KOMAI NISAN JIFA CHAPTER 2

 KOMAI NISAN JIFA CHAPTER 2

Murmushi atif ya tsayayi yayinda mubinat taketa faman juyi akan gado.

“Barkanki da farkawa gimbiyan mata”

Kunya sosai taji,dan gabad’aya tamance cewa ba’agidansu takeba yanzu. D’an murmushi tayi batare datace komaiba ta mik’e zuwa toilet. Byan fitowartane shima ya shiga yayi alwala yazo sukai sallah.

Abincin da umma takai musu hospital shiya d’auko musu yakawo sukaci tare sannan ya bata magungunanta tasha.

“Sis mubinat” yakira sunanta. “Na’am” ta furta tana kallonsa.

“Kizo ki zauna muyi magana” babu musu taje kusa dashi ta zauna tare da zuba mishi ido.

Fiskarsa cike da fara’a yace “inaso kigayamin abinda kike so da kuma wanda bakya so domin in kiyayesu musami  zaman lfy atsakaninmu”

Ajiyar zuciya tayi sannan tace “indai kamin alk’awarin cewa bazaka nemi wani abu daga gareniba bayan wanda ka nema d’azu toshikenan babu wata matsala”

“Kina nufin babu tarayyan aure tsakanina dake kenan”?

Shuru tayi ta kasa amsamishi. “Sis mubi,idan dai kinaga hakan daidaine toba komai,nayi alk’awari bazan kusancekiba harse randa kika fara ganina amatsayin mijinki”

Manyan idanunta ta d’ago tana kallonsa cikin tausayi dajin kunya tace ” dan Allah kayi hak’uri ya atif,kad’anmin hak’uri har zuwa… shiii kidena damuwa sis mubi nafahimceki,kuma zan jira harse lokacin da kika fara sona amatsayin miji ba yaya ba. Janyota yayi zuwa jikinshi ya rungumeta yana shafar bayanta tare da rad’a mata cewa “ina so wannan maganar yazama sirri atsakanina dake,sannan inaso kisaki jikinki dani kidena kunyana sannan bazaki hanani hugging nakiba hakama kuma kiss,kin amince da wannan”? Kai ta d’aga masa alaman eh ta amince tare da murmushi a fiskanta.

Shima murmushin ya mayar mata tare da tsunbatan goshinta yana jin dad’in ganin yadda ta sake dashi ayanzu. Cikin zuciyarsa kuwa cewa yake “ya Allah ka karkato da zuciyar mubinat zuwa gareni,Allah ka bani ikon cikamata wannan alk’awari dana d’auka mata ameen”

Bayan sallan isha atif ya tafi gidansu domin karb’a musu abinci,bai jimaba dan dama ya sanar da mum nashi cewa tayi musu abinci.

  Mubinat ta gama shirin bacci dan rigar bacci ne ajikinta amma bamai fitar da siffan jikintaba.

Jin k’aran motar atif ne yatabbatar mata da cewa ya dawo. Sallamarsa taji tare da shigowa ya bud’e mata hannayensa,cikin jin kunya ta mik’e taje ta shige jikinsa,shikuwa d’agata yayi sama tanata faman dariya tana cewa “pls ka saukeni ya atif nifa ba shureim bace” hhhh to ai da kad’an kika fishi,bazan saukekiba harse na kaiki kan daining. Dariya takeyi harya direta akan kujera,ita ta zuba musu abincin sukaci sannan tasha maganinta suka wuce d’akinta. Dama sunyi wanka dan haka brush kawai sukayi sannan suka kwanta cikin bargo d’aya kowa da tunanin da yakeyi cikin ransa.

Babu wani abu daya faru atsakaninsu illa kissing nata dayayi tare da mannata ajikinshi da haka sukai bacci.

Atif yana son kissing arayuwarsa,amma kuwa wannan alk’awari yada d’auka zai iya cikawa kenan?… hmmmm muje dai

Gari ya waye sukai sallah sannan suka koma bacci,cikin ikon Allah jikin mubinat yayi sauk’i sosai sedai muce Alhamdulillah…

Farhan kuwa yana can sararin samaniya inda jirginsu ta d’auki hanyarzuwa madina. Tafiya akeyi amma gabad’aya seyaji dama baiyi tfyanba,ya gwammaci yana nigeria koda lbrntane yadinga ji.

Koda suka isa bro nashi mai suna Abdullahi da kuma sauran ‘yan’uwansa maza biyu sukaje tararsa a airpot. Sunyi farincikin ganisa matuk’a tare da murnan memorinsa ya dawo normal yanzu babu wata matsala atattare dashi.

Cikin harshen larabci suketa magana sun rugumesa,murmushi yakeyi dan shima yayi kewarsu sosai. Haka suka d’au hanyar gida yayinda abdullahi yake jan motar.

Wata balarabiya ce kyakkyawar gaske ta fito sanye da doguwar riga irin tasu,ga wani murmushi na farin ciki da takeyi. Farhan naji ya furta “Ummi” tare da wani kalamai dayayi cikin harshe larabci suka rungume junansu tana kwalla tare da cewa “Alhamdulillah habibi” sauran kalaman nata dai cikin yarensune wato larabci,amma zaka iya fahimtar abinda take cewa dan yadda take kuka tare da furta sunan mubinat abakinta.

Hannunsa ta rik’o yana kwalla suka shige cikin gida wanda base na gayamuku irin tsarinsaba.

D’akinsa ya nufa ya watsa ruwa sannan ya fito aka zauna jera masa abinci kala kala amma kad’an yaci sannan aka shiga hira.

Dukdai hirar tasu akan mubinat ce,dan mahaifiyar tasa se hawaye takeyi tana rarrashinsa kamar sabon jariri. Koda yake dama larabawa akwai iya nunawa yaransu k’auna fiye da mazajensuma.

Fararen matane biyu suka shigo tare da rungume farhan suna magana cikin harcensu na larabci. Shi kuwa farhan murmushi yad’anyi ba laifi sannan suka zauna kusa dashi anata faman hira…

Mubinat ne zaune da amal da aisha se kuma shureim a palo suna hira. Amal tace “seku tashi mutafi ai tunda naga jikin nata da sauk’i”

“Nidai ba yanzu zan komaba” cewar shureim.

Amal tace “to aisha tashi mutafi dan wlh banso ya atif yadawo ya samemu” mik’ewa aisha tayi tace “to mubinat Allah ya sauwak’a se kuma kin sake ganinmu”

“Dan Allah kudinga zuwa kullum muna hira pls”

Amal tace “to shikenan semunzo gobe amarya mai magarnar sugar”. Tafawa sukayi ita da aisha suna mata dariya sannan aisha tace “yanzu shikenan mukuma semuyita yawon zuwa gidanki dan bamu da gurin zuwa,ai wlh kafin ki sake ganin k’afarmu agidannan zai dad’e”

Kallonsu mubinat ta tsayayi tare da harara “hakama zakucemin ko”?

“Mayar da wuk’an aminiyata,kinsan koda aisha zatak’i zuwa tofa nikam zaki ganni wlh” murmushi mubinat tayi tace tona gode kugaidasu umma. “Tashi mutafi shureim” cewar aisha.

“A’a wlh kubarshi idan ya atif yazo zaimaidashi” inji mubinat. To ai shikenan suka had’a baki,tare da zuwa gun motarsu inda driver’n su aisha yake jiransu.

Bayan tfyarsune shureim yakeyiwa sis mubinat hira yana cewa “sis mubi ya farhan ma bayida lfy d’azu abbansa yakegayawa abba wai ciwon kai yakeyi sosai”Kuma dama yace min in kawo masa hotunanki,guda biyar ya d’auka acikin kits nashi yacemin idan kina kuka indinga share miki hawaye sannan ince miki ki zauna da ya atif da zuciya d’aya kuma kiyi masa biyayya dan bayaso kizama d’aya daga cikin wanda ake azabtarwa ranan gobe.”

Tunda shureim ya fara magana mubinat take zubar da kwalla harya gama. Hannunsa ta kamo tace “yaushe ya gaya maka wad’annan maganganun?”

“Jiya da dare daya kira wayar umma shine yace abani mugaisa”

Ajiyar zuciya tayi tace “nagode shureim,kace mishi naji sak’onshi” hon d’in motar atif suka jiyo,da sauri ta goge kwallanta dan bata so yasan tayi kuka. Shureim ya fita da sauri yace “dama kainake jira kamaidani gida”

“Amma ai zaka bari inshiga in sanar da sis mubinat tunda bataga shigowanaba”

“To barina tayaka shigar da kayan kafin ka fito”

Kansa atif ya shafa yace “yawwa tona gode” sannan ya wuce da ledan hannunsa ciki.

Sayayyan drinks ne sosai atif yayi dakuma abinda basu dashi. Tas shureim ya shigar zuwa store sannan ya dawo palo ya zauna yana jiran atif.

Rungume yake da ita yace”bari in maida shureim kar dare yayi kina son wani abune”?

“A’a seka dawo”

“Are you sure”?

“Uhm”

“Ok tose na dawo” tare da manna mata kiss a lips nata sunayiwa juna murmushi yafita.

Bayan ta tabbatar da sun tafine ta bud’e wayanta da suka taho mata dashi tana kallon hotunan ya farhan habibinta. Musaman wanda yake bata hak’uri lokacin da shureim ya goge mata komai na wayanta tace seta dakeshi,hakan yasan farhan had’a hannayensa guri d’aya yana bata hak’uri akan karta dasheshi sanye da bak’in shets ajikinsa. Ganin yayi mata kyaune alokacin yasa tayi mishi wannan hoton.

Koda ta dawo daga duniyar tunani seta sake fashewa da kuka tana cewa “Allah yabaka lfy ya farhan…”Bayan Atif ya dawone yake gayawa Mubinat cewa ta shirya dan gobe zasu wuce abuja. Marairaicewa tayi tace “gobe kuma,mezamuje muyi acan d’in?”

“Hutawa mana sis mubinat,kinsan fa ni angone ina so muje yawone kinji?”

Kallonsa tayi cikin shagwab’a “pls mubari se wani sati kagafa ko gurinsu mum bamujeba kuma ina so ind’an k’ara samun lfy kafin muyi tfy pls Ya atif.”

  Ganin yadda take mishi shagwab’ane yasa ya amince da cewa “Ok naji,but wani satin bazan sake k’arb’an wani escuse nakiba agree?”

“Yes no”

“Hhhh” yayi dariya tare da rungumeta yace you don’t stard ba?”

“Hahah nop I’m just kidding you” tare da rungumesa tana tuna farhan…

Haka dai rayuwarsu taci gaba da kasancewa babu wani damuwa.  Alk’awarinsu yananan kamar dai yadda suka amincewa junansu.

Ta hakanne mubinat take moransa sosai,ga wani sabon k’aunarta dayake shigansa fiye dana da.

  Aduk lokacin data buk’aci yin magana da Ya farhan Sam baya Janata,hakan yasa tasake dashi sosai dama kuma can akwai k’auna atsakaninsu.

Duk cikin yayyunta tafi son Ya atif kodon gida d’aya suke zama oho.

Yanzu kam da kanta take musu girki kala kala masu dad’i,daga ita harshi sun fara kyan gani dan hankalinsu akwance yake.

Ta b’angaren farhan kuwa sauk’in shine mahaifiyarsa,yana matuk’ar son mahaifiyar saboda k’auna da take nuna masa. Cikin ikon Allah ya fara samun sauk’i,amma k’aunar da yakeyiwa Sis mubinat yananan acikin zuciyarsa wanda shikam se’a hankali zai fita.

  Ganin kamar ya fara mancewa da itane yasa wan mahaifiyarsa yayi masa magana akan wata yarinya acan d’in kozai aureta.

“Farhan baya iya b’oye abu kokuma wani nuk’u-nuk’u,dan haka ya gayawa uncle nasa cewa gaskya hakan bazaiyuba amishi hak’uri.”

Tun daga wannan rana babu wanda yasake mishi magana akan aure…

Can gida Nigeria kuwa su Atif yau suke hangar tafiya abuja.

Dake flight sukabi basu sha wahalan hanyaba. Abokansa dake canne d’aya daga cikinsu wato Nazir,shiyaje ya d’aukosu yakaisu d’aya daga cikin gidajensa da babu kowa aciki yakaisu.

Shidai Nazir sana’an gidaje yakeyi da kuma bada haya,dan shinema ya hana Atif sauka a hotel.

Gidane flat hud’u acikinsa,ukun da mutane aciki,d’ayan kuma babu kowa dama sabbin gidajene. Atif yace tofa guy ka kama k’asafa,murmushi yayi tare da cewa “aiban kaikaba ango suna dariya tare da shigewa ciki.

Komai dai Sabone aciki, kuma awadace 2bedroom ne se parlour da raining dakuma kichine.

Nazir bai zaunaba yace”barinaje gida zamu taho da sweetheart dan girki na musamman tayi muku wlh.”

Bayan tafiyarsane Atif ya shiga musu da kayansu sannan ya rik’o hannunta tare da fiskantarta yace “gurin ya miki,kodai mutafi hotel?”

Murmushi cike da fiskanta tace “yayi,kuma kaga ga mutane agidan zan samu k’awayen hira.”

“Are you sure’bana so kitakura jus tell me the truth” yana shafar firkarta

“I’m serious wlh nan d’in yayi thankyou, ta rungumesa”

Dad’in hakan yaji ya d’agata sama zuwa d’akinsu tana dariya. Akan gado ya direta sannan tace bari nayi wanka,murmushi yayi yace to idan kin fito Nima sena shiga.

Nazir ne da matarsa da kuma ‘yarsu d’aya mai suna Kismat. Idan ka gansu atare dole su burgeka,ga kyakkyawar babynsu kismat ‘yar kimanin shekaru biyar.

Hira sosai sukayi cikin hara dajin dad’i har 3:00pm kafin sukai sallama suka tafi.

Bayan isha Nazir da abokinsa sukazo da Mota biyu,d’ayan sun kawowa Atif ne dan zaga gari shida Mubinat sannan suka koma a d’ayan.

Haka sukaci gabada zama a abuja har tsawon sati d’aya,sunyi yawo sosai ga kuma matan abokan Atif Sunada kirki sosai. Hakan yasa suka shak’u kamar sunyi shekaru tare.

Suma matan da suke zaune a gida d’aya da mubinat d’in suna da kirki sosai ba laifi,Soyayya sosai sukeyi da mazajensu Dan dukkansu amarene.

Hakan yasa wani lokaci Atif yake sa damuwa aransa. Dan wani soyayyanma agabansu akeyi akan idanunsu wanda hakan baisa ya karya alk’awarin dayayiwa mubinat ba,sedai wani lokaci yana tsintar kanshi cikin tunani ko kuma ince damuwa.

Wata rana mubinat tayi wanka cikin english wears riga da wando,rigar hannu d’ayane kawai gata ja. Kyau sosai tayi yayinda tayi parking gashinta a tsakiyar kai.

Tunda Atif yadawo idanunsa na kanta ya kasa d’auke kai,ahankali yabita kichine inda take yanka musu fruit tana wak’an *Umar m sharif* abakinta.

West nata ya rik’o yayinda ta razana sosai dan batasan yashigo kichine d’inba. Bayan ya juyo da itane suna kallon junansu wanda hakan yasa taji tsoronsa dan duk kamanninsa ya sauya idanunsa sun k’ank’ance

Magana yake cikin murya mai kashe jiki yanacewa

“You look beautiful in this dress”

Cikin rawan murya tace “thanks”

“What’s is going on sis mubinat,I won’t do anything I promise okay”

“Silent”

“Why are you quite, say something”

“Please stop it Ya atif” ta furta daidai lokacin da yake neman wuce gona da iri.

Mubinat bataga alaman zai bariba dan haka ta tureshi gefe da k’arfi tana hawaye “pls stop it”

Ajiyar zuciya ya sauk’e amma sam baiji dad’in hakanba acikin ranshi, baice da ita komaiba yabar kichine d’in. Da Sauri ta biyo bayanshi danta lura da yanayinsa na rashin jin dad’in abinda tayi mishi. Yana zaune a parlour rufe da idanunsa ta k’arasa gurin ta zauna kusa dashi tare da sunkuyar da kanta k’asa tace “i’m sorry”

“Silent”

Kanta ta d’ago tana kallonsa cikin nadama ta sake cewa “Ya atif i’m sorry please”tare da rik’o yatsun hannunsa tana wasa dasu.

Hannunsa ya janye tare da mik’ewa ya wuce d’aki batare dayace mata komaiba. Jiki sanyaye tabi bayanshi tana zubar da kwalla.

Kayan jikinsa yake cirewa,gabansa taje ta tsaya tana share kwalla sannan ta sake cewa “Ya atif i’m sorry tsorone ya kamani shiyasa nayi haka…”Tsoro fa kikace,wani irin tsoro kenan sis mubunat,i am your husband yakama kisa hakan aranki kidena guduna pls it’s really hurt  can’t you understand!”

“And ki duba irin shigar da kikayi yanzu,kuma kina expecting inyi ignoring d’inki?”

“Kina ganin kinmin adallaci kenan sis mubinat?”

“Nifa mutum ne d’an Adam mai lafiya ajikinshi kika kafa min dokanki nakuma amince miki amma kuma shine zaki tayarmin da hankali kuma kice zan iya jurewa kinaga bakiso kanki sosaiba sis mubinat?”

Tunda ya fara magana take kuka dan yadda taga ranshi ya b’aci yana magana cikin fushi harse daya gama sannan tace “kayi hak’uri dan Allah bazan sakeba” kota kanta baibiba ya wuce d’ayan d’akin ya kwanta abinsa rai ab’ace.

Koda mubinat tabi bayansa amma setaji k’ofar arufe. Bugawa take tana cewa “pls open the door Ya atif I don’t mean to hurt you wlh bazan sakeba pls karkayi fushi dani.”

“Ya atif please open the door”

“Just leave me along sis mubi”

“Please stop saying that, hakan yana nufin kayi fushi danine kenan?”

“Banyi fushiba kawai ina son kasancewa ni kad’aine”

“Dan Allah karkamin haka Ya atif kazo muje mu kwanta,kasan kariga daka sabar min yin bacci tare dakai i’m sorry please…

Atif yana jiyo kukanta da kuma kalamanta amma sam yak’i bud’ewa saboda abinda tamishi yamishi zafi sosai. Yana matsayin mijinta amma babu hali yayi wani abu,atunaninsa Mubinat ta fara sakewa dashi ya d’auka zai sami damar kusantarta ayanzu amma ashe sam ba yadda yake tunanibane.

“Me take nufi kenan wai,mema nayi mata ayanzun dahar zatace ta tsorata dani?”

Shikad’i yake zancen zuci batare daya furta komai afili ba. Muryarta ya jiyo tana cewa “Haba ya Atif dan Allah ka bud’emin”

“Sis Mubinat kije ki kwanta ina buk’atan kad’aicewa ni d’ayane a halin yanzu”

“Please Ya Atif kayi hak’uri kaji?”

“Naji kije kicire kayan jikinki kisa wani ina zuwa”

Bamusu ta wuce taje tasa kayan bacci wanda baya nuna komai na jikinta sannan ta zauna akan gado tana jiran zuwansa. Wayantane ya soma ringing,tana share k’walla ta d’auka da sauri ganin Ya Farhanne ke kiranta.

“Assalamu alaikum” ta furta cikin muryan kukan.

“Wa’alaikumus salam sis Mubinat lfy naji muryanki wani iri haka?”

Dai-daita kanta tayi sannan tace “lafiya k’alau yasu Ummi da Abdullahi?”

“They are all fine,how is Atif?”

Nanne ta fashe da kuka ta kasa cewa komai se kuka. Hankalin Farhan ya tashi yayi magana cikin sanyin murya “Sis Mubinat are you okay?”

“Yes i’m fine”

“Then why are you craying?”

“Ya Atif ne” dai-dai nan Atif ya bud’e kofar ya nufo k’ofarta,jin abinda Mubinat take cewane yasa ya tsaya sauraro. Taci gabada cewa Farhan “Ya atif ne yake fushi dani dan Allah kabashi hak’uri Ya Farhan banaso Allah yayi fushi dani acikin wannan daren.”

Shuru Farhan yayi yana nazarin kalamanta sannan yace “Shikenan kishare hawayenki kidena kuka pls,i will talk to him kinji?”

“Thankyou Ya Farhan,i’m missing you so much…”

“Shhhhh,komai zai dai-daita kidena damuwa please.”

  Koda Farhan ya ajiye wayan seyaji ba dad’i aransa yadda yaji tana kuka sannan ya tuna da kalamanta na k’arshe datake cewa “i’m missing you so much Ya Farhan.”

   Tashi yayi zaune ya rasa meke mishi dad’i, wayansa ya d’auka ya kira number’n Atif amma akashe. Runtse idanunsa yayi yana zancen zuci

  “Tome yake faruwa tsakaninsu,duk yadda akayi akwai wani abu” number’n Atif ya sake kira karo na biyu kuwa seya shiga, “Alhamdulillah” ya furta tare da jiran Atif ya d’auka.

Shikuwa Atif tuni ya koma can d’akin ya kunna wayansa,ganin kiran Farhan ne seya d’auka,dan yasan idan ya sanar da Farhan abinda yake faruwa tofa lallai zaiyiwa Mubina nasiha akan hakan sosai,dan haka ya d’auka tare da cewa “hello”

Bayan sun gaisane Farhan yake tambayarsa meke faruwa tsakaninka da Sis Mubinat dantacemin kana fushi da ita pls inyi maka magana kayi hak’uri.”

“Karka damu komai ya wuce insha Allah,mund’an samu sab’anine but komai ya dai-daita nagode.”

Farhan yayi shuru nad’an wani lokaci sannan yace “toshikenan Allah yabaku zaman lafiya da kuma hak’uri da juna”

“Ameen” cewar Atif sannan sukai sallama.

Komeyasa Atif ya fasa gayawa Farhan abinda ke faruwa oho…

Tana kwance yayi sallama,zunb’ur ta tashi zaune tana kallonsa. Kusa da ita ya zauna tare da janyota jikinsa yace”Wato shine kika fad’awa Farhan ko?”

“Hakan shikad’aine mafita agareni Ya Atif,amma kayi hak’uri bazan sakeba”

“Hakan ya nuna duk lokacin da muka samu sab’ani zaki gaya mishi kenan?”

“Bazan sakeba” ta fad’a kanta asunkuye.

Hannunsa yasa yarik’o fiskarta sannan yace “Please karki sake gayamishi komai a zamantakewarmu dake kinji?”

“Ban tab’a gayamishi komaiba se yau,insha Allah bazan sakeba”

Murmushi yayi yace “promise?”

Kai ta d’aga mishi tana murmushi tace “yes”

Rungumeta yayi yace “i’m sorry dasaki kuka danayi yanzu”

Yatsanta tasa akan lips nashi “shhh, kadena bani kak’uri aikai zanba hak’uri nima bazan sakeba”

Dad’i yaji sosai dan sam Mubinat bata da girmankai indai wajen baiwa mutum hak’urine. Bakaman wasu matanba,dasuke ganin baiwa miji hak’uri asarace atasu fahimtar na jahilci dan wannan jahilcine babba wlh,Allah ya shiryar damu yasa mu gyara ameen…

Haka sukaci gaba da zamansu babu wani matsala dasuke samu. Sedai har yau babu wani abu na auratayya daya shiga tsakaninsu. Kuma ayanzu ita kanta Mubinat tana son tasan menene dad’in auren amma kuma tsorone cike aranta, domin suna hira sosai da mak’waptanta akan mazajensu.

Hakan yasa tabawa Atif daman wasada jikinta koda zata dena jin tsoronsa. Dad’in hakan yaji sosai tun wani rana datace mishi k’irjinta yana ciwo, tambayarta yayi ta ina kikejin ciwon?

Hannunsa takai dai-dai tsakiyar bubs nata tana yawo dashi tare da cemishi “kaga daga nan har nan har tananma duk ciwo yakemin” yayinda take yawo da hannayensa akan bubs nata.

Gogan naku aise ya rikice yana lumshe idanu tare da cewa “sorry” yana matsesu ahankali.

Ita kanta taji dad’in hakan sosai dan lumshe idanunta tayi tana jin yadda yake mata.

Tunfa wannan ranan yasamu daman wasa da k’irjinta cikin sauk’i,azuciyarsa kuwa cewa yayi “saura can…”

_Hmmmm! Mekuke hangowane readers? Muje zuwa dai_

Wasa-wasa su Atif watansu guda kenan a abuja,aurensu kuwa wata d’aya da sati d’aya kenan.

Dukkansu sunji dad’in zamansu a abuja sosai,amma Mubinat tana kewar gida sosai. Gashi Atif yace sesun k’ara sati biyu kafin su koma,hakan yasa ta hak’ura ta amince masa.

Ana sauran sati d’aya su koma Atif suka fita da wani abokinsa mai suna Hamza wanda bayi da aure.

Bayan sun gama zaga garine yace da Atif muje club mana. Atif yace “wato kai har yanzu baka shiryuba ko? Nidai nabar muku gaskiya kuyita fama.”

“Hhhh muje to ka rakani ba jimawa zanyiba wlh” cewar Hamza. Atif baice komaiba suka d’auki hanyan club,tunkafin su isa ‘yanmata suke layi akan titi kowacce da irin adonta. Daga nesa kake hango surarsu mai d’auke hankali dan akwai kyawawa sosai gasu farare tas.

Atif se binsu da kallo yake d’aya bayan d’aya,yana k’yallara idonsa akan wata yace “kai kaga wata anan” hhhh hamza yayi dariya “komu tsayane?”

Tsaki Atif yayi yace “wannan aiseku dabaku da mata.”

Parking hamza yayi yace “toka jirani acikin mota ango,bazan wuce 30minit ba shap-shap zanyi infito dan already tana jirana acikine.”

Kai Atif ya d’aga mishi sannan ya wuce ciki,shikuwa Atif yana zaune acikin mota.

Kyakkyawar yarinyace fara k’irjinnan nata abud’e gasu aciccike tana tsaye ajikin motan tana bugawa ahankali.

Atif ya sauke glass tare da cewa “ya dai?”

Marairaicewa tayi tace “kud’inane sukai short kuma gashi dare yayi please can you help me?”

Hannu yasa a aljihunsa yaciro 2k yamik’a mata batare dayace komaiba.

  Ganin bayida niyan kulatane yasa ta sake matsowa dab da motar sannan ta k’arb’i kud’in da hannunta biyu tareda rik’e hannusa ta shafashi akan bubs nata.

Atake Atif ya rikice yakai idonsa gunda hannunsa yake aiseya lumshe ido. Ita kuwa ganin halinda yake cikine yasa ta zura hannunta tacikin glass d’in zuwa kan wandosa…

  😔Allah ya dad’a karemana mazajenmu ameen…..

Duk wani wuta dayake jikin Atif sedaya d’auke cak. Ita kuwa se wani murmushi take mishi tana kashe mishi ido d’aya. Hannunsa yasa ya bud’e mata k’ofar baya ta wuce ciki sannan tajanyo k’ofar.
Mazauninsa ya canja daga gaba zuwa baya batare da b’ata lokaciba Atif ya rabata da kayan dake jikinta tare da taimakon ita yarinyar nan take suka fara aika-aika acikin mota.
“Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un,Allah kayi mana katanga da irin wad’annan shaid’anun matan ameen.”
Duk wani nau’i na farin ciki wannan yarinyar seda ta nunawa Atif,saboda taji dad’i sosai har cikin ranta wanda hakan yasa ta rik’eshi tsam ajikinta tak’i sakeshi.
Shikuwa gudun kar Hamza yazo ya tatdasu ahakanne yasa ya k’waci kansa tare da maida suturarsa dama ba dukka ya cireba ita yarinyarce dai ta cire komai na jikinta.
Bayan ta kimtsane lokacin ya koma mazauninsa can gaba seyace da ita “kiyi sauri kifita ga wannan bana so abokina yazo ya tarar dake acikin motarnan.”
Dubu biyar ya bata,tasa hannu ta karb’a tare dayin godiya sannan ta fice tana murmushi.
Harta fara tafiya se kuma ta dawo tace”kozan samu number’n wayanka,dan gaskiya zanso mu sake mu’amala irin ta yau”
Atif da hankalinsa yake tashe yace” badamuwa kibani naki number’n zan nemeki inhar buk’atan hakan ta taso”
Cikin rawan jiki ta cire paper a jakarta ta rubuta ta mik’amishi sannan ta tafi.
“Innalillahi wa inna ilaihir raji’un” shine abinda bakin Atif yake furtawa tare da cewa “wannan wace irin masiface haka take shirin faruwa dani? meka aikata hakane Atif meyasa kayi hakan bayan ga Sis Mubinat naka agida?”
  Wad’annan tambayoyi yaketa jerowa kansa yayinda yaketa dana sanin abinda ya aikata.
Tsawon ninti goma kenan sega Hamza ya dawo yana murmushi yace “sorry for keepping you so long muje ko?”
Shuru Atif yayi sannan yace “muje” cikin sanyin murya.
“Yadai ango koharka fara yin baccine?”
Murmushi Atif yayi tare da cewa “please muje, and kuma kayi sauri.”
Bamusu Hamza ya d’auki hanyar gidansu nanya ajiyeshi sukai sallama sannan ya wuce.
Tunda sukazo abuja Atif bai tab’ayin dare a waje shi kad’aiba sedai idan tare suka fita da Mubinat koda sauran abokansa da matansu.
Hakan yasa Mubinat tad’an damu dan har 11:24pm seta kwanta a parlour tana jiran isowarsa.
Ai kuwa setaji yana nocking tare da cewa “Sis Mubi”
Da sauri ta mik’e ta nufi k’ofan tare da b’udewa,ai kuwa seta tsaya turus tare da had’a rai tace “meyasa kajima haka Ya Atif?”
Cikin fargaba ya rufe k’ofan sannan ya juyo ya rungumeta yace “nasan nayi laifi i’m sorry Sis Mubi hakan bazai sake faruwa insha Allah” yana rungume da ita.
“To amma meyasa ka dad’e haka yau,waima ina kajene haka?”
“Na raka Hamza abokina hirane,yakaini danmu gaisa da matar da zai aura acan muka b’ata lokaci wlh please kidena fushi dani kinji?”
“Aiba fushi nake dakaiba,kawai dai naga baka tab’a dad’ewa irin yau bane shiyasa na damu,but bakomai muje dan bacci nakeji tun d’azu amma na gagarayi.”
“I’m sorry my Sister bazan sakeba,kinyafemin?”
“Yafewa kuma?”
“Yes,kina jin bacci nahanakiyi ai dole in nemi gafararki”
“Hhh dama aini banrik’eka azuciyaba Ya Atif”
“I know,nidai kice kinyafemin” ya had’a hannayensa biyu agu d’aya.
Murmushi Mubinat tayi sannan tace “nayafe maka to shikenan?”
“Yes,thankyou so much” ya fad’a yana murmushi tare da d’agata cak se d’aki ya direta akan gado.
Peak ta manna mishi akunnensa tace ” i love you” tana dariya.
Kamar daga sama yaji kalman akunnensa sannan ya juyo gareta yace “what?” Cikin mamaki
“Kallonsa take cike dajin dad’i tace “yes i love you Ya Atif”
Dad’i yaji har cikin ransa seya rungumeta yace “i love you more Sis Mubinat,inama da ace wannan kalmar da kika furta yana nufin kina sonane amatsayin mijinki ba Yayankiba,danafi kowa farin ciki yau aduniya.”
Shuru tayi dajin kalamansa tare da sunkuyar dakanta kasa.
Furkarta ya d’ago yace “karki damu hakanma naji dad’insa sosai har cikin raina,bari naje na watsa ruwa.”
Tana ganinshi ya cire kayan jikinsa dagashi se shorts nashi ya wuce toilet.
Mik’ewa tayi ta kwashi kayan zuwa mazauninsu sannan tadawo ta kwanta. Zancen zuci tashigayi “Ya Atif nayi k’ok’arin dasa soyayyarka acikin zuciyata amma dai still amatsayin Ya Atif nake ganinka akoda yaushe.”
Atif seda yayi wankan janaba sannan yayi wanka ya fito ya sameta ta tsunduma ciki tunani.
Ruwan fiskarsa ya watso mata wanda hakan shiyadawo da ita daga tunanin data tsunduma cikinsa.
Murmushi tayi tare da k’are masa kallo,Atif ya had’u kota ina,wanda ta tuna da irin ‘yanmatan dake bibiyansa har gida gashi da farin jini dake shi d’in d’an k’wallo ne… “Sis Mubinat is everything okay?” Ya tambayeta
“Yeah, I’m fine” tafad’a tana murmushi
“No i don’t believe you” ya fad’a tare da zama kusa da ita ya mannata da jikinshi inda ta jingina dashi tare da lumshe idanunta tace ” I’m fine”
Peack ya mata a wuyanta yace “are you sure?”
“Uhum” tace dashi cikin sanyin murya,shikuwa ya kasa fahimtarta dan haka yayi shuru tare da sake mannata dajikinshi sosai yana shak’ar kamshin dake jikinta…
Tun daga wannan ranan bai sake fita batare da Sis Mubinat ba.
Ita kuwa wannan ‘yar iskan tayita zuba ido domin ganin kiran Atif ko zuwansa amma sam babu kod’aya. Hakan yasa ta damu sosai ita adole takamu da sonshi.
Yanzu watansu d’aya da sati biyu harma da kwana uku agarin abuja. Yau suka shirya suka dawo gidansu.
Mubinat se murna takeyi yau gata ga Ummanta ga kuma Shureim dan gidansu direct suka sauka kamar yadda ta nemi hakan agun Atif kuma ya amince mata.
Umma taji dad’in ganin ‘yarta danta k’ara haske sosai sedai sam batayi jikiba.
Shureim yace “Sis Mubi Ya Farhan ma zai dawo nanda sati d’aya”
“Da gaske kake?”
“Eh bakwa wayane?”
“Gaskya mun kwana biyu”
“Tomeyasa Sis Mubinat?”
kanshi ta shafa tace “saboda Ya Atif baya so muna yawan magana dashi shiyasa,inaga yana zargine shiyasa kawai nima nadena kiransa.”
“To Sis Mubi dama shi Ya Farhan d’in baya kirankine seke?”
“Uhm gaskya bai tab’a kiranaba nine nake kiransa,ranar dai nayi mishi gorin baya kirana shinefa ya kirani sau d’aya kuma tun daga rananma bamu sakeyin maganaba har yau sedai kawai Ya Atif yacemin Ya Farhan na gaisheni.”
   Shuru shureim yayi yace “to Sis Amal bata da lafiya kwananta biyu a kwance zazzab’i da mura yake damunta”
“Subhanalillah, kwana biyu ina kiran wayanta akashe wlh” mik’ewa tayi taredasa takalmi Shureim yayi saurin cewa “ina zakije Sis Mubi?”
“Zanje duba Amal”
“Sis Mubi baki tambayi Ya Atif bafa,a islamiyya an gayamana cewa duk matar auren data fita batare da izinin mijintaba to tsinuwar Allah da Mala’ikunsane kebinta har taje ta dawo.”
Jikin Mubinat yayi sanyi sosai dajin kalaman shureim k’aninta d’an shekara goma sha uku… tsayuwar mutum taji abayanta,tana juyowa sukayi ido hud’u da Atif.
Sunkuyar da kanta tayi,dan tasan yafahimci cewa fita zatayi.
“Ina zakije?” Ya tambayeta
“Gidansu Amal” ta bashi amsa cike dajin kunya
“Toki gaisheta,kuma 4pm zamu tafi gida.”
Da sauri ta d’ago kai suna kallon juna tayi magana cikin sanyin murya “haba Ya Atif bamunyi dakai se bayan isha ba?”
Gwalo yayi mata tare da cewa “nafasa”
K’afafunta ta buga ak’asa tare da zunb’uro baki “ni wlh ban yaddaba”
dariya yayi tare da wuceta ya kamo hannun Shureim yace “dan Allah bakaga tayi muni ba Shureim?”
Shureim yayi dariya hhhh sannan yace “tayi kam.”
  Itama dariyan suka bata sannan tabi shureim wai zata dakeshi,aikuwa se Atif ya d’agashi sama suka fara zagaye gidan da gudu suna mata dariya😄… nima dai maman shureim natayasu dariyan,kufa readers?
Mubinat ce zaune da Amal suna hira. Ita kuwa yadinkon Amal tana tsaye tana sauraron dukkanin hiransu batare dasun saniba.
Amal tace “Amma fa kinyi kyau sosai kodai mun samu baby ne?”
Wani irin bahagon kallo Mubinat ta jefeta dashi tare da cewa “Bana son wulak’anci yaushe akai auren dahar zaku samu baby? Ke nifa gaskya babu abinda ya tab’a shiga tsakaninmu.”
Amal ta tashi zaune “Me kikace Mubinat,amma dai daga gurinkine dan nasan halinki”
“Hmmm towai dan Allah ku har zakuyi zaton wani abu anan kusa? Kowa shaidane akan bana son Ya Atif dan haka baikama kuyi tunanin abu makamancin hakaba a tsakaninmu tunda shi kansa yasan hakan.”
“To amma dai Mubinat ai yanzu kam ya kamata ace kinyi hak’uri tunda ya zama mijinki,kuma ki sani wlh Allah zai kamaki muddin kika hanashi hakkinsa… “Dan Allah ya isa haka malama Amal,ni dubaki dajiki nazoyi kuma naganki Allah ya k’ara sauki” ta mik’e daniyan tafiya se Amal tace “Oo danna gaya miki gaskya shine zaki tafi ko? To shikenan ameen nagode kigaida gida”
“Kina nufin bazaki rakaniba kenan?”
“Wani irin rakiya kuma keda bakya so agayamiki gaskya,wai Mubinat yaushe kika zama hakane?”
Murmushi Mubinat tayi “Yaushe na zama haka kamar yaya? Bazan iya sauraran maganganunkibane kawai.”
“Wlh kin canja tunda kika rasa Ya Farhan gabad’aya halaiyarki suka canja,sam bakyajin magana yanzu wlh,Allah ya kyauta nidai na gayamiki gaskya Ya Atif yana da hakki mai girma akanki garama ki ajiye komai agefe kibashi hakkinsa kodon samun rahamar Allah atattare dake.
“To naji na kuma gode semunyi waya” daidai nan yadikkon Amal tabarsu zuwa d’akinta.
Koda mubinat ta shigo gida tunanin kalaman Amal kawai takeyi wanda gaskiya Amal tagaya mata,dalilin dayasa Mubinat take k’aunar Amal sosai kenan,komai d’acin da zakaji tofa lallai seta gayamata gaskiya,haka ake son k’awa tagari ta kasance da fad’an gaskiya…+
Mubinat bata samu kowa a palon Umma ba,kuma taga motar Ya Atif acikin gida,wanda hakan ya tabbatar mata da cewa Atif ya dawo kenan.
Parlour’n Abba ta wuce kai tsaye,duk suna can suna hira inda shureim yake kwance aciyar Atif.
  “Slm,sannu Abba” cewar Mubinat.
“Yawwa sannu mamana kindawo,ya jikin Amal d’in?”
“Da sauk’i sosai”
“To alhamdulillah”
“Dama yanzu nake cewa shureim yaje ya kiraki kutafi”
Sunkuyar dakanta tayi batare datace komaiba.
Umma ce tace “Sekije ki d’auko muku abincinku kutafi dashi.”
“Toh” tace tare da ficewa daga parlour’n.
Sam bata son tabar gidansu,amma yazama dole,haka ta d’auko hand bag nata tare da wayanta da kuma abincin ta fito.
Abba da Umma ne suke biye da Atif hargun mota,inda shureim ya karb’i abincin yak’arasa dashi mota sannan suka wuce.
Tunda suka fara tafiya babu wanda yayi magana har kusa kai tsawon minti biyu sannan Atif yace “Wato shine kikabar wayanki a gida ko?”
“Banyi tunanin zaka kirabane that why”
Hannunta ya kamo da d’ayan hannun nashi yana murzasu ahankali batare dayace komaiba.
Jin shurun yayi yawane seya kira sunanta “Sis Mubi lafiya naji kinyi shuru?”
“Banso tafiya bane kuma Abba yace mutafi”
“To amma ai dama bamuyi dake cewa zamu kwanaba”
“Nasan hakan,kawai dai gidanne bai isheniba”
Shuru yayi nad’an wani lokaci sannan yace “Tokiyi hak’uri,wani sati zan kawoki da safe kizo ki yini hakan yamiki?”
“Da gaske kake?”
“Yeah”
“Nagode sosai” tana jin dad’i acikin ranta dayake tasan kafinnan lokacin Ya Farhan yadawo.
  Bayan sun isa gida seda sukai wanka sannan sukaci abinci se bacci.
Tunda ta kwanta take tuno hiransu da Amal amma ina, batajin zata iya baiwa Atif kanta ayanzu sedai wani lokacin.
Shikuwa yana manne da ita yana mata wasanni da hakan sukai bacci…
Yau take ranan laraba, kuma yaune Ya farhan zai shigo gari. Bacci sosai Mubinat takeyi yayinda Atif yaketa wasa da gashin kanta.
Mik’a tayi tare dayin magana cikin muryan bacci “Please Ya Atif kabarn”
“No, tashi zakiyi kinmanta yaune zamuje yini gida?”
Furgit ta tashi “Are you serious?”
“Yes,kinsan yaunema Farhan zai dawo so gara mucika gidan kamar yadda muke ada”
Rungumeshi tayi cikin farin ciki tare da fad’in “I love you Ya Atif”
“I love you too Sis Mubi,sannan suka fara tsunbatar junansu. Sun jima ahakan sannan ya janye lips nashi ahankali yayinda take rufe da idanunta tana lashe lips nata da harshenta.
Sam tak’i bud’e idanunta,ganin hakan yasa Atif sake kai lips nashi kan nata suka sake sabon shafi.
Hmmm abun nasu babu sauk’i sam,tun suna zaune har suka koma suka kwanta. Ita kanta Mubinat abun mamaki ya bata saboda sam bata so Atif ya saki lips nata,wanda lokuta da dama itace ke fara janye jikinta daga nashi.
Ganin yadda Mubinat ta saki jikine yau Atif ya samu daman sarrafata yadda yakeso,azuciyarsa yace Allah ya d’aurani akanki yau dadare zan gwada neman hakkina agareki Sis Mubinat.
Idanunta ta bud’e tana kallonsa cike dajin kunya,da wuri ta kare fiskanta da hannayenta tana murmushi.
“Yadai Sis Mubi?” Ya tambayeta yana cire hanunta daga fiskanta.
Mik’ewa tayi zuwa toilet tana dariya tare da kallonsa. Shima toilet d’in ya nufa amma seta sa key. “Ni kikawa haka ko? Zamu had’u anjuma ai” ya furta sannan ya wuce d’akinsa don shiryawa shima.
Anko galila ash colour sukayi wanda yasha aiki mai kyau sosai. Mubinat riga da skeet ne,shi kuwa tazarce sunyi matuk’ar kyau fiye da tunani sannan suka kama hanya.
  Hira sukeyi cike daban sha’awa har suka isa gida. Shureim yanata murnan zuwansu da kuma na dawowar Ya Farhan d’insa.
Dama tea da bread sukasha kawai agida,dan haka sukaci abincin Umma sannan suka zauna hira.
10:20am Mubinat tacewa Atif zataje ta taya Umma aiki,hakan yasa yace da ita zaije gun friends nashi kafin isowar su Farhan.
Hira sosai Umma takeyi da ‘yarta tana maijin dad’i aranta,danta lura yanzu kamar babu wata damuwa atattare da Mubinat,addu’a tayi acikin ranta na Allah ya basu zaman lafiya yasa ta mance da Farhan  gabad’aya tunda taga babu wata matsala kuma Atif ma bai tab’a cewa komaiba koda Abba yake tambayarsa ranan seyace wlh babu wata matsala suna zaman lafiya.
Umma ta gama komai cikin sauri dake itada Mubinat sukai aikin. Hakan yasa suka wuce yin sallan azahar,ai kuwa se suka jiyo horn.
Da gudu Shureim ya fita yana “Oyoyo Ya Farhan”
Muryan Farhan taji yana cewa “Ooh my Shureim,I missed you so much”
Dariyan Shureim take jiyowa da muryan Ahmad yana cewa “To shureim shikenan hankalinka ya kwanta ko?”
“Sosaima Ya Ahmad,idan kaga dama karka sake zuwa dubani yanzukam tunda Ya Farhan d’ina ya dawo.”
Muryan dariyansu takeji dai-dai nan ta idar da sallan tana murmushin itama. Da hijabin ajikinta ta fito,sukuwa sun shigo parlour’n tare da sallama.
“Wa’alaikumus salam,Ya Farhan sanu da dawowa” ta furta yayinda sukeyiwa junansu kallon kewa. “Yawwa Sis Mubi nasameku lfy?”
“Lafiya lau yakabaro su Ummi?”
“Alhamdulillah lafiyansu k’alau suna gaisheku” yafad’a yana mai kallon yadda ta k’ara haske.
Gaisuwar da takeyiwa Ahmad ne yasa ta katsewa Farhan tunaninsa. Umma ce ta fito,nanma aka sake gaisawa sannan suka wuce sides d’insu Farhan danya watsa ruwa. Seda suka isa sannan Farhan ya tuna da cewa bai karb’i key d’in d’akinsaba gun Umma,gashi su Shureim sunje mota kwaso kayansa,hakan yasa yayi niyan komata gun Umman kawai seka Mubinat rik’e da key d’in Umma ta aikota.
Kallon juna suka tsayayi sannan ta mik’a mishi tace “Wai inji Umma tamance bata baka key ba”
Hannunsa yasa ya karb’a yace “Nagode”
Juyawa tayi ta koma, yana tsaye yana binta da kallo azuciyarsa kuma yace “Ooh habibty, I miss you” duk akan idon Atif…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *