KUSKURE NA CHAPTER A

 KUSKURE NA CHAPTER A

_HALL_ d’in cike yake damk’am da da mutane, ko ina ka kalla al’umma ne zazzaune da alamun ba’a fara gabatar da occasion d’inba.

   _Nima a dai_dai lokacin nasamu isowa k’ofar babban d’akin taron, agogon dake hannuna na duba 7:25 am, hakan ya tabbatarmin saura 5 minutes afara gabatar da occasion d’in, wani security ne ya dakatar dani dacewa “madam can i see your get pass ” ? Ina k’ok’arin manna siririn glasses a ido na d’ago na kalli security nace ” I don’t have a get pass but i am from *Muslim Sisters Organization  of nigeria (m.s.o)* na k’arasa fad’ar haka ina me nunamasa wata sheda dake manne ajikin mayafin danayi roling kaina dashi ,  cikin kulawa securityn yace” you highly welcome madam  please your name before you enter and your phone number and email address if available” ?  okay RAMLERT Y SALIS is my name my no is  081…… , thank you ya fad’a sannan na doshi k’ofar shiga hall d’in kafin na k’arasa k’ofar ta bud’e ina shiga ta koma ta rufe_

 Babban d’akin tarone ya tsaru iya tsaruwa hall d’in babbane na gaban kwatance, wannan shine karona na farko dana ta6a halartar  _Transcorp Hilton Hotel_  duk iya tunanina baza’a samu wajen taro me kyau da tsari haka a nigeria ba ammah dana tuna _Transcorp Hilton_ shine babban hotel a duk nigeria sai na dena mamaki but the place is interesting is nice place.

 Kowa ka gani acikin hall d’in yayi shiga irin ta Alfarma wayancin mutanan danake kallo sunsa too expensive clothes hakan ya tabbatarmin _the occasion is noble and significant_,  mutanen dake d’akin taron sun had’a da manya_manya ‘yan siyasa matansu da maza ma aikatan gidan radio da TV ga manyan ‘yan jaridu da sauran manyan mutane ,   waje nasamu na zauna banfi mintuna 2 da zama ba sautin speaker ya fara tashi.

  _AYANZU NE NIKUMA MARUBUCIYARKI ZAN FARA KAWO MUKU RAHOTO, HAR IZUWA K’ARSHEN LITTAFINA NA *KUSKURENA* ASHA KARATU LPY_

Matashi ne baxai wuce shekaru 35 ba sanye yake cikin black court, daganinsa kaga wanda ya gama jika acikin hutu a hankali yake magana cikin speaker d’in.

       “Assalamu Alaikum Warahamatullahi Wabarakatuhu, muna k’ara godewa Allah da ni’imarsa har ya kawomu wannan rana me tarin daraja da tarihi, Aminci ya k’ara tabbata ga Annabi (s a w)da dukkan iyalansa da sahabbansa da dukkan wanda ya bada gaskiya da ranar lahira ameen,  godiya ta musamman game girma _Governor_ da muk’arrabansa , ‘yan majalissu da mutananu, Abonka aiki da sauran al’ummar dasukaxo dan tayamu murna”.

 Sai yayi shuru na d’an wani lokaci sannan ya d’ora dacewa”At the first place _JAFAR MUHD_ is my name I am the best friend of groom _SAFRAZ  HASHIM MUHD_, We are waiting for our groom and his bride along side with his _first lady_ keep waiting please.

Rufe bakinsa keda wuya, hayaniya ta d’an fara shigowa hall d’in daga wata k’ofa dake can watakusurwa a hall d’in hakan ya tabbatar ango yasamu isowa tare da amarya da kuma first lady kamar yadda jafar ya fad’a.

Baka ganin komai sai haske cemara dake ta haskawa nanfa masu video suka fara aikinsu da masu hotuna da ‘yan jaridu da sauransu.

Su uku suka jero sun sashi a tsakiya, daka ganshi zaka tabbatar shine angon kallo d’aya zaka masa kace balarabe ne haduwa kam ya gama ya k’are kamar shi yayi kansa dan kyau _SAFRAZ_ yana da tsayi ammah ba can sosai ba ba siriri bane kuma bashi da jiki fari ne tas yana da manyan danuwa da dogon hanci da  k’aramin baki, sajensa ya kwanta a fuskarsa tamkar gashin jararin da aka haifa yau se jajayen la6ensa dasuma dace da fuskarsa,  let stop describing ,  nasan me karatu you already visualize,  to  see  him in your eyes mind.

 Amarya ce a gefensa na hagu tayi shiga cikin tsadaddun kaya sai walkiya takeyi, siririyace tana da tsaya medium, chocolate colour ce sai dai daganin fatanta ta gaki da hutu da jin dad’i,  tana da doguwar fuska da matsakaicin hanci da baki medium eyes fuskarta tasha kwalliya, Sai wacce ke gefensa na dama da alamun matarsa ce domin yana sak’ale da hannunta kallo d’aya zaka mata kaga tayima masifar kyau, kwarjini, da burgewa, mace ce ajin farko ko mace ‘yar ‘uwarta idan ta kalleta sai ta k’ara balle kuma ace namiji , komai nata idan ka kalla zai burgeka farace ammah ba fari irin tas ba dan mijin ta ya fita fari , ba siririya bace kuma bata da k’iba tana da dara_daran idanuwa da dogon hanci bakinta d’an dai_dai le6enta bak’ine sai gashi daya kwanta a gaban goshinta tanada diri sosai.

 Inda aka tanada dan zaman ango da amarya nansuka nufa, ammah sai dai kujeru guda buyune awajen na alfarma ganin hk yasa _IZZATU_ ta fara kwace hannunta dg hannun mijin nata dan tasan kujeru biyun data gani nashine shida amaryarsa babu ita a lissafin, shima safraz ya gane abinda matar tasa izzatu take nufi ammah sai yayi kamar be fahimta ba yakuma rik’e hannunta sosai ta yadda bazata iya kwacewa ba.

    Sam ranta baiso ta karasa wurin zaman ba ammah hk ta bisu suka isa ga mazaunin nasu, Amarya _KARIMA_ inda aka tanada dan ita tasamu ta zauna zuciyata a cunkushe ranta sai tafasa yakeyi ganin yadda safraz yake wani mannewa matarsa kuma wai agurin shagalin bikinta bata k’ara jin 6acin raiba sai data ga safraz yana tayiwa izzatu magiya dan Allah ta zauna itakuma izzatu ganin yadda ya marairaice mt kuma gashi people duk su suke kallo sai ta zauna ammah ba dan ranta yasoba tana zama kuwa shima ya zauna karima jitayi kamar tasa hannu aka tayi ihu ganin sun zauna a kujera d’aya wanda ango kawai aka tanadarwa.

  Ina !anan hall d’in ya d’auka wasu na dariya da shewa wasu kuwa ransu a 6ace suna ganin abinda angon yayi bai daceba.

Jafar da yake shine minister of the occasion yana dg inda yake yana kallonsu ko kad’an abokinnasa bai bashi aushinba saima burgesa da yayi, sai da hall d’in ya lafa sannan jafar ya fara mgn kamar hk” Alhamdulillahi kamar yadda muka riga muka gani ango da amarya sun iso tare da first lady ayanxu ne km zamu fr gabatar da wannan taro namu God willing, so, batare da 6ata lokaci our first presenter itace hajiya km malama izzatu wato first lady uwargida awajen ango,  idan me girma uwargida ga ango ta shirya muna sauraronta”

Cikin mamaki izzatu take sauraron abinda jafar yake cewa, safraz ta kalla sannan tace” Besty why do that to me ?ni mezance idan na tashi ?hb besty nasan wannan plan d’in duk naka ne u have nothing to say ni gaskiya” ta karasa maganar kamar zatayi kwalla, murmushi safraz yayi sannan yace” hb reality don’t say that pls kina da abinda fad’amana sosai i am your one and only pa inason kije ki tabbatarwa jama’an dake hall d’innan bawai mijinki ya k’ara aure bane dan by sonki ke har yanxu sabuwace a gurinsa sauran mt suyi koyi dake my queen ” ya k’arasa mgnr yana d’anyin dariya izzatu dataji ya fr irin wad’annan zancen nasa sai ta galla ms harara ta mik’e a hankali  ta fara tafiya, karima da tn jin duk abinda suke cewa ta ta6e baki duk haushi ya isheta.

Taku takeyi cikin nutsuwa fuskarta d’auke da fara’a  kowa ya maida hankalinsa kanta wasu na mamaki ganin yadda fuskarta ta nuna kamar tana cikin farinciki sosai batayi kama da wacce akeyi kishiya ba.

 Tana isa wajen jafar ya bata abin mgn shima yasamu waje ya zauna, sai data dai_dai ta tsayuwarta sannan ta fr mgn kamar hk-

‘Alhamdulillahi ala kulli halin, I am Izzatu Abubakar the wife of safraz hashim muhd groom of today, okay before i begin let me greet you like am suppose to do so may peace be upon you, Ina yiwa dukkan  bak’inmu barka da zuwa muna godiya sosai da sosai dan zuwa tayamu murna a wannan rana me,matukar daraja  ’ sai tayi shuru na d’an wani lokaci sannan tacigaba da cewa-

 ” ‘Y ar fad’akarwar da zanyi zuwa ga amarya zanyi, 1  _Kiji tsoron Allah a zamanta kewarku Allah zai sanya miki mafita a dukkan lamuranki._!

2 _Aure ibadane kisani cewa zaki iya ji ko ganin abinda rai baya so, don hk kiyi hakuri sai ki sami aljannarki cikin sauki.!_

3 _Hak’uri da juriya, rayuwar aure bata wata d’aya bace ko shekara d’aya ko goma ba, rayuwace ta har abada sai da hakuri da juriya.!_

4 _Miji shugabane a gareki, dan hk duk abinda yake buk’ata akowane lokaci dole ki aikatashi muddin ba sa6on Allah bane._!

5 _Nisantar abinda miji yake k’i, dukkan abinda mijinki bayaso ki nisanceshi domin yawan sa6awa miji zai jawo miki tsana._!

6 _Yin abinda miji yakeso, ki kula da da dukkan abinda mijinki yakeso, ki aikatashi koda zaki wahala wajen aikatawa domin wannan shi zaisa mijinki ya k’ara sonki da k’aunarki, kuma ki sani aljannarki tn k’ark’ashin duga_dugan mijinki, ma’ana yin biyayya agaresa zai shigar dake aljannah.!_

7 _Yin taka tsan_tsan da shawarwarin k’awaye, ki kula da dukkan shawara da ko wacce k’awa zt baki, ki za6i mace mai ilimi kuma ma’abociya addini a matsayin abokiyar shawararki.!_

8  _Rik’e sirrinki, kada ki dinga yadda wani yana sanin sirrinki tsakaninki da mijinki koda kuwa ‘yan’uwankine.!_

9 _Kyautata zamantakewaki da ‘yan’uwan mijinki kiyi iya k’ok’arinki dan ganin kin kyautatawa  iyayensa, yayyensa k’anansa, da sauran  danginsa.!_

10 _Gaskiya da rik’on amana , kiyiwa zamantakewarki ado da yin gaskiyaduk abinda zakiyi kiyi gaskiya km ki rik’e  amanar mijinki.!_”

_HALL_ d’inne ya d’au tafi wasu kuma suna kabbara, izzatu ta burge mt da sama a wajen harma da mazan gurin shikuma safraz sai murmushi yakeyi ganin yadda jama’a ke jinjinawa matarsa amarya karima kuwa jikinta yayi sanyi sosai ganin babu wanda yata6a yimata nasiha ta gaskiya km me ratsa jiki irin izzatu wai kuma kishiyartace sai taji ta burgeta sosai ammah sai wani 6arin na zuciyarta ya ce mt ay kawai izzatu ty hkne dan kawai ta burge mutane ayi zaton ko dan Allah tayi.

 Sai da hall d’in ya d’an saurara sannan izzatu tacigaba dacewa –

” Yake amarya ki bud’e kunnanki sosai ki jini  ki kiyaye wad’annan Abubuwan da zan fadamiki su yanxu guda goma domin suna daga cikin _SUNNONIN AURE_ Idan har kika kiyaye su zaki zm ‘yar auta agurin mijinki‘’

_NA D’AYA_………

~Sannu _sannu kwana nesa muje zuwa page na 2 yau da gobe bata bar komai ba~👌🏻NA D’AYA :

Sanya tozali wato (kwalli).

NA BIYU:

 Yin kunshi.

NA UKU:

 Daina nuna yawan kish i, (domin mabud’in rabuwane).

NA HUD’U :

Daina mita, surutu,zaigi, ko naci.

NA BIYAR :

Yin ta’ammali da ruwa, (wato tsabta).

NA SHIDDA:

 Gano abinda zai faranta ran mijinki a yayin dayake cikin fushi.

NA BAKWAI:

 Kawar da kai akan laifin da yayi miki.

NA TAKWAS:

 Barin yin mgn lokacin da miji yake cikin fishi.

NA TARA :

Ban da dukan miji, ki zama mai biyayya a garesa.

NA GOMA:

 Kamewa dg kai koke_koke zuwaga iyaye ko k’awaye tare da barin d’aga murya sama da tashi.

D’akin taron rud’ewa yayi da hayaniya kowa yana fad’in albarkacin bakinsa, sai da komai ya lafa sannan izzatu tacigaba da cewa:

“Rayuwar aure tana buk’atar abubuwa da dama wanda ko rabi ban lissapa ba, ammah komai yana samuwane a lokacin da matar gd ta zama mai ilimi da wayewa domin ilimi shine jigon komai a rayuwa” . shuru tayi nad’an wani lokaci sannan tacigaba da cewa:

Ilimi shine darajar mace

Shine asalin ‘ya ko wace

Don shike hanata ta lalace

Kuma ilimi shike d’aukaka ‘ya mace.

Ba sanya tufafi tsadaddu ba

Ba d’aura atamfa super ba

Ba zinari dasu fashion ba

Ba shak’e kabot da kiristal ba

Rozis ba alfahari ne ba.

Faharin ‘ya mace kyawun tarbiyarta

Da kula da kiyaye mutuncinta

Da biyan dokar addininta

Haka nan kyawunta d’abi’arta

Ta kwarai ba kyawun fuskaba

Sanin addinine wayewa

Badan kin girma a birni ba.

Wannan karon ma wasu na kabbara wasu na tafi, kowa ka gani fuskarsa d’auke da murmushi musamman safraz da sai washe hak’ora yakeyi.

Izzatu tacigaba da cewa, ” Bari na tak’aita jawabina anan, ina,fata amarya ta fa’idantu,da dukkan abubuwan dana fad’amata,dama dukkan sauran mata baki d’aya, Alhamdullilah Allah yasa abinda na fad’a yazama hujja agareni ba hujja a kainaba , subhanakallamu ashhadu Allah ilaha illah anta astagfuka wa’atubu alaik”. Cikin nutsuwa ta fara takunta dan ta bar gurin.

  Safraz cikin hanzari ya taso ya iso inda izzatu  take suka jera suna taku d’aya bayan d’aya, Nan da nanhall d’in ya d’au tafi izzatu ta burge,kusan ko wacce mace har mazan dake gurin ammah sai dai wasu matan suna matuk’ar mamakinta gnin ko ajikinta bata damu da auren da mijinta zaiyiba, wasu mazan km na al’ajabi suna raya cewa idan dasu keda izzatu babu wt mace da zata burgesu balle suyi tunanin k’arin aure.

 To, haka aka ringa d’auki ba dad’i, muhawara ta barke a tsakanin people dake hall d’in, Nima dai RAMLERT kaina yaso ya d’aure ammah burina kawai ng antashi dg event d’in dan nasamu na isa ga first lady izzatu dan zanso inji labarin ta dan yadda nake gani har tafi mijin nt farinciki a bikin.

An gabatar da manya malamai sunyi fad’akar mai matuk’ar amfani taron yayi gwanin ban sha’awa ya burgewa kowa, Anci ansha delicious food dan save yourself ne kowa yaci abubuwan dayake so an raba gift masu kyau da tsada , sannan taro ya tashi lpy+1, kowa yafi da farinciki da annishawa.

 Ina tsaye a premises hotel d’in ina jiran ng fitowar su izzatu sai da kusan kowa ya watse sannan na hango fitowar su kusan su biyar.

Ta gabana suka zo zasu wuce sai alokacin na kula ashe amarya ce kawai da ita da tawagarta dagani abinne bai musu dad’iba shiyasa suka taso amaryasu agaba.

Ba’ada’au wani lokaci ba ng safraz da izzatu tare da jafar da wata mata tana d’auke da baby dagani kasan iyalan jafar ne  dukkan su sun nufa inda nake dayake ina tsaye a wajen parking lot ne,  sai da sukazo dai_dai dani zasu wuce sannan namu sallama.

Wa’alaikassalam, izzatu ta amsamin.

‘yar’uwa idan babu damuwa inasonyin mgn dake, na fad’a ina kallon izzatu.

Tana murmushi ta cemin, babu wt damuwa ina sauraronki.

A dai_dai lokacin jafar da matarsa suka iso gurin muna gaisawa suka wuce shima safraz yabi bayansu yarage dagani sai izzatu.

Izzatu ce ta fr cemin, ni kuwa sis like i realize your face, kamar RAMLERT Y SALIS ko?

Cikin mamaki nake kallon izzatu ganin ta kira sunana, nace eh! but how come ?

Dariya ta saki sosai tace wonderful ashe idona ba k’arya yayi ba, lallai Ramlert wato har kin manta IZZATU A .A ko?

Wai meke faruwa ne ?na ware ido ina k’ara kallon izzatu sai alokacin na gane dawa nake mgn my lovely friend since at secondary shchooling.

  Am i dreaming or are my eyes deceiving me this face look like that of IZZAT A.A   Na fad’a ina matuk’ar farinciki mukayi hugging juna.

Yes it’s me , RAMLERT Y SALIS izzatu ta fad’a.

Munyi matuk’ar farinciki sosai domin izzatu classmate d’inace a secondry school munyi abota da aminci tun bayan graduated bamu k’ara ganin juna ba domin ni ina kano itakuma tana Abuja, sai gashi yau cikin ikon Allah mun had’u.

 Izzatu tace, Ramlert nayi farincikin had’uwarmu gaskiya, ya bayan rabuwa shekaru da dama.

Nace, i am glad to see you too!komai Alhamdullilah but you vanished without a trice.

Izzatu tace, ba hk bane sis kinsan lokacin da mukayi graduated from secondary acikin mu babu wacce ake bari ta rik’e waya duk shine matsalan ba number gashi bama gari d’aya ammah yanxu we will start !, ta k’arasa mgnr tana dariya.

Nace maganarki gaskiya ne A .A  but akwai abubuwan danake son sani sosai ammah baxaiyiwu now ba.

Y salis zaki fara tambayoyin naki kenan ko a school hk kike kamar wata journalist. cewar izzatu.

Dukkan mu mukayi dariya.

Izzatu tace, gobene d’aurin auren mijina kinga yau akayi banquet (waleema)ko?

Nace, Eh! ai shine tambayen nawa sis ina mamaki na duk da cewa ba abun mamaki bane.

Izzatu tace, a gobe za’a d’aura auren sannan agobe amaryar zata wuce england domin cigaba da karatunta ammah one week zt dawo tana yin jarabawar k’arshene domin ta kammala degree d’inta.

To!ikon Allah, ammah meyasa baza’a jira ta kammala ba before ayi bikin?

Dariya izzatu tayi sannan tacemin kiban address d’inki sis zamuyi mgn.

Munyi exchanged na phone number da address sannan mukayi sallama akan cewa duk wanda ya samu dama zai  ziyarci  d’an’uwansa.

 ******

*****

****

***

**

**

*

AFTER 6 DAYS

Sis Ramlert dan Allah muje ki kammala cin abincin sai na baki labarin dalla2, cewar izzatu tana k’kok’arin jan hannuna zuwa deining table.

Nace, izzatu wallahi ni na k’agune ba lallai in iya cin wani abuba dama bari kikayi sai mungama, na k’arasa maganar ina marairaice fuskar.

Dole izzatu ta hakura muka koma falo muka zauna.

Izzatu na kallah nace sis ina saurarenki, kuma dan Allah karkiji kunyar fayyacemin komai ba wai ina nufin ki fad’amin sirrinki bane a’a, kamar yadda mukayi a school hk nake son yanxu karki 6oye min.

Izzatu ta nisa sannan tace, Hb Ramlert koda bama tare kina zuciyana banajin zan 6oyemiki wani abu daya danganceni a yanzu sabida ina da tabbacin ke k’awace me gaskiya da rok’on amana, wallahi ina cikin damuwa igiyar aure tana rawa takeyi kodai tayi rauni ko ta tsinke cikin biyu d’aya zai iya faruwa, mijina yana sona fiye da tunanin me tunani  ammah anyi mana katanga ni dashi watanmu biyu da Aure ni da shi a yanzu hk ya d’au son duniya ya d’oramin har zuwa yanxu babu wt mace da zata kaini a zuciyarsa ammah jin dad’in rayuwar aure babu shi acikin rayuwar mu nidashi  kuma dukkan abubuwan dake faruwa KUSKURENA,  izzatu ta k’arasa fad’ar hk hawaye nabin fuskarta.

Jikina ne yayi sanyi jin kalaman izzatu, maganganunta sun d’auremin kai, tears rolling down in her checks har zuwa lokacin, cikin sanyin jiki na kalleta nace, sis pls come down wipe your eyes pls bansan me kikeji a rankiba ammah ki d’aure kidena zubar da hawayenki BAYAN WUYA SAI DAD’I dukkan tsanani yana tare da sauk’i.

Murmushin k’arfin hali tayi sannan tace, thank for your encourage this is my friend tamin alamar jinjinawa, dukkan mu mukayi murmushi.

Izzatu tacigaba dacewa, idan bakayi aure ba ace bakayiba idan km kayi sai matsala!alokacin daka dad’e agidanku bakayi aureba sai anayima kallon d’an isaka bayan kayi aure yadace ayima wani kallo ?ki dubw mijina namijine ra’ayin ko wace ‘ya mace bashi da matsalar komai me zaisa wani namiji ya burgeni ya wadatani da komai na more rayuwa ammah sis mijina ya d’aukeni mazinaciya fasik’a mecin amanar aure.

Sannu_sannu kwana nesa muje zuwa page 3 yau da gobe batabar komai ba👌🏻Wani  shocked jikina yayi na ware ido ina kallo izzatu wacce itama ni take kallo, na razana da jin abinda ta fad’a taya hkn zata faru bayan yadda safraz ke nuna son izzatu a gaban kowa.

Izzatu tace, kamar yadda kika sani munyi graduated on 2008, na fr university on 2009  ina shekaran k’arshe befi saura two month na kammala degree ba muka had’u da safraz , Aranar naje _B U K_old side, naje domin wani program da za’a gabatar a ranar domin ni a _B U K_ new side, nake attending lecture department d’inmu na Islamic studies a _B U K_new side yake idan kinga na shiga old side to ko zanje wani program da za’a gabatar a can, to aranar ma hkne domin najene wani program _GLOBAL MONEY WEEK_ wato satin kud’i na duniya, a ranar Allah yayi had’uwata da safraz.

Byan an kammala program ina cikin,tafiya tun kafin na fito dg _B U K_ sai mota ta talalace nayi duk iya k’ok’arina motan yak’i tashi ga yamma tana k’arayi ga babu me gyaran mota akusa da waje mutane kad’an kad’anne ma suke wucewa ta gurin, Ina cikin tunanin yadda zanyi sai ga wata mota tazo ta wuce har tayi nisa sai kuma ta dawo da by, Jafar ne ya bud’e motan ya fito ya iso inda nake yana murmushi, sallama yamin na amsa sannan yace,  Can i help you ng kamar your car has broke down,

Nace, hkne zan samu me gyara kuwa a nan ciki?

jafar yace, bazaki samu me gyara ba sai dai idan kin ft waje but you will suffer before you get, if there’s no problem kuzo mu rage miki hanya idan yaso gobe sai kizo da me gyaran sabida yanxu dare yayi i am sure ba wanda zai ta6a miki motanki ko?ya k’arasa maganar yana d’aga mata giransa.

 Hk akayi izzatu motan su jafar ta shiga ta bar tata monta a nan, koda ta shiga safraz ta gani a zaune a matuk’in driver sai da suka fita get sannan jafar ya juyo ya kalli izzatu yace, hajiya wace unguwa ce ?

Izzatu tace, a’a babu komai ku sauk’eni  a nan tunda kunkawoni main road zan samu abin hawa sai na k’arasa.

jafar yace, no madam baxa’ayi hk ba kibarmu mu k’arasa ladanmu ki taimaka wane unguwa?

izzatu tace, kar na shiga lokacinku maybe you have something important to do.

jafar yace, karki ji komai inane?

izzatu tace, sharad’a pes 1, nagode sosai.

jafar yace, okay mune da godiya.

 Tun lokacin da izzatu ta fara mgn safraz ya tsinci kansa a wani yanayi na jin dad’in muryanta hakan yasa ya d’aga ido ya kalleta ta glass itama a dai_dai lokacin ta kalli glass gaban mutar caraf suka had’a ido, safraz ya sakar mt murmushi itama ta maida masa da martini sai kuma gabanta ya shiga fad’uwa duf!duf magar gaskiya tsabar kyawun safraz sai daya firgita izzatu shikuwa har da gyara glass d’in sosai ta yadda zai dinga kallonta da kyau, izzatu kuwa sunkuyar da kanta ty k’asa domin ta gane kallonta yake tayi. 6angaren jafar kuwa duk yaga abinda safraz yakeyi dariya taso ta kwace masa awani 6angaren km murna yakeyi dan yaga alamun yarinyar zata samu shiga agurinsafraz dan yafi kowa farinciki idan hk ta faru domin babbar burinsa shine yaga safraz yasamu yarinyar da tayi masa  yayi aure domin yammata sudena kawo masa hari ga safraz kuma baya kula yammata ammah yau dayaga sun wuce izzatu yaga safraz harda juyawa ya kalleta shiyasa yace masa su d’anyi baya.

A dai_dai k’ofar gida suka sauk’e izzatu, tayi musu godiya ta shifa gida.

Haushine ya cika jafar ganin,har sukayi sallama da izzatu safraz baiyi mt mgn ba balle ya k’ar6i number ta. hk suka tafi hanya jafar yana tayiwa safraz masifa shikuwa safraz kallon jafar yayi yana marairaice fuska yace, Ay kasan ni bansan ya akeyiba shiyasa na d’auka zakace mt wani abune shiyasa, jafar da haushi ya isheshi sai yayiwa safraz babza kamar be jisaba.

Abu kamar wasa safraz kwance kan gado ammah sam yakasa bacci, daya rufe ido izzatu yake gani hk kawai sai maganganunta su dinga dawo masa  _kar na shiga lokacinku maybe you have something important to do_. A daren dai bai samu bacci ba hk ya kwana yana tinaninta,  koda yagari ya waye suna breakfast  cokali kawai yake juyawa a flat ba abinda yake ci, ba wanda ya fahimci halin dayake ciki sai mahaifiyar bayan kowa ya kammala Abbansu yayi sallama dasu ya fita, ya rage daga safraz sai maminsu da k’annansa shahida da shahida.

Mami tace, twins maza a tafi school karku zama late comers.

A tare suka mik’e, shahid ne yace,  mami and big bro sai mun dawo.

mami tace, yauwa yaran kirki adawo lpy Allah ya taimaka.

safraz yace, pls try to study hard banda wasa sannan ku kulamin da kanku sosai and don’t forget the azkar.

shahida tace, big bro shahid is too much play with his friends by karatu yanxu.

safraz yace, lah! shahid kaifa d’an albarkane gaka yaron kirki why too much playing ?

shahid ya 6ata fuska sannan yace, big bro yarinyar nan fa joking takeyima.

shahida ta kwashe da dariya sannan tayi waje shima shahid yabi bayanta already driver yana jiransu a parking lot.

Mami ta kalli safraz tace, safraz what’s happening ne ng yau duk baka da walwala?

safraz yace, mami nothing gajiya ce kawsi.

mami tace, hym ay ba hk kakeyiba ko gajiyar ce to ma wai me kayi da zaka gaji ?

safraz yace, weather ce kawai mami ammah normal nake.

mami tace, baza dai kawai ka fad’amin ba if don’t share your problem with me whom you share with ?i am your mother your worries  is my wworries

 Or telling me your worries will not help matters ?

safraz yayi saurin kallon mami yace, nop mami ba hk bene .

mami tace, to menene.

safraz ya tattara nutsuwarsa ya kalli mami sannan yace, dama jiyane … ya kwashe duk yadda had’uwarsu da izzatu ya kasance ya fad’wa mami sannan yacigaba da cewa, mami shine fa too much thinking about her since yesterday i don’t know ?

dariya mami ta dingayi sannan ta kalli safraz tace, wallahi safraz kacika d’an fari  yanxu baxaka iya yiwa budurwa mgn ba?

safraz sosa k’eya yayi yace, yace mami to me zance.

Dariya ta kuma yi sannan tace,  to ni yanxu koyama zanyi ko ya?

safraz yace, ehmana mami.

Mami tace to tunda kaga gidansu yanxu abinda za’ayi shine kaje kayi wanka ka sanya manyan kaya ba wai court ba, kaje gidansu idan kaje bawai ita zaka k’iranaba  a’a da mahaifinta zakayi sallama idan kuka gaisa sai kace masa kaxone idan baiyiwa ‘yarsa mijin ba kanason ya baka izini ka fara zuwa gurinta, to anan zai iya yiwuwa ba ita d’aya bace ‘yarsa budurwa idan yace wacce sai ka kwatanta masa ita, daga nan sai kaji me me zai cema idan ba’ayi mt mijinba to shikenan, daga baya  sai ka fr binciken halayenta dama nagarta gidansu ammah idan anyimata to sai kayi hakuri domin haramne neman aure acikin neman aure. Idan kasamu ganin yarinyar bawai ka tsaya kana yimata wannan murmushinaka ba, idan kun gaisa sai kacemata dama tun dana gankine jiya sai naga kin burgeni Allah yasa kema hkne agurinki, sai kayi shuru kaji me zata ce idan kuma tayi murmushi kawai to kaima ka burgeta, sai ka fad’amata kai manufarka akanta itace aure bawai asha soyayyah ba. To my son sauran aykin saika k’arasa inamaka fatan nasara kuma na haneka da k’arya, sannan ka kiyaye kayi tsabtatacciyar soyayyah banda romantic kaji tsoron Allah watarana kaima ubane km baxaka so ayiwa taka ‘yar ba to saika kiyaye domin Annabi yace abinda kayi shi za’aymaka.

Safraz da murnansa yace, mami nagode this my mom da sauri ya matsa inda take yayi mata kiss a check d’inta duk farinciki ya cikashi ya rasa me zaiyiwa mami ya burgeta, sai kuma ya tashi kamar wanda aka tsikara da Allura ya nufi 6angarensa d’insa.

Sai daya shirya tsaf sannan ya fito a falon yakuma samun mami ammah duk sai yaji kunya ta kama sa, safraz yace, mami na tafi need your prayer.

mami tace, my son wish all the best !

mami bayansa tabi da kallo tana,murmushi, itama ta tsincin kanta acikin farinciki tana son taga safraz yayi aure sabida yana buk’tar kulawar mace ayanxu.

 Kamar yadda mami ta fad’awa safraz hk yayi,  mahaifin izzatu yayi matuk’ar  farinciki km ya k’ar6esa hannu biyu domin izzatu ita kad’ai ya haifa baya barin kowa zuwa wajenta sai akan safraz yaji ya aminta dashi bai 6ata lokaci ba ya bashi izinin zuwa wajenta har cikin gidan yashiga ya gaida mahaifiyarta dukkansu sun amshesa da mutunci.

 Mahaifin izzatu prof, Abdullah Abubakar professor ne, d’an salin jahar kano ne matarsa d’aya itace hajiya Rukayya, wato mahaifiyar izzatu, ‘yarsu d’aya itace izzatu mahaifinta yana da ra’ayin ‘yarsa tayi karatu akan yasa ko samari izzatu bata kulawa sai abin yaxama abin munafurci a unguwa ammah duk da hk hakan bai dami izzatu ba da iyayenta sunajin zagi iri_iri  ammah sun toshe kunansu.

  Prof Abdullahi, mutumne kamili kuma salihi bashi da abokin fad’a  ammah mutane sun samishi ido, itama hajiya rukayya bata da shige_shige irin na mata hk ma izzatu dan ko k’awa bata shi a unguwar sai dai a shchool ammah suna zaune da mak’otansu lpy, izzatu yarinya ce me nagarta sai dai akwai sa idon mutane a kanata.

Safraz da izzatu soyayyah ce ta shiga tsakaninsu me tsananin k’arfi, zakayi tunanin sun dad’e a tare jafar kusan yafi safraz son kasancewarsa da izzatu.

Ba’a d’au wani lokaci ba aka saka ranar aurensu, sai alokacin ‘yan’uwa da abokan arziki suka san,da zancen.

 Safraz d’ane ga Alhaji Hashim Muhammad,  Alhaji hashim babban kusane a gwamnati ya rik’e matakai iri_iri  wanda a yanxu yana d’aua dg cikin masu nemsn takarar gwammna a kano, Mahaifiyarsa safraz  Hajiya maryam muktar babbar mace ce mai ilimi da dattko, safraz shine d’ansu na farko sai twins shahid da shahida,

Hajiya maryam tana da yayarta wacce itace ta rik’eta tun rasuwar iyayensu kuma su biyu kawai suka haifa sunanta momy Adama suna matuk’ar kama da hajiya maryam daka gansu kaga asalin fulani kyawawan asali.

momy adama tana da ‘yaranta mata guda biyu karima itace babban sai sailuba.

*************************************

Momy Adama ce zaune a falon hajiya maryam dagani ranta a 6ace yake ta had’e girar sama da k’asa,

Hajiya maryam ta kalleta tace, Aunty adama nima sai da akayi komai mahaifinsa yake sanarmin sunsa ranar auren safraz wata biyu wallahi bansaniba.

Maryam tunda d’ankinne ai dole kice hk kin nunamin bani da iko akan ‘ya’yanki, tun yaushe nake cemiki karima tana son safraz km na hanata kula ko wanne saurayi idan ta dawo sai su dai_daita kansu ammah kawai sai inji kwatsam wai safraz yana neman wata a can.

~Sannu_sannu kwana nesa muje zuwa page 4 yau da gobe batabar komai ba~👌🏻Hajiya maryam tace, Aunty adama shi yaga yarinyar yace yanaso kinsan mahaifinsa besan da zacen ba shi kanshi safraz kwanaki dana fara yimasa zancen yaje ya nemi karima cemin yayi shifa bayason ayimasa tallar mace yafison idan ya ganta da idonsa intayi masa to, ammah Aunty bawai bawai naki karima da auren safraz bane bugu da k’ari naga karima ta fita waje karatu shiyasa da safraz yazomin da zacen yaga wata yarinya ban hanashi domin maybe alokacin yake buk’atar auren.

Cikin 6acin rai momy adama tace, Au yanzu kariman ce anyi masa talla?yarinyar da maxa ke tururuwar zuwa wajenta ammah na hana nace ni d’ana zan bawa domin zumunci ya k’ara dank’o ammah ni safraz yayiwa hk ? wallahi tallahi indai safraz yak’i amince da za6ina to kuwa zumuncinmu yana daf da rushewa ko ke maryam na isa na fad’amiki kiji balle d’anki ko kin manta ni wace agareki ?

Hajiya maryam cikin raunanniyar murya tace, Aunty adama dan Allah karkice hk yara bazasu ta6a sawa zumuncinmu ya rushe karki manta mu biyune fa tak iyayen mu suka haifa bamu da kowa sai Allah yanxu me zaisa wani k’aramin dalili ya rabamu, In dai nice na haifi safraz to wallahi insha Allah sai ya auri karima ammah inason kimin afuwa kar a rusa wannan zancen neman auren nasa kiyi hakuri yayi auren bayan karima ta kammala karatun ta sai ayi musu aure alokacin.

Wani murmushi momy adama tayi tace, Hb ai sai yanxu naji mgn ammah nasan karima batason kishiya sai dai tayi hakuri, taya zanyi na d’auki ‘yata d’aya na bawa bare ammah idan safraz ne ko na mutu bani da wata matsala nasan zai rik’eta amana sabida ‘yar’uwarsace.

Hajiya maryam tace hk Aunty nima bani da burin daya wuce ng zumuncinmu ya d’ore har abada.

Daga nan suka cigaba da hirarsu, ammah zuciyar hajiya maryam a cunkushe take tunani takeyi kala_kala tasan,cewa karima sam ba irin matan da safraz ke so bane bugu da k’ari bata da wata tarbiya, wannan tunanin shike damu hajiya maryam.

******************************************

A 6angaren iyayen  izzatu kuwa sunata shirye_shiryen biki, bikin ‘ya d’aya tilo awajensu komai na bikin na musamman ne har zuwa kayan da suka yiwa d’iyar tasu oder wajece masu kyau da tsada.

 A yau takasance ana saura sati d’aya biki,  safraz ne zaune shida hajiya maryam.

Safraz yace, mami meyasa zakimin hk ? ni bana santa bai dace na aureta ba mami ya aza’ayi ace bayan aurena da wata biyu kuma ace sai na k’ara yin wani auren, me zancewa izzatu ?auren soyayyah zamuyi da ita fa mami banyi mata adalci ba da munyu aure wata biyu na k’ara aure zansata a zargin mutane dole mutane zasu tsammanin wata matsalace da ita shiyasa zan k’ara aure , mami ki taimakeni kujanye wannan zancen bazan iya yiwa izzatu kishiya ba.

Mami itama da ranta yake k’una tace, safraz nice na haifeka na isa na saka abu kuma kayi wallahi nima ba’a son raina,hk zata kasance ba, umarni momynku ta bani kuma wallahi safraz baxan iya tsallake umarninta ba koda zan 6atawa kowa ita zan faranta mata sabida tamin halacci a rayuwa wanda ko da uwata tana da rai iya abinda zatamin kenan, naji kuma na yarda baka son karima ammah kayi hakuri ka sharemin hawayen dan Allah ba danni ba, ta k’arasa maganar tana matse kwallar dg idonta.

 Da sauri safraz yasa hannunsa yana wiping d’in tears dg checks d’inta, shima duk hawaye ya cika idonsa yana cewa, hb mami meyasa zaki 6ata hawayenki mami duk abinda zaisaki farinciki a duniya zanyisa kinji, nothing is more  painful to me then tears in your checks my mom, mami in kince na hakuri da izzatu ma zan hakuri sai na auri karima, insha Allah zanyi dukkan abinda kika ce.

Mami murmushin k’arfin hali tayi sannan tace, thank you so much my son, your are my pride i love you so much because you love me too, Allah ya maka albarka safraz ya yayima jagoranci, bance ka hakura da izzatu ba innayi hk ban damu da farincikinka ba Allah ya bk ikon rik’esu su biyu ameen.

 Koda safraz ya koma d’akinsa komai dagule masa yayi izzatu kawai yakeji taya zai sanar da ita, besan sa’adda hawaye suka dinga bin idanuwansa ba duniya yaji duka tayimasa zafi, wani tunanine yazomasa, fita yayi ya nufi gidansu izzatu.

Yayi sa’a kuwa ya tadda baban izzatu a gida, bayan sun gaisa baban izzatu da kansa ya isar da safraz zuwa falon bak’i.

Safraz yace, Abbu ina so muyi wt mgn ne dama.

Abbu dayake niyar fita dg d’akin sai ya dawo ya zauna.

Abbu yace, safraz ina sauraronka, Dm tun daga wannan bakin naka nasan akwai mgn, ya k’arasa maganar yana dariya.

Anan safraz ta kwashe duk yadda dukayi da mami ya fad’awa Abbu dukda yadda yake matuk’ar  jin kunyarsa.

Dogon numfashi Abbu yaja sannan yace, hak’ik’a safraz ka cika d’a km ka burgeni matuk’a, ka k’ara shiga raina na k’ara yin farinciki sosai sabida nasan wa nabawa auren ‘ya ta, umarnin iyaye abune me girma da km nauyin gaske ba kowa yake iya binsa ba, Ina maka addua Allah ya tayaka rik’onsu duka biyu, ina k’ara yima nisiha akan bin iyaye, sannan kuma karka fad’awa izzatu wannan mgn ko mahaifiyarta ka bari sai bayan biki domin mata akwai ‘yan zuga zasu iya lalata lamarin.

Safraz yy farinciki sosai hk ya tafi yana yabawa da hali irin na mahaifin izzatu, sai alokacin hankalinsa ya kwanta sannan har zuwa time d’in yanajin a ransa bazai iya zaman aure da karima ba sai dai kawai bayason mami ta shiga damuwa.

Karima dake can k’asar England tana,karatu sam bata da labarin safraz zaiyi aure tunanin ya k’are akan da ta kammala karatu ita zai aure kamar ance ta d’auki wayarta tayi connect d’in data ta duba twitter daga nan tayi facebook sai ta koma whatsAp kuma Hankalin karima ne ya tashi alokacin ta ta fara karanta wanu posting cewa _SAFRAZ HASHIM MUHD_ d’a ga Minister ilimi na jahar kano zaiyi aure ranar sunday wanda alokacin ya rage kwana biyune kacal,  hankalinta ne ta tashi sosai ganin ko tantama babu safraz d’intane saima dataga hotunan safraz da izzatu dasuka biyo bayan sak’on alokacin numfashinta ya fr sama_sama kamar zai d’auke, cilli tayi da wayar ta fr farfasa abubuwan dake d’akin hardasu bedshit duk tabi ta yayyaga alokacin dai ta zama tamkar mahaukaciya sai data gaji dan kanta sannan ta fad’i gefe guda tana maida numpashi daga nan ta fashe da dukaka mai ban tausayi , wayan ta d’auko ta har had’a sannan ta fara neman number mahaifiyarta wato momy adama.

~Sunnu_sannu kwana nesa muje zuwa page 5 yau da gobe batabar komaiba~👌🏻

Ringing biyu tayi  aka d’aga, karima fashewa tayi da kuka sai kuma taji magana kamar ba momy ba.
   Aunty what wrong with you ?cewar sakina lokacin data d’aga wayar taji karima na kuka.
Karima jin k’anwarta sakina ce ta d’aga wayar yasa ta dakatar da kukan nata, cikin tsawa tace, why received the calling if i need talk to you i will call your phone not momy’s phone.
  Sakina tace,  hb Aunty what i did it’s a something bad?
Karima takuma hasala sannan tace, kinga stop disturbing me where is momy?is she around ?
Sakina tace, hym mutum kullum cikin fad’a sai kace barkono, momynsu dake gefe a zaune sakina ta mik’awa wayar.
 Momy tarik’e wayan tana cewa;sakina ke dawa kike mgn ne ?
fuskar sakina a d’aure tace, momy kinsan baxai wuce wannan ‘yar girman kan ba mutum yayi nesa ma ammah hali yana nan jiya i’yau.
Karima da duk tanajin abinda sukeyi ranta yakuma 6aci, sai alokacin momy ta kara wayan a kunenta tace, Hello mutanan england yau kuma an tunamu da sassafe hk ?
daga can 6angaren karima tace, momy 6an taba tunanin za’ayimin hk ba, sai kuma ta fashe da kuka.
Momy hankalinta yaso ya fara tashi jin kukan karima domin ta d’au dukkan soyayyar duniya nan ta d’ora akan ‘ya’yanta biyu tak karima da sakina bata k’aunar dukkan abinda zai ta6a su musamman ma karima. A duk tinaninta karima na kukane sabida abinda sukayi da sakina yanxu domin sam batason tasan safraz zai yi aure dan akwai tashin hankali sosai  shiyasa bata fada mata ba har sai ta dawo.
Momy cikin rarrashi tace, hb karima me ya had’aki da ‘yar’uwar taki har zai saki kuka hk so kike ta rainaki kou ?
Cikin hasala bawani ladabi karima tace, wai wayace miki ni wannan banzar ce damuwata, ashe momy baki damu da farincikina ba kamar yadda kike fad’a ke da bakinki kikace safraz bashi da matar data wuceni ammah momy why zaki 6oyemin safraz zaiyi aure ?sai Dai ingani a magazine da social media, ta k’arasa maganar tana kuka.
Shuru momy tayi domin tayi matukar kad’uwa da mamaki, ko sa’ilin taso ta boyewa karima tace k’aryane to ammah sai ta tuna cewa tace a jarida ta gani da social media ba damar ta k’aryata, yazama dole ta fad’a mt gaskiya.
Karima ta kuma cewa, momy kikayi shuru ko kina nufin kema kice baki saniba ne ?
 Momy tace, kai!karima kinsan banason damuwarki wannan ba abin tashin hankali bane, kinsan bana mgn biyu kamar kin auri safraz kin gama kisa wannan a ranki da zaki bar wannan maganar ki bari sai kin dawo tukunna kwata_kwata kwana nawa ya rage miki ne naga.
karima tace, ni ban gane me kike nufi ba pa momy, safraz zaiyi aure acikin satinan ammah kina maganan kamar na auresa na gama, kina nufin zai hakura da auren ne ko kuwa nice zan zauna da kishiya!?
Momy ta kuma kada murya tace, matsalana dake bakya cin ribar zance, Anan momy ta kwashe duk yadda sukayi da k’anwarta wato hajiya maryam mahaifiya ga safraz ta fad’awa karima.
Wata irin k’ara karima ta saki wanda yasa momyn ma ta firgita tare da cewa, momy!ni ! ni ! ni ! ni za’ayiwa kishiya ?momy kinsa me kike fad’a kuwa ?safraz ya aureni a ta biyu, wallahi Impossible wallahi yau nasan bakya sona har zaki amince ‘yarki ta zauna da kishiya this is play child momy and i sure you hate me momy.
momy tace, hb sha lelena baki tsaya kinji k’arshen zancen ba ai listen to me pls zaki gane gatan da zammiki.
karima tace, na gama fahimtanki momy you have nothing to tell me stop deceiving me the game is over, kibarni ni zan sharewa kaina hawaye wallahi gobe zan dira a 9geria sai nayi me yiwuwa dan lalata lamarin auren nan. Bata jira me momy zatace ba ta katse wayan.
Momy ta dinga k’iranta ammah tak’i d’agawa duk tashiga damuwa ta rasa inda zatasa kanta. Sakina dake zaune a gefe ranta itama a 6ace jin yadda karima ke yiwa mahaifiyar tasu mgn babu ladabi.
Sakina tace, momy wannan abinda kikewa aunty wallahi ba gata ba ki duba fa kiga bata jin shakkar fad’amiki ko wacce irin mgn ammah momy a hk kike binta kina rarrashinta, safraz sam wallahi bai dace ya auri mara tarbiya irin aunty ba kuma wallahi momy baya sonta kune dai kuka dage zakusa mami tayi masa dole kuma dan ansan shid’in mai tarbiya ne ammah ai ba’ayiwa namiji auren dole ko aunty tayi nasarar aurensa wallahi zata gane tayi babban _*KUSKURE*_ , momy karki manta damu da safraz duk d’ayane awajen ni ni tabbata bazaki ta6a yadda mu auri wanda bama so ba ammah to meyasa shi akeson ayimasa dole sai ya aureta momy kamar fa talla ne aunty takeyi da kanta ta bari yaxo yace yana sonta ammah karta kai kanta garesa.
Momy ta gallawa sakina wata harara tace zaki rufemin baki ko kuwa sai na sa6amiki, sannan ta mik’a mata wayar tace, a6i nan zoki rubutamin text in tura mata ko hankalinta zai kwanta.
 Sakina tace, momy dan Allah karkisani acikin wannan lamarin momy ki rubuta text d’in da hannunki dan Allah ko ki k’ara k’iranta ki fad’amata ni dai gaskiya bani acikin wannan lamarin.
Momy ta 6ata rai tace, okay ban isa nasaki abu kiyi ba kou?ko kuma kin raina ni ne bansaniba idan na isa da ke sai kin rubuta ke baki damu da damuwar ‘yar’uwarki bane kou?
Dole sakina ta kar6i wayan ta rubuta dukkan abinda momy ta umarce ta rubuta.
A can d’aya 6angaren karima data gama shiryawa da nufin ta nufi airport dan ta shirya yadda zata tafi nigeria gobe, text ne ya shigo wayanta sai tayi kamar bazata duba ba sai kuma ta bud’e ganin text d’in dg momy ne yasa ta koma da baya ta zauna akan wata ‘yar k’aramar
Sakina tace, momy dan Allah karkisani acikin wannan lamarin momy ki rubuta text d’in da hannunki dan Allah ko ki k’ara k’iranta ki fad’amata ni dai gaskiya bani acikin wannan lamarin.
Momy ta 6ata rai tace, okay ban isa nasaki abu kiyi ba kou?ko kuma kin raina ni ne bansaniba idan na isa da ke sai kin rubuta ke baki damu da damuwar ‘yar’uwarki bane kou?
Dole sakina ta kar6i wayan ta rubuta dukkan abinda momy ta umarce ta rubuta.
A can d’aya 6angaren karima data gama shiryawa da nufin ta nufi airport dan ta shirya yadda zata tafi nigeria gobe, text ne ya shigo wayanta sai tayi kamar bazata duba ba sai kuma ta bud’e ganin text d’in dg momy ne yasa ta koma da baya ta zauna akan wata ‘yar k’aramar kujera dake gefen bed ta fara karanta wa;
_My daughter come down pls, karki dami kanki akan wani k’aramin dalili ni na d’au alwashin cika miki burinki ko ta halin k’ak’a, Ba boka ba malam safraz zai aureki ina bin a sannu ammah ke kinfi son ayi gaggawa no karima ku nutsu ki fahimci abinda zan fad’amiki, mu rabu da safraz yayi aurensa ammah kinsan me?tun dg first night d’insa shida amaryarsa zamu fara kula kiyaye a tsakaninsu zamu rabasu da kwanciyar hankali shi da kansa zai saketa tun kafin su cika watanni biyu da aure ke kuma nan da wata biyu kina dawowa zaki shiga  gidan koda be saketa ba kekuma kina shiga zakiyi waje da ita, ammah idan kikace sai munyi yadda zai hana yayi aurensa to zai tsaneki ne a ransa muda muke neman soyayyah dole ta k’asa zamu dinga bi, makirci kisisina tare da kissa duka zaki koya karki kuskura wani ya gane kina bak’in ciki da auren ki kirashi ma a waya ki tayasa murna karki na nuna komai a fuska ki danne kawai idan kin samu dama ma kizo bikin ko kwana uku ne saikiyi ki koma_
Karima tana gama karantawa sai taji ranta ya d’anyi sanyi, sai alokacin ta gane me momy take nufi tabbas yanxu hankalinsa yana kan wata bazai saurarenta ba duk abinda zatayi, murmushi tayi sannan ta tafi laluben number safraz.
_*BAYAN KWANA BIYU*_
*****************
*************
**********
********
*****
**
*
Taro yayi taro, jama’a iya jama’a bikine daya tara manyan mutane, naira tayi kuka an zubar da ita tamkar ba’a so kamar ba’asan zafin nemanta ba _SAFRAZ HASHIM MUHD, TARE DA AMARYARSA IZZATU ABDULLAHI ABUBAKAR_
Kowanne 6angaren sun nuna bajintarsu, kowa cikin farinciki yake musamman ango safraz momy adama ta zage tana ta hidima tamkar babu komai a ranta hakama karima ranar d’aurin aurw da sassafe ta diro nigeria sun gama kulla komai ita da mahaifiyarta sam basu bari sakina ta san abinda suke kullawa ba, mami taji dad’in yadda yayarta momy tayi hidima sosai a bikin abin ya bata mamaki ganin karima itama ta sake babu wata damuwa a ranta.
Zuwa can da yamma mami da momy suna zaune a d’aki su biyu suna hira,
momy tace, gaskiya na yaba da hankalin yarinyar da safraz ya za6a Allah ya basu zaman lpy.
mami tace, ameen aunty adama iyayenta suna da dattko sosai sun samu yabo sosai awajen jama’a.
momy tace, hk ake so ai, yanxu inason in k’ira sakina da karima da shahida suzo su fara shirya musu kalolin abincin da za’a kai musu gobe da safe wanda zasuyi breakfast dashi ko ya kika ce?
Mami tace, duk yadda kikayi aunty yayi dai_dai.
momy waya ta d’auka tak’ra karima, hello karima kina ina inason yanxu keda shahida da sakina kuzo ku sameni a d’akin maminku maza.
karima tace, momy ai mu tuni munyi nisa wallahi yanxu hk muna gidan amarya kuma baxamu taho ba sai an kawota momy, mezamu yi miki momy ?
momy tace, hb karima ku taho mana ba sai ku koma ba dg baya, inason kuzo ku fr shiya abinda ango da amarya zasuyi  breakfast dashi gobene.
karima ta marairaice murya kamar zatayi kuka tace, hb momy ki bari sai mun dawo idan banga amarya yauba gobe around 10 fa zan tafi, momy ai yanxu ma andena kai abinci dg gida kawai masu aiki zaku nema musu kamar guda biyu hk, gidan fa da nisa momy har yaushe akayi girki da safe aka kai musu koda anyi da sassafe momy kuma fisabilillah da sassafe sai aje a tashesu koda basu tashiba  wannan tsarin baiyiba momy ga store d’insu acike da kayan abinci kicewa mami tasa yanxu aje anemo me aiki kawai dan ko me gadi babu a gidan. Tana gama fadin hk ta katse wayan batajira momy ta k’ara cewa komaiba.
 Dayake wayan yana speaker mami tana jin duk abinda karima tace, sai taji abun yayi mata dad’i kuma karima ta burgeta duk da tana son safraz hakan bai hana ta fad’i gaskiya ba, mami taji dad’i sosai.
_Abinda mami bata saniba hakan duk yana cikin mak’ircinsu da suka shirya_
hk akayi kuwa mami ta amince da abinda karima ta fad’a, nan take momy ta k’ira wata k’awarta tace, a turo mata masu aiki guda biyu.
Momy dama tuni tasan suwa za’a turomata wasu ‘yan daudune guda biyu dukkan sunyu shigar mata ba wanda zai kallesu yace mazane ba mataba sun sa kaya tsaf_tsaf daka gansu zaka rantse matane har maganarsu sunyi cikon ko ina ajikinsu kamar mata.
Momy ta kallesu tacewa mami sunyi ko?mami tace ba wata matsala ng suna da tsafta sosai harda kwalliyarsu abinsu sunyi.
momy ta kallesu tace ya sunanku?
Ta farkon tace, ni sunana Abu itakuma wannan k’anwata ce sunanta ma’u.
momy tace to yayi,  yarona ne yayi aure yau shiyasa nakeson ‘yan aiki.
Abu tace, Allah ya sanya alkhairi ajiya, insha Allah zamuyi aiki da gaskiya zasuji dad’in aikinmu.
mami tace, to nawane za ana biyanku duk wata ?
Abu tace, girki, wanke_wanke, da gyaran gida da share_share da aike da sauran d’awainiya harma da wankin matar gida da yara ana biyanmu dubu talatin duk wata, ammah idan baza’a bamu wajen kwanaba ana biyanmu dubu ishirin duk wata, muba agari mukeba hayan dak’i muke kamawa duk wata dubu goma shiyasa muke cire dubu goma ya zama ishirin idan za’a bamu  wajen kwana a gidan.
Mami ta kalli momy tace ya kika gani?momy tace to dole dama amasu wajen zama tunda safraz yana fita aiki itama matar tana karatu kou?mami tace, hkne wannan to yanxu za’a baku wajen kwana sannan za’a dinga biyanku dubu talatin d’in insha Allah.
A dai_dai lokacin safraz ya shigo d’akin nan mami tayi masa bayani shima kuwa yaji dad’in zancen sosai take yasa driver ya kai su Abu gidansa aka nuna musu wani d’aki daga gefen part d’in izzatu nan ne d’akinsu tun zuwansu karima ta hangosu sai wani farinciki takeyi wato shirinsu ya tafi dai_dai ba wanda zai gane mazane ba mt ba.
An kawo amarya kowa ya watse, ‘yan aiki suna 6angarensu, amarya da ango suma suna part d’insu,
safraz ya kalli izzatu datake lullube cikin mayafi  yace, Izzatu tun da nake a duniya banta6a jin farinciki irin yauba.
 Izzatu ta kuma rufe fuskanta da mayafin tana murmushi, hira suka dinga yi a tsakaninsu sannan suka gabatar da sallah raka’a biyu da addu’o’i da suka zo a sannu.
A gidan mami kuwa ‘yan biki duk sun watse saura kad’an wanda ‘yan’uwa ne na nesa, mami ta kalli shahida dake saka kaya a sif tace, shahida kaina wani irin ciwo yakemin  nemiomin maganin ciwon kai ga hajijiya da nake ji.
shahida tace, Ayya! mami sannu ko dai tarone yasa kikejin gajiya hk ?
mami tace a’a shahida wannan ya wuce hayaniyan taro sosai nakejin ciwon kan.
shahida fita tayi dan ta d’auko mata maganin.
Momy kuwa tana falo ta idar da sallah tana jiran result d’insu ya fito, wato tun lokacin da jama’a  suka fara watsewa momy tasa aka kawo musu abinci tasa mami a gaba tace ta zauna su ci abinci domin taga alamun sam bata ci wani abin kirki tun safe, mami ta zauna sukaci karima ta kawo musu lemo ammah saida lemon da mami tasha sun riga sun zuba maganin bacci over aciki yadda zai iya fitar da mutum acikin hayyacinsa wannan shi yasa mami ta farajin alamu.
Shahida tana kawo wa mami maganin ciwon kan sai ta samu mami rana ta juyi akan gado sai k’iran wayyo Allah takeyi duk tabi ta fita hayyacinta.
Nan da nan shahida ta fara kukan neman taimako, da sauri momy ta shiga d’akin tana farinciki maganin ya fr aiki momy itama taso ta firgita ganin yadda mami takeyi ammah sai ta kalli shahida tace maza d’au waya ki k’ira safraz, dayake shahida yarinyace bata wuce shekaru 12 ba batayi tunanin bai dace a k’ira safraz ba nan da nan ta k’irashi.
Safraz yana zaune kusa da izzatu yanata magiya akan ta bud’e baki yasa mata naman daya yago tak’i, sai ga ringing ya shigo wayansa ya d’au wayan da niyar yayi rejectint call d’in sannan ya kashe wayan kawai sai yaga number mami ne da sauri ya d’aga sai yaji muryan shahida tana cewa;
Big bro mami zata mutu sai kuka takeyi tana cewa wayyo Allah, sai ta fashe da kuka.
safraz mik’ewa tsaye yayi zumbur ya yar da naman da yake hannunsa, cikin firgita yace, shahida meya sameta ?shahida tace, bro i don’t know but she said she have a headache right now.
Safraz cikin rud’ani yace, ina zuwa. shahida ta kashe wayan momy datake k’ok’arin d’aga mami tacewa shahida me yace?shahida tace yanazuwa yanzu.
Alokacin shahida da karima suka shigo d’akin dayake namiji yafi mace hankalin nan da nan shahid ya k’ira Abbansu ya sanar masa shima Abban baya gida yace masa su k’ira driver ya kaita hospital gashinan zuwa ammah kar a fad’awa safraz.
Shahid yace Aunty karima ku kamata mu kaita mota Abba yace driver ya kaimu hospital, momy tayi saurin cewa kai ajira safraz yazo mana shahid yace, momy Abba yace kar a fad’amasa.
Dan kar su shahid da shahida su gane yasa momy tasa suka kama mami har zuwa mota a harabar gidan sakina ta gansu hankalinta ya tashi sosai ganin halin da mami take ciki ita tayi drivering ta kaisu har hospital d’in momy  bataso hk ba taso sai safraz yazo tukunna su kaita hospital d’in tare, ammah sai ta tuna yace yana zuwa sai ta d’an ji dad’i hakama 6angaren karima sai tunani takeyi ya za’ayi safraz yazo batan tuni momy tasa shahida ta fad’a masa ba.
Safraz cikin gaggawa ya bar gidan da yayi kamar ta tafi tare da izzatun kuma sai ya tuna bai daceba hk yasa ya tafi ya barta badan ransa yaso ba, koda yazo gd aka sheda masa sun tafi asibiti sai ya k’ira number mami, momy ce ta d’aga ta fad’amasa hospital d’in da suke, ba 6ata lokaci ya isa asibitin, lokacin daya isa har likita ya dubata ya mata wata allura,  likitan ya sheda musu karsu wani damu nan da mintuna ishirin zata farka kuma zata dawo normal abinda yasa hakan ya faru da ita maybe tasha wani  magani ne over ammah babu wata matsala.
D’akin suka shiga dukkansu suka zazzauna mami itakuma tana bacci, safraz ne yaje bakin gadon ya dafa goshinta da yake ta zufa duk sai yaga idonta ya zurma ciki lokaci d’aya.
 Bayan mutuna 12 Abba ya iso shima, nan suka fad’a masa abinda likitan yace, Abba yayi_yayi safraz ya koma gida ammah safraz yaki wai sao ya jira ta farka.
ba’a dad’e ba mami ta farka ware ido tayi tana kallonsu one by one, dukkan su suka hau murna.
murya a dashe tace, meyake faruwa naga ango a nan a ina ka bar ‘yar mutane?
Safraz yace,  wallahi mami na tsorata sosai ammah wane magani kikasha me k’arfi hk?
mami tace, ciwon kaine naji me tsanani ban ma sha ko wanne magani ba.
momy tace, to likita yace kin sha wani maganine da yawa.
mami tace, Allah yanxu garau nake jina km ba wani magani dana sha.
Abba ya kalleta yace, ko dai kinsha batare da kinsaniba sabida tsananin ciwon kan ?
mami tayi dariya tace, sai kace wata ‘yar kwaya zansha abu ban saniba
Abba ya kalli safraz yace, kai wuce ka koma gida, nace kar a fad’amaka ammah sai kazo kou?maza tafi muma yanxu zamu tafi.
Safraz yayimusu sallama ya tafi, yana driverint ammah Allah_Allah yake ya isa ga izzatunsa.
 Momy ta fita ta kira Abu me aiki ta sanar mata ga safraz nan yanxu zai dawo.
Izzatu tana zaune bakin gado ta kwantar da kanta a kan gadon taji shigowar mutum da sauri ta d’aga kanta dan tunanin safraz ne ya dawo ammah kawai sai ta ga wani mutum tsaye a kanta.
A tsorace ta mik’e zaune, tana k’ara bin mutumin da kallo shi ba saurayiba ammah km shiba magidanci ba, a hankalin ya dinga matsowa inda take har sai data jingina da bango.
Jikin izzatu rawa ya fr yi duk da air conditioning dake d’akin ammah zufa takeyi, kamota yayi ya cillata kan kado sai alokacin ta gane nufinsa, kuka ta saki me k’arfi tana cewa ;
Dan Allah kayi hakuri, menayi ma?dan Allah karka cutar dani.
Stood ya samu ya zauna dake gefen gadon, sannan yace, mlm izzatu kwantar da hankalinki babu abinda zan miki bazan miki abinda kike tunani ba ammah fa idan kinji km kinyi abinda zan ce miki, da fari nidai nazone badan namiki fyad’e ba kamar yadda kike tsammani, akwai wani aki danazo yi ammah saikin bani had’in kai zai tafi dai_dai idan km kika k’i to wallahi zammiki abinda kikayi tsammani ammah idan kikayi zamu rabu lpy. Da fari ina wayarki ?
Jin yace bazai yi mt komai ba yasa izzatu ta d’an rage tsoronsa, a hankalin ta jawo jakarta ta ciro wayar ta mik’amasa.
Number sa yasa a wayar izzatu sai ya k’ira layinsa nan da nan kuwa wayarsa ta fr ringing  d’aga k’iran yayi tana ta tafiya zuwa kamar mintuna biyar sai ya kashe sannan sai ya cillah mata wayarta.
Izzatu batasan me yayi ba dan hk bata duba ba, ta d’auka number ta kawai ya d’auka, zuciyarta cike da tsoro addua takeyi Allah ya kawo safraz cikin gaggawa.
Mik’ewa tsaye yayi ya cire kayan jikinsa ya bari dg shi sai gajeran wando da singlet, izzatu takuma firgita sosai kuka takeyi sosai.
Tsawa ya daka mata yace; ke nace miki babu abinda zanmiki zaki dena wannan kukan ko kuwa sai na koyamiki hankalin, sai ya fr nufowa inda take.
 Hannun tasa ta toshe bakinta sabida ta kasa tsayar da kukannata, sai yaja da baya yace, karki k’ara idan km……sai ya girgiza kai.
Tsayawa yayi yana k’aremata kallo, sai ya d’aga gira yace, maganar gaskiya naji tausayinki wannan ranarkice ra farinciki ammah kuma……sai yy shuru.
yace, inason yanxu ki shiga toilet kiyi wanka.
A  tsorace izzatu ta d’ago idonta ta kallesa tana zare ido.
izzatu tace, bawan Allah kaji tausayina yau itace ranata ta farko a gidan mijina dan Allah karka 6atamin rayuwa.
yace, mlm izzatu na rantse miki da Allah babu abinda zanmiki idan har kikayi dukkan abinda zan sakaki ai ba’awasa da Allah, Allah bazan miki abinda kike tsammaniba, yana gm fad’in hk ya matsa kusa da ita ya janye mayafinta jikinta sai rawa yake tsoro cike da ranta.
Izzatu kuka yazo mata ammah sai maidashi takeyi banda karkarwa babu abinda jikinta yakeyi, d’an kwalin kanta yaja shima ya ciresa, kallonta yayi yace saura aikinki.
kallonsa takeyi tana d’aga kai, yace ko bazakiyi ?
da sauri ta girgiza kai, yace, cire zaninki ai nasan akwai siket aciki, izzatu da sauri ta dira akan gadon tayi hanyar toilet dan ta shiga ta sa key.
  Shikuma cikin hanzari ya cafko ta, tsinka mata mari yayi yace, naga abin naki wasa ne bazakiyi abinda nasakiba ko ?har sai mijinki yazo ya samemo mu ko?da kokawa ya cire dukkan kayan dake jikin izzatu duk karfinta sai daya kare wajen kwace kanta ammah ta kasa toilet ya jata ya kaita ya tufeta daga ita sai pant ne a jikinta.
Izzatu tuni ta sare duk tunaninta fyad’e zai mata, ilahirin jikinta duk ya mutu bata da wani k’arfi kukan ma ya kasa zuwa mt.
Shima bakin gadon ya samu ya zauna yana maida numfashi, Ana hk yaji shigowar mota harabar gidan ta window ya lek’a ya hango safraz ya nufo part d’in.
 Da sauri ya tashi shima ya shige toilet d’in, alokacin izzatu ta d’aura towel ajikinta, ruwa ya shashshada ajikinsa tamkar wanda ya fito dg wanka hakama izzatu ya  fincike towel d’in dg jikinta ya watsa mt ruwa dg sama har k’asa sannan ya maida mt towel d’in ba musu ta k’ar6a ta d’aura dan zuwa lokacin ta dena tsoro abin mamaki kuma yake bata meye nufinsa shine abinda bata ganeba.
Yanajin safraz ya shigo d’akin ya bud’e k’ofar yacewa izzatu ta fita.
Safraz da saurinsa ya shigo d’akin yana cewa, slm my sweet sorry for keep waiting. turus yayi ganin kayan izzatu a tsakiyar d’akin ga kuma kayan maza jens da t-shirt bai kawo komai a ransaba yace, my izzat kina ina are you in toilet ?hanyar toilet d’in ya nufa a dai_dai bakin toilet d’in yace mine na dawo kiyi hakuri kinji in shigo dear ?
Izzatu sai alokacin ta gane me mutumin nan yake nufi wato sharri yazo dan ya kulla mata ji tayi hajijiya ta kwasheta ta tafi luuuuuuu zata fad’i da sauri yasa hannayensa ya tarota a dai_dai lokacin safraz ya bud’e toilet d’in.
Tsayawa safraz yayi sororo yana binsu da kallo, idan ba mafarki yakeyi ba kamar izzatunsa yake kallo a jikin wani ?da sauri ya murza idanuwansa da gani yake tamkar ba gaskiya yake gani ba, shikuwa mutumin shima da sauri ya saki izzatu itama cikin hanzari ta dafa bango dan tafiya tayi zata fad’i.
 Cikin d’aga murya safraz yace, Izzatu waye wannan ?wayeshi ?wayeshi nace miki har kukayi wanka tare?ya k’arasa maganar yana d’aga murya sosai.
zuwa lokacin izzatu tama rasa me zata fad’a danta kare kanta agurin safraz hawayene kawai suka fr bin idonta, dukkan su suna tsaye sai kallon kallo sukeyi.
Safraz dukan k’ofar toilet d’in yayi ya k’arasa shigowa, kafad’unta ya rik’e duka biyu yana girgizawa yana cewa;wayeshi nacemiki izzatu ?meye had’inki dashi me kukayi izzatu ?lokaci d’aya fuskar safraz ta canza idanuwansa suka juya daga fari zuwa jajazur, izzatu kuwa kuka ta fashe dashi me ban tausayi, shikuwa mutumin ko ajikinsa sema ya tsaya yana kallonsu babu alamun zai gudu ma.
Ran safraz ya kai matukar 6aci zuciyarsa tana k’una yana rayawa a ransa “wato abinda yake zargi shine ya faru kenan shiyasa ta kasa bashi amsa”
tas! tas! kakeji, safraz ne ya kwashe mutumin da maruka guda biyu, muryar safraz a shak’e ya kalli mutumin sama da k’asa yace, me ya kawo cikin gidana?meye had’inka da matata ta sunna ?kai waye ?safraz ya dungule hannu zai naushi mutum sai mutumin ya rik’e hannun safraz da sauri yace, kai malam dakata ! , meyasa zakaga laifina dan ka ganni a gidanka gidanka d’in banza, nafi k’arfin inbi matarka sai dai ta bini, ko zanzo gidanka mezaisa nazo a ranar daren farkonka kai da ita, ita ta k’irana tacemin nazo ka fita nacemata bazanzo ba sabida maybe ba nisa kayiba karkazo ka tarar damu sai tacemin mahaifiyar kace bata da lafiya da alamun idan katafi zaka dad’e kar na damu nazo kawai koda ka kamamu ita bata shakkar a ganni tare da ita dan tayi imanin babu namijin da zaiyi mata abinda nakeyi mata.
Kirjin safraz ne yake fad’uwa duf ! duf !, da sauri ya kalli izzatu hawaye na bin fuskarshi yace, Dan Allah izzatu kicemin bakuyi sex ba, dan Allah karki cemin kunyi, Itama shi take kallo kuka yaci k’arfinta tana tsananin mamakin tarkon da mutumin ya d’anamata bame k’aryata shi.
  Muryan mutum sukaji yace, izzatu wallahi nayi nadamar amsa k’iranki, kin k’asak’antar dani a gaban mijinki, da lokacin da muka kammala kin barni na tafi da baizo ya samemu ba ammah kikace sai munyi wanka tare. Ya k’arasa maganar yana jan tsaki.
Izzatu tace,Wallahi k’arya yakeyi, wallahi ban sanshi ba ban ta6a ganinsa ba sai yau, besty karka yarda dashi sharri yakeso yamin,
 Mutumin yace, au hk zakice izzatu ?idan namiki k’arya ai shi ba makawo bane ya ganmu tare kina nufin ni kwartone?wayarki ma ai shedace domin da ita kika k’irani.
 Safraz da k’yar ya dafa bango ya fito daga toilet d’in idonsa yana gani dishi_dishi yana isowa tsakiyar d’akin ya fad’i yanajan numfashi da k’yar hakan ya bawa mutumin damar fitowa ya fice abinsa.
 Itama izzatu fitowa tayi hawaye nabin fuskarta, ganin safraz a tsakiyar d’akin a kwance yasa  ta k’arasa idan yake hankalinta ya tashi ganin da k’yar yake jan numfashi, hannu tasa ta rik’esa tana cewa, besty kar abin ka gani yayi tasiri a ranka dan Allah wallahi tallahi sharrine nima ban sanshi ba wallahi.
Hankad’eta gefe yayi sai da towel d’in jikinta ya kunce da sauri ya kawar da idansa itama cikin hanzari ta maida ta d’aura.
  A hankali ya mik’e tsaye ya bar d’akin, kan kujera yasamu a falo ya zauna, tunani kala_kala suna zuwa masa ransa.
Izzatu kayanta ta d’auka tasa zuwa lokacin hawaye ya k’afe a  idonta zaman dirshan tayi a k’asa tarasa me yakeyi mata dad’i tunanin ta d’aya ” laifin metayiwa wanda ya aikata mata hk, aikoshi akayi ko kuwa dan kasan yayi” a hankalin take takawa har zuwa ta fito falon.
Ma’u me aiki tana zaune a d’akin da aka basu ita da Abu a gefen part d’in izzatu a ranta tana cewa” Anya kuwa Allah zai yafema na kuwa?muzo danmu lalata rayuwar auren bayin Allan nan hk kawai sabida za’a bamu kud’i, yaune fa darensu na farko ammah nasan Abu tuni ya gama lalata musu wannan daren, tabbas yarinyar abin a tausayamata ne a ina zatasa ranta ?yanzu kuma idan aka kama Abu yazamuyi ?”  tana cikin wannan tunanin taji an banko k’ofa da k’arfi.
Abu ce ta shigo da sauri tasawa k’ofar ki sannan tazo kusa da ma’u ta zauna tana sauk’e ajiyar zuciya.
zuwa can sam’u tace, ya ake ciki?
Abu tace, komai ya tafi dai_dai sai dai fa angon yana cikin matsala sosai dan yanxuma ya fad’i kamar sumamme hakanne yabani damar fitowa.
Ma’u tace, to muk’ira hajiya mu fad’amata ammah kar muce mt akwai wata matsa domin gaskiya ni inajin tsoron abin da kaje yazo.
Abu tace, ke wannan fa bawani abin tsoro bane miliyan d’ayafa za’a bamu cas a hannu gobe, dan mu kashe auren yarinya nan ni a ganina babu wani shiga hakkinta da mukayi dan ‘yar gidan masu hannu da shuni ce kota bar nan gidan cikin daula zata cigaba da rayuwarta agidansu,  kinga kayan da aka zuba mata kuwa yadda kikasan ba a duniya kikeba idan kika shiga d’akinta,   mukuwa talauci yayi mana katutu kamar ya kashemu abincin damukeyi ma yanxu ba’a wani cinikin kirki.
Ma’u tace, hmmm hkne ammah wallahi inajin tausayinta sosai adaren farko aka mt wannan sharri me girma hk .
Abu tace, matsala dake ai kenan, idan kinsan bazaki iya wannan aikin ba tun wuru ki fad’a kar sai tafiya tayi nisa kisa agane mu mazane ba mataba.
ma’u tace, hb yama za’ayi hk ta faru zan kiyaye dukkan hanyar daza tasa a fahimci mu mazane ba mt karki ji komai.
Abu ce ta ciro ‘yar k’aramar wayarta me k’iran nokia, number momy adama tak’ira wanda alokacin 11:37 na dare ammah nan da nan aka d’aga.
momy tace, saminu ya sai?
Abu tace, hajiya komai ya tafi yadda kikace.
momy tace, yauwa hk nakeson ji daga gareku, muma yanxu hk ab sallamemu dg asibitin muna gida.
Abu tace, hajiya babu wani abu wanda za’ayiyanxu ?
momy tace, babu komai, yanxu kawai zamu jira zuwa gobe ne muga mai zai biyo baya, duk abinda za’ayi zan fad’amuku sannan inason ku kiyaye sosai kar a fahimci ku suwaye.
Abu tace, indai wannan ne hajiya karki samu damuwa angama, daga nan suka kashe wayar.
_Saminu da k’aninsa Ado ‘yan daudune da suke aikin dafa abincin siyarwa a kasuwa, ko acikin ‘yan daudun da suke aikin dafa abinci a kasuwarsu saminu yayi k’aurin suna kowa yasanshi idan a harkar fitsane a kalla zai kai shekaru 31, Ado kuma k’aninsane me bin umarninsa duk abinda yasashi, saminu shine yake amsa sunan Abu shikuma Ado shine ma’u._
Har izzatu ta iso inda safraz yake baisan ta zoba, yana kan kujera a zaune yayi nisa a tunani ga kuma hawaye yana bin kumatunsa.
   Safraz izzatu ta fad’a, d’agowa yayi ya kalleta sai alokacin yasan tazo gurin.
 Tacigaba da cewa,  Dan Allah ka fahimci ne safraz, karkamin mummunan zato dan Allah, wallahi ni ba fasik’a bace bazan ta6a iya aikata abinda kake tunani ba nasan kayi bincike akaina kafin ka nemi aurena kasamu sheda me kyau akaina da iyayena, wallahi ban ta6a sanin wani d’a miji arayuwata ba ban ta6a zubda mutuncina ba wannan abun daya faru makircine da sharri akeson a k’ullamin bansan menayiwa wanda ya aikatamin hk ba dan Allah safraz kamin kyakykyawan fahimta. Ta k’arasa maganar tana fashewa da kuka me ban tausayi.
 Har cikin zuciyarsa yaji tausayinta bayanson zubar hawayenta kokad’an yanaji tamkar yayi hauka sabida tsananin sonta da yakeyi,  kukan datakeyi yanzuma ji yakeyi kamar ana sukar kirjinsa da mashi, ammah taya zai yarda da abinda tace bayan abinda ya gani da idonsa.
Ya isa!safraz ya fad’a yana kallon izzatu.
Yacigaba da cewa, kidena kukan nan hk ya isa come over.
 ya fad’a yana mik’a mata hannunsa.
A hankalin ta taso ta matso inda yake, hannu daya mik’o mata bata da za6i itama ta mik’a masa nata bisa mamakinta taji ya jawo jikinsa.
Rungumeta yayi sosai ajikinsa kamar zai maida ita ciki, A hankali yake sauk’e ajiyar zuciya, sun dad’e a hk zuwa can safraz ya fara cewa;
 Hakik’a izzatu ina matuk’ar  k’aunarki a raina yadda nakeji babu abinda nakeso kamarki a duk duniya baki d’aya kece mace ta farko dana fara so a zuciyana nasha fad’amiki ban ta6a soyayyah ba izzatu, nayi rayuwa a k’asa shen turawa ammah ammah hakan baisa na ta6a aikata zina ba duk wani burina yana kanki izzatu dukkan tanadina nakine my dear but why do that to me?meyasa kikamin hk ?koda kin kasance kina aikata hk kafin aurenmu meyasa baki hakura ba  alokacin da mukaza ma’aurata muyi rayuwa me kyau ki nemi yafiyar ubangiji akan wanda kika aikata a baya, Ammah izzatu naji bak’in ciki sosai duk tunanin ban ta6a tunanin you can do that ba but why izzatu ?kuka yakeyi sosai izzatu dake kan kirjinsa rungume tanajin zubar hawayensa akan fuskarta, D’agowa tayi itama hawaye sun cika idonta hannun tasa tana goge masa hawayen dake zuba a fuskarsa shima hannu yasa yana gogemata hawayen dake zuba a fuskarta.
 Izzatu tace, Ka yarda dani dear wallahi ban aikata ba gaskiya nake fad’ama.
Safraz ya kwantar da kansa akan bayan kujeran sannan yace, idan sharri yazo yamiki ya akayi yasan nafita bana nan bawanda zaiyi tunanin zan fita inbarki a dai_dai wannan lokacin idan ba fad’a akayiba taya yasan mamice bata da lpy ?izzatu na kasa yarda dake gaskiya.
Izzatu tace, wallahi bansan ya akayi ya saniba ammah bani bace na aikata hk dear believe me pls what am telling you is true.
Dukkansu sukayi shuru ba wanda ya k’ara cewa komai.
 Safraz ne ya fara zame jikinsa daga jikin izzatu ya tashi sai da yayi tafiya kamar taku biyar sannan ya juyo ya kelleta yace sai da safe.
  Wani d’aki dake kusa da d’akin izzatu ya bud’e ya shiga yasa key ya rufe, bed ya fad’a ya fara kukan zuci wanda yafi na fuska ciwo.
Ko da izzatu tazo ta murd’a kofar taji yasa key har zata wuce d’akinta kuma sai ta fasa ta durkushe a wajen taba ta kuka marar saiti a wajen ta kwanta a kan tile yadda taga rana hk taga dare sai zuwa can kusa da asuba bacci 6arawo ya saceta.
Shima safraz hk yake a 6angarensa be rintsa ba sai dayaji ankusa tayar da salla a masallaci sannan ya shiga toilet yayi alwala.
 Yabud’e k’ofar dan fita masallacin kenan yaganta kwance a bakin k’ofar tayi fillo da d’an kwalinta gashin kanta ya rufe fuskarta bacci takeyi tana sauk’ar da ajiyar zuciya alamu tayi kuka har ta gaji.
 kwalla yaji tana neman zubowa a idonsa da sauri ya danne, hannayensa yass ta d’auke ya nufi d’akinta, har kan gado ya kaita sannan ya janyo bedshit ya lullu6eta  dashi ya fice.
 Ko daya dawo dg masallacin ya lek’a yaga bata tashiba sai ya wuce d’akinsa.
  I zzatu farkawa tayi ta ganta a d’akinta batayi mamakiba tasan safraz ne ya kawota, bayan tayi sallah akan sallar bacci yakuma kwasheta Sai k’arfe 8 ta tashi.
Jitayi gidan ya d’au kashin turare me dad’i, toilet ta shiga tayi wanka ta shirya cikin bak’ar doguwar riga me dogon hannu d’an kwalin rigar ta yafa a kanta ta fito falo, ga mamakinta sai taga an gyara ko ina tsab_tsab sai ganshin turare ke tashi a falon,  tana cikin mamaki ma’u ta shigo falon d’auke da kayan abinci Abu tana biye mata baya itama da kaya a hannunta.
 Deining table suka wuce suka jere kayan, sannan suka nufo inda izzatu take tsaye. dukkansu suka zube k’asa.
Ma’u tace, hajiya ina kwana?
Izzatu ta amsa da lpy tana murmushin yak’e.
Abu ba ta gyara murya tamkar mace tace, Batka da safiya hajiya dafatan ku tashi lpy?
Izzatu ta kalleta tace, lpy qlau. suna had’a ido da Abu gaban izzatu ya yanke ya fad’i tas!hk kawai idanuwan matar yayi mata kama da mutumin daya shigomata jiya ammah kasancewar Abu tasa jambaki sasu goda harda eyeshadow yasa kamar ta so ta 6ace.
Ma’u tace, mu masu aikine da aka d’aiko jiya nasan Alhaji ya sanar miki d’akinmu yana dg wajen lambu bayan wannan part d’in, mungama komai ko akwai abinda za’ayi miki ?
Izzatu tayi murmushi tace, Ayyah sannunku babu komai ku huta hk kunsha aiki.
Ma’u ta kuma cewa, idan kinban izini zanje in gyara miki d’akinki.
Izzatu tace, A’a ku ht hk babu komai zan gyara zuwa anjima.
Abu tace, a’a hajiya yana dg cikin aikin da hajiya wato mahaifiyar mijinki tace mudinga yi d’akin mijinki ne kawai bamu da hakkin gyarawa ki barmu muyi kar musaki wahala ranki ya dad’e.
murmushi izzatu takumayi tace, to shikenan kuyi ammah ai bawani aiki bane me wuya da kun barshi.
Ma’u tace, ai tace kar mu barki ki d’au koda tsinke inda muna nan.
Izzatu tace , Allah sarki nagode ya sunaku?
ma’u tace ni sunan ma’u itakuma wannan yayatace sunanta Abbu.
Izzatu tace, Ayyah sannunku da k’ok’ari nagode.
Abu tace, mune da godiya hajiya, sannan Abu ta kalli ma’u tace kije ke ki gyara d’akin ni zanje in gyara kitchen inyi wanke_wanke.
Izzatu data gaji da jira safraz bai fito ba dan hk itama ta koma d’akinta aikuwa tas ta ganshi sai k’anshi dake tashi a d’akin har toilet duk anwanke tsab.  Kayan mutumin nan ta gani ma’u ta ninke ta d’ora mata a kan gado sai taji hawaye na zuba a idonta aranta tace ‘wato  ma’u tayi zaton ko kayan mijina ne’  window ta zuge ta watsasu ta baya.
Tsawon sati d’aya Haka izzatu da safraz suka ciga da rayuwa alokacin amarci ammah su yazama lokacin kunci da damuwa domin babu abinda yake had’asu sai gaisuwa wani lokacin ma ko izzatu ta gaishesa baya amsawa, sai dai duk randa ta wuni bata fito faloba hankalinsa zai tashi sai yaje yaga abinda yake faruwa abinci ma wani lokacin idan yaga bataje deining taciba har d’akinta yake zuwa ya kawo mata shidai kawai sam bayan ta masa mgn sabida ya kasa manta abinda yagani a daren farkon su.
 Satinsu biyu da yin aure iyayen izzatu zukazo yimata sallama domin zasu tafi k’asar America wani aiki ya tasowa babanta itama mahaiyarta zata bisa, Izzatu rayi kuka kamar ranta zai fita har ummi wato mahaifiyarta taso ta gane akwai matsala a zamantakewa aurenta da safraz, sun rabu dukkansu suna jimami domin izzatu ita d’ayace ‘ya agurinsu.
Alokacin da sukayi wata d’aya cif da aure izzatu duk tabi ta rame ta kod’e kamar wacce bata da jini ajikinta, Babu abinda ya canza tsakaninta da safraz kullum idan ya fita office tun safe sai yamma yake dawowa, tayi masa zancen komarta makaranta tunda ashekarar k’arshe take zata kammla degree d’inta  ammah yace bai yarda ba zata dinga had’uwa da mutumin dazo masa gidane dan hk ta hakura da karatun ba yadda ta iya hk ta hakura kullum cikin zubda hawaye takeyi, wani lokacin mami tana zuwa ta dubata tana janta jiki sosai hkm shahida da sakina suna zuwa mata lokaci zuwa lokaci.
Ba wanda yasan halin da suke ciki jafar abokin safraz daya fahimci akwai abinda yake damun safraz daya tambayesa yak’i fad’amasa idan ya takura sai yace masa kawai bayanson ya bar izzatu agida ita d’ayane abinne yake damunsa,
Momy kuwa har ta gaji da zura ido taga me safraz zaiyi ammah shuru, ammah tabbas ta fahimci basa zaune qlau shida izzatu domin fuskar izzatu cike take da damuwa duk sanda taje gidan, mami kuwa duk ta d’auka ko izzatu ta fara laulayi ne shiyasa bata tambayarta meke damunta.
Yau ya kasance watan izzatu d’aya harda sati d’aya dayin aure, tana zaune a a falon safraz yayi sallama ya shigo ya dawo dg office.
Izzatu tace, sannu da zuwa.
safraz bai kalli inda takeba yace, yauwa sannu.
Taje tasa hannu dan ta kar6i jakar hannunsa ammah yace ta barshi. d’akinsa ya wuce ya shiga.
Yayi kamar mintuna talatin da shiga izzatu ta tashi ta shiga d’akin itama, wannan shine karo na farkon data ta6a shiga d’akin safraz duk sanda tazo shiga akulle take samu kota buga baya bud’ewa.
A dai_dai lokacin data shigo safraz ya fito dg wanka d’aure da towel, da sauri ta sunkuyar da kanta k’asa.

Kanta a sunkuye kunya ta kamata, “Da tasan zata shigo ta sameshi hk da bata shigoba” sai taji kamar ta koma da baya.

  Shima safraz mamaki yakeyi ganin izzatu a d’akinsa  ammah duk da hk yaji dad’in biyoshi da tayi dan sau da dama yana son zuwa d’akinta ammah sai ya kasa musamman idan ya tuna ganinta da yayi da wani najimin ammah ko kad’an har yanzu baiji zai iya hakura da izzatu saboda abinda ta aikata masa ba saima matsanancin sonta da kullum yake k’ara shiga zuciyarsa awani 6angaren kuma yana feeling d’inta kamar ya mutu ya rasa taya zai tinkareta bayan tayi mu’amala da wani bashiba idan ya tuna bazai sameta a budurwa saiji duk duniya tayi masa zafi.

A hankali ya zauna a gefen gadon yana binta da kallo har zuwa lokacin kanta yana k’asa a sunkuye. wani 6arin na zuciyarsa yana cemasa” anya bana cutar da izzatu ?laifin da tayimin ya kai na k’aurace mata hk inason izzatu a raina kamar ny hauka ammah daren aurenmu na farko na kama izzatu da k’warto a gida meyasa baxanyi hakuri na rungumi matata muyu rayuwar farinciki ba sai dai na kasa mantawa da abinda idanuwana suka gani”

Katse tunaninsa yayi da cewa, Izzatu !
A sanyaye ta d’ago kanta tace, na’am.
Sai ya rasa me zaice mata kawai sai yace, kina buk’atar wani abune ?

Izzatu tace, a’a um um inason muyi mgn ne dama ammah bari naje falo kafin ka gama.
Tana gm fad’in hk tayi sauri ta juya zata fita.
K’irjinsa ne ya fara dukan uku_uku a ransa yana tunanin  “maganar me izzatu zata fad’amasa kodai zatace ta gaji da zama da shine hk’? hk kawai yaji ya damu kuma yaji zaman da sukeyi kamar lefinsa ne bata da wani laifi.

Cikin hanzari ya bita ya rok’o hannunta alokacin har ta murd’a hannun k’ofar zata fita.
Muryansa a k’asa_k’asa yace, muje ki tayani saka kaya mana Reality dm ko bakizoba yau zanzo gurinki in baki……
Sai kuma yayi shuru ya kasa k’arasawa.
Izzatu kuwa har cikin ranta taji dad’in abinda yace ammah tana cike da kunyarsa ji takeyi kamar tayi hugging d’insa ko zata rage kewar dad’ad’an kalamansa da tayi tun kafin suyi aure.
Kasa yimasa musu tayi hannunta yaja har gaban sif d’in kayansa sannan ya kalleta yace,  za6amin kayan da zansa reality.
Sai data gama k’arewa sif d’in kallo sannan ta d’auko wata bak’ar T_shirt da breeches wato k’aramin wandon daya wuce gwuiwa kad’an shima bak’i.
  Kallonta yayi yay murmushi yace, Nice colour reality, muje ki gyaramin gashin kaina ki shafamin mai sannan kisamin k……
Sai yayi shuru bai k’arasaba yana kallonta ta gefen ido.

Mamakine ya cika ran izzatu sosai gani takeyi kamar ba safraz bane a gabanta yake wannan maganar, ga kunyarsa da takeji musamman idan ta tuna abinda ya faro a first night d’insu.

gefen gadon ya zauna bayan ya kwaso mata abubuwan da zatayi masa amfani dasu.

mayukan ta d’auka tana dubawa tana karanta batare data tambayesa ba.

A hankalin take shafa masa mai ajikinsa tamkar wacce bata jini ajikinta, shikuwa safraz rufe idonsa yayi sun masa nauyi sam ya kasa bud’ewa har ta gama, sannan ta fara gyara gashin kansa dake kwance tamkar na jinjiri tana shafa masa mai d’aya bayan d’aya.

Na gama izzatu ta fad’a sai alokacin ya bud’e idonsa dasuka sauya dg fari zuwa ja, da ido ya nuna mata kayan,

Ringar ta d’auka ta fr k’ok’arin saka masa har ta gama sannan ta d’au wandon ta rik’e a hannunta kawai ta rasa yaya zatayi, zuwa can safraz yaji shuru sai ya bud’e idonsa yana kallonta, yanayinta daya gani ne yasa ya gane kunya takeji sai yasa hannu ya kar6a yasa da kanshi.

Mik’ewa tsaye yayi sannanya rik’e hannunta yace, zo muje in rakaki d’aki kiyi wanka ko zakaiyi a nan ?ya d’afa mt girarsa.

Murya k’asa_k’asa tace, Ban dad’e dayin wanka ba.

Safraz yace, Okay muje falo sai ki fad’amin maganar.

tare suka jera har zuwa babban falon, daf da daf suka zauna.

Zuciyar safraz tana cike da tsoron jin abinda izzatu zata fad’amasa  sai zulumi yakeyi, tsoronsa d’aya kar ta furta abinda yake zargi.

Dan ya shashantar da maganar sai ya kalleta yace, madam nifa yunwa nakeji zo muje muci abicci sai muyi maganar dg baya kou?

Bata masa musuba ta tashi ta bishi tajin dad’in  yadda suke a tare yau, tanaji a ranta “koma kawai ta fasa yimasa zancen da zata yimasa ammah wata zuciyar tana cewa a’a kiyimasa kikasani kou ya koma kamar da d’in” da hk suka isa deining itace tayi saved d’insa bata zubawa kantaba, Abinda yakuma faranta ranta a baki safraz yadinga bata har ya tabbatar ta k’oshi.

Bayan sun kammala safraz ya kalleta ammah duk da hk yanajin fargaba a ransa shi yanajin a ransa “zai manta da komai kamar ba’ayiba ya nunawa matarsa irin sonta dayakeyi” safraz yace, Reality ina saurarenki.

Izzatu da fuskarta ta nuna alamun damuwa tace, Dama inason in bk hakuri ne akan abinda ya faru, zaman da mukeyi ni dai hkn yana damuna kayi hakuri dan Allah.

Sai alokacin safraz yayi ajiyar zuciya daya tabbatar ba abinda yake tsammani zt fad’aba, yace, izzatu koni naso na danne namanta dashi  ammah na kasa babu abinda yafi 6atamin rai da kikak’i yarda kin aikata kikace sharri ne, ammah yanxu kinyarda ?

Kwallace ta cika idanuwanta zuciyarta na bugawa da k’arfi tanajin rad’ad’i me zafi a ranta “Allah ya isa tsanina da duk wanda ya kullamin wannan sharrin, ya Allah ka bani mafita” izzatu ta fad’a a ranta.

Safraz yace, izzatu ina saurarenki ni wallahi idan kika fad’amin gaskiya babu wanda zan fad’awa idan kinajin tsoron ko zan fad’a i will keep your secret.

Wani 6arin na zuciyar izzatu yace mt” gara ki amince kinyi laifin akan ku ringa irin wannan zaman tunda yace bawanda zai fad’awa”

A hankalin ta d’aga idonta da suke cike da kwalla tace, am!kayi hakuri na yarda, sai ta fashe da kuka me ban tausayi.

A firgice ya d’aga idonsa ya kalleta nan da nan yaji  jikinsa ya d’au rawa kanshi yana juyawa.

Itama kuka yaci k’arfinta atake taji kuma nadama tazo mata tafara dana sanin amsa laifin da batayiba.

_IZZATU DA TAKE BANI LABARIN HAWAYE NABIN IDONTA TA KALLENI TACE, RAMLERT AMSA LAIFIN DA BANYIBA WANNAN SHINE BABBAN *KUSKURENA* NAYI DANASANI MARA AMFANI.TACIGABA DA BANI LABARIN KAMAR HK……_

Idonsa sunyi jajajir fuskarshi a d’aure yace, meye amfanin hkn da kika aikata?dama kin kasance kinayi meyasa da kikayi aure bazaki hakura ba?izzatu ko dm bakya sonane?

Batace masa komaiba tacigaba da kuka tana takaicin amsa laifin da tayi.

Sai kuma taji zuciyarta ta dake kwata_kwata rayuwar auren ta fita a ranta.

Muryanta  a dake tace, safraz bani da banki da zancema komai ammah dan Allah inason ka sauwak’emin na koma gaban iyayena hkn zaifi.

A afirgice ya kalleta ransa yayi matuk’ar 6aci cikin 6acin rai yace,  harni zaki kalla kice na sauwak’e miki ?ke da yin laifi ammah ni da kika yiwa laifin bance zan sauwak’e miki ba sai ke?dama kinsan bakya sona why zaki yarda ki aureni ko kina nufin kin aureni ne dan ki dinga kawomin kwartayanki gidana ?Impossible wallahi, Kinason in sakeki kou?kibari zanyi tunani idan na,yankw hukunci zakigani *fasik’a* kawai. Yaja tsaki tare da buga table dake gabansa.

Hawaye nabin fiskarta tace, safraz nice fasik’a?karka k’ara cemin fasik’a niba fasik’a bace. Cikin sanyin murya ta fad’a tana kallonsa ido cikin ido.

A harxuk’e yace, nafad’a fasik’a kuma mazinaciya idan banda fasik’acin kafin kiyi aure kina aikata zina bayan kinyi aure mezaisa kiyi?wallahi izzatu kin cuceni idan badan darajar mahaifinki ba dana hakura dake idan yaso ciwon sanki ya kasheni ammah ina duba halin da iyayenki zasu shiga idan suka sani ‘yarsu dy tilo abinda takeyi, kin bani kunya sun d’au son duniya sun d’oramiki ammah kinci amarsu tir dame hali irin naki izzatu.

Yana gm fad’an hk ya tashi ya bar gurin ya wuce d’akinsa.

Kasan tile izzatu ta zube tana kuka me d’aga hankali da ban tausayi, ta dad’e tana kuka har kanta ya fr ciwo dan kar masu aiki su shigo kwashe kayan dasukaci abinci su ganta yasa ta tashi da k’yar tawuce d’akinta.

Safraz yana shiga d’akinsa ya fad’a gado shima kuka yayi sosai har ya gode Allah, sai da kukan nashi ya lafa sannan ya tashi zaune, sai kuma alokacin ya fr danasanin abinda yayi mata tausayinta ya kamashi kamar yaje ya bt hakuri sai km yaji bazai iyaba.
Izzatu meyasa zakimin hk?inasonki kamar na mutu why do that to me?dm bakicemin kinyarda ba dama kinkuma cemin sharri akayi miki, Yazanyi da raina Allah hk kaso ka ganni, hk safraz yadinga sambatu shi kad’e har bacci ya fr d’aukarsa.

Karima ce dg can england rik’e da waya a hannunta tana magana:

haba momy ni wallahi na gaji da gafara sa banga k’ahoba yanzu fa harsunyi wata d’aya dayin aure ammah shuru babu wani labari.

momy tace, nima dai abun ya d’auremin kai sosai ammah da masu aikin sun sanarmin kamar basa zaman lafiya dan tun safe yake fita by dawowa sai yamma kinga babu wani zaman lpy a tsaninsu ni a tunanima yarinyar nan ba hk ta barsaba ta asircesa ammah idan banda hk ya kamata da k’warto ammah har yanxu suna tare.

karima tace, momy yanxu to yaya za’ayi?saura baifi wata dy ba na kammala karatuna yanzu hk saura 5 days musamu hutu na 3 weeks sannan mu dawi muyi final exam. yanxu zanzo nayi hutu ns 3 weeks a nigeria inason kafin na dawo ayi waje da ita gaskiya.

Momy tace, ki kwantar da hankalinki koda bata ft ba idan kika shiga zan fad’amiki yadda zakiyi ki fidda ita,  nizanfi so idanma kinzo hutun kawai a d’aura auren idan yaso sai ki koma kiyi exam d’inki idan kin dawo saiki tare kou?

karima tace, Wow!wallahi hkne momy shiyasa nakesonki sosai fa!momy sai naxo kawai.

A dai_dai lokacin sakina tashigo falon momy hkne yasa momy ta kashe wayar dan kar taji mesuke cewa.

sakina ta kalli momy tace, momy nasa da aunty kuke waya kou?wai momu haryanxu baku hakura da zancen safraz bane?ni dai har kullum ina k’ara fad”a muku  kuji tsoron Allah. yanxu idan akayiwa big bro dole ya auri aunty kina tinanin za’ayi zaman lpy kuwa?wallahi matarsa me mutunci bata da fitina ammah aunty fa masifa tayi mt yawa zata dinga kawo rigima iri_iri.

Momy cikin tsawa tace, ke!zancimiki wallahi sakarya kawai sha_shar banza, karna k’arajin wannan zancen a bakinki kona 6atamiki rai wallahi.

Sakina tace, Allah ya baki hakuri momy ban fad’a danna 6atamiki raiba.

Momy taja tsaki sannan tace, tafi can kibani waje sai iya ladabi kamar gaske, nawa kika samu ciromin ?

Momy bank d’in da layi saosai shiyasa na dad’e ammah abin yaban mamaki sosai me akayi da million d’aya momy ?yaushe aka cire?

momy tace, babu ruwanki bani sakona.

Kud’in ta mik’amata sannan tace, yauwa momy yau na had’u da kawu a banki yace na gaisheku, yana tacemin sailuba!sailuba ammah sam bangane da ni yakeba sai da wasu sukamin mgn.

momy tace, hym!muna amsawa.

sakina takuma cewa, yauwa momy meyass akadena k’irana da sailuba aka kuma sakina?

Momy tace, Dangin ubankune da wannan kinibibin da tsohon cikinki babanku yarasu bayan na haife sukace wai asamiki sunan ‘yar autarsu sailuba nikuma naga bsbu wanda yamin rainon cikinki balle rainon goyo shiyasa nake k’iranki da sunan da na za6a bawai za6insuba.

Sakina tayi murmushi tace, kai momy ai da kin barsu da ba’a rabamin sunaba.

momy tace to uwata. tare da harararna, ni tashi ki d’aukomin jakana driver ya kaini gidansu shahida.

***
**
*

Karima dake zaune ita da wata k’awarta aminiyarta fauzan, alokacin da karima ta gm waya sai fauzan ta kalleta tace,

wai ya ake cikine ?
karima ta kwashe duk sharrin da suka lak’anawa izzatu ta fad’awa fauzan, sannan ta k’ara da ceea, ammah kinsan me?haryanxu bai saketa ba tanan a gidan munafuka.

fauzan tayi dariya tayi shewa tace, lallai ke wawuya ce waya fad’amiki hk ta barshi ai tini ta gm dashi da asiri, idan zakice zaki jira sai ta ft sannan zaki shiga to ai kin tabka babban *KUSKUREN* ai kawai malama tunda har kinsamu za’asashi ya aure dole to ki shiga kawai inyaso k’yasan yadda zakiyi dh baya ammah idan kika tsaya kallon ruwa to kwad’o zai miki k’afa.

Karima tace, hkne fa kou?sis

**************************

Rayuwar izzatu abin tausayi komai yakuma jagulewa babu abinda yake had’ata da safraz

Momy tace, Dangin ubankune da wannan kinibibin da tsohon cikinki babanku yarasu bayan na haife sukace wai asamiki sunan ‘yar autarsu sailuba nikuma naga bsbu wanda yamin rainon cikinki balle rainon goyo shiyasa nake k’iranki da sunan da na za6a bawai za6insuba.

Sakina tayi murmushi tace, kai momy ai da kin barsu da ba’a rabamin sunaba.

momy tace to uwata. tare da harararna, ni tashi ki d’aukomin jakana driver ya kaini gidansu shahida.

***
**
*

Karima dake zaune ita da wata k’awarta aminiyarta fauzan, alokacin da karima ta gm waya sai fauzan ta kalleta tace,

wai ya ake cikine ?
karima ta kwashe duk sharrin da suka lak’anawa izzatu ta fad’awa fauzan, sannan ta k’ara da ceea, ammah kinsan me?haryanxu bai saketa ba tanan a gidan munafuka.

fauzan tayi dariya tayi shewa tace, lallai ke wawuya ce waya fad’amiki hk ta barshi ai tini ta gm dashi da asiri, idan zakice zaki jira sai ta ft sannan zaki shiga to ai kin tabka babban *KUSKUREN* ai kawai malama tunda har kinsamu za’asashi ya aure dole to ki shiga kawai inyaso k’yasan yadda zakiyi dh baya ammah idan kika tsaya kallon ruwa to kwad’o zai miki k’afa.

Karima tace, hkne fa kou?sis

fauzan tace, ni na d’auka ke wayis ace dod’isce mtsss

Hk suka dinga hirarrakinsu du akan izzatu.

**************************

Rayuwar izzatu abin tausayi komai yakuma jagulewa babu abinda yake had’ata da safraz ko giftawarsa ma yanxu tadena gani sai dai wani lokacin taji motsacinsa hk sukeciki har tsawon sati d’aya, kusan kullum sai tayi waya da iyayenta ammah bata bari sun fahimci tana wt matsalaba, sakina da shahida suna zuea mata sosai sun shak’u da ita sosai wani lokacin harda shahid, yanxu harta saba da rayuwarta a hk ta rage damuwa wani lokacin tayi kallo ko cht hkm k’awayenta suna kawo mt ziyara duk da ba wasu k’awayene da itaba dg sumayyah, Aisha sai firdausee k’awayenta ne na university.

Izzatu tana zaune a falo tana kallon tashar TV ta Arew24 sai jin sallamar mami tayi, zuwa tayi ta tarota cikin farinciki da jin dad’i,

Bayan sun gaisa ta kawowa mami kayan motsa baki, sun dad’e suna hira  sannan mami ta kalli izzatu tace,

izzatu nazone inason muyi wata magana.

Dub!k’irjin izzatu ya buga, “kar dai safraz ya fad’awa maminsa abinda ya faru”? izzatu ta fad’a a rabta.

A tsorace izzatu ta d’ago ta kalli mami, alamun tashin hankalin suka bayyana a fuskarta.
Mami tace, inason ki nutsu izzatu dan abinda zan fad’amiki ba lallai yamiki dad’i ba.
 Jitayi kamar falon yana juyawa zuciyarta sai harbawa takeyi “wato abinda take zargi ya tabbata mami tasan zancen kenan” izzatu take sak’awa a ranta.
Mami takuma cewa, Izzatu nasan kina da ilimi kuma da hankali, ki k’ar6i abun da zan fad’amiki a matsayin k’addararki karki tashi hankalinki, kinga a yau kuke da wata d’aya harda sati biyu keda safraz dayin aure, safraz zai k’ara aure nan da sati biyu masu zuwa izzatu kiyi hakuri badan baya sanki ba sai dan hk Allah ya k’ddara.
A firgice izzatu ta ware manyan idanuwanta tana kallon mami, nan da nan kuwa hawaye ya suka fara rolling into her checks. muryanta na rawa tace, ma  mi wal  lahi nafad’amasa ba……
 Sai mami tayi cuting d’inta da cewa, pls izzatu wipe your eyes wallahi safraz shi da kanshi bayason k’ara auren da bayadda zaiyi ne shiyasa. nasan kinaso ki cemin kin fad’a masa bakyason kishiya kou?kiyi hakuri ki saurareni zaki fahimta insha Allah.
 Sai alokacin izzatu ta fahimci ba abinda take tunanin mami zata fad’amataba, Amma hankalinta ya kasa kwanciya sabida zancen safraz zai k’ara aure.
Mami ta kalleta tace, Nice da kaina na bashi umarnin sai ya k’ara aure ammah ba wai shine yace zai k’ara da kanshi ba, kuma nima banyi hk danna k’untata mikiba izzatu, wallahi nima umarni ne na yayata bayadda na iya dashi nasan kinsan momynsu sakina yayata mu kad’ai ne awajen iyayenmu izzatu, akwai yayar sakina sunanta karima itace ‘yar aunty adama ta farko yarinyar tanason safraz tun kafin ta tafi karatu england to hkn ne yasa aunty adama tazomin da zancen tun kafin aurenku keda safraz ba yadda na iya nima na tuntu6i,safraz da zancen ammah ya nunamin shi bayaso ban k’ara yi masa zancen ba har lokacin daya had’u dake kuka fara soyayyah alokacin da zancen aurenku ya bayyana sai aunty adama ta nunamin 6acin ranta sosai akan dole safraz ya auri ‘yarta sakina tanason mu k’ulla zumuncin, hakuri na dinga bata akan cewa ta barshi ya aureki idan yaso dg baya sai ya auri karima tunda anriga da anyi maganar aurensa da ke kuma shiya ganki yce yanaso, akan hk muka bar zancen izzatu ni nasan safraz bayason karima ko kad’an ammah bayadda zanyi auty adama ta fahimceni shiyasa nabi umarnin ammah nima badan nasoba sabida itace tazamamin uwa alokacin da muka rasa iyayenmu.
Nasani cewa na cutar da safraz nayi masa dole kema nashiga rayuwarki wasu ma zasuyi tsammanin wani mummunan abine yasa mijinki k’ara aure tun baki dad’e agidansa ba, ko ajiya dana,k’ira safraz nace,masa ya fad’amiki cewa yayimin wallahi shi bazai iyaba sabida zai tayar miki da hankalin kuka ya dingayimin sosai wai bayason abinda zai sa ki damuwa kuma zakiyi tunanin yaudararki kawai yayi ya aureki, nima nashiga damuwa sosai ganin halin daya shiga, anan na sanar masa dama niyafi dace nazo na fad’amiki ammah na masa alk’awarin indai hankalinki ya tashi kuma baki amince ba to zan janye umarnin  danayi masa na auren karima dan ku zauna lpy, izzatu ina rok’onki dan Allah ki bani goyon baya akan zancen nan, nasani inhar na baki labarin irin halaccin da aunty adama tamin a baya to kema zakiga cewa bai dace na juyawa buk’atarta ba.
 Tabbas aunty adama tayi matuk’ar k’ok’ari akaina, Iyayenmu bawasu masu k’arfi bane talakawa ne, Muna rayuwa cikin rufin asiri akaha har akayiwa aunty adama aure ya rage saura ni kaid’e alokacin ina da shekaru12, Awata damuna da akayi a can baya watarana akayi ruwa mai k’arki da dare fi sai d’akin da ummanmu da babanmu suke kwance ya rushe akansu wannan shine sanadin rasuwarsu.
   Bayan anyi arba’in d’insu aunty adama ta sanar da dangin mahaifanmu cewa tanason ta d’aukeni na koma zama a wajenta hk akayi ba wanda ya hanata mijinta ma ya amince.
  A gabanta na cigaba da rayuwa tana ‘yan sana’o’in hannun dasu take biyamin kud’in makaranta har na gama primary na shiga secondary,  Muna cikin rayuwa ahaka sai Allah yayiwa mijinta rasuwa.
 A hk muka koma gidan yayan babanmu shima dai bashi da wani k’arfi kusanma aunty adamace take ciyar mu ni da ita domin matansa basa bamu abinci ko yaushe ga wulakanci da rashin mutunci kala_kala, aunty adama ta kuma yin wani auren ammah wanda ta aura yana da mata guda biyu itace ta uku, bata dad’e dayin aureba namma ta d’aukeni na koma gabanta da zama domin tasan irin zaman gidan yayan babanmu, to muna cikin hk har naje secondary aji hud’u ammah sai dai yaran mijinta sun takuramin sosai agola suke cemin, ‘yar talakawa wai su nufinsu ni amakarantar gomnati nake sukuma amakaranta kud’i suke, wani lokacin sumin duka sosai, idan aunty adama tayi mgn mijinta yace shifa baxa’a takura yaransaba su da gidan ubansu, kullum cikin matsalan muku da aunty adama ta gaji sai ta fara ramamin duk yarinyar data dakeni, shima mijin idan matansa suka fad’a masa sai yazo ya daki aunty adama hk zamu zauna,muyi kuka a d’aki har mu gaji, A na hk watarana badawo daga makaranta ina shigowa suka fr tsokana ta dasukaga namu shuru sai duka a nan sukamin duka sosai dukkansu ‘yammata kamarni 15 years, a ranarma aunty adama ta ramamin, dana fita zanje kanti na siyo aunty adama fulawa domin tanayin fanken siyarwa da safe duk dan inyi karatu, sai suka bini hanya sukamin dukan tsiya nayi wujiga_wujiga har kaina ya fashe abinka da farar fata tuni fatata tayi rud’u_rud’u, a hanya na fad’i sai kawoni gida akayi.
 Ko wanne  asibiti aka kaini sai suk’i k’ar6ata wai dole sai da ‘yan sanda saboda ciwokan dake jikina, aka muka dinga wayo asibiti zuwa asibiti a k’arshe dole sai da Aunty adama taje police station ta d’au d’an sanda sannan aka dubani.
  Bayan angama komai anrubuta min magani an sallameni, Sai ‘yan sandan suka tambayeni wayamin hk, Na fad’amusu , sukace ai dole sai sun kaiwa mahaifin yaran dasuka dakeni sammaci, A nan aunty adama tace dasu a’a ai ‘yan’uwane ta yafe zatayiba masa mgn da kanta, ‘yan sanda sukak’i dole hk suka bimu har gida.
 Alokacin da muka iso gida shima mijin aunty adama a dai_dai lokacin yana gida, ba yadda aunty adama batayiba ammah sai da suka tafi dashi, wajen k’arfe 10 na dare sai gashi ya dawo nan ya dingawa aunty adama masifa wai ta d’ebo masa ‘yansanda akan k’anwarta wai dole sai dai ta za6i d’aya ko dai ta maidani gida ko kuma ya saketa,  da safe yakuma shigowa d’akinta ya tambayeta tace masa ita sai baxata iya maidani gidaba inhar yaga bazai iya zama da ita tare daniba   to shikenan ya sauwak’e mata.
Hk muka koma gidan kawu da zama yau da dad’i gobe babu dad’i, Duk wanda ya fito neman auren aunty adama sai tace masa inya amince zata d’auke ammah duk yawancinsu saisu k’i, dg k’arshe tace bazatayi aureba har sai na kammala karatuna nayi aure sai itama tayi.
 Ita ta ringa d’aukan nauyin karatuna da sana’o’in hannu da takeyi har naje 2 hundred level a university, Anan ne na had’u da Abbansu safraz alokacin shikuma  lecturer a university d’in, Ya taimakamin sosai ina karatu mun fr soyayyah har naje 4 hundred level ina cikin watan k’arshe a school aka sa ranar aurenmu dashi, shi kuma alokacin  ya k’aro karatu ya tashi dg lecturer duwa Dr.
Akawana Atashi babu wuya na kammala karatuna na fita da first class, University dana gama karatu acikinta su suka d’aukeni aiki, Anan rayuwa ta kuma canzs mana,muka fr mantawa da wahalhalun rayuwa domin na fara d’aukan albashi every my month ga Dr hashim shima yana min kyaututtuka sosai, Ahk har lokacin bikinmu yayi aunty adama tayi bajinta sosai da sosai domin tamin kayan d’aki da kayan kitchen masi tsada da kyau da sauran kayayyaki dukda shima Dr hashim yabani kud’i masu yawa, hk akayi biki aka kaini gidana.
Nayi haihuwa ta farko safraz kenan, sai bayan shekaru biyar bayan na haifi safraz sannan aunty adama tayi aure, albashina biyu muke rabawa ni da ita duk wata, safraz yana sa wajen shekaru 13 sannan aunty adama ta haifi karima,  bayan 2years takuma haihuwar sakina tunkafin a haifi sakina mijin aunty adama ya rasu da wata biyar nima na kuma haihuar shahid da shahida.
A lokacin Abban su safraz ya fara siyasa lokacin kud’i suna shigomin sosai hakan yasa na ginawa aunty adama babban gida ta dawo ciki ita da yaranta biyu, karima na kammala secondary na d’au nauyinta ta tafi england karatu duk dan inason aunty adama tayi alfahari dani kamar yadda naji dad’in kulawar da tayi akaina,
Mami ta kalli izzatu tace, izzatu wannan shine labarina wanda akwai abubuwa da dama wanda na tak’aicesu kyautatawar da tayimin ina yarinya izzatu wannan yasa bazan iya kallon idonta nace a’a ba, mutum ce me zafi wani lokacin shiyasa nakeson inbita a sannu dan wallahi mutane da yawa sun d’auka itace ta haifeni, pls do me a favor, kowa da irin k’addararsa mu kinga munyi rayuwar wahala a baya ammah yanxu kinga _*BAYAN WUYA SAI DAD’I*_(my fomer book).
 Nasan kwanciyar hankalinki shine samun nutsuwar safraz, keda safraz ba banbanci awajena a yanxu izzatu.
Sai izzatu taji kwarin gwuiwa sosai a ranta jin labarin mami datayi, sai tasa a ranta itama wannan itace k’addararta , sai taji a ranta tabbas tayi babban _*KUSKURE*_ zaman da sukeyi da safraz ba ruwan wani da wani kamata yayi ta gyara _*KUSKUREN*_ ta tunkafin wata taxo ta k’ace mata miji wanda tana da tabbacin yana masifar sonta.
Da kwarin gwuiwan izzatu ya d’ago ta kalli mami tace, mami kinfi k’arfin ki nemi alfarma koki rok’eni, umarnin kawai zaki bani kuma dole nabi domin uwace ke wajena, mami namiki alk’warin zaman py dani da karima da safraz  insha Allah. Ke uwace ta gari kuma wacce za’ayi alfahari da ita domin kina k’ok’arin rama alkhairi da alkhairi tsakaninki da momynsu sakina tabbas ta cancanci kiyimata fiye da hk ma, bayan nanma karima koda bayan babu momy kece me za6a mata miji, ina alfahari da wannan had’in mami Allah ya tabbatar da alkhairi.
Mami taji dad’i sosai aranta da kalaman izzatu tana murmushi tace, izzatu naji dad’i sosai gaskiya Allah ya miki albarka kinji Allah ya baku zaman lpy, nayi farinciki sosai izzatu Allah ya miki albarka.
Sun dad’e tare sai yamma mami tabar gidan, shikuwa safraz sam hankalinsa kasa kwanciya yayi a wunin ranar ga ayyuka masu mahimmanci a office ammah ya kasayi tunaninsa d’aya idan izzatu yaji zancen nan mezai faru, koda ya taso dg office gidan mami ya nufa domin sanin halin da izzatu ta kasance lokacin sa mami ta fad’a mata.
A main falo ya tarar dasu dukkan su har Abbansu, dasuka gaisa Abbansu ya kalli shahid da shahida yace, twins give me a space. Tare suka bar falon sannan Abba yayi gyaran murya ya kalli safraz yace, Am safraz naji dukkanin zance dg bakin mahaifiyarka but am not satisfy i need explanation i am listening to you.
Safraz da bashida za6i daya wuce ya kare mahaifiyarsa ya d’ago yace, Hkne Abba there’s relationship between karima and i since before she want  england to study, but i think she don’t marry me if she cameback this why i get marriage with izzatu but i still love her i want to marry her that all.
Abba yace, hym!i understood but is too early to get marriage again now, because you only spented one month and something with izzatu’s married now you have to stop like one year or so.
Safraz har ransa yaji dad’in abinda Abbansa ya fad’a ammah sai ya tuna mami sai ya kalli Abba yace, Abba izzatu is a easy going lady she already understand my point and accepted, but karima is expecting i am try to deceive her  pls Abba allow me to marry her now they will leave peacefully insha Allah.
Abba yace, shikenan is allright i can’t reject your request safraz you have a chance to marry more then two wavies, But try to do justice between them don’t be a selfish man, may Allah assist you.
Safraz yace, Amen Abba.
besamu damat tambayar mami ba saboda  Abbansu yana gurin hk ya tafi.
 Safraz yana zuwa bakin k’ofar falon zai shiga yaji wani k’amshi ya doki hancinsa, Labulene ya fara yimasa sallama da wani daddad’an k’amshi, da sallama ya shiga ammah sai ya tsaya turusa ya kasa gaba ko baya, Izzatu ya gani ta fito dg kitchen d’in dake falon d’auke da kayan abinci a hannunta, sanye take da mini skirt bekai gwuiwaryaba sai ‘yar wata top itama bata rufe cibiyartaba me k’aramin hannu ga gashin kanta ya sauk’o kan kafad’unta sai shek’i yakeyi, fuskarta d’auke da simple makeup.
Deining taje ta ajiye kayan da yake hannunta ta taho da gudunta tana cewa:
 Oyoyo reality, tana isowa ta rungumesa so tight sannan she kiss him in his rehead and check.
March 3,  is special day for me, because it’s the day of my   _BIRTHDAY_  I congratulated myself _20_ Years in the world, I beseech Allah to forgive me about what I did and accept what I will do in the future.*
_*I am on cloud nine today I feel over the Moon (very happy), HAPPY BIRTHDAY TO ME*_🎂😍
Jiyayi kamar ba izzatunsa ba sai yayi tunanin kodai bacci yakeyi, itama lamo tayi ajikinsa sai tajita wani iri sabida rashin sabo , hannayensa yasa duka biyu shima yayi hugging d’inta.
  Sun d’an jima a hk kowa yanata sak’e_sak’e a cikin zuciyarsa izzatu ce tayi yunk’irin raba jinkinsa da nata, kallonsa tayi da murmushi d’auke a fuskanta tana rik’e da hannayensa tace, Sannu da zuwa reality ya office ?
Ji yayi komai enough wani farinciki ya tsarga har cikin zuciyarsa, muryansa d’auke da farinciki yace, babyna Alhamdullilah  about everything, Am ya gida ?
Izzatu da Tuni kunya ta rufeta ta daurewa kawai takeyi ta kuma d’aga ido tace, Reality gida babu dad’i idan babu kai aciki, ta k’arasa maganar tana me sunkuyar da kanta k’asa.
 Safraz  da tuni ya fahimci kunya takeji sai ya d’an tsukunna yana kallon fuskarta dake sunkuye tana kallon k’asa yace, baby why shame?
 Rasa me zatace tayi dan itama farinciki a ranta ya kasa misaltuwa sabida kasancewarsu a hk, sai kaiwai ta rufe idonta da sauri tayi hugging d’insa.
Jinsa yakeyi tamkar wanda akabawa kyautar aljannah, “Tabbas sai yau yakuma tabbatarwa izzatu itace farincikisa, ya amincewa zuciyarsa komai izzatu zata aikata masa bazai iya rabuwa da itaba babu irin abinda zuciyarsa bata raya masaba
akan ya hakuri da ita sai yau ya gane da yayi hk daya tabka babban *KUSKURE* a rayuwarsa”
Dariya yayi yace, okay ni kikejin kunya kou ? Sai ya d’agata cak ya nufi d’akinsa.
A kan gado ya sauk’eta tayi kwanciyarta, ji yayi ya kasa daurewa kwanta yayi kusa da ita yayi hug d’inta saitin fuskarta ya matso da fuskarsa batayi yunk’urin hanashi ba, kissing mouth d’inta ya ……
Koda babu abinda ya wakana tsakaninsa da izzatu ammah sai yaji wasai yadan rage feeling.
ta taimakesa yayi wanka ya shirya sannan suka fito falo duk tana manne ajikinsa.
Safraz dai ya kasa control d’in kansa  domin wani irin farinciki yakeji a ransa, suna zaune a dining tana zaune kan cinyarsa tana saving food da zasici a dai_dai lokacin Abu me aiki ta shigo sai da ta kusa fad’uwa domin kafafuwanta hard’ewa sukayi ganin yanayin da safraz da izzatu suke, tayi matuk’ar mamaki shaushe suka fr zaman lpy hk .
 Sallama tayi musu suka amsa  sannan ta durkusa ta gaishesu, sai kuma ta rs me zatace domin dm  gulmace ta kawota.
Abu ta k’ak’alo k’aryarta Tace. Am Hajiya dama zuwa nayi na tambayeki ko kina da maganin ciwon kai ma’u ce  tun safe take fama da ciwon kai gashi  babu kud’i a hannuna.
A dai_dai lokacin Abu ta d’ago fuska suka had’a ido da izzatu, DAS! Izzatu taji k’irjinta ya buga  kwayar idon  Abu sai yayi mata kama da mutumin daya shigo mata a first night d’inta a gidan,  Abu ma Taso ta fahimci hk  sai tayi sauri  ta kauda kanta. Izzatu sai ta share kawai.
Cikin kulawa izzatu Tace, subhanalla! Amma banji  dad’i ba gaskiya tun safe ace sai yanxu zaki fad’amin tana fama  da rashin lpy baki kyautaba Abu, ai hakkine a kula da lpyr Ku ya jikin nata?
Abu Tace, da sauki Hajiya naga kinyi babbar bakuwa ne shiyasa ban zo na fad’a mikiba.
Izzatu Tace, wannan ba hujjabace Abu da Saurita tashii  dg kan ciyar  safraz ta nufi daki, minti kad’an  ta dawo d’auke da maganin ciwon kai da kud’in 10k.
Gashi kibata tasha, da safe sai kikaita hospital amma idan kinga  abun ba sauki kimin mgn sai Mu kaita hospital ko.
 Abu ta k’ar6a Tace, mun gode sosai Hajiya mun gode , ta tashi ta fita, safraz da bece komaiba tun dasuka fara mgn yabi bayan Abu da kallo.
Kasa 6oye abun dake ransa yayi ya kalli izzatu yace , reality kinsan me?
Izzatu Tace, a’a dear.
Bazan 6oyemikiba hk  kawai sai indinga jin ban yarda da wannan matarba.
Izzatu Tace, Abu? Ya mata sigina alamun eh.
Dariya tayi Tace, tana da kirki kuwa sosai ga ta iya girgiki sosai da ayyukan gida, ba komai ka cire  komai a ranka dear blame babu kyau koda gaskiya ne
Safraz ya yamusha fuska yace, no dear is not a blame kawai sai ina ganin tana min kama da namiji how about you?
Izzatu dariya ta k’yalk’yale da, sosai takeyin dariyar safraz ya tsaya yn kallonta sai tayi masa kyau sosai ya kasa d’auke idonsa a kanta, har sai da ta hura masa iska a idonsa.
Izzatu tana cigaba da dariyar Tace, why are you gazing at me dear?
Safraz ya saki murmushi yace, duk kin canza ne baby the way you laughing it brings your beauty out.
Yana lumshe ido yayi mata wani irin kallo  yace, long time baby?  Zaki iya tuna rabonmu da sabun farinciki irin yau?
  Tana kallonsa Tace, yeah since before our marriage, wani yanayi zuciyarta ta shiga  tsoronta dy kar ya Taso da zancen da zai wargaza musu happiness.
Kwantar da kansa  yayi a bayan kujera tare da sauk’e ajiyar zuciya,  izzatu ya furta a hankali.
 Itama in softer voice Tace, na,am.
Safraz yace, I am with forever ya rik’e hannuta yana murzawa.
 Sunci  abicci sun kammala abin gwanin ban sha’awa, sannan suka koma  falo  suka zauna suna hira time to time sabida rashin  sabo yasa dukkansu basu wani saki jikinsuba.
Zuwa wani d’an lokaci safraz ya kasa danne abinyke zuciyarsa, cikin dabara yake toughing different part of her body that interested him.
Abu da sauri  ta yi d’ankinsu lokacin da tabar part d’in izzatu, lokacin data Shiga d’akin ma’u ta kalleta tace  hajiyata lpy kuwa nagabki sai kace  wacce aka koro?
Abu ta yatsuna fuska Tace, hoho hooo ai da korowace da sauk’i, kinsan aikin da mukayi ya warware kuwa, ke nifa bagaji da zaman gidannan aradu dukda ban rasa komaiba amma kullum ina yawo cikin hijab sai kace wata mace   Ni Wallahi a takure nake .
Ma’u Tace, to meye ya faru mudai ba ankusa yin aurenba Mu kama gabanmu.
Abu Tace, Yau daya kamata ace matarnan ta tashi hankalinta da taji  zancen zai kr aure amma infad’amiki wata sabuwar soyayya suka fad’a abinsu, Ni bansan me zamucewa Hajiya adama  bama wallahi.
Bata gama rufe bakiba sukaji ringing d’in waya , Abu ta kalli ma’u Tace Hajiya ce  me zancen yanxu Ni? Ko inyi mata k’arya kawai ince  tanacan sunata rigima bazata zauna da kishiyaba.
Ma’u Tace, um to nidai ganina ki fad’amata gaskiya kinga  Tace zata k’aramana kud’i idan zata sallamemu fah.
K’iran ya katse, sai ga wani yakuma  shigowa, da Sauri Abu ta d’aga.
Muryan aunty adama ne  dg daya 6angaren tana cewa, ya dai meke faruwa?
Abu Tace, to Hajiya babu wani labari asalima alamu sun nunamin  babu ranar Dana ta6a ganinsu atare  cikin jin dad’i  irin yau ba gaskiyar mgn Hajiya a yau suka shirya domin kullum ina lura da shige da ficensu amma yanxu dawowarsa da yamma  suna mak’ele da juna kamar batasan dazancen za’ayi mt kishiyaba harda yimin kyautar dubu goma sabida tana cikin farinciki.
Ran aunty adama  yayi matuk’ar 6aci sosai dajin  zancen , cikin 6acin rai take cewa “wai Ni yarinyar nan metayiwa safraz ne HK wane irin asirine hk  wallahi sai naga bayanta a gobe goben nan, yanzunan kazo zan baka  wani Abu koda baka  sameni a gidaba kujirani”
Basu wani 6ata lokaci ba suka tashi suka nufi gidan aunty Adama.
Itama aunty adama  Tana gama wayan ta tashi tafita sakina  dake la6e tana jinta  kanta ya d’aure tarasa gane  dawa momy tayi waya  “me suke nema km yanxu tunda sunyi yadda zasuyi sun cusawa safraz aunty karima  me momy take cewa zatayiwa aunty izzatu ne zataga bayanta a gobe gobe metake nufi kenan? Yau sai naji mezasu aikata in sha Allah bazasuyi nasaraba” sakina ta gm saka  hk  a ranta.
Tana zaune saiga momy ta dawo fuskarta a daure babu annuri, momy sannu da zuwa Sakina ta fad’a.
Yauwa, fuskarta babu walwala.
Sakina  tace, momy Inason zanje gidansu asma  zamuyi karatu zuwa bayan isha’i zan dawo.
Momy cikin jin dad’i  tace , yauwa dg nan ki biya gidan Mami kice  Nace Zanzo gobe.
Sakina  cikin shagwa6a Tace, momy kibari sai gobe sai inje gidan Mami sabida yanxu ba mota zan d’aukaba.
Momy Tace HB daughter kije mana.
Wata dabara ta fad’owa sakina  Tace momy amma kwana zanyi a gidan mami.
Da sauri  Mami Tace, to shikenan ki kwana.
Sakina  ta mik’e Tace, na tafi momy bazan d’au motaba.
Adawo lpy my princess, momy ta fad’a.
Sakina  tana fita ta zagaya waje ta samu ta la6e ta bayan falonsu ta yadda zata iya jin komai dake faruwa acikin falon.
  Tana fita momy ta d’au waya ta k’ira Karima,  nan da nan Karima ta d’aga hello momcyna. Karima ta fad’a.
Momy Tace , ke stop no time for joking, safraz fa yana son matar fiye da tunaniki duk sharrin  da aka kullamata haryanxu suna jone  kamar tip da taya, idan ya aureki bazai damu  dake ba itace zata kwace gidan sai yadda Tace Yanxu na kawo mafita dole sai dai Mu kawar da ita idan ba HK ba wallahi idan kika Shiga gidan a hk  bazai ta6a saurarenkiba.
Karima Tace, momy hankalina ya fr tashi yanxu ya za’ayi?
Momy Tace, yanxu nan na fita na siyo poison zan bawa  ‘yan aikin  su Sa mata a abinci taci  ta mutu kawai.Dayake momy idan zatayi waya a handsfree  take sawa, sakina  dake la6e tanajinsu har abinda Karina take fad’a.
Hawayene suka fara wankewa sakina  fuska fargaba tashin  hankali ta tsinci kanta aciki, Kisa kisa  tayi ta maimaitawa a zuciyarta aranta tana cewa” Innalillahi wa’inna”ilaihirraji’un, Dama momy bata tsoron Allah? Momy zata iya kashe  mutum dama? ” ta Shiga rud’ani sosai hankalinta yayi matuk’ar tashi mamaki ya mamayeta k’irjinta sai dukan  3_3 yake.
Da wanine  yace mata mahaifiyar zata aikata haka bazata yadda ba amma sai gashi taji  da kunnanta, momy ce  taciga da cewa, kinga  idan nabawa ‘yan aiki suka Sa mata da taci sai lahira idan yaso  ko d’aga bikinku dashi sai ayi tunda za’ace matarsa ta mutu dole za’a d’aga.
Karima  Tace, momy kisa? Anya bazamu aikata *Kuskure* ba momy kuwa, gaskiya ina tsoro momy Mu canza wata shawarar amma banda kisa  momy.
Ke ! momy ta daka  mata tsawa, Matar da zata zama kishiyarki itace kike tausayi? Kinsan ita me zata shirya miki ne?
Karima Tace, momy ba wai hk  bane kawai ina tsoron wani Abu ya biyo bayane, Ni a ganina a kuma gara  a kuma yimata sharrin  kwarto da akasheta amma yadda kika gani momy.
Momy Tace, baki da hankali wlh waya fadamiki hk  ta bar safraz idan ba ta asircesa ba ya za’ayi adaren aurensu na farko ya kamata da kwarto amma yacigaba da zama da ita kiga pa sharrin  da aka kulla  mata a daren aurenta na farko amma babu wani Abu daya biyo baya.
Karima tace,  hkne momy amma Be kamata Mu aikata kisa ba sabida ina tsoro wallahi.
Momy taja  tsaki sannan Tace, shikenan dama ai ke zanyiwa gata  tunda hk  kikace yawuce, amma kisani pa nacire hannuna a cikin wannan lamarin ko safraz ya aureki ko bai aurekiba matsalarkice.
Hankalin karima  ya fr tashi domin tayi nisa  a son safraz idan bata auresaba gani take kamar mutuwa zatayi, Da sauri Karima Tace, momy pls kiyi hakuri Dan Allah I don’t mean that, shikenan shikenan ayi yadda kikace momy.
Momy Tace, ko kefa amma da kina Neman kawo matsala, yarinya ina hango miki daula  da rayuwar jin dad’i  safraz yana da makudan kud’i hkm  mahaifinsa ga mulki kuma.
Wani dad’i Karima takuma  ji Tace, shiyasa nk jidake momcyna Allah ya barmanake.
Hirarsu suka cigaba dayi daga bisani sukayi sallama, sakina  dake la6e a bayan falon tana jinsu tuni gumi ya gama jikata, da k’yar take d’aga k’afarta tayi hanyar get ta fita a gidan.
Kai tsaye gidansu aminiyarta Asma ta nufa,  Sun dad’e  suna hira sannan  sakina Tace, Asma  Inason fad’amiki wata mgn.
Asma  dake fito da littatafai a jaka  Dan suyi karatu Tace, Tom sis inajinki Allah yasa ba lbr wannan bazan lecturer zakimin ba danni na tsani ko lbrnsa wlh.
Sakina  tayi murmushin k’arfin hali Tace, ba lbrnsa bane tunda kince bak’ya yinsa aybaza’a miki dole ba.
Asma Tace, menene sis naga fuskarki kamar akwai matsala ?
Sakina  da ta kasa daurewa sai hawaye ya fara fita a idonta.
Subhanallah sis meye hk  wlh kinsa zuciyana ya karye, cewar Asma.
Sakina  ta goge hawayenta ta kalli Asma Tace, akwai matsala babba  sis bawai zan tona  miki asirina bane narasa wazan tinkara da mgnr ne.
Asma da tuni jikinta yayi sanyi Tace, Meke faruwa sis in sha Allah zamu samu mafita?
Sakina  Tace, Asma  akan lamarin aurena da safraz ne wani sabon al’amarine  Wanda ban taba tunani daga  mahaifiyata da Aunty karima , Sai hawaye ya fara bin kumatun sakina  Anan ta kwashe dukkan abinda taji lokacin da momy da Karima suna waya.
 Tun kafin ta gama fad’,amata itama Asma  tuni zufa ta fara jik’ata.
 Sakina  tacigaba dacewa, Wannan wacce irin rayuwa ce  Asma  nidai a yadda bake zuwa gidan uncle safraz na fahimci babu zaman lpy da jituwa a tsakaninsa da matarsa amma ban ta6a tunanin momy da aunty Karima sunada Sa hannu acikin ba, Asma  wallahi ban ta6a tunanin mahaifiyata zata iya aikata kisaba. Sai ta fashe da kuka.
Itama Asma  rasa abin cewa tayi, sai zuwa can tace , Stop crying pls wipe your eye sis,  cry is not our solution now.
Asma  taciga dacewa, Tabbas abun bazai miki dad’i ba koni nayi bak’inciki sosai Wanda nasan ke sai kin fini ji, To amma me we have to thank God tunda har basu kai ga aikatawa ba mukuma  sai Mu warware lamarin cikin yardar ubangiji.
 Sakina  Tace, Asma  yanxu what’s the solution?
Asma ta nida zuwa can Tace, iya abinda tunanina ya bani babu Wanda yakamata Mu tinkara da maganar nan sai Aunty izzatu.
Dup ! Sakina  taji k’irjinta ya fad’i , tana zaro ido Tace kamar Yaya sis? Aunty izzatu zan sanar  da ita abundake faruwane?
Asma  Tace a’a ba hk  nake  nufiba, kinga  da farko bamuce zakije ki tinkari momy da wannan zancen ba Bazataso ace kinsan sirrinsu  ita da yayarkiba inada tabbaci bazata saurarekiba kuma zata iya gargad’in idan wani yasani zata fad’i wani mummunan Abu akanki kinga  ba yadda kika iya zakiyi shuru dole idan kikaji tsoron furucinta, idan kuma kikace Mami mahaifiyar safraz zaki tinkara da wannan zancen itad’in k’anwar mahaifiyar kice  hakan zai iya lalata alakarsu da zumuncinsu dukda Mami mutum ce  me sauk’in hali amma bazata ta6a jin dad’in  kashe  matar d’anta da yayarta take yunk’urin yiba dole safraz zai San zancen idan mahaifiyarsa tasanj zai dena ganin girman momy dole zai fasa  auren aunty Karima itama aunty izzatu zata sani abun dai bazai kyauba, Amma kinga  idan muka tinkari aunty izzatu da wannan maganar Mu dakatar da ita daga  cin abinci ‘yan aikin  nata  idan ta kama Mu sanar da ita abinda yake faruwa dole Mu sanar mata bazatak’i rufa asiriba sabida ke bakya tare dasu bakida wata manufar cutar da ita zata fahimta wlh, kinga  anrufa asiri sukuma muyita musu addu’a Allah ya ganar dasu saiki ta yiwa momy nasiha cikin dabara tunda ba yadda kika iya mahaifiyar kice .
Sakina  kuka  ta fashe dashi me ban tausayi sai datayi me isarta sannan ta kalli Asma  Tace, Hkne Asma  wannan shawarar taki  haka zanyi, Nagode sosai Asma  ina alfahari da samun k’awa kamarki Dan Allah Mu rufe wannan maganar dagani sai ke.
Asma  Tace, karki damu  sakina  zaki sameni me rik’emiki sirrinki in sha Allah.
Sun tattauna akan lamarin sosai sannan sukayi sallama ta nufi gidan Mami.
Momy tana zaune a falo  Abu da ma’u suka shigo bayan sun gaisheta ta amsa.
Momy ta kallesu tace , Babu lamarin wasa a maganar dazan fad’a muku Ku kiyaye idan ba hk  ba komai zai iya faruwa daku, Jakar  dake gefenta ta bud’e ta d’auko wata farar roba kamar ta magani  ta mik’awa Abu ta kar6a, Momy taciga dacewa, Inason gobe idan safraz ya tafi office Ku tabbata Ku zubamata acikin abinci taci  kuma Ku tabbata ita kadaice zataci abincin kar safraz yaci na fad’a muku sai idan baya nan zaku Sa mata Ku kiyaye wannan.
 Abu ta kalli momy Tace, Hajiya angama in sha Allah za’ayi yadda kikace.
 Momy tace , Rabin murfi zakusaka mata sannan sauran ku zubar dashi Ku jefar da robar a inda kwata_kwata bazata gantaba.
Hk suka tashi suka baro  gidan momy akan hanyar su komawa gidan safraz ma’u take cewa Abu “Ni gaskiya bazan aikata kisaba badaniba wannan aikin  wlh idan kai kaga zaka iya to sai kayi Amma duk abinda ya biyo baya babu ruwana gaskiya, Son kud’i ba hauka  bane Ni a gobe ma zan koma kasuwa incigaba da harka  d’audu   yafiyemin wannan mak’ircin da’ake  shiryawa.
Abu Tace, Aikin  bazan kai kasani takarema cikin talauci inaga kafison  hk  A sauka lpy har suka k’arasa gidan ma’u bata k’aracewa komaiba.
Lokacin da sakina  ta k’arasa gidan Mami da alamun damuwa a fuskarta hakan yasa Mami ta dinga tambayarta Amma sai Tace mt ciwon kai take fama  dashi, daga  k’arshema sakina  ta tashi a falon ta tafi d’akin Shaheeda tayi kwanciyarta har gari ya waye.
Da sassafe sakina  ta shirya ta kalli Shaheeda tace , sis idan Mami ta tambayi inda naje  kice  mata akwai marasa lpy danzan duba a hospital zuwa anjima zan dawo, Shaheeda Tace, Tom Anty sakina  a dawo lpy.
A dai_dai k’ofar gidan safraz adaidaita sahun  ya sauk’e sakina.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *