KOMAI NISAN JIFA CHAPTER 10
Washe gari Umma ta zaunar da Mubeenat tana gaya mata ra’ayin Farhan a kanta. “Dan yayi wa Abbanku magana,yanzu ke dama akwai wanda kike sone kodai babu?”
Cikin jin kunya tace “Babu Umma,amma dai ina so ad’an bani koda kwana biyu ne.”
“Ba damuwa kije kiyi tunani,amma ni senake ganin kamar kinyi babbar sa’a idan kika zab’i Farhan a matsayin miji dan Yaron akwai nitsuwa ga addini bayi da matsala sam gashi kuma na gida an san kowa nashi.”
“To Umma nagode” sannan ta mik’e ta fice.
Atif ne zaune a parlour Umma shida
Mubeenat “Ina jinki Sis Mubee gayamun”
“Ya Atif dama Ya Farhan ne yazo min da wani batu wai yana sona kuma da aure.”
Hannunta ya rik’o “Da gaske kikeyi? Indai gaskiyane to lallai na tayaki murna sis Mubeen,Farhan cikakken mutum ne wanda yasan yakamata gaskiya kinyi dace dan haka na amince dashi 100% kema kice kin amince kinji?”
Dad’i taji sosai “Da gaske kake Ya Atif?”
“Yes, i’m serious wlh ai samun miji irin Farhan abune mai wahala a rayuwarmu ta yau.”
Nan Atif ya fara tunanin wata rana daya cewa Farhan suje yawo mana danshi yana da wata budurwa duk randa buk’atarsa ya tashi to gurinta yake zuwa ta biya mishi buk’ata kaima idan kana so sena nema maka d’aya. Amma sam Farhan seya nuna mishi shifa ba irin wannan samarin yake ba,tun daga lokacinne alak’arsu tad’an ja baya sosai,yafi jin dad’in alak’arsa da Ahmad dan shima baya irin wannan harkar banzan wanda a zamanin yanzu da k’yar ne mace ta samu saurayi wanda kwata-kwata a rayuwarsa bai tab’a yin zinaba gaskiya yana wahala sosai,dan acikin kashi d’ari toda k’yar ne a samu kashi d’aya yana matuk’ar wuya sedai muci gaba da Addu’a Allah ya k’ara shiryar mana da Mazajenmu,Yayyunmu da kuma k’annemmu ameen.
Bayan Atif ya gama wannan tunaninne yayi ta yabawa Mubeenat Farhan sosai,dan haka taji dad’i tare dayi masa godiya.+
A islamiyya Farhan yana yiwa matan aure darasi acikin littafin *ZADUZ-ZAUZAINI* inda yake musu bayani akan ana auren mace dan abubuwa guda hud’u ne.
_Limaliha: dan dukiyarta_
_Walhasabiha: dan nasabarta_
_Wal jamaliha: dan kyanta_
_Wal diniha: dan addininta_
_Fasfar bizatitdeen: kurabauta da ma’abociyar addini._
Karatu yake musu dalla-dalla ta yadda zasu gane. Bayan ya gamane yake tambayarsu “Menene aure?”
Nan dai kowa ya fara bada amsa da cewa kafin ayi aure ana buk’atar abu hud’u
-Mata da miji
-Waliyai
-Sadaki
-Shaidu
Idan aka samu wa’innan to aure yayi Malam.
Shuru Farhan yayi kamar maiyin wani nazari sannan yace dasu “Eh to wannan ai kunmin bayanine akan d’aurin aure,amma me ake nufi da ita AURE?”
Nan kowa yake bada amsar shi da cewa Malam aure dai shine Sadaki don idan babu sadaki toba aure.
Murmushi Farhan yayi tare da cewa “Dukfa ajin nan zallan matan aure ne,amma ace babu wacce tasan ma’anar kalmar aure? Na yadda da amsoshinku,amma ba ita bace Kalmar aure ina zuwa.”
Nan ya fita ya shigo ajin su Mubeenat yace “A cikinku wacece zata gaya min me kalmar aure yake nufi?”
Kowa yanata bada irin amsar da ajin matan aure suka bayar. Farhan yace sam ba haka bane, dama Amal da Mubeenat basuyi magana ba,dan haka Amal ta mik’e tsaye tace “Malam na sani”
“Kin tabbata Amal?”
“Eh”
“To shikenan kibiyoni muje,idan kika dawo seki gayawa ‘yan ajin naku ma’anarsa”
“To Malam” sannan ya fice tana biye dashi a baya har suka shiga ajin matan auren.
Farhan ya kalli aji yace “To Amal,inaso ki gaya mana me ake nufi da aure?”
Kunya sosai taji,amma tasan babu kunya a wurin neman ilimi kuma na addini dan haka tayi magana ta yadda kowa zaiji.
“Aure yana nufin saduwar Mace dana Miji.”
Farhan ya tambayeta “Kin tabbata?”
“Eh Malam wannan itace kalmar aure a wana fahimtar.”
“Nagode Amal zaki iya komawa aji”
Bayan ta fitane ya kalli Aji “Wannan fa budurwa ce batama yi aurenba,amma ta fiku sanin menene aure,idan kuma kun sani kunyace ta hanaku fad’a inaga wannan ba hujja bace,dan babu kunya a wurin koyar addininka” nan dai yayita musu bayani har suka fahimta.
Bayan an tashine Farhan da Shureim suka wuce mota suna zaman jiran Mubeenat da Amal sakamakon wani Malami dake ajinsu.
Can ya hangosu suna fitowa dan haka yace da Shureim ya koma baya ya zauna.
Mubeenat ce ta zauna a gaba su Amal kuwa a baya.
“Ya Farhan kayi hak’uri Malamin Tauhid ne bai barmu mun fitoba wai se kowaccenmu tayi mishi bayani akan Sallah.”
“Kuma mun gaya mishi cewa Sallah Addu’a ce amma yace sam ba haka bane muje munemo mishi ma’anar sallah dan gobe kowacce seta bashi amsa daga waje kafin ta shigo aji.”
Murmushi yayi yana kallonta “Habibty bakisan me sallah ta k’unsa ba?”
Shuru tayi tare da sake kallonshi “Abinda Sallah ta k’unsa kuma?”
“Ahan,abinda sallah ta k’unsa shine ma’anar sallah ai”
Amal dake zaune a baya tace “Ya Farhan kayi mana bayani ta yadda zamu gane please?”
“Ok”
_Sallah wata ibada ce data k’unshi Karatu,Ruku’u da kuma Sujjada,ana farata da Kabbaran harama sannan a k’arasheta da Sallama”_
“Idan kuka gaya mishi haka zai barku ku shiga aji,wannan ita ce Sallah a nawa fahimtar.”
Murmushi sukayi tare da cewa “Mungode” sannan suka wuce gida.
Bayan isha ya kira wayar Mubeenat bugu d’aya ta d’auka “Hello”
“Habibty nasha gaya miki sallama ya kamata kiyi ba hello ba.”
Murmushi tayi “Sorry Ya Farhan slm”
“Wa’alaiku mus salam,ya kike to?”
“Lafiya lau,kaifa?”
“Ni?”
“Eh ina nufin kaima ya kake?”
“Hhh lfy ta k’alau amma sed’an wata damuwa da take damuna.”
Cikin d’aukin son jin damuwar shi tayi magana “Me kuma yake damunka Ya Farhan?”
“K’aunarki ne Habibty,zuciyata ta kasa samun sukuni dan rashin jin amsarki da bata yiba.”
Murmushi tayi “Ka sanar da zuciyarka data samu salama domin zuciyar Mubeenat takace kai d’aya tak”
Farhan baisan me zaice da itaba dan wani ni’ima ce yaji yana shigarsa ahankali.
“Alhamdulillah,Allah na gode maka daka sa Mubeenat ta amince dashi,Allah ka tabbatar mana da alkhairi Nida Ita”
“Ameen” suka amsa tare sannan yace “Habibty nagode sosai da amincewa dani da kikayi.”
Cikin jin kunya tayi magana a hankali “Nima na gode daka zab’eni a matsayin wanda kake so ta zama abokiyar rayuwarka,domin aganina nama fika sa’a a rayuwa.”
“Ana Hubbuki Habibty”
“Me kenan Ya Farhan?”
“I mean I love you”
Kunya taji dan batasan me zata ceba.
“Ke kuma seki ce min Ana Hubbuka Habibi”
Dariya sosai Mubeenat tayi “Hhhh ashe dai zan koyi larabci?”
“Sosaima daga yau indai ni dake ne toki kirani da Habibi zan iya jin wannan sunan a bakinki?”
“Habibi?” Ta tambaye shi cikin wata irin murya.
Murmushi yayi tare da cewa “Yeah gashi kinfi kowa iya kiran sunan kuwa.”
Hmmm! Wannan daren dai shine dare mai dad’i acikin rayuwarsu domin sunfi awa biyu suna hirarsu tare da farantawa junansu rai dukda dai ita Mubeenat tana jin kunyarsa idan ya mata wani maganar.
Haka sukaita zuba soyayyarsu tsawon wata uku ne kacal amma kowa yasan da batun soyayyarsu,dan a company da store duk Farhan ya sanar da mutane har gidan TV anyi hira dashi akan Company nasu daga k’arshen hiranne yake sanar da al’umma cewa ya samu matar aure dan haka a tayashi da addu’a. Suma ‘yan jaridan sunzo suji wacece haka,amma seya ce musu nan gaba kad’an zai gabatar musu da ita.
Iyayen suma Farin ciki sukayi sosai dangi gaba d’aya kowa yana murna da san barka amma banda Hajiya Kaka wanda ita burinta a duniya bai wuce taga Atif da Mubeenat sunyi aure ba. Hakan yasa sam bata farin cikin soyayyar Farhan da Mubeenat.
Tsawon wata bakwai kenan da fara soyayyar Farhan da Mubeenat wanda a yanzu kamar son da Mubeenat takeyiwa Farhan yayi yawa amma fa a nawa ganin. A ganin Farhan d’in kuwa soyayyarsa tafi na Mubeenat.
Wata rana Hajiya Kaka ta kirawo Atif tana gaya mishi burinta a duniya bai wuce taga ya auri Mubeenat ba “Taya ka bari Farhan ya wuce maka gaba bayan itama Mubeenat d’in tana sonka?”
Murmushi Atif yayi “Hajiya Kaka babu soyayya kamar yadda kuke tunani a tsakanina da Sis Mubee,shak’uwa ce kawai wlh niba sonta nake ba.”
“To idan ma ba sonta kakeba kaki gaggawan dasa soyayyarta a cikin zuciyarka Atif,ai idan kaine zaka aureta abin zaifi burgewa tunda kai yayantane kuma bazata k’ika ba dan ni wlh nasan tana k’aunarka.”
Atif yayi shuru yana nazarin maganar Hajiya Kaka da kuma wanda abokansa ‘yan k’wallo suka mishi akan ya akayi ya bari Farhan ya baiyanawa Mubeenat soyayyarsa?
“Atif kai kafi dacewa da auren mubeenat ba wani bare ba wlh,da nasan ba sonta kakeyiba wlh da tuntuni na shiga danna dad’e ina k’aunar Mubeenat amma yadda naga kun shak’u se nayi tunanin ko soyayyace a tsakaninku Atif kayi missing wlh…”
“Wai tunanin me kakeyine Atif?” Cewar Hajiya kaka.
Ajiyar zuciya yayi yace kaka bake kad’ai kika min wannan maganarba abokaina da dama sunmin wannan maganar amma lokaci ya k’ure Hajiya kaka kuma ina ganin Farhan shi yafi dacewa da auren Sis Mubee nasan zai kula min da Sweet sis fiye da yadda zan kula da itama dan gaskiya Hajiya Kaka Farhan ya fini da komai dan haka ina taya Sis Mubee murnan samun Farhan.”
Lokaci bai k’ureba inhar kana sonta kabar komai a hannuna kaji?”
“Me zaki iyayi akai Hajiya kaka,Abba ya riga daya basu kuma kinsan yadda yake da Abbin Farhan babu yadda za’ayi yace ya fasa sannan ita Sis Mubee tana matuk’ar k’aunar Farhan ta yadda bata jin kiran kowa a yanzu.”
“Tashi kaje Atif,kaidai kad’an ja baya da ita yanzu nasan ta yadda zan b’ullo mata.”
Shuru kawai Atif yayi tare da barin Hajiya kaka ya wuce gida inda yaga Farhan da Mubeenat suna hira a parlour’n Umma.
Cikin murna tace “Ya Atif sannu da dawowa”
“Yawwa” kawai ya furta tare da barin gurin.
Daga Mubeenat har Farhan sunga canji a gareshi dan haka jikinta yayi sanyi tace “Yau lfy naga Ya Atif haka?”
“Kodai akwai abunda yake damunsa ne ko kuma k’ila wanine ya b’ata mishi rai daga waje?” Cewar Farhan.
“Habibi idan bazaka damuba ina so inje muyi magana dashi”
“Bakomai Habibty dama nace miki fita zanyi,kije nima na fita sena dawo.”
“To Allah ya kare min kai” ta fad’a tana murmushi.
“Ameen” sannan ya fice tana biye dashi a baya har seda ya fice a gidan sannan ta wuce gun Atif ta shiga da sallama…”