KOMAI NISAN JIFA CHAPTER 12
What? Shi Atif d’in?”
“Eh wlh yanzu ta kirani pls kayi sauri ka tafi kar lokaci ya k’ure”
Cikin hanzari ya shige motarsa tare da barin gidan a 260.
Ita kuwa Mubeenat gudu takeyi suna zagaye gidan,tana bashi hak’uri amma sai dayayi nasanar kamota ya d’auketa cak sai d’akin su.
“Ya Atif lafiyan ka kuwa? Wlh bana so kasan halin da kake ciki so kake ka cutar dani ne? Kodai dama soyayyar k’arya ce kake min?”
“Ko d’aya Sis Mubee,bazan tab’a cutar dake ba har abada,amma kuma gaskiya bazan so in rasa kiba dan ina k’aunarki sosai Sis Mubee kema kuma kinsan hakan”
“Kaga Ya Atif kazo muje gida,baikama muci gaba da zama anan daga ni sai kai ba,sannan gaskiya ka fara bani tsoro.”
Mik’ewa tayi da niyan barin d’akin,amma sai ya janyota zuwa jikin shi yana son kissing nata da karfin shi.
Nan dai yafi k’arfinta dan haka har riganta yake k’ok’arin cirewa, dai-dai nan Farhan ya iso bakin gate d’in inda ya tsayar da motar shi daga waje ya nufi cikin gidan da sauri yana kiran sunanta “Sis Mubee!”
Daga ita har Atif d’in sunji muryar Farhan dan haka Atif yayi saurin sa key a kofan tare da cire key d’in yayi jifa dashi a cikin d’akin da suke.
Nanne hankalinta ya sake tashi sai kuka takeyi tana cewa “Ya Farhan dan Allah ka taimakeni yasa key a d’akin”
Nan Farhan ya koma motarsa ya d’auko wani key wanda ko wace irin k’ofa ce zai bud’eta dan daga madina ya taho dashi.
Atif ya rabata da riganta bra kake hangowa sai kuma dogon siket d’in jikinta na atamfa tana ta faman kokuwa dashi da dukkan k’arfinta duk da dai tasan k’arfinsu bazai zo d’aya ba.
Jin ana bud’e k’ofa ne yasa Atif saurin danne Mubeenat da dukkan k’arfinsa,ita kuwa kuka take fiye dana dah tana mishi magiya.
Hankad’owar k’ofa sukaji dukda hakan Atif bai fasa aikata abinda yayi niyan yiba.
Wani irin takaicine ya tokari Farhan har zuciyarsa baisan sanda yayi kan Atif ba ya hankad’a shi gefe tare da fara kai masa duka wane Ubansa.
Ita kuwa Mubee sauri tayi ta d’auki rigarta ta fice zuwa parlour,sai data kimtsa kanta sannan ta sake dawowa se fad’a sukeyi babu wasa sam a fuskar ko wannen su.
Mubeenat kuwa tama rasa me zatayi dan haka ta fara kuka tare dasa ihu kamar wanda wani abu ya sameta. Hakanne yasa Farhan barin Atif ya nufo Mubeenat a rud’e yana kiran sunanta tare da k’are mata kallo ganin ta zube a k’asa.
Sunkuyowa yayi yana kallonta tare dayin magana “Habibty are you okay?”
Jin sunan daya kirata dashi yasa ta bud’e ido tana murmushi tare da kai idonta gun Atif da yake shirin bugawa Farhan vas d’in flawer mai shegen nauyi. Jarumta tayi da dukkan k’arfin da Allah ya bata tayi sauri tashi zaune tare da hankad’a Farhan da k’arfinta ya fad’i a gefe sannan wannan vas d’in ya fashe a kanta nan ta fad’i sumammiya gefen kanta na fidda jini.
“Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un” Farhan da Atif suke furtawa a tare.
Nan suka nufota dukkansu kowa na kiranta inda shi Atif yake cewa “Sis Mubee i’m sorry”
Shi kuwa Farhan yana cewa “Habibty…”+
Nan haushi da takaici ya kama Atif dajin sunan daya kirata dashi,dan haka ya nufi Farhan da fad’a na gaske sosai.
Hmmm sai a yanzu ne Farhan ya nuna masa cewa shi yarone nan yayi masa duka alamu ya nunama ya karya masa k’afa dan ya kasa tashi sai ihu yakeyi yana saiya kashe Farhan.
A haka Farhan ya d’auki Mubeenat a hannushi bai tsaya ko inaba sai motar shi inda ya nufi asibiti da ita hankalinsa a tashe.
Tunaninsa na farko shine halinda Mubeenat take ciki,na biyu kuma mezai gayawa su Abba dan ya tabbata ya raunana Atif da gaske. Da wannaan tunanin ya kira Ahmad ya gaya masa komai ya kuma ce mishi yaje ya duba Atif.
Koda Ahmad yaje Atif ya kasa komai sai kukan takaici yake wai Farhan ya d’auki Mubeenat da hannayenshi kuma yana gani amma bai iya yin komai akai ba.
Nan Ahmad ya taimaka masa ya kaishi asibiti amma ba inda Farhan ya kai Mubeenat ba kamar yadda suka tsara shida Farhan d’in.
Anan aka tabbatar da cewa Atif ya samu karaya a k’afa.
Asibitin da aka kai Mubeenat kuwa Doctor ya d’an wanke gurin da spirit aka mata komai tare da tabbatar musu da cewa bakomai insha Allah karsu damu kansu.
Nanne hankanlin Farhan ya kwanta sannan ya kira Abba ya sanar dashi cewa suna asibiti da mubeenat.
Babu jimawa saiga Abba ya iso yana tambayar meya sameta?
Nan dai Farhan ya bashi labari cikin girmamawa bai b’oye masa komai ba.
Salati Abba ya shigayi tare da tambayar yanzu ina Atif d’in?
“Yana asibitin shima shida Ahmad”
“Dan Allah Abba kayi hak’uri ya k’urenine shiyasa”
“Abun baimin dad’iba Farhan,ban tab’a tunanin zaka biyewa Atif har kuyi doke doke ba”
Sunkuyar da kansa ya sake yi “Dan Allah Abba kayi hak’uri,insha Allah hakan bazai sake faruwa ba”
“Bakomai Farhan,Allah ya basu lafiya”
“Ameen Abba nagode”
“To bari naje can asibitin na duba Atif d’in,zan turo koda Umman tane saita zo ta zauna kaima ka huta”
“To Abba ai bakomai ma,inaga indai ta farka zasu sallamemu ma”
“To Allah ya kyauta”
“Ameen”
Bayan tafiyar Abba da kusan 30minit sai Mubeenat ta farka,har yanzu dai Farhan ne kawai agun yanata fama kallonta.
A hankali ta fara bud’e idonta tana kallonsa zaune yana yimata sannu.
“Kayi hak’uri Ya Farhan duk laifina ne har kukayi fad’a”
“Karki damu ai ya wuce,ya jikin naki?”
“Da sauk’i”
“Me yasa kika zab’i ki cutu akan ni?”
“Ya Farhan hakan shine irin kariyar da naketa burin in baka koda so d’ayane nima a rayuwata kamar yadda kayi min a baya da kuma yanzu,duk da dai nasan bazan iya biyanka abubuwan daka minba,amma inhar ina kusa da kai bazan tab’a bari a cutar dakai ba Ya Farhan”
Lips nashi ya lasa tare da kiran sunanta acikin wata irin murya mai cike da k’auna “Habibty thankyou”
“Na kuma godewa Allah daya tak’aita ya kare ki baki samu mummunan rauni ba,da bansan ya zanyiba Habibty”
Murmushi tayi tare da cewa “Ya Atif fa?”
“Shima yana asibitin”
“Asibiti kuma? Meya same shi?”
Mik’ewa Farhan yayi tare da shafar gashin kansa yace “Habibty na kasa hak’ura akan halin danaga kin shiga,zuciya ta d’ebeni harna raunana shi yana asibiti”
Tashi tayi zaune tana kallon sa cike da mamaki “Me kayi masa Ya Farhan?”
“Kiyi hak’uri Habibty,Atif ya samu karaya a k’afarsa a sanadiya ta”
“Haba Ya Farhan,kai da kanka kake fad’a min haka? Karfa ka manta da cewa shi Yayana ne,sannan duk abunda yakeyi ba’a sonshi bane damuwar da yake cikine ta haifar masa da hakan”
Kansa ya sake shafa tare da juya mata baya sannan ya sake juyowa yana kallonta har cikin ido itama kuma haka “Isbiri Habibty,ke kanki kinsan waye Farhan kinsan mezan iya yi kin kuma san me bazan iyayi ba,shaid’anne yayi nasara akaina wannan karon,amma ina tabbatar miki da cewa zanyi k’ok’arin kiyayewa insha Allah,musamman ma danaga ranki ya b’aci a yanzu” yana kaiwa nan ya fice daga d’akin ya barta a zaune kamar wanda ruwa ya daka…