu inshaa- Allahu…

  ●●●●
      ” Ya akayi haruna bai fito ba har yanzu?

     ” Nima haka nagani har goma tayi bari naje na duba shi!…

     ” Toh dauke Baby biy din tunda kin goya girl din…

    ” Tana shiga ta ganshi a kwance hakan yasa tayi diriss domin tasan abunda ke damunsa Amma bari tayi kokari…

     ” Baku kwanta ba?

           ” kawo maka su nayi sukwana agurinka…

      ” Toh kema sai kizo ki kwanta akusa dasu..

       ” ga gadonsu nan bari na shimfide su…

     ” Tohm yace sannan yaje kusa dasi ya sumbace su ita kuma kande tayi wanka ta canja pad Nan ta kwanta ta rungumeshi…..Please ki kyaleni kada ki haukatane bayan… +

     ” kafin yakarasa tafara kissing dinsa sai data gigitashi A hankali tace ai narage maka wane abun…

     ” rungumeta yayi yace kwarai! nan ya firgece ahaka ta dinga kokari duk da babu halin saduwa sai dataga ya samu nutsuwa yadda yadinga wasa da ita hakan ya bata tausayi ahaka, daga karshe kuma sai taje dadi yadda yaketa murmushi yana mata addu’a….

      ” ina sonki kande ina sonki sosai please kada ki rabu dani Ke zaki gyara ne inba haka ba zan samu matsala…

     ” Zanyi iya kokarina mijina…

      ” Iya habu data gaje da zama ta huce taje ta kwanta…Ina sonk’i k’ande ina sonk’i sosai please k’ada k’i rabu dani K’e zak’i gyara ne inba haka ba zan samu matsala… +

     ” Zanyi iya kokarina mijina…

      ” Iya habu data gaje da zama ta huce taje ta kwanta…

Da safe bayan sun karya iya ta sakata agaba sai tayi wanka an hada ruwa ga darbejiya tanata jiranki….

   ” Allah iya yanzu andaina wankan darbejiya ga zafi ga azaba please adaina….

     ” lahhh ha’ilah kinji min mara kunyar ‘ya mu iyayen ku duk shi mukayi shiyasa jikin mu yayi sumul shige kafin na bata miki….

     ” Tunda ta shiga toilet din sai datayi kusan rabin awa sannan ta fito rik’i da towel chair din mirror dinta ta jawo sannan ta zauna tana mammatsa kanta…

    ” Haruna ne yace sai yanzu kika fito?

       ” Lah yaushe ka dawo?

     ” yanzun nan nakasa zama a office din gwara gani gaki…

         ” murmushi tayi mai kawatarwa yayin da take shafa mai tace Nema in banda dole me zaisa na rabu da kai? Yauwa wai wane suna zakasaka wa twins dinnan?

      ” wannan haihuwa dama ne zan saka musu in yaso ke kyasakawa nagaba….

     ” Ah aine ba yanzu ba hu’un…

    ” maccen sunanta zainab shi kuma sunansa Nurah…

    ” Kai Amma sunan yayi dadi Allah yayi musu Albarka yasa al’umma su amfana da shi….

     ” Ameen! Ita zee za’adinga ce mata!…

     ” Ne kuma Noor zan dinga kiransa!…

    ” see you later bari naje office na dawo ya matso kusa da’ita me zan siyo miki a hanya din?

     ” kada idonta tayi tace kwakwar manja nakeso!.

     ” banma santa ba but zan nemo miki ita…

     ” A hankali ta sumbace bakinsa sannan ta fita…

    ” wane murmushi yayi me cike da soyayya da kauna da kedemiwa….

     ” iya habu ke ta faman masifa ja’ira kawai kin tafi wai ke dadi miji kin barsu sai kuka sukeyi suna son nono…

     ” haba iyah kiyi hakuri mana mekomin zainab din har zata zauna a kasa iya tace ohhb Kande *ke ta dabance* to dakko filo ki zauna kada ki zauna akasa…

      ” Turo baki tayi toh saboda me?

        ” mace budewa takeyi idan tana zama a kasa…

    ” Tohm iya ke dura abinci kafin afara zuwa….

     ” ina zan iya ta sheriritar ki tun yaushe har na gama shinkafa….

     ” Dariya kande ta saka tace ai girkun naku ne a gurinku muka koya…

      ” Hahaha Allah miki Albarka kande nagode gashi yau Allah ya nunamin nura da zainab…

    ●●●●●

Farida ke sintiri ita da ‘danta a hannu tana jiran zuwan hamza shigowa yayi….

       Rungumeta tayi bai ankaraba sai kuka tun tun tun dazu nake jiranka Amma kayi banza dani……

      ” dago da idonta yayi yana kallonta cikin ido yace ita kauna ajikin mutum take kinsan ina naje kuwa?

     ” Shiru tayi batace masa k’ala ba….

      ” To daga zariya nake Na amso wane takardu!..

      ” sorry dear bari na zubo maka abinci…

     ●●●●●●
Firdausi ke faman Dariya tana shafa cikinta yau watan cikina biyu…

     ” Aliyu ne ya rungumeta yace kinga karshen me hakuri ko?

    ” Murmushi tayi tace nagane mijina Allah ubangiji ya yafemin…

     ” Ameen yau zakije gidan kande ne?

        ” eh Amma ta chan zakazo ka kaine bikin tunda kaga a kano ameyi kuma harda na yaya Abbas….

      ” Tohm shikenan shirya sai mu tafi ….

      ●●●●●
     
          Mumy ce ta bayanin gurin da za’ayi kamu karfe 4!sumayya ce tace kyanta su firdausi su tawo nan sai ku tafi tare… +

     ” Anty ce tace kinga maryam tashi kije ki dakko dinkunan ku ku gwada kafin ummi ta karaso muku da sauran….

      ” Dady ne yashigo yana gidanku yayi kysu sosai bama ace ke maryam  …..

      ” murmushi sukayi suka sunkuyar da kansu ….

     ” Anty dan kira kande mana please ita tatawo…

     ” ai kudaina saka kande zataje bikin ku dan Allah haruna bazai barta ba….

      ” mumy tace ai gobr ne ma suna ga kayan gararta can…

      ” munsan me zamuyi Allah zamuje mu tawo da’itah…

     ●●●●●●

Tun karfe 2 aka cika agidan masu barka makota mutanen arzuki har su momy dukkansu suna nan anata hira…

     ” sumayya da maryam Kunga ku tafi kwalliyar nan da wuri…

     ” mudai fatan mu zakije…

         ” ummi ce tace banson sha shanci gobe fa zatayi sati daya fa…

    ” Kai ummi me zai hanani zuwa tabbejan iyama fa zataje kuma sai yaya ya riki noor na riki zee…

     ” Tohm shikenan ai tunda haka kikace daman tunda da lafiyarki kuma ya yarda shikenan ai…

      ” Murmushi tayi sannan ta shiga daki wane sabon less dinta ta dakko ta dakkowa twins dinta ma!…

     ” Sallamar ya haruna ce ta katseta sai da kirjenta ya buga, Har kadawo? …

    Eh muna tare da abbas ne Akan zancen biki. ..

     Ina zakije Naga kinfito muku da kaya???

       ” saura anjima fa zaa afara kamun su sumayya ….

    ” kina nufin zuwa zakiyi? Yaushe kika haihu?

       Haba yaya yazakayi kace haka tare da anty fa zamuje wayannan kanina ne kuma yayyena ne why zance bazanje ba gaskiya ne sai naje…..

     ” cikin zafin zuciya yace bazakije ba tunda bakisan ki kula da kanki ba bakisan ki kula da ‘ya’yanki ba baki kuma kisan abunda yakamata ba komai kikeso kice zakiyi daidai ne ko ba daidai bani ba To ban aminci miki fita ba….

     ” me iso kakeso ka hanani sadar da zumunci me isa kakeso ka kuntata min wannan shine kaunar? Haba yaya ko dan zumunta ai naje kadaina biyewa zuciyarka, idan kafita tun safe baka dawowa sai 6 Ne kadai agida ne ban fita ba kai baka fitar dani ba….

  ” gurin kidan zaki kaisu gurin shaidanun lallai sai yau na tabbatar *ke ta dabbance* Na kara gayamiki ban Aminci ba idan kinga banda ikon tsayar dani to sai kije ke daya kibar mun ‘ya’yana….

     ” Yana fita ta rusa wane kuka kusan mintina 20 tana kuka dak’in iya tashiga aguje ta fada kanta tana kuka….

     ” haruna yana kallonta uffan baice ba!..

     ” daina kuka uwata kigayan me akayi miki ki daina wannan kukan fa zai illatar dake…

       ” wai wai bazanje bikin su maryam ba…

    ” iyah habu a zuciyarta tace yanzu innace zanyi mata fada tace bayan dana nagoya can sai tace to kai haruna menene na hanata?

    ” Haba iya habu kande fa ta huce sawun yara sai angaya mata abunda ya kamata?

    ” Tu ai kai zakaje bikin wannan ai san kaine…

    ” iya habu ce ta daketa mijin naki kike gayawa haka? Kai kuma haruna kasan Kande *ta dabbance* sai kana hakuri…..

    ” Cikin tsiwa kande tace ai dama kinfi sonsa akaina..

    ” kullah naje magabar nan abakin ki…

       ” Ne Amarya zan sake Nan da sati biyu gaba daya ma na kaita sabon gida….

     ” Nan da nan sabon kuka ya barkewa kande harda rik’i iya noor da zee ma sai kuka sukeyi Amma bata tasu…

     ” Ita kanta iya habu yadda haruna ya fada sai da ranta ya bace…

    ” Kande dai ta ma fasa ta biki ga matsalar datake ciki…

     ” yinin ranar kowa yatafi biki sai ita kadai tace kukanta ta koshe duk lokacin dataga xee da noor especially idan sukayi fara’ar nan kamar ta babansu….
  
Ita kuwa iya habu kasa cewa tayi komai domin kuwa bataso ta shiga tsakanin miji da mata tazo taje kunya, Mama farida ce ta katse mata tunanin ta yar tsohowa ina uwar dakin naki?

     ” Tana gida sai kuka takeyi…

     ” Daman ai nasan bazai barta ba in banda abun kande ma da ragowar kuruciya a tattare da ita yau kwana 6 da haihuwa kice sai kin fito….

      ” uhm zamanin kenen iyah habu yazo da abubuwa da dama sai dai Allah yayabamu hucewa lafiya….. +

    ●●●●●

Abunda ke kara tayarwa da muneebah hankali bai huce wasu narka narkan kuraje da suke fito mata ajiki ba gashi yanzu bata samun ko sisi in taje bara jira takeyi ta d’an  samu abun kaiwa baka, taja keken guragunta….

      ” ke ke.. sau nawa zangaya miki ki daina zama a kusa damu?

     ” kai fitsararre don’t see me like this! Am a rich woman, pretty beautiful ne watace kaje india ka tambaya….

     ” lallai ma ke gurguwar nan kin haukace dubeki jaki ma yafiki kyan gani kyan sura da komai hahaha goggon beri kenan bari kiga na faskara miki kanki….

     ” sauri tayi tana tuk’a keken ta tana gudu, sai cewa takeyi zaka hadu da daidai kai…

   ●●●●●

Ba’a gama kamu ba sai gurin 7 tukun, kande har ta saki jikinta ma ta daina damuwa yanzu matsalarta kishiyar da haruna ke ambata….

      ” gurin karfe 9 tanayiwa noor wasa iyah ta fito tace aa babana sarkin fara’a wasa akeyi ne?

      ” iyah yagajiyar bikin naku yayi kyau ko?

      ” Ah fadama bata baki ce biki yayi kyau sosai da sosai…

     ” Uhm kinga tufa nafeesa takawo ga taki ko nayanka miki…

     ” aa tukunna fara mikomin zainab din tukunna…

      ” Haruna yana tsaye yana jinsu basusan ya shigo ba ..

     ” kande sai cewa tayi wai iyah me isa yaya bayajin maganarki…

     ” dariya iya habu ta saka tace uwar biyu mekika gane?

    ” agabanki fa yace zai kara aure bakisan wacce zai auro ba?

   ” Ai Allah ne yabada umarnin ayi har mata hudu kuma nasan duk wacce zai auro tagare ce domin ya iya zabe haruna…

   ” Lallai iyah soma kikeyi yakara aure?

     ” To ba dole ba yakawo wacce zata kular masa da yaransa….

     ” yadda kande ta bata fuskarta ya kusa saka haruna dariya…

   ” To ne ne ne ban ma san me na rasa yi masa ba Allah inason mijina iyah bazan iya zama da kishiya ba….

      ” Ai bakyajin maganarsa shiyasa zaiyi auren…

      ” wallahi zanfara daga yau please kice yafasa zan dinga yimasa duk abunda yakeso…

     Assalama yayi sannan yashige dak’insa dariyar mugunta yayi tare dajin sabon shaukin soyayyar matarsa….

   ” kinga gobe suna kishige kije ki kwanta…

     ” Tohm iya bari na kaimasa yaransa na dawo…

    Abincin fa?

         ” Tun dazu Na shiga dashi cikin dak’in…

       ” Tana shiga cikin dak’in ta tarar yasa towel zai shiga toilet zainab tafara ajiyewa sannan ta ajiye noor yanata murmushi kiss ta kaimai tana tayi musu wasa….

     ” wayar haruna ce tafara ringing kirjenta ne ya buga dataga asma’u sallama tayi hello sir an kawo furniture din by tomorrow zamu fara shiryawa…

     ” ita dai kande batace kalaba tafara duba gallery kusan duk hotunan tane dana twins, wane gida ta hango yahadu sai data gama kallah tas sannan tace mashaa Allah…

    ” fitowa yayi yana tsane jikinsa yace wayace ki daukar min wayata?

     ” cikin dariya tace mijina…

     ” Shima dariyar yayi yace ince kun gaisa da asma’u???

    ” wai Dan Allah da gaske kakeyi ta saka kuka Please kayi hakuri idan batamaka rai nakeyi please yayana! Allah banaso naganka tare da wata…

    ” murmushi yayi ya zauna kusa da’ita is that serious kina sona?

     ” haba mijina fadar inasonka ai kullum ne kai ne rayuwata farin cikin ka nakeso, Nasan kaine mahadin rayuwata, you are the blessing from Allah and you are the treasure of my life…

    ” wane lallausan murmushi yasaka mai ciki da murna da kuma sha’awar ya kasance da matarsa ayanzu, Kin yarda duk abunda nace shi zakeyi….Kallonsa tayi ta daga kai… +

     ” oyahhh kiss me..” A hankali tayi kiss dinsa,…

     ” Toh ne ai baiyimin ba wannan…

      ” twins dinta ta kwamtar tayi musu Addu’a sannan ta dawo kusa dashi ta fara kissing dinsa nan da nan hankalinsa yafara kokarin rabuwa dashi, can kuma ta tsaya…

     ” cikin wata murya da’ita kanta sai da tasakata acikin wane yanayi yace kin riga kin konane da soyayyarki *ke ta dabance*…..

       ” haka ta danyi dabarunta domin ta gusar masa da sha’awarsa har kusan 2…
  
     Da safe bayan iyah habu ta dama kunu tayiwa twins wanka itama ta shirya cikin wata dakakken lesi dukkanin jikinsa walwali yakeyi tayi daurenta ta saka turare haruna take kallah tace how do i look?….

   ” ohhh fantastic mum twins kinyi kyau sosai muje dakkon tea dina ki bani….

     ” Tana cikin bashi zainab tasa kuka daukarta tayi tana jijjigata har bacci ya kwasheta….

    ” Allah yayi miki Albarka my wifeyyyy….

     ” Amin mijin Mace daya…

    ” Dariya yasaka oyah ne zan fita?

    ” Toh Allah yakiyaye minkai daga sharrin ‘yan matan zamani yakuma dawo da kai lafiya…

     ” murmushi yayi yace Amin uwargida…

      ” banason uwar gidan nan Amarya dai sannan yafita…

      ” iyah habu tace kaje ja’ira har kun shirya…

      ” Kai iyah habu babu kyau fa sa ‘ido…

      Kafin kace me gida ya cika da mutane ko’ina aciki kayan barka kuwa ba’a magana ko goggo kala 30 tayi musu ummi da dady nasu sunyi dare ita kande tama rasa me zatace in banda murmushi da taketayi abinci snacks kaji yadda kukasan suyi magana, mamie ma sai data kawo kayanta dayawa, suna yayi suna ba’a tafi ba Sai takwas na dare ko wanne lungu da sako sai da suka gyara….

    ” wai mumy anjima zaku tafi dinner ne?

      ” eh anan zamu shirya kema ki shirya ki tafe mana…

     ” yau fa 7 days da haihuwata ko farida datayi tsofa ajego bataje ba ballantana ne…..

     Sai 10 suka watse daga ita sai iyah wanka tayi ta kwanta sanadiyar baccin dake make aciki idanunta….

Karfe 11 haruna ya shigo dukkanin su sunyi bacci keys yasaka a kofofi tukunna yayi wanka ya shiga dak’insa kande yagane ta bararraje tana kokarin danne zainab, yasan in yayi mata magana zatayi masa burus a hankali ya kwanta kusa da’ita ya saka hannunsa a rigarta…

    ” mikewa tayi tace yaya menene haka?

     ” zaki danne xee becareful…

     ” badai kafine sonta ba ko? Tana dariya tagyra musu kwanciyar tashi to kije ki ki zubomin abinci…

    ” Tohm tace sannan ta mik’i ta zubo masa oyah bani abaki…

      ” bataci masa komai ba har tagama ta wanke hannunta tace yaya wannan gidan dana gani awayarka gidan wanene?

     ” gidan dazamu koma ne fa amaryata ne!…

     ” Tayi shiru nadan lokaci sannan tace Allah yasanya alheri gidan yayi kyau ne anan zaku barni kenan?

     ” ai Amarya asabon gida take zaune…

     ” hakane kam bari ne na kwanta…

●●●●●

   Tun ranar lahadi aka kai amare ansha biki kuma ankashe kudi kowanne yana gidansa tare da mijinsa…

   ” Kande ke faman jijjiga zainab haba tun dazu sai kuka kikeyi kin hanani sakat…

     ” iyah habu ce tafito tace Haba uwar dakina? Wannan fadan dakikeyi jinki takeyi ai dama raino sai hakuri…

     ” kuka kande tafashi dashi tun fa dazu awa 3 kenan nabata nonon ma taki sha!…

     ” Ke dai *ta dabance* wallahi menene Na kuka?

     ” kara fashewa tayi da kuka kashe ma sukeyi fa ne Allah nagaji…

     ” kinji ja’ira ki kinsan wahalar dakika bayar?

     ” haruna ne yayi sallama sannan ya karbe xee din ya zauna kusa da noor toh gani nadawo nawa rainon yanzu zai fara…

     ” uwar dakina abunda nakeso kisane wannan kalmar dakika fada babu kyau Allah babu yadda baya iyawa haihuwa ta Allah ce duk dabarar mutum na rashin son haihuwa Sai kiga Allah yabashi shi kansa d’an jarraba ce tun daga haihuwar zuwa girmansu shiyasa , kamar yadda hadisi ya nuna duk wanda Allah ya ba shi ‘ya‘ya mata ya ba su tarbiyya har suka balaga, to za su zama sutura a gare shi daga shiga wuta ranar kiyama, da kuma wacce yayanta suka mutu suma zasu ceceta, maza kuma aljannarsu tana gurin iyayensu mu dinga fatan Allah yarayasu yakuma yimusu albarka saboda haka Adduar uwa mustajaba ce batada hijjabi direct Allah yake karba….. +

  *‘ YA‘YA NI’IMA CE DAGA ALLAH Lalle yana daga cikin ni’imar Allah ga danAdam da Ya ba shi ni’imar ‘ya’ya, duk wanda ya yi aure bai samu xa ba, ba shi cikin kwanciyar hankali*…..

   *Kullun fatarsa Allah ya ba shi haihuwa Mun ga yadda Annabi Zakariyya yake roqon Allah ya ba shi da wanda zai gaje shi duk da cewa Allah ya ba shi Annab ta amma bai tsaya ba saboda neman samun da wanda zai gaje shi…*

  *Wannan ya sanya yake tashi cikin dare yana roqon Allah ya ba shi da wanda zai gaje shi Allah ya amsa addu’arsa ya ba shi yaro mai suna Yahya wanda shi ne na farko mai wannan sunan kuma Annabi Allah ya ba mu labarin Annabi Ayyub bayan ya warke daga rashin lafiyar s a kuma Allah ya ba shi ‘ya‘ya….*

*Annabi Ibrahim sai da ya tsufa sannan Allah ya ba shi da Allah ya ce masa rahama ce da albarka ga gidanka..*

*Manufar aure ita ce domin a hayayyafa yadda manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam zai yi alfari da yawan mu ranar kiyama*

ﻟِﻠَّﻪِ ﻣُﻠْﻚُ ﺍﻟﺴَّﻤَﺎﻭَﺍﺕِ ﻭَﺍﻟْﺄَﺭْﺽِ ﻳَﺨْﻠُﻖُ ﻣَﺎ ﻳَﺸَﺎﺀُ ﻳَﻬَﺐُ ﻟِﻤَﻦْ ﻳَﺸَﺎﺀُ ﺇِﻧَﺎﺛًﺎ ﻭَﻳَﻬَﺐُ ﻟِﻤَﻦْ ﻳَﺸَﺎﺀُ
ﺍﻟﺬُّﻛُﻮﺭَ ﺃَﻭْ ﻳُﺰَﻭِّﺟُﻬُﻢْ ﺫُﻛْﺮَﺍﻧًﺎ ﻭَﺇِﻧَﺎﺛًﺎ ﻭَﻳَﺠْﻌَﻞُ ﻣَﻦْ ﻳَﺸَﺎﺀُ ﻋَﻘِﻴﻤًﺎ ﺇِﻧَّﻪُ ﻋَﻠِﻴﻢٌ ﻗَﺪِﻳﺮٌ 
Mulkin sammai da qassai gaba dayan su na Allah ne, Yana halittar abinda ya so yana ba da kyautar mata ga wanda ya so yana kuma ba da kyautar ‘ya‘ya maza ga wanda ya so, ko ya hada wa mutum maza da mata ga wanda ya so, ko kuma ya bar shi bakarare (mara haihuwa)Lalle shi Allah masani ne kuma mai iko ne….

    Ta yaya kika manta da wannan karatun?

     ” Amma nagode iya Allah Yakara girma please kibare sai jibe sai ki tafi….

      ” Abunda bazaiyihu ba kenan yau satin ku uku gobe zantafi….

     ” yaya please kasa baki kefa bamijine dake bafa…

     ” au abun gori ne to ke ga mijin nake ai zan tafi nabarki dashi…
  ●●●●
    firdausi kuwa tsohon ciki ne da’ita, farida kuwa babynta yayi wayo har yafara tafiya, goggo duk ta auran da ‘yan mazanta saura sadiya kawai itama ankawo kudinta da haneef biki watan gobe….

     ●●●●●●

    Hello kande kina lafiya ya jikokina?

     ” Anty gasunan sunata yimun fita kinga kinga kokarin rarrafawa sukeyi…

    ” Toh mashaa Allah ashe kuma kinyi sabuwar amarya anjima za’akawo miki ga kuma gurin zama…

     ” bata karasa maganarta ba sai kuka ta kashe wayar yau yaya zai dawo daga tafiya tunda tayi Arba’in take son zuwa gida amma ya hanats yau ma kamar kullum kwalliya ta tasha shddarta tayi masa girke zee sai wasa sukeyi ita da noor suna jin sallamar dady dinsu suka fara fara’a suna dariya…

    ” mikewa tayi sannu da zuwa sannan tayi hugging dinsa shima ya sumbace ta, wanka yafarayi sannan yace abinci tace masa ya hanya???

      ” hmm abroad ba dadi fa!

      ” saboda me?

   ” saboda babu ke mana!

     ” murmushi tayi wanda bai kai har zuciyarta ba tace well known…

    ” Yana ganki wane iri?

    ” bakomai kawai banjin dadine shiyasa…

    ” Allah sawake ya dauke zee yana yimata wasa tanata dariya noor ne ya kallesa shima yayi dariya…

     ” Ne bari naje na kwanta ka kula dasu…K’i shirya zamu tafi kauye…

     ” tohm tace sannan tasaka sharaton dinta, shikuma ya shirya twins din basu isa ba sai kussan karfe 3 tana zuwa ta rungume goggo nayi kiwarki mahaifiya….

     “Ahh kamar bake ba dubi yadda kikaye kyau kin bar haruna da dakon yara….

    ” Ai babansu ne, suka sa dariya yana shigowa goggo tadinga wannan gida yaye kyau Allah yakara bude ita dai batasan me ake magana akai ba daga nan ta huce gidan anty fatima sunsha hira har tabata wasu tsumen kala kala….

    ” Sai gurin karfe 8 Na dare tukunna suka dau hanya abu mai kamar mamaki sai taga sun dauki wata hanya ta daban wato sabuwar unguwa ……

     ” Sai satar kallon ta haruna yakeyi ko zata tambayi shi, gate aka bude suna shiga taga wasu narka narka motaci guda uku, ga katoton fili, fitilu kuma sun zagaye ko’ina, zee ta dauka sannan ta fito shi kuma dauke da noor….

    ” Kallonsa tayi cikin mamaki yaya wannan gidan su wanene mukazo da daddare…

    ” Cikin hade rai yace gidan amarya tace…

     ” To me zamuyi mata? Ita yakamata tazo bamu ba! Karfa kamanta ne kafara aurah, to me yakawo tsohuwar motata cikin gidan? ….

     ” zata kara magana ya rike hannun ta suka fara bude wasu kofofi ita kanta sai data girgiza yadda suka hadu wane palour ne anyi masa adon ash sai dakuna 4 a cikin sa kowanne daki da toilet, kanayin gaba wane palour ne shikuma purple ne yace wallpapers ga dak’i biyu sai baranda, kana fita sai wane fili kitchen ne katoto anyi masa orange decoration sai kuma wata matattakala palour ne daya da dak’i biyu sai toilet da swimming pool…

     ” sak’kowa tayi aguje har tana kokarin bigewa…

     ” Haruna ne ya beta ya riko hannun ta menene na kuka?

    ” fashewa takarayi da kuka haba yaya amma kasan wannan rashin adalcine gidanta yafi nawa kyau kuma…kafin takarasa sai wane sabon kukan….

    ” basmala yayi ya ajiye noor, wane rashin Adalci nayi??

      ” au bak’ayi komai ba kenan? to ne kamai dani gida kuje….

     ” wannan shine sabon gidanki nakine, jar motar waje tak’ice, kasannan duk na k’ine ke da ‘ya’yanki nagina miki wannan domin farin cikin ki…

     ” Da gaske baka kara aure ba? Kana nufin daga ne sai kai?

    ” zama yayi yace kwarai kuwa…

      ” Batasan lokacin da tayi tsalle ta rungume shi ba, ina kaunarka ina sonka, kaine farin cikina, kaine ruhina, mijina… I’ve been up and above all I’m grateful to God almighty,He
deserves nothing but praise, praise and continuous praise,I’m more than happy for the blessings, mercies and favours he’s bestowed on me and my family over the years, batasan lokacin data fara kissing dinsa ba tuni suka bar duniya dama shi haruna a matse yake….

     ●●●●●●
Muneebah yau tana zaune tana cin wane k’anzo tanata danna ashar tana tuk’a kekenta wata mota katuwar mota tayi kanta ko salati batayi ba tanata ihu ashe dai akwai ajali yazo washe gari wasu ‘yan iska suka zo suka binne ta…

    ●●●●

      Bayan shekara 5 zee sai homework takeyi, shi kuma noor yana karatun al’kur’ani…

     ” Kande ce ta fito tace noor? Zee? Dad is calling…

    ” we are coming mom….

      ” suna zuwa suka wada kansa dad here we are….

      ” hope kunci abinci, noor ne yace i don’t think mum is finish…

   “oya kuzo muje gida mu dawo, shiryawa sukayi suka tafi…

     ” firdausi kuwa mujeep yayi wayo, yusrah ma ta haife yarta mace duk sun hadu agida anata hira kande haihu yau ko gobe…

   ●●●●
      Da daddare haruna yana kwance kande ta shigo, mijina me ke damunka ne yau naganka kayi wane iri…

     ” bakomai kawai dai ina bukatar na huta…

     ” rike hannunsa tayi tana murzawa baka taba gayamin wannan kalmar ba! Na kasance mata agareka mtsalar ka tawace idan baka sanar dani ba wazaka gayawa?

    ” dady ne yayi order din kaya for 15million kuma an kwace hakan zai iya jawo karayar arzikin sa so shine nace ko sakar masa nawa ne na dau asara…

     ” Duk wanda ya saurareka alokacin da kowa yak’i ka in daga baya yayi maka sharri to kada kamanta da wannan alheri…alheri…kuma kasan ladan taimakon wani….

    ” kana nufin nadau asarar..

     ” Tabbas Allah kaikuma ya mai da maka da Alheri dear….

      ” murmushi yayi yafara sarrafata ta ko ina….

    ●●●●●●●

   A kwana atashi babu wuya ga mai rai yau kande Tana zaune kusa da mijinta noor da zee sunata yiwa new born baby dinta wato fatima wasa….

     ” Dady we love you so much!…

         ” mumy you’re the best….

      Allah yayi muku albarka……..

Sai k’okarin dadara bero nak’eyi ashe ya k’are, ina k’okarin dak’ko wane sai naga nauyin littafin ya k’are, jiyowa nayi naga har bangon littafin ya cik’a ina k’okarin kara jiyowa naga wane sabon littafi ne, Tagumi nayi tare da Hamdala ina Nazari kamar haka:-

     * lallai fitsara da rashin kunya babu inda yake kai mutum sai ga nadama, kuma duk abunda kayi karka manta sai anyi maka fiye da abunda kayi kokuma daidai da yadda kayi…

    * girmama manya sai mace tagare duk wacce akace ta girme ka to ya kamata ka girmamata domin samun Albarka…

    ” Darajta mutum abune mai kyau, arayuwa bakasan mai yimaka rana ba, Duk abunda mutum yayi maka to kada karike shi……

   * sharri mugun abune kuma ya kanbi mai yinshi, komai iya makircinka da sharrin ka karshe kanka zai koma kamar muneebah, dukiyar ka Arzukin ka da kyanka bazaiyi maka komai ba indai ba aikata aiki mai kyau kayi ba…..

* Yadda da kaddara wajibi ne ga dukkan Musulmi, domin kaddarori na Allah akwai Alheri mai yawa a tattare dasu, idan kayi hakuri zaka samesu, Raki da kuka da dukan jiki basu canza hukuncin Allah, Don haka ya kai dan uwa, hakurta da kanka, ka kore damuwa, ka daina raki, ka nemi taimakon Allah akan duk wata musiba tazo maka, kasani Mahakurci shi ne mawadaci…..

*  lahira Ya bayin Allah! Lallai hakuri abu ne mai daci a lokacin da ake yin sa, amma abu ne mai zaki a karshen al’amari…

   Allah Madaukaki Ya ce, “Kuma idan kuka yi hakuri, lallai shi ne
mafi alheri ga masu hakuri, Kuma ka yi hakuri, kuma hakurinka ba zai zama ba face
domin Allah, kuma kada ka yi bakin ciki saboda su, kuma kada ka kasance a cikin
kuncin rai daga abin da suke yi na makirci.” (k:17: 126-127). ….

   Kuma Allah Madaukaki Ya
kara da cewa: “Kuma wadanda suka yi imani, kuma suka aikita ayyukan kwarai, lallai zaMu zaunar da su daga cikin Aljanna a gidajen bene, koramu suna gudana daga
karkashinsu, suna madawwama a cikinsu. To madalla da sa kamakon masu aikin kwarai,Wadanda suka yi hakuri kuma suna dogara ga Ubangijinsu kawai.” (k: 29: 58-59)…

   * ki riqi aure domin jigo ne ga rayuwar mu. Ya ke ‘yar’uwa ki yi haquri da rayuwar da ki ka tsinci kanki a gidan auren ki, ko daci, ko wahala, ko daci, ko
zaqi, sanyi, zafi, ku jure ki yi haquri ki roqi Allah ya yi miki sauyi na alkhairi, ki tallafi mijinki da ‘ya’yanki, idan kina dasu, ki tausaya musu, ki basu tarbiyyar ta gari, ki dora mijinki a hanya ta qwarai idan ya kauce, ya ke ‘yar’uwa ki yi qoqarin kyautata dabi’unki, biyayyarki, haqurinki, sauqin ta tare da Ibada zuwa ga Allah shi ne samun Aljannarki…..

  * I’m just hoping that people understand that Islam is peace and not violence…

  * Stay positive and happy,Work hard and don’t give up hope,Be open to criticism and keep learning,Surround yourself with happy, warm and genuine people….

  * Life is like the ocean. It can be calm or still, and rough or rigid, but in the end, it is always Beautiful. الحمد لله

  * Things won’t alway go the way we want them to. We may need to let things go to build up new ones. It’s painful. But it’s part of His plan!

  * May ALLAH SWT Guide our right, ,may HE protect us from all evils,countinue to shower his mercy blessings on us…..

   ALHAMDULILLAHI ANAN NAKAWO KARSHEN LITTAFINA MAI SUNA  *KANDE*
   (KE TA DABBANCE)


GODIYA TA TABBATA GA ALLAH MADAUKAKIN SARKI TSIRA DA AMINCI SU KARA TABBATA GA MANZON RAHAMA (SAW)

   ABUNDA MU KAYI BA DAIDAI BA ALLAH YA YAFE MANA!

   WANDA MU KAYI DAIDAI ALLAH YABAMU LADA!

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *