KWAI CIKIN KAYA CHAPTER A
BOOK2
Typing📲
ƘWAI cikin ƘAYA!!
Bilyn Abdull ce🤙🏻
Assalamu alaikum, barkanku da wannan lokaci, barkanmu da sake dawowa filin daga, insha ALLAHU zan cigaba da littafin ƘWAI CIKIN ƘAYA kamar yanda na fara, inafatan haɗin kai daga gareku, haɗin kan kuwa shine tsaftataccen Comments da zai iya zaburar dani akan abinda nake rubutawa, masu ɗaukar littafi su ɗaura a youtobe wlhy wlhy na rantse duk wanda ya ɗauramin ƙwai cikin ƙaya a youtobe kar yay kuka dani akan matakin da zan ɗauka yay kuka da kansa. Masu cewa kuma na maida littafin na kuɗi kudaina yimin ƙarya, inda naso hakan da tun a 1 zance na kuɗine. Masoya kumuje zuwa, yanzu za’a fara wasan😉🤓.
14
BOOK TWO
(1)9
…………Kowa yana cike da murnar dawowar aunty Shahudah a gidan amma banda ni, ba komai ya jawo hakanba kuwa sai irin tarbar dana samu daga gareta bayan dawowata aiki a randa ta dawo.
Cikin ɗokin ganinta da kewa na nufeta, amma saita kalleni cikin wani yanayi na wulaƙanci da ƙyama kamar yanda ta sabamin a baya, daga ƙarshe ta koma dariyar aikina. Hakan ba ƙaramin ciwo yayminba, musamman yanda naga harsu Mom sun biye mata suma suna tayata dariyar. Daurewa nai nima na tayasu, dan na ɗaukama kaina alƙawarin insha ALLAHU sun daina ganin raunina a yanzu. Sai da muka gama dariyar sannan na nufi ɗakina nabarsu, su Aunty Aamilah na bata labarin yanda akai nazama dss a yanzu.
Ina shiga ɗakina na faɗa saman gado na fashe da kuka, tabbas wulaƙanci bashida ƙyau sam a rayuwa, ƙasƙanci ga mutum abune mai muni, amma a wannan duniyar babu abinda mutane suke alfahari dashi kamar ƙasƙanta ɗan uwansu musulmi.
“Sai kaga mai dukiya yana ƙasƙanta talaka koda da magana ne, mai ilimi na ƙasƙanta marashi, mai mulki na ƙasƙanta mabiyansa, miji na ƙasƙanta iyalansa, ɗan uwa na ƙasƙanta na ƙasa dashi. koyaya mutum yafi wani saikaga yana hura hanci wajen ganin yayi tozarci ga wanda bai kaisaba, kaicon mutane da wannan ɗabi’a, kamanta ALLAHN daya baka shima bai manta da shiba, sannan badan ka fisaba ya baka shi ya hanashi, ikonsane wannan yabama wani ilimi yayi wani jahili, ya bama wani dukiya yayi wani talaka, ya bama wani haihuwa yayi wani babu ɗa, ya bama wani mulki yayi wani mabiyi, ya bama wani lafiya yayi wani mara lafiya, kowa a rayuwa akwai jarabawarsa, kaine wane bashike nuna kafi kowa ba, kai ka samu kaza ko kake da kaza bashike nuna ALLAH yafi sonka ba, nima ALLAH yana sona, kuma ina sake gode masa da yanda yayini aunty Shahudah…….”5
Tun daga wannan ranar na sake jabaya ga kowa da komai na gidan, Dad dama bai dawoba, hakama Yah Qaseem yayi tafiya tun washe garin dawowar aunty Shahudah gidan. ko a wajen aiki bani da wata walwala, Ummie da wasu abokan aikina sai suka danganta rashin walwalar tawa da kewar Yah Qaseem da bayanan, dan zuwa yanzun mutane da yawa sun san alaƙar dake a tsakanina dashi.
Ni kuma a ɓangarena ba damuwar rashin yah Qaseem bane da lamarin gidanmu kawai kecin raina, akwai wani abu daban danaketa ƙoƙarin tureshi a raina, dan bana fatan gaskata zancen zuciyata koda da wasa kuwa.
★★★★★★★★
Yau data kasance juma’a dai-dai da dawowar aunty Shahudah da kwanaki huɗu Dad shima ya dawo, kowa yay murnar dawowarsa tamkar yanda muka saba, ya kuma samu tarba daga matarsa harma da Aunty Shahudah dake ganin wannan dawowar tatace. Nidai ina daga baya-baya dukda jana a jiki da Dad keyi, dan motsi kaɗan ya sako sunana a cikin zancensa, hakan na kula baƙaramin sosa zuciyar Aunty Shahudah ya keyi ba, hakama Mom. Dana kula abin zaiyi tsamari saina zare jikina na gudu ɗaki, dama dai muna zaune ne muna cin abincin dare.
Ban sake yunƙurin fitowaba kuwa har safiyar washe gari domin nima naji a raina yakamata na basu waje su gana da mahaifansu. duk da kasancewar asabar ce babu aiki ban iya komawa barci ba, dan narigada na saba yanzu da yanayin tashin sassafe. Ina zaune akan abin sallah tun bayan idar da sallar asubahi ban tashiba, na lazimci azkar nai karatun Qur’ani, rashin abunyi ya sakani tashi nahau gyaran ɗakina, hakan sai ya jani tsayin lokaci har kusan tara da wasu mintuna.
Sama-sama nake jiyo hayaniya kamar na kuka, kukan kuma yaymin kama da muryar Mom. Nai azamar ajiye tawul ɗin dana ɗauka zan shiga wanka na fita. Sosai gabana ya faɗi saboda cin karo da Mom dake kuka iyakar ƙarfinta, Dad na riƙeta, daƙyar na iya haɗa maganganunsu, daga ƙarshe na fahimci ƙanin Mom ɗine ALLAH yayma rasuwa mai suna Usman, tabbas naji suna yawan faɗar sunan Uncle Usman, sai dai ban sanshiba, ban taɓa ganinsaba, dan duk zamana a gidan ban taɓa zuwa gidansu mom ɗinba, bankuma cika ganin ƴan uwanta suna zuwaba, kowa dai yasan halin wasu ƴan bokon nan da aƙidar rashin son takura.
Nima dai tausayin Mom ya sakani bin sahun masu sharar hawaye, nan dai Dad ya cigaba da lallaɓata, kafin yajata sama, muma yace duk mu shirya domin tafiya can gidan. Hakanne ya saka kowa nufar ɗakinsa mu duka.
STORY CONTINUES BELOW

______________________________
A daren jiya juma’a misalin ƙarfe sha biyu da wasu mintuna mummunan labari ya iso gidansu Jawaad, cewar Uncle Usman ya samu haɗarin mota a hanyarsa ta dawowa daga tafiyar da yayi ta kwanaki biyu.
Lallai wannan gida sun fuskanci tashin hankali na bazata, dan bayan mahaifin Jawaad basu ƙara rasa ko ɗaya a cikinsuba, kaf ƴaƴan malam Yusif Abdul-aziz ne kawai ALLAH yayma rasuwa. Saiko shi malam Yusif ɗin da matarsa ɗaya sai mama maryam, idan ka cire waɗanan huɗun sauran duk sunada ransu, saima yaɗuwa da suka sake yi saboda haihuwar jikoki harma da tattaɓa kunne.
Ruɗanin da mama Atika ta shigane ya sakata yanke jiki ta faɗi, dan abune da tunaninsu bai taɓa kawo musuba anan kusa duk da sunsan mutuwa tabbacice ga duk mai rai, ba Uncle Usman ba ko ita kanta data tsufa sosai bata tuna mutuwar zata iya ɗaukarta a yanzu balle shi da ayanzune ake ƙara shiryama duniyar filin zama.
Lokacin da gidansu Jawaad ke cikin wannan ruɗanin shi yanacan suna gumurzu da wasu gungun ƴan ta’adda da suke fako tun kusan sati uku da suka shige, sai a yaune ALLAH ya basu nasarar yin fito na fito dasu, sun sami nasarar kama wasu a cikinsu, yayinda wasu suka gudu.
Kusan ƙarfe huɗu na dare suka iso station ɗinsu da waɗanda suka cafko, sunyi tiɓis da gajiya, ga yunwa dake cin hanjinsu ta bala’i ma kuwa, sai dai jarumtarsu da juriya mai haɗe da trianing ɗin da suka gogu a ciki duk ya ɓoye gazawarsu. Rose cema dai kawai ta kasa juriyar kasancewar ƙarfin zuciyar mace dana namiji ba ɗayaba, dukda itama ta cancanci a kirata jarumar kuwa, Jawaad ma baiso akai aikin da itaba, amma ta matsa akan sai taje, badan yasoba ya barta ta bisu.
A station ɗin suka ƙarasa kwanan, washe gari safiyar asabar ana idar da sallar asuba Jawaad ya kira gimba akan yazo ya ɗaukesa. Yanda yaji muryan gimban ne ya bashi mamaki, cikin yanayin gizagonsa yake jefa masa tambayar lafiya?.
Sanin halinsa baya son ɓoye-ɓoye a magana ya saka Gimba faɗa masa gaskiyar tashin hankalin da ake ciki a gidan nasu.
Dukda halin da yake ciki da matsalolin dangin mahaifin nasa hakan bai hanashi shiga ƙololuwar tashin hankaliba, a take ya birkicema su Jabeer, waɗanda suma jin rasuwar tai bala’in sakasu a ruɗani. Basu wani ɓata lokaciba suka nufi gidansu Jawaad ɗin kai tsaye, duk da halin gajiya da buƙatar hutun da suke a ciki. Sun iso gidan ƙarfe kusan bakwai da wasu ƴan mintuna, hankalin Jawaad ya sake tashi sosai ganin halin da ahalinsa ke a ciki, tuni ya manta da gajiyar dake tattare dashi.
Bai zaunaba su Uncle Nasir suka jashi zuwa asibitin da gawar Uncle Usman take domin su amso, abinda yasa ba’aje tun jiyaba saboda ba’a nan cikin gari bane, inda ya baro yafi kusa da inda yay haɗarin, shiyyasa aka maidashi asibitin can garin.
★★★★★★★
Ƙarfe goma da wasu mintuna muka iso gidansu Mom, katafaren gida na alfarma da ƙawa, dukda cikin tashin hankalin mutuwa mukazo hakan bai hanani mamaki da jinjina dukiya irinta wannan ahaliba, lallai dolene su aunty Shahudah suyi wulaƙanci yanda sukeso, kaga gida tamkar ba hannune ya ginashiba, harabar gidan kawai naganimafa kenan, sai mutanen gidan da zakaima kallo ɗaya ka fahinci ƴan bokone na haƙiƙa tun zamanin da boko keda tsada da daraja kuwa……
Ina cikin wannan tunanin ne nafara jiyo ƙarfin koke-koke na ƙaruwa, babu shiri na dawo hayyacina, a sannanne na lura ashe an iso da gawar mamacinne.
Har ciki sosai Ambulance ɗin dake ɗauke da gawar ta shigo, ta tsaya dai-dai sashen danaji wasu na ambata da sashen mama Atika mahaifiyarsu Mom. Zuciyata tai masifar harbawa saboda ganin wanda ya fito daga Ambulance ɗin.
Cikin tsagwaron mamaki na furta “Boss kuma anan?” akan laɓɓana, kamar yanda nakejin zuciyata aduk sanda ta samu kusanci dashi yanzunma bata canja zaniba, dole na shiga karanto addu’a gudun kar nayi abinda zai jawo hankalin mutane a kaina.
Nayi nisa a tunanin da har aka fidda gawar ban saniba, saida suna gab da shiga sashin ne nakai idanuna kansu tare da sauraren koke-koken mutane, su biyune kawai ke ɗauke da gawar a mankara, tana lulluɓe da farin ƙyalle da yay face-face da jini, alamar dai mamacin ya bugu sakamakon Accident ɗin da yayi, nantake sai zuciyata tai rauni saboda tunowa da mutuwar nawa mahaifin, sai kawai na durƙushe a wajen na fashe da kuka mai cin rai da zuciya.
STORY CONTINUES BELOW

Isowar gawarce ta saka gidan ya kuma cika sosai, koke-koken da akeyi ya sake ƙaruwa, ban kuma ganinsaba kuma har aka sake fitowa da gawar kusan sha biyu na safe, da alama dai yanzu an masa sutura za’a miƙashi gidansa na gaskiyane. Wani da nake ƙyautata zaton ɗansane ya rugo da gudu ya riƙe mankarar da aka ɗakko yana kuka da roƙon su ajiye masa Dadynsa, yarone da bazai gaza shekaru sha uku ba a duniya, sai ƴanmata guda biyu da zasu iya kawai 23 da 20 suma sukazo suka riƙe. Hakan ya kuma tada hankalin jama’a, ni kaina sunyi masifar bani tausayi, suma kenan da suke da gatan dangi dana jin daɗin rayuwa, na tuna sanda baba ya tafi ya barni, har aka binnesa ma ni bansan ina nawa hankalin ya keba.
Na share ƙwallar dake gudu bisa kumatuna, dai-dai isowarsa, wajen da alama yanzune ya fito, shine ya janye yaron ya rungumesa a jikinsa yana bubbuga bayansa, hakan ya saka ƴan matanma sakin mankarar suka durƙushe a wajen suna kuka. Bai saki yaronba har saida aka fita da gawar, ya shafa kansa yana ɗago fuskarsa, babu wanda yasan miya faɗama yaron, amma kowa ya kula magana yay masa kafin ya sakesa ya fice shima zuwa waje inda za’a sallacesa.
Tashin hankalin da ake cikine yasa ban samu damar tunanin alaƙar gidan da boss ba sam, bankuma sake ganinsaba, sai dai ganin nasa da nayi yana nan daram a zuciyata, dan kwanaki kusan shida kenan ban gansaba ko’a office, tun fitar da sukai ranar sai yaune na ganshi. A mamakina sai naji raina sakayau, bakamar yanda na tsinci kaina cikin ƙunci ba a kwanakinan.
★★★★★★
Tun bayan zuwanmu gidan ban sake sanya ƴan gidanmu a idonaba, har zuwa yanzu da aketa hada-hadar sallar azhar da cin abinci, garama dad bayan sun dawo daga binne gawar ya shigo cikin gidan shi da wasu manyan mutane sunyi gaisuwa, daga haka ban sake saka ko ɗaya a cikinsu a idanunaba.
Mutane nata shiga sassan gidan domin gabatar da salla, sai dai ni narasa ina zan dosa koda na tashi, waɗanda nazo dominsu ban sake ganinsuba, ina zan shiga nikan nace zanyi salla? Tunda babu wanda ya sanni babu kuma wanda na sani.
Ina nan zaune ina saƙa mai fishsheni a zuciya budurwar dake zaune a kusa dani ta miƙomin jakkarta da waya akan na riƙe mata tana zuwa, kamar zanyi magana sai kuma na amsa ina maida mata murtanin murmushin da takemin, ina zaune a wajen ban motsaba nai uban tagumi harta dawo.
Na miƙa mata kayanta, ta amsa tana min godiya, harta tafi sai kuma ta dawo da baya idonta a kaina.
“Ƴar uwa kozaki taso muje muyi sallane? Naga kowa na harama amma ke koma motsi bakiyba, ko dai kina hutune?”.
Murmushin yaƙe naimata, sai dai ban motsaba, nace, “Karki damu zan nema waɗanda mukazo tare sai nayi a wajensu”.
Tai ɗan shiru tana kallona, kamar bazata tankaba, dan harna fara murnar ta barni, sai na tsinkayi muryarta tana faɗin, “Yanda mutane ke cike a gidannan kafin ki ganosun ai kin wahala, sannan duk inda zakiy salla a gidannan yau bazai kai nutsuwar inda zamujeba, dan sashen yaya ne kawai nasan babu mutane, indai ba kina tsoron karna saidaki bane”.
Ta bani dariya, amma sai banyiba saboda yanayin da ake ciki, sai kawai na miƙe batare danace komaiba, dan na lura akwaita da surutu.
Tun shigowarmu sashen na yarda da zancenta, dankuwa tsit yake babu wata hayaniya anan, tamjar ba cikin gidan yakeba. Sai wani daddaɗan ƙamshi daya shige mini hanci, batare dana shiryaba na shaƙa na haɗiyeshi cikin maƙoshina, karon farko a rayuwata da naga falon da yafi na gidan Dad ƙyau da tsari, ada tunanina yana bani babu gidan da yakai na Dad haɗuwa da tsaruwar kayan alatu, dan dukkan gidajen iyayen su Ummie basu kai na Dad ba, amma a yau dana tsinci kaina cikin wannan aljannar duniyar duk sai na raina wancan alfaharin nawa, yanda aka ƙawata matattakalar benen dake falon kawai abar kalloce ga mai kallo duk wayewarsa kuwa. Ban gama bama idona abinciba budurwar taja hannuna zuwa wani ɗaki, mun iske mutum uku suna salla, sai ɗaya data fito daga bayi da alama alwalar itama tayo, sai wata kwance a kan gadon dake ɗakin da yara biyu suna kallon waya. Duk suka zubomin ido na rashin sani, wadda ta fito daga bayice tace, “Wai ina kikajene haka Nabeelah? an aika Ammar ya kiraki amma yace bai gankiba”.
Hannuna ta saki tana saɓule jakkarta dake a kafaɗa, “Babu inda najefa Aunty Hanifah, ina can jikin sashen Uncle Sulaiman zaune, nima yanzu saida na leƙo naga kuna nan sannan ai na taho”.
Batace mata komaiba, hakanne ya sakani gaisheta dan naga babbace ta girmeni, na juya ga wadda ke a saman gadon tare da yara itama zan gaisheta sai tai saurin gaisheni. Murmushi kawai nayi, dan ita zan iya girmarta, suma yaran sai suka gaidani, na amsa musu da kulawa ina tambayar sunayensu. Namijin yace Ammar, macen kuma Islam. Yaran sun birgeni, gasu masu ƙyau. Wadda muka shigo tare da aka kira da Nabeelah ce tace min na shiga bayin nayo alwala, cikin tsokana take faɗin “Karnayi abin kunya gashi bansan sunan ƙawar tawabama”.
Ƴar dariya nai babu shiri, ina ƙoƙarin shigewa nace mata sunana Bilkisu. A tare naga duk sun kalleni suna ɗora hannu a bakunansu, hakama biyu a masu sallar da suka idar suma suka juyo suna kallona. Yanda naɗanyi diri-diri na alamar shakkune ya saka ɗaya a cikin waɗanda suka idar da sallar babbar mace tai murmushi da cewa “Mai babban sunace ashe”. Numfashi na sauke a hankali kafin na gaisheta cikin risinawa, ta amsamin tana sake faɗaɗa dara’ar fuskarta, kafin tace naje nai alwalar kar lokaci ya ƙure. Shigewa nayi bayin nima da tunanin ko sunan waye nasu Bilkisun? Daga gani kam dai suna girmama mai sunan sosai.
Ina fitowa Nabeelah ta shiga, suma duk sun tashi daga abin sallar alamar sun bamu waje, sai wadda muka iske tayo alwala kawaice ke salla a wajen, na gaida sauran biyun da bamu gaisaba suma sannan na kabbara sallata.
Bayan mun idar da sallar a cikinsu babu wanda ya tambayeni game dani, sai dai sunata ƙoƙarin sakoni cikin hirarsu wadda duk ta karkata ga mai irin sunana danaji manyan na ambata da Yaya Bilki, yaran kuma na kiranta Mah-mah Yanda suke hira akanta cikin damuwa da kewane ya sakani tunanin ko bata da raine? Bani da mai bani wannan amsar, dan haka na haɗiye abina cikin rai ina cigaba da saurarensu….
Kusan mintuna talatin ina sauraren hirarsu mai cike da birgewar kasancewarsu ahali ɗaya, kafin na miƙe domin tafiya, dan ya kamata naje na binciki inda su Mom suke koda su basu damu da nemanaba.
Duk kallona sukai cike da alamar tambaya.
Murmushi nayi, nace, “Zanjene kar abokan tafiyata suyita nemana”.
Suma duk murmushin sukaimin, Nabeelah ta miƙomin wayarta tana faɗin, “To sakamin Number ki muke zuminci, danni dai nayi ƙawa daga yau”. Ban musaba na amsa wayar tata fuskata har lokacin da murmushi, na saka mata Number ta ina miƙa mata wayar, wadda naji suna kira Aunty Batool tace, “Lallai kin jajubarma kanki kuma Ummien mu, dan shegen surutun Nabeelah takai a guji ƙawance da ita, gaki keman daga gani bakida yawan magana”.
Sanin dani take yasani faɗin, “Aunty ai sunfi daɗin ƙawance irinsu Nabeelah”.
Atake kowa ya shiga faɗin a’a-a’a, yayinda Nabeelah keta ƙoƙarin kare kanta, niko ina musu dariya. Godiya na sake musu kafin nai musu sallama.
Zuciyata tai wani irin harbawa lokacin da akai knocking ƙofar ɗakin tare da sallama cikin wata irin sassanyar murya dake nuna mai ita yana a matuƙar gajiye, tattare da tsagwaron damuwa. Akusan tare suka amsa, nikuma na janye hannuna dana ɗora akan mariƙin ƙofar cike da fargaba, ban gama tattara fahimtata waje gudaba aka turo ƙofar aka shigo, kaɗan ya rage ya bugeni, nai saurin ja baya kaɗan dan na bashi hanya sosai.
Idanunane suka fara sauka akan ƙyaƙyƙyawar ƙafar da baƙin wandon jeans ya sake haskawa, jijjigar da zuciyata keyine ya dasamin tsoron yarda da hasashena, dan haka na kasa ɗago idona naga wanene? Dukda ƙamshin turarensa ya nema saka zuciyata faso ƙirjina ta fito……
Ganin yaƙi shigewa ya bani hanyane ya sakani ɗago idanuna a hankali nakai dubana gareshi, a lokaci ɗaya idanunmu suka shige na juna saboda shima dai-dai ya kalleni. Naɗan sake ja da baya na alamun mamakin sake ganinsa anan, amma shi a mamakina sai naga ya janye nasa idanun babu wani alamar mamakin ganina da ya nuna.
Yanda naji su Nabeelah na rige-rigen gaishesane ya sakani aro jarumta nima nabi layinsu na gaidashi, sau ɗaya ya amsa mana tare da amsa ta’azziyar da mukai masa ya ƙarasa ga iyayensu Nabeelah, hakanne ni kuma ya bani damar saurin ficewa cike da sassarfa daga ɗakin……….✍🏻
2
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.13
Alhmdllh inama kowa fatan alkairi, nakumaji daɗin wannan tarba, naso ace zan iya jurewa na biku ɗai-ɗai na amsama kowa Comments ɗinsa, sai dai nace kuyi haƙuri, kamar yanda matsalan ido ta dakatar dani da typing dolene yanzuma na ringa lallaɓawa saboda kunada ɗunbin yawa, akwai group insha ALLAHU da aka buɗe a shafin manhajar Telegram, masu amfani da wannan shafi su maza su garzaya idan suna buƙata, domin canne zai zama dandalin tattaunawa akan littfin ƙwai cikin ƙaya da sada zuminci, duk mai karatu yana buƙatar dandali na tattaunawa akan littafi, dan da yawanmu hakan na bamu nishaɗi da sake fahimtar da mu abinda bamu fahimtaba, kuma yana ƙarama writer ƙarfin gwiwar typing koda batai niyyar hakanba, ku maza kar a baku labari. Zakuna samuna koda yaushe a can domin ku tabbatar ina tare daku, masoyan bily kuma na isar da saƙonku gareta akan ta daina tsoron jay😂, masoyan Shahudah tana miƙo muku gaisuwa itama🤓.+
https://t.me/joinchat/TIsXYRvhtri2kQ9E4x7w6g20
Wannan shine link ɗin group namu mai suna MASARAUTAR BILYN ABDULL A manhajar Telegram😘😘.
7
2
…………..Koda na fito daga ɗakin saida na huta a falon saboda yanda zuciyata ke mutsu-mutsu a cikin ƙirjina, ina matuƙar mamakin wannan al’amari dake yawan faruwa tsakanina da mutumin nan, na kuma rasa wazan tunkara da maganar halin da nake tsintar kaina akansa kozan samu fashin baƙin saɓanin wanda zuciyata ke kissima min, nidai nasan ba tsoronsa nakeba, to minene dalili? Wannan amsar nake neman mai bani.
Gwiwa a sage naja ƙafafuna na fice daga sashen zuwa harabar gidan. Yanzunma dai ban sami ko ɗaya daga cikin su aunty Aamilah ba, gashi banida Number kowa a cikinsu. Dole na sake nemar guri na zauna inda babu yawan hayaniyar mutane, sai jefi-jefi nakan ɗanga sun gittani.1
★★★★★
Yanda Jawaad ya nuna halin ko in kula da ganin na Bilkisu bazaka taɓa tunanin yama santaba, sai dai harta fice daga ɗakin yana kallontane ta wutsiyar ido, acan ƙasan zuciyarsa na raya masa “Ita kuma miya kawota nan?” sai dai a fili bazaka taɓa fahimtar komaiba.
Zama yay a saman ƴar dirowar dake farkon shigowa ɗakin, cikin girmamawa ya gaisa da iyayensa, sukai masa gaisuwar ta’aziyyah tare da jero addu’ar neman gafara ga mamacin, har suka cigaba da ɗan tattaunawa akan rasuwar wadda ta jasu tunowa da rasuwar mahaifin Jawaad ɗin shima da ɓatan mahaifiyarsa.
Haɗiyar zuciya kawai Jawaad yake famanyi, amma bakinsa ya kasa furta komai, daga ƙarshema saiya miƙe yana faɗa musu zaije ya ɗan kwanta, gimba zai kawo musu abincin da zasu ci.
Basu hanashi tafiyaba, dan yanayinsa ya nuna yana buƙatar hutun sosai.
★..::..★
Sai kusan ƙarfe biyar na hangi Mom suna gaisawa da wasu gungun baƙi da sukazo musu gaisuwa, da sauri na miƙe na nufeta karta sake ɓacemin, dan matuƙar gajiya na gaji da zaman ni kaɗai, danma naɗanyi cheating dasu Rebecca ne a group ɗin da muka buɗe iya mu biyar kawai na rage kaɗaici. Daga gefe na tsaya harta gama gaisuwa da mutanen suka tafi kafin na ƙaraso gareta, gaidata na farayi a ɗarare, tunda nasan bani da wata fawa a gareta, amma a mamakina sai naji ta amsa harda tambayata ina na shiga tun ɗazun bata ganniba? wani sanyi ya ratsa zuciyata, kasancewata marainiya ina matuƙar buƙatar kulawar mahaifiya koda kaɗanne, rashin samu kuma na sakani a ƙunci sosai, sai dai ina ƙoƙarin shanyewa ba kowa ke fahimtar hakanba. Cikin girmamawa na bata amsar tambayarta, saita bani umarni akan muje ciki naci abinci.
Ban sake sakashi a idonaba har zuwa dare bayan sallar isha’i da muka fito domin tafiya gida, ƙiri da muzu Aamilah da aunty Shahudah suketa ƙoƙarin zamewa haɗa tafiya dani, duk da basu fito fili sun faɗaba na fahimci haka da kaina, dan kafin nagama kimtsawa harsun fice daga sashen na Mama Atika, sai tare muka fito da Mom, sai muka iske harsun tafi wai tare da Yah Salman.
Banji haushiba, saima murmushi da nayi kawai, driver ne zai tafi da Mom, dan haka nima su zanbi dole. Mom ta tsaya gaisuwa da wasu mata da suma zasu tafi, ƴan gayune sosai da kallo ɗaya zakai musu ka fahimci naira ta zauna musu, nidai bayan na gaishesu jikin mota na koma na jingina kawai ina kallonsu da mamakin yanda naga Mom ta sake dasu sosai, yanda na santa da wulaƙanci, koda yake masu iya magana kance wata gaban tafi gaban raini ai.
Zuciyata ta motsa da ƙarfi a cikin ƙirjina, hakan ya saka tsoro ziyartar raina, koban faɗaba nasan hakan na nufin Dodona ya kusanto wajen koma yana wajen, zuwa yanzu nafara sabawa da wannan SABON AL’AMARIN namu.
Ilai kuwa ina ɗago idanu akansa na sauke, tsaye yake ɗan nesa damu kaɗan, hannunsa ɗaya cikin aljihun wando, ɗayan kuma ya riƙe waya dake kunnensa, wadda ke nuna alamar yana magana da wanine, ɗan taku yake ɗaya biyu cike da nutsuwa da cikar haiba, ba kayan ɗazun bane a jikinsa, daga wando har rigar jikinsa na yanzu duk fararene tas, gefe wando na duka ƙafar biyu akwai ratsin dogon zare jaa daga sama har ƙasa, sai agaban rigar shima anyi rubutu da ja, hasken dake ƙwanyar a tsakar gidanne ya sani ganin abinda aka rubuta, sai silifas fari shima, sosai kayan sukai masa ƙyau, har na iya kasa janye idona a kansa dukda wutsilniyar da zuciyata keyi kuwa.
STORY CONTINUES BELOW

Haka kawai Jawaad dake waya da Jabeer yaji a jikinsa kallonsa akeyi, kallon kuma irinna wanda keda kaifin gani da baiwar ƙarfin kwarjinin idanu, duk yanda yaso basarwa tamkar yanda ya saba hakan sai ya gagara, dole ya fara wulƙita nasa fararen idanun kozai samu nasarar cafko wannan mayen idon dake neman saukar masa da gajiya. Karaf kuwa idanunsa suka sauka akanta, shima ƙirjinsa ya motsa alamar harbawar zuciyarsa. Tabbas yaji a ransa itace ke kallonsa, amma a mamakinsa sam idanunta da hankalinta basa kansa, karon farko da miskilancin yarinyarnan ya motsa zuciyarsa, tun ganinsa da ita na farko a airport ya fahimci miskilace ta bugawa a jarida, kasancewar ALLAH ya azurtashi da ilimin karantar hallayyar ɗan adam cikin lokaci ƙanƙani, zuwa yanzu mamakin ganinta yabar ransa, dan ya kula akwai alaƙa tsakaninta da Qaseem…….
“Hello…hello…” Da Jabeer keta ambatane ya sakashi dawowa hayyacinsa, dan tuni ya saki wayar da suke ya kama sabgar bilkisu, abinda bayayi sam a rayuwarsa (wato shiga abinda bai shafesa ba), yaja siririn tsaki yana murza goshinsa da hannunsa daya ciro daga cikin aljihu.
Dai-dai lokacin da Bilkisu ta buɗe gaban mota ta shiga ta zauna, dan Mom harta shige baya itama.
Wani irin harɗaɗɗen numfashi ya sauke har Jabeer na tambayarsa “ko lafiya?”.
Gutun tsaki yaja yana yanke wayar batare daya bashi amsaba, yakuma jan wani tsakin har sau biyu yana takaicin kansa da shiga hurumin da ba nasaba.
_______________________________
Washe gari ban biyosuba, dan inama barci suka fice, babu wanda yace a tasoni, nima koda na tashi kuku ke sanarmin sun tafi banji komaiba a raina saima daɗi, tunda nasan zuwana bazai ƙara komaiba koya hana, hasalima banason gamuwa da Dodona.
Bayan na karya ɗaki na koma nai wanka, nai shiri cikin doguwar riga ta atanfa data samu zaunannen ɗinki, bawata kwalliya naiba, nasaka turare sama-sama na fito bayan na yafa ƙarmin gyale.
Kai tsaye gate na nufa wajen baba maigadi dake zaune shida mai bayin filawar gidan suna hira, suna ganina suka shiga gaisheni cikin girmamawa, sam banason hakan da sukemin, dan kuwa niba kowa bace a gidan face maicin alfarma, sannan duk sun girmeni, baba maigadi ma a haife ya haifeni, shima mai bayin fulawar kobai haifi kamata ba nasan yanada manyan ƴaƴa…..
“Hajiya fita zakiyine?”.
Baba mai gadi ya katsemin tunanina, kaina na girgiza masa ina murmushi. “A’a baba ba fita zanyiba, hasalima wajenka nazo muyi magana idan ban takura makaba dan ALLAH”.
Da sauri yace, “Haba wace takura kuma” yay maganar yana miƙewa da sauri, babu jimawa sai gashi da farar kujera, ajiyemin yay gefensu alamar na zauna, mai bayin fulawa kuwa yay mana sallama akan zaije gida yakai cefane.
Sake gaisawa mukai da baba maigadi, yay min ta’aziyyar rasuwar da akayi, nako amsa masa tare da tambayar lafiyar iyalansa, bayan amsamin da yay muka ɗanyi shiru, tunani nake ta ina zan fara abinda ya kawoni garesa?. Zuwa wasu ƴan mintuna sai dabara ta faɗomin, nai murmushi ina sake maida hankalina gareshi da kunna voice recorder dan na samu damar kwashe dukkan abinda zamu tattauna nayi nazari a tsanake a kansu.
“Uhm… Baba dan ALLAH niko wata tambayace dani?”.
Fuskarsa faɗaɗe da murmushi yace, “ALLAH Yasa na sani hajiya”.
Murmushi naɗan masa, nace, “Insha ALLAHU inada tabbacin kama sani ɗin”.
Baice komaiba sai hankalinsa daya maido kaina baki ɗaya, nima sai na sake nutsuwa sosai.
“Baba dan ALLAH ko zaka iya tuna ranar da abinnan ya faru da Amina a gidannan da wanda ba’asan ko waneneba?”.
A bazata maganar tazo masa, dan haka kawai saiya hau tari babu shiri. A rikice na shiga masa sannu, na jawo ruwan dana fito dashi daga ciki na miƙa masa da sauri bayan na ɓalle murfin, amsa yay har hannunsa na rawa ya kafa goran a baki ya ɓaɓɓaka, saida yasha kusan rabi kafin ya sauke, idanunsa harsun kaɗa sunyi jajur, sai naji tausayinsa ya kamani, koda ya dawo dai-dai shiru nai ban sake masa tambayarba har tsawon wasu mintuna.
Na sake jeho masa tambayar a karo na biyu, yanzunkam a mamakinawa shiru yay bai tanka minba, sai dai yanata ƴan kalle-kalle tamkar mai tsoron a ganmu ko wani ya jimu. Jin bashi da niyyar bani amsa ya sakani kallonsa, a karo na uku na sake maimaita masa tambayar da sigar kwantar da kai………
“Ɗi!! Ɗi!!! Ɗi!!…” mukaji horn ɗin mota daga waje, hakanne ya sakashi tashi da sauri ya nufi gate ɗin, na tabbatar dama hanyar da zai gudu yake nema, sai kawai na samu kaina da ƙura masa idanu ganin yanda har yanzu jikinsa ke mazarin rawa.
Hancin motar Dad ne ya danno kai cikin gidan, na sauke ajiyar zuciya ina miƙewa tsaye, saboda tsayawar da driver yayi a saitin da nake zaune, shi kuma Dad ya sauke glass ɗin ɓangarensa yana mani murmushi.
Nima murmushin nake masa ina miƙewa na nufesa, da hannu yaymin nuni nazo, dole nabi motar da direba yaja zuwa ciki inda zaiyi fakin.1
STORY CONTINUES BELOW

Tare da Dad muka shige cikin falo yana tambayata miyyasa banbi su Mom ba can gida?, cikin girmamawa na bashi amsa akan sun wucene ina barci lokacin. Nayi zaton zaiyi faɗa, amma sai naji kawai yay ƙaramar dariya. Mun yada zango a falon ƙasa, ya bani Umarnin naje nasa kuku ya haɗa masa abinci mara nauyi yunwa ya keji, ya fita bai karyabane.
Koda naje kicin ɗin sai ban fitoba na zauna mukayi abu mai sauƙi wa Dad ɗin ni da kuku, dan zuwa yanzunkam Alhmdllh hannuna yay masifar faɗawa akan girki kala-kala na zamani, na gargajiya kuwa dama bani da matsala a kansa, innata tarigada tayi min wannan horon tun ban gama fahimtar muhimmancin girki ga ɗiya mace ba.
Bayan mun kammala nice da kaina na kawoma Dad, lokacin yana waya, na ɗora tiren bisa tebir ɗin tsakkiyar falon na jasa gabansa, buɗe masa komai nayi tare da tsiyaya masa ruwa a kofi sannan na koma gefe na zauna, a haka ya faracin abincin yana cigaba da wayarsa data jashi tsayin lokaci, sai yazam yanacin abincinne kawai a shiririce. Dan harya kammala wayar baici ko kashi ɗayaba bisa uku, ya ajiye wayar yana maido hankalinsa gareni, “Taso muci mana ɗiyata”.
“Lah Dad nakane, ni ban daɗema da karyawaba fa”.
Cike da kulawa yacemin, “Da gaske?”.
Na langaɓe kai gefe ina ɗagawa alamar eh. Murmushi yayi ya cigaba dacin abincinasa yana mani hirar data bani mamaki, dan kuwa akan kasuwancinsane ya ɗakkomin hira, yana faɗamin alkairi da kullum kamfaninsa ke samu da yanda kuɗaɗe ke shigo masa babu ƙaƙƙautawa. Banda masha ALLAH da ALLAH ya ƙara sanya albarka babu abinda nake iya cewa, danni kam dai ban fahimci dalilin mani labarinba, tunda a ganina ai sirrinsane wannan, ko a cikin ƴaƴa kuwa a ganina sai wanda ka aminta da amanarsa.
Kamar kuwa ya karanci mike raina, sai cewa yay, “Kinji inata baki labarin abinda bai shafekiba ko?”.
Murmushin yaƙe naɗanyi ina gyaɗa kaina, shima ya murmusa yana mai kai cokalin romon farfesun daya ɗobo a bakinsa.
“Karkiji komai a ranki Bilkisu, na yarda da kene kawai shiyyasa, dan na fahimci keɗin yarinyace mai hankali da tarin nutsuwa, sannan sam baki da yawan surutu, waɗanan halayyar taki na ƙaramin ƙaunarki sosai”.
Murmushi yanzunkam nayi har haƙorana na bayyana, nace, “Nagode Daddy”.
Ƙaramar dariya yay yana miƙewa bayan ya ajiye kofin da yasha ruwa, “Kinga bara naje naɗan kwanta na huta, zuwa yamma saimu tafi gidan rasuwar muma”.
Kaina na jinjina masa kawai, dan nima tuni nake buƙatar keɓancewa, inason yin nazari akan halinda mai gadi ya shiga akan tambayar danai masa ɗazun kafin zuwansu Dad daya gaza amsa mani.
Koda Yammar bamuje ko inaba, dan banga Dad ba sai bayan la’asar lokacin da yah Salim ke dawowa gidan. Harare-hararen da yaketayine ya sakani tashi na barmusu falon na koma ɗaki.
★..★…:::::…★..★
Washe gari litinin kowa yasan tushen aiki, hakanne ya sakani shiri tun a farar safiya, lokacin dana fito babu wanda ya fito a mutanen gidan, tea kawai nasha driver ya ɗaukeni zuwa station ɗinmu kamar yanda a yanzu da Yah Qaseem bayanan kullum shine ke kaini.
Nayi mamakin rashin ganinsa yauma a office, bayan nasan ya dawo, daga baya sai nayi tunanin kodan dai rasuwarcan ne da bansan minene alaƙarsa da mamacinba, dan har yanzu ina mamakin ganinsa a gidan su Mom ɗin, dukda wani sashe na zuciyata na rayamin shima ɗan uwansune ƙila sunje gaisuwane.
Daga haka ban daɗaba ban ragaba har lokacin tashi yayi muka tashi.
Tare muka tafi a motar Ummie, dan ita Dadyn ta ya bata mota ƴar ƙarama tun fara aikinmu, tun tafiyar Yah Qaseem sai yazam direba na kawoni da safe, ita kuma mutafi tare idan mun tashi sai ta ajiyeni gida ta wuce nasu gidan.
Kiran da Nazifa tai minne a waya muke amsawa tare da Ummie dake tuƙi, dan a amsa kuwwa (Hans free)na saka wayar yanda itama zataji, munzo dai-dai shataletalen (roundabout) ɗin da zamu ɗauki hanyar gida danja (traffic light) ta tsaidamu, sai kwasar dariyar labarin da Nazifa ke bamu mukeyi.
Kusan minti goma muna a haka, saina fahimci sam motocin basa motsawa ma, buɗe motar nai na leƙa, hayaniyar mutane sosai ke tashi, dan motocin dake tahowa a dukkannin titinan huɗune suka cure waje guda, watama ta mugun bugama wata, sun saka jami’i mai bada hannu a tsakkiya sunata zabga masa masifa. Mamaki ya sake kamani, nadai dawo na zauna, mun cigaba da hira kusan ta minti ɗaya nadai sake jin abin bai zaunamin a raiba, dan wannan go slow ɗin yafi kama da wanda aka haɗa da gangan, gashi motoci sai sake taruwa sukeyi titin na sake cinkushewa. Ummie na bama Nazifa amsa ni kuma na maida kallona ga mirror ɗin waje, har yanzu dai babu alamar motsin motocin a dukkanin titinan huɗu da suka raba kansu, sai naɗan kalli Ummie ina yamutsa fuska, dan na lura har yanzu ita bama ta fahimci halin da ake cikiba.
“Ummie akwai matsalafa, tabbas wannan cinkosan haɗashi akayi akan sani”.
Da sauri ta katse wayar tana cema Nazifa muna zuwa.
Kashe motar tai duk muka fita a hanzarce, tabbas an haɗashine da gayya, hakkanne ya sakamu fara ƴan dube-dube muna kutsawa tsakanin motoci domin san isa ainahin wajen da danjar take.
Gaba ɗaya wajen ya hargitse, sai hayaniya ke sake tashi, duk yanda mai bada hannun keson dai-daita komai hakan ya gagara, ga waɗanda motarsu ta gogi junama sun fara faɗa na shirin danbe. babu yanda za’ai muyi magana muma wani ya sauraremu, dan abin yafi karfinmu.
Kalle-kalle na maida hankalina wajenyi sosai kozan samo bakin zaren,
Idona ya kasa barin wata baƙar mota mai baƙin gilashi {tinted glass}, na wuceta yafi sau uku ina sake dawowa gareta, dan sai buga azababben horn mai motar yake nason a bashi hanya ya wuce tamkar shi kaɗaine yafi kowa buƙatar titin kosan tafiya.
Glass ɗin na ƙwanƙwasa, dan na tabbata koma wanene a ciki shi yana kallon na waje ai, ba’a saukeba na sake bugawa, dan haka kawai nakejin wata irin jarumta da ƙarfin zuciya da bansan daga ina tazo minba……..
A fusace aka bugo mirfin motar ya bugeni, kafin na dawo daga jin zafin da nayi kawai naji ƙarar harbin bindiga har sau biyu.
Take wajen ya hargitse da ihu, nima na toshe kunnena ina mai duƙewa ƙasa, mutane sai fita suke daga mota suna gudu, masu dabara kuma na kwanciya a ƙasa, tuni jama’ar dasuka taru suna hayaniya kowa ya kama gabansa, wasu sai son jan ababen hawansu baya suke suna komawa da baya-baya domin ƙoƙarin barin wajen.
Cikin tunanin da yazomin daga UBANGIJINA ya sani fahimtar akwai matsala.
Murfin motar da bai gama buɗuwaba aka ziro hannu ahaka aka ƙara wani harbin na kalla, da ƙafa na turashi ya bigi motar, hakan yasaka hannun da yay harbin ya matse sosai, ƙara ya saki yana sakin bindigar itama ta faɗi ƙasa.
Jan motar sukai da wani irin ƙarfi, dukda motsocin dake gabansu bila adadin, tuni wajen ya sake ruɗewa, jikake garraaam!! Kaccaam!! Na haɗewar motoci, wata na bugar wata, gilasai sai fashewa suke famanyi, waɗanda suke a motocin basu fitaba sunata ihu na firgita.
Saura kaɗan su takemin ƙafa, nai azamar sunkuyawa na ɗauki bindigarsa data faɗi, banyi zato ko tsammanin zan iya abinda nake yunƙuriba, amma cikin amincin UBANGIJI koda na harba sai harsashin ya sauka akan tayar motar ta baya.
Tangal-tangal motar ta fara, hakan kuma ya sake hargitse wajen da ihun mutane. Kuma harbin ɗayar tayar nayi, hakan ya saka motocin dake gefenta, sukuma suka bigi fitilar dake a tsakkiyar titi ta tsaya cak.
Gaba ɗayansu suka fito kuma lokaci ɗaya, dukansu sanye cikin baƙaƙen kaya, gaba ɗayansu bindigace a hannayensu, hatta da wanda na bugama hannu da ƙofa na ɗauka tashi yana tare da wata, hannunsa dana buga sai faman jale-jale yake tabbacin na jimasa ciwo…….
Da ƙarfi naji an fisgi hannuna, dai-dai shigar ihun Ummie cikin kunnena tana faɗin “Bily!!! harsashi!!”………………✍🏻
3
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻9
Page 3
……………Shuuuu yazo ya wuce sai jikin glass ɗin wata motar bus.
Saurin kallon wanda ke riƙe da hannuna nayi, gabana yay masifar faɗuwa saboda cin karo da nai da fuskar da ban taɓa tunanin gani a wajenba ko tsammani, ya sake fisgar min hannu muka duƙe bayan wata mota saboda tahowar wasu harsasan huɗu kanmu.
Cikin matuƙar fusata ya girgizamin hannu yana faɗin, “K shashasha ki dawo hankalinki!!”.
Yanda yay maganar da wata firgitacciyar muryace ta dawo dani duniyar mutane, amma hatta da kunnuwana da sun doɗe baki ɗaya ko ƙarar harbin banaji.
Ya jefamin wata bindigar a jiki, cikin zafin nama na cafeta.
Sosai Jawaad yaji mamakin salon na bilkisu, sai dai babu wannan lokacin a garesa yanzun, dan haka ya maida hankalinsa akan abinda ke gabasu.
Wajen ya sake hargitsewa da musayar wutar harbe-harbe, kowa burinsa ya kare kansa, mutane kam bamuda tabbacin halin da suke ciki a yanzu.
Bazan iya tantance muku halin dana tsinci kainaba a ciki a wannan lokacin, amma ni kaina nasan na zama jaruma mai ban al’ajabi..+
Kowa ya jigatu a wajennan. Bagamu jami’an tsaronba baga ƴan ta’addaba, balle kuma jama’ar gari da suka fimu shiga ruɗani da tashin hankali. Sai dai abin farin cikin shine mutum biyune suka haɗu da tsautsayin harbi a farar hula, ɗaya a ƙafa ɗaya a hannu, amma Alhmdllh babu wanda ya rasa ransa sai a cikin ƴan ta’addar da aka harba a ƙirji. Mun sami nasarar cafkesu baki ɗaya, su biyarne, ɗaya ya mutu, ɗaya naji masa ciwo a hannu, sai raunika da sauran suka samu da wasu a cikinmu harda ni da gilashin wata mota ya yanka a hannu.
Wannan shine karon farko dana taɓajin mummunan rauni makamancin haka a rayuwata, sai dai lokacin dana jisa ruɗani baisa na maida hankaliba dukda inajin wani masifaffen zafi da raɗaɗi na ratsani, a cikin ƴan uwana kuma babu wanda ya lura sai da ƙura ta lafa, zuwa sannan na zubar da jini sosai, harma takai ina ganin jiri a idanuna, dama gashi inajin yunwa sosai. Rose da hankalinta ya fara kaiwa kainace ta iso gareni da hanzari, dan tuni hayaniyar mutane data ababen hawa data cika wajen ta fara yima kunnuwana nisa, duhu ya fara mamaye idanuna, hakama numfashina sai tattarewa yake waje guda yana dunƙulewa a cikin ƙirjina, abinda kawai zan iya tunawa shine taroni da tai na faɗa jikinta, daga haka ban sake fahimtar komaiba daga duniyar mutane.
★★..::..★..::..★..::..★★
A hankali nake buɗe idanuna da sukaimin masifar nauyi, naɗan motsa kaɗan ina cije leɓe kafin na samu nasarar buɗe ido da ƙyau. ‘Asibiti kuma?’ na ambata a hankali ina waige-waige da kallon ɗakin dana buɗe ido na ganni cikin bazata. A saman hannuna dake naɗe da bandegi na sauke ganina, sai yanzune abinda ya faru yake ƙoƙarin dawomin a zuciya, a hasashena zan iya cewa jiya kenan abin ya faru, dan yanzu dai ranace ƙwanyar na fahimta, idan kuma ban mantaba ƙurar jiya ta tashine da yammaci har zuwa duhun mangariba, kenan a cikin asibiti na kwana?.
Bani da amsar tambayar tawa, kamar yanda babu alamun akwai mai amsa mani ita a kusa, dan babu kowa a ɗakin sai ni kaɗai.
Na ɗauki tsawon wasu mintuna da bazan iya ƙididdige yawansuba sallamar Ummie ta riski kunnuwana, nakai dubana gareta yayinda take ajiye madaidaicin kwandon data shigo dashi a hannu,
“Bily ashe kin tashi ma?”
Tai maganar tana matsowa daf dani. tare da taɓa hannuna da naji ciwon. murmushi nai mata, kafin na buɗe baki a hankali ina bata amsa da “eh”. Zama tai a kujerar gaban gadon, tana murmushi, tace, “Kai Alhmdllh, bily kin bala’in rikitamu jiya, wlhy mun zata bazaki sake buɗe ido ki ganmu ba”. Da tsagwaron mamaki nace, “Miyasa?”. Tai ƙaramar dariya tana miƙewa, “karki damu zan baki labarin komai, yanzu dai bara na kira Doctor danya dubaki, daganan kici abinci ko, dan tun kiran sallar farko na tashi domin na haɗa miki shi”. Kaina kawai na iya rausayarwa gefe ina binta da murmushi, tare da tarin ƙaunar da nake jinmu tamkar jini guda.
Ba’a ɗauki wani dogon lokaciba Doctor yazo, yaymin tanbayoyi kafin ya bama Ummie Umarni akan ta taimakamin nayi wanka ga bayi nan, idan na kammala naci abinci nasha magani, zuwa yamma ƙilama su sallameni tunda sunga komai normal.
Da taimakon Ummie na sakko a gadon, sai yanzune na kuma fahimtar a ɗaki na musamman nake, kuma ni kaɗaice a ciki, na kalli ledar jini dake rataye a ƙarfe cikin mamaki, Ummie data lura saita bani amsa da faɗin, “Ke aka ƙaramawa, dan sanda muka iso jininki ya zuba da yawa, amma Doctor yace babu wata damuwa a hakan, idan an ƙara miki zai amfaneki, idan kuma ba’a ƙaraba bazaki cutuba, sai dai boss ya dage akan a ƙara miki jinin dole, anbuƙaci gwada su oga Hafiz koza’a samu na ɗaya a cikinsu yay dai-dai da naki, amma sai boss ya hana a gwada kowa, a cewarsa jininsa yana rukunin da zai iya bama kowa, dan haka a ɗeba nashi, kowa yasha mamakin furucinsa, amma bawan ALLAHN nan ya fuske abinsa, babu ma wanda ya samu ƙofar kawo masa wargin tambayar dalilin hakan, daga ƙarshe dai jininsa aka ɗiba aka saka miki…….”
Lokaci ɗaya nai masifar zabura da zaro idanuna waje, har ina bige hannuna mai ciwo, hakan ya sakani cije lip ɗina na ƙasa kafin nace, “Jininsa fa kikace?”.
Sosai ta ƙyalƙyale da dariya, “Wlhy karkiji wasa, jinin Boss ne ke gauraye da naki suna aiki a kowacce kafar jijiyarki a halin yanzu”.
“Na shiga uku ni Bilkisu” nai maganar ciki yanayin ta ƙaremin. Dariya Ummie ta cigaba dayi, dan na lura sam bata fahimci tashin hankalin da nake a cikiba da gaske, ban sake iya maganaba har taimin rakkiya cikin toilet ɗin ɗakin dake tsaf babu datti, ga ruwan ɗumi ta haɗa mani kuma.
A cikin dabaru nake wankan gudun karna jiƙa hannun dake naɗe da bandeji, sai dai zuciyata sam bata tare da hankalina, sai faman juya maganar sakamin jinin Boss da Ummie tace anyi nakeyi, haka kawai naji hawaye masu ɗumi suna sauka bisa kumatuna, bansan na mineneba, sannan bansan dalilin zubar tasuba, sai dai wani gefe na zuciyata na danganta saukarsu da ganin kamar bankai matsayin da za’ace jinin wannan bawa ya gaurayu da nawaba, da kuma zaka tambayeni dalilin faɗar haka a lokacin bazan iya cewa komaiba balle yin fashin baƙi. Haka dai na kammala na fito, da taimakon Ummie na kimtsa cikin kayan da tazomin dasu, ta shafa min mai harda ƴar hoda fara ta sakamin dan karna zauna fuska na ƙyalli, na zauna a saman gadon jingine da filo ita kuma ta haɗamin tea, tare da zubamin farfesun kan rago daketa ƙamshin kayan yaji.
“Ummie ƴan gidanmu kuwa sun sani?”.
Sai da ta miƙamin tea ɗin kafin tace, “Eh, tun jiya da daddare sukazo ai, Daddy, Mom sai Aamilah da Shahudah da Salim, lokacin bakisan inda hankalinki yakeba, anama ƙara miki jinin ne”.
Kaina na gyaɗa mata sannan na amshi kofin, cikin suɓucewar harshe nace, “Sanda sukazo Boss na nan?”.
Tsareni tai da kallon tuhuma, ni kuma na basar cikin kauda mata shakkun dake neman yin ƙutse a ranta, fahimtar hakanne ya sakata daidaita yanayinta itama, tace, “A’a sun tafi lokaci harsu Oga Aliyu, ni kaɗaice kawai, saboda nima Daddy ne yace na jirashi shida Mami zasuzo su dubaki saisu tafi dani, tunda Doctor yace basa buƙatar kowa ya zauna dake”.
Bansan miyasaba sai kawai naji zuciyata tamin daɗi da rashin haɗuwar tasu, na cigaba da shan tea ɗin a hankali, Ummie ce ta kuma maido hankalina gareta da faɗin,
“Ammafa kin bala’in burgeni jiya wlhy Bily, wai dama baki da tsoro ashe?”.
Murmushi nayi kaɗan ina lumshe idanuna tare da muskuta zamana yanda zanji daɗi sosai, “Ummie ba tsorone banda shiba, wani lokacin tsoro da kansa yana jin tsoron mai tsoronsa, sai dai ba kowacce ƙwarin gwiwa ke fahimtar da hakanba, a duk lokacin da kikejin tsoron abu to kawai ki tunkareshi koda kina tunanin zaki halaka ne, ina mai tabbatar miki shi wannan abin tsoron shine zai koma tsoronki, da gaske daga jiya na ƙarajin ƙarfin gwiwar yima ƙasata aiki bakin rai bakin fama , alƙawarin danai da izinin ALLAH bazata tashi a banzaba, daga yanzu zan cigaba da tunkarar kowanne irin abin tsoro daka iya tsoratar da al’ummar ƙasata koda zai sakani fuskantar ƙalubale, bani da kowa sai kaina Ummie, akwai irina da yawa a faɗin duniya, waɗanda sukafini shiga gararin rayuwa da buƙatar jin ɗumin duniya a dalilin rashin majingina ta iyaye, wadda mutuwa ta nisantasu, kokuma iyayen na raye ƙaddara ta nisantasu, sai dai ita duniyar ta juya musu nata bayan saboda bata buƙatar nasu ɗumin, waɗanda kuma keda kusanci da duniyar suna hantararsu saboda basu da buƙatar taimakonsu koda da nuna tausayawane, irina da sukasan wannan zafinne kawai yakamata ace suna iya tunawa dasu da waiwayensu a lokacin da suka sami damar ƙutsawa jikin duniya ta ƙarfin tsiya. Na shiga aikinnan ne domin ALLAH, zanyi hidima wa ƙasata domin ita ƙasata ce, zan rungumi marayu irina domin ƴan uwanane, zan kare haƙƙin ƴan ƙasata domin suɗin ahalinane, nabar kallon allon tsoro a gabana a yanzun, allon jajircewa kawai nake burin cinmawa insha ALLAHU, abokan tafiya kawai nake buƙata, waɗanda basai naje farautarsuba, da kansu nakeso suzo gareni, hakkane kawai zaisa na tabbatar da sun cika sharuɗɗan abokan gwagwarmaya dai-dai da yaƙar tsorona, jiya ta wuce, yanzu a yau muke, abi mafi muhimmanci shine mu fiskanci gobanmu idan muna cikin masu rabon gani”.
Sosai Ummie keta faman jinjina kai da dogon bayanina da bani da tabbacin zai zama abin fahimta ga kowa har ita kanta, wani zai iya kallonsa ta fuskar ƙuruciya, wani yace rashin hankali na mata, wani yace wauta ta mara gata, wani yace zaƙewa ta ƴaƴa mata masu san nuna daidaita kafaɗunsu da maza, hakan bazai dameniba a duk yanda fahimtarka ta baka, abinda na sani kawai zuciya sirrin mai ita kawai takeji, duk bin diddigin ma’abocin kusanci koya kasa kunnuwa bazaiji komaiba sai bugawarta, idan kuwa har mun yarda gaibu sunanta gaibu, to yazama tilas muyi imani da hankali koda bama ganinsa a zahiri saita yaƙini kawai.
“Maganganunki irin na mutanene masu himma bilkisu, sannan masu duba gabansu mizatazo dashi, bawai yau ɗinsu kawaiba, da jiyansu data shuɗe ta zama tarihi, tun haɗuwata dake ta farko na fahimci kinada wata baiwa ɓoyayya da bakowa ALLAH ya bama ilhamar hasasotaba, daga lokacin kuma da muka kasance ma’abota kusanci na tabbatar da zamu ribantu da junanmu, sai dai taki ribar da zamu samu saita ɗara tamu muhimmanci da amfani a garemu, k…….”
“Sam ban gamsu da bayanankiba Ummie” na faɗa cikin ɗaga mata hannu saboda yanda ta kwararo zance.
“Miyasa kikace haka Bily?”.
“Banason faɗa kice na maida hannun agogo baya, mubar zancen kawai watarana ma ƙarasa, mizai hana kije wajen Doctor kimasa maganar ya sallamemu haka, banason zaman asibiti a rayuwata”.
kafin Ummie ta samu damar yin magana aka turo ƙofar aka shigo da sallama, Dad ne, hakanne ya sakani faɗaɗa murmushi akan fuskata, saurin tashi tsaye Ummie tayi ta bashi kujerar da take zaune akai, kafin ta gaidashi cikin girmamawa. Nima gaidashi nai, ya tambayeni jikina cike da kulawa. Naji daɗin ganinsa sosai, nakumaji daɗin alhinin daya nuna akan halin dana tsinci kaina, sai dai nayi ƙoƙarin daƙile alwashinsa na buƙatar nabar aikin, danshi kam ya fara tsorata dajin cewa wannan aikin namu da gaske bai dace da ɗiya mace ba, musamman ma irina da nake yarinya ƙarama.
Cikin murmushi da girmamawa a garesa nace, “Dad addu’arku kawai muke buƙata, idan har zamu cigaba da sakawa a ranmu mata basu dace da irin kowanne aikiba saboda matsalolin cikinsa, to lallai yankinmu bazai daina fuskantar koma bayaba, hakama sauran mata masu tasowa bazasu daina fuskantar ƙalubale na daƙile burinsu akan kansu da ƙasarsuba”.
Sosai Dad yay murmushi, ya shafa kaina da cewar, “ALLAH yay miki albarka kinji, lallai tunaninki ƙyaƙyƙyawane Bilkisu, ALLAH ya kiyaye gaba to, nabiya ta wajen likita, ya baki sallama yanzu haka, sai dai ya tabbatarmin daga office ɗinku an turo ɗaukarki, ɗan aiken na hanya kuma, dan haka ni zan wuce, dama daga nan airport na dosa”.
“Dad badai har zaka sake wata tafiyar ba?”.
Murmushi yaymin mai ƙayatarwa yana jinjina kansa, “Hakane bilkisu, masu iya magana nacewa na kwance baiga gariba, muma addu’arku muke buƙata tamkar yanda kuke buƙatar tamu kinji, wannan karon kuma bazan jimaba, dan sati ɗaya kacal zanyi, idan na wuce hakan kuwa bazan zarta gomaba”.
“To Dad ALLAH ya tsare hanya, ya kuma bada nasarar abinda za’a fita nema mai albarka”.
“Amin ɗiyata, nagode sosai”.
Itama Ummie tai masa addu’a, ya amsa mata da kulawa kafin ya ajiye mana kuɗaɗe masu kauri ya fice daga ɗakin”.2
Koda Dad ya fice fuskarsa ɗauke take da murmushi tare da ɗunbin tausayin yarinyar a ransa, shidai haka kawai ALLAH ya dasa masa ƙaunarta a zuciya, yaɗan juya ya kalli ɗakin yay murmushi kafin ya cigaba da tafiya……..
Gaff sukaci karo da mutum, Gimba yay saurin fara jero kalamun ban haƙuri a gareshi. Batare da Dad yay masa wani kallon arziƙiba yace babu damuwa, yay wucewarsa. Binsa da kallo Gimba yay cikin wani tsagwaron mamaki da juya abinda ya gani a cikin zuciyarsa, sarai ya gane mahaifin matar Boss ɗinsace ta da, kuma mijin Gwaggonsa, afili yace, “To mikenan? Mi yazo yi nan? Minene ma’anar wannan kallon da yayma ɗakin nan? Minenema haɗinsa da ɗakin?”. Bashi da mai amsa masa wannan tambayoyin, dan haka yaja bakinsa ya tsuke dan bai dace ya shiga abinda babu ruwansaba, Boss na yawan masa nasiha da kiyaye abinda ba huruminsaba koda a inane, kuma koda akan minene.
A ɗaki kuwa bayan fitar Dad yabo Ummie ta shiga jero masa, yayinda Bilkisu ke tayata tare da ƙara buɗe ƙyawawan halaye na Dad waɗanda Ummie batasan da suba. A haka gimba yay sallama a ƙofar ɗakin, sai da na suturta jikinna kafin mu bashi damar shigowa, dukda bamusan shiɗin waneneba.
Mun gaisa da juna cikin girmamawa, sannan ya kora mana bayani akan cewar Boss ɗinsa Jawaad ne ya bada umarnin yazo yakaimu gida dan an bani sallama.
Kallon juna mukai ni da Ummie, kowanne baki a hangame, sai dai bamu da damar bin ba’asi akan wannan umarnin, dan kuwa dai yana sama damu, mizaisa mu tuhumesa da abinda bamu da bakin zarensa. Haka muka shiga kimtsawa har Doctor ya shigo, ya ƙara mana bayani akan yanda zan kula da cuwon saboda gudun karya zarta haka, tare da kwanakin da zan ringa zuwa asibitin domin tabbatar da ingancin kulawar da nake bashi.
___________________________
JAWAAD
___________________________________
Zaune suke a office ɗinsa su huɗu, aminan juna kenan da sukejin kansu jini guda, sannan abokan amanar juna masu taruwa wajen magance matsalolin juna da ƙarfin zuciya dana aljihu.
Sunyi nisa cikin tattauna abinda ya faru a yammacin jiya ne, domin dai da gaske Jabeer ne ya haɗa cinkoson jiya da gangan saboda son cimma burin kama tsagerun da suka biyo, amma sai suka ɓace musu, ganin zasu rasa wannan damarne Jawaad ya bama Jabeer umarnin nuna ƙwarewarsa kasancewarsa masani sosai ta ɓangaren na’ura mai ƙwaƙwalwa.
A take kuwa ya nuna gwarzantakar tashi, ya haɗa cinkoson da su Bilkisu suka riska saboda tabbacin nan kaɗaice hanyar da masu laifin zasubi su tsira da wuri, ita kuma Bilkisu tayi tarar aradu daka akan abinda bata da tabbaci.
Aliyu ne ya fara faɗin, “Maganar gaskiya na daɗe banga jarumar mace mai ƙarancin shekaru irin yarinyarnanba, a yanda labari ke fitowa da ga bakunan mutane na yanda ta tari motar mutanen da suka fara ganin farkon al’amari da yanda ta tunkari mutanen zai baka tabbacin da gaske tanada kaifin zuciya akan aikinta”.
Cikin jin jina kai na tabbaci Jabeer yace, “Lallai maganarka tana akan gaskiya wlhy Aliyu, nifa abindama ya sake birgeni da ita shine, dukda mugun ciwon da taji, amma saita dake dan tabbatarma da duniya lallai ita ma’aikaciyar tsaroce ta gaske ba ƴar burgaba”.
Fuska shimfiɗe da murmushi Hafiz yace, “Sosaima kuwa Jabeer, dolene ƙaimin yarinyar ya burge kowa, dan kuwa da ƙwaƙwalwa tai amfani wajen fahimtar motar tana da alaƙa da rashin gaskiya, ta kuma nuna himmarta na sadaukarwa koda hakan na nufin zata cutu a wajensu, ta cancanci kowanne irin jinjina ga hukumarnan tamu, musamman idan akai la’akari da shigowarta cikin aiki jiya-jiya kawai, bana tunanin kuma an taɓama fita da ita wani aiki makamancin haka koda sau ɗaya”.
Duk wannan zance da suke faman zubawa akan yabon Bilkisu da jinjina himmarta Jawaad na zaune shima a cikinsu, yana sanye cikin baƙaƙen suit kamar sauran da a kullum suke ƙara masa kwarjinin kasancewarsa ma’aikaci, sai dai ya cire rigar sama, yana zaune ne kawai da baƙin dogon wandon da rigar ciki mai dogon hannu kalar kore mai haske, maɓallan rigar uku a buɗe, hakanne ya bayyana singlet ɗinsa kaɗan fara tas, yaci zanzaro, ya tsuke ƙugunsa da belt kalar shirt ɗinsa.
Abinda zai baka mamaki ko tari bai yiba akan maganar, baima nuna ya fahimci mi suke tattaunawarba sam, yana zaune ne ƙafa ɗaya kan ɗaya tamkar wani basarake, kansa sunkuye yanata faman danne-danne a cikin tab… ɗinsa ta kamfanin Apple, sam fuskarsa babu wata walwala, kuma ba’a tsuke take sosaiba.
Aliyu ne yakai dubansa garesa, tare da faɗin, “Ka fuskanci abinda muke tattaunawa game da yarinyarnan kuwa Jay?”……………✍11
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.16Page 4
……………Shiru tamkar bazai tankaba, kusan sakanni sha biyar kafin yay magana batare daya bar danne-dannen tab… Ɗinba balle ya kallesu, “Wace yarinya kenan?”. Yay tambayar cikin nuna halin ko’in kula balle su sami ƙwarin gwiwa akan ya jisun.
Duk kallonsa sukai da mamaki saboda yanda sukasanshi dason mutum mai himma, amma yanda ya amshi maganar ya matuƙar basu mamaki a yanzun.
Jabeer ne yace, “Yarinyar jiya daka bama jini mana Jay”.
“Humm” yace kawai ya sharesu bai sake tankawa ba, tsawon mintuna duk sun zura masa idanu suna jiran ƙarin bayani, dan sunyi tsammanin fara jin yabon yarinyar da ga bakinsa ma kafin su su furta, amma ya share kamar ya manta dasu ma a office ɗin.
“Wai boss lafiya kuwa?” Hafiz yay tambayar a wani yanayi.
Sai yanzune ya ɗago ya kallesu su duka, kallo irin a taƙaice ɗinan ya janye mayatattun idanunsa masu cikar gashi da haske tamkar madara, ya taɓe baki kaɗan kafin ya miƙe daga wajen ya nufin kujerarsa ta zama, dan da suna zaunene a rukunin kujeru da’aka shirya a office ɗin domin hutawa ko ganawa da baƙi na musamman.
Sai da ya zauna sosai ya juya kujerarsa tana fuskantarsu kafin yace, “Abun harinmu a yanzu shine mutuwar jami’inmu da sir Ahmad yamin bayani, minene shawararku akan hakan?”.
Aliyu ne ya samu damar faɗin, “Bincike akan shi ɗin wanene? Tunkan fara aiki a wannan hukumar har zuwa farawar tashi, tare da sanin masu bashi gudunmawa akan aikin da yazama sanadinsa, da kuma sanin a ƙarƙashin wa ya samu umarnin”.
“shawara mai ƙyau” Jawaad ya faɗa yana lumshe idanu da kwantar da bayansa jikin kujerar yana lilawa a hankali fuskarsa ɗauke da murmushi, kusan sakanni biyar kafin ya sake ɗagowa yana kallonsu da nazartarsu. Ya ɗauke idanunsa tare da sake komawa jikin kujerar ya kwanta, “Idan an sallamota daga asibiti zatayi bincike akan dukan bayanan Aliyu”.
Cikin matuƙar mamaki suka kallesa, cikin harɗewar harshe Jabeer yace, “wai kana nufin yarinyar?”.
Kallonsa kawai yay ya janye idanu, sai dai baice komaiba. Sun fahimci amsar kenan, dan haka Aliyu yace, “Amma boss baka ganin aikin zai mata girma? Musamman idan mukai dubi akan shine na farko?”.
Cikin halin ko in kula ya taɓe baki, ba tare daya kallesu ba yaja wasu takardu dake saman tebir ɗin nasa yana faɗin, “Maybe hakan, maybe kuma ba hakan baneba, naga kuma da kanku kun yarda da ƙwazonta, to miye kuma na kokwanto yanzun?”.
Babu wanda ya sake cewa komai. sai dai a ƙasan ransu duk sai suka kasance cikin nadamar kwarzanta ƙwazon yarinyar da yawa irin haka, dan a ganinsu bata kai ƙwarin da za’a sakata a irin wannan babban aikin hakaba mai haɗari, musamman idan sukai dubi da ko rose data daɗe a cikinsu baya bata irin wannan damar.
Takardar da ya maida hankali a kanta ya ɗago saitin Hafiz, “Hafiz wanene da wannan bayanan haka?”.
Tasowa Hafiz yay ya dawo gabansa, ya zauna a ɗaya daga kujerun gaban tebirin yana mai amsar takardar, nazarin mintuna biyu ya ɗago kai yana kallonsa, “Akan case ɗin yaron nan da aka samu makamai a shagonsu ne, Aliyu ne akan binciken kuma”.
Jawaad ya maida kallonsa ga Aliyu, hakan ne ya saka Aliyun tasowa ya nufosu shima.2
__________★★__________
BILKEESU
_________________________________
Wani irin mayataccen ƙamshi ya shiga rige-rigen zirarawa cikin ƙofofin hancinanmu yayinda muke shiga motar da boss ya turo ɗaukarmu, batare da kowannenmu ya fargaba muka tsinci kawunanmu da lumshe idanu muna sake buɗe hancunan namu sosai. A haka yaja motar muka bar asibitin, tabbas wannan ƙamshine daya cancanci ajiyeshi a ma’ajin zuciya da ƙwaƙwalwa saboda ya kasance na musamman, bansan miyasa na kirashi na musammanba, sai dai kawai zan iya fassara hakan da kasancewarsa na musamman a duk lokacin da hanci ya shaƙa koda ba namuba. Naji tamkarma kar motar ta tsaya ace na daina shaƙar wannan ƙamshin, sai dai babu yanda zanyi dan hakan tilasne. A wannan yanayin muka isa gida, ya ajiyemu a gate ya juya, mukuma muka shiga ciki bayan mun masa godiya.
Mun iske gidan babu kowa, suna gidan rasuwa su duka, dan haka mukai zamanmu dagani sai Ummie da tace boss ya bata umarnin ta zauna dani harna warke tun a jiya. Ban tambayeta daliliba, kamar yanda itama bata kawo komai a rantaba game da hakan, sai dan tana ganin ya fahimci bani da wadda nakeda kusanci da shi sama da ita a station ɗin namu.2
STORY CONTINUES BELOW

__★.:.★__________★.:.★__
JAWAAD
_____★.:.★__________★.:.★_____1
Suna tsaka da cigaba da magana shi da su Aliyu kira ya riskesa daga office ɗin B.G, duk da kiran ya bashi mamaki daga shi harsu Jabeer ɗin hakan bai hanashi fita domin cika umarni ba.
Galala nai da baki ina kallon haɗuwa da tsari na office ɗin da Jawaad ya shiga, komai yaji babu algus. Banma kaina buƙuluba nabi ko’ina daki-daki da kallo a office ɗin, kafin na sauke idanu ga mai ikon faɗa aji na hukumar tasu. Danƙari, na ambata a zuciyata dan kuwa munzo ƙarshen zance, sam babu alamun fara’a balle sassauci tattare dashi, Jay ya miƙa gaisuwa cikin girmamawa kafin ya samu izinin zama daga gareshi.
“Sir Ance kana kirana” Jawaad ya faɗa cike da girmamawa.
A cikin maƙoshi ya bashi amsa da cewar, “Uhhm” daga haka yaja bakinsa yay tsit. Gani nai shima Jawaad ɗin ya sake kame kansa ba tare daya sake tankawa ba, kusan mintuna huɗu suna a haka kafin ya ɗago kai tare da juyama Jawaad fuskar lap-top ɗin dake gabansa, hotone mai motsi (video), Bilkisu ta bayyana tana harbi da bindiga har guda biyu a rikicin jiya, gaba ɗaya bidiyon bai wuce na minti ɗaya da wasu sakanni ba, saboda iya itaɗin kawai aka nuna, ƙarewarsa ce ta saka Jawaad kallonsa cikin rashin fahimta.
Cikin zafin rai da fusata ya zazzaroma Jawaad ɗin idanunsa jajaye, “Wannan yarinyar tanada izinin yin harbi ne kamar haka dama?”.
Jawaad da ya tsuke fuska shima ya girgiza kansa kawai.
“Ya akai tayi kuma?”.
Sai da Jay ya furzar da huci kaɗan kafin yace, “Sir bamu da wani zaɓine bayan hakan, domin musayar wutace, idan kuma bata da makamin kare kanta a hannu rayuwarta na cikin haɗari, musamman daya kasance da taimakonta muka riski masu laifin”.
“Hakan yana nufin shine matakin ƙarshe da kuke da mafita kawai?”.
Shiru Jawaad yay bai motsaba, sai maƙogwaronsa ne keta kai kawo a cikin wuyansa, yayi kicin-kicin da fuska.
“Da kai nake magana Captain!”.
“Sir nasan munyi kuskure, amma a duba uzirinmu muma, musamman na isa wajen a ƙurarren lokaci, sannan a duba irin rawar da yarinyar ta taka, duk da kasancewarta ƙaramar ma’aikaciya, wadda ta shigo jiya-jiya cikin wannan hukumar tamu, ta nuna ƙwazon da ya kamata a jinjinama ƙoƙarinta ba ƙalubalantar taba, domin kuwa ita bata da laifi, nine mai laifi dana bata bindigar”.
“Uhyim, kana nufin yanzu dai ka kareta?, sannan dukkan hukuncin da zai biyo baya zaka ɗauka kuma?”.
Shiru tamkar bazai amsaba, sai kuma ya ɗago idanunsa harsun kaɗa da ɓacin rai, a kasaushe yace, “Aimin duk hukuncin da za’ai matan babu damuwa”.
Shiru B.G yay kawai yana kallon Jawaad ɗin, yasan yaron dama akwai taurin kai, dan tun shigowarsa hukumar ƴan sanda ma da tsaurin ido ya shigo, kasancewar wanene mahaifinsa yasa aka hana kowa nuna masa yatsa, himmarsa da zafin nama ne ya saka aka maidoshi cikin hukuma DSS, shi kuma har cikin ransa yaron bai masaba, sanin dalilin kuwa wannan sirrinsane….
“Kaje zamu nemeka” B.G ya faɗa a daƙile.
Uffan Jawaad baice ba, ya miƙe kawai tare da yin salute nashi ya fice abinsa yana haɗiyar zuciya, duk wanda zai iya ganinsa a wannan lokacin dolene ya fahimci ransa a matuƙar ɓace yake, mai makon ya wuce office ɗinsa sai ya nufi office ɗin L.C, wato sir Ahmad barewa, canne kawai zai kai damuwarsa ya samo mafitar da yake buƙata.
Bayan yay knocking ƙofar aka bashi izinin shiga, ya riga da yasan ya gansa ta cctv, tunda ya turo ƙofar ya shigo sir Ahmad ya fahimci akwai damuwa, ya kafeshi da idanu kuwa, yayinda shi kuma Jawaad ɗin yaƙi yarda su haɗa idanu.
Sai da ya miƙa gaisuwa Sir Ahmad yay masa nuni da kujera alamar ya zauna.
Koda Jay ya zauna sai baice uffanba, sai ajiyar zuciya kawai yake faman yi, sir Ahmad yay murmushi irin nasu na manya masu kaifin tunani, kafin ya miƙe daga mazauninsa ya nufi firij ɗin dake a office ɗin, goran ruwa ya ɗakko ya miƙa masa batare da yayi magana ba, babu musu ya amsa, ya ɓalle murfin yana kai goran bakinsa, sai da ya shanye fin rabi sannan ya ajiye yana sauke numfashi a jajjere.
Wani murmushin Sir Ahmad ya kumayi, sannan ya zauna a kujerar dake kusa da Jawaad ɗin suna kallon juna “Captain! Lafiya kuwa? Waya zinguro mazajene?”.
Idanu Jay ya ɗago ya kalli Sir Ahmad, sai kuma ya janye yana shaƙar numfashi da zafi…..
“Jay!”
Sir Ahmad ya kirayi sunansa yana ɗora hannunsa bisa kafaɗarsa.
A karo na Biyu Jawaad ya sake kallon Sir Ahmad barewa, ya cije leɓensa da ƙarfi yana faɗin, “Daga office ɗin B.G nake Sir”.
“Na sani ai” cewar sir Ahmad yana murmushi.
Cikin sauri da tsagwaron mamaki Jawaad ya kalli Sir Ahmad, kallo irin na tuhuma.
Ƴar dariya sir Ahmad yayi, ya kuma kai hannu ya bubbuga kafaɗar Jawaad ɗin a hankali, “Kar kai fushi yarona, karkuma ka shiga ruɗani, banason ka manta kanka a cikin mutane masu kaifin basira, za’ai amfani da yarinyarne kawai ai wasa da hankalinka, kaga kenan an samo lagwonka da damar bama maƙiyanka yin wasoso a saman mutuncinka, kar kaga laifin B.G, shima sashi akayi, domin bana tantama umarni ya samu daga sama, sai dai wanene? Akan minene? Shine ban saniba”.
“Zuutt!” wani abu dake tsaye a maƙoshin Jawaad ya faɗa cikin cikinsa, ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, saboda dai Sir Ahmad ya dawo dashi a hayyacinsa da wuri…
Sir Ahmad ya miƙe yana murmushinsa na kamilallun mutane, ainahin kujerar zamansa ya koma ya zauna..
“Abin bai baka mamakiba ace iya inda take harbin kawai aka kawo masa, sannan kuma ita kaɗai, bayan kuma batakashin da kuka gwabza a wajen ku kusan goma ne”.
“Sir ai abinda ya matuƙar ɓatamin rai kenan, taya za’ai ace itace kawai za’a ɗauka?….”
“Saboda ita kaɗai tazo da salon da ya ajiye ruɗani a zukatan masu fargaba akan jajircewarka”.
“Salo kuma sir?!”.
“Yes! Jawaad, salo mai ƙayatarwama kuwa, andaɗe ba’a samu mai ƙaracin shekaru irinta da wannan ƙwazonba, abin ƙarin mamakin kuma gata mace, yarinyar da alama zata ajiye tarihi a wannan hukumar, dan alamomin hakan sun farane daga jiya”.
“Sir! to amma su wanene ke ganin hakan matsayin ƙalubale garesu? Miyasa kuma….?”.
“Nima ban saniba Jay”.
Shiru Jawaad yay na wasu sakanni kafin yace, “Saboda mi suka zaɓi hukuntata bayan karramawa ta cancanta dashi sir?”.
Sir Ahmad yay gajeruwar dariya idonsa akan Jay, yace, “Saboda ƙwazonta abin dubawane ga mai hankali, sannan abin tunani ga irin waɗanda basa buƙatarta, wannan shine aiki na farko da yarinyar tayi, kuma ba sakata akayiba, sai dai ƙwazonta ya girmi matsayinta da gogewarta a aikin, hakanne ya sakasu saka maka alamar tambaya (?), musamman daya kasance tare da kai aka fara ganin baiwar ta ta”.
Karan farko da Jawaad ya ƙyalƙyale da dariya harda dukan tebir ɗin gabansu, Sir Ahmad dake kallonsa shima murmushinsa ya faɗaɗa, ya juyo sosai yana fuskantarsa, har yanzu kuma fuskar tasa da sauran dariyarsa irin wadda kafin yayita akan kai ruwa rana,
“Sir kasan minene kuwa?”.
“Saika faɗa Jawaad”.
“Sun bani dariya ALLAH, danni Ko sunanta ban saniba fa”.
Dariya shima sir Ahmad ya shiga ƙyalƙyalawa, kafin yace, “Cakwakiya kenan, to tabbas kuwa daga masu wannan ƙullin abun ba haka bane ba Jawaad, kallon ƘWAI CIKIN ƘAYA sukema lamarin”.
“Nima na fahimci hakan a yanzu sir”.
“Yayi ƙyau. Miya faru jiya?”.
Tun daga farkon zuwansu inda abun ya faru har ƙarshe Jawaad ya bama Sir Ahmad labarin komai bai ɓoye masaba.
Kai kawai Sir Ahmad yake jinjinawa har Jawaad yakai ƙarshen jawabinsa, ya sauke numfashi kaɗan yana faɗin, “Zamu shiga meeting anjima, kuma nasan akan wannan maganarne, shawara ɗaya dazan baka yanzu shine, kai ƙoƙarin gano wanda ya ɗauki wannan bidiyon, sannan kayi gaggawar samo bidiyon da yafi wannan na wajensu tsaho, ka kumayi saurin rubuta bayanai akan komai ka tura office ɗin L.G tare da bidiyo ɗin daka samo ɗin”.
Kamar Jawaad zaice wani abu, sai kuma yay shiru yana miƙewa da faɗin, “Okey sir, zanyi ƙoƙari insha ALLAH”.
★★★★1
Gaba ɗaya kan Jawaad ya kulle da wannan lamari, ya rasama ta yaya zai fassara al’amarin, maganganunsa da Sir Ahmad kawai ke masa kai kawo a cikin zuciya, tare da zuwansa office ɗin B.G, ya rasa ina zai kama ma shikam? Yana buƙatar ganin su Jabeer tare dashi yanzunan, sai dai tabbas bazai yuwu a station ɗinanba, dan yanzu dukkanin motsinsa abin bibiyane.
Ƙaramar wayarsa ya ɗauka ya turama Hafiz saƙo, kafin ya tura wayar aljihu bayan ya kasheta gaba ɗaya ma, wasu takardu ya ɗiba ya fito a hanzarce, hana kowa ya bisa yayi, ya shiga mota shi da Gimba kawai suka fice daga station ɗin.
Danne-danne yaketa famanyi a lap-top, hakan ya saka gimba kallonsa ta cikin madubi, “Boss! Ina zamuje?”.
Ba tare da ya ɗagoba yace, “A.Y Street”.
Cikin girmamawa Gimba ya amsa, tare da juya kan motar suka nufi hanyar gidan Jawaad ɗin dake anguwar A.Y street.
Sunyi wajen mintuna talatin da zuwa kafin su Aliyu su iso. A falo suka iskeshi har yanzu yanata faman danne-danne a lap-top, a haka ya amsa sallamarsu ko ɗagowa baiyiba ma. Sai da suka zauna da kusan mintuna biyu sannan ya ɗago ya kallesu, kallo ɗaya yayma Rose ya ɗauke kansa, hakan yay bala’in sosa ranta, dan akwai kwallin data shafa, an kuma tabbatar mata idan suka haɗa ido da shi zai haukace mata, yabar kallon kowacce mace da gashin arziƙi sai ita, amma ɗan rainin wayon tun’a station takeson su haɗa ido da shi hakan ya gagara…
“Boss! Lafiya dai ko?”.
Aliyu da ya kafeshi da idanu ya faɗa.
Lap-top ɗin ya ajiye yana faɗin, “Da dai sauƙi Aliyu, an yanka ne ta tashi”.
“Kamar ya?;” suka faɗa cikin haɗa baki su uku, rose ce kawai da bata fahimci hausarba batace komaiba.
Cikin takaici Jawaad yace, “Ƴan uwana wasan jiya ya koma yaƙi, kukan tsuntsuwa mai zanen kanari ya zame mana abin magana”.
Sun fahimci zaurancensa, saboda wannan yana ɗaya daga cikin salonsu, musamman akan aikin da suka samu gamayya da waɗanda basa cikinsu, sai dai basu fahimci dalilin zaurancenba a yanzu, saboda duk sune a wajen babu baƙon ido.
Jabeer yace, “Jay bansan miyasa ka zaɓi ƙin buɗe zancenba, bayan kuma duk mune babu wani bare a cikinmu?”.
Jawaad yace “Nima bansan miyasa harshena ya zaɓi hakanba Jabeer, sai dai saƙon kamar tun daga zuciyane”.
“Idan na fahimta, kamar zuciyarka na ɗarsa maka akwai ɗan baya ga dangi kenan a cikin tafiyar?”. Hafiz yay maganar cikin taraddadi.
Cikin sauke nannauyan numfashi Jawaad yace, “Bani da tabbas, sai dai zuciyata na rayamin akwai idon mikiya a bayanmu”……………✍
13
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻1Page 5
………….Duk Kasa cewa komai sukai, sai idanu da suka zubama Jawaad tamkar wani bakonsu.
Rose da zuciyarta ke tafasa akan rashin kallonta da jawaad baiyiba ta kasa daurewa, ta dubesu baki ɗaya a wani yanayi, “Boss wai mike fauwane? tai maganar cikin harshen turanci da tsare Jawaad da idanu tana fatan ta dace yanzun.
A mamakinta yanzunma dai ƙin kallonta yayi, sai Lap-top ɗinsa ya miƙa mata kawai, ya koma ya zauna tare da ɗaukar tab.. Ɗinsa ya shiga tafa saƙo da hanzari.
Gani nai Aliyu ya ɗago ya kallesa, yay masa wani salo da ido tare da cije baki, murmushi Aliyu yayi kawai ya maida kansa, kafin ya miƙe yabar falon, hakama Jabeer da Hafiz duk ya tura musu suma, Hafiz shima tashi yay ya fita, Jabeer kuma ya koma kusa da Rose dan kawai ya ɗauke hankalinta da aikin da Jay ya bata itama.
Bayan fitar su Aliyu da kusan mintuna tara ya miƙe yabar falon ya nufi bedroom ɗinsa. Sai da ya kulle ƙofar kafin ya ciro ƙaramar wayarsa yay kiran Hafiz.
“Hafiz yaya? An dace kuwa?”.
“Ba’a daceba Boss, amma ga shawara mana?”.
“Micece shawarar taka?”.
“Mu bincika kowanne manhajar yanar gizo ko zamu dace wani ya ɗauka, kasan yanzu ba’a raba mutane da ƴan ɗauke-ɗauke a waya, maganar gano wanda ya kaima su B.G kuma ba abune mai sauƙiba ace yanzu da gaggawa, sai dai mu canja shawara ta wannan gaɓar”.
“Na fahimceka Hafiz, yanzu kayi duk yanda ya dace, amma inaji a raina koma wanene yakai wannan bayanan yana da kusanci damu Hafiz, amma banason zargin kowa”.
“Boss zargi dolene, kuma koma wanene ya daɗe a jikinmu, a sannu zamu cinmasa da ƙarfin ƙudirar UBANGIJI, dan shine ke haska mana hanya a dukkan lamuranmu”.
“Insha ALLAHU Hafiz, yanzu dai sai na jika”.
Yana yankewa yay kiran Aliyu shima, sai dai daga ɓangaren Aliyun an dace, dan ya turo masa dukkan bayanai akan Bilkisu da abinda ya shafi shigowarta hukumar tasu, da horon data samu, da ƙwazon data nuna tun a wajen horaswa, alaƙarta da Qaseem, sai dai babu wani bayani kafin zuwanta gidansu Qaseem ɗin, hakkanne yaɗan tsayama Jawaad a zuciya, har yakejin dolene ya sake binciken, dan karfa nan gaba ta zame masa ƘWAI CIKIN ƘAYA kuma kamar yanda ƴan bayan fage ke hasashe.+
Daga ɓangaren Hafiz ma an dace daga baya, dan kuwa cikin amincin ALLAH ya samo bidiyon faruwar komai tun daga lokacin da Bilkisu ta kaima motar masu laifin caffa kafin zuwansu, har zuwa sanda abubuwa suka lafa.
Yaci karo da Bidiyon ne a wani chennal na youtobe, bayan ya shiga manhajar Google yay Searching, sai dai abinda ya bashi mamaki yana kammala sauke video’n akan manhajar ta youtobe wanda ya ɗora ɗin ya saukeshi daga accaunt ɗin, hakan sai yay bala’in ɗarsa mamaki a zuciyar Hafiz, harya kasa haƙuri ya kira Jawaad ya shaida masa.
Murmushi Jay yayi yana shafa kansa, “Ba abin mamaki bane Jabeer, musamman idan mukai la’akari da babu wata kafar yaɗa labarai da dama ta saki bidiyon mai tsawon hakan, sai wasu ɓangarori da dukansu iya inda muke musayar wutane kawai”.
Hafiz yace “Hankalina sam bai kaiba sai yanzu kam, koma miye yake a ɓoye ALLAH zai bayyanashi ai, mudai domin ALLAH mukema ƙasarmu aiki, duk mai yunƙurin daƙilemu kuma ALLAH zai mana maganinsa”.
“Insha ALLAHU kuwa Hafiz” Cewar Jay cike da takaici.1
Kafin dare duk sun haɗa bayanan da ya kamata akan maganar, sun tura iya waɗanda Sir Ahmad ya umarcesu zuwa Office ɗin, L.G, sauran kuma sun adana a wajensu domin ya zame musu hujjar kare kai, hatta da bidiyon suma gutsira sukai suka tura, sauran kuma suka adana a wajensu.
___________★__________
SHAHUDAH
_________________________________
Tunda suka fara zuwa gidan rasuwarnan sau ɗaya taga Jawaad, harga ALLAH ita kuma dominsa take zuwa, a tunaninta idan suka haɗu zai matuƙar rikicewa da ganinta, musamman ma yanda ta sake canjawa da ƙyau mai ƙayatarwa, sosai ta gama shirya shika-shikan rama dukkan abubuwan da yay mata kafin ta yarda da buƙatarsa ta komawa gidansa.
Sai dai abin mamaki da al’ajabi dukkan tunaninta sai bai zama gaskiyaba, dan kuwa ko a randa suka haɗu kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa, komai kuma a kan idanun Mom ya faru, dan suna a falon mama Atika ne a washe garin rasuwar ya shigo da baƙi su Sir Ahmad da sukazo gaisuwa. Sarai idanunsa sun gane masa Shahudah, amma sai ya ɗauke idanu cikin nuna halinsa na ko’in kula da abu.
Abin ya sosa mata rai sosai, amma saita danne da yaƙinin ƙila yayi hakane saboda ganin suna cikin jama’a. Koda suka koma gida sai basuyi maganar da Mom ba, saboda kowa ya dawo a gajiye wajen bacci yafi buƙata. Washe gari kuwa kwalliya tayi ta musamman dan Jawaad nanma babu sa’a, dan har dare da suka baro gidan bata sakashi a cikin idanunta ba, washe gari kuma suna isowa gate ɗin gidanne motar Jawaad ɗin ke fita da alama ya nufi office ne. Waɗanan akasin da akaita samune suka jefata a cikin damuwa har yau ta kasa daurewa.
STORY CONTINUES BELOW

“Mom kinga abinda Bb ya kemin kuwa? Bayan ya kamata ace ya nuna zalamarsa da kewata na shekarun da muka kwashe bama tare”.
“Huhm” Mom ta faɗa tana shafa kan Shahudah dake saman cinyarta, dan kuwa suna cikin bedroom ɗin Mama Atika ne ita da Shahudahn kawai, dan ta fahimci ɗiyar tata na tare da damuwa, yau tunda sukazo gidan ta shigo ɗakin Mama Atika bata sake fitaba, shiyyasa ta biyota, sai ta isketa cikin damuwa, hakanne ya sakata zama ta dora kan Shahudah a cinyarta tana shafawa, itakuma take bata labarin ruɗanin data shiga akan tarbar data samu daga wanda batai tsammaniba daga Bb ɗinta (Jawaad).
Mom ta haɗiye abinda ya tsaya mata a maƙoshi tana sake yamutsa sumar Shahudah’n, “Kar taurin kan yaron nan ya ɗaga hankalinki fiye da haka Shahudah, ki barsa, ni da kaina zan sauke masa wutar dake ci a kansa, bara dai a gama hidimar rasuwarnan kinji”.
Kai Shahudah ta ɗaga mata cike da shagwaɓa, har ƙwalla na sakko mata a kan kumatu tace, “Amma Mom wane mataki zaki ɗauka to?”..
Mom ta share mata hawaye tana murmushi, “Karki damu Shahudah zaki gani, kedai sonake kicigaba da kwantarmin da hankalinki, nan kusa kaɗan zaki dawo ɗakin mijinki”.
Kai Shahudah ta ɗaga mata tana murmushi da rungume mom. Murmushi mom tayi taci gaba da lallashinta cikin so da ƙauna.
Nikam nace, “Mai uwa a gindin murhu baya cin tuwonsa gaya ai Shahudah😋😜🤸🏼.2
..::..★__________★..::..
BILKEESU
____★..::..★__________★..::..★____
Kwanaki huɗu cir bana zuwa Office ina gida ina jiyyar hannuna, yayinda kullum Ummie ke tare dani, ƴan gidanmu kuwa basa yini suna gidan rasuwa, barci kawai ke kawosu gidan. A kwana na biyar nai shirin komawa aiki, dan naji sauƙi sosai, a kuma daren ranarne Yah Qaseem ya dawo, nayi farin cikin dawowar tasa, dan nikaina nasan idan nace banason Yah Qaseem na yaudari kaina, a ƴan kwanakinan da bayanan sosai nayi kewarsa.
Tun a daren yake jeramin tambayoyi akan hannuna, bai samu amsa ko ɗaya ba daga gareni sai murmushi kawai.
Koda muka tashi da safe ma dai bai fasa sonjin musabbabin ciwonba, da naga ya damu sai kawai nace masa tsautsayine ya gitta mani a wajen aiki, badan ya yardaba ya ƙyaleni kawai, kasancewar yau zan koma aiki nima sai na bisa muka tafi tare kamar yanda muka saba kafin yay tafiyar.
Yah Qaseem na gama daidaita fakin motarsa wani jami’inmu na isowa wajen, ya isarmin da saƙon kira daga office ɗin B.G, maganar da jami’in yazo da itane ya sakamu kallon juna ni da yah Qaseem ɗin.
Idanuna na janye daga cikin na Yah Qaseem daya tsatstsareni da kallon tuhuma, da ƙyar na haɗiye yawun da ya tarumin a baki, dan girman office ɗin mai kiran nawa na kalla da kuma tunanin minene dalilin kiran?.
Yah Qaseem da har yanzu idanusa ke kaina da alamar tambaya na kuma kallo, ya gyara tsaiwarsa yana mai jehomin tambaya,
“Bilkisu mikike ɓoyemin ne?”.
Da sauri na girgiza masa kaina, “Wlhy Yah Qaseem bana ɓoye maka komai, nima bansan minene dalilin kiranba, amma bara naje najiyo”.
Ban jira amsarsaba na bar wajen cikin tafiyar sassarfa, zuciyata sai bugu take da sauri-sauri, dan inaji a raina wannan kiran bana lafiya bane ba, musamman idan nai dubi da ƙaramin matsayina a hukumar.
Koda na iso sai da na jira aka bani izinin shiga sannan, wannan shine karon farko da zan shiga office ɗin a rayuwata, ba shi kaɗai bane a cikin office ɗin, jinai wani abu ya tsargamin daga saman kaina har zuwa yatsan ƙafata, na aro jarumtar dole na yafama kaina tunda bansan minene dalilin kiranba. Na miƙa musu gaisuwa cikin girmamawa kafin na zauna inda aka nunamin.
Tambayar farko da aka jefamin ta sakani ɗago idanuna na kallesu badan na shiryama hakanba, ba firgici ne ya sakani kallon nasu ba, nutsuwace ta zomin saɓanin yanda na shigo a rikice, dan kuwa a nawa tunanin inhar akan rikicin daya faru kwanaki biyar da suka wucene banga wani abin kuskure dana aikata a cikiba, zamana na gyara na fara amsa musu tambayarsu da iya gaskiyata dana sani.
Yanda Bilkisu ke amsa musu kowacce tambaya kanta tsaye babu ko ɗigon firgici ko rawar harshe ya sakasu kafeta da idanu, su kansu iya zallar gaskiyarta suke gani a saman fuskarta da furucinta.
Sun mata tambayoyi sosai, domin sake tabbatar da gaskiyar tata suka sake maimaito mata dukkan tambayoyin da sukai matan a farko, abinda ta faɗa daga farko shine ta sake maimaitawa saboda hakan shine gaskiyarta.
Kusan awa ɗaya da wasu mintuna suka sallamoni na fito, a raina sai juya wannan al’amari nakeyi…
_________________________________
JAWAAD
Zaune yake a office yanata aikin duba wasu tulin takardun dake gabansa yaji knocking ƙofa, siririn tsaki yaja dan baya buƙatar kowa a irin wannan lokacin, izinin shigowa ya bada batare daya ɗago ba balle kallon wanene?.
Ƙamshin turarenta kawai ya bashi amsar wacece, harta zauna bayan gaisheshi da tayi bai ɗago ɗinba, a haka ya amsa mata.
“Mi kike buƙata?”
Ya faɗa yana cigaba da aikinsa batare da ya ɗago ɗinba.
Duk da taji haushi sai ta danne, abinda ta gani kuma ta jiyo game da kiran Bilkisu da akayi office ɗin B.G ta zayyane masa, karon farko da ya ɗago ƙyawawan idanunsa ya sauke akan rose, sai dai baice komaiba. Duk da tsawon kwanaki kenan tana buri da buƙatar irin wannan kallon daga garesa saboda kwallin da take sakawa na jawo hankalinsa kanta sai ta kasa jurewa, dan wani irin kwarjininsane ya kuma cika mata idanu da gangar jikinta, tai azamar janye idanun nata ƙirjinta na wata irin harbawa.
Har lokacin idon Jawaad na akanta, ya cigaba da ƙare mata kallon nazari har kusan mintuna biyu kafin ya janye ya maida ga aikinsa.
Ɓoyayyen numfashi rose ta sauke, daga can ƙasan ranta kuma wani daɗi na sake mamayeta, dan kuwa dai tasan ta gama da taurin kan Jay kamar yanda bokanta ya sanar mata, inhar suka haɗa ido wannan kwallin na idonta to lallai tagama da mallakarsa har abada, ba kuma zai sake kallon kowacce maceba bayan itaɗin.
Sakanni kusan ashirin bai tankaba, bai kuma sake kallonta ba. Takaici ya sake mamaye zuciyar rose, ta buɗe baki da nufin yin magana ya miƙe tsaye, bindigarsa da wayoyinsa dake saman tebir ya ɗauka ya tura cikin aljihun Blue jeans ɗinsa, tare da ɗaukar tab… ɗinsa a hannu. “muje” ya faɗa batare da ya kalleta ba.
Binsa tai da kallon mamaki, harya buɗe ƙofar office ɗin ya fice, dole itama ta tashi da hanzari ta bisa, a ranta tana ayyana cewar ‘Yau ƴan wulaƙancinne a kansa kenan?’.
Fitowar Jay daga office yay dai-dai da fitowar Bilkisu daga sashen office’s ɗin su B.G, kaɗan ya rage suyi karo, kasancewar hanyar data haɗa shataletalen office’s ɗin ɗayace kafin su ƙarasa su hau lifter da zata kaisu kasa.
Da sauri naja baya ƙirjinna na motsawa, cikin dakewar harshe da banyi zaton inada shi ba nace, “Kayi haƙuri dan ALLAH , bansan ka taho bane”.
Ƙyawawan fararen idanunsa ya zubamin kansa tsaye, kusan sakan biyar tamkar zai cinyeni dasu sannan ya janye batare da yace dani komaiba. ya raɓani zai wuce, hakan yasa na matsa baya na bashi hanya, tafiya ya fara tare da faɗin, “Biyoni”…………..✍
6
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻 10😂😂🤣😂🤣😆😆😆Kunsan miyasa nake dariyarnan? Akan yanda kuke ganin kamar bily tsoron Jay takeyi, dukfa halin da take shiga shiba fahimta yakeba, hasalima kallon miskila idan kun lura yake mata, akwai masu samun kansu a irin yanayin bily akan wani ko wata, sai daga baya suke fahimtar dalilin shigarsu irin wannan halin, itama bily lokaci zai warware mata komai har muma mu sami amsa, ina muku fatan alkairi aduk inda kuke, sosai Comments naku na sakani nishadi da sani typing kodama ban niyyaba.
I love you wujiga-wujiga irin trillions ɗinnan🤸🏼🤸🏼🤸🏼 😍😘😍😘😍😘🤗.
10
Page 6
Ko kaɗan ban fahimci dani yakeba, musamman dana waiga naga rose data fito daga office ɗinsa a bayanna, wani kallo naga ta watsamin mai kama da takaicin tabi bayansa. Numfashi na sauke mai nauyi na shafa ƙirjinna dai-dai saitin zuciyarta dake harbawa da sauri-sauri, duk da na fahimci kallon da rose tai mani sai hakan bai dameni ba, dan bata ita nakeba. Nima fita nai daga wajen, na fito ainahin harabar station ɗin domin nufar sashenmu.
“Ɗi! Ɗi! Ɗi!!” gimba ya danna mata horn kamar yanda Jay ya bashi umarni.
Duk da naji horn ɗin hakan baisa na fahimci da ni akeba, saboda idan akai dubi da sauran jami’ai irina daketa kaikawo a harabar wajen, kowa da hidimarsa.
“K! Wace irin daƙiƙiyace da baƙya fahimtane? A haka kike tunanin zama jami’ar tsaron al’umma!!?”
Maganar Rose a tsawace ta shiga dodon kunnena ina gab da shiga lungu da zai sadani da office ɗinmu. Da sauri na juyo, idona ya sauka akan rose dake huci da jifana da kallon takaici mai nunin tsana. Duk da naji zafin kalaman datai amfani dasu a gareni sai na danne saboda tana sama da ni, a ladabce nace, “Kiyi haƙuri maa! Bansan dani kike ba”.
Tsaki rose ta buga, tare da juyawa tabarni a wajen, wani jami’i dake tsaye kusa damu ya kalleni da tausayawa, dan shi dai yarinyar tunda tazo station ɗin ɗabi’unta birgesa sukeyi, ganin ban fahimci manufar rose ba sai yay min fassara akan nabi bayanta maybe kirana akeyi.
Godiya nai masa, kafin nabi bayanta cikin nutsuwata, sam ban iya sauri ko rikita kaina a tafiya ba koda kuwa a tsorace nake, a yanzunma duk da zuciyata na cike da tunani da baƙin cikin abinda tamin ban rikita kainaba a yayin bin bayanta, can na hangota jikin wata farar mota mai ƙyau da ɗaukar hankali, na cigaba da takawa a nutse gareta, ina isa jikin motar ita kuma tana buɗe gaba ta shige, hakan sai ya sakani a duhu, dan bansan kuma wajenwa zanje ba. Saitin inda take na ƙarasa, na ɗan risina yanda zata ganni ina faɗin, “Gani maa!”.
Kafin ta bani amsa ƙofar murfin baya naga ta buɗe, ita da drivern naga duk sun kalli bayansu, hakanne ya sakani kallon murfin ta waje nima, muryar drivern ta katse min tunani, “Ki shiga” ya faɗa yana nunamin bayan.
Duk da na shiga ruɗani, ga harbawar da ƙirjina keyi hakan bai hanani bin umarninsaba, koda wasa ban kalli waye a bayanba, na shiga kamar yanda aka umarceni, sai da na zauna ne wani mayen ƙamshi ya samu cikakkiyar damar surɗaɗawa a ƙofofin hancina, da sauri nai ƙoƙarin kallon gefena, gabana ya faɗi dan ganin wanda banyi zatoba, fuskarsa babu alamar wasa kamar yanda na gansa yanzu da mukai karo…..
“Sai kin gama kallona zaki rufe ƙofar ne?” muryarsa ta daki dodon kunnena babu zato, kaina na girgiza da sauri ina tattaro busashen yawun bakina da ƙyar na haɗiye, tare da jawo murfin motar na rufe. Nama rasa yanda zan fassara wannan al’amarin sam, gashi yanayin dana tsinci kaina ya hana mani damar yin nazarin daya dace da hakan.1
Ɓangaren Rose da Gimba kuwa mamakine fal a rayukansu, gimba shaidane akan bai taɓa ganin rose ta shiga bayan motaba kusa da boss, baima taɓa bata wannan damarba koda a fuskane, idan har kaga wani ya zauna a kusa da shi to lallai sai dai cikin su Aliyu ne, amma yau abin mamaki sai gashi shi da kansa yasa hannu ya buɗema yarinya ƙarama murfin mota, ya kuma bata lasisin zama a gefensa, ‘Anya kuwa?’ ya ayyana akan laɓɓansa yana mai satar kallonsu ta mirror.
Ita kanta rose a kume take da mamaki, ita duk zatonta wani abun zai saka yarinyar, bata kawo a ranta wannan abar zuwan jiya hukumarsu har tanada lasisin shiga cikinsu ba, balle harma ta shiga motar da boss yake ciki, a kusa da shima, shi da kansa ma ya bata lasisin zaman, abinda ita bai taɓa bata fuska a kaiba, ko zaman gaban motar da yakema sai ya gadama yake barintayi koda taso hakan kuwa, idan ko bata mantaba wannan itace shekara ta bakwai cif tare da shi tana aiki a ƙarƙashin group ɗinsa, ‘To mi hakan ke nufi?’ tayi tambayar a zuciyarta.
Shi kansa Jawaad mamakin kan nasa yake, amma da yake shi kogine babu mai gane gabansa balle bayansa sai bai nuna koda a fuskaba, hasalima tunda suka fice daga station ɗin kansa na duƙene yana danna tab.. Da alama wani abun yakeyi, sai dai ƙamshin turaren bilkisu duk ya addabi hancinsa.
Kowa da abinda yake kissimawa ransa har suka iso inda yake buƙata, gimba ya samu waje yay fakin, babu wanda yay yunƙurin buɗe motar a cikinsu balle ai tunanin fita, duk suna jiran umarni daga garesa. Shiko yay burus tamkar baiji motar ta tsayaba, sai faman danne-dannensa yake cigaba dayi a tab ɗin.
STORY CONTINUES BELOW

Sosai zaman ya gundureni, ba komai ya jawo hakanba sai matsuwar da zuciyata ta samu saboda kusancin dana samu da shi tare da lokaci mai tsayi da hakan bai taɓa faruwa ba, da gefen ido na saci kallonsa, sanye yake da wandon jeans kalar bulu, sai t-shirt fara, ta kwanta a jikinsa luf, dan yanda ƙirarsa ta bayyana ta cikakken mutum mai motsa jiki kawai ya isa baka amsa, dogon hannu gareta, amma ya tattareshi sama ya koma iyakar gwiwar hannun, sai agogon fata baƙi mai azabar ƙyau a tsintsiyar hannunsa da gashi ke kwance na alamar jin daɗi, na sauke idanuna bisa yatsansa dake cakalar tab ɗin, sanye yake da zoben azurfa mai tambarin stone babba tamkar diamond, da gani kasan zoben zaiyi tsada koda ba’a faɗa makaba……..
“Gimba ka tabbatar nanne wajen?”.
Maganarsa ta katse min dogon nazarin dana tafi na babu gaira babu dalili.
“Eh wlhy boss nanne, kuma wannan shine dai-dai lokacin da a kullum yake zuwa cin abincin safe shi da abokin nashi, a yanzu haka kuma inada tabbacin abokin nasa na cikin wajen, nanda mintuna ƙalilan zai iya fitowa”.
Uffan bai ceba, ya kuma cigaba da sabgarsa tamkar bashine yay tambayar aka bashi amsaba, a fuska dai baiyi kama da miskiliba, abinda kawai na fassara halayyar wannan mutumin shine Ɗan wulaƙanci ne lamba ɗaya kuwa, babu wanda ya sake magana tsahon wasu mintuna, bansan mi sauran sukeba, ni dai ina takure ne jikin ƙofa idona a waje ina kallon shiga da fitar mutanen dake fitowa a cikin wajen cin abincin (Restaurant), kasantuwar gilashin motar mai duhune nasan babu mai ganinmu, sai dai mu mu gansa, hakan ya sakani baje idanuna nake kallon komai daki-daki.
“Yauwa boss ga shinan ya fito” gimba ya faɗa da sauri yana nuna ƙofar shiga da fita na gidan abincin. Nidai kallon wajen nayi, shikam ko motsi baiyiba, bai kuma ɗago ya kalli abinda drivern ya nunaba, sai cewa da yay “Rose! Kibi wancan mutumin, duk yanda zakiyi kiyi magana ta shiga tsakaninku, magana kuma irin wadda zata iya zama mai kusanci”.
“Okey boss” ta amsa da sauri tana buɗe motar ta fice, sai lokacinne naga ya ɗago kansa ya kalli wajen, ba tare da ya sauke gilashin motarba, “Gimba ka tabbatar ka ɗaukesu a hoto mai motsi” yay maganar idonsa a kansu.
Saurin amsawa drivern yayi, tare da buɗe motar ya fice da sauri. Gabana ya faɗi dan ganin an barni daga ni sai shi a motar, sai dai nayi ƙoƙarin kamewa gudun karna zubda darajata da akasan ɗiya mace mai tarbiyya da ita, kallonsu na cigaba dayi kamar yanda shima na fahimci hankalinsa na kansu.
Muna kallo rose ta bigi saurayin da ya fito daga wajen cin abincin yana latsa waya, wayar hannunsa ta faɗi, kusan a tare suka duƙa domin ɗauka, bakin rose ɗin na motsawa, sai dai mu bamajin mi take faɗa, saurayinne yay murmushi suka miƙe tare bayan ita ta samu nasarar tattara wayarsa data tarwatse a hannunta, magana yake mata tana bashi amsa da murmushi saman fuskarta, sai dai shima bamajinsa, ta miƙa masa wayar tana faɗaɗa murmushin fuskarta tamkar yanda shima yake faɗaɗa nashi, bai amshi wayarba sundai cigaba da magana, sai kuma mukaga suna ƙyalƙyata dariya a tare, hanya ya nuna mata alamar suje, babu musu kuwa tabi umarninsa, tana gaba yana biye da ita har wajen wata Blue ɗin mota, shine ya buɗe mata ta shiga ta zauna sannan shima ya buɗe ya shiga sashen mai tuƙi, munata kallonsu har suka bar harabar restaurant ɗin……
Numfashi ya sauke a hankali yana ɗauke idanunsa da ga wajen, hakan ya sakani nima sauke nawa a ɓoye ina gyara zama cikin alamar takura, addu’ata da fatana bai wuce drivern ya dawo cikin motarba kona samu sauƙi, babban fatana kuma yace na koma gaba inda rose ta tashi, sai dai har tsahon mintuna biyar da barin su rose gidan abincin baiko motsaba balle ya kalleni, saima kansa da ya kwantar jikin sit ya lumshe idanu, “Ƙil!-ƙill!!” tab dinsa tai motsi alamar shigowar saƙo, bai motsaba, hakan yasa mamaki ya kamani……
“Ɗauki ki duba mi tace?” ya faɗa ba tare da ya motsaba. Gabana ya faɗi, dan nadai fahimci dani yake, kuma yana nufin tab.. Ɗin tasa zan ɗauka, ganin bai sake maganaba ne ya sakani kallonsa, a ɗarare nace, “Dani kake sir?”.
“A’a da kaina nake” ya faɗa a daƙile……
Kafinma ya rufe baki na kai hannu na ɗauki tab ɗin da ya ajiye a tsakkiyarmu, gabana sai wata irin faɗuwa yake tamkar zan haɗiye zuciyata a cikin bakina, madannin na danna ta kawo haske, wani haɗaɗɗen hotonsa ya bayyana, duk da son kallon hoton da naji ya tsargamin hakan baisa na tsayaba, saima mamakin ganin babu lock a jikin tab din ne ya kamani, naja hoton yay sama kawai, a take apps da yawa suka bayyana, baza ido na shigayi wajen neman messeges app, da ƙyar na tsaida hankalina na ganosa, ina buɗewa kuwa da sunan rose na fara cin karo, na buɗe saƙon nata, abinda ta turo bai shige kalmomi hamsin ba. “boss ya buƙaci nabisa, duk abinda ake ciki zakaji daga gareni”.
Cikin ɗan rawar baki nakaranto masa kamar yanda ta rubuto da harshen turanci, bai motsaba, bai kuma tanka mani ba, hakan yasani ajiye tab ɗin ina mai satar kallonsa, sai da ya ɓata lokaci kafin ya jehomin tambaya.
“Ya sunanki?”.
‘Ikon ALLAH’ na faɗa a raina kafin na bashi amsa da, “Bilkisu Adam makaho”.
Yanda ya buɗe idanu da sauri a kaina ba ƙaramin firgitani yay ba, mayun idanunsa masu saka tsigar jikina tashi ya dasamin, bansan miya bashi mamakiba, sunan nawane? Kokuwa na babana? Kokuwa makahon dana ambata a ƙarshe?. bansan amsarba, bani da ƙwarin gwiwar tambayarsa kuma. Tsahon minti ɗaya da sakanni yana kallona kafin ya janye idanunsa yana motsa baki tamkar mai son cewa wani abu,ni dai ta wutsiyar ido nake kallonsa shi da jin kansa.
Baice dani komaiba ya buɗe motar ya fita, ajiyar zuciya na sauke, dan fitar tasa sai naji kamar ya bani wani ƙaton filin cin karena babu babbaka ne…….
“Ko sai an fiddoki?”. Furucinsa ya daki kunnena, da azama na buɗe murfin na fice nima, gani nai ya wani zubomin idanu, bansan mi yake nazartaba daga gareni, sai jefani a ruɗanin zuciya dana takurar kaifin idanunsa da yayi, hakan yaja nai ƙasa da kaina dan bazan jura kallonba.
Takunsa kawai naji alamar ya matsa daga kusa dani, na saci kallonsa, sai naga yana ƙokarin ciro abu daga cikin but ɗin motar da ya buɗe, nufonin da yayne ya sani saurin ɗauke idona, ya miƙomin farar coat ta mata da tsayinta zai iya kaiwa gwiwa, ban musaba na amsa, sai dai ina buƙatar ƙarin bayani, “Saka” ya faɗa yana wuceni.
Sosai naketa mamaki, na warware rigar na saka a jikina saman Uniform ɗin dana sanya, sai ya zam rigar ta ɓoye bayyanar ni wacece, baƙin wandon kawai ake iya gani ta ƙasa, daga sama kuwa farin baby hijjab ɗinane ya bayyana, sai rigar ta fiddamin da wani tsari daban daya bayyanar da sirrintaccen kwarjinina da wasu ke iya ambata da ƙyawu. Bai cemin komaiba yay gaba na bisa a baya, dan zuwa yanzu kam na fara fahimtar hallayarsa da hanyoyin maganin zama da shi.
Sai da muka gabato shiga ƙofar wajen sannan ya tsaya muka daidaita tafiya, ƙasa-ƙasa na tsinkayi muryarsa yana magana.
“Ki kula sosai, sannan ki tabbatar da yanayinki ya canja tamkar munada dangantaka, idan kikamin shirmen da aikina ya buɗe lallai sai kinyi nadamar hakan”.
Sosai maganganunsa suka tsirgamin zuciya, dan kuwa ban gama fahimtar ma’anarsu ba balle manufarsu har muka ƙarasa shiga wajen.
Wajen yay bala’in haɗuwa, daga gani kasan masu abokan magana a aljihune kawai keda hurumin shigarsa, dan danan akai mana tarba ta mutuntawa, yanda ya ƙawata fuskarsa da murmushi ne ya ɗauren kai, hakan yasani nima aro irin basajar tasa na yafama kaina ina murmushin, ɗaya daga cikin yaran wajenne ya nuna mana wajen zama, bayan mun zauna yake tambayarmu komi muke buƙata.
Boss ya juyo yana kallona fuskarsa shinfiɗe da wani murmushin da ya kusa zautani, “My princess! Mi kike buƙata?”.
Wata masifar harbawa zuciyata tayi, kaɗan ya rage ban fallasamu ba, nai azamar haɗiye zuciyata dake niyyar fitowa ta baki saboda salon da yay amfani wajen kiran sunana da yanayin fitar sautin, da ƙyar na iya dai-daita kaina nai wani farin da bansan na iyaba da idanu, ina wani narke murya nace, “Duk abinda ka zaɓa mana yayi my king”.
Ɗauke idanunsa yay daga kaina, har zuwa yanzun fuskarsa ɗauke da murmushin da ya fidda lotsar dimples ɗinsa masu ɗaukar hankali, ya duba waiter ɗin yana bashi umarnin ya bashi list ɗin abinda suke da shi ya duba.
Da girmamawa ya amsa yana barin wajen, saurin yin ƙasa nai da idanuna ganin ya maido kallonsa gareni, murya ƙasa-ƙasa yace, “Ina sake gargaɗinki a karo na biyu”.
Kaina na jijjiga masa ina saurin gyara yanayina. Sallama wata matashiyar budurwa taimana saɓanin wanda yazo ɗazun, sanye take da Uniform ɗin wajen itama, cikin girmamawa ta ajiye goran ruwa biyu da kofuna dake saman tire ƙarami, kafin ta miƙa masa ɗan littafi dake a hannunta. Amsa yay yana dubawa, tare da yin alama da pen ɗin data haɗa masa da shi akan duk abinda muke buƙata, baifi sakan sha biyarba ya miƙomin littafin yana fadin, “Duba yayi?”.
Amsa nayi ina kuma matse nutsuwata, nai nazarin duk abinda ya zaɓadin kafin na ɗago ina murmushi, cikin salon da bansan nayiba na ɗaga masa gira ɗaya da juya ƙwayar idona kaɗan alamar yayi.
Idanunsa ya lumshe tare da buɗewa a lokaci ɗaya yana sakin wani lallausan murmushi da yafi na ɗazu.
‘Innalillahi….’ Na iya ambata ina saurin maida fitsarindake neman kufcemin.
Tana barin wajen ya kalleni da sauri, murya ya rage ƙasa sosai, wanda yake nesa damu zai ɗauka soyayya mukeyi, maganar da ya faɗamince ta sakani jinjina masa kai da sauri, ina kuma murmushi, badan tanada alaƙa da murmushin nawa bane, sai dan kawai barin murmushin akan fuskar tawa ya zama tilas saboda kiyaye gargaɗinsa25
ALLAH ka gafarta iyayenmu😭🙏🏻18Barka da juma’a.
5
Page 7
……………..Mintuna kaɗan budurwar ta dawo da tire babba a hannu, wanda aka jero abubuwan da muka buƙata a kansa.
Tana ƙoƙarin ajiyewane Jay ya miƙa hannu zai ɗauki ruwan da aka fara kawo masu, a salon da babu wanda ya isa fahimtasa har bily bata kulaba ya tanƙwaɓi tiren ya suɓuce, jikake “Tarats!!! Tass! Tatass!!” kwanikan da suka zube na fashewa, abinda ke cikinsu gaba ɗaya sun koma jikinsu sun wankesu, duk jikinsu ya ɓaci daga shi har bily da bata san mafari ba, a take duk hankalin mutanen dake kusa dasu ya dawo kansu.
Na ɓata fuska saboda harga ALLAH banji daɗin yanda jikina ya ɓaciba. Cikin langwaɓe kai na kallesa kamar zanyi kuka.
Da ƙyar Jay yay ƙoƙarin haɗiye dariyar dake neman kufce masa saboda yanda Bily tayi fuska kamar zata fasa ihu, ga mai da yay tsalle harkan fuskarta sai naso yake.
A fusace na miƙe saboda ganinma dariya yake neman yimin, dan da gaske haushi naji har raina, maimakon ya mata faɗa amma kuma tsabar wulaƙanci yake neman yimin dariya a cikin mutane, bamma san sanda na fara zazzaga mata masifa akan tayi hakanne da gangan ba, yanda ta rikice ba ƙaramin tausayi ta baniba, amma kuma uwar mi take kallo da zata wankemu haka?, shima jinake kamar na juya na talle masa ƙeya yasin.
Jawaad ya tsaya kawai yana kallon bakin Bily dake masifa, babu shiri murmushi ya suɓuce masa, ganin tamkar abin nata da gaskene shima sai ya miƙe, cikin son maidota hayyacinta ya nema riƙo hannunta, amma sam taƙi yarda, dan danan wasu ma’aikatan nasu sukazo, da alama suɗin manyane, haƙuri suketa bamu amma naƙi saurarensu, daga ƙarshema nai ficewata, shikuma yay azamar biyoni yana faɗin, “princess! Princess! Please ki tsaya mana”.
Ƙo juyowama banyiba na nufi motarmu na buɗe zan shige, saurin riƙe murfin yayi yasha gabana alamar hanani shiga motar, ya wani marairaice yana lallashina, wlhy da kunsan yanda zuciyata ke harbawa sanda muke a wannan yanayin da kun bala’in tausayamin, a haka budurwar da wasu ma’aikatan wajen suka iso suka taddamu, haƙurin suka cigaba da bamu, sai da muka ɗan garasu da kalamun cewar bazamu sake zuwa wajenba tunda basusan kimar Customers ba kafin na nuna na haƙura da ƙyar, dan zuwa yanzu na dawo hankalina akan shirinmu.
Sun buƙaci mu koma wajen a bamu wani abincin amma na tubure akan bazan koma ba, sai dai a haɗo mana takeaway, ba musu suka amince da bukatata, ganin sunbar wajen ne ya sani sauke ajiyar zuciya ina matsawa baya saboda kusancin da muka samu ni da shi neman karya ƙwarin gwiwa da nake bama kaina ya keyi, gashi yay masifar tsareni da idanunsa.
Shima matsawa yayi, ya nuna min mota alamar na shiga yana zubamin harara, “saurin shigewar nayi kuwa, ya rufemin murfin ya zagaya ɗayan ɓangaren, da sauri gimba dake bayanmu tsaye yana kallon dramar tamu ya buɗe masa, hanasa rufewa yayi, saima ya zauna ƙafafunsa duka a waje. A haka budurwar ta dawo ɗauke da takeaway ɗin da muka buƙata, gimba ya amsa ledojin, shi kuma ya miƙa mata atm card ɗinsa tare da wata takarda yana magana ƙasa-ƙasa, “Saboda baƙwason ya tona muku asiri kuka kasheshi?”.
A firgice budurwar ta kalli Jay, sai kuma ta hau waige-waige jikinta sai tsuma yakeyi.
Ya sake faɗin, “Ki daina ɓatama kanki lokaci, akwai address ɗin inda zaki sameta (ya nuna bily) a jikin takardar nan ranar lahadi, yarage naki kizo ko kiƙi zuwa, sauran bayani mahaifinki zanyimawa”.
Sake rikicewa tayi, jikinta sai wata masifar tsuma yakeyi. Yanda taketa kallonsa a firgicene ya sakani tabbatar da maganar bamai daɗi ya faɗa mataba, tabar wajen da sassarfa, yayinda gimba ya take mata baya domin amso atm ɗin idan sun cire kuɗinsu.
Wato dai duk yanda nake tunanin aikin nan namu yafi ƙarfin tunanina, irin wannan makirci haka tamkar wani shirin film.
Gimba bai wani jimaba ya fito da ɗan hanzarinsa, motar shiru tamkar babu mutum mai numfashi, nidai takurace ta hanani yin ƙwaƙwƙwaran motsi, danma ALLAH ya soni yanzu a gaba nake ba kamar yanda muka zoba, shiko bansan mi yakeyiba, dan nakasa kallonsa koda ta mirror ne, abinda ya faru a wajen da wanda nayi keta dawomin a rai, sai naga kamar na zaƙe da yawa, ko a gidan uwarwama na samo ƙwarin gwiwar zuba masifar irin haka?’.
Sai da gimba ya tada mota sannan yace, “Boss zamu koma station ne?”.
Shiru bai bashi amsaba har muka fice daga gate ɗin wajen muka hau titi, ni nama ɗauka ko barci yakeyi, sai jinai ya bashi amsa da,
“A.Y….”
Ban fahimci ma’anar maganarba, amma shi gimban naga kamar ya gane mi yace. Wayata daketa vibration tun ɗazun na kalla, yah Qaseem ne yanzuma, wannan shine kira na kusan bakwai kenan, tun muna cikin wajen cin abinci kiransa keta shigowa, sai dai bansan miyasa nakasa ɗagawa ba, a hankali na sauke ajiyar zuciya jin wayar ta yanke, kasheta nai baki ɗaya ma, dan bansan dalilin kiranba, idan kuma na ɗaga bansan mizance masaba, bankuma saniba ko ɗagawar zai iya zama laifi a wajen wanda muke tare. Isowarmu wani gida mai ƙyau da tsarine ya yanke tunanina, tunda aka buɗe mana gate muka shigo naketa bama idona abinci nidai, gimba ya tsaida mota ya buɗe ya fita, ni dai banyi yunƙurin fitarba harshi aka buɗe masa ya fice, akan idona yabar wajen ya nufi wata ƙofa mai alamar shiga ainahin cikin gidan, na sauke ajiyar zuciya kaɗan ina lumshe ido, fatana yazam shikenan yace a maidani station………
Kallon gimba dake bani umarnin shiga nai da sauri, yay murmushi yana sake maimaitamin, “Ki shiga inji boss”.
Jinai tamkar na fasa ihu, amma bani da ikon cewa ba hakaba, dole na fito ina sake bin harabar gidan da kallo, gimba ne yaymin jagora har ciki, ‘Masha ALLAH’ na faɗa akan laɓɓana saboda haɗuwar da falon yayi, babu kowa a ciki sai ƙamshi mai daɗi dake tashi a cikinsa….
Gimba yace, “Ki shiga nan saiki gyara jikinki”.
Murmushi naɗan masa ina jinjina kaina, na nufi ƙofar raina cike da tsoro da mamaki, sai faman tambayar kaina nake ko ina matar gidan? Dan naji gidan tsit. ‘Kika sani ko tare suka shige ciki?’ zuciyata ta ayyana min haka, bakina naɗan taɓe, na tura ƙofar na shiga da sallama. Ɗakine babba, akwai komai na amfani kuma a ciki, sai dana gama ƙare masa kallo kafin na nufi ƙofar da nake ƙyautata zaton bayine, bayan na rufe ƙofar sai kuma nai tsaye ina ƙarema kaina kallo ta cikin madubin dake toilet ɗin, Toni ta inama zan farane? Ni bawasu kayane dani ba, gashi kayana sun ɓaci sosai, na zare rigar saman da ya bani, wadda kasancewarta fara ta ɓaci sosai, hakama wandona, amma da yake baƙine shi ba gani akeba, sai ƙamshin miya da yake da mai dakemin naso a jikine zaisa ka gane ya ɓaci shima sosai, shawarar cirewa na wanke nayi, dan haka na cireshi a ɗarare.
Ban fahimci kuskurena na jiƙa wandonba sai dana gama wankesa nanfa tunanin inda zanje na shanya, da kuma ta yanda zanma fita shanyawar tunda bawasu kayanne daniba yazomin. jinai hawaye sun cika idona, ‘Ni balki naga takaina’ na faɗa a hankali ina haɗiye kukan dake neman zuwamin. A bayin na shanya wandon na fito ɗaure da sabon tawul dana gani, na zauna a bakin gadon na rabga tagumi ina addu’ar neman mafita.
Nai firgigit jin an turo ƙofar kamar a fusace, fuskarta a haɗe ta shigo hannunta ɗauke da leda yellow mai tambarin M&N, cike da kallon tsana ta miƙamin ledar, amsa nai nidai cikin girmamawa amma ina mamakin yanda takemin a ƙasan raina. Juyawa tai zata fice na bita da kallo, sai da ta buɗe ƙofar sannan tace, “Ana jiranki” kawai ta fice abinta.
Numfashi na sauke a hankali, na buɗe ledar na fidda kayan ciki, wandone da riga duk baƙaƙe, sai baby hijjab fari irin waɗanda nake sakawa, tashi nai na saka kayan, sunmin bala’in ƙyau, sai dai inajin kunyar fita a haka sosai, dan sun wani lafe a jikina dukda dai rigar bata matseniba, bani da zaɓin daya wuce daurewa na fita a hakan kawai, danma baby hijjab ɗin ya rufemin ƙirji, na maida kayan dana cire a jikina cikin ledar harda wandon dana jiƙa ɗin, kaina a ƙasa na fito daga ɗakin, zuciiyata sai harbawa take da sauri-sauri.
Wani iri naji a raina ganin kusan su biyar ne a falon, sai na kumajina a matuƙar takure musamman saboda kayan dake jikina, ƙarasawa nai cike da aro jarumtar dole ganin su hankalinsuma ba’a kaina yakeba, sallama nai duk suka amsa mani, na gaishesu da girmamawa nanma suka amsa, na kula kamar kallon mamaki sukemin irin kamar basuyi tunanina ganina a wajenba, hakan sai ya sakani jin wani iri, na saci kallon dodon nawa, dan tunda na fito baiko ɗaga kai ya kalli sashen da nakeba, yana zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya tamkar wani basarake, idonsa na bisa takardun dake hannunsa, shima ya canja kayansa zuwa farin wando da baƙar t-shirt mai gajeren hannu, rigar ta kwanta masa a jiki, hakan yasa ta fidda ainahinsa na ƙaƙƙarfan mutum…….
“Bismillah zauna mana”
Oga Hafiz ya katse min satar kallon boss dana shagala yi, kaina na jinjina na zauna a inda ya nunamin ɗin a ɗarare.6
Tun fitowar Bilkisu a idanun Jawaad ne, duk kuma abinda take yana kallonta ta gefen ido, amma babu wanda zai iya fahinta, idan akai dubi da yanda ya maida dukkan hankalinsa ga takardar hannunsa, ɗago idanunsa yay yana kallon Aliyu dake danna lap-top, yace, “Aliy ya buɗe ne?”.
Girgiza kai Aliyun yayi yana guntun tsaki, ya juya masa fuskar lap-top ɗin da faɗin, “Ni banama zaton yana amfani da accaunt ɗinnan gaskiya, boss wai mizai hana mu aika wani cikinsu kawai, sai naga haka kamar zaifi komai sauƙi da muzauna a bayan fage muna wahal da kanmu, tunda bamu da tabbacin yarinyar zata bamu haɗun kai”.
Kafin Jawaad ya bashi amsa Rose dake gefensa tanata wani cika da batsewa tai caraf ta amshe zancen, “Boss dabaran Aliyu yayi sosai, kaga sai a aika yarinyarnan kawai cikinsun”.
Wani mugun kallo da ya bama kowa mamaki a wajen Jawaad ya watsama Rose, sai kuma ya ɗauke kai batare da yace mata komaiba.
Duk zuba masa ido sukai suji ko zai bama rose amsar maganarta, ni dai kaina a ƙasa ban ɗagoba inata wasa da yatsun hannuna, na ɗan saci kallon nasa nima sai naga ya cigaba da duba takardar hannun nasa ma tamkar baisan mi akeba. Tsawon mintuna bakwai muna a haka kafin muga ya ajiye takardan hannun nasa ya miƙe, wata ƙofa ya nufa, duk suka sake binsa da kallo harni da nakeyi a munafunce. yana shigewa duk suka maido dubansu gareni, inaga ganin yanda na takura kaina ne da ganin kamar bare a cikinsune ya saka oga Jabeer sakarmin murmushi, cikin tsokana yace, “Anya kuwa wannan ƙanwar tamu ba matsoraciya bace?”.
Karon farko da nai murmushi, na ɗan kallesa na ɗauke idanuna da faɗin, “A’a Sir”.
Dariya duk sukayi, amma banda Rose da ta ɗauke kai tana taɓe baki.
Oga Aliyu dake danna lap-top har yanzu yace, “To idan ba matsoraciya bace ki saki jikinki damu, munan duk yayunkine ba surukaiba, minene sunanki?”.
Naɗan kalli sashen da yake fuskata ɗauke da murmushi nace, “Bilkisu Adam makah..o”.
Na ƙare maganar a hankali saboda yay dai-dai da fitowarsa daga ɗakin daya shiga, ya ɗoro baƙan jacket saman kayansa, ido muka haɗa, nai saurin janyewa nawa ina haɗiye murmushin kan fuskata saboda maganar da su Hafiz sukeyi na cewar “Ashe mai babban sunace, duk mai wannan sunan kuwa jarumace”.
Duk dariya sukayi, amma banda rose da shi da muka sake haɗa ido a bazata, saurin janye idanuna nayi zuciyata na wata irin harbawa, hanyar ƙofa ya nufa yana faɗin, “Kumuje” Yana ƙoƙarin gyara baƙar jacket ɗin daya ɗoro saman rigarsa.
Rose ce farkon miƙewa ta fice, niko ban motsaba sai da suka gama fita sannan na zama ƙarshe.
Jikin motar da mukazo na hango rose tsaye, ta wani haɗe fuska, shi kuma yana daga gefe waya a kunnensa, hannunsa ɗaya a aljihun farin wandonsa, ido muka haɗa nai saurin janye nawa nidai, dan sam banyi zaton sashen da nake yake kalloba ma, a raina ina mamakin yanda duk sanda zan saci kallonsa nakan kama idanunsa a kaina shima, sai naji haushi na balla masa harara ta gefen ido duk da baisan inaiba.
Duk tsaye mukai muna jiran ya kammala, kusan mintuna uku kafin ya sauke wayar ya tako wajen motar da rose ke tsaye, muma duk muna kusa, ya kalli Hafiz yana faɗin, “Yanzu yaya za’ai kenan?”.
Hafiz yace, “Boss inaga ku koma Office, ni da rose da Aliyu zamuje can anguwar mu sake bincikawa, maybe mu samu wani a gidan yanzun”.
“Okey hakan yayi” yay maganar yana yunƙurin buɗe motar, dole Rose data cika fam da haushi ta matsa, har zai shiga ta katse hanzarinsa da faɗin, “Boss nikam da sun wuce, sai na biku, zan ɗauka wayata dana manta a office, zan bisu a baya tunda nasan anguwar”.
Ɗagowa yay yana kallonta fuskarsa babu walwala, ya janye idanunsa a kanta batare da ya bata amsaba ya maido kaina dan duk kallonsu mukeyi, “Mimaa! Shiga mota muje, ke kuma ki bisu kubiya ta station ɗin tare sai ku ɗauka wayan ku wuce”.
Duk da naga idanunsa a kaina suke sai ban fahimci dani yakeba saboda sunan daya ambata, gashi har yayi shigewarsa motar.
Jabeer dake kusa dani yay murmushi, “Dake yake fa, kije kutafi”.
Kaina na jinjina masa kawai ina murmushin ƙarfin hali da sake juya sunan a raina, ‘Mimaa;? To wannan sunan kuma daga ina haka?’. Na ƙarasa zan shiga gaba, sai dai rose taƙi matsawa a wajen, na kalleta nace, “Zan shiga ciki maa”.
Shiru bata motsaba, bakuma ta tanka minba…………..✍
11
Rose yau kinga idi wajen bily team, dama hauhinmu sukeji😥🤐.
90
Asha weekend lafiya😜😑😉🤗🤗.
14
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻17Page 8
………….Jawaad dake kallonsu daga ciki yay murmushi kawai yana girgiza kai, dan ya fahimci wani abu daga Rose ɗin. hannu ya miƙa ya buɗe murfin ɗayan gefensa, Hafiz dake ta wajen tsaye yace, “Kinga mai sunan Momcy zo tanan”.
Amsa masa nai da “to” na nufi can duk da a raina banso hakanba dai, sai dai haka kawai naji inason bama shegiyar rose ɗinnan haushi yanzun, dan na kula sam bata ƙaunata dai, su mutanen duniya dasun ganka shiru-shiru saisu dinga ɗaukarka sakarai ko bakasan abinda kakeba, indai nice kuwa tasa kanta a ramin damisa wlhy. Ina shiga Hafiz ya rufe murfin, gimba yay ma mota key, bansan yanda aka ƙare da rose ba mukabar gidan bayan oga Jabeer ya shiga gaba bisa umarnin Boss da yay masa magana.
Har muka isa station oga Jabeer da gimba na hira, amma ni dashi kamar mun haɗiyi kwaɗo. Yanda na takurama babu abinda nake buƙata kamar mu iso na sauka nidai. koda gimba ya tsaida motar ban fitaba saida duk suka fita, baiko kalli kowaba a cikinmu yay gaba abinsa zuwa hanyar office ɗinsa, Jabeer ne kawai ya kalleni fuskarsa ɗauke da murmushi yace, “To mai sunan mom sannu da ƙoƙari, ki ƙara ƙaimi da jarumta dan aiki da boss sai jarumi na gaske”.
Duk da ban fahimci zancensaba nai murmushi ina ɗaga masa kai, sannan nace, “ngd” a ƙasan raina kuwa ina tunanin wai sunan wa? gareni suketa wani boyen suna.
Murmushi yay shima, ya nunamin cikin motar yana faɗin, “Karki damu babu godiya a tsakaninmu, ki tattara masa tarkacensa kibisa office dasu, ai kinsan office ɗin ko?”.
Tamkar na fasa ihu haka naji, amma sai na daure nace, “Ban taɓa shigaba dai, amma na sani”. Yace, “To Alhmdllh saiki kaimasa ni na wuce office ”. Kaina na jinjina masa batare da nace komaiba, shima yay murmushi kawai ya wuce abinsa.
Duƙawa nai na tattaro wayoyinsa da tab da wasu takardu daya bari sai bindiga da keys da bansan kona miyeba, sai ƙamshi suke tamkar suma turaren ake fesa musu, ledar takeaway ɗinmu gimba ya bani, ban musaba na amsa, dan duk zatona duk shi zan kaimawa, sallama nai masa na nufi hanyar da zata kaini office ɗin da kaya riƙi-riƙi saikace wata ƴar gudun hijira, danma na barma gimba ledata akan idan na fito zan karɓa dukda yacemin gida zaije. Sai da na hau lifter domin office ɗinsa na hawa na uku ne, sai saƙawa da kwancewa nake ina zancen zuci, na iso shataletalen da ya raba hanyoyi uku na offices ɗinsu, ɗaya nasan hanyar dazata sadaka da offices ɗin su B.G ne, wanda suke a hawa na ƙarshe, sai kuma ɗayar hanyar bansan offices ɗin suwayeba a wajen, sai ɗayar hanyar da naga ya fito ɗazun, nan na nufa kai tsaye, dogon corridor ne da ƙofofi jere kusan goma, hakan yasa na fara bi ina karanta rubutun saman gudun kuskure, sai da naje na bakwai sannan naga an rubuta Captain Jawaad A yusif, inada tabbacin nanne, dan tunda aka gayamin cikakken sunansa bantaɓa mantawaba koda a second ɗaya ne kuwa. Sai da na daidaita kaina da sake ƙarfafa zuciyata da ke neman faso ƙirjina ta fito sannan nai knocking har sau uku, amma banji an amsa maniba, nai jim kusan na minti ɗaya kafin na ƙara yin knocking ɗin kamar mai tsoron a jita, nanma shiru, nakai hannu zan sake aka amsa mani. Ajiyar zuciya na sauke a hankali kafin na tura ƙofar da sallama na shiga, office ne da ya amsa sunansa office, dan kuwa yayi ƙyau, babu wasu tarkace komai kuma tsaf, ga mayen turarensa ya kama office ɗin haɗi da freshener mai daɗin ƙamshi, sai suka bada ƙamshi na musamman, kallo ɗaya naima inda yake zaune a kujerarsa ta office na duƙar da kaina, shima kuma bai kalleniba, baikuma cemin komaiba, yanata rubuce-rubucensa hankali kwance tamkarma baisan wani ya shigoba. Jinai tsayuwar ta isheni, dan haka na gyara kaɗan ina yamutse fuska, batare dana ɗago na kallesa ba nace, “Sir gashi inji oga Jabeer”.
Jay da tun ɗazu ya daina rubutun ya kwantar da bayansa jikin kujerar kawai yana kallonta da jinjina shegen miskilancinta ya lumshe idanunsa ya buɗe a lokaci ɗaya, sai faman goga ƙasan biron hannunsa yake a jikin laɓɓansa, ko motsi baiyiba ballanta ya amsa mata. Tsabar miskilancin yarinyarne kawai ke bashi mamaki, ya ɗan taɓe baki tare da maida kallonsa ga Computer ɗin dake kan desk ɗinsa, bironsa ya ajiye yana lafe jikin kujerar ya fara sarrafa keyboard ɗin Computer ɗin.
Ƙaran danna keyboard da najine ya sakani ɗago idanuna nai masa kallon second 2 na janye, karan farko a rayuwata dana sake jinjina wulaƙancin mutuminnan, ‘kenan bazai tanka mani ba komi yake nufi?’ na ambata a zuciyata ina maijin takaicinsa. Satar kallonsa na sake yi sai muka haɗa idanu, da sauri na janye nawa ina tura baki gaba batare dana san nayima hakanba.
Sautin fitar ƙaramin tsakinsa ya sakani saurin sake kallonsa, yako dallamin harara alamun har yanzu idonsa a kaina suke, “Kin zama bodyguard ɗinane shin?” yay maganar a hankali kamar baison yi.
Kaina na girgiza masa, duk da bani da tabbacin kallon nawa yake har yanzu, takawa nai zuwa gaban tebir ɗin na ajiye kayan harda ledar abincin, ban kallesaba bai kuma tankaminba na juya zan fita.
“Zonan”
Na tsinkayi umarninsa. Juyowa nai kaina a ƙasa batare dana kallesa ba, “Zauna” ya sake faɗa a daƙile. ‘Kai nikam na shiga uku da wannan mutumin’ na ambata a zuciyata ina mai jina a matuƙar takure, zuciyata sai faman harbawa take da sauri-sauri. Shiru office ɗin ya sake ɗauka na kusan minti ɗaya, sai ƙarar keyboard da yake dannawa kawai kake ji. Knocking ƙofa akai ya bada izinin shigowa, matashin sauriyi ma’aikacinmune ɗauke da takardu a hannu, kallo ɗaya nai masa na ɗauke idona, duk da shi na lura sai kallon mamakin ganina a nan ɗin ya keyi, har takai boss ya daka masa tsawa.
“Kallon mutane aka turoka yine!?”.
Cikin sauri da ladab yace, “Sorry sir”.
Banji ya tanka masaba, danni kaina a duƙe banma ɗagoba, sai sautin siririn tsakinsa naji kawai, shidai saurayin sai faman nanata kalmar haƙuri ya keyi kusan sau huɗu kafin ya fara masa bayani akan takardun hannunsa, banji ya tankaba, hakan yasani satar kallonsu, gani nai ya miƙa hannu ya amsa takardun yana dubawa, kafin ya ɗago ya kallesa da sake miƙa masa ta kardun yana faɗin, ”Ka kaisu office ɗin Lieut..; Richard, kace ya duba, zuwa anjima sai yazo dasu ina nemansa”. “Okey sir” ya faɗa cike da girmamawa kafin ya amsa ya fita ko sau ɗaya bai sake gigin kallon sashen da nakeba.
Ɓoyayyen numfashi na sauke bayan ficewarsa, saima naji yaɗan bani tausayi……..+
STORY CONTINUES BELOW

“Bani malt.. A cikin fridge”. maganarsa ta dawo dani hayyacina, miƙewa nai ina ɗan dube-dube a office ɗin danson gano fridge ɗin, shi kuma yaja ledan abincin ya buɗe, ganin fridge ɗin da nayi bayansa kaɗan ya sakani nufar wajen, kasancewar ƙaramine madaidaici yasa saida na sunkuya, malt ɗin ne kawai a ciki da coc… nidai na ɗakko abinda ya sakani tare da kofin dana gani a saman fridge ɗin kusan guda shidda saƙale jikin wani ƙarfe mai ƙyau, gabansa naje na ajiye ina haɗiye yawu da ƙyar, dai-dai yana buɗe takeaway ɗin gasashen naman kaza daketa ƙamshi, ina ajewa nabar wajen na koma inda na fara zama a ɗaya daga kujeru biyun dake gaban tebir ɗinsa, ganinai kawai ya turo naman gabana, na ɗago na kallesa muka haɗa ido, kuma tamke fuska yay ya nunamin naman. Tamkar zan fasa kuka nace, “Nifa na ƙoshi, azumima nakeyi”. Banza yaymin tamkar baima jiba, ya ɗauki gwangwanin malt ɗinsa ya ɓalle hancin ya kai baki, kafin ya ajiye ya maida hannunsa kan keyboard ɗin Computer ya cigaba da daƙilarsu. Mun kwashi kusan minti uku a haka, bai tankaniba, nikuma banci namanba dukda ƙamshinsa ya addabeni.
kamar daga sama naji yace, “Karki bari na sake miki magana, kiyi ki fitarmin a office”.
Batare dana shiryaba bakina ya suɓuce wajen faɗin, “Toni nacefa azumi nake, sokake na karya azumina ne?”.
Tunda ta fara magana ya dakata daga daƙilar Computer’n ya zubama laɓɓanta idanu da kumatunta da take ɗan kumburawa, sai da takai aya sannan ya janye ya maida ga abinda ya keyi batare da ya nuna yamaji mita faɗaba.
A matuƙar takure nake gaba ɗaya bugun zuciyata da numfashina sun dawo a maƙoshina, kaɗan nake jira na amayota kowama ya huta, yaƙi kulani, sannan yaƙi cemin na tafi, ganinfa yama manta dani saina miƙe abina na nufi hanyar ƙofa, bai tanka maniba har saida na kama ƙofar zan buɗe sannan yace, “An taɓa karyaki?”. Cak na tsaya, ni ban fitaba, ni ban komaba, bamma iya sakin mariƙin ƙofarba saboda yanda furucinsa ya daki ƙirjina, sai da na shaƙi iska na fesar sannan na juyo a hankali ina kallonsa, kauda kaina nayi saboda ganin shima niɗin yake kallo, ya wani haɗe fuska tamkar hadarin tsakkiyar ogusta.
“Idan kika bari na sake miki magana ki kuka da kanki”.
A yanda yay maganar da tsananin kaushi sai tsoro ya sake tsirgamin, dama dai ƙarfin hali nake kawai, dole na dawo na zauna ina sake haɗe fuska dan nikam gaskiya an sakama rayuwata ido, komawa nai kujerar dana tashi na zauna. Ina zama shikuma yana miƙewa ɗauke da wasu takardu ya fice daga office ɗin abinsa batare da yace dani komaiba. Na sauke nannauyan numfashi ina kallon naman, bani da zaɓinda ya wuce nacin kawai kodan ya barni na tafi, na ɗauki cinya nakai bakina ina ambatar bismilla, ɗanɗanon naman da laushinsa ya sakani lumshe idanuna, ko ba’a faɗaba dama namannan zaiyi ɗankaren daɗi ai, ban ankaraba na laƙume cinyar na sake ɗaukar wata tsoka irin ta haƙarƙarinan, (Damafa inaso shegen gulma ne. Lol) ina gab da cinyeta aka turo ƙofar da azabar ƙarfi aka shigo, a tsananin razane da ganin wanda ya shigo ɗinne ya sakani miƙewa babu shiri ina kallonsa. Shima idanunsa ya zubamin tamkar zai cinyeni da su.
“Ubanmi kikeyi nan Bilkisu?!!”
Idanuna na lumshe saboda tsawar tashi ta rasha kunnuwana, na buɗe a hankali kansa, cike da dakiya na zubasu a kansa nace, “Yah Qaseem miya faru?”.
Wata malalaciyar harara ya zubamin kamar zai juye idanunsa ƙasa, ya fara takowa inda nake, taku baifi ukuba tsakaninmu ya rage aka buɗe ƙofar office ɗin aka shigo. Ni da shi duk kallon ƙofar mukai, sai dai shi a take ya janye nasa idon yana jan uban tsaki. Nikam numfashi na sauke a ɓoye dan koba komai na samu kuɓuta daga wannan yunƙurin na yah Qaseem da bansan mi zuciyarsa ke kissima masa yaminba.
Jay da ya shigo kuwa kallo ɗaya yay musu ya ɗauke kansa ya taka zuwa ga kujerarsa ya zauna.
A mamakina sai naga yama cigaba da daƙilar Keyboard ɗin Computer ɗin hankalinsa kwance kamar baisan damuba. Shima yah Qaseem ɗin bai tanka masaba ya kalleni yace, “Wuce muje”.
Jawaad daketa danne-dannensa batare daya ɗagoba yace, “Kai ka kawotane?”. Dogon tsaki yah Qaseem yaja yana damƙar hannuna da faɗin, “Miye na azarɓaɓi ƙaramin tsagera, ai zan dawo kanka idan na gama da ita”. Ya ƙare maganar da fisgar hannuna muka nufi ƙofa. Jinake tamkar na kurma ihu, ‘Nikuma wannan wace fitinace na shigo ciki haka?’……….
“Wlhy kika fita daga office ɗinan saina saɓa miki kamanninki!”
Muka tsinkayo kakkausan furucin boss yayinda yah Qaseem ya murɗa ƙofar zamu fice. Bani kaɗaiba hatta da yah Qaseem ɗinma tsayawa daga yunƙurin fitar yay, ya juya yana kallonsa, nidai kaina a ƙasa na gaza kallon kowa a cikinsu, addu’ar ALLAH ya kuɓtar dani daga tsakaninsu kawai nakeyi a raina, dan bansan wazan bijiremawaba? Wakuma zanma biyayya ba?. Yarfar da hannuna yah Qaseem yay ya nufesa, zafin da najine ya sakani durƙushewa a wajen ina sakin siririyar ƙarar azaba.
Qaseem daya ƙarisa gaban Jawaad ya bugi tebir ɗin gabansa har wasu abubuwan na faɗuwa, “A matsayinka na ubanwa zaka saɓa mata kamannin?”. Ko motsi Jawaad baiyiba balle ya kalli Qaseem, aikin gabansa kawai ya cigaba dayi hankalinsa kwance. A kausashe Qaseem ya sake maimaita tambayar tamkar zai mari Jay ɗin. Ɗago idanu Jawaad yay ya zubasu akan Qaseem, cike da gadara yace, “Qaseem fitarmin daga office!!”.
“Anƙi a fita, kayi duk abinda kaga zaka iyayi” Qaseem ya maida masa amsa a zafafe shima.
Jawaad bai sake magana ba, ya miƙe ya nufi Bilkisu dake durƙushe tana hawaye saboda hannunta dake zugi.
Tsayuwar mutum kawai naji a kaina, cikin bada umarni yace, “Tashi”. Miƙewa nai babu musu, na saci kallonsa, ganin shima kallon nawa yakene yasa na janye nawa ina goge fuska, kafin ya sake wata magana yah Qaseem yazo ya shiga tsakkiyarmu, ”Wuce muje” ya faɗa yana nunamin hanya, haushin murɗamin hannu da yayne yasa naƙi motsawa. Ganin naƙi motsawarne ya sake hasalashi ya ɗaga hannu zai saukemin mari.
Rufe idona nai da sauri naja baya saboda masifar firgita da nai da ihun da yaymin akai, na ƙanƙame jikina ganin ya ɗaga hannu zai makeni, shirun da naji yasani ɗago kaina kaɗan naga miya hanashi dukan nawa da yay niyya.. Saurin waro idanu nai waje ganin boss riƙe da hannun Yah Qaseem da ya ƙara kumbura sai hura dogon hancinsa yake.
“kika fita saina karyaki a office ɗinan Miemaa” boss yay magana a dake kamar yanda na fahimci halittarsace yin magana kai tsaye koda a gaban wa yake. Saurin duƙar da kaina nai saboda tsatstsareni da yay da idanu, nai baya daga kusa dasu cike da tashin hankalin sakani tsakkiya da sukai.
yah Qaseem ya fisge hannunsa dake cikin na boss ya kai hannu zai damƙoni ina ƙoƙarin matsawa. Cikin matuƙar zafin nama boss ya fisgi yah Qaseem ɗin gefe, hakan sai ya bani damar mannewa a bango na sake musu kuka kawai, dan zuciyata bazata iya ɗauka ba.8
A cikin tsagwaron fushi Qaseem ya damƙi wuyan rigar Jawaad zai shaƙeshi, “Amma kasan zan iya illataka ko?”.
Murmushi Jawaad yayi yasa hannu ya ture hannun Qaseem dake damƙe da wuyansa, cikin halin ko in kula yace, “Ka illatanin mana Qaseem, kai wai wace irin banzar zuciyane da kai haka? Mace zaka ɗaga hannu ka daka?”. A matuƙar masife Qaseem yace, “ina ruwanka? Miye matsalarka?” baki Jawaad ya taɓe yana watsa hannayensa da ɗage kafaɗa yace, “Banda” ya ƙare maganar da juyawa zai koma kujerarsa. Saurin maidoshi baya Qaseem yay, hakan ya saka Jawaad tsayawa sai dai bai juyo ya kalli Qaseem ɗinba, ƙoƙarin danne zuciyarsa yake dan bayaso su raba hali gaban yarinyarnan kamar yanda ya kula Qaseem yana buƙata. Cikin nunashi da ɗanyatsa Qaseem yace, “Wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe da zaka sake saka Bilkisu! cikin lamarinka, itaɗin matar dazan aurace, ya rage naka ka kiyayi ko kaci gaba”.
Rumtse idanu Jawaad yayi saboda jin yanda Qaseem ya ambaci sunan mahaifiyarsa gatsal, ya juyo a hankali yana kallon Qaseem cikin ido, cikin ƙunar zuciya yace, “Ko wacece ita a wajenka baya gabana, sai dai kai kasani baka isa hanani sakata aikin dana gadamaba tunda har tazo station ɗinnan a ƙasana, kasa a ranka yanzu aka fara wasan kuma, ina gargaɗinka Ka kiyayi kai hannu kan mace da nufin duka”. ya ƙare maganar a wani irin yanayin rainin wayo. Hakan sai yay masifar sake fusata Qaseem, a tsawace yace, “Matsayinka na ubanwa?”…………..✍
1
Qaseem team & Jawaad team banda faɗa kuma 🚴🏼🏋🏼🤼🏼😂😖.32
Ina Bil-Qas team nidai😜🤫🤸🏼.20
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻21Page 9
…………A matsayinka na ubanwa?” cewar Qaseem a fusace.
Cike da rainin wayo Jay yace, “Lokacine zai nuna maka”.8
Jabeer da ya shigo office ɗin kusan mintuna biyar da suka shuɗe, amma jaraba ta hanasu ganinsa yay gyaran murya.
Duk kallon ƙofar mukai, Cikin nuna alamun tamkar baima fahimci mike faruwa a office ɗinba ya kalleni tare da miƙamin kwalin dake a hannunsa, “Momcyn mu kikai wannan Office ɗin MM; daga nan ki wuce ƙasa naga ana nemanki”.
Kaina na ɗaga da sauri, na amsa kwalin na fice ina mai godema ALLAH da zuwan oga Jabeer da yay belina hannun waɗanan zakunan.
Babu wanda yay magana tsakanin Jawaad da Qaseem ɗin har Bilkisu ta fita, Jabeer ya maida kallonsa kansu yana ɗan murmushi, “Haba basawanmu, ya zaku saka yarinya tsakkiya kuna yaƙi? Ai saiku rikitata, miye nata a ciki tunda batasan miye tsakaninku ba?, yakamata kumata adalci, aiki take kamar yanda kuke aiki, ku sakata abinda zaku sakata matsayinku na waɗanda suke sama da ita, amma bawai ku sakata tsakkiya akan abinda ke zukatanku ba”.
Juyowa Jay yayi, kamar zaiyi magana sai kuma ya girgiza kansa kawai ya juya yana mai ɗaura hannunsa a kafaɗar Qaseem ɗin yaɗan bubbuga kaɗan ya koma mazauninsa. Binsa da kallo Qaseem yay cike da takaici da baƙin ciki, a ransa yana rayama kansa inhar Jawaad yay gigin cigaba da kutse a al’amuran Bilkisu wlhy wannan karon sai ya karta masa rashin mutuncin da bazai taɓa mantawa da shiba har ƙarshen numfashinsa, yaja tsaki tare da harar Jabeer ya fice daga office ɗin..
Jabeer dake binsa da kallo ya girgiza kai kawai sannan ya juyo ga Jawaad da ya cigaba da harkar gabansa, ƙarasawa yay ya zauna yana ɗora wayarsa a tebirin Jay ɗin, “Boss dan ALLAH son yarinyarnan kakeyi ne?”.
A bazata maganar ta zoma Jawaad, dan haka babu shiri ya ɗago idanunsa da sukai sirkin jaa da ƙara girma ya watsama Jabeer ɗin wata uwar harara, sai kuma yaja tsaki ya maida kansa ƙasa.
Jabeer ya haɗiye dariyarsa yana gyara zamansa, “ALLAH ba wasa nakeba Jay, kuma idan hakan ta kasance wlhy zanyi murna, dan nutsuwar yarinyar na burgeni, g……”
“Motsoww! Jabeer banason shirme, wace irin banzar maganace wannan, Please banaso karka sake”.
Hannu Jabeer ya haɗe waje guda alamar ban haƙuri, Jawaad ya kuma hararsa ya ɗauke kai. Shidai Jabeer yay murmushi kawai, cikin son kauda zancen yace, “Yanzu nakeji su Sir Ahmad sun sake shiga meeting akan batunnan”.
Jawaad da kansa ke durƙushe yana aiki yace, “Basai suyi tayiba tunda basu da tunanin kansu sai abinda aka ɗorasu a kai”. Jabeer yace, “Wlhy Jay ni mamaki suke bani ma, saboda ALLAH maimakon subama yarinya ƙwarin gwiwa akan abinda ta fara sai kawai su ɓige da tsugunne-tsugune, kai yanzu mi kake tunani akan batun?”.
Kallonsa Jay yayi fuska a taɓe, sai kuma yaja tsaki ya maida kansa ga abinda yakeyi, “Tunanin mizanyi akan wannan shirmen Jabeer, iyakaci suce zasu dakatar da ita na wani lokaci ta huta, ko su canja mata wajen aiki ai dai ko? Tunda basu isa suce ta ajiye aikiba akan hakan”.
“To ai babu wanda ya kamata kabari ya kasance a ciki” cewar Jabeer yana kafe Jay da idanu.
Shiru Jawaad yay bai tankaba, tsahon mintuna biyu harma Jabeer ya fidda rai da samun amsa sai yaji yace, “Akanmi zan hana ni kuwa? A matsayina kuma nawa? Dukansu ogannina ne, suna sama dani nesa ba kusa ba, to mizan iya musu kona hanasu?”.
“Jay! Saboda ina ƙwaɗayin yarinyar ta shigo tawagarmu”.
“Humm” Jawaad ya faɗa a taƙaice.
Jabeer da ya fahimci amsar kenan sai ya cigaba da faɗin, “Ba ƙaramar nasara bace hakan a garemu Jay, dan inaji a raina zata ƙara kawomana nasarori, amma kadaiyi tunani akan hakan”.
Ƙin cewa komai Jawaad yayi, hakan yasa Jabeer sakin zancen shima ya ɗakko masa na aikin da suka fara yau kawai, ananne Jay ɗin kuma ya bashi dukkan attention ɗinsa suka shiga tattaunawa.1
★★★★★★★
lna fitowa daga office ɗin MM naci karo da Ummie, bansan miyasa na tsinci kaina da gyara yanayinaba na sakar mata murmushi, hararata tayi ita kuwa tana fusgar hannuna mukai gaba. Masallaci muka nufa dan lokacin sallar zuhur yayi.
Bayan mun idar da sallane mun fito Ummie ke tambayata akan ina naje? Mi kuma ya sami kana?. Ban wani ja zancenba na bata labarin abinda zan iya, sai dai ban bata labarin miya faru tsakanina da yah Qaseem ba da kuma ceton da boss yay min a hannunsa yanzun.
Sosai naga mamaki a wajen Ummie tattare da labarin nawa, harna kasa haƙuri nai mata tambaya, tai ƴar dariya kawai da cewar, “Abunne da mamaki ALLAH, wannan mutum mai fuska kamar hadarin tsakkiyar damina ɗin?”.
“Ba abin mamaki bane Ummie, ni kawai na danganta lamarin da abinda ya farune ranar, ganina yake kamar wata jarumar gaske, baisan lamarin duk buge bane kawai” sosai Ummie ta kwashe da dariya cike da shaƙiyanci, nakai mata duka ta kauce tana cigaba da dariyarta, sai da tai mai isarta sannan ta dawo tana bani haƙuri muka shirya, daga haka muka cigaba da tsokanar junanmu da aikin dake gabanmu kuma.
Har lokacin tashi yayi ban sake saka boss da yah Qaseem a idanunaba, dama bai zama lallai na gansunba kasancewar bani da hurumin hakan sai idan sune sukaso, haɗuwarmu a inuwa ɗaya dama sai da ƙwaƙwƙwaran dalili. Haka kawai na tsinci kaina da tsoron bin yah Qaseem, sai kawai nabi Ummie ta saukeni a gida
STORY CONTINUES BELOW

★★★★★
Bayan sallar magriba ina zaune a saman abin salla ina azkar aka turo ƙofar ɗakina aka shigo, kaina na ɗaga ina kallonsa, yanda fuskarsa ke a tamke saida naji gabana ya faɗi, amma sai na dake abina nace, “Yah Qaseem ka dawo?”. Baice dani uffanba sai wata uwar harara daya makamin, ɗauke idona nai tamkar ban ganiba, ya ida shigowa cikin ɗakin yana bin ko ina da kallo, bakin gado ya ƙarasa ya zauna, hakan sai ya sakani jin wani iri, dan kuwa ni kaɗaice a gidan, koda na dawo ban iske kowa ba, su mom basu dawo daga gidan rasuwaba. A daƙile yace, “Waye ya maidoki gida?”.
Kaina tsaye nace, “Ummie ce, na jiraka naga baka fitoba gashi magrib ya gabato, sai kawai na biyota”.
Shiru yay tamkar bazaice komaiba, sai numfashi yake saukewa da sauri-sauri, hakan yasani tsira masa ido, “Yayah lafiya kuwa?”.
Wata harara ya sake danƙaramin kamar idonsa zai faɗo ƙasa, “Uwar miye haɗinki da shi Jawaad ɗin? Da har zaku fita tare? Ban miki Warning akansa ba?”.
Zamana na gyara sosai akan abin sallar saboda jin ƙafata ta fara yami, duk da na lura bawai maganar wasa yakeminba inata ƙoƙarin dakewa.
Bansan yanda zan bashi amsa ya fahimtaba, amma ni banajin kuskure nayi tunda akan aikine ai. “Dake nake magana Bilkisu!!”. Saurin kallonsa nayi danjin yanda yay maganar a kausashe, nace, “Aiki muka fita fa”.
“Aiki? Duk jami’an dake cikin Station ɗin babu wanda zai ɗauka suje aiki sai ke?”.
“Yayah ni wlhy ban saniba”.
Saida yasake watsamin harara dayin ƙwafa sannan yace, “Su kuma waɗannan kayan na jikinkifa da nagani ɗazun? Ina kayan da kika fita dasu daga gida da safe?”.
Kaina tsaye nace, “A wajen aiki da muka fita ne a mistake jikinmu ya ɓaci, to shinefa sai… Sai… Sa………”
“Sai ubanmi? Bilkisu!!”.
“Sai Rose ta bani wasu kayan na zanja”.
“Harda ita kuka fita?” yay maganar cikin kakkafeni da idanu. “Eh” na bashi amsa cike da ƙwarin gwiwa.
Karon farko da yaymin murmushi, ya sakko daga saman gadon ya zauna kusa da ni sosai ya tanƙwashe ƙafafunsa (Dan zuciyarsa tayi sanyi jin basu kaɗai bane, amma hakan ba yana nufin zaiƙi saka musu ido bane ba). Yanda muka samu kusancine ya sakani matsawa baya kaɗan, baice komaiba, saima hannuna daya kamo cikin nashi, nai ƙoƙarin amshewa amma sai ya hanani damar yin hakan, murya a sanyaye yace, “Bilkisu!”.
Amsawa nai idona na kawo ƙwalla, dan banason kama hannuna da yayi……
“Kinsan kuwa yanda nake sonki da kishin ganin wani ya raɓeki?”. Shiru nai bance komaiba, shima bai jira amsata ba ya cigaba da faɗin, “Daga yau karna sake ganinki da Jawaad, idan kuma ba hakaba to lallai zan saɓa miki kuwa! Domin koba aurenki zanba yayankine ni, dolene na saka miki ido gudun karki lalace”.
Yanda ya ƙare maganar sai yaban dariya, a raina nace, ‘Kaima ka samu dama ai lalatanin zakai’, amma a fili sai, nace, “Yayah nifa banice naje wajensaba, bayan na fito daga kiran da akai minne mukai karo dashi a hanya, shi kuma ya fito daga office ɗinsa, shine yace na biyosa, da farko ma bansan dani yake ba sai da ya sake aikowa sannan, amma dan ALLAH kayi haƙuri”.
Murmushi yay min yana jinjina kai, yace, “Nasan dama ba laifinki bane, amma zan takama al’amarin birki tunkan yay nisa kinji, ina sonkine da yawa shiyyasa bazan juri ganinki da waniba ballema maƙiyina Bilkisu…”
Ya ƙare maganar a hankali yana matsowa jikina sosai, gabana ne ya shiga faɗuwa, nai ƙoƙarin ja da baya amma sai hakan ya gagara saboda riƙon da yaymin bana wasa bane, sannan ƙarfina da nasa ba ɗaya bane, matsananciyar rawa jikina na fara sabida ƙoƙarin kawo fuskarsa kan tawa da yake, na shiga girgiza masa kai ina hawaye, roƙonsa nakeson yi, bakina sai motsawa yake amma na kasa furta komai, ya riƙe kaina da ƙyau yana ƙoƙarin ɗora bakinsa kan nawa na ƙwalla ƙara.
Da sauri ya sakeni shima yaja baya saboda tsorata da ƙarata, jikina sai ɓari yake na tashi a guje na shige toilet ɗina na banko ƙofar harda murza key. ‘innalillahi wa inna ilaihirraji’un’ naketa ambata, wace irin masiface kuma wannan ni Bilkisu, kuka na shiga rusawa a bayin sosai, duk da inajin ƙwanƙwasa ƙofar da yaketa famanyi yana kiran sunana da bani haƙuri banko tankashiba, kusan mintuna talatin naji shiru alamar yabar wajen, ban buɗe ƙofarba har sannan sai bayan wani lokacin sannan na buɗe kaɗan na leƙa, babu kowa a ɗakin saima ƙofa dana gani buɗe alamar ya fita, komawa nai toilet ɗin na ɗauro alwala na fito, sai da na sakama ƙofar key kafin na tada sallar isha’i.
Haka nai kwanciyata da yunwa ban fitaba duk da inajin motsin su mom da suka dawo kusan ƙarfe goma, ina idar da sallar asuba nai shirin barin gidan, dan gwarama na shiga gidansu Amina daga baya sai na wuce wajen aikin, bazanbi yah Qaseem ba. Sauri-sauri na kammala na fito, gabana ya faɗi ganinsa zaune a falo yana shan shayi alamar dai shima harya gama shirinsa, yanda ya tsatstsareni da idanu kuma ya sakani tsayawa cak nai ƙasa da kaina, “Kizo kisha shayi mu wuce, dan sauri nake yau”.
Bance dashi komaiba na wuce zuwa kicin, kaɗan na haɗa tea a kofi na zauna a kicin ɗin ina sha, dan kuku ma bai kai ga fitowaba, saurin kallon ƙofar nai jin an shigo, nai masa kallo ɗaya na ɗauke kaina gefe, baice komaiba nima banceba, sai ajiye kofin da nai na nufi ƙofa, matsawa yay ya bani hanya, a ɗarare na raɓashi na fita yabi bayana.
Badan raina yaso ba na shigar motar Yah Qaseem yau ɗinnan, shiru motar babu mai cewa komai ni da shi, ko redio bai kunnaba, tuƙi yake a hankali kamar bayaso, mun ɗanyi nisa da gida ina lafe a jikin kujera da karanto addu’ar neman tsarin ALLAH daga shaiɗanin dake ingiza zuciyar yah Qaseem ga abinda bai daceba gareni naji motar kamar ta tsaya, idanuna dake cike da barci na buɗe, naɗan waigo na kalleshi, ganin ni yake kallo sai na janye idanuna ina sake gyara zama, wlhy bazan ɓoye mukuba a tsorace nake, bani da ƙarfin dazan kare kaina ga murɗaɗɗan namiji irin yah Qaseem koda ace yay shirin cutar da nine, cikin dauriyar dole nace, “Yah Qaseem lafiya muka tsaya?”.
Ajiyar zuciya ya sauke a hankali, har lokacin inajin idanunsa na yawo a kaina, sai dai baice komaiba, kusan mintuna biyu suka sake shuɗewa, a bazata na tsinkayi muryarsa, yace, “Kiyi haƙuri Bilkisu akan abinda ya faru jiya, banyi hakan da niyyaba tunda kinsha faɗamin baƙyaso”.
Ajiyar zuciya na sauke inajin daɗin kalamansa, na share hawayen da suka zubomin, ba tare dana kallesa ba nace, “Na haƙura Yah Qaseem, amma dan ALLAH ka rufamin asiri, kaji tausayin maraicina ka barni da mutuncina, gidanku itace mafakata ta ƙarshe da nake alfahari da ita, idan shaiɗan ya lulluɓe maka ido ka tuzguɗemin ita bansan ina zan dosaba, haramunne a addininmu, sannan cutarwace a garemu, wannan ba shi bane soyayya kamar yanda yake a tunanin yahudu da nasara, ƙoface kawai ta saɓon UBANGIJI, kuma tushen fasiƙanci, daga kama hannuna da kakeson yi a koda yaushe matsala zata fara, tun inaji banason hakan wataran sai kaga shaiɗan ya ƙawatamin nafara jin daɗi, a tafi matakin sumbata, makulin buɗema shaiɗan ƙofa kenan da komai na baɗala zai iya wanzuwa tsakanin namiji da mace, duk takatsantsan ɗinmu wataran kafin mu farga sai akai ga aikata zina, ‘Wa’iyazubillah’. Yah Qaseem namiji da mace duk hukunci ɗaya garesu wajen ALLAH idan suka aikata zina, amma a zahirance ta rayuwar duniya mace itace ke fara ƙasƙanta a idanun al’umma makusantanta dama na nesa da ita, domin itace ke ɗaukar ciki, itace wasu almomi ke fara bayyana a gareta, farko rasa mutunci, ƙasƙanta mutincin gidansu dama ahalinta, tabon da zaita bibiyar rayuwarta har ƙarshen zuri’arta, ita ake fara aibantawa kafin abokin tarayyarta, itace ke rasa mijin aure, ita akafi nunama ƙyama, itace keda rauni. Abin tausayi da tashin hankali ƴa mace na fuskantar waɗanan matsalolin koda ace fyaɗe akai mata. Yah Qaseem indai sona kace da gaske dan ALLAH ka daina min waɗanan abubuwan, wlhy banaso, basa burgeni……”
Qaseem yaja wani bahagon numfashi saboda tausayi da bily ta bashi, harga ALLAH sonta yake da gaskiya ba yaudaraba, ALLAH ne ya jarabcesa da sonta batare daya shiryama hakanba, yanda take kuka sai ya kumajin tausayinta sosai a ransa, murya a sanyaye yace, “Na fahimceki Bilkisu, insha ALLAH kuma zan kiyaye, idan kin amince zanma Dad magana akan aurenmu”.
Sauran hawayena na share tare da kallonsa, ganin ni yake kallo sai na ɗaga masa kai alamar na amince. Ya saki wani murmushi najin daɗi yana sake tsatstsareni da idanunsa farare tas, a hankali ya furta, “Inasonki da yawa Bilkisu na, gara dai nayi na mallakeki kusa dani na huta da wa’azinnan”. Murmushi nayi ina ɓoye fuskata, shima yay ƙaramar dariya yana mai tada motar muka cigaba da tafiya. Hira yaytamin har muka ƙarisa station ɗinmu duk da ba amsa nake bashiba sai dai eh ko a’a da murmushi kuma.1
BAYAN KWANA UKU.
A kwanaki ukunnan Boss bai sake shiga harkataba, harna ɗauka gargaɗin Yah Qaseem ne yasa ya barni, tunda ina ganin dai yana sama dashi. Shima a ɓangaren Yah Qaseem na samu sauƙin yawan kai hannunsa jikina da yakeyi, sai dai wasu take-taken Yah Salman a gidan yanzu suke cazamin kai, ya masifar samin idanu, kowane motsina sai ya tanka magana a kai, Aunty Shahudah cema naga dai tayi sanyi, bansan mike damuntaba, amma saina lura kamar bata cikin nutsuwarta.
Ban sake cema baba maigadi komaiba game da zancen Amina saboda saka idon Yah Salman a kaina, amma inata wasu shirye-shirye a gefe nabin matakan da zan gano bakin zaren, dan abinda baba mai gadi yayi ranar yana nan tsaye cak a zuciyata bai gogeba. Da wannan tunaninma yau na fita wajen aiki.
Tunda muka dawo sallar zuhur muna a office ɗinmu da boss ya dunƙulemu, kowa yana hidimar aikin daya dace, yayinda Ni da Ummie muna aikine muna ƴar hirarmu data shafemu, hakama sauran kowa nayi da abokin maganarsa, hakanne yasa ɗakin ɗaukar kananun surutai sama-sama. A bazata naji office ɗin ya ɗauki shiru tamkar ruwa ya cinye kowa, batare dana ɗagoba nai ƙaramar dariya ina faɗin, “Ummie mutuwace ta gitta a office ɗin namu ne?”.
Shiru naji Ummie batace komaiba, hakanne ya sani ɗagowa a tunanina batajini ba.
‘kutumelecy’……………✍1
Assalamu alaikum.2
Inason naɗanyi bayani da nake fatan a fahimceni, akan maganar aikinsu Jawaad, inason mai karatu ya fahimci wani abu anan, aikin da muka dangantasu dashi bawai yana nufin ainahin abinda ya shafi ma’aikatan zahirin bane, bamusan komai da ya shafesu ba, tayaya zamuce komai nasu sai ya shigo labarinmu, domin ba’akan hakan muke rubutu ba, da yawanmu ma idan za’a tambayemu bazamuce munsan waɗanan ma’aikatanba kai tsaye, domin su aikinsu bawai a bayyane yakeba kamar ƴan-sanda da dai sauransu da suke cikinmu ba, aikine na wanda kai kanka idan ba wani daliliba bazaka taɓa ka gansu suna yawo gama gari ba ko wani aikinsu a bayyane, so na danganta waɗanan jaruman littafine da hakan saboda mutunci da himma da ƙwazo na irin jami’anmu da mu kanmu bamu saniba, matasanmu kuma su zama masu himma dason bama ƙasarsu gudunmawa da zuciya ɗaya a kowace ƙasa suke ba lallai sai tamu ba, tom inaso ku kalli wannan kawai a matsayin labari bawai lallai abinda yake a zahiri ba, ko yake lallai mu bibiya, matsayinsu, misukeyi? Mizasuyi? Duk iyakarsa labari irin na marubuci {ƙirƙira}, bani da hurumin shiga abinda bani da lasisi a kai, domin bamma sani ba, waɗanan jami’an littafine bawai na zahiri dake aiki a ƙasarmu ba, idan kun kula sam babu wani sunan gari dake nunama a ina suke, ko a wane waje suke, musa a ranmu kawai ƙirƙirarren labari muke karantawa, ilimantarwa, nishaɗi, da faɗakarwa, ba akan kowaba, domin ba’akan kowan mukeyi ba, duk abinda zamu iya ganin yaci karo da waccan rayuwar ta zahiri to kawai fiƙira ce irin ta marubuci bawai dan inada ilimin sani ba ko bibiya balle bincika, ina fatan duk wanda ke bibiyar wannan littafi a ko’ina yake zai kasance maiyin ƙyaƙyƙyawan fahimta akan inda muka dosa, sannan abinda kake ganin na karkace ko shiga hurumin da banawaba ina fatan zakuyi gaggawar dawo dani hanya, ALLAH yasa mu dace, ALLAH kuma ya ƙarama dukkan jami’an tsaronmu lafiya da ƙwazo da nagarta a duk duniyar da suke.🙏🏻
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻17
Page 10
…………‘Kutumelecy’ na faɗa a cikin raina ina saurin janye idanuna dana ware a kansa da tsaida taunar cingam ɗin da nakeyi lokaci ɗaya, ganin yanda ya tsatstsareni da muggan idanunsa. Zungurin ƙafata dana ɗora saman tebir ɗina Ummie tayi.
Kallonsa na sake sata sai naga shima idanunsa yanzu akan ƙafar tawa suke harma da sauran ƴan uwana, da sauri na sauke ƙafar ƙasa na nutsu kamar yanda kowa yayi. Bai tankama kowaba ya ida takowa tsakiyyar ɗakin yana binmu da kallo daki-daki, har tsawon mintuna biyu muna a haka tamkar ɗan doka da ƴan gidan kallon ƙwallo ko ɓarayin agwagi, nidai sai faman jan addu’a nake saboda jin yanda zuciyata ke bugawa da sauri-sauri tamkar ko yaushe idan na samu kusanci da shi.
Ganin bazai tankaba sai muka shiga gaisheshi ɗaya bayan ɗaya, hannu kawai yake ɗaga mana amma bai sake kallon kowaba baikuma amsa mana da bakiba. Yaja kujerar dake gaban tebir ɗin Uchie ya zauna, bamusan mi suke tattaunawaba har kusan tsawon mintuna sha biyar kafin ya miƙe ya fice. Yana fita muka shiga sauke a jiyar zuciya, yayinda wasu suka shiga gulmarsa musamman ma matan cikinmu, nidai sabon cingam na ɓare na jefa a baki na cigaba da sabgar gabana.3
____________________________________
A gidan su Jawaad kam taron meeting Mom ta tara da ƴan uwanta, sunɗau tsahon lokaci suna tattaunawa akan Jawaad da maganarsa da Shahudah, duk da dai da farko Uncle Nasir yaso bijirewa, a cewarsa suma sunada ƴaƴan da zasu bama Jawaad ɗin ai ya aura. Shahudah ta kiya musu hankalin da bai kamata su sake sakata a sabgarsu ba.
Kuka mama Atika ta fasa musu, tare da ɗakko musu maganar data saka suka nutsu waje guda.
“Munsan Sabira tayi laifi da tafka kuskure a baya, amma kuyi haƙuri munada tabbacin zuwa yanzu ta magantu za’a samu gyara musamman idan mukai dubi da yanda take son yaron, amma ni na yarda da shawarar Nasiru, mu fara ma Jawaad maganar auren wata a cikin yaran gidannan, idan ya nuna rashin amincewa saimu tirsasashi ya maida Sabira ɗakinta, dan baikamata mu zubamasa ido yana yawo sakaka babu aureba, shekararsu kusan biyar kenan da rabuwa, amma yaƙi aure, inba neman matan banza yaron nan yakeba yaza’ai mutum mai lafiya kamarsa ace yanaƙin aure?, su waɗancan dangin uwar tasa sakarkaru da yake tsoronsa sukeji sun gaza masa magana kuma, tomu bai kamata mu saka masa idoba, dan kuwa mune duniya zata zaga basuba, amma yaya kuka gani? Danni dai shawarace na kawo matsayina na uwa a gareku, da Badiyya nada isashiyar lafiyama tare zamuyi muku, yanzu saiku zauna ku yanke shawara a tsakaninku” ta ƙare maganar da tashi ta fice daga falon.
Duk binta sukai da kallo harta fita, Uncle Sulaimam ya sauke numfashi yana faɗin, “Nidai ƴan uwana na yarda da maganar mama, dan nidai zaman Jawaad bayamin daɗi a haka, da Abdul-aziz nada rai bazai zubama gudan jininsa ido kamar yanda mu muka kasa riƙe amana mukaiba, duk da bana zargin Jawaad da neman mata, dan mu shaidane akan tarbiyya da sanin yakamata na yaron nan”. Duk shiru sukai basu ce komaiba, wasu na hararsa ta gefen ido wasu na ƙunƙuni a cikin rai, dan suma sunsan ƴaƴan Mama Badiyya sam nasa tare da burinsu a gidan, su kaɗaine masu ƙaunar Jawaad dan ALLAH badan dukiyarsaba. Jin shirun yayi yawane ya saka Mom yin magana. “Nima na aminta da maganar mama, kuma ina goyon bayan ɗan uwana Sulaiman”.
Daga maganar Mom sai kowama ya fara faɗar abinda ke ransa, daga ƙarshe dai suka ajiye shawara akan zama da Jawaad ɗin idan ya dawo aiki da wuri yau, kokuwa weekend idan ALLAH ya kaimu.4
_____________________________________
A makare yau Jawaad ya tashi a wajen aiki, saboda fitar da sukai shi da Hafiz zuwa wani waje da yamma, basu dawoba sai bayan magriba, akwai abinda zai ɗauka a office shiyyasa suka dawo, amma da daga inda sukaje gida zai wuce. Bayan ya tattaro abinda zai ɗakko a office ɗin nasa sai yaga lokacin sallar isha’i ma yayi, dan haka suka tsaya sukai a station ɗin.
Koda suka fito yunwar dake cin cikinsa yasa yace su tsaya wajen wani haɗaɗɗen gashin kaji, gimba ya amsa masa da girmamawa. gimba ne ya fita domin amsowa, kasancewar wajen ba baƙonsu bane akaima gimba tarba ta sanayya, kamar yanda Jawaad ya bashi umarni takeaway biyu akayi sai fura da yogurt masu sanyi aka saka ɗaɗɗaya a ciki, gimba ya bada kuɗin sannan ya dawo mota suka ƙarasa gida.
Ganin da sauran mutane da keta shigi da fici a sassan gidan sai ya bashi mamaki, a ganinsa dai tunda anyi addu’an bakwai mikuma mutane keyi tunda ba taron biki bane. Saurin kauda abin yay a zuciyarsa dan a ganinsa hakan ba huruminsa bane, yaso shiga sashen Uncle Usman ya gaida Mama Zainab matarsa kamar yanda yakeyi kullum tunda akai rasuwar, sai dai a matuƙar gajiye yake, ga masifaffiyar yunwa dake cin hanjinsa.
Tare suka shiga sashensa da gimba dake ɗauke da tarkacensa, bayan ya ajiye masa a falon ƙasa yay masa sallama ya fita, shima bai iya ƙarasawa bedroom ba ya yada zango a falo, sai da ya huta na wasu mintuna sannan ya miƙe ya haura sama, duk da yana buƙatar fara cin abinci haka ya daure, dan shi mutumne mai yawan cin abinci, idan bai samu bane dai yakanyi haƙuri kawai. Ɗakin barcinsa ya ƙarasa ya watsa ruwa, kusan ƙarfe tara ya fito tsaf dashi sai baza ƙamshi yake. Ya shiga kicin ya ɗakko kofi da filet, a falon ƙasa ya zauna ya kunna tv domin kallon labarai, yana kallonne yana cin abinci, lokaci-lokaci kuma yakan amsa waya idan an kirashi, ya daɗe zaune a falon har aka kammala labaran kafin ya miƙe yay ciki dan yana matuƙar buƙatar hutawa.
STORY CONTINUES BELOW

SHAHUDAH
Saboda son haɗuwa da Jawaad yasa yau taƙi binsu Mom gida, a cewarta nan zata kwana, Mom bata hanata ba, suka tafi ita da Aamilah kawai saboda Salman ne yazo ɗaukarsu dama ba driver ba.
Wajen ƙarfe goma ta kammala kwalliyarta, tai shiga cikin kayan barci masu taushi da ƙyau, dan sunyi masifar fidda mata surarta, sai ƙamshi take kamar jikar gidan mai turare, a ranta ta ƙudiri aniyar maido hankalin mijinta kanta yau, dan ta gaji da wannan wasan ɓuyan da sukeyi, ta kuma shirya karɓar cikin da yake buƙata. (Karku manta Shahudah batasan Jawaad ya saketa ba fa😥🤦🏻, ɓoye mata shine kuskuren dasu mom suka tafka).
Hijjab ɗin mama Atika da ya kai mata har ƙasa ta ɗauka ta saka, babu kowa a sashen na mama Atika, itama tayi barci ma tun ɗazun, kai tsaye Shahudah ta nufi sashen Jawaad tanata zuba murmushi, dan ita kaɗai tasan abubuwan data shirya masa, yau ɗinan basai gobeba sai ta zautar da gayen nan, ta sake sakin tattausan murmushi lokacin data murɗa ƙofar taji ta buɗe. Jawaad ya manta shaf bai rufeba ya haye sama, sai da ta gama ƙarema falon kallo, komai tsaf tamkar ba namiji ke zauneba, tasan Jawaad yanada tsafta, sam bayason ƙazanta, duk jin kan nan nasa baya ƙyashin tashi yay shara yay morping wa sashen,, ya samu wannan horonne a zamansa da kakarsa Mama maryam, hatta da girki Jawaad ya iya, kawai rashin isashen lokacin kai ne ke hanashi yi. batasan miyasa bayason masu hidimaba. Ta sake sakin murmushi kafin ta fara taka steps ɗin a hankali tana wani yauƙi saikace tarwaɗa, a falo ta cire hijjab ɗin ta jefa saman kujera, ta kuma gyara rigarta da gashinta sannan ta nufi hanyar ɗakinsa.
Jawaad kam a gajiye yake matuƙa. hakan yasa yana shigowa bayan yay brush da alwala yay adduar barci ya kwanta, bai wani jima da kwanciyaba barci yay gaba dashi, fitilar gefen gado ce kawai a kunne, itama ta ɓangare ɗaya, hakan yasa ɗakin yay dim babu haske sosai, bai kumayi dunɗum ba. Shahudah data murɗa ƙofar ta shigo a hankali ta sauke ajiyar zuciya tana mai shaƙar ƙamshin da ɗakin keyi, komai na Bb’n ta daban yake dana kowa, bata ganin fuskarsa, dan ya juya ma ƙofar bayane, sannan ya lulluɓa da bargo saboda uban AC’n daya ƙure ɗakin da shi, ‘ko tsoron murama bayayi’ ta faɗa tana ɗaukar remote ɗin acn ta rage ƙarfinsa.
Jawaad da baisanma hidimar da akeba barcinsa yake hankali kwance da mafarki mai daɗi, hakan yasa yaketa faman sauke numfashi a hankali. Ya sauke ajiyar zuciya lokacin da Shahudah ta hawo gadon a hankali ta kwanto bayansa bayan ta ɗaga bargon ta shiga, itama ajiyar zuciyar ta sauke ƙwallan kewarsa na taruwar mata a idanu, jitake tamkar ta haɗiyesa ta hutama kawai. Cikin salon data shirya masa a wannan dare ta fara yawo da hannunta a jikinsa, Jawaad dai bai motsaba, amma da alama jikinsa na karɓar saƙwannin Shahudah kamar yanda tai fata. Mafarkin da Jay keyi da saɓanin Shahudah yay dai-dai da abinda take masa a zahiri, hakanne yasa ta samu haɗin kan gangar jikinsa har takai ya gyara kwanciyarsa yana sake rungumeta, hakan yayma Huda daɗi kuwa, ta ƙara ƙaimi kan abinda takeyi, kamar wasa saiga tafiya tayi nisa a tsakaninsu, dan tuni ya fara maida mata murtanin sumbatarsa da takeyi.
Yanda take sauke numfashi ne da sauri-sauri akan fuskarsa ya sakashi farkawa, dan kuwa tabbas wannan al’amarin ya wuce a mafarki kawai, a matuƙar razane ya hankaɗeta daga jikinsa yana ambaton “Innalillahi wa-inna ilaihirraji’un. Wace ƴar iska ce haka ta shigomin ɗaki?”. Yay maganar yana ƙoƙarin kunna fitilar ɗakin.
Shahudah daya jefar gefe duk da taji zafi tai ƙoƙarin tashi zaune tana sauke numfashi a gwame, hasken daya gauraye ɗakin ne ya basu damar ganin juna. Kansa ya dafe yana ƙara ambaton “Innalillahi….” Shahudah ta matso jikinsa tana neman kwantawa a kafaɗarsa ya sake tureta a fusace, “Wai ke wane irin dabbanci ne wannan? shin baki da hankaline Hudah?”. Tabbas maganganunsa sun mata zafi, amma saita daure cikin dakewa da tsiwarta tace, “Dan nazo wajen mijina zakacemin banda hankali?, to ka ɗauka ni da kai duk mun zama mahaukatan”.
Karon farko Jawaad ya waro idanu waje, yace, “Miji!?, Hudah rashin ilimin addinin naki harya ƙara faɗaɗa haka? Kinga bani da lokacin wannan haukar tashi ki fitarmin daga sashe kafin na saɓa miki kamanni, kuma wlhy wannan yazama na farko na ƙarshe da zaki sake shigomin nan”.
Kuka Shahudah ta saki, ta nuna kanta tana faɗin, “Yanzu nan tsanar da kaimin bb har ta kai haka? To wlhy babu inda zanje, dan inada haƙƙi a kanka ai, duk ma abinda zakayi sai kaitayi, amma ka sani niba ƴar iska bace, amma wlhy da tuni naje na nema wani namijin a waj…….”
Mari ya kai mata tai saurin kaucewa, cikin daka tsawa yace, “Tashi ki fita a ɗakinan kafin na raba kanki da wuyanki wawuya kawai!!”. Saurin sauka tay a gadon, dan yanda ya harzuƙo ɗinan zai iya maketa, batasan ma bashi da wannan ƙarfinba a yanzu, dan ta sakashi a kwale-kwale. Da ƙyar Jawaad ya iya sakkowa a gadon saboda tashin hankalin da Shahudah ta sakashi, duk ƙoƙarin kame kansa da dauriyar da yakeyi yau ta kwanto masa liƙi, ya murzama ƙofar key ya dawo saman gadon jiki babu ƙwari. Gaba ɗaya kansa ya toshe, yama gaza yin tunani akan Shahudah.
Duk yanda Jawaad yaso yayi barci a wannan daren ya kasa, gashi maganin da yake sha ya barsa a office saboda ya ƙare ya sayosu jiya, sai kuma ya manta bai ɗakkoba, ya watsama jikinsa ruwan sanyi yafi sau shidda kafin asuba, sosai mararsa ke masa masifar ciwo, ko sallar asuba bai fitaba a ɗaki yayi, sai bayan ya idarne barci ɓarawo ya sacesa, shima a matuƙar wahale yayisa.
Shahudah kuwa da kuka rurus tabar sashen zuwa sashen mama Atika, a falo ta zube tacigaba da kukanta har barci ɓarawo ya saceta.
6
___________________________________
Yau ma har muka fito Office banga kowa a cikin ƴan gidanba, cikin nishaɗi muke ƴar firarmu da Yah Qaseem har muka iso, saida na rakashi har office da tarkacensa sannan na fito nima zuwa namu.
Ummie bata isoba, hakan yasa na zauna bayan mun gaisa da waɗanda na tarar, ƴan abubuwan da baza’a rasaba na shiga yi, gefe ɗaya kuma ina amsa hirarsu Dawood sama-sama akan aiki, a hankali mukaita ƙaruwa har kowa ya gama isowa, Ummie ta zauna saman tebirina tana faɗin, “Bily gulma da ɗumi-ɗuminta fa”.
Kallonta nai ina faɗin, “Ƴar sa ido mikika samo mana?”. Ƙaramar dariya tayi da sauke murya ƙasa tace, “Ankawo kuɗin Nazifa”. “Dan ALLAH da gaske?” nai maganar cikin waro ido waje bakina washe da fara’a. Ummie tace, “Wlhy da gaske nake, kema tace ta kiraki bai shigaba, amma ta tura miki saƙo ai”. Wayata na ɗauka ina faɗin, “Kashewa nai da zan kwanta, tunda na tashi kuma ban buɗe data ba, oh ni su Nazifa an mana wayo, da Al-mustaphan dai?”. “Shi kuwa” cewar Ummie tana dariya.
Fita mukai zuwa can baya nai kiran Nazifa a waya, bugu biyu ta ɗauka tana faɗin, “Inba gulmaba Bily miye na kirana da farar safiyarnan?”. Dariya mukai ni da Ummie, nace, “Ai gara dai muci gulmar da ɗuminta basai ta huceba, yarinyarnan da gaske dai kin dage aure kikeso?”. “Ban isa bane?” Nazifa ta faɗa tana dariya. “Kin isa kuwa tsaf” Ummie ta bata amsa. Haka muka cigaba da hira cikin so da ƙaunar juna har bamusan lokaci yaja ba.
Daƙyar muka iya katse hirar muka koma office gudun kar’a nememu.
JAWAAD
Kamar da wasa ƙaramar magana ta zama babba, dan kuwa dai daga kwanciyar da Jawaad yay bayan sallar asuba sai zazzaɓi mai azabar zafi ya rufesa, duk yanda yaso ƙoƙarin tashi yay shirin office lamarin ya gagara. Wani wahalallen barcin nema ya sake awan gaba dashi bayan ya koma saman gado yaja bargo.
Gimba yay shiri da wuri kamar yanda yasan suna sammakon fita, sai dai yafi tsayuwar awa guda wajensu baba maigadi babu alamar boss ɗin nashi, dama kuma bai gansa a massallaci ba yau da asuba. Bai dai tambayi kowaba ya cigaba da jira har zuwa ƙarfe tara, zuwa lokacin dai kam abin ya fara bashi mamaki, abinda zai riƙe boss har ƙarfe tara bai fita office ba to lallai dole ya saka kokwanto a zuciyar duk wanda yake tare da shi, wayarsa yay kira har sau uku ba’a amsaba, ya sake daurewa dai ya zauna awa ɗaya ta kuma shuɗewa goma tayi. Yanzu kam tilas ya miƙe ya nufi sashen, yay knocking har kusan sau goma baiji motsin kowaba, hakan yasashi murɗa ƙofar, cikin sa’a kuwa ta buɗe, sai dai koda ya shiga babu kowa a falon, babuma alamar wani ya fito cikinsa. Nan kawai yake da hurumin shiga dan haka bai ƙara gaba ba ya juya ya fita. Yabar wayarsa a mota har baisan su Oga Aliyu nata kiransaba suma jin Boss baizo office ba, sun kuma kira wayoyinsa duka babu wacce ya ɗaga, shine suke kiran Gimban suji ko wani waje sukaje? Amma shima kuma bai amsa musu ba.
Misalin sha ɗaya da wasu mintuna sai ga Nabeelah da Ummansu sunzo gidan domin sake yima mama Zainab gaisuwa, dan rabonsu da gidan tun ranar rasuwar. Bayan sun shiga sashen mama zainab sun fito sai suka shiga wajen mama Badiyya don su gaisheta da jiki, basu jimaba suka fito zuwa sashen mama Atika, ananne suka iske Shahudah babu lafiya, tana kwance cikin doguwar kujera lulluɓe da bargo, sun mata addu’ar samun lafiya suka miƙe zasu tafi amma sai mama Atika ta tsaidasu da zancen auren Jawaad, murmushi Ummah tayi kawai, tabama mama Atika haƙuri akan zasu masa magana, baki kawai mama Atika ta taɓe, su Umma kuma suka fito abinsu Nabeelah nata ƙunƙuni akan ansama yayansu ido. Basuyi zaton samun Jawaad a gidaba, dan haka sukai yunƙurin barin gidan, Gimba daketa dakon jiran fitowarsu yay azamar isowa garesu yana gaida Umma, da mamaki ta amsa masa, “A’a gimba baku fita office bane ko dawowa kayi kai?”.
“Wlhy mama bamu fitaba, har yanzu boss bai fitoba, bansan ko lafiya ba? Nai knocking na kirashi amma duk babu wani amsa”.
Shiru Ummah tayi na wasu sakanni, sai kuma ta fasa shiga motar ta nufi sashen Jay, Nabeelah ma data tuƙosu harta shiga mota ta kunna ta kashe ta fito tabi bayan Ummah.1
____________________________________
kasancewar juma’a ce yau ɗin bayan an sakko salla mun fito zamu fita neman abinci saboda yunwar da nakeji mukaci karo da Oga Jabeer zai shiga mota, har mun gaishesa munwuce sai kuma yay kirana. Dawowa nai ina amsa masa da girmamawa, yace, “Shigo mota ki rakani wani waje”.
Duk da banso ba sai ban masa musuba na shiga Ummie kuma ta wuce tana min dariyar mugunta…………✍
“Saura muji wani yace Hudah🙄 ehe😏.
10
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
9Page 11
……………Tafiyar da batafi mintina talatin ba muka iso inda ya bani mamaki, bandai cema oga Jabeer komaiba har aka buɗe mana gate muka shiga. A dai-dai sashen da mukai salla ranar rasuwar Uncle Usman yay fakin, ya kashe motar yana faɗin, “Muje ko”.
Bance komaiba na buɗe murfin na fita kamar yanda shima yayi, yana gaba ina biye da shi har zuwa ƙofar falon, sai kalle-kalle nake ina ƙara jinjina girman wannan gida, koba’a faɗaba kasan an narkar da dukiya wajen ginashi, Oga jabeer ne yay knocking, babu jimawa akazo aka buɗe ƙofar.
Cikin murmushi Nabeelah data buɗe ƙofar tace, “Yah Jabeer sannu da zuwa”. “Yauwa Nabeelah” ya amsa yana mata murmushi shima. Sai da ya shige sannan ta ganni, cike da mamaki ta waro idanu alamar ganina a bazata da tai, kafin ta daka tsalle ta ɗaneni tana dariya, “Lah ƙawata dama rai kanga rai?”. Murmushi nayi ina mai jinjina wautar Nabeelah a raina, cikin surutunta tace, “Dama kinsan Yah Jabeer?”. Amsa na bata da cewar, “Eh, wajen aikinmu ɗaya”. Zata sake jehomin wata tambayar Jabeer ya katseta, “To Akku mai bakin magana kaimu ɗakin da yake”.
Yanda tayi da fuskane ya sakani yin murmushi, ita a dole taji haushin ance mata Akku, hannuna ta kama tana tuttura baki gaba tai mana jagora har sama, bansan minene ya kawomuba balle tunanin wajen wa mukazo, ni dai kawai inabin Umarnine. ‘Tabɗi’ na faɗa a raina saboda ganin yanda falon saman ya haɗu matuƙa shima, sai sassanyan ƙamshi ke tashi, muryar kamilar mace ta amsa mana sallamar da mukai tare da faɗin, “Jabiru sannunku, ku shigo mana”.
Oga Jabeer ya amsa da “Yauwa Umma, ashe kema kina nan?”. Tace, “Eh muma bamu jima da zuwaba, nazo na sakema Hajiya Zainab gaisuwane sai Gimba ke cemin basu fita Office ba, yanata jiran Jawaad ya fito bai fitoba, shinefa na shigo na iskesa kwance rijif cikin zazzaɓi”.
“Ya salam, wlhy muma a office tun ɗazu muke zuba idon ganinsa amma shiru, mun kirasa bai ɗaukaba hakama Gimba, tomu tunaninmu koma wani wajen sukaje tunda munga jiya lafiya lau yabar office, sai daga baya ne gimba ya kira yasanar mana ai baida lafiya, ko sallar juma’a ma da ƙyar in zai iya fita, shinefa nace bara mu sakko massalaci nazo naga jikin nasa, tunda su Hafiz sun fita wani aiki”.
Sosai gabana ya faɗi da jin sunan Boss a zancensu, harda ƙarin furucin rashin lafiya, banji amsar data bama Jabeer ba saboda tunanin dana tafi…….3
Hannuna da aka riƙone ya katse mani tunani, na kalli Ummah data riƙonin nai ƙasa da kai ina faɗin, “Ina yini”. Ummah tace, “Lah kece Auntyna? Aini bamma ganekiba da farko wlhy nama zata Maman Areef ce (Matar Jabeer). “A’a Umma nice” na bata amsa kaina a ƙasa, kafin ta samu damar yimin tambaya Jabeer ya bata amsa da cewar, “A’a Umma ba Fannah bace, Mom ɗinmu ce, da alama ma kin santa kenan?”. Ummah tai murmushi tana zaunar dani a kujerar kusa da ita, tace, “Nasanta Jabiru, ƙawar Nabeelah ce ai, ina ka samo mana ita ne haka? Ko dai ta biyu ce?”. Yanzun kam ƙaramar dariya Jabeer yay yana girgiza kansa, “Wai Ummah ta biyu kuma? A wannan marrar ɗayarma ya aka ƙare, sai dai idan zaki nemarwa ɗanki ne, shine gwauro, wajen aikinmu ɗaya da Mom ɗinmu” ya ƙare maganar idonsa a kaina.
Dariya tayi tana sake riƙo hannuna, cikin sigar tambaya tace, “ɗiyata kina son ɗana?”. Kasa cemata komai nai sai ƙasa dana ƙarayi da kaina, a raina ina faɗin, ‘Ni inada Yah Qaseem ɗina’. Jin bance komaiba ta maida kallonta ga Jabeer,
Cike da mamaki tace, “Waima tsaya Jabiru, kana nufin itama irin aikin naku takeyi?”. “Sosaima kuwa Ummah” ya bata amsa cike da karsashi. Haɓa ta riƙe tana sake damƙe hannuna, “Oh ni ɗiyata, kekuma abinda ya burgeki kenan? To Nabeelah kinji fa jaruman mata, ba irinki matsoraciya ba” Nabeelah da mamaki ya kashe tace, “Wai dan ALLAH da gaske?”. Hararta Jabeer yay yace, “Da gaske mana”. Nabeelah tace, “Tab, wlhy bari Yah Jay ya warke nima ƴar sanda zan zama”. dariya Umma da Jabeer sukai mata, nidai na murmusa ina kallonta da faɗin, “Dakin burge kuwa, kinga ƙawata ta dawo kusa dani”. Da sauri ta cafe da faɗin, “Karki damu ƙawa ina nan tafe, kam Nabeelah ƴar sanda, ashe zan ragargaji ƙattai”.
Jabeer yace, “ko kuma ke su ragargajeki ba”. Ɓata fuska tai da tura baki, “A’a wlhy Yah Jabeer kar kai min baki tun yanzu”.
STORY CONTINUES BELOW

Kafin ya bata amsa Ummah tace, “Kaga Jabiru kubar wannan ba gajiya zataiba, ku shiga yana ciki, amma ban saniba ko idonsa biyu dan Doctor ya saka masa ruwa tun ɗazun”.
Miƙewa mukai muna faɗin ALLAH ya bashi lafiya.
Oga Jabeer na gaba ina biye da shi har cikin ɗakin nasa da ya gama haɗuwa, babu wani datti balle tarkace, nayi zaton zamu sami matarsa a cikin ɗakin, amma sai naga shi kaɗaine kwance a kan gado lulluɓe da farin bargo, hannunsa ɗaya liƙe da ruwan da ake saka masa, ya ɗora ɗayan saman cikinsa, fuskarsa tayi wani irin fayau alamar yaɗan rame. Yauce rana ta farko dana iya masa kallon kai tsaye kuma na tsawon mintuna, ƙyaƙyƙyawane, komai nasa dai-dai da fuskarsa………
“Momcy zauna mana” Oga Jabeer ya faɗa cikin katsemin tunani, kaina na jinjina na zauna saman stool ɗin daya ajiyemin kusa da gadon kaɗan, shi kuma ya zauna a bakin gadon kusa da shi, hannu yakai saman kansa yanason jin yanayin jikin nasa, ni dai ɗauke kaina nai na maida wajen kallon ƙaramin hoton dake drawer gefen gadon, da gani tsohon hotone, ƙyawawan mata da miji da suke a ganiyar shekarun ƙuruciya, sunyi ƙyau sosai da dacewa da juna, ga hoton ya ɗauku duk da bana wannan zamanin bane.
Jawaad ya buɗe ido a hankali saboda hannu da Jabeer ya ɗaura masa a goshi, akan Bilkisu dake saitinsa ya saukesu, ya ɗan lumshe ya sake buɗewa akan nata, sunɗan kumburo sannan sun sake girma, daga ciki sunyi jaa kaɗa alamar dai bayajin daɗi. Jabeer ya kalla kafin ya sake maida idonsa kan Bilkisu, ya kuma janyewa yabi inda yaga idonta na kallo shima, hankalinta nakan kallon hoton Mamansa da Abbansa daya ajiye a bed side drawer, shima Jabeer kallon wajen yayi, amma a mamakinsa sai yaga Jawaad yakai hannu ya juya hoton. Murmushi Jabeer yay yana girgiza kansa.
Hankalina na dawo ganin an juya hoton, nai saurin bin hannun daya juyaɗin da kallo har zuwa fuskar mamallakin hannun, idanunsa a kaina suke, dan haka na janye nawa ina ɗan yamutsa fuska, a raina nace, ‘Baida lafiya ma bazai bar shegen kallon mutane ba’.
Jabeer dake binsu da kallo shidai yay ƴar dariya kawai, kafin yace, “A kacema ka warke mu tashi muje kawai?”. Harara Jawaad ya zuba masa, sai kuma ya miƙa masa hannunsa da aka saka ruwan, yay masa alama da ido akan ya cire masa. Kallon ledar ruwan Jabeer yay, yace, “Ya za’a cire bai ƙareba?, saura kaɗan ai, kaɗan sake haƙuri”. Jawaad da sai yanzune zaiyi magana ya yamutse fuska da motsa laɓɓansa a hankali saboda rashin jin ƙarfin jiki, “To sannu likita, kaga ni ciremin, dama Ummah ce ta takura aka sakan”.
Kafin Oga Jabeer yace wani abu na katsesu da cewar, “Ina yini, ya jiki”. Ban yarda na kallesa ba. hakan yasan bansan a yanda ya amsa minba.
Kallonta Jawaad yay ya janye idanunsa, akan laɓaɓansa yace, “Alhmdllh”.
Sallamar Ummah yasa duk muka kalli ƙofa, tace, “A ya ake cire ruwan bai ƙareba?”. Jabeer yace, “Wlhy Ummah kema ƙya faɗa, cayay a cire wai”. Ummah tace, “Kaci gidanku Jawaad, saurin mikake to? Duk abinka dai bazaka fita aikiba yau, dan a gidannan ma zan yini, dan karna tafi ka saci jiki kace zaka tafi ma agogo sarkin aiki”. Fuska ya ɓata, yace, “Kai Ummah ni nagaji da kwanciyarnan, kumafa naji sauƙi” “Haka mukeso dama ai kasamu sauƙin, amma babu inda zakaje, barama na haɗa maka ruwa kai wanka kaji daɗin jikinka”.
Yanda ya cuskule fuska ni saima yaban dariya, a raina nace ‘duk girman ɗa a gaban uwa shi yarone’ Har Ummah ta nufi haɗa masa ruwan sai naga kamar bai dace ba ina zaune na barta da aiki, miƙewa nai ina faɗin, “Ummah ki barshi bara na haɗa, inane bayin?”. Murmushi Umma tayi tana kallon Bilkisu da yaba hankalinta, tace, “To ɗiyata kuma Yayata nagode kinji, ga shinan shiga”. Kaina na jinjina mata na nufi inda ta nuna mani.
Jabeer da yaji daɗin abinda Bilkisun tayi yay murmushi yana kallon Jay, “Jay wlhy yarinyar nan tanada hankali”. Banza Jawaad yay masa tamkar baijiba. Jabeer yace, “Nasanfa kaji minace”. “Malam ka cikani da surutu, zaka fita a ɗakinan fa” dariya Jabeer ya kwashe da ita, dan shikam dai ransa na bashi abubuwa da dama. Idanun Jawaad dake harar Jabeer tamkar zasu faɗo ya nuna masa hanyar fita. Jabeer yace, “ALLAH babu inda zani, dama kasamu mukazo dubaka, bara na kira su Hafiz nace karma suzo ka warke”.2
STORY CONTINUES BELOW

Koda na shiga toilet ɗin saida na tsaya nagama ƙare masa kallo, ‘Humm’ kawai na iya faɗa, dukda babu wani datti sai naga dacewar fara wankewa kafin na haɗa ruwan, cikin mintuna ƙalilan na gama tsaftace bayin kafin na haɗa masa ruwa mai zafi sosai, a ganina idan yazo bai masa dai-daiba sai ya sake sirkawa, lokacin dana fito iskesa nai zaune a bakin gadon, kayan barcine jikinsa farare, wandon dogo har ƙasa, hakan yasa banji na takuraba, maganar aiki sukeyi yanzunkam, sai dai shi yana dafe da kansa alamar yana masa ciwo ko yay masa nauyi. nace, “An haɗa ruwan”. Jabeer ne kawai yacemin “Sannu da aiki” shiko baima kalleniba ya miƙe ya nufi bayin yana tafiya a hankali.
Bayan shigewarsa Oga Jabeer ya miƙe yana faɗin, “Bara na sayo masa abu na dawo, kiɗan gyara masa ɗakin”. Kaina kawai na ɗaga masa dukda banso hakanba, sai mita nake a raina akan ‘to ina matarsa da ita bazatazo ta gyaraba, ni kofa haɗa ruwan wankanma dan naga Ummah ce zatayi, a matsayinta na babba kuma bai kamata na bartaba bayan ina zaune a wajen’ haka naita mita ina aiki, na gyara gadon tsaf tare da jera filolin a wani style mai ƙyau, nidai kawai nayine saboda inason gyaran gado dama can, balle irin wannan da yaji kayan shinfiɗa na alfarma, ga filos da yawa. Ina cikin gyaran gadon ne Nabeelah ta shigo da kayan shara. Tace, “Lah ƙawata daga zuwa dubiya sai a sakaki aiki? Ummah tace kije ki huta bara na gyara”. Murmushi na mata nace, “A’a ki barsa kawai, ɗakinma ai babu datti”. ƙasa tai da murya tana kallon toilet tace, “Yayanmu ba’ai masa abin arziƙi ai, kaɗan daga aikinsa ya fito ya sakaki wani aikin kuma”. Tabani dariya yanda takeyi tana kallon bayin, nace, “Dama ya fito ya jiki”. Kafin na rufe baki ta fice a ɗakin da gudu tana faɗin, “Saikin fito, dama girki nake masa”. Kaina na girgiza kawai naci gaba da aikin ina jinjina wautarta, gata dai zamuyi sa’anni, amma nakula Nabeelah autace kodan shiriritarta.
Har na gama gyara komai tsaf bai fitoba, na kammala morping tsaf kafin na ɗauka turaren ɗaki dana gani saman ƴar dirowar farkon shigowa ɗakin kala-kala, ɗauka nai nahau fesawa jikin labuloli da saman gado dama ɗakin gaba ɗaya, a bazata naji an buɗe ƙofar bayin, hakanne ya sakani kallon wajen babu shiri, ai kallo ɗaya nai masa na juya da sauri na nufi ƙofar fita ɗakin, gwangwanin freshener ɗin na ajiye na ɗauki bokitin danai morping nai waje abuna.
Jawaad dai yana tsaye a ƙofar bayin yana binta da kallo harta fice, shima baiyi zaton samun kowa a ɗakinba shiyyasa ya fito kansa tsaye, dukda ma dai sanye yake da rigar wanka a jikinsa ba towel ba, cikin rashin jin ƙarfin jiki ya tako zuwa cikin ɗakin, har yanzu mararsa a ƙulle take, dukda dai bakamar jiya da dare ba, da kuma safiyar yau, danma ƙin faɗama Doctor ɗin ainahin abinda ke damunsa yay, cayay kawai zazzaɓine ke damunsa, shi kaɗai yasan yanda yakejin haushin Shahudah da kuma matakin dazai ɗauka a kanta. Idanunsa suka sauka akan gadon da yanda akaima filolin, kasa ɗauke idanunsa yay har na tsahon mintuna kusan biyu, sosai gadon yay masa ƙyau, sai yaga tamkar ba gadonsa ba.2
Tunda na fito Ummah keta faman jeramin sannu, ni dai murmushi kawai nake, na gyara falon saman ma duk da babu datti, falon ƙasa dai Nabeelah na iske ta gyara harma tana morping. Kiran da Umma taimin daga kicin na amsa, ta miƙamin ƙaramin tire data ɗaura kofin tea a kai yanata turiri, “Yauwa ɗiyata dan ALLAH miƙama yayanku wannan ya fara sha kafin wannan uwar shiriritar ta kammala girkin, daga nan sai kiji ko yana buƙatar wani abun kuma”. “To” kawai na iya ce mata na amsa na fito. Koda na fito sai na roƙi Nabeelah tazo ta rakani, catai ALLAH naje ni kaɗai, dan inhar mukaje mu biyu cazai anmasa gayya.
Badan nasoba na nufi saman ni kaɗai, addu’a nake a raina Oga Jabeer yazo mu wuce. Sai da nai knocking ya bani izinin shiga sannan na shiga da sallama, kaina a ƙasa ban yarda na kalli ko inaba sai gabana, saida naje dab da shine sannan na kallesa sau ɗauya na ɗauke idona, har ya saka kaya, baƙin wando da yellow ɗin riga folo, yana zaune ne a bakin gado da waya a hannunsa, hannunsa ɗaya dafe da kansa yanzu ma, nidai na ajiye tiren a gabansa ina faɗin, “Gashi inji Ummah, tace kanason wani abune?”. Banji ya tankaba, bankuma damu da yace ɗinba dama na miƙe zan fita.
“Zonan” ya faɗa a hankali. Dawowa nai ina jan numfashina da ƙyar, dan duk a takure nake, danma zuwa yanzu kamar naɗan fara sabawa da kasancewarmu tare zuciyata ta sassauta min wajen bugun da takeyi idan har muna tare. Nace, “Gani”. Shiru yaymin kamar ba shine yay kiranaba, sai da yaja wasu sakanni kafin ya nunamin dogon table ɗin dake a gaban gadon ta gaba, “Ɗauka waɗancan keys ɗin, kije Gimba ya kaiki station, zaki ɗakkomin abu a office”.
Duk yanda naso daurewa sai da gabana ya faɗi, ta yaya zanje na buɗe office ɗinsa nikam? A matsayin wa? Na shiga uku, mutumin nan nason jefani a matsala shidai na lura……
“Miemaa!” ya faɗa a ɗan tsawace ganin dukma bayanin da yake mata hankalinta baya tare da shi. Firgigit na kawo numfashi tare da kallonsa, yanda ya danƙaramin harara ya sakani saurin duƙar da kaina. “Ina miki magana kina wani banzan tunani”. “Sorry sir” na faɗa da sanyin murya, dan harga ALLAH banji miya faɗaba”. Ƙaramin tsaki yaja, ya miƙomin waya batare da ya ce min komaiba, amsa nai ina jiran ƙarin bayani, amma sai ya shareni yama ɗauki tea ɗinsa ya fara sha.
“Tashimin a kai kafin na canja miki kalar fuskarki”. Fuska na kumbura na juya na fita ina ƙunƙuni a raina.
Jawaad dake binta da harara yay ƙaramin tsaki da faɗin, “Miskilar banza kawai”.10
Banason zuwa ni kaɗai, hakan yasani cema Nabeelah tazo muje ya aikemu, da yake batasan gaskiyar zancenba sai ta bini muka bar Ummah na haɗa masa abinci. A jikin mota muka iske gimba da alamar yasan da tafiyar, zai buɗe mana mota nace ya barsa kawai, murmushi yayi ya shiga mazaunin driver yana tambayarmu “ya jikin boss ɗin” da sauƙi, muka faɗa kusan a tare sannan muka gaidashi.
Tunda muka tafi Nabeelah ke zuba mana surutu, Gimba nata biye mata, nidai murmushi ne nawa idan sunyi wani abun dariyar, har mamaki nake yanda Nabeelah bata gajiya da zance saikace wata akku.
Nidai har Gimba yay fakin addu’a nake ALLAH yasa karna haɗu da Yah Qaseem, gefe kuma ga maganar shiga Office ɗinsa bansan yanda za’a fassarani ba, sauƙinma na taho da Nabeelah ne, tunanin zuwa office ɗin Oga Aliyu ko Hafiz nayi, saisu kaimu office ɗin, a ganina hakan sai yafi, jan Nabeelah nai zuwa Office’s ɗin nasu sai dai munyi rashin sa’a duk a rufe alamar bamasa station ɗin kenan…………….✍
“Team Bil-Qas & Jay-Hud. Saura wani yace sunan baiyiba😏😜😂”
44
Fatan alkairi a gareku baki ɗaya😍😍😘👌🏼
10
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.24
Page 12
………….Babu yanda na iya dole naja hannun Nabeelah muka nufi office ɗin, sai dai tunma a hawan farko aka dakatar da Nabeelah, ni kaɗai aka bari na wuce, kamar na fasa kuka haka naji, sai dai nayi mamaki a raina yanda babu wanda ya tambayeni mizanje yi?.
Office ɗin na nan tsaf, duk da yau ba’a gyaraba tunda baizoba babu wani datti, yau kam ban cuci kainaba saida nagama ƙare masa kallo gabas da yamma kudu da arewa, hatta da hotunan saman tebir ɗinsa sai da na gama kalleso, tsabar jan magana irin tawa na zauna saman kujerarsa ina gwada yanda yake zama, nakai kusan mintuna huɗu ina shirirtata kafin kira ya shigo wayar da ya bani, ƙurama wayar ido nayi tamkar mai tsoron ɗauka har sai da ta kusa katsewa sannan na ɗauka nasa a kunne batare da nayi maganaba. Daga canma shiru anƙi cewa komai harna tsahon sakanni.
“Baki iya sallama bane?” muryarsa ta daki kunnena a bazata, idanu na zaro waje dan wlhy banyi zaton shi bane, nace, “Sorry Sir” bai amsa minba sai cewa da yay, ki buɗe ƙaraman drawer na jikin table akwai faran leda da kwali a ciki ki ciroshi” na amsa da “to”. Ina ƙoƙarin jawo ledan kwalin ya fita a ciki, hakanne ya sani cirosu ɗai-ɗai shi da ledan, haka kawai na tsinci kaina dason karanta abinda aka rubuta a kwalin, dan da alama na magani ne, shaf na manta da wayar a kunne take bai kasheba, na hau karatun rubutun jikin maganin ina faman zaro idanu saboda fahimtar danai maganin na miye. Daga can Jawaad da yaji a jikinsa akwai abinda ta nutsu takeyi wanda ya ɗaura zarginsa akan maganin cikin sanyin murya yay magana saboda cikinsa dake murɗa masa a lokacin, “Bincike kike mini?” a bazata naji maganar tasa, shiyyasa na saki kwalin ƙasa batare dana shirya ba, cikin rawar baki, nace, “A…a’a sir” shiru Jawaad baice komaiba idanunsa a lumshe yana faman cizon lip ɗinsa na ƙasa, sai da ya lafa masa sannan ya sake maida hankali akan wayar, nikam duk a tsorace nake, gani nake tamkar ya gane mi nakeyi, cigaba yay da lissafo min duk abinda yake buƙata, na sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya jin yabar waccan maganar, na ɗauka kwalin maganin na maida a ledar ina cigaba da ɗaukar duk abinda yace, inda kuma ya faɗa anan nake ganinsa, bayan na haɗasu na zuba a wata leda baƙa na fito.+
A ƙasa na iske Nabeelah ta cika tai fam da haushi, taban dariya, hakan yasa na murmusa ina kamo hannunta, ƙwafa tai tace, “ALLAH yayanmun nan ko, saina rama abinda yay min”. Nace, “Miyay miki?” ta sake yin ƙwafa, “Bakiga yasa a hanani shiga office ɗinsa ba, ALLAH nima duk randa na fara aiki bazan bari yazomin office ba”. Yanzunkam kasa jurewa nai saida na dara, “Oh Nabeelah yaushe ya hanaki shiga Office ɗinsa, jami’anmu dai sun hanaki”.
“Kutt wlhy bakisan halinsaba ne, nasan shine yace karsu barni”. Nace, “To kiyi haƙuri, Yaya yayi laifi”. Tunanin zamu dawo yanzu da oga Jabeer yasa ban shiga ko inaba, Mun isa wajen Gimba ya ɗaukemu muka koma, yanzu kam a falon ƙasa muka iskesu harda su Aliyu, mamaki ƙarara na gani a idanun Rose saboda ganina, a tare na gaishesu gaba ɗayansu na ƙarasa gaban sarakin dake kwance a doguwar kujera, cikin girmamawa na ajiye ledan da keys ɗin da wayar a table ɗin dake gabansa nace, “Gashi”. Idanunsa dake rufe ya buɗe ya zubasu a kaina, “Dama tare da Nabeelah na aikeki?” yay maganar yana hararata. Ƙasa nai da idanuna ina girgiza masa kaina alamar a’a. Ƙwafa yay ya ɗauke kansa, ganin hakan yasani barin wajen da nufin bar musu falon ma.
“Waye zai ɗauke miki kayan nan”. juyowa nayi, kafin na ƙaraso wajensa Rose dake zaune a kujerar dake inda ƙafafunsa suke ta miƙe ta ɗauki ledan da cewar, “Ƙyale shashasha boss ina za’a kai?”. Banza yay bai tanka ba, niko na sake juyawa zan fita. “K! Ina wasa dake ko?”. Nazata da Rose ɗin yake hakan yasa nai yunƙuri cigaba da tafiyata Aliyu ya kirani.
“Momi zoki amsa ki kai masa sama kinji”. “To” nace, na dawo na miƙama rose dake ɗauke da ledan hannu alamar ta bani, wata banzar harara ta zubamin ta dangwarar da ledar ƙasa ta koma ta zauna, bance da ita uffanba na ɗauka ledar da keys ɗin na nufi sama, dama duk abinnan da ake tuni Nabeelah ta haye tunda muka shigo ta gaida su Hafiz ta haye abinta.
Bily na gama hayewa Jawaad ya miƙe cikin dauriya ya ɗauki ɗaya daga ruwan da aka ajiyema su Hafiz yabi bayanta yana tafiya a hankali, dan inhar yace zaiyi hanzari dolene a fahimci matsalarsa, ca yay musu yana zuwa. Rose ta bisa da kallo a wani irin yanayi maisa ƙuna a zuciya, a ƙufule ta kalli su Aliyu tana faɗin, “Wai miye haɗin wannan yarinyar da Boss ne?, shishshiginta yayi yawafa” dukansu da mamaki suka kalleta, duk da sun fahimci tsagwaron kishi tattare da zancenta, Jabeer ya kare bakinsa da hannu yana dariya ƙasa-ƙasa, sai da Hafiz ya hararesa sannan ya haɗiye da ƙyar, ya kalli sama sannan ya maido dubansa ga Rose data sake cika fam. “Wai Rose kina nufin sonta yake?”. Da sauri tace, “Itaɗin banza, kaima kasan Boss ya wuce da ajinta, kawai dai itace ke shishshige masa”.
Hafiz yace, “Humm” Aliyu dake murmushi ne ya bata amsa, “Toke tunda kinsan haka miye na damuwar, dan ya sakata aiki sai ya zama wani abu, sau nawa ke ya sakaki ayyuka da sukafi wannan?”. Baki ta taɓe, cikin hausanta da bawani fita yakeba tace, “Amma tunda muke nama taɓa zuwa nan gidan ne? Itako daga gani tana nan tun ɗazun”. Cike da jin haushi Hafiz yace, “To idan ya sakko saiki masa wannan tambayar kuma ai”. Harar Hafiz tayi, dan tun dama can basa shiri, baya shiga sabgarta sai dole, dama sunfi ɗasawa da Jabeer duk cikinsu, Aliyu kuwa baida yawan hayaniya, dan harma yafi Jawaad rashin son magana. Babu wanda ya sake cewa komai, sai Rose daketa kallon hanyar benen tana cika da batsewa da sauke tagwayen ajiyar zuciya.1
STORY CONTINUES BELOW

A sama kuwa koda na isa Nabeelah na bama kayan akan yace takai masa su ɗaki, har Nabeelah ta amsa zata wuce sai gashi ya hawo, hakan yasani saurin riƙo ledan saboda wata uwar harara daya sauke min, Nabeelah ta juyo zatai magana itama ta samu rabonta na harar, sakarmin ledar tayi da sauri tana barin wajen, ni kam dai ƙasa nai da kai kawai.
Duk abinda sukeyi Ummah na zaune tana kallonsu, sai dai tayi kamar batasan sunayiba.
Jawaad ya wuce ɗaki batare da yace komaiba, dan shikuma baima lura da Ummah ba, bayansa nabi gudun karna sake wani laifin. baice dani komaiba harna ajiye ledan nai hanyar fita. Na sauke numfashi ganin na fito lafiya, a raina ina mitar ‘mutum sai baƙar takura’ matarka dai taga banu yasin, a can ƙasan raina kuma tunani nake yanada mata to miya haɗashi da shan magani irin wannan?, nifa dukma sai naji inajin kunyar abun yasin, nikam bazan sake yarda idona ya shiga cikin nashiba, wannan abun kunya har ina haka. Muna a falon Nabeelah na fama dani akan abinci data zubo ya fito, bai kalli kowaba a cikinmu ya sauka ƙasa.1
Ban sakko ba har saida suka tashi tafiya Jabeer ya ƙwalamin kira, lokacin dana ƙaraso duk sun fice daga shi sai Jabeer ɗin, inda yake Jabeer ya nunamin alamar yana kirana, na ƙarasa gabansa dan yanzu ya tashi zaune, batare da ya kalleni ba yace, “Ranar lahadi ƙarfe goma na safe kije ku haɗu da wannan yarinyar, Jabeer zai baki address ɗin wajen”. nidai nace masa to ina jiran ƙarin bayani, sai dai bai sake cewa komaiba, oga Jabeer yace, “muje to, Boss ALLAH ya ƙara sauƙi”. “Amin” ya faɗa akan laɓɓa, nima nace ALLAH ya ƙara sauƙi nai gaba batare da jiran ya amsaba, dan yaban haushi.
Ni da Jabeer a motarsa muka koma, su Aliyu kuwa suna a motar Hafiz da sukazo a ciki, ina kallon yanda Rose keta bina da baƙar harara nai tamkar ban ganiba.
Munzo fita daga layinne naga motar Mom zasu shiga su kuma, nace, “Lah ga mom can”. Jabeer dake tuƙi yace, “Ƙila itama zataje ganin boss ne ko?”. Kallonsa nai nace, “ganinsa kuma? Wai da gaske Ƴan uwansu ne?” dariya yay yana harba motar kan titi, yace, “Momin mu kemafa na kula akwai shiririta wani sa’in, bakiga gidansu ɗaya bane, ai da mom da Abban Jay babansu ɗaya, sannan Jay shine ya auri Shahudah kafin su rabu”.
Mugun waro idanu nayi baki a hangame, nace, “Wai dan ALLAH oga kana nufin dama shine mijin aunty Shahudah?”. Jabeer dake murmushi yace, “Ƙwarai kuwa, ammafa a da kenan, amma ke yaya kuke dasu Shahudah da har bama kisaniba?”. Daƙyar na iya ce masa kamar yanda Mom suke da Abban Boss, nima da Abbansu Aunty Shahudah da Mamana babansu ɗaya”.
Kai Jabeer ya shiga kaɗawa yana faɗin, “Tab cakwakiya kenan, kice shiyyasa Qaseem beson kowa ya raɓu dake? Kodai ƴar gida zamuyi?”. Murmushin yaƙe kawai nai masa bance komaiba, danni gaba ɗaya kaina ya toshe, koda wasa ban taɓa kawo cewar boss mijin aunty Shahudah bane ba, to yama akai na kasa fahimta? Koda yake bai taɓa zuwa gidanba ina nan, bankuma taɓa ganin koda hotonsa ba a gidan, amma kuma inban mantaba nasha jin sunan Jawaad a bakin ƴan gidan, ‘ya salam, miya toshe min kaina haka?’. Har mukaje station wannan tunani ne keta kaikawo tsakanin ƙwanyata da zuciyata batare da nasan ma’anar hakanba, shima kuma oga Jabeer bai sake cemin komaiba saima redio daya kunna.
Koda muka iso office nabi oga Jabeer kamar yanda ya umarceni, ya bani ƙaramar takarda ta address ɗin wajen da boss yace sannan na fito. Na iske su ummie sunata shirin tashi, dan biyar tayi, ALLAH ma ya soni nayi sallar la’asar yanzu da muka koma gidansu boss, nima ɗaukar tarkacena nai muka fito tare, dan Ummie zanbi, na leƙa office ɗin yah Qaseem bayan na fito daga wajen oga Jabeer na iske bayanan ya fita wai. Daurewa nai na cire alaƙar Aunty Shahudah da boss data tsayan a rai ba gaira ba sabar na biyema Ummie mukaita hirarmu, har gida ta kaini, sai dai bata shigaba iyakarta gate na sauka ita kuma ta juya.
Na iske su a falo aunty Shahudah kwance Doctor na saka mata ƙarin ruwa, ba hurumina bane tambayar abinda ya sameta, na gaishesu tare da mata sannu cikin jimami sannan na wuce ɗaki abina. Bansan miyasa na tsinci kaina cikin rashin jin daɗin komaiba, nai wanka na canja kaya, ganinma magrib tayi saina bari nai salla sannan nai zaman yin azkar har aka kira sallar isha’i, itama tashi nai nayi sannan na fito falon dan sake duba Aunty Shahudah, dan banajin yunwa, tun abincin da naci a gidan boss bai sauka ba, duk da saida Nabeelah ma tai fushi sannan naci bayan ummah ta saka baki.
Na iske aunty Shahudah ta koma ɗaki, sai yah Qaseem kawai a dining yana cin abinci, sannu da dawowa nai masa, yay murmushi yana min alamar nazo. Ban musaba naje garesa, naja kujera nima na zauna, “Kinyi ƙyau” ya faɗa yana kashemin ido ɗaya, murmushi kawai nayi bance komaiba. Haka yayta ɗan jana da hira harya kammala, ya miƙe domin zuwa yay wanka, nima miƙewar nai nace bara na sake duba aunty Shahudah naje na kwanta na gaji.
Zaune na isketa Aunty Aamilah na bata magani, na sake mata sannu da ALLAH ya ƙara sauƙi na fito, ɗaki na koma nai kwanciyata duk da nasan gobe idan ALLAH ya kaimu babu aiki, amma inason na kira Dad da safe idan ya bari sai naje gidan Inna Zainabu na gaishesu, da wannan tunanin barci ya kwasheni.
A ɗakin Shahudah kam bayan fitowar Bilkisu Aamilah ce ta sauke ajiyar zuciya tana mai fuskantar ƴar uwar tata da ƙyau. “Sister ga shawara mana” Shahudah da duk tazama kalar tausayi ta jinjina mata kai alamar tana saurarenta. Aamilah ta sake jan numfashi kafin tace, “Ina ganin yarinyar nan Bilkisu zamu iya sakata tai mana wani abu” murya a dasashe Shahudah tace, “Ban ganeba Aamilah “. “Sister ina magana ne akan Brother Jawaad, da nayi tunanin Broth ne a farko, sai dai daga baya nasan bamai yuwuwa bane, musamman idan mukai dubi da yanda basama shiri tun suna yara, sam jinin Qaseem da Jawaad bai haɗuba, bankuma san lokacin dazai haɗunba, so idan mukace zamu ɗorasa akan ya taimaka mana sai dai ya ɓata komai tunda dama can bason aurenku yakeba, yanzu da yarinyar nan ta shigo, sai naga mizai hana mu amfanu da ita, dan kinsan bata da yawan hayaniya da surutu, sannan mutumin dake da irinki bazai kalletaba da sigar birgewa balle akai ga so, ballantana zuciyarmu tayi tunanin ko zata iya cin amanarmu, ko shi yaji wani abu a kanta”. Shahudah datai shiru tana kallon Aamilah tace, “Maganganunki kawai naji Aamilah, amma ban gane ina suka dosaba sam, wane taimko zamu nema akan Bb?”. “Yauwa, yanzu kikai tambaya mai ƙyau Sisi na, inaji a raina Yarinyar zata taimakemu, sai dai bani da tabbacin wajen aikinsu ɗaya, duk da dai naga kullum tare take fita da Broth, kuma Broth da Brother Jawaad wajen aikinsu ɗaya ne, amma wannan ba wani abu bane, zamu iya tambayarta”. Kai kawai Shahudah ta jinjina alamar gamsuwa, Aamilah tace, “ki kwanta ki huta zamu tattauna zuwa da safe, tunda weekend ne tana gida babu inda take zuwa”. Nanma da kai Shahudah ta amsa mata..
★★★★★
Washe gari da safe na tashi nai ƴan ayyukan dazan iya harda kayana da sukai datti, na gyara ɗakina tsaf nai wanka sannan na fito, babu kowa falon dan har lokacin ma bana tunanin wani ya tashi a jama’ar gidan, kicin na nufa na samawa cikina abinci naci, kafin na sake komawa ɗaki na shiga neman Number dad da ya kirani kwanaki uku da suka shige, kusan duk Numbers nashi na ƙetare inada ita, dan yakan kirani lokaci-lokaci idan yay tafiya tamkar yanda yakema sauran ƴaƴansa, bata shigaba, na sake gwadawa har sau uku saina haƙura, bazan iya zuwa ko inaba bayan wajen aiki saida umarninsa, dan banida wani jagora sama da shi a halin yanzu a duniya, sai ko yaya Qaseem da nake fatan ya zama na biyu a matsayin miji. Na aje maganar zuwa gidan Inna zainabu akan sai idan ALLAH ya kaimu gobe, idan naje inda boss yace na gama abinda nakeyi sai na shiga wajen wanke kai daga nan na wuce can koda ban jimaba sai na gaishesu na taho gida, da wannan tunanin na miƙe da nufin zuwa gidansu Amina.
Harna fice babu motsin kowa, muka gaisa da baba mai-gadi na fice abina. Da sallama na shiga gidan, Amina dake a tsakar gida tana wanke-wanke ta amsa tana kumbura fuska, dariya nayi ganin yanda tayi, dan nasan dalili, ta ɗauke kanta da faɗin, “Munyi fushi, ki koma a binki”. Kafin nace wani abu mama tace, “Kwarai kuwa Amina ina bayanki”. Kunnuwana na kama duka biyu na kneeling alamar dai na tuba, dariya suka sanya daga mama har Amina da yayan Amina daya fito da ga bayi, shine yace, “A ni dai na yafe ma ƴar ƙanuwata, nasan aikine ke mata yawa”. Nace, “Yauwa Yayanmu, shiyyasa nake yayinka a koda yaushe”. yay dariya da haɗe yatsun sa babba da manuniya alamar dai-dai👌🏼 kenan.
“Oh, mu baƙya yayinmu kenan? To kin ƙarama kanki laifi har tsallon ƙwaɗo sai kinyi” Amina ta faɗa tana miƙewa ɗauke da kwandon data saka kwanikan. Mama tace, “A’a auta nimafa na huce, ama mai-gadon lu’u-lu’u haƙuri”. Dariya muka saka gaba ɗayanmu saboda furicin mama, Amina tace, “Shikenan na haƙura tunda mama ta saka baki, amma da yau ɗinan saina tsamar da ƙafafunki”. Harararta nai kafin na zauna a inda ta tashi na gaida Mama da Yaya Sule, daga nan muka hau hirarmu.
Wajen sha biyu Amina na tayani tsifar kai muna hira, mama kuma nata ƙoƙarin ɗaura awara da muka tace da Amina bayan munje munkai markaɗe, nace, “Amina!”.
“Na’am” ta amsamin tana leƙo fuskata. Ɗalli namata a fuska da ɗan yatsa, ta matsar da fuskarta tana ɓata fiska saboda zafi, niko na kwashe da dariya, “Ke ɗince kin wani kawomin fuska saikace maison leƙa ramin gwal”. Dariya itama tayi tana ranƙwashina a kai, “Ai bazakici bulusba kuwa”. “ALLAH da zafi” na faɗa ina harararta” tace, “Nima ai naji zafin shiyyasa na rama”. “Ba komai zaki gane shayi ruwane. Maganarnance dai zamu sake”. Shiru tayi kamar bazatace komaiba, tsifar da takemin ma ta koma min ita a hankali, na zungureta da hannu dan nasan ta faɗa kogin tunanin nata. Numfashi ta kawo a hankali, tace, “Ina saurarenki”.
“Amina, a zaman da kikai gidanmu na tsahon wasu shekaru, nasan zakisan halayyar kowa dake cikin gidan nan”. Tace, “Hakane” “Alhmdllh, mizan iya sani akan Qaseem da Salman?”. Shiru tai na wasu sakanni kafin ta sauke numfashi, “Duk abinda kikeson sani zan iya faɗa miki Bilkisu inhar na sanshi, wanda kuma ban sanshiba zance miki ban saniba, kimin tambaya zanfi fahimtar mikike son sani game dasu?”.
Cike da gamsuwar maganarta nace, “Hakane, Qaseem da Salman suna neman mata?”…………….✍
Asha weekend lafiya🤫🤭😉😍👌🏼
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻17
Page 13
……………..Shiru tai na wasu mintuna kafin tace, “Ban taɓa ganinsu da idanunaba a gado ɗaya da mace, amma tabbas Salman yakansha zuwa da ƴammata gidan idan kamar basa nan, ko kuma suna barcinsu na ƙaddara, dan akwai lokacin farkon dawowarsu da yataɓa zuwa da wata yarinyar ƙabila suka kwana a gidan, da safe ta fito zata tafi ALLAH ya haɗasu da Alhaji a bazata, koda ya tambayeta daga ina? Saita faɗa masa Salman ne ya kawota, wlhy a lokacin nazata Alhaji zaiyi kiran Salman yaymasa tatas a gaban yarinyar, ya kuma gargaɗesa sake kawo wata sai kawai naga ya sallami yarinyar ta tafi, shikuma ya shiga mota abinsa ya fita rai a ɓace, dan ko driver hanawa yay ya tuƙasa da kansa yaja mota ranar. Bilkisu bansan miyasa Alhaji keda sakaci wajen tsawatarma yaransa akan abinda ba daidaiba, ya gwammaci ya shanye ɓacin ran a ransa komin zafin da abun yay masa da kuma illarsa garesu da yazauna ya nuna musu kuskurensu, gaskiya ban taɓa ganin wanda yayma boko da rayuwar yahudu ƙazamin ruƙo irin Uncle ɗinkiba, sai dai ina tausaya masa, dan banyi tunanin waɗannan ƴaƴan nasa zasu masa addu’a ba a lokacin da ƙasa ta rufe idanunsa, sai dai dayake UBANGIJI gafurunne kuma rahimun ba’a shigar masa al’amari, ikonsane ya canjasu kosu ƙare rayuwarsu a haguggunce kamar yanda suka tashi. Qaseem kam dai bazance na taɓa ganin ya kawo mace gidan nanba, sai dai nakanji yana waya, dan kusan sau uku ko biyu inajin yana waya da ambatar sunan hotel, ba sunan hotel daya shigo ciki bane kawai yasa nai tunanin hakan, sunan mata dakan shigo a zancen nasa da salon yanda yake wayarne kawai dai ya ɗarsa mani haka. Sai kuma faɗa da naji wataran Hajiya na masa akan batun aure, take cewa ya zauna yanata shashanci a waje sai ya gama tsufa baiyi aureba, idan soyake wata ta haifa mata jika a waje sai ya bada himma. Kinga a zancenta yana nuna kenan yana yin abinda bai daceba ta kamashi ko aka kawo mata labari. Sai dai shima babu tabbas, tunda ba ido da ido nidai na gansaba. Abu na biyu kuma Qaseem baya shaye-shaye, baida wulaƙanci tamkar Hajiya, dan baya shiga huruminka sai idan kaine ka saka kanka a ciki ko wani dalili ya haɗaku, da wahala kiga yana hantarar masu aiki sai idan sun ƙuresa gaskiya, shiyyasa lokacin da kikazo gidan naga yanata biyema su Hajiya akan abinda suke miki nata mamaki, dan nasan ba halinsa bane, sai daga baya na fahimci soyayyace yake miki batare da shima ya saniba, shiyyasa baya iya yin shiru akan al’amarinki. Salman yana shaye-shaye, dan ɗakinsa ma zaki gansu zube baya shakka balle shayin kowa, sannan ɗan wulaƙancine dason yanƙwana mutum, sai dai shi kuma akwai ƙyauta, dan bashi da rowa, akwai kuma tausayi idan ƴan mutuncin na kansa bai cake ba, dan wani rashin mutuncin nasa abinda yake sha ne ke azashi bisa hanyar aikatawa. Haka rayuwa take, duk inda kika samu mutum da mugun hali zaki samesa da ƙyaƙyƙyawa kuma”.
“Hakane kam Amina” na faɗa ina sake juya maganganunta a cikin raina.2
Tunda na dawo gida maganganun Amina ne kawai keta kai kawo a raina, na idar da sallar la’asar ina cikin naɗe abin sallar Aunty Shahudah ta shigo, sosai nayi mamakin ganinta harma fuskata ta kasa ɓoyewa, dan tunda aka bani ɗakinta bata sake shigowaba, hasalima a wancan lokacin catai ƙyanƙyami kayan ciki take tunda na taɓasu.
Sai da ta gama ƙarema ɗakin kallo sannan ta zauna a bakin gado, fuskarta wasai babu alamin turɓune wa kamar yanda takeyi da, sannan babu kallon banza balle hantara.
“Oh, sai kallona kike tamkar kin samu tv Bilkisu”. Murmushin da ban shiryaba nayi, dan inaga yaune karan farko dana fara jin sunana a bakinta, nace, “Aunty Shahudah ai mamakin shigowarki nan nake, nasan dai…..” sai kuma nai shiru ban ƙarisa ba. Batace komaiba sai gefenta data nunamin da hannu alamar na zauna. Nima ban musaba na zauna ɗin inata ƙara mamakinta dai. Cikin katsemin tunani tace,
“Bilkisu aiki nazo kimin, konawa kike buƙata zan biyaki”. Kallonta nai da mamaki, sai kuma na girgiza kaina, “Aunty Shahudah ni yanzu dan zaki sakani abu har sai kin biyani? Bana buƙatar ki dinga kallon haka tsakanina dake, ki sakani kominene kike da buƙata a matsayinki na wacce take sama dani kuma nake ƙanwarki, nikuma nai miki alƙawarin inhar baifi ƙarfin himmata ba zan yimiki shi”. Tai guntun murmushin da ke ƙarama ƙyaƙyƙyawar fuskarta ƙyau tana jinjina kai, Tace, “Bansan haka kike da kirkiba ai, amma duk da haka zan biyaki, domin aikin ya cancanci hakan”.
“Humm” kawai nace mata.
Ta sake muskuta zamanta da cewar, “Waje ɗaya kuke aiki da Broth ko?”. Nasan Yah Qaseem suke cema haka, dan haka nace mata “Eh”. Tace, “Yauwa, a Station ɗinku, akwai wanda nakeson kimin aikin a kansa, sunansa Jawaad, bai zama lallai ki sanshiba, dan shi mutumne da baya shiga kowane tarkace, yanzu ɗinma sai munyi shawara da dogon nazarin da har zaki iya samun kusancin taimakon nawa a wajenshi, dan nasan bazai kulaki ba kai tsaye”. Ta ɗanso bani dariya a maganganunta, amma sai na danne banyiba, dan nima nasan gaskiya dukta faɗa akan halayyar Boss, to amma yanda take faɗan magana a habaice kuma tanason na mata aikine ya saka abin son bani dariya. Tace, “Abinda yasa na zaɓeki a aikin nan saboda, baki da surutu, sannan kin iya hausa sosai, zaki fimu sanin hanyoyin da zaki fahimtar dashi ya fahimta saboda shi mayen son yaren hausane”. Yanzunkam kasa daurewa nai sai da na murmusa, banda shirme irin nata dasu da suka ɗauki yaren wani wata tsiya, ai sai sakarai ke ƙin yarensa.
“Tom aunty Shahudah, yanzu mikikeso nayi ni?”. Jim tayi alamar tunani akan abinda ke’a ranta, sai kuma zuwa can ta sauke numfashi, “Zan ringa baki saƙo kina kai masa kulum, wannan shine kawai aikinki, idan kuma ya tambayi wani abu game dani, sai kisan yanda zaki tsarashi da manya-manyan hausarnan naku. Amma dai Aamilah zata sake miki bayani yanda zaki fahimta, danni harma narasa yanda zaki sake ƙara fahimtata”.
“Karki damu Aunty, ko a yanzunma na fahimceki, matsalar kawai shine yanda zan samu kusancin dashi, da har zan sako masa babbar magana data shafi rayuwarsa ne, dan kinga wannan babbar maganace data kasance sirrinsa da ya shafesa ba zancen aikiba, amma namiki alƙawarin zan gwada ta wasu hanyoyi, saiki dage da addu’a kuma”.
“Okey, zuwa anjima zamu fita ni da Aamilah, zamu sayo abinda zakije masa dashi ranar Monday”. Na jinjina mata kaina kawai, dan bansan miyasa take bani tausayiba yanzu, na kula tana sonshi sosai, to ai Boss ya cancanci a soshi, sannan ita kanta ina mamakin yanda ya iya sakaci da wannan ƙyaƙyƙyawar halittar, ba namiji irinsaba hatta dani mace aunty Shahudah na birgeni, tana cikin mata ƙyawawa ajin farko da ba cikin baƙaƙeba kosu kansu fararen ta shiga cikinsu saisun yabata, sun dace sosai matsayin ma’aurata ita da Boss, ‘sai dai nikam ta yaya zan tunkaresa da maganar nan?’.7
STORY CONTINUES BELOW

JAWAAD
Tun sanda yasha maganin sai ya dinga samun nutsuwa a hankali harya farajin ɗan ƙarfi bayan tafiyarsu bilkisu, sai kuma yaƙi da zuciya, sosai maganin na masa aiki, amma yasan wataran zai daina tamkar yanda na bayama sukai yayi suka shuɗe, ko abokinsa Doctor Sooraj ɗin da ya bashi shawarar amfani da wannan maganin ya tabbatar masa na wani ɗan lokacine kawai, babbar mafita shine yay aure, inba hakaba ƙwayoyin da yakesha domin kare kansa daga faɗawa halakar da yake gudu to lallai zasu iya masa illa ma wataran, tunda har ALLAH ya bashi lafiya da muhalli, dukiyar aure mi yakema zaman jira? Idan matarsa yakeso ya dawo da ita mana yabar cutar kansa. A lokacin da Dr Sooraj kema Jay wannan maganar ƙin ce masa uffan yay, daga ƙarshema sai yay masa sallama ya baro office ɗin.
Da daddare bayan tafiyar su Ummah gida ya samu kira daga Uncle Nasir, duk da bayajin ƙwarin jikinsa haka ya tashi ya fita bayan ya saka dogon wando a jikinsa, dan harma ya riga yay shirin barci shi. Kansa tsaye falon Uncle Nasir ya nufa, bayan yay sallama aka bashi izinin shiga sannan ya shiga, Uncle Nasir na zaune shida matarsa suna hira da kallon labarai, ya gaishesu da girmamawa. Duk fuskokinsu ɗauke da fara’a suka amsa masa, Uncle Nasir yace ya taso susha Fruit salad ɗin da yake sha, Jawaad ya amsa da, “Alhmdllh Uncle na ƙoshi”.
“Aiko saika shashi” cewar Hajiya Sumayya matar Uncle Nasir, ta cigaba da faɗin, “kai yanzu Jawaad kenan ka girmi cin abincin kowa a gidan nan?, tunda kai aure shikenan, da ai ba haka kakeyiba, mu yanzu ka yayemu daga iyayenka kenan?, inaga ko shayin wajenan rabon daka shashi tun daren ɗaurin aurenka da Shahudah, to ni dai yanzu kamar yanda na saba a baya kullum zan zubo abinci na aiko dashi sashenka, idan kaso kaita jerenshi kamar ɗakin amarya”.
Murmushi yayi tare da kai hannu ya shafi kansa, yace, “Nayi laifi Ammi, amma ayi haƙuri, kinsan yanayin aikinmune yasa, wani lokacin bana shigowa da wuri, kuma ina fita da wuri, amma daga yanzun indai na dawo da wuri zanyi magana a kawo mani”. “To yanzu naji magana, bara na zuba maka fruit salad ɗin”.
Uncle Nasir dake saurarensu yace, “
Ke nama lura sake ɗaure masa ƙugun zama babu aure kikeyi, yanzu ba zancen adinga kai masa abinci nai zamanyi ba, zancen wadda zata dinga dafa masa kamar kowane magidanci zanyi”. Tace, “Ah Alhaji indai nan ne aini ina bayanka, ga ƙannensa nan su Abdur-rahman za’ai musu haihuwa ta bibbiyu, shiko ya zauna ruwan ido kamar wanda bai ɗanɗana auren yajiba”.
“Barsa, ai na shirya maganinsa wannan karon, idan har bai shiryaba ni a shirye nake na zaɓi ɗaya daga yaran gidanan na aura masa”. Da sauri Jay ya kalli kawun nasa harda waro idanu. “Kalleni da ƙyau fa, ALLAH inhar baka yunƙuro a cikin shekararnan ba, a yaran gidanan zan aura maka, karkuma ka ɗauka maganar wasa nake maka, gobema insha ALLAH zanje na sami Alhaji babah muyi magana (Kakansa mahaifin Mamansa), idan kuma matarka kakeso ka dawo da ita”. Shiru Jawaad yayi baice komaiba har Uncle Nasir ya gama masa faɗa sannan ya bashi haƙuri akan insha ALLAH zaiyi abinda sukeso, amma su ƙara masa lokaci.
Uncle Nasir yace, “Ba damuwa, ALLAH ya kawo mafita, amma ranar lahadi idan ALLAH ya kaimu akwai meeting da za’ai ƙarfe huɗu, sai kai ƙoƙari ka halarta, karka bari ayi kuka da kai kamar ko yaushe dan ALLAH”.
“Insha ALLAHU Uncle zan kiyaye”.
Ya daɗe a sashen suna hira dan sai kusan ƙarfe ɗaya ya koma sashensa, kasancewar yasha barcin rana sai bai iya yin na darenba da wuri, lap-top ya buɗe ya shiga wasu ayyukan, sai wajen biyu da rabi ya rufe ya tashi, alwala yayo yay nafilfili tare da jero doguwar addu’a akan mahaifinsa da mahaifiyarsa, dama sauran al’umma baki ɗaya.
Sakamakon rashin kwanciya da wuri ya sashi makara sallar asuba, ya tashi a gaggauce ya nufi toilet ya ɗauro alwala, bayan ya gabatar da salla yay wanka ya gyara gadonsa sanan yay shirin fita, Gimba ya tafi gida weekend, dan haka shi da kansa yaja motarsa sai ƙaton gidan gonarsa da ya gada wajen mahaifinsa dake can asalin ƙauyen kakansa Alhaji Yusif, inda sukai rayuwa da kakarsa mama maryam, garin kuma da mahaifinsa yay rayuwar ƙuruciya harma data girma. Sosai an samu cigaba da abubuwa masu dama a cikin ƙauyen wanda duk sanadin mahaifinsane, an musu titi, an kuma kai musu wuta, ga dam ɗinsu da har yanzu suke noman rani, dan garin yana ɗaya daga cikin manyan garuruwan da ake amfanuwa da nomansu da kiwo a jihar tasu dama maƙwaftanta baki ɗaya. Alkairin mahaifinsa da shi kansa wanda yakeyi yasa a kullum yake mai daraja a wajensu, idan yaje ji suke tamkar su haɗiyeshi, saika rantse wani sarakine.
Kamar yanda ya saba gidan mai gari ya sauka, dan haka ya keyi a duk lokacin da yaje ƙauyen, hakan na ƙara masa daraja da kwarjini, kamar yanda shima yakejin daɗin abinda suke masa ɗin, dan maigari yana masa abu tamkar uba, kasancewarsa abokine ga mahaifinsa Abdul-aziz tunna ƙuruciya. Ya samu tarba kuwa ta mutuntawa, inda akaita haba-haba dashi da abincin gargajiya masu tsafta kamar yaune aka fara ganinsa matsayin baƙo. Sam Jawaad bashi da girman kan zaɓar cima ko raina cimar ƙauye, hasalima suna masa saɗi fiye dana zamani, idan har yaje ƙauyen nan komi suka bashi cin abinsa yake, saboda yanada yaƙini akan tsaftar iyalan baba maigari, tun yana ƙanƙanin yaro mahaifinsa ke zuwa dashi, hakama mama maryam na kawosa kafin ta rasu, hankalinsa kwance yaci ya ƙoshi, dan dama da yunwarsa yazo, bayan sun gaisa da baba maigari da jama’ar dake fada suka nufi gidan gona shi da Abbati ɗan baba maigarin da zasuyi sa’anni da Jawaad, dan abokinsane na amana, dukkan sirrin gidan gonarsa yana hannun Abbati, shike kula da komai, Abbati dukda yayi karatu har matakin degree na biyu yana zaune ne anan ƙauyen tare da iyayensa, iyakarsa yaje birni wajen aiki ya dawo garinsu ya kwanta, matarsa ɗaya da ƴaƴa huɗu, yayi ɗan gininsa na zamani saboda ƙauyen yanzu yanada dukkan cigaban da ake hangensa a birnin, kuma mafi yawansu sunada aƙidar son zaman gida sai dai waɗanda aiki ya tilastama komawa birnin akan dole, dan a dalilin Abdul-aziz mahaifin Jawaad ƙauyen yanada manyan ƴan boko matasa masu jini a jika dake taka rawar gani sosai a sassan ƙasar.
Suna tafe suna hirarsu cikin nishaɗi, inda Abbati keta kiran sauran abokansu dake gida ta waya yana sanar musu Jawaad yazo. Jawaad ya fige wayar yana hararar Abbati, “Malam ya isheka haka, sai gayyatomin ƴan iskannan kake salon kuzo ku addabeni da surutu mara ma’ana”. Abbati ya kwashe da dariya, “Oh ashe kana tsoron surutun namu? Ai indai kaga munbar maka surutu kuwa sai kayi abinda mukeso, ka dubemu daga mai yara uku sai masu huɗu amma kai ka zauna ruwan ido Jay, ai kosu Jabeer da kuke tare a birni sunada iyalansu, wai kodai da kurwanka Shahudah ta tafine bani labari kafin su Isa su zo”.
Kafin Jay yay magana sukaji ance, “Ai gamu mun iso”. Daƙƙuwa Jay ya watsama abokan nasa huɗu da suka iso wajen yanzu-yanzu, waɗanda suma duk sunyi karatu kowa da abin yinsa, kuma suna bada gudunmawa a gidan gonarsa suma. “Duk kunci ƙaniyarku zomayen banza, uwarwa ya gayyatoku nan?”.
Dariya suka sanya baki ɗaya, Labaran ya dunƙule hannu ya bigi damtsen hannun Jawaad yana faɗin, “Bar wani mazurai gaye, munfika ƙarfi fa inma hayaƙin kakeji, dan mu kullum matanmu ƙara mana sukeyi” duka shima Jawaad ya kai masa, Labaran yay saurin duƙewa. “Ɗan iska da ka tsaya naima fuskarka damage sai naga ƙarfin da Asiyan ke baka, mara mutunci”. Dariya suka sanya su dukansu, Aminu yace, “Mudai mun gaji da ganinka haka ALLAH kuwa”. “Gaskiyane Aminu, ya kamata ka duba Jay” cewar isa. “Hakane kam lokaci baya jira fa, kullum girma muke ƙarawa ƙuruciyarmu na guduwa” cewar Salisu dake dafe da kafaɗar Jawaad. Murmushi kawai Jawaad yayi, yasan halin abokan nasa, tunkan yay auren farkoma haka sukaita addabarsa, sai da akai bikinsa da shahudane suka sama masa lafiya, yanzunma ko waya yake dasu faɗansu kenan, shi kansa ba auren bane bayaso, gidan jiya yake tsoron komawa…….. Adam ya katse masa tunani da cewar, “Idan kuma a birnin babu wadda tai maka ka duba a garin nan mana, auren nan shine cikar martabar mutum”. Abbati yace, “Maganarku nakan hanya ƴan uwa, ko ɓato maka rai akai daga waje kana shigowa gida kaga iyalanka sai kaji ka huce, musamman idan kayi dace da macen datasan yanda zata tattali dukkanin farin cikinka, koda gajiyarka ka kwaso kanada inda za’a nuna tausayinka a sauke maka ita da kulawa”. Jawaad ya shafa kansa yana sauke numfashi da girgiza kai, “Kudai baku da magana saita aure dai jarababbu, ko hutawa bakwayi, karku damu zanyi, kumin addu’a kudai. a tare suka shiga masa addu’ar kuwa kafin su fara bashi hannu suna gaisuwa.
Jawaad nason abokansa na ƙauyensu, dan suna bashi nishaɗi da faɗa masa gaskiya komai ɗacinta, shiyyasa ko kansa ɗaukar zafi yay a wajen aiki tuni yake ƙoƙarin ware weekend ɗin da zai shigo, dan yasan zai samu nutsuwa sosai…………..✍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.3
★