KANDALA CHAPTER 9

KANDALA







CHAPTER 9








Tunda suk’a shiga k’irjen k’ande k’e faman bugawa… +

” my humairat ba na hanak’i tunani ba?

” Murmushi tayi tace to Allah ya hanine ni ma…

” Nan mamee ta zabar mata sun tafi zuwa biyan kudin kenan kande tace malam bani sweet din gefanka…

” dago kansa Aliyu yayi cikin mamaki yace kande???

” Tana daga kanta tace ya Aliyu…sai ta sume ………

Mamee ce tace subhanallhi ‘yata ‘yata tana jijjigata…

” abdul ne ya rike wuyan aliyu yana fadin kai wanne irin azzalumi ne kai wane irin mugu ne kana ganin yadda take takawa yanzu gashi ta suma wallahi in ta mutu sai na daure ka….

” Kuyi hakuri karku yanki hukunci batare da sanin ne wanene ba….

   ” mamee ce ta kallishi idonta duk hawaye tace abdul kutowo mukoma gida yiwa doctor waya yazo gida…

    ” Aliyu ne yace Dan Allah hajiya kuyimun alfarma nabiko Dan Allah….

    ” alokacin da ta isa bakin kofa tace zaka iya binmu..

   Suna shiga mota wayarsa ya dauka bugo daya yasamu goggo nan yace ku kwantar da hankalinku naga kande….

   ” mamee da abdul ne sukace kande kuma?

     ” anya kai ba dan yankankai bani ba cewar abdul….

     ” Aliyu baice musu kala ba…

    Suna isa gida doctor yana zaune yana jiransu dak’i akayi da kande Nan ya yimata allura sannan yace sai nan da 1hours zata miki dan haka ku jirata akusa domin zata iya tashi a furgeci….

    ” abdul ne cikin gigicewa yace dr kafar tata data wade akanta fa ?

    ” babu Abunda kafarta tayi ga magunguna Nan sai kuje kusiyo mata….

    ” abdul ne ya dau key sau chemist hankalin sa duk ya tashi cikin murya tattausa yace Ya Allah kasa ba rabamu za’ayi da my humairat ba bani tunanin a hakuri na alokacin dabata kusa dani, wata zuciyar tace kasanar da’ita abunda kakeji mana….

    Kauye

  Ke sadiya kirawo iya habu kirawo ta Alhamdulilahi Allah ya amshi addu’ar mu…

    ” kabiru ne yace An gantane? Aina? Yaushe kuma?

     ” Anganta kabiru yanzu Aliyu yayi min waya….

    ” Alhamdulilahi to ki kirawo birni mana kisanar kinsan suna cikin cha kwakiya….

    ” Aliyu yace min a dan dakata amma bari nakara lalubar numbar tasa cikin dakika daya takira Amma sai aka sanar daita cewa arufe take….

    ” to kidan tsagaita musaurari shi zuwa anjima, aa iya anga ‘yar taki…

    ” iya habu tace Alhamdulilahi Allah kulli hal, ku bani ita awaya muje muryarta mana….

   ” Aliyu yace a dan jinkirta…

   ” ashe ma tana garin jigawa! To Allah ya jiyar damu Alkhairi, tazo muje tayaya ta bar gida…

    ” kabiru yace zancen baya ya huce iya habu gwara afuskance gaba …
   ” ai sai angyara baya gaba yake kyau…

   Birni…

Dady ne yake faman sunturi acikin palour firdausi da farida duk sun durkusa agabansa suna kuka, jikinsu duk ya fashe saboda duka..

   ” mama farida ce tafito tace wai mike faruwa Alhaji ya dakesu gashi kai sai gumi kakeyi?

     ” baki suka hada sukace danAllah kayi hakuri baba mun tuba bazamu saki ba….

    ” a fusace ya wanka musu mari au kunsan abunda kukayi ne? Kunsani nace ?  Ku kayamun kafin nakarya ku..

   ” mama farida ce tace adaiyi hakuri Alhaji…

     ” kika kara bani hakuri sai na saba miki…

  ” mumy ce ke daki cikinta duk ya duro ruwa hankalinta duk atashi tasan Alhaji zai iya sak’inta….

    “Cikin murya mai karfi yace ke mumy sakko kizauna…jikinta babu kwari tafito palour sai tsuma takeyi…. +

     ” kunfi kowa sanin halina da talaka da me kudi duk daya na daukesu bana bambanci, bana tozarta mutane,hasalima danuwana shi yakeda zafi, ban iya fada ba komai nawa da sanyi Nakeyi nasha gayamuku kudinga tsoron Allah kudinga tunawa da mutuwarku ko kun manta ku matane tsaf zaku fuskanci dubun abunda kukayi, mari ya kara kai musu sannan yace Na taba cewa ku zalunce wani?….

     ” Kuka suka saka A’a baka taba….

     ” To me isa kuka aika? Zaku gayamin ko saina karya ku???

    ” tsautsayi ne kuma kuma…

    ” kuma me? Ko kun manta lokacin da haruna yake gidannan wane zagi da cin mutuncine bakuyi masa ba, bazan manta watarana da wai ke firdausi kikace masa bakiga asararriyar da zata soshiba, Ko aka gaya muku ita zuciyar mahaukaciya ce dabatason wanda ke ganin darajarta…

” sharrin shedanni…

     ” Tohm shikenan tunda kungani kuskuranku kuje wacce ta sakaku ta dinga biya muku kudin skul wacce ta sakaku ta dinga baku abinci abu daya na yadda kuyi amfani dashi agidan nan wato ruwa shima sadaka nabaku kuje kuma gurinta tazame muku uba ne nacire hannuna akanku.

    ” wayyo dady danAllah kayi hakuri wallahi bazamu kuma ba wallahi bazamu kuma yiba…

     ” mumy ce jikinta yayi sanya sannan tace ku kuka sani ai mugun halinku…

    ” farida tace ai ke kika jawo mana dabaki sakamu ba da haka bata faru ba…

     ” mama farida tace Allah ya sauwake dai ta tashi ta huce dak’in Alhaji….

      ” haruna ke faman sintiri lallai mutum abun tsoro ne, yanzu to ina kanden take wane hali take ciki ma?

     ” dady ke kwance akan gado yana zubda hawaye..

     ” mama farida ce ta shigo cikin doguwar rigar duk ta kama jikinta sallama tayi ahankali ta kwanta tana kallonsa hawayen da tayi kicibus dashi shiyasata kuka sannan ta dau hannunta ta goge masa!…

    ” kallonta yakeyi sai ga wasu sabon hawayen sun sauka..

    ” a hankalin ta rungumesa sannan ta goge masa! Cikin murya mai sanyi tace ya mijina wannan hawaye dakakeyi bakomai bani face sanya kanka cikin damuwa da kuma masoyi yarka, kuka ta fashe dashi Dan Allah kadaina…

     ” kara rungumeta yayi yace to ke menene na kukan?

   ” cikin sanyin murya tace ta yaya bazanyi kuka ba Alhalin samuwar dakikeson saka sanka zata iya taba maka lafiyar ka!..D
    ” ta yaya bazanyi kuka ba bayan nayi sakace an wulakanta marainiyar yarinya mai ladabi…

     ” fuskarsa ta shafa tace kadaina fadin haka domin Allah ne ya rubuta hakan kuma su firdausi basu da laifi face shedan da ya rudesu, ‘ya’yanka ne bai kamata kayi musu wannan tsatsauran hukuncin ba na tabbatar da kande tana nan zatace ta yafe musu…

    ” mahaifiyar suce tasaka su kuma wannan hukuncin shine daidai dasu domin ta haka zan rage wannan dacin na zuciyata….

     ” kallonsa tayi ta saka hannun ta a rigarshi ta shafa kirgen tace na tabbatar zuciya tana yin gyara kamar yadda tana batawa bakayi musu addua ba domin Allah ya shiryesu Amma kayi hakuri ka chanja hukunci….

      ” bude bak’in dayayi ta kai nata bakin Nan hankalinsa ya hushi salo ya canja..

       ” su firdausi ke faman kuka akan yaya zasuyi farida tace bari muje gurin anty ta tayamu bashi hakuri mekiwa sukayi suka hau samanta bata nan Nan suka tabbatar tana dak’in dady suna shiga sukayi sallama sannan suka zauna aka anty Dan Allah ki tayamu bashi hakuri…

     ” kada kudamu Allah shikansa yanason mai neman yafeya yanzu dady yana bandaki yana wanka bari Na dubu ko ya fito sai kukara bashi hakuri…

    ” tana shiga ta tarar dashi ya gama saka kaya cikin murya tattausa tace wai ina zakajeni kaketa faman shiri?

    ” murmushi yayi yace wannan kayan fa sunyi miki kyau!

    ” murmushi tayi tace toh baka bani amsa taba tana rausaya kai…

    ” please kibarne naji meeting din nan karki sa nakasa fita!…

     ” hahaha mijina abin sona ai kayi mantuwa a fitar taka ta dakko turare ta fesa masa gaskiya kayi kyau karfa wata ta kyasa….

      ” hahaha k’ullum kiyita tallina 
k’ina kuma bani shawarwari masu kyau, in ina cikin damuwa sai kiyita bani hakuri kina kwantar min da hankali wallahi mata ni’ima ce, Allah yayi miki Albarka… +

   ” Ameen Abokin rayuwata yauwa su firdausi suna jiranka…

     ” Tohm ya hade fuskarsa…

       ” to kadanyi dariya mana!

Jigawa

    Abdul ne ke faman sannu my humairat babu inda yakeyi miki ciwo ko?

    ” sannu kande cewar Aliyu, kiyi hakuri kinje bansan bakyajin dadi ba da banyi miki magana ba!…

    ” hawaye ne ya wanke fuskarta ta tace ina iya habu? Ina goggo?

     ” Duk suna lafiya lou iya tayi kukan har ta gaji wai ta yaya kika bata?

    ” labari ne me tsawo Amma wayannan mutanen su suka taimakine su suka kula dani, mamee ga yayana…..

    ” Allah sarki ashe kai wanta ne kayi hakuri munyi maja juyayyeyar fassara cewar abdul…

     ” kin bar iyayenmu cikin tunani da takaici yakamata ki tashi mutafi zuwa kauye…

   ” mamee ce tace Aliyu karka rabani da ‘yata karka rabamu wallahi ina sonta DanAllah ka taimaki ne…

     ” Nema bazan bishiba mamee karki damu kinje?

    ” tafiyarki zata haifarmin da damuwa Amma yakamata kije kiga mahaifan ki hakan ne kwanciyar hankalinki!

    ” ki tashi mu tafi k’ande…

    ” Nifa bazan koma birni ba yaya abdul ka kaine saika dawo dani..

    ” aliyu yayi murmushi yace toh kutaso muji din…

    ” mamee ce kuka yasuboce mata ta rike hannun kande tana fadin karki tafi ‘yata karki tafi please….

    ” kande ce ta rungumeta tace banason kukanki mamee zandawo kinga da yaya muka tafi ….

    ” Aliyu ne yayi saurin fita yace goggo gamunan zuwa amma dakyar ta yarda ki kirawo kawu hassan dasu yaya haruna su tawo muna hanya….

    ” Tohm duk zangaya musu…

      ” mamee ce ta rike kande sukayi hanyar fita sannan Abdul yace mamee innaji zan nemi auren humaira!!!

     ” cikin mamaki kande ta zaro idanunta tana maimaita maganar azuciyar ta aure aure aure?

     ” Ina tare da kai abdul ka nemi aurenta ina tare da kai…

          ” kande ce ta dago kanta cike da hawaye ta kalli mamee dakyar suka rabu sannan suka dau hanya…

      Birni

   Bayan dady yagama yimusu wa’azi kuma da sharadin basu ba kudinsa har wata 4 sun amince office ya huce bai dawo gida ba sai gurin karfe biyar….

    ” mama farida tana kitchen firdausi ta shigo tace sannu anty zan tayaki…

       ” Tohm firdausi tuwo ma na dura Nasan halin dady yanzu zai dawo shine na dura masa indomie…

    ” Ai kuwa sallamar sa taje sannan ta fita zuwa tayi masa sannu da zuwa takawo masa Abinci…

     ” suna cikin magana wayarsa tayi kara ya amsa can kuma ya miki anganta aina aina???

     ” Kowa ya fito har hamza da haruna da suka kasance suna gida….

     ” Tohm ganinan gamunan haruna ja motar muje hamza dakko key din…

     ” mama farida dakyar dady ya yarda tabesu ita kuwa mumy duk ta kidemi yanzu ko mu busu firdausi…

    ” farida ce tace sallon kikara jawowa kanki wane laifin?…

    Jigawa

       Abdul ne suketa hira da Aliyu yace Ashe babu nisa kauyen naku?

     ” Aliyu yace wancan layin zamu shiga ga gidan can!…

     ” suna isa abdul tafito ya budewa kofa yace my humairat fito to!…

    ” Ahankali ta fito tana shiga kowa ya miki iya habu ta rungumeta tana kuka itama kukan ta fara…

     ” dady kifaman kiyi hakuri kiyi hakuri uwata laifina ne!…

     ” abdul ne suka gaisa nan ya basu labarin duk yadda akayi…

    ” Hamza da yakejin kamar ya rungumeta ya gudu da’ita dan dadi…

     ” Haruna kuwa shiru yayi yana kallon Abdul tsoronsa Allah kar yace yana sonta….

      ” goggo ce tace kiyi magana mana kande kiyi magana…
    
    ” A hankali ta daga kanta tace dady bakomai ya huce ai…

  ”  Iya habu tace Cewarki ba, babu inda zaki koma ai…

      ” Abdul ta k’allah A hankali yace Tun lok’acin da na bugek’i k’ande naje ina sonki ina kuma so Na aureki Nayi shiru ne domin Ki samu sauk’i sai nasanar dake…..

    ” Hamza ne yace Saboda ke Na samu ciwo saboda ke mukayi  fada da ummina duk saboda soyayyarki kuma yanzu ne lokacin daya kamata ki amince Na aureki… +

     ” Haruna cikin sarkewar murya yace Nayi dak’on soyayya tun kina karama, Na dakatar da dukkan soyayyar wata ‘ya mace saboda ki na k’oyawa zuciya ta hakuri har lokacin da Naso ki cika burinki Na karatu yanzu kin cika shine Daidai lokacin da yakamata ki yarda da maganar Aurena…..

     ” hawaye ne ya wanke mata fuskar ta cikin karamin furuci tace To wa zan zaba????……Haruna cik’in sark’ewar murya yace Nayi dak’on soyayya tun k’ina k’arama, Na dak’atar da duk’kan soyayyar wata ‘ya mace saboda k’i na k’oyawa zuciya ta hakuri har lokacin da Naso ki cika burink’i Na k’aratu yanzu kin cika shine Daidai lok’acin da yak’amata ki yarda da maganar Aurena….. +

     ” hawaye ne ya wanke mata fuskar ta cikin karamin furuci tace To wa zan zaba????……

  Maganganun yaya haruna ne suka fara kokarin rinjayar zuciyar ta, Nan kuma ta tuna da irin kulawar da ya abdul ya nuna mata ko ciki daya suke iya kacin son da zai nuna mata kenan, yaya hamza kuma saboda ne ya chanja halayen sa saboda ne ya shiga ma yuwancin hali To ne yaya zanyi da raina ne ya Allah kataimaki ne….

    ” Dady ne yave iwata karki damu kanki sai wanda kikezo zamu aura miki nidai abunda nakeso daki kiyi hakuri kikoma hanuna Nakasance nizan aurar da ke domin Nasamu lada agurin Allah, Kuma Abunda matanah da ‘yayana sukayi miki kiyi hakuri….

       ” iya habu ce tace lallai hassan bakada kunya ta koma gurinka? Me zatayi maka? Bayan wannan uban tozarcin da kukayi mata? Ko kashita kakeso suyi?

     ” Iya kidinga afuwa DanAllah kinga mun saba da kande bai kamata ace kin raba mu ba, kuma kinga karatun ta takeyi…

     ” goggo ce tace yakamata mudinga sakawa zuciyar mu silama, iya ki barshi su koma mana!…

      ” Mama farida tace ai itama kanden tanason komawa kuma karatu takeyi bazataso akatse mata karatun ba!…

       ” hamza ne yace kubarta ta huta taci abinci kafin lokacin takara samun nutsuwa sai atattauna akan komawar tata kuma abina shima yanason daukarta…..

     ” abdul yace gashi lokacin sallah ya karato ya kamata mutashi mutafi zuwa massalaci…

     ” Dady ne ya miki dukansu suka fita…

    ” iyace ta rigo habar kande to ke menene Na kuka? Ke fa kikece min komai hakuri akeyi dashi ballantana rayuwar duniyar da zata kare….

     ” ita dai kande in banda kuka babu abunda takeyi daga karshe ta miki ta huce bandaki tana fitowa tayi Alwala Dak’in goggo ta shiga ta tada ikama sannan tafara sallah bayan ta idar tafara addu’a idanu wanta cike da kuka, maganar mamee ce ta fado mata inda take cewa Duk abunda k’e damunk’i  ki k’asance me rik’e sarrin k’i domin babu Wanda zai yayi mik i Sai mahaliccin k’i ki k’asance k’ina ‘Kai kuka gareshi k’i k’uma dinga sadak’a da sallah Akan lok’aci ki Duk da nasan baki da wasa da sallah k’i same mahaifiyar ki k’i gaya mata domin ta tayak’i addua domin addu’ar mahaifiya mustajabace…..

   K’uma kema k’i dinga kokarin tashi cikin dare Duk da naga kina tashi domin Allah Yana sakkowa zuwa Sama ta uku Yana cewa Ina masu neman arzuki, ina masu damuwa inyayi musu…to kema sai k’i k’okarta tashi k’i gaya masa shi k’adai zai yayi mik’i, karkice zaki kaiwa malamai kudi wai suyimiki ke menene amfanin ki? Kema malamar kanki ce kawai dai kikasance mai  saka tsoron Allah A ranki wallahi shi kadai zai biya miki bukatarki….

  Duk lok’acin da k’ike cikin damuwa ko bakin cik’i sai kidinga karanta
إِنَّمَا أَشْكُو بَثِّي وَحُزْنِي إِلَى اللَّهِ 
Cikin suratul yusuf Aya ta 86…,Ko kuma  kina karanta اللّهُـمَّ لا سَـهْلَ إِلاّ ما جَعَلـتَهُ سَهـلاً، وَأَنْتَ تَجْـعَلُ الْحَـزَنَ إِذا شِـئْتَ سَهـْلاً , Ku kuma ki karanta adduar annabi ayub acikin suratul anbiya ayata83
ٰ رَبَّهُ أَنِّي مَسَّنِيَ الضُّرُّ وَأَنتَ أَرْحَمُ الرَّاحِمِينَ
Addu’oin ta cigaba da maimaitawa tana kuka sallama goggo tayi hakan yasa kande ta shafah tayi shiru tana jiran me goggo zatace mata….

     ” kande?

           ” Na’am goggo..

    ” Ne mahaifiyar kice ina sonki acikin ‘ya’yana kuma wallahi bazanso aci yau kin wulakanta ba inaso k’i sanar dani wa kikafe so acikin mutane ukun nan?

    ” kuka ta saka ta kwanta akan cinyar goggo tace dukk’an su inason su goggo!…

     ” kanta ta shafa tace duk’a fa kikace kande tabbas akwai wanda yafi kwanta miki arai inaso kar shedan ya rude ki tashi kiyi istikhara ki nemi zabin Allah, ke kumayi shawara da mutanen kirki Allah yabaki Nagare…

     ” Tohm goggo zanyi yadda kikace goggo, goggo mamee mutuniyar kirkice ki taimaka kibarni nakoma gurinta…

    ” kande zamanki gidan kawunki shine Alherin ko dan ilimin ki Zaman tare ai yagaje haka jini da fata ma akan samu zabani ballantana Dan Adam da Dan adam hakurin ka da iya maganar ka da iya kalaman soyayyar ka ba zaisa ake batawa ba komai jindadinku watarana sai kunje babu dadi shiyasa kowacce mace ta kasance tana addua allah yabata namiji mai fahimta da saukin Kai,Kuma shi fada  gyara yake kawowa sai kiga mutum ya kullacike da zarar kun dan samu sabani kowa zai fadi abunda ke ransa daga nan ya huce sai kiga kun koma kamar bakuyi ba,Hausawa sukanci zaman tare ba fada munafurci ne domin kowa yana kullatar kowa inda zaku bisu cikin ransu dabakuso kunje me suke kullawa ba,Kagaya mata ta gyara tagaya maka ka gyara shine zaman kauna kuma kinga mahaifinsu ya kasance mutumin kirki…..

       ” Hakane goggo zanyi hakan Allah yakara mana hakuri…

   ” yanzu ki kwanta kiyi baccin ki wannan kukan naki ki tsayar kinje…

      ” Tohm inna..

Bayan haruna yayi sallah tsayawa yayi yana addu’a indai  kande ba Alheri bace agareni Allah ka hadani da Alheri na, ya ubangiji kasaka min hakurin rashinta in tace bata sona, magriba ya tsaya yayi sannan ya shiga gidan tarar dasu su kayi sunata hira, kande ce tace yaya abdul kaci abinci ne naga kayi shiru?

    ” haruna ne kirjinsa ya dan buga, sannan ya jingina da bango zuciyarsa cike da kunci…

    ” Naci my humairat, so nakeyi Natafi yanzu ma!…

    ” goggo bani wayanki  , yauwa yaya rubutamin number matarka data mamee da takah!…

     ” tohm shikenan mikomin, to goggo ne zan tafi sai gobe zan dawo inshaa Allahu…
   
   ” Ka gaida gida..

       ” mikewa tayi tace yaya bari na raka’ka, lokacin da ta huce taga  haruna a tsaye sallama sukayi da kande sannan ta dawo gida haruna tagani tace yaya ya naganka atsaye?

   ” kallon ta yatsaya yanayi har nakusan mintuna…

    ” Hannun ta ta kiftamasa yaya lafiya kuwa…

      ” bakomai lafiya..

   ” Okay shikenan..

Haruna ne ya kalleta har tashiga cikin gida lallai kande bata sonsa sai yanzu ya yarda da hakan cikin gida ya shigo sannan ya samu guri ya zauna…

     ” goggo ce tace gasu hamza can suna cin abinci Naka yana dak’in su…Goggo a koshi nake jiran Alhaji nakeyi mukuma ne bacci ma nakeji…. +

      ” haba haruna tun karfi 1 fa kuka fito mai kaci da zakace ka koshi?

     ” murmushi yayi yace akoshi fa nake fa!..

    ” kande ce ta sace kallonsa taga idonsa duk yayi wane iri mik’ewa tayi tashiga dak’in da iya habu take yar tsohuwa ta har yanzu baki idar da sallar bani?
     ” Na idar yanzu nake shirin fitowa, ashe harkin warware kin daici abinci ko?

     ” Naci tuwon dadi wallahi, Amma yaya haruna yak’i ci tundazi sai fama dashi goggo takeyi…

    ” ke kyaleshi ai ba yaro bani ba da za’a dinga lallabashi…

      ” haba iya kefa kike cewa mudaina zama da yunwa please kije ki saka baki yaci…

     ” Toh tashi mu fita, binta tayi daga baya iya ce ta samu guri ta zauna…

     ” Mama farida ce tace oh kedai da kande sai Allah! Tun dazu tana nane dake…

        ” iya ce tayi dariya tace kuma haka za’abarmu ba!…

     ” kande tace gayamata dai..

        ” kai kuma haruna ina jinka anata fama kaci abinci sai kace yaro, tashi kije kande ke dakko masa nasa….

    ” mikewa tayi ciki da jindadi da bai musa ba dan tasan halinsa tsaf zai iya cewa bayaci, sallama tayi acikin dak’in ya hamza tagane shi kadai yana danna waya….

     ” A’a Aisha shigowa kikaye mugaisa?

      ” wayancewa tayi tace uhm dama tambayar ka zanyi abi yana lafiya ko?

     ” yana lafiya kalou wallahi naji dadin tambayar nan ummi ma tace nagaida ki…

     ” Ina amsawa kadai ci abinci ko?

    ” Naci tun dazu kinga na haruna ina tunanin bazaici ba sai ki tafi dashi..

     ” murmushi tayi ta dauka tace tohm sai anjima…

      ” my dear Aisha inasonki ina kuma kaunarki kisan wannan….

        ” murmushi ta karaye daya bayyana hushiryar ta, wane abun ba raban mu bani shiyasa ya kamata muyita addu’a….

       ” shiru yayi yana nazarin zancen…

       ” Tana karasawa tsakar gidan ta tsugun na ta ajiyewa yaya haruna…

       ” ko kallonta baiyi ba ta mik’i ta dawo kusa da iya habu…

   ” Dady ne ya shigo yana kufito to mutafi, kande taso…

      ” iya ce ta katse wallahi babu inda zataje yau dinnan har sai ta amince kwazo ku karbe ta….

     ” Dady ne yace tohm iya yadda kikace haka za’ayi, hamza ne ya fito ya shiga mota nan haruna yayi musu sallama…

     ” Can kande tace laah wayar yaya haruna bari na kai masa tana dannawa taga hotonta ne akan screen din tiris tayi tana kallo tana gaba tana kallo taje tayi karo dago kai tayi tace ga ga gashi….

     ” shan kunu yayi yace mik’i keyimin da waya?

     ” Kallon screen din takarayi sannan tace mantawa fa kayi ta chanja murya tace Amma kayi hakuri!…

     ” to ai bakiyimin laifi ba!…

    ” cikin shagwaba tace gashinan ka bata fuska…

     ” murmushi yayi yace bye sai goben kee….

     ” yaya tsaya please!

         ” yaya akayi?

   ” wayata a kan mirror sai kayana please ka ibomin…

      ” A nawa zan ibo miki?

     ” Dariya tayi tace duk kudinka kai kafiye zolaya nidai kataimaka please…

     ” Haha tohm bye, maganar da sukayi ita takara watsakar dashi sai yaji dadi a ransa jiyaye acikin ransa kamar tace ta Aminci dashi…

Birni
   Farida da firdausi ne suka gama gyara gidan sannan suka dora taliya da miya sai da suka tabbatar sun jera komai akan dinning sannan suka huce suka tafi sallah, mumy ce tashiga dak’insu sannun ku Allah yayi muku Albarka…

     ” Ameen mumy Allsh dai yada kande ta dawo domin zama da’ita zaisa mu amfana awannan lokacin da muka gane kuskuran mu…..

      ” Firdausi tace Ne wallahi islamiyar da ta shiga nakeson shiga bakije karatu ba…Wallahi na tuba sosai nakuma fahimce ita duniya bakomai baciba face abunda Allah ya rubuta shi zai faru… +

     ” Firdausi tace Allah yabamu mazaje Nagare yakara shiryar mu…

     ” mumy ce tace ku tashi mu sauka gasu can sun dawo…

      ” Duk suna zaune akan dinnig dady sannu da zuwa…

     ” Hamza ne ya kalle farida yace lallai su o’e anyi hankali, yanzu babu girman kan kenan…

     ” jikin da zai zama gawa me ya jawo girman kai? Ai dama wata fitinar wa’azi ce….

     ” murmushi yayi yace Ai hakan yayi kyau…

     ” Dady ne yayi wanka yasa jallabiyar sa sannan ya kwanta…

      ” mama farida ce tayi wanka sannan tafesa turare ta saka wasu kaya masu kyau ta nufe dak’in dady kofa ta bude Amma bai juyo ba kashi fitila tayi sannan taje ta kwanta rungumeshi tayi ta baya ya mijina banason ganinka cikin damuwa!…

     ” jiyowa yayi ya rungumeta sannan yace yaushe iya zata daina ganin bak’ina akan batan kande?

      ” sha kirjensa tayi sannan tace ai ta dadi da daina ganin bak’inka mijina kawai dai tana bukar kande ne nakwana biyu!…

      ” Tohm haka dai kikace Nan tafara gigetashi dakyar ya saketa da asuba sukayi wanka sannan tafita dura break fast! ….

     ” bayan ta dawo tace ina kwana mijina?

     ” lafiya lou dama inason in tambayiki da umara da aikin hajji wanne kikafeso?

    ” rike kirjenta tayi tace kaddai biyamun zakayi?

    ” kwarai kuwa yadda kike faranta min kema ya kamata na faranta miki ina sonki farida ina kuma son kasancewa dake…..

   ” mekewa tayi takarasa kusa dashi zama tayi akasa tace kullum naganka cikin walwala shine burina, in ban faranta maka ba wazai yimaka karfa kamanta lada nake samu, nagode maka mijina Abin al faharina….

    ” murmushi yayi sannan ya sauka kasa domin karyawa……

Jigawa…

   Nifa Abban meenal bangani maka ba fa tunda kamayar da wannan humairat din kak’i walwalah jiya through out karatu da sallah naga kanayi yanzu ma kak’i cin abinci please kagayamun damuwar ka mana?

   ” Au dama kindamu dani kenan koma menene ai ke kika jawo, kuma inbanyi ka daicin my humaira ba kadaicin wa zanyi? Ta daukeni sai kace yayanta ke kuwa kin banzatar dani hakkina ma ba bani kikeyi ba abincin ma sai kinga dama kike dafawa, in naci miki ga abunda nakeso sai kice wai ke ba hakaba to ya kikeso Nayi??? Kin kasa fahimtar halin humaira ke kanki kika zauna da’ita sai kin karu!…

    ” Nasiba ce tace yanzu dai kana nufin Aure zaka kara kenan?

     ” soonest ma kidai ki zuba ido kigane, Nifa d’a namiji ne koda inajin dadin aure zan iya karawa domin nasamu karen jindadin Amma bama Naji dan Haka karawa zanyi…

     ” shiru tayi bataci komai ba har yafita….

    ” Lokacin daya isa gidan mamee Nan ya bata labarin dagen kande da irin mutuncin  irin nasu…
     ” yanzu bazasu barta tadawo ba kenan?

      ” wai mamee bakiga fadan da sukayi akan a kauye zata zauna ko birni ba!..

    ” Toh yaya kayi maganar auren nata?

    ” Allah dai kawai ya taimakine dan can ma tanada wayanda suke sonta!…

      ” Toh Ameen, nema in ankwana biyu kakaine naji naganta naga tanason system sai kasiya mata….

      ” Eh har wayama nake tunanin siya mata bari naji office inada aiki anjima zanje naji yadda ake ciki….

     ” Toh Allah ya taimaka yakuma yimaka Albarka yasa rabonka ce!

       ” Ameen mameetah..

     
   Kauye

      Da asuba bayan kande ta tashi wanka tayi sannan tayi sallah ta tsaya tanata addu’oi Allah ya zaba mata miji nagare, magungunanta tasha, ta dakko nasha fawa, tsintsaya ta dakko tafara shara gashi bata iya sun kuyawa sosai saboda kafar tata batayi kwari ba….

     ” menene haka kande kinaso ki mayar da baya gaba ne? Ke da kafarki batayi kwari ba? Bani tsintsayar nan jik’i koma baccin ki…

  ” To yaushe sadiya zata dawo daga gidan anty badariya? Kuma da kin barni ina iya sharar fa!…

     ” karki damu anjima zatadawo, kuma Gani da ‘ya’ya maza su sukeyi min ai karki damu…

      ” Goggo Ai kwashi ladan sukeyi bari toh nahada huta!..ai yanzu arusho nake girke in kabiru yafito zai dura… +

       ” toh ne gaskiya inason yin wane Abun…

     ” Kande  *ki ta dabbance*Allah ubangiji yayi miki Albarka, ya kuma baki miji nagare…..

     ” Ameen goggota, bari to naje Na kwanta tana shiga dak’in taga iya habu tanata lazumi, yar tsohowa kina burgene fa ke agurin ibada bakya sanya shiyasa nake tsoron fishin ki ko fadanki…

     ” kema ai haka kande, wallahi nafeson kiyi zamanki anan, in ma baki zaba acikin wayannan yaran ba, Allah yakawo miki wane anan kiyi Aurenki ko?

    ” yauwa iya gwara dakika tunamin kinga dai kidaina yiwa dady abunda kikeyi masa kinga babu dadi karyaga kamar ninake sakake….

      ” kinji ki ai in ba haka ba raina ki za suyi….

     ” Raini kuma iya Ne wallahi rainun su baya gaba na indai Allah ya yarda dani shikenan walhi…..

      ” hakane toh Nadaina bani wayarki zanyi waya karba tayi tashiga cikin daki kan katifar sadiya numbobin Nasiba takirawo ringing daya ta dauka! Salamu alaiki….

     Wslm, wake magana?

      ” humaira ce dafatan kina lafiya ya yaya abdul dasu meenat….

     ” Na tacciya lafiya menene kuma?

     ” Dama na bugo ne nayi miki godiya abisa Abunda mijinko yayimin Allah yakara bude! Nasan yana yawan yimiki maganata kuma hakan baya miki dadi, toh Agaskiya abunda zangaya miki shine kije tsoron Allah kiso mijinki domin shine rufin asirinki, ki tararrayi abunki, ki kuma kula dashi, karfa ki manta Aljannar ki tana tafin kafarsa, yanzu kuma rayuwa ta zama abun tsoro wallahi kikama mijinki kokuma wasu awaje su kama miki, kuma ya bani labarin kema marainiya ce why not ki zauna ki riki abunki yazamar miki uwa da uba ga ‘ya’yanki nan kiyi musu tarbiya, ki
kula da lokacin cin abincinsa,da nutsuwa lokacin baccin sa, saboda yunwa tana sa mutum ya fusa ta, kwaramniya kuma lokacin da mutum yake bacci babu dadi, ki kula da mijinki sai ya zamarmiki abokin rayuwar ki, In nataba yimiki laifi ki yafemin Allah ya hada fuskokin mu da Alheri….
    ” Nasiba ce tace Amin nagode lallai humairat ta dabance….

     ” haruna ne yayi sallah hannunsa rik’i da leda ya shigo sai da suka gaisa da goggo sannan ya huce dak’in iya habu…

    ” lah haruna ina kasuwar? Karkusa yarinya agaba tafara ramewa…

    ” murmushi yayi yace toh ai suna hanya su alhaji ma ina kande take ga sakonta na dakko mata?

    ” jira ba yanzu ta dauki wayata tun dazu taki waya ni kartama cinyi min katina shiga ka kaimata….

    ” dak’in yakarasa tana bak’in katifa tana ganin sa ta ajiye wayar! Ina kwana yaya?

    ” zama yayi akan sallayar kusa da’ita yace dawa kike waya?

    ” yadda ya bata ran shine ya bata dariya can tace wa kake zargi nayi waya dashi?

    ” ki bani amsa dawa kike waya?.
   
    ” shiru tayi taga lallai da gaske yake!…

   ” wayar ya dauka yabi number sai yaji ance Nafa gode yaruwa, murmushi yayi yace toh naji dadi yanzu ga kayanki…..

    ” Nagode sosai wayar tana ciki ne?

     ” eh suna ciki duk’a..

           ” ga koko in zakasha nasan balallai ka karya ba!

     ” aa firdausu ta dafamin indomie ta kuma hadamin zobo

      ” lokaci daya ta tsinci kanta cikin kishi…

      ” ya naji kinyi shiru, ko bakyaso ta dafamin ne, ita tadamu dani bata barina cikin yunwa kalle cake din datayimin ma ko zakice…?

      ” Allah ya sawake naci, abunda nafita iya? Kuma ai bakaci min nayi maka ba!….

     ” Ai naga baki danu daniba shiyasa Amma bakomai tunda haka kikace kima sai kiyi naki gwanin tar….

     ” yana ga katashi ko tafiya zakayi daga zuwa?

      ” eh zankai su farida unguwa ne kuma inada kayan da zan dakko a airport!!!

    ” unguwa kuma kai dan aikin sune?

    ” To ba kanina bani ba?

      ” mikiwa tayi tace Allah bazaka tafi yanzu ba!

      ” ai kuwa babu abunda zai hanani tafiya…

     ” kuka tafashi dashi sannan ta zauna tace dama ai baka damu dani ba???

      ” hanyar fita yayi yaji dadi sosai har cikin ransa yadda tanuna kulawarta akansa…

       ” indai katafi wallahi karka kar kara kulani… +

     ” baya yadawo sannan yazauna to kinsani gaba sai kace ‘danki…

     ” shiru tayi ta bude ledar me zata gani laptop da sabuwar waya kunnawa tayi zuciyar ta cike da murna kunna wayar tayi abunda da tafarah gani yasata dariya I am entirely yours, that if I might have all the world given me, I could not be happy but in your love, Nagode yayana…

     ” bana bukatar godiya so nakeyi naganki cikin farin cikine…

    ”  bari Na kira yaya abdul mu gaisa…

     ” yadda taga idonsa ya kada yasa ta wayance tace au ashi ma zaizo magaisa…

      ” Bari na tafi toh..

   ” mikiwa tayi tace please yaya karka kaiso ko’ina kaifa ba driver din su baniba….

    ” Tohm shikenan sai anjima..
     Su goggo ta nunawa da iya habu nan suka dinga yi masa mata murna!..

    ” yaya kabiru yace ga tea dinki can kije kidauka…

   ” oh su yaya an iya girki, bari naje gurin yaya kabiru nadawo dak’insa ta shiga…

    ” ya akayi mutuniyar? Yanzu dai kinzaba? Ko

      ” Nidai yaya duk istikharar danayi hankali na yafi kwanciya da yaya…

     ” haruna ko? Nima dai hankalina yafi kwanciya dashi…

     ” murmushi tayi tace eh shi…

       Tohm zan sanar dasu goggo…

    Lokacin da sadiya ta dawo rungume yar uwar tayi tanata murna chan tace yaya kinga yadda kikaye kiba..

    ” mashaa Allah su hamza taga sun shigo gaisawa sukayi sannan sukayimata yakarin jiki, Nan goggo ta gayamasa wadda kande ta zaba sai da jikin hamza ya mutu dakyar yace Allah toh yasanya musu alkhairi…

    ” hamza ne ya shiga dak’in da kande take yauwa inason dama ganinka…

     ” me zakice min kim yaudari ne kin yaudari zuciyata haba aisha yazakiyi min haka….

     ” kuka tafashi dashi sannan tace yaudara fa kace ya hamza yaudarar ka fa kace ta yaya nasanar dakai na nunama nakuma gaya maka Allah yana gani ban yaudarika ba kuma yaya zanyi da kaddara Da Allah yarubuta kaifa kacemin matar mutum kabarin sa, in har hakan ya bata maka rai to ina neman afuwarka kuma kasa aranka ni ba alheri   bace kuma Alkhairin ka ta na nan….

    ” Nayarda na kuma gode!

     ” kada kayimin haka kada ka kullecine….

     ” juyowa yayi idonsa jajir yace Wallahi inasonki aisha yaya zanyi da son naki?

    ” Allah zaicire maka.. 

      ” fita yayi sannan ya huce gurin su goggo can yaje goggo tace…

    ” yaya maganar taka da farida hamza kaga sai ahada danasu kande..

    ” cikin kunar rai yace tananan toh…

     ” dady yace Amma naji dadi kinga yanzu anyi sittle din komai ko?

    ” Dakyar iya ta yadda suka tafi da kande da sharadin duk sati zata dinga zuwa…

    ” tun amota idon kande yayi jajir babu abunda taki sai kuka sai da suka ajiye da dy a office sannan suka huce gida bude motar yayi sannan ya kallita yace na amince da hakan kuma na yarda zan aure farida…

   ” cikin mamaki tace da gaske?

      ” kada mata kai yayi sannan yace eh…

      ” murmushi tayi ta shiga cikin palour nan suka gaisa dasu mama farida da mumy sannan ta huce dak’inta tsintsiya ta dakko bashiri mama farida ta shigo ta karba kinsan an hanaki shara kawo na share miki…

     ” Hamza kuwa kusan awansa daya acikin mota babu abunda yakeyi sai tunani zazzabi ne ya rufeshi da kyar ya karasa dak’insa cike da Addu ar Allah yasa Hakan yafi Alheri…

    Jigawa

  Nasiba ce tayi wanka tasaka kananan kaya sannan ta gyara gidab ko’ina kamshi yakeyi abdul ne ya shigo mamaki ne ya kamashi yadda yaga gidan ya gyaru!

    ” mikewa tayi ta rungumeshi sannan ta rik’i jakarsa da hannunsa sai dak’i toilet ta kaishi tace kayi wanka tukunna…

    ” ya kusan 30 mint yana tunani can kuma yafara wankan..

      ” abincin sa ta zuba masa ta zauna a dining domin jiransa..

   ” can yafito yace yau kuma yanaga kin chanja mini?

      ” murmushi tayi tace Akwai abunda yafi mijina?

   ” murmushi yayi yace babu kamar mata ta nima…

    ” to sai kazo kaci abinci, bayan yagama ni yace nikuwa ince kaje gurin humaira yau?

     ” A’a banjiba, sai gobe barci nakije bari naje tashi tayi itama tai wanka tashafa turare ta saka kayan bacci tana zuwa dakin ta kwanta dama abdul amatse yake baisan lokacin daya fara shafata ba, sai da ya tabbatar jikinta ya mutu sannan ya fara aika mata sako… +

    Birni

   Yau aka kai kudin auren kande da haruba dubu dari da kudin auren farida da hamza dubu dare sai kudin auren firdausi da Aliyu ansaka bikin wata 5 nan gaba…

     ” murna gurin haruna ba acewa komai sai addua yakeyi yana nuna godiyar sa ga Allah….

     ” lokacin da dady ya tambayi wa firdausi takeso tace Aliyu dama shi aliyu yana sonta…

    ” Farida ma saboda murna sallah tafarayi…

    ” Kande na kwanci haruna ya shigo a hankali yace my wifey…

     ” murmushi tayi tace Naam…

    ” Duramin indomie kikuma hadan zobo zanje katsina yanzu be past…

   ” cikin turo baki da shagwaba tace katsina kuma???…K’ande na k’wanci haruna ya shigo a hank’ali yace my wifey… +

     ” murmushi tayi tace Naam…

    ” Doramin indomie k’i k’uma had’an zobo zanje k’atsina yanzu be past…

   ” cik’in turo bak’i da shagwaba tace k’atsina k’uma???…

” cik’in zuciyar sa yace wannan shagwabar Ne bansaba da ita ba!….

    ” yaya Am talking fa? K’a shiga Duniyar tunani ko maganar ce bata yimaka bane?…

     ” uhm ya d’an gyara tsayuwar sa kinsan dai ak’an business dina zanji k’o k’uma kinaso Na hak’ura da zuwa?

   ” Murmushi tayi sannan tace har naji dadi wallahi da banyi maka laifi ba, kuma ina zanso yayana yake fita neman halak d’insa?

    ” shima murmushi yayi ya sosa kiyarsa yanayin yadda take magana yana burgesa!…

    ” Can k’uma tace Ne kuwa yaya kunyi waya da yaya abdul ne??

      ” Cikin chanja fuska yace ba muyi ba!..

    ” wayanta ta dauk’a tace kaga in Na kirashi sai Naji switch up…

      ” A hankali yace that’s your problem, kuma let me tell u ban sai miki waya dank’i dinga kiran maza ba Na siya miki ne d’an karatu!…

    ” Wane iri taji tace karkace haka yaya akwai mutanen da suke da Mutukar mahimmaci gareni ya kamata aci Muna gaisawa….

     ” has you what to say it! Ne banida mahimmanci kenan? Okay that’s good dama bakya sona ninake fafutuka ta!….

    ” Tsayawa tayi tana kallon sa cikin ikon Allah tace haba yaya mekake kokarin cewa ne???

     ” bude kofar yayi yafita…

       ” Biyo bayansa tayi, atsayi taga firdausi tana cewa, kacemin fa zakayi tayi kuma kaci abincin ne!…

    ” Na k’oshi ya shige dak’insa…

         ” k’ande tiriss tayi tana kallon su batasan lokacin da i’danu wanta suka kawo ruwa ba….

” firdausi ce tace oh k’ande ashe kin tashi?

    ” Sauri tayi ta goge hawayen fuskarta tayi murmushin da kowa yasan yak’ine, eh Na tashi yanzu Nake shirin fitowa, ince dai baku gama girki ba?

    ” Allah sarki, Ai mungama tun dazu cous cous Na dafa!

   ” rik’e goshin ta tayi tace ohhh bancin cous cous bari Na dafa indomie hope akwai zobo?

    ” eh Akwai bari Naje zanshiga skull yanzu shiyasa…

       ” okay, kitchen ta shiga sannan ta hada indomie, cikin mintuna ta hada zobo ta tawo hanyar palour kenan ta hadu da ya hamza!..

    ” kanwata wane dadin kika dafa mana?

     “Murmushi tayi tace indomie ce ko zakaci ne?

    ” yayi dariya dadi na dake bakida rowa wallahi bari na tafi office see you later!…

    ” okay, ta shige bangarin ta dak’in haruna ta shiga a tsaye a zaune ta ganshi gefen gadon sa, ya sun kuyar da k’ansa…

    ” sallama tayi Amma shiru bai amsa ba! A hankali tace yaya Nashigo??? Nan ma Bai bata Amsa ba, karasowa tayi tana fadin subhanallhi yaya what wrong? Ga indomien na dafa maka…

     ” Dauk’i abarki kibarmin dak’i tunda ne banda mahimmanci a gurinki yaushe zakije tausayi na yaushe zaki tausayawa zuciya ta kinsan tsawon lokacin da Na dauka ina dak’on kaunarki me isa kikemin haka me isa kikeson kisani cikin wane hali?

     ” hawaye ne ya fara wanke mata fuska cikin sarkarkiyar murya tace kadaina fadin kalaman dakake fada bana nufin in bata maka, Nema ina kaunar ka kayarda dani!..

     ” Cikin mamaki yace dagaske? Da gaske kina sona!…

     ” hawayen ta ta goge i mean it yayana!…

    ” matsalata daya da aka kaimun bikina nesa ina bukatarki kusa dani!….

    ” komai lokacina, kamar yaune zaizo, ya baka tafi ba???

    ” ta yaya zan iya tafiya bayan kinki ki dafamin? Ta yaya zan tafi dake azuciyata?

     ” murmushi tayi tace bazan iya barin ka katafi batare da kaci abinci ba, karbe abincin  kaci kaje yayana…

     ” tohm matas mik’omin nace…..Hawayen fuskar ta ta goge..cikin sanyin murya tace  ‘mean it yayana’!… +

    ” murmushin jindadi yayi can k’uma yace Matsalata daya da aka kaimun bikina nesa ina bukatarki kusa dani!….

    “Shiru tayi Nadan lokaci can kuma tace komai lokaci ne, kamar yaune zaizo, ya bak’a tafi ba???

    ” Ta yaya zan iya tafiya bayan k’inki k’i dafamin? Ta yaya zan tafi dak’e azuciyata?

     ” Murmushi tayi tace bazan iya barink’a k’a tafi batare da k’aci abinci ba, banaso tun yanzu ka saba dacin Abincin waje…karbe abincin k’aci kaje yayana…

     ” wane lallausan murmushi yasaki sannan yace matas mik’omin nace…..

  ” mik’amai tayi bari naji gurin Anty farida akwai maganar da zamuyi da’ita…

      ” Okay tohm kice mata ta turomin da kayan da tace tanaso ta whatsapp kuma kafin nadawo kice ayi passport din!..

     ” Zan gayamata, tana fita taga mumy kunya ce duk ta isheta..

     ” ya jikin Nak’i k’ande, tun dazu nake cewa su farida su kiraki kice Abinci….

     ” mumy jikina Alhamdulilahi, yanzu ma sama zanje zan shiga dakin nasu ai…

       ” Toh haka nakeson ji abunda nakeso Dan Allah kicigaba dayin hakuri komai Na rayuwa mai hucewa ne komai yayi farko kuma zaiyi karshe, Abunda nayi miki kiyi hakuri sharrin shaidan ne…

    ” lah mumy ai yahuce ai ne amatsayin kaddara Na dauka…

     ” murmushi mumy tayi sannan ta huce kitchen…

    ●●●●

Anty kiyi hakuri sai yanzu nashigo nadan dafa Abinci ne…

      ” A’a amaryar haruna bada kanki Asare, Allah dai yayi damo ga harawa haruna ne dai mijin naki…

     ” hmm ta’ina yazama mijina ai ba’a daura ba kubare in aka daura sai ku k’ak’aba min shi, kuma nifa ba sonsa nake ba babu yadda zanyi…

    ” hahaha Ne zakiyiwa siyasa ina shekara 32 kice bansan halinki ba?

     ” Taba baki tayi tace anyway menene Na kiran nawa? Inaso Naje skull yau!..

    ” yauwa kande inaso ki dau komai amatsayin ya huce, ki duba kiga bantaba tunanin wannan samarin naki da sukace suna sonki abun zaizo da sauki haka ba, Amma saboda addu’ar dakikeyi komai yayi sauki har su su firdausi sun hakura!…

     ” hakane me kuma akace nayi? Wallahi nifa in aka kara matsamin sai nabar musu haruna nakoma kauye na nayi aurena sai kace shine autan maza….

    ” kinje ki ko har yanzu baki iya magana ba, Ai shi makeyi abunda zaka k’untata yakeso, wallhi kiriki haruna dakyau kina dai ganin harkar business yakeyi yana haduwa da matan da suka fiki komai….

    ” Nagode, yanzu wannan bayanin dakika gamayi wanne karatun ne a karshe?

     ” Dady nakeso ki samu kibashi hakuri akan su firdausi kinga yanzu suke bukatar kudi gashi jibe graduation nasu….

     ” kina nufin akaina yake fushi dasu har mumy?

      ” tabbas dan naji yace indai baji yayi kince masa kin Yafemu suba to wallhi yanzu suka fara fuskantar abubuwa….Zan kokarta Anty bari nasha maganina nayi Sallah.. +

   
●●●

   Hello haruna wai kana inane remain 5mins flight ya tashi…

     ” kamar yaya flight ba mukhtar ne zashi india ba?

     ” ka duba document naka kaine so be worry please…

     ” ai kuwa yana dubawa ya sunansa! Opps ya Allah ai ne ban kulaba, jakarsa ya dauka da wayarsa sannan ya fita straight sai airport Nan akayi search suka tashi, zuciyar sa wane iri yanzu bamuyi sallama da matas ba ohh shit…

      ●●●●

K’ande ce tashiga cikin fara’a tace a’a ‘yan uwa ashi kuna daki?

     ” farida tace yanzu muke shirin fitowa ai…

      ” kande ce taji babu dadi sannan tace hooo Nima makaranta zanje see you later!…

     ” firdausi ce tace see u later dear…

     Bayan fitar ta farida tace nifa bazan taba son yarinyar nan ba ta wane zo ta zauna mana agida sai kace Nasu….

      ” haba sister kanwarki cefa, ki daina fadin irin maganganun ba…

     ” mikewa tayi tace mtseww kikaga zaki iyah…

●●●

   Sai after 5 su haruna suka sauka, setting din komai sukayi, haneef ya samar musu hotel suna shiga kowa ya wada dak’insa haruna dayayi wanka sai ya huce zuwa masallaci yana dawowa yaga yarinyar nan mujeeba data mayanci masa ko kallonta baiyi ba ya shigo dak’insa …..

     ” Murmushi tayi sannan ta huce dak’in haruna budewa tayi batare da neman excuse ba…

    ” mik’iwa yayi sannan yace how thr you da zaki shigomin daki babu knocking???

    ” haba harun shigo nayi mugaisa fa, some tips zan baka naga company namu sun dauko ka! Cuz I don’t think zaka’iya dasu…

   ” tsaki yayi yace see this idiot what ur concern da iyawata da rashin iyawa ta….

    ” murmushi tayi sannan tasamu seat tazauna tafa hannu tayi tace this is serious, look at you up and down wai Nik’ake wulakanta wa, how men Nake hulda dasu manyan attajirai….

      ” you’re bastard, quickly walk out from my room…

     ” cool down! i will walk out..but kasani it most to u to love me .. let me tell you ma in bakayi wasa ba har aurena sai kayi so becarefull am mujeeba…

    ” actually you’re totally mad look at you DanAllah dai kace pastor shine zakice saina soki? Toh inada matata mai hankali mai kuma kaunata…

    ” as u said it bazaka soni ba! Hahaha Am muneeba keep watching…

    ” enough idiot walk out….

     ” Bude kofa tayi sannan tafita directly office nata ta shiga manager tasamu i need to talk tou u so be quick…

    ” muneeba what wrong? Naganki cikin bacin rai, kinsan banaso ganin bacin ranki….

    ” that’s good in bakason ganin bacin rai na ina bukatar biography akan haruna right known…

     ” haha ya nuna miki halin Nasa kenan! First of all yarone matashi yayi karatun sa akan business yazo kuma yayi arabic, shekarar sa 34 i think yakusa 5 ma yanada mutunci yana da kuma kudi baya shiga harkan yanmata kuma yanada zafi…

     ” bashi nakeson kagayamin ba yanada aure kokuwa???

    ” bashida aure but remain 4mouth bikina da wata cousin tasa…murmushi tayi tace cool…u can walk out… +

” fitar da manager yayi yasa ya dafe kansa! How come’s muneeba ta fada soyayyar haruna..

    ” murmushi ta’ima tayi tace zan horashi zai san ya hadu da hastsabibiyar mace, zuwa tayi ta buncika schedule dinsa sannan ta huce hotel din….

●●●
  Mek’e faruwa haruna tunda muka dawo daga company kayi tsit…

    ” haneef when zamu tafi ne?

    ” tooo anya lafitarka? Har yaushe akayi drawing tshirt din? Kasan sai fa an sarrafata tukunna…

     ” yanzu to zai kaimu how many mouth…

    ” to abarshi 2 to 3 arashin sanina…

      ” Dogon breath ya dauka sannan ya saki,tashi muje resturant din nan kasan ina son gurasar su…

   ” okay let go!..

       ” muneeba tana ganin fitowarsa ta gyara wayan hannunta..

     ” k’allon ta yayi ya kau da k’ansa..

     ” murmushi tayi tace haneef ko?

     ” suna tafi tare yace yes in ban manta ba muneena ko?

     ” yes am muneeba, ya aikin naku hope yana tafiya well?

      ” haneef Ne ya nuna haruna yace haruna baka ganita baniba?

     ” kai dakake kula kulin mata kai kadai zaka ganeta!

      ” dariya tayi tace gaskiya haneef Abokin ka is to harsh..

      ” No fa karkice yaka, bahaka yakeba wallahi kema zaki saba dashi…

     ” kuma hakane yanzu ina zakuje, yunwa nakeji fa…

      ” abokina kison gurasa..

     ” yeap kasan kuwa nema ita Nakeson ci..sai ku tawo mu tafi tare…

     ” banza yayi musu ya cigaba da tafiyarsa sai da suka isa gurin yana zama ta zauna kusa dashi yayi saurin mikewa ya chanja chair…
   
” haneef ya kalle muneeba sorry muny abokina daban ne fa!…

     ” Nop bakomai fa so don’t mind Na fahimce shi…

      ” haruna ne ya kunna wayarsa number kande ya kirawo kusan 5miss call bata dauka ba, ransa ne ya baci sannan ya mayar da wayar bayan sun gama cin abincin hucewa yayi yabarsu…

    ” haneef ne ya shiga dak’i yace haba haruna why bazakaje dadi ba wannan pretty din…

     ” Actually idan kanason mudinga mutunci da kai so karabu da yarinyar nan, kai ko kunya bakyaji aganka da yar iskar Nan?

     ” haka dai kace Amma ai tanada mutunci kuma tana da k’ima ahaka..

     ” hs u said it…

   Nigeria..

Tun bayan sallar la’asar kande ta shirya cikin kayan makarnta dak’in mumy tashiga tace mumy natafi…

     ” firdausi ce tace Nima zan shiga please nawa ne form din?

     ” ya haruna ne ya siyomin ki tambayi shi but bana tunanin yayi dubu hudu …

      ” Ai yanzu sun isa india, anjima zan kirashi…

    ” cikin ranta tace india? Katsina dai kuma ko sallama baiyi min ba…

      ” A hanya k’adaicen uncle isyaku ya ‘isheta duk abu ya dameta to ko yayi aure ne? Amsar data kasa bawa kanta kenan sannan ya shiga makaranta Nan malamai suka dinga yi mata Allah ya kiyaye gaba…

STORY CONTINUES BELOW

    ” fatima ce tace k’awata yaya ak’ayi haka tafaru?

     ” Nan kande ta bata labari…

     ” Hmm Ai mutum sai Allah kawata, Allah yakara mana hakuri dai!

     ” Ameen fati me naki gani kamar jarabawa akeyi?

     ” yau dai za’a fara ince dai bazakiyi ba?

       ” Haba kawata me zai hana aine naji dadi sosai Da yasa ba’a faraba…Nan Akazo Aka raba musu jarabawar Nan kowa ya duk’ufa gurin rubutu.. +

    ” Ahankali fatima tace Aisha wane hadisi ne ma yake magana Akan tsayuwar dare?

      ” hadisi mai number 2756 cikin imamu muslim An karbo daga Abi Huraira Allah ya qara yarda a gareshi cewa an tambayi Manzon Allah SAW wace sallah ce tafi falala bayan salloli na farillai? Sai yace: *Mafificiyar sallah bayan sallar farilla ita ce: Sallar cikin tsakiyar dare*…..

    ” Yauwa Dan Allah gayamin sharhin to…

” kande ce tace kiyi a hankali malam usman yana kallon mu.. ki rubura Wato sallar nafila wacce tafi falala ita ce ta dare, sallar dare tana farawa bayan sallar issha’i, in mutum zai iya tashi cikin tsakiyar dare to tafi falala in kuma bai samu ba sai kafin ya kwanta itama tayi kuma Annabi SAW yanayin raka’a 11 ko 13 ne, amma in ba zamu iya hakan ba to dai ayi wutri wato: 3,5,7,9,11,13….

    ” yauwa Nagode…

   Suna gamawa kande tace gobe wanne zamuyi yan aji?

     ” gobe mumada tarihi da kuma tafseer!!..

      ” Allah dai yabamu sa’a kowa yace Amin…

     ” fatima tace yanzu masu kokarin sun yawaita A aji ko su wanene zasu zo ta daya..

    ” kowa murmushi yayi sannan ya fuskanci gida…

●●●

   Gurin karfe takwas Na dare kande ta fito palour dady ta tarar yana karanta jarida zama tayi Akasa…

     ” A’a uwata yakikaje da jikin naki? Akusa kuma akafi muku Admission sai ki shirya, wane satin za’akawo lefe so ina yimiki fatan Alheri…

    ” Dady naji sauki, Dan Allah hakuri Nazo nakara baka, mukanmu mukanyi lefi kuma Allah ya yafemana, wallahi na yafewa su mumy har cikin raina kuma banda niyar yimusu komai kaima kayi hakuri please…

    ” Tohm uwata bakomai Na yafe musu Allah yayi miki Albarka, du haruna suna india zasuyi kusan wata 3 ina fatan yagayamiki?

     ” eh Amma haka yacemin katsina zaije!

     ” eh Ansamu akasine, Duk abunda yake damunki kisanar dani kinje nima kamar iya habu naki…

     ” Tohm Dady..Tashi tayi tana hawa sama taje farida tana ta zagen wata kawarta ga wasu hadisai da take kawowa dabasu inganta ba…

     ” Sister wannan fadan kuma lafiya?

    ” ke banson fi’ili malama kama kanki, Ko aka gayamiki ke kadaice kikasan ilimin addinin?

     ” firdausi ce tace haba farida what is all this ne haba!!!

      ” k’ande ce tace babu yarda za’ayi mutum ya furta zance kowanne iri face mala’iku sun masa e diddika akai..Dan haka ubangiji ta’ala ya umarci mu dayin adalci acikin zance, ku fadi zance na adalci shine zance na daidai,zance wanda yake da gaskiya babu karya acikin sa, Dan haka yar uwa yana da cikin nauk’ika Na zantuka da ya kamata mu kiyaye su, mu nisantar da Kawunan mu daga barinsu, mu nisantar da harshe nan mu daga fadin su fadin zance bisa da jahilce gama  da ubangiji,  kafadi magana bisa ga jahilce ga ubangiji muninsu yafi kowanne kaba’ira dak’asani,  fatawa bisa ga jahilce, shara’anta wane abu kace abu kaza haramun ne ko abu kaza halal ne baka da dalili? Duk’kan wata bidi’a da mutum zai k’ago! Duk’kan wane hallacci ko halacci wanda bashida ma dogara ashara ance,  bakada qur’ani ko hadisi daya tabbatar maka dashi? dan haka ya kamata mukiyaye harshen mu, ka ambaci dan uwanka da abinda bayaso ko da kowa bayaso jifan juna da sunan banza,  ka fadawa dan uwanka zance shi yana tunanin gaskiya kake fada ashi karya kake masa wannan ya isa mutum kayan lefe aranar lahira, kada kace ka shaida alhalin baka nan akayi! Kar ka fadi kowanne irin abu sai kanada ilimi akansa, wannan haramun ne cikin addinin musulunci, duk’kansa abun tambaya ne ranar tashin Al kiyama, Dan haka mukiyaye har shinan mu!…Yauwa yar’uwa gwara da kika gaya mata.. +

    ” ita dai kande batace komai ba sallah taje tayi sannan ta huce dak’inta wane bacci ne yake kokarin k’washar ta, wayanta ta dak’ko sannan ta dak’ko cik’in layen bacci, domin baccin yana kokarin rinjayarta dubawar dazatayi taga 7misscall bashiri ta kira cikin wata sunyin murya tace yaya kun sauka lafiya??

      ” kina ina tun rana naki kirank’i?

      ” cikin sanyin murya tace bana kusane naje makaranta ya india?

        ” murmushi yayi yace lafiya lou Aisha..

      ” har cikin jikinta sai da taje sunan, murmushi tayi tace bacci nakeji yaya mayi magana anjima….

     ” karki katsimin wayar nan wallahi wannan muryar taki dadinta nakeji, Dama aci muna gado daya tare!…

    ” subhnlhi yaya wannan wacce irin magana ce?

    ” Haba aisha yakikeso nayi ne? Ina bukatar mace dama ace kina rungume dani yanzu…

     ” wane tsaki tajah addu’a tayi ta cigaba da baccin ta…

    ●●●●
Jigawa

  Abdul kuwa tunda yaje kauye akace masa Ankawo kudin kande bai kara komawa ba! Ahaka naseeba ta dinga jan hankalin sa…

    ” Mamee ce tace haba abdul menene na fushi da abunda ba alkhairi ne garika ba?

     ” haba mamee duk kulawar dana bata tafa san ina sonta!…

      ” banson sha’shanci sau nawa nake cimaka kayi hankali da shakuwar ku? Yanzu sai kayi hakuri ne wane satin zanje Naganta!..

    ” Allah ya huce zuciyarki mamee kiyi hakuri…

      ●●●●
Birni

  Ke kande kifa muke jira! Da tune mun tafi fa!

     ” kuyi hakuri nagama, a mota suketa shirye shiryen bikin ita dai uffan batace ba in ta tuna da maganganun yaya haruna yayi mata jiya sai taja tsaki haka aka dinga taro sai yamma aka dawo…

    ” Anan firdausi tacewa Aliyu me isa bai zoba?

    ” haba feedy ta ina hanyar zuwa gurinki yanzu dan aikine ya rukine!

      ” yauwa bebie ina jiranka, kitchen ta shiga ta hada masa lemo da meatpie…

      ” kande ce suke hira da anty tace Wai bakyajin  kamshi ne…

    ” inaje firdausi ce aliyu zaizo…

    ” kande ce ta shiga kitchen a’a kice dadi akeyi mana!..

     ” murmushi firdausi tayi tace mijina nakeyi wa…

    ” ahh abun babu kunya? Ko an daurane?

     ” hahaha kunyar taki zance kinga taimakan ki rufemin wancan hadin salad din…

     ” tsaki taja sannan tace bari naji mugaisa kafin kizo…

       ” sallama tayi tace ohhh yaya ali mutuminah yasu goggo da iya habu?

    ” Duk suna nan lafiya kinga transfer akayimin abuja fa!

    ” haba kace zamuje abuja yaya firdausi tare zaku tafi?

    ” eh ai dayake abi yabani gida da mota…

      ” mashaa Allah sai mugode Allah yaushe za’a kawo lefen?

    ” karfa ki ishene!…

  ” wallahi dadi naji dana ganka ya ali dan uwa ai yayi arayuwa…murmushi yayi yace ga katin har an buga fa wai kowa nashi zaiyi…

       ” shiru tayi itada Haruna sai kusan saura sati 2 zai dawo, toh Allah ya kaimu inada jarabawa bari Natafi…

     ” Tm, sallama firdausi tayi ta tsugunna ta gaidashi..

    ” cikin murmushi yace Amma fa kinyi kyau! Congrat kuma angama skul Allah yasa Albarka!

    ” Ameen yauwa dinner 2 za’ayi sai kamu…

     ” Eh haka hamza yacemin ga katinan ma…

   ” ansa tayi tanata kallo taga yarda yayi kyau…

    ●●●●
Abuja…

    Sumayya da maryam ne sukace broz neex week su sister zasu dawo…

     ” ummi ce tace ai daman nagaya maka baka isa auran yarinyar nan da ko cikakken ilimi batada shi…

      ” kema dai kyafada shima uncle hamzan ko ta yaya yace yana sonta?

      ” kema kyafada sumayya!

    ” Hmm! Gaba daya dinner din baza’ayi a abuja ba!

    ” ummi ce tace kai dai kafiye akida ai sai kayita yi…

     ” Ga katin naku nan Yanzu zan huce kano sai kuma jibe…

    ” okay bye Safe journey…

    ●●●●

  Yau watansu 3 a india kullum muneeba kokarin shawo kan haruna takeyi Amma ina sai dai ya kalleta ya kau da kansa!

    ” yau zasuje meeting na karshe directly office din joseph ta shiga knocking tayi sannan yace…

    ” come in!..ohh muneeba 2days?

     ” Am fine!.. i have some important things to talk to u!

    ” i don’t get you?

        ” mertesgerd company is among the best company over the world…

     ” yes i know that, and we also invited one guy which called haruna he’s so gifted and he has many ideas on..

    ” She just smile and said that’s what am trying to said , I want u to make me his security when we attend today’s meeting…

     ” why?

     ” To say the truth our company need some advice, and idea’s to improve.., so only when I meet him I can ask some important question and his tips and co…

    ” glad..that’s good ideas muneeba I trusted you!

    ” she wnk her eyes and said thank you sir…

   ” Tunda akafara meeting haruna yake Sanna phone when dayaji an ambaci muneeba Nan ya ajiye phone dinsa yana kallonta.

    ” Murmushi tayi sannan..

   A nagama meeting tabi bayansa harun harun hannun sa Riko…

   ” wane shock yaji sannan ya fusge hannunsa…

    ” kallon idanunsa tayi taga yadda ya koma red murmushi tayi ta cije lebanta sannan ta huce koina najikinta is moving…

    ” zama yayi akan wata kujera sannan yace ya ilahi…●● +

Ya aka kawo lefen kande akwati 8, farida akwati 12 sai firdausi tara..

   ” mumy ce tace ohh wannan manyan atamfofin na kande kamar sunyi yawa…

    ” mama farida ce tace ne wallahi danaga akwati 8 sai anyi tunanin basu da wane yawa kwata kwata…

    ” mumy tace ai daman ba yawan akwati ba kayan ciki…

     ” yau ma kande tayi shirin bacci kenan haruna yakirata…

  “My darling kin kwanta ne?

   ” no kawai tacemasa…

    ” yace kinganne inata missing naki,Dama kina kusa dani..

   ” sai da safe ta katse wayar ta kasheta gaba daya..anya kuwa?

Da safe masu gyaran jiki suka fara zuwa kowacce aka fara yimata…

   ” kullum sai dady yakawo fruits da salad gidan mumy sunata gyara ‘ya’yan Nan kande tace zataje kauye dady yace tabari sai satin bikin…

    ” tun mukhtar ya kawomata kati take rarrabawa cikin kwaba 4 tagama yau akace su haruna zasu dawo gidan sai aiki akeyi…

   ” farida ce ta sakko tace yauwa sisters dinner farko shine zamu saka kaya iri daya, ta biyu kuma kowa yasa nasa…

    ” kande ce tace whynot musa duk iri daya?

     ” farida tace daidai ruwa dai dai tsaki…

    ●●●●

Muneeba ma yau english wears aka saka ta bazo da gashinta, office ta shiga ta samu haruna cikin sanyin murya tace harun yazanyi wannan?

     ” hucinta yakeji sannan ya daga kansa gaskiya tayi masa kyau…

     ” Murmushi tayi tace yadai? 

    ” Nothing! ya nuna mata Nan tafita ta huce office nata…

     ” agogo ya duba cikin hanzari ya huce airport…

    ” haneef ne yace wallahi da bakazo ba tafiya zanyi na barka!…
  
     ” haha ai nasan baza ka’iya bah…

●●●●

K’ande ce taci kwalliya tasaka blue din dogowar riga Amma in ta tuna wasu kalamai sai taja tsaki…

    ” Su mumy ne suka dinga yimasa sannu da zuwa nan suka gaggaisa sannan ya huce daki wanka sannan yayi sallah…

     ” kande tana zaune bakin gado firdausi ta shigo sister yaya yace bazai iya fitowa palour ba kikaimasa abinci…

   ” okay tace sannan ta mik’i har ta mik’i sai kuma tasa mayafinta…

    ” sallama tayi sannan ta turo kofar dak’in ina yini yaya?

     ” lafiya tunda ke baki damu dani ba sai yanzu kika shigo…

    ” ba haka bani ina…

         ” katseta yayi tare da dafata my aisha yakike?

     ” mikewa tayi tace an daura auren ne dakake dafani?

     ” tashi yayi ya nufo gabanta tana ja da baya sai da yakaita karshen bangon sannan yace wallahi ilove u dear please kiss me ko sai dayane…

    ” cikin hawaye tace dama kai dan iska ne ka yaudari ne? Hankada shi tafita dak’in aguje…

     ” bayan ta fita ya rungume pillow yace am in love with u, kwana4 nan jina nakeyi kamar shekarah hudu…

      
    Tun daga lokacin ta daina bari ma su hadu, yau ana gama yimata kunshi haruna yazo ya huce yaga kunshin yayi mata kyau firdausi ya kirawo…

    ” sister kije inji yaya haruna…

     ” kande ce tace me zanyi masa? Ke bazan zoba…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *