KWAI CIKIN KAYA CHAPTER B
BOOK2
Page 22
……………“Bazai yuwuba, Ka gaggauta fita!! Ka gaggauta fita!!!” na jiyo wata murya mai amo sama-sama tana amsa kuwwa a cikin ɗakin lokacin da numfashin ke gab da barin gangar jikina. Daga haka ban sake fahimtar komaiba dake a cikin duniya sai wayar gari nai na ganni kwance a ɗakin Momy.
A hankali na shiga buɗe idanuna da sukaimin nauyi, na shiga bin ɗakin da kallo daki-daki, dan bamma fahimci inda nakeba da farko saboda zan iya irga shigowata ɗakin Momy a tsawon zama gidan, da ƙyar na tashi zaune ina sake mamakin abinda ya kawo ni nan ɗin, hakan yayi dai-dai da shigowar Momy ɗakin.
“Yauwa kin tashi Bilkisu?”. Kaina na ɗaga mata a hankali, saboda jikina yaymin wani masifar nauyo, na buɗe baki da ƙyar nace, “Momy miya faru na ganni anan?”. Hankalinta nakan ciro abu a cikin drawer ta bani amsa, “Za’a gaya miki daga baya, tashi kije ɗakinki kiyi wanka”. Da “to” kawai na amsa mata na sauka jikina duk yana wani masifar ciwo, ga tunani fal raina, wani abin mamakinma na sake tararwa a folon ƙasa, dan kuwa cike yake da dangin Momy, na gaisar da waɗanda zasu iya jina na wuce ɗaki kaina na kuma ɗaurewa. Akan gadona dake mugun yamutse na fara sauke ido, ‘Kowaye yay masa haka kuma?’ na ayyana a cikin raina, dukda banajin daɗin jikin sai nai tunani bara na fara share ɗakin, gadon na shiga kakkaɓewa, ƙarar faɗuwar abu naji kamar ƙwandala a ƙasa lokacin dana ɗaga zanin gadon, dube-dube na fara, sai dai banga komaiba, sharewa nai kawai na gyarashi tsaf, nakoma shara. A wajen shararne na sharo abinda ya faɗi ɗazun ashe wajen gado ya shige, Wuri ne kalar ja, sai dai wannan yafi wurin dana sani girma, haka kawai na samu kaina daƙin maidashi a sharar, saima na jefashi cikin jikkar islamiyya ta dake kusa dani, na cigaba da sharata. Da ƙyar na kammala aikin na lallaɓa bayi nai wanka, ganin baƙona ya tafi saina haɗa da wankan tsarki. Ina shiri ina mamakin barcin danai daga daren jiya zuwa safiyar yau ace bamma farkaba kamar yanda na saba a lokacin sallar asubahi dukda bana salla, yanzu hakafa sha biyu ma, ni saima yanzu maganar zuwa aiki tazomin a rai, gaba ɗaya wani iri nakejin kaina
tamkar birkitacciya, wayata na shiga dubawa, sai dai kuma ban gantaba, ƙarasa shirin nai da tunanin naje ɗakin Momy na duba ko tana can idan na gama. Sallamar Momyn ce ta kacemin tunani na juya ina kallonta. taci kwalliya cikin rantsatstsen lase ɗan ubansu sai walƙiya yake, ga gwalagwalai ta zuba a wuya da hannu, taimin murmushi irin wanda tsahon zamana da ita ban taɓa cin karo da shiba sai yau, “Bilkisu irin wannan kallo haka” kunya naɗanji, dan haka na murmusa ina mai duƙar da kaina, nace, “Kinyi ƙyaune Momy”. “To nagode sosai” tafaɗa tana zama a bakin gadona da ajiye ledan data shigo dashi a hannu. takai dubanta gareni, “Kinga cire waɗannan kayan waɗanan zaki saka, nasan akwai tambayoyi fal ranki, karki damu zamu baki dukkan amsoshinsu zuwa dare idan baƙi sun tafi, fatanmu dai kizama maiyin biyayya a garemu kamar yanda kika saba, batun zuwa aiki kuma yau bazaki jeba”. Shiru nai kawai ina kallonta, sai kuma nace mata, “To momy, wayata fa?”. Miƙamin tayi tana faɗin “kin ganta nan, dama anata kirankima kuwa tun ɗazun”. Amsa nayi, itakuma ta miƙe ta fita. Da kallo na bita kaina na sake ɗaurewa da abubuwan da ban saba ganinsuba sai a mafarki, ganin ta ɓacema ganina saina sauke nannauyar ajiyar zuciya, wayar na duba, miss calls kam da yawa harma bansan dawa zan faraba, Yah Qaseem, Ummie, Amina, harma da Numbers ɗin da bansan na wanene ba, kafin nayi wani yunƙuri kira ya shigo, sunan Masarauta danai saving ne ya fito ɓaro-ɓaro a jiki, ɗagawa nai muka gaisa a mutunce kamar ranar, daga ƙarshe take sanarmin bayan an sakko massalaci zasuzo kawomin cards ɗina, murmushi nayi ina mata godiya, kafin mu yanke wayar. tunanin yaya zanyi na shigayi, dan yakamata ace koba komai nai musu tarba ta girmamawa ko badan gidan da suka fitoba, to amma yanda gidannan ke cike ta ina zanma fara nikam? Wlhy gaba ɗaya yau kaina ya ɗauki zafi, sam tunanina baya tafiya dai-dai dana sauran mutane. Kasa yin komai daya dace nayi, nai zaune a inda Momy ta barni, niban canja kayan datace ba, bankuma miƙe na nemawa baƙin abinda zasuciba idan sunzo balle kuma cikina dake Masifaffen ƙugin yunwa kamar zanci babu. Ina a wajen har ƙarfe ɗaya ta buga, tashi nai jiki a sanyaye na ɗauro alwala, gabana sai wata iriyar muguwar faɗuwa yake wadda ban taɓa jiba, idan girata ta haggu ta harba sai ta dama ma ta harba, sai kuma inji wata faɗuwar gaba ta biyo bayansu. Haka nai sallar azuhur batare dana fahimci abinda nama karanta a sallarba, dan wasu irin mugayen halittu na rinƙa gani suna zuwa gabana, haka dai na dake raina na cigaba da sallar inata faman kwarar da zufa tamkar wadda take a cikin ruwan zafi, a sujidar ƙarshema sai naji wata iriyar muguwar dariya a ɗakin tamkar za’a fasashi, sai kuma aka fashe da kuka, zuwa can aka kuma saka dariyar datafi ta farko. Na kasa ɗagowa daga sujidar ma gaba ɗaya tsahon lokaci, saida naji an taɓani ne a baya da magana kamar muryar Ummie sannan ALLAH ya bani ikon ɗagowa. Shiru naji ɗakin ya ɗauka sannan bana ganin komai a gabana harna kammala na shafa addu’a. Na sauke idanuna akan Ummie dake zaune da a bakin gadona tana latsa waya, sai dai na kasa cemata komai saboda wani irin yanayi da nakejin kaina mai masifar tashin hankali, jina nake tamkar ana kunnamin garwashin wuta a jiki……..
“Bily! Bilyy!!” na tsinkayi muryar Ummie na faɗa tana girgizani. Kallonta nai na amsa da ƙyar, dan bansanma tazo kainaba, bana gane komai a yanzu bana kuma fahimtar komai hatta da kaina neman suɓucemin ya keyi. Tace, “Na shiga uku, Bilkisu lafiya kike kuwa? Wai mike faruwane haka?”. “Ban saniba nima Ummie” nai maganar hawaye na ziraromin akan kumatu. Kafin ta samu damar jehomin wata tambayar muka jiyo matsananciyar hayaniya ta kaure illahirin gidan tamkar ana faɗa. Mu duka kallon ƙofa mukai, hakan yay dai-dai da bugo ƙofar da aunty Shahudah tai hannunta ɗauke da wuƙa tana kuka.
A tare muka miƙe da Ummie, dan lokaci ɗaya wani ƙarfi yazomin da bansan daga inaba kuma, ganin kaina tayo da wuƙar saina zaro idanu waje ina faɗin, “Au…aunt…aunty Shahudah lafiya? kuw….” bankai ga ƙarasawaba ta kawomin suka tana faɗin, “Wlhy kasheki zanyi, tsinanniya jinin asara jinin masifa, jinin tsafi….” wani mugun tsalle nai na kauce mata, amma dukda haka saida taɗan yankeni a damtsen hannuna. Ɗakin ya cika sai ƙoƙarin janyeta ake tana ihu da tabbacin yaufa ita saita halakani.
Bansan hawaba bansan saukaba kawai naji aunty Aamilah da wasu ƴammata sun rufeni da duka sukuma, tun ina ƙoƙarin kare kaina harna gaza dan sunfini yawa, gashi kuma bayan Ummie babu mai yunƙurin karɓata.16
STORY CONTINUES BELOW

Tun Bilkisu na fahimtar abinda ke faruwa harta sume, amma idanunsu ya rufe bama su fahimci bata numfashiba, haka suka jawota ƙiyyy!! waje har tsakar gida suna duka, abinda zai baka mamaki babu wanda ya hanasu acikin manyan iyaye irinsu Momy, suma kansu ruɗanin abinda yazo musu babu zato baisa sun kula da abin ƴaƴansu sukeba na yunƙurin kisan kai, Ummie ce kawai ke kuka da Amina da mama da suka shigo gidan saboda jin matsananciyar hayaniyar dake tashi.
Shahudah kuwa tun tana kuka da iƙirarin kashe Bilkisu har itama ta yanke jiki ta faɗi ƙasa babu numfashi, nanfa gidan ya kuma harmutsewa, babu mai iya fahimtar yaren wani balle ka samu tabbacin abinda ke faruwa dahar ya kawo wannan tashin hankalin.1
________________________________
Abinda ya faru shine, a daren jiya su Mom sun dawo misalin ƙarfe sha ɗaya da wasu mintuna sai sukaci karo da wani irin ihu maiban tashin hankali da saka firgici a gidan, babu wanda bai tsoraba a cikinsu dan Aamilah harda fitsari ta jiƙe jikinta, sai bayan wasu mintuna komai ya lafa sannan suka fahimci daga ɗakin Bily wannan ƙara ta fito, sai dai a cikinsu babu wanda ya iya jarumtar shiga ɗakin. Mom ce ta ɗaga waya ta kira Dad hankalinta a tashe ta sanar masa komai, shima hankalin nasa a tashe ya tabbatar mata gashinan zuwa gidan dama ya fita rakkiyar su Alhaji baba ne da sukazo.
Duk wannan ihu yau Yah Qaseem bai jisaba sam, yana ɗakinsa yana barci, saida Shahudah taje ta tasoshi bisa umarnin Momy. Kafin isowar Dad Yah Qaseem ne ya fara shiga ɗakin, sai ya tadda bily a sume, ga ɗaki a hargitse tamkar anyi sukuwar salla a cikinsa. Babu wanda abun bai taɓa zuciyarsaba a gidan har Dad daya iso yanzun, sun shiga yayyafama Bilkisu ruwa amma ko motsi bataiba. sunkuma bi duk wasu dabaru shima bata farfaɗoba, hakan yasa Dad bada shawarar a maidata ɗakin Mom ta kwana a can, shikuma zuwa safiya zai ɗauki mataki akan wannan abun dake faruwa.
Daga Aamilah har Shahudah suma a ɗakin Mom suka kwana, da ita kanta Mom ɗin harma da Dad kansa saboda a firgice suke yaran da Mom. Har ALLAH ya wayi gari lafiya Bily kam bata dawo hayyacintaba sai kusan ƙarfe sha ɗaya da wasu mintuna ko nace sha biyu saura na rana.1
Abinda ya farunne ya saka Dad yanke shawarar ɗaura auren Bily da Qaseem a wannan safiya ta juma’a dan kowa ya huta duk da basusan ainahin abindama ake bibiyar Bilkisu da shiba, ɗari bisa ɗari Mom ta bashi goyon baya. Ana idar da sallar asuba Dad ya nufi gidan Alhaji baba ya sanar masa halin da ake ciki tare da neman alfarmar haɗawa dana Shahudah da Jawaad, zuwa bayan salla idan ALLAH ya kaimu a cewar Dad sai ayi biki su tare. Alhaji baba bai musaba, dan yana fatan jikan nasa matsalarsa ta zama babu aure tazo ƙarshe. Daga gidan Alhaji baba gidansu Jawaad Dad ya wuce, a canma sun tattauna dasu Uncle Nasir kafin ai kiran Jawaad dake shirin tafiya Office.
Koda suka sanar masa shirinsu shima babu musu ya amsa musu, harma amincewar tasa da gaggawa ya basu ɗunbin mamaki, amma shi saiya fuske abinsa tamkar baiga mamakin nasuba sam ko bai fahimtaba, ya kuma fiddo kuɗin sadaki a take ya direma Uncle Nasir har dubu ɗari biyar. Kasa haƙuri kam sukai saida suka tanka akan hakan, batare daya kallesuba yace ai Alhaji baba ne ya kirasa ya sanar masa kafin su sukirashi, cikin gamsuwa da maganarsa Dad yace to ya rage kuɗin sunyi yawa, dubu ɗari sun isa. Murmushi Jay yayi yana wani susar ƙeya, kansa a ƙasa yace, “Karka damu Dad nariga na fidda kuɗin matsayin sadakin, Uncle kuje dasu wajen ɗaurin auren kawai please. Albarka suka saka masa tare da sallamarsa, yay musu sallama ya tafi fuskarsa ɗauke da wani shegen murmushi daya tsayama Uncle Nasir da Dad a ƙahon zukata. Dad ya dawo gida, yayinda Jay yanufi office ya nema alfarma tare da gayama Sir Ahmad abinda ake ciki. Sannan ya sanarma su Hafiz ma, sunyi matuƙar mamaki, amma ganinsa a wani yanayin da suka kasa yima fassara sai basuja zancen da nisaba suka shiga faɗama mutanensu nanan office da waɗanda suke kusa irinsu Abbati ta waya.
Maza nata haramar tafiya massallaci, inda daga canne za’a ɗauro auren bayan idar da sallar juma’a, yayinda ahalin gidansu Momy keta tururuwar zuwa gidan harma da tsiraru na ɓangarensu Dad kamar su inna Zainabu. Duk wannan abunda ke faruwa babu sanin bily, tanacan tanata barci abinta.
Massallaci ya cika tab da al’ummar musulmi yara da manya da matasa da tsoffi harma da mata dakanje sallar juma’a kasancewar wannan ranar ranace ta musamman a garemu, bayan an idar da sallar juma’a kamar yanda aka saba akai sanarwar ɗaure-ɗauren aure daza’ayi daban-daban wanda harda nasu Qaseem a ciki. Duk wanda yaga Qaseem a yau zai tabbatar yana cikin farin ciki, dan kuwa yaci ado da wata ɗanyar shadda fara ƙal da Dad ya bashi ya sanya, sai walƙiya da walwalin angwanci yakeyi kamar ka sacesa ka gudu, ga haƙoransa farare tas sun kasa rufuwa. Sai dai nayi iya dubana da waige-waige bangano ko mai kama da Jawaad ba balle shiɗin kansa, saisu Aliyu da suma duk suke sanye da shaddoji a yau, da alama dai gida suka koma bayan zancen ya riskesu suka canja shiri.
An fara ɗaura aure guda biyu da baida alaƙa dasu Dady, kafin a ɗaura wani da yaso bama kowa mamaki, wato dai Sabira da wani waishi Habib, ankuma roƙi Uncle Nasir dake kusa ya zama wakilinsu saboda wai wakilan amarya masu isoba har lokacin, wannan shine ya gogema mutane da yawa abinda ya taɓa musu zukata, ɗaurin aure na huɗu daya biyo baya shima bashi da alaƙa dasu Qaseem ɗin, saida akai kusan na mutum uku kafin a ɗaura na Qaseem da Azeema, jikin Qaseem har rawa yake ya miƙe zaiyi magana amma sai Uncle Uwaisu ya maidashi ya zaunar yana mai sanar masa bafashi ake nufiba maybe wasune daban, ajiyar zuciya Qaseem ya sauke dukda dai hankalinsa bai kwantaba, gashi iya dubansa baimaga Dad a wajenba, bayan kuma tare dashi sukazo masallaci, ɗaurin aure na ƙarshe baki ɗaya shine ya tada hankalin dukkan mai alaƙa dashi, wato Jawaad Abdul-aziz da amaryarsa Bilkisu Adam, Alhaji Baba wakilin amarya Uncle Nasir da yay zaton da Shahudah ya kasance wakilin Ango, saida aka ambatanefa yaji wasan ya canja salo. Qaseem yama manta a ina suke, take yanke yaci kwalar imam da masa tambayar yaya haka ta faru?. Da ƙyar ƴan agaji suka ɓanɓare imam a hannun Yah Qaseem, cikin tsagwaron tashin hankali Dad da Qaseem ya gaza gani ɗazun a masallacin ya shiga jeroma imam tambayoyi shima. imam da duk bai fahimcesuba yace shifa a haka aka kawo masa sunayen anguna da amaren da za’a ɗaurama aure a yau, kuma iyakarsu kenan ya kammala gama takardar. Yay maganar yana nuna musu.
Ganinfa za’a iya bama hammata iska a massalacine ya saka ƴan agaji sallamar kowa akace su Dad su fito a shiga inda ya dace ayi magana, sannan ana neman dukkan angunan da aka ɗaura aurensu ba dai-dai ba.
Yah Qaseem kawai aka gani a cikin anguna, amma babu Jawaad babu Habibu da aka ɗaurama Shahudah, kuma kowa yayi imanin yaga Jawaad a massallaci kafin a tada sallah, yanzukam an nemesa ƙasa da sama tamkar allurar mayya an rasa. Kowa ƙoƙarinsa ya kira wayar Jawaad amma sam taƙi shigama, gefe kuma ana jajen wanene habib ɗin da aka ɗaurama aure da Shahudah?.6
STORY CONTINUES BELOW

Lokacin da ake waccan dambarwar a lokacinne shikuma Salman ya kira Shahudah ya sanar mata komai, kafin ya kira Momy itama, yana tsaka da sanar mata abinda ke faruwa Shahudah ta nufi ɗakin Bilkisu da wuƙar data ɗakko daga kicin tsirara tana iƙirarin yaufa saita kasheta.
A masallaci komai ya hargitse, imam ya tara dukkanin ƴan agajin massallacin dake da alhakin rubuta sunayen waɗanan anguna da amare anata jera musu tambayoyi, dan kuwa dai Dad da kansa shine ya kawo list ɗin farko kuma an tabbatar yanada banbanci da wanda yake a hannun imam a yanzu. Sudai ƴan agajin dakeda wannan alhaki sun tabbatar abinda suka gani kenan, sannan kuma ga takardar farko da Dad ya kawo an samo kuma bata da alaƙa data yanzun. Abun ya ɗaurema kowa kai hatta da imam ɗin kansa, dan shidai yanada yaƙinin babu yanda za’ai ƴan agajin su bada abinda ba haka yakeba, dan invitations ake kawo musu na ma’auratan da duk za’a ɗaurama aure a satin, sukuma saisu rubuta sunayensu a takarda gabaki ɗaya domin samun sauƙi, nasu Jawaad kuma a rubuce Dad ya kawo tunda ba’a buga invitation card ba abin yazo a ƙure. TO A INA MATSALAR TAKE?.
Wannan itace tambayar dake a bakin kowa a wajen musamman lokacin da Yah Qaseem ya yanke jiki ya faɗi a sume shima. Dai-dai kuma da kiran da akaima Dad akan tashin hankalin dake faruwa a cikin gidansa. Abin tausayi sai kawai Dad ya fashe da kuka shima yana neman faɗuwar, cikin amincin ALLAH Uncle Sulaiman ya samu damar tarosa da faɗin, “Haba Alhaji Ali, ka kwantar da hankalinka mana, na tabbata saɓani aka samu ko kuskure, kuma abune mai sauƙi da nake ganin zamu warwaresa da gaggawa, Jawaad ya sakima Qaseem matarsa, haka shima wannan da bama asan ko wanenen ba ya sakema Jawaad matarsa”. Kasa magana Dad yayi, dan babu abinda yake fahimta daga kalaman Uncle Sulaiman, gaba ɗayama numfashinsa neman barin gangar jikinsa yakeyi.
Shugabannin massallacin dai nata ƙoƙarin binciken tushen wannan matsala da basu taɓa cin karo da itaba a tsahon rayuwarsu, anɗaura auren da babu adadi a shekarun wanzuwar massallacin amma hakan bai taɓa faruwaba koda da kuskure kuwa, babban tashin hankalinsu ma shine wanene Habib da aka ɗaurama Shahudah aure dashi?, dan kuwa dai an nema wakilan nasama an rasa balleshi kansa, matsalar Qaseem da Jawaad kam kowa yana ganin tanada mafita tunda su an rigada an sansu gasu kuma ƴan uwan juna.
Imam da kansa ya gama ɗaukar zafi gaba ɗaya ya cire rawanin kansa yana sharce gumi da faɗin, “Wannan wace irin matsalace haka? Tayaya za’ace an ɗaura auren da sam bashi da alaƙa da juna?”. Qaseem shine mijin Bilkisu, an ɗaurama Jawaad, Shahudah itace matar Jawaad an bama Habib, Habib shine mijin Azeema, an bama Qaseem, Qaseem da Jawaad ahali ɗaya suka fito, a tare kuma aka kawo sunayensu, to yaya akai shi Habib mai mata azeema suka shiga cikin wannan sarƙaƙiyar? Idanma ance wajen haɗe sunayen waje ɗayane dan a sauƙaƙama liman wahala to tayaya abin ya kasance haka? Kenan suk yandama akai aka dawo akwai saka hanun hadiman masallacin kenan?. hakan bazai kasance mai yuwaba dan gashi dukkan bincike anyi babu wani baƙon al’amari daya shigo har aka bama imam ainahin takardar amare da angwayen wannan satin, wadda kuma kowane ɓangare suke nuna ba ita bace imam yay amfani da ita, kenan dukkan matsalar a yanzu tadawo ta tattarane gama shi imam ɗin dan kowa shi yake zargi.7
★★★★★★
Ganin babu wata mafita anan Alhaji baba ya shawarcesu da tafiya gida kawai aje a samu nustuwa kafin a fuskanci matsalar cikin kwanciyar hankali a nema masalaha a kanta.
Kowa yay na’am da batun Alhaji baba, dan haka aka ɗunguma zuwa gidan Dad da tushen matsalar take.
Isowar motocin su Dad yay dai-dai da isowar motar gidan Sarki Sameer Saifudden dake ɗauke da ƴaƴansa ƴanmata a ciki, waɗanda suke cikin farin cikin samun fita yawo a wajen da basu saniba. Babu wanda ya fahimci su wanene su ɗin?, saboda kowa baya cikin hayyacinsa, ga matsananciyar hayaniyar data fiddo ƴan anguwa gaba ɗaya dake tashi daga gidan Dad.
Su Amaturrahman da kansu ke a kulle sunbi ayarin masu shiga gidan ganin shine gidan da Bilkisu ta tura musu address ɗinsa, sai dai gidan a harmutse yake har basu da damar fahimtar komaima. Isowar su Dad kuma ya sake harmutse gidan saboda ganin halin da Bilkisu da Shahudah ke ciki, ita kanta Momy bata cikin hayyacinta, ga Yah Qaseem can an wuce dashi asibiti shima, sai kawai Dad ya yanke jiki ya faɗi shima ganin ƴaƴan nasa biyu ga Qaseem kwance tamkar sun mutu.
Tashin hankali wanda ba’a saka maka rana kenan ke wanzuwa a wannan lokaci, a take aka kwashesu su uku aka fita dasu daga gidan zuwa asibiti domin ceto rayukansu, tuni suma sauran jama’a suka bisu a motoci, ƴan anguwa kuma suka shiga tattaunawa, danma anguwace ta manya kowa yana harkar dake gabansa babu ruwan wani da wani, amma a yanda lamarin yazo duk rashin shiga harkar junansu yazama dole a tattauna.
A wannan kace nace na ƴan anguwa su Amaturrahman suka fahimci wasu abubuwan, ciki kuwa harda fahimtar wadda sukazo gurintama tana cikin waɗanda aka fita dasu tamkar gawa daga gidan. Jikinsu a sanyaye suka koma mota driver ya jasu sukabar anguwar, Safah sai kuka take akan itafa subi suga wane asibiti aka kai Bilkisu, saida Amaturrahman tai kamar zata bugeta sannan ta nutsu tai musu shiru.4
★★★★★1
A ɓangaren su Jabeer kuwa tun dambarwar farko ta massallaci suka shiga ayarin ƴan neman Jawaad, sai dai komai kama dashima basu ganiba, bayan kuma a tare suka shigo dashi massallacin har aka tada salla, bayan an idarne suka nemesa suka rasa gaba ɗaya, a lokacin basu kawo komai a ransuba saboda ba’akai ga ɗaura aurenba, sai bayan an ɗaurane tsoro ya kamasu da tunanin kodai yanada masaniyar komai, to amma mizaisa yayi hakan kuma? Tunda sunsan halinsa sarai, suk son da yakema Bilkisu inhar babu wani dalili bazai zama mai aikata wannan abunda dake faruwaba domin kawai ya aureta, dolene su nemesa domin jin minene ke faruwa? Shine? Kokuwa shima bai saniba.
Sun fara da station, sai dai bai koma canɗinba kamar yanda kowa ya tabbatar, sannan gidansuma bai komaba, gidansa dake Abdul-aziz Yusif street nanma dai baima jeba, gaba ɗaya kuma sai kansu ya kulle ɓam akan komai.
Suna tsaitsaye a ƙofar gidansa na A.Y street ɗin saƙo ya shigo a wayar Jabeer. Jikinsa har rawa yake ya buɗe saƙon ganin Jawaad ɗinne ya turo.
“Kubar wahal da kanku wajen nemana, zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu zan bayyana, akwai aikin dana tafi yine, sannan karku zargeni akan abinda ya faru kamar yanda nasan rashin ganina anjima kaɗan zai ɗarsama wasu daga cikin ahalina, sam bani da hannu a ciki, akwai ɓoyayyen al’amarin danima ban sanshiba, lokacine kawai zai warwareshi. Inason kuyi duk yanda zakuyi kafin nan da awa uku a canjama Miemaa asibiti, dan nasamu labari yanzunan akwai matsalar data faru gidansu, karku barta ta kwana a asibitin da aka kaisu, karkuma wanda yasan kun ɗauketa daga asibitin har Alhaji baba”.
Kallan kallo aka komayi tsakanin Jabeer da Hafiz da Aliyu akan wannan saƙo na Jawaad da ya kuma ɗaure kansu akan wannan al’marin…………✍46
Yau dai gashinan na muku words 3700😲 kuci ku ƙoshi har safiyar litinin.😉👌🏼18
Barkanku da juma’a, kar a manta da saka bayin ALLAH a addu’a dan ALLAH.
Ƴan facebook kuma ga naku saƙon, gaisuwa da fatan alkairi a gareku a duk duniyar da kuke.
Asha weekend lafiya my sweet fans, banda taƙaddama kuma.😂😂😘😘😘😍👍🏻👌🏼
12
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻24Page 231
……………Tunkan su isa asibiti Dad ya farfaɗo, lokacin kuma da suka iso sun iske shima Qaseem ya farfaɗo, duk yanda Doctor yaso yayma Qaseem ɗin allurar barci danya huta yaƙi yarda, hakama Dad bai yarda ko dubashi ayiba, cayay babu damuwa su barshi. Bilkisu da Shahudah kawai aka shiga bama taimakon gaggawa, wanda daga farko Momy da catai baza’a duba Bilkisu ba, sai da Dad ya nuna mata ɓacin ransa a fili sannan ta nutsu, sai dai tanata ƙananun magana akan hakan.
Haka suma sauran family dake harabar asibitin saboda yawan da suke dashi aka tsaidasu nan kowa nata tofa albarkacin bakinsa, saidai mafi yawan kalamansu suna ɗora laifinne akan Bilkisu ce tai asiri. Yanda suke jifanta da mugayen kalamai dolene kaji tausayin Bilkisu, dan zaka ɗauka akan wata uwar mata suke maida yanda akayin. Hayaniyarsu ce ta saka Uncle Nasir cewa duk su wuce gida domin zamansu anan ɗin bashi da wani amfani. Badan sunso hakanba sukabi umarninsa.
Motocinsu na cikin fita su Jabeer suka iso asibitin suma domin cika umarnin Jawaad, mamakine yay masifar kamasu ganin wannan uwar gayya tamkar anan ake bikin. Shi Hafiz ma abin haushi ya bashi, ya buga tsaki cikin magana ƙasa-ƙasa yace, “Mutanen nan suna bani mamaki da al’amarinsu, to wannan gayyar kuma ta miye?”. Aliyu dake jinsa yace, “Kaima dai ka faɗa”.
Fitowa sukai a motar suka isa inda su Uncle Nasir ke tsaitsaye shi da Dad, da Uncle Sulaiman, sai Qaseem dake zaune cikin mota, Salman kuma yana zaune a saman motarne yanata latse-latse a waya tamkar baida wata damuwa a duniya. Gaishesu suka shigayi cikin girmamawa, tare da musu jajen abinda ya faru. Cike da kulawa suma suka amsa musu, Uncle Sulaiman yace, “Ina Jawaad ɗin shi yake? Tun ɗazun sai neman wayarsa muke taƙi shiga”. Duk kasa cewa komai sukai, dan kuwa suma dai basusan amsar daya dace ace sun basuba akan inda Jay yake, tunda suma basu saniba.
Uncle Nasir ya buɗe baki zaiyi magana ya fasa saboda shigowar motar Jawaad harabar asibitin, duk bin motar sukai da kallo harsu Jabeer, cike da mamaki suka tsatstsareshi da idanu lokacin daya fito a motar, yana sanye cikin wata dakakkiyar shadda ƴar ubansu ruwan zuma, sai maiƙo take, sosai ɗinkin ya zauna masa a jiki cif. Kosu kansu su Uncle Nasir ɗin ya musu ƙyau, dan kafin kaga Jawaad da manyan kaya akan daɗe saboda yanayin aiki, shiyyasa idan ya saka ɗin sai ya zama na musamman. Nufowa yay inda suke fuskarsa sam babu walwala, Qaseem da babu wanda ya lura da fitowarsa a mota yasha gabansa.
Kallonsa kawai Jay ya tsayayi batare daya iya cewa dashi komaiba, cike da ɓacin rai Qaseem yakai hannu zai shaƙosa, da sauri Jawaad ya ɗaga masa hannu, da watsa masa wani irin kallo mai razani dake gauraye da ɓacin rai, “Qaseem bani hanya”. “Anƙi a baka ɗin” Qaseem ya faɗa a zafafe. Jawaad baice komaiba ya raɓashi zai wuce, sake shan gabansa Qaseem yayi, Jawaad yay wani murmushi mai ciwo idanunsa na sake ƙanƙancewa tsabar masifar dake cin zuciyarsa, cikin wata irin muryar data bama Qaseem mamaki Jawaad yace, “Qassem ka riƙe girmanka, banason ka kaini bangon da zan sakaka dana sani mara amfani”. Kafin Qaseem yace wani Abu Uncle Sadiq ya ƙaraso wajen. “Ku wane irin shashancine haka kukem mutane anan?”. Jawaad baice komaiba, sai Qaseem ne ya bama Uncle Sadiq amsa da, “Uncle bazaka ganeba, wannan yaron munafukine, wlhy ko rantsuwa nai babu kaffara nasan yanada hannu akan wannan abun daya faru, kuma wlhy dolene ka saki Bilkisu a yau ɗin nan basai gobeba”. Murmushi Jawaad yay cikin taɓe baki ya raɓasu ya wuce batare da yace komaiba.
Ƙarasawa yay wajen su Uncle Nasir ya gaishesu, Uncle Nasir yace, “Kaikuwa ina kaje anta nemanka tun ɗazun Jawaad?”. “Amin afuwa Uncle, naje wani wajene”. “To amma saika kashe wayarka? Minene amfanin hakan?”. Jawaad dai baice komaiba.
Uncle Uwaisu yace, “Amma dai kasan miya faru a wajen ɗaurin aure ko?”. Cikin nuna halin ko in kula Jawaad yace, “Uhmmm na sani”. Ran Uncle Nasir a ɓace yace, “Ka sani? Amma shine dan wulaƙanci katafi wani waje ka barmu da nemanka?”.
Kafin Jawaad yace wani abu Uncle Sadiq yace, “Yaya nikam inaga wannan ba maganar nan bace, kamata yay muyi haƙuri yaranan su dawo cikin hayyacinsu sai ayi maganar a nutse a gida kamar zaifi, sannan kuma mu maida hankali wajen neman shi wancan angon da aka ɗaurama Shahudah aure dashi da ita Azeema take kowa”. Duk sunyi na’am da hakan, Jay ya kalli Uncle Nasir a wani yanayi, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru kawai.1
STORY CONTINUES BELOW

Bayan sallar la’asar su Uncle Nasir suka wuce gida harda Dad da Qaseem da aka tilastama dole akan yadace suje su watsa ruwa kodan suji ƙarfin jikinsu, anbar momy kawai wajen Shahudah, Ummie da maman Amina kuma suna tare da Bilkisu, Jawaad bai shiga duba kowaba a cikinsu.
Suna isa gida ya shige sashensa, wanka yay yasha magani saboda kansa ciwo yake masa sosai, duk yanda yaso ya kwanta ya huta hakan ya gagara, ya shiga zagaye bedroom ɗinsa cikin faɗawa wani dogon tunani akan wannan dambarwar da suka wayi gari da ita yau, tabbas yasan kaso mafi yawa na abinda ya faru, musamman akan sarƙaƙiyar ɗaurin auren, sai dai akwai wani al’amarin daya ɗaure masa kai sam ya kasa samun amsa akai, kuma yazama dole ya nemo wannan amsar, Tabbas saiya nemota, itace zata zama tsanin buɗe masa hanyar fahimtar abinda ya kasa fahimta a yanzu da duk sauran jama’a ma. Ya sauke numfashi mai zafi tare da kwanciya a kan gadonsa ƙafafunsa a ƙasa.
Shi da kansa shine ya canja list ɗin ɗaurin aure a masallaci, sai dai daliline mai ƙarfi ya sakashi aikata hakan, kuma duk wanda zaiji dalilinsa anan gaba zai tabbatar abinda yayi shine dai-dai kuma shine ya dace, to amma tayaya zai fahimtar da mutane sukuma su fahimta batare da ya fito da ainahin maganar filiba?. Wannan tambayar itace keta cin ransa da sukarsa a ƙahon zuciya. Barci ɓarawo shine ya sacesa a wannan lokacin batare daya shiryama hakanba, bai farkaba sai gab da magriba, wasu massallatanma har sun fara kiran sallar. Wanka yay a gaggauce yay shiri cikin ƙanan kaya ya fita riƙe da key ɗin mota da wayoyonsa, mota ya buɗe ya zubasu sannan ya nufi massallacin ƙofar gidansu sukai sallar magriba.
Koda ya dawo bayan an idar mota ya shiga ya fice daga gidan.14
★★★
MASARAUTAR GAGARA BADAU
Koda su Amaturrahman suka iso masarauta sai suka iske gimbiya Munaya tana sashen mai martaba, haƙura sukai akan idan ta fito saisu sanar mata da duk abinda ke faruwa. Safah dai batace komaiba, tana ganin yayun nata sun nufi ɗakinsu ta zare jiki zuwa sashen mai-martaban batare da sun saniba. Sai dai koda ta nema Jakadiya tai mata iso saitace mata gimbiya na tare da takawa, tasan kuma babu mai shiga ganinsa inhar yana tare da matansa. Tarbiyyar da su Safah suka tashi ciki akwai girmama hadiman gidan, dan koda wasa Gimbiya Munaya bata yarda yaranta suce zasu taka koda bawa na gidan yanda suke soba, tsaye take kan tarbiyyarsu daga ita har mai martaba da Mommah. Safah sai ta kwantar da kai cike da shagwaɓa tana lallaɓa jakadiya, harda bata ƙyautar dubu biyar. Baki Jakadiya ta washe, tace, “A uwar masu gida ai dolene nai miki iso, ammafa inhar basa falon farko to saidai kiyi haƙuri anjima saiki dawo.
Safah tace, “Na yarda, amma dai ba falon farko kawai ba, dan ALLAH harna biyu, dan kinsan inhar Ummu na tare da Abbu bazasu zauna a falon farko ba, nikuma maganace mai muhimmanci zanma Ummu”. Rigimar Safah da Jakadiya ta sani yasa ta amince zataje har falo na biyun. Safah na nan tsaye a ƙofar ƙatafaren falon mai-martaba Jakadiya ta shiga domin mata iso. Iyakarta falon farko tai kira ta wayar landline kamar yanda tsarin Sarki Sameer yake. Munaya ce dake masa tausa ta ɗaga, cike da girmamawa Jakadiya ta isar da saƙon Safah. Daga can Munaya zata fara faɗa akan Safah ta jirata saita fito Sarki Sameer yaymata nuni data bari Safah’n tazo, badan tasoba tabi umarninsa.
Cike da ɗoki Safah ta shiga kamar yanda Jakadiya ta sanar mata anbata izini, tun daga falon farko har zuwa na uku bata iske kowaba, hakan yasata wucewa ƙaramin falon da bakowa keda lasisin shigarsaba saisu da iyayensu. Tai sallama a bakin ƙofa suka amsa mata kafin a bata izinin shiga. Sarki Sameer na kishingiɗe a ƙasan lallausar daddumar da aka ƙawata falon da ita, ya zubama ɗiyar tasa da bazata gaza shekaru sha uku ba ido yana murmushi, itama murmushi take masa tana satar kallon Ummu dake zuba mata harara ta gefen ido. Ganin tayi tsaye taƙi ƙarasowa garesu mai-martaba yakai dubansa ga gimbiya Munaya, hannu yakai yanda Safah bazata ganiba ya Mintsineta, gimbiya Munaya ta ɓata fuska irin taji zafinnan, gira ɗaya ya ɗaga mata yana murmushi da cewar, “Kin tsaremin yarinya da ido takasa ƙarasowa, Ummuna kinga zo naji mike tafe dake?”. Da sanɗa Safah ta raɓa gefe taje ga mai-martaba daya tashi zaune sosai, hannunta ya kamo ya zaunar da ita kusa dashi. Safah akwai shagwaɓa da ƙulafucin iyaye, gashi tsiwarta data gada ga Munaya yasa Sarki Sameer ke tsananin sonta sosai, danshi idan tana abu Munaya kawai yake gani a zamanin ƙurciya. A jikinsa ta lafe tana kumbura fuska, cikin raɗa tace, “Abbu dan ALLAH kacema Ummu tabar hararata ni tsoron idanunta nakeyi, kumafa abu mai muhimmanci zan faɗa”. Murmushi mai-martaba yayi, ya maida dubansa ga Ummu data tsume fuska. “Ummu Please kiɗan saki fuska mana, kinga dai tsoron idanunki mukeji”. Yanda yay maganar cikin marairaice fuska ya sakata yin murmushi ta ɗauke kanta daga garesu.
Safah ta gyara zama ganin Ummu tabar harararta tace, “Abbu kasan miya faru a inda mukaje kuwa?”. “Saikin faɗa Ummuna”. duk abinda suka iske na rikici a gidansu Bilkisu shi Safah ta zauna tsaf ta zayyanema mai-martaba da Ummu, sosai abin ya basu mamaki, sai dai basuce komai akan batunba Ummu tace, “Tunda kin gama faɗa tashi kije idan na fito zanyi magana dasu Amaturrahman”. Sosai Safah ta kumbura harda hawaye, tace, “Abbu kajifa ni bandani za’ayi maganar bayan aunty nace”. Murmushi takawa yay yana mai girgiza kansa, ya shafa kanta yana faɗin, “Ai dolenema ayi magana da magajiyar Ummu, bayan ma kece kika kawo zancen”. Cikin ɗoki tace, “Yauwa Abbunmu shiyyasa nake sonka, bara naje na faɗama Mommah itama”. Kafin wani cikinsu yay magana ta fice da gudunta.
Ummu tace, “ALLAH dai ya shiryeki Safah, nikam bansan irinkiba”. Murmushi takawa yay tare da ɗora kansa saman cinyarta, yakai hannu ya shafi kumatunta yana mai lumshe idanu, “Dukfa rawan kan Safah a wajenki ta gada, kinsan kawai dai shi ɗan gado idan ya gaji abu saiya zarta mai shine”. Murmushi gimbiya Munaya tayi itama tana shafa kansa, tace, “Kaikuma gashi baka mantuwa yallaɓai”. Sosai ya buɗe idanunsa a kanta yana mata wani sassanyan kallo, cije lips ɗinsa da yay tare dayin ƙasa-ƙasa da murya kamar mai tsoron ajisu yace, “Yallaɓiya ai Sameer bai cancanci mantawa da ƙuruciyarki ba, kin bani wahalafa da yawa madam”. “Kamar yanda nima ka baniba”. Dariya sukayi a tare. Saida suka tsagaita takawa ya tashi zaune sosai idanunsa akan gimbiyar tashi. Yace, “Ban fahimci zancen Safah ba, mike faruwane?”. Cikin nutsuwa gimbiya munaya ta zayyane masa komai akan farkon haɗuwar Bilkisu dasu Safah ɗin a wajen Saloon ɗinta, har tafiyarsu yau domin kaimata l’d cards ɗin da Safah ta zama sanadin ɗakkosu. Shiru baice komaiba tsahon wasu mintuna, itama Ummu bata sake cewa komaiba. Harma ta sakin zancen sai y jeho mata tambaya akai “Toke yanzu mi kika fahimta a zancen nata kenan?”. “Eh to inason nasamu ƙarin bayani wajensu Amaturrahman ne, daga nan sainaga idan maganar nada muhimmancin da zamu shiga ciki, dan na lura a zancen Safah kamar ita yarinyar ba ƴar gidan bace”. Kansa ya jinjina mata kawai, daga nan suka saki zancen suka cigaba da hirarsu.
STORY CONTINUES BELOW

_____________________________________
Kai tsaye asibiti Jawaad ya nufa, Ummie ta wuce gida tun ɗazun bayan zuwansu Batool da Jawaad ya kira Ummah babba ɗazun yace taje asibiti ta kwana a can wajen Bilkisun, babu musu batool ta amsa sukazo tare dasu Ummah suka duba Shahudah da bilkisu, su su Ummah sai suka koma gida akabar batool din anan, da Nabeelah ma ta tubure nan zata kwana tana ta hawaye ganin halin da Bilkisu ke ciki, harda rantsuwar saita rama mata, saida ummah ta lallabata saboda sunyi yawa, kuma Jawaad tunda ba ita yaceba idan yazo ya sameta tasan kaniyarta zaici ne..
Batool na zaune suna ɗan hira itada maman Amina akan abinda ya faru yay knocking ƙofar, a zatonsu Doctor ne ya dawo. Ganin Jawaad ya saka Batool mamaki, dan cayayma Umma sai da safe zai dawo daga inda yaje, zatai magana yay saurin saka yatsansa saman baki alamar tai shiru, shirun kuwa tayi. Ya gaida Maman Amina cikin girmamawa dan dama sunsan juna tun lokacin da take aiki gidansu Shahudah kafin ta barma Amina saboda matsalar ciwon ƙafa data isheta. Takawa yay zuwa gaban gadon da Bilkisu ke kwance dama tunda ya shigo idanunsa a kanta yake, baya ganin fuskarta saboda ta juyama ƙofar baya. Cikin dabara maman Amina ta fita daga ɗakin.
Ta inda bily ta juya fuska Jay ya zagaya, tsaye kawai yay ya zuba mata manyan idanunsa da sukai jazur da ɓacin rai, tsawon mintuna uku kafin ya kalli Batool dake tsaye itama tana kallon bilyn. Cikin ɗacin murya yace, “Waye yay mata wannan dukan?”. Itama Batool muryarta da alamun baƙin ciki ta bashi amsa da cewar, “Su Aamilah ne akace, inason dan ALLAH kaci uban yarannan Brother, saboda wannan abin da sukai tsabar cin zaline ai da hauka, yaran gidannan naku sam tarbiyya bata ishesuba na lura, mtsoww!”.
Baice da Batool komaiba, sai dai yanda fuskarsa ta ƙara tsukewa zakasan lallai ran ƴan maza sun ɓaci, tsahonsa ya rage tare da ranƙwafowa akan bily da duk batasan anaiba, yakai hannun damarsa a hankali gefen kumatunta da yafi ko ina kumbura, motsawa tai tare da yatsine fuska alamar taji zafin taɓawar da yay ɗin, ya sauke nannauyar ajiyar zuciya yana mai janye hannunnasa. Tsaye ya miƙe idonsa har yanzu akan Bilkisun yace, “Mi Doctor yace yanzun?”. “Sunyi magana da Ummah, bansan miyace mataba gaskiya”. Bai sake cewa komaiba ya cigaba da kallon Bilkisu na tsahon lokaci, kafin ya sauke numfashi da zare hannunsa ɗaya daga aljihun wandonsa ya ɗauki file ɗin daya gani a drawer gefen gadon, saida yagama dube-dubensa sannan ya ajiye yay ficewarsa batare da yacema Batool komaiba. Itama da kallo kawai ta bisa, haka kawai yau takejin matsanancin tausayin ɗan uwan nata da ya kasance shi ɗaya tilo, babu wa babu ƙani, babu iyaye baki ɗaya sai dangi.
Magana yaje sukai da Doctor, ko kallon ɗakin da aka kwantar da Shahudah baiyiba yay ficewarsa daga asibitin, daga nan gidan Alhaji baba ya nufa.
Kiraye-kirayen sallar isha’i da akeyine ya sakashi shiga massallaci, saida aka idar ya shiga gidan. Shima Alhaji baban shigowarsa kenan babu jimawa, Jawaad ya zauna ya gaishesa, amsawa Alhaji baba yay idonsa akan jikam nasa. fuskar Alhaji a ɗaure baba yace, “Daga ina?”. Batare da Jawaad ya kallesaba yace, “Gida”. “Ɗazun kumafa da akaita nemanka a wajen ɗaurin aure?”. “Aiki naje”. Alhaji baba yace, “Humm aiki? Kenan bakasan miya faru a wajen ɗaurin aureba ma?”. Kan Jawaad a ƙasa dan yaƙi yarda su haɗa ido da kakan nasa yace, “Na sani, ninema na canja list ɗin ai”. Idanu Alhaji baba ya ɗago daga littafin addu’oin dake hannunsa ya kafe Jawaad ɗin da kallo, cikin sake ɗaure fuska yace, “Ai nasan bazai wuce kaiɗinbane daman, miyasa kai hakan?”. Kallonsa Jawaad ya ɗago yayi sai kuma ya ɗauke kansa yana wani ɓata fuska, dama yasan ko kowa bai gano shi bane da wuri Alhaji baba sai ya gane.
Alhaji baba yay ƙwafa yana maida kansa ga littafin da faɗin, “A hatsabibancinka dana sani hakan ƙaramin abune a gareka Jawaad, amma ince tun randa mukaje gidan Alhaji Ali akan maganarnan ya tabbatar mana da ɗansa zai aurama yarinyarnan kace ka haƙura?”. “Hakane baba, kamar yanda na faɗa a gabanku na haƙura na barmasa da gasken na haƙuran, sai dai kuma dalilin daya biyo bayane yasa na canja shawara”. Ran Alhaji baba ya fara ɓaci, dan haka cikin zafi yace, “Kasan zan iya saɓa maka ko Muhammad? Har wane irin banzan dalili ka riƙe da bazakazo ka sanar minba kafin ka yanke masa hukunci? Banason wannan shegen taurin kan nakafa kaima ka sani”. Sosai idanun Jawaad suka sake kaɗawa sukai jajur, jijiyar kansa dukta fito ruɗu-ruɗu, yasan duk sanda zaiyi abu saiya zo ya sanarma Alhaji baba, dan a halin yanzu shine kawai ke iya nuna masa ɓacin rai idan ya aikata ba dai-daiba kuma ya tsawatar masa akan ya kiyaye gaba, to amma akan wannan shi kansa baisan miyasa zuciyarsa taƙi aminta da ya nema sharar kowaba akan batun har sai bayan ya aiwatar……….
“Ina maka magana ka tafi tunani”. Jawaad da maganar Alhaji baba ta maido hayyacinsa yay ajiyar zuciya, cikin sanyin murya yace, “Nayi laifi kayi haƙuri, amma zuwa nan gaba kaɗan zaka fahimci hakan danai shine dai-dai baba……”
“Dai-dai ɗin ƙaniyarka, ka sakar musu yarinya ta auri wanda suka zaɓa mata, shikuma wancan habibun halan shima kaine ka kawosu shi da Azeemar? Tunda kasan har cikin ranka bakason maida yarinyarnan miyasa ka amincemin zaka maidatan?”.
“Baba nifa bani na kawosuba, su Uncle Nasir pretending kawai suke akan maganar suma, dan sunsan wacece Azeema, tunda da saninsu aka ƙulla aurama shi Qaseem ɗin ita, sannan sakin yarinyar zai zama babban kuskurene, akwai wani abu da suke ɓoyewa akan yarinyar, ka bani damar bincikosa sanan, na yarda inhar nine banda gaskiya ka ɗauki kowane hukunci”. Shiru Alhaji baba yay yana kallon Jawaad da nazarin kalamansa a ƙwaƙwalwa, kusan mintuna biyu suna a haka shiru kafin Alhaji baba ya ɗauke kansa daga kallon Jawaad ɗin ya maida ga littafinsa, “Ka dainamin ɓoye-ɓoye, ka fito fili kasanar min abinda ke faruwa?”. Ajiyar zuciya Jay ya sauke da faɗin, “Duk abinda zan faɗa a yanzun zai iya zama kuskuren abinda yake a zahirin gaskiya ne, nima a yanzu bakomai na saniba baba, sai dai insha ALLAH zan binciko duk abinda yake a binne nanda ƙanƙanin lokaci insha ALLAHU”. Tsagwaron gaskiya Alhaji baba ya hango a kalaman Jawaad, hakan yasa bai sake cewa komaiba.
Miƙewa Jay yay ya nufi bedroom ɗin kakan nasa yay kwanciyarsa.
Alhaji baba ya bisa da kallo har saida ya shige, tabbas ya fahimci akwai abinda Jawaad ke ɓoyewa, kuma da alama yanada alaƙa da Uncles ɗin nasa, bazai matsa masaba akan sai yaji komai a yau, dan yasan idan yana fushi takura masa akan abu sake busar masa da zuciya yake, sai dai yasan duk abinda Jawaad ya dage a kansa to lallai akwai abinda ya hango a cikinsa, shi kansa akwai mafarkan da yake a kwanakinnan suna damunsa, ya kuma rasa ina suka dosa?, abin mamakin shine kullum mafarkin maimaita kansa yakeyi, kayi mafarki sau ɗaya sannan ka sake maimaitashi gobe, har tsahon wasu kwanani dolene kasaka masa alamar tambaya koda kaso tureshi a ranka. Tsahon lokaci yana zaune a falon yana tunani bai shiga ɗakinba sai kusan sha ɗaya, lokacin tuni Jawaad yay barcima shi. Shirin barcin yay shima ya hau gadon, idanu ya tairama Jawaad dake barci fuska a ɗaure alamun cikin ɓacin rai yay barcin, Alhaji baba ya sauke numfashi tare da shafa kan jikan nasa, a ƙasan ransa yanajin tausayinsa, gefe kuma yana jin matuƙar tsoron irin hatsabibancin Jawaad da rashin tsoro, yana tsoron kar wani yay amfani da wannan halayyar tasa ya cutar dashi wataran. Da waɗanan tunane-tunanen fal ransa yay barci shima.13
★★★★★★
Bayan tafiyar Jawaad Maman Amina ta dawo ɗakin, macece ita mai yawan ibada dama, bata wasa da ibada ko kaɗan, dan haka koda ta dawo saita ɗauro alwala takoma gefen bilkisu ta zauna a kujera dan ganin wata irin zufa da Bilkisu keyi mara dalili, gashi sai mutsu-mutsu take kamar wadda aka saka cikin wuta, Batool kuwa tana gadon mara lafiya ɗaya daya rage a ɗakin tai kwanciyarta itama. Addu’oi maman Amina taita tofama bilkisu dan zufar ta bata mamaki da tsoro, gashi akwai fanka a ɗakin tana aiki kuma, bakuma wani uban zafi akeba a garin balle ace, da alama dai mafarki Bilkisun keyi. Ahankali-ahankali gumin ya fara tsanewa daga goshin bilkisu, ta koma sauke numfashi ahankali saɓanin da datake yinsa da sauri-sauri, takuma nutsu waje ɗaya. Tajima tana mata addu’ar har kusan ƙarfe ɗaya kafin ta miƙe ta shimfiɗa abin salla ta fara nafilfilinta data saba a zaune saboda ƙafarta bata jimirin tsaiwa.
Wani irin sukur-sukur maman Amina keji a ɗakin, tun tana ɗaukar motse-motsen da takejin a wasa hartakai ta fara waige-waige, tabbas tanaji a ranta akwai wani abu a ɗakin da itama bata iya hasasowa ba, tashi tai ta ɗakko jikkarta datazo asibitin da ita ta ciro Qur’anin da tazo da shi, karatu ta fara cikin suratul baƙara, sai motsin da takeji ya ƙara ƙarfi, ɗaga kan da zatai sai idanunta yaci karo da wata irin halitta mai kama da ƙadangare yana fitowa daga ƙarƙashin gadon da bilkisu ke kwance, sai dai kuma shi wannan farine fat tamkar babu jini jikinsa, sannan ƙaton gaske kamar kada ta cikin ruwa, jikinsa sai wata iriyar muguwar walƙiya yake tamkar ruwan dake kwance cikin teku, dukda zuciyarta ta girgiza da kallon wannan halitta mai ban tsoro dake nufota sai bakinta bai daina karanto ayoyin alƙur’anin ba kasancewarta jaruma mai dakakkiyar zuciya, tsayawa yay cak a tsakkiyar ɗakin batare da ya ƙaraso gareta ba, ya shiga goga kansa a ƙasan ɗakin kamar wanda ake duka, kafin kuma ya juya bindinsa har gab da ita ya fuskanci ƙofar fita, da gudu ya fice tamkar an masa umarni. Cigaba tai da karatunta har lokacin ta gaza ɗauke idanunta daga ƙofar. Sam Batool batasan wainar da ake toyawaba, barci take kashirɓan, bily ce dai bazamuce ga halin da take cikiba. Sautin karatun alkur’anin da Mmn Amina keyine ya tada Batool, itama samun kanta tai da shiga bayi tayo alwala, ta idar kenan ta miƙe tana gyara ɗan kwalinta zata fito taga wani ƙaton maciji jajur dashi yana silalawa ta Window toilet ɗin zai fita, ƙara ta ƙwalla tare da fitowa a guje jikinta na masifar rawa. Tazo ta ƙanƙame maman Amina dake cigaba da karatu dukda hankalinta yayi masifar tashi da ƙarar Batool ɗin, tanaji a ranta itama wani gamon tai a bayin…………….✍30
Sannu sannu bata hana zuwa saidai a daɗe ba’a zoba. to aljanin daya canja takarda ya bayyana😂, sai muje zuwa domin jin dalilin Jawaad na canjawar da kuma tayaya ya canja ɗin, da alama kuma ya fara bankaɗo wani sirrine da zai bamu hasken sanin ina muka dosa🚴🏼. ALLAH ya daidaita sahun Jawaad akan lokaci😂, bara na fece nidai kafin ya karyani🚴🏼🚴🏼🚴🏼.9
Barkanmu da dawowa, ina fatan kunsha weekend lafiya?.
25
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.27
Page 24
1
Godiya ta musamman ga UMMINRASHIDA CARE FOUNDATION, saƙo ya iso gareni, ina muku fatan alkairin nima, tare da godiyan bangirma da jinjina, alkairin ALLAH yakai gareku aduk inda kuke. Nagode da wannan girmamawa taku a gareni, duk da har yazu dai bilyn Abdull rarrafe takeyi, Inai muku so irin trillions ɗinnan😍😍😘😘👍🏻
9
…………….Jin Alhaji baba ya fara sauke numfashi Jawaad ya buɗe idanu a hankali, juyi yay domin ya tabbatar barcin baba yay nisa tamkar a cikin barci yake, shiru baiji Alhaji baba ya motsaba, yay murmushi tare da sauka daga gadon a hankali, cikin sanɗa ya fito daga bedroom ɗin, a falonma yanayi yana waiwaye harya fice, gudun matsala yasa yabar motarsa anan ya fice daga gidan baki ɗaya, wayarsa ya ciro a aljihu ya duba time, sha biyu saura kwata, ya maida wayar a aljihu yana furzar da iska. Daga gidan zuwa titi babu nisa sosai, hakan yasa ya taka da ƙafa ya samu napep. Saida suka fara tafiya ya sake fiddo wayarsa ya duba saƙon su Jabeer daya shigo tun ɗazun, ɗan typing yayi kaɗan ya tura musu cewar gashinan a hanya.
Cikin mintuna kaɗan suka iso gidansa na A.Y, sai dai bai bari sun ƙarasa gidanba ya sauka, dubu guda ya miƙama mai napep, yana ya tsaya ga canji amma Jawaad bai saurareshiba yay wucewarsa. Mai napep ya cusa kuɗinsa a aljihu yana faɗin “gaba ta kaini inma bakasan ka baniba”.
Oho Jawaad baisan yanaiba, tunima ya shige gidan. A falo ya iske su Aliyu, kowa da hidimar da yakeyi, ya zauna cikin kujera yana faɗin, “Kuyi haƙuri na rikeku anan ga madams suna jiranku a gida”. Hafiz dake aiki a lap-top yace, “Babu damuwa ango, yanzu dai mike faruwa?”.
Ajiyar zuciya Jawaad ya sauke yana faɗin, “Akan abinda ya farune yau, nasan kuma duk a ƙage kuke da sonjin yadda akayi?”.
Hakane boss. Suka faɗa a tare idanunsu na akansa.
Bayansa ya jingina da kujera yana mai ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, cikin ɗacin murya yace, “Kamar yanda nasan tunaniku na akan nine na canja komai hakane, nayi ne saboda labari dana samu daga majiya mai ƙarfi akan abinda Momy ta ƙulla ita dasu mama Atika. A zahiri sun tsaida bikin Qaseem ne da yarinyarnan Miemaa, sai dai a baɗini sun tanadarma Qaseem mata batare dashi kansa ya saniba. Azeemar da aka ɗaura aurensa dashi ɗiyace ga Gwaggo Hajarah ƙanwar Momy da suke ɗaki ɗaya”.
Sosai mamaki ya cika zukatan su Jabeer, Hafiz yace, “To amma miyasa sukai hakan?”.
“Wannan itace amsar da nakeson mu nemo nima Hafiz, har yanzu mamaki baibar ɗawainiya da zuciyataba akan wannan al’amarin, miyasa zasu aurama Qaseem Azeema bayan sunsan ga wadda yace yanaso?”. Jabeer yace, “Nidai a nawa ganin kamar dama basason aurensa da Mami ne, sunsan kuma kosun hanashi bazai hanuba, shine suka zaɓi bi ta bayan fage su haɗa masa guda biyu, zaɓinsu da kuma nashi zaɓin”. Hafiz yace, “Maganarka akwai ƙamshin gaskiya Jabeer, to amma idan hakane shi Habib ɗinan miya kawosa cikin wannan al’amarin, sannan wanene shiɗin kuma?”.
Aliyu datun ɗazun baice komaiba yay ƙwafa, “Ni wlhy kusan kawai minake saƙawa a wannan lamarin kuwa; Duk kallonsa sukayi suna jiran ƙarin bayani. ya cigaba da faɗin, “Inagafa su sun tsara al’amarinne akan boss ya auri Shahudah, Qaseem a bashi Azeema, ita kuma Mami su aura mata Habib ɗin, inhar ba hakanne tsarinsuba miya kawo shi habib ɗin a zancen tunda alama ta nuna babu matarsa a cikin list ɗin ɗaurin auren?”. Zaune sosai Jawaad ya tashi idanunsa akan Aliyu, yace, “Aliy wannan maganar taka haka take, abinda yake cin raina anan inhar hakanne to kenan shi Dad bai fahimci Mom batason aure Miemaa da Qaseem ba kenan? Kokuwa shima ta shirya cin dunduniyarsa ne? Tunda ɗiyar ƴar uwarsa ce”. Hafiz yace, “To nima dai abin yasani wannan hasashen, amma kuma idan mukai dubi da yanda ya tada hankalinsa bayan faruwar abun harda suma hakan na nufin baisan su Momyn Shahudah sun shirya hakanba?”.
Shiru duk sukai suna nazarin maganar Hafiz ɗin, Jawaad ya miƙe tsaye hanayensa duka cikin aljihun wandonsa, kallo ɗaya zakai masa ka fahimci ransa a ɓace yake, yace, “Basu kaɗai suka shiryaba, hardasu Uncle Nasir, abinda yasa abin ya tsayamin arai shine, miyasa shi Uncle Nasir zai zama munafuki a tsakaninmu? Shinefa ya jagorancemu wajen Dad ni da Alhaji baba akan maganar Miemaa ɗin, saboda Ummah ta matsa akan sai dai Alhaji baba ya nemamin aurenta tare da Hudah kodan hakan ya zama gargaɗi gareta, kenan yasan shirinsu da Momy, amma kuma ya amsama Alhaji baba cewar muje muyima Dad ɗin maganar a haɗamin auren Miemaa da Hudah? Sannan sarai yasan Qaseem an tsaida masa ranar aure da Miemaa! ɗin kuma?”.
“To tabbas kam wannan matsalar daga nan take boss, Uncle Nasir yasan komai, amma kam bai ƙyautaba, dan nikam ina bala’in ganin girmansa wlhy saboda yanda ya riƙeka, ashe ba har zuciya bane, wannan wane irin zumincine muke fama dashi a wannan zamanin?, kaga yanda aka cukurkuɗe abu saboda kawai buƙatun wasu dason faranta musu, kuma duk idan kaje ka dawo zaka fahimci ita Mami itace akai shirin sakawa a tsaka mai wuya, miyasa sukaso mata wannan mugun ƙullin to?”.
Duk hankalinsu suka maida ga Jawaad da yay shiru yana nazarin kalaman Jabeer na ƙarshe akan uncle Nasir da maganar ƙullin da akaso yima Bilkisu. Cikin son maidosa hankalinsa Hafiz ya zunguresa, kallonsa yay. Hafiz yace, “Mi muke ciki yanzun? Dan ko game da Mami muna buƙatar bincike mugano gaskiyar maganar Jabeer, mizaisa suyi shirin cutar da ita?”.
Guntun Murmushi kawai Jawaad yay ya koma cikin kujera ya zana, kwantar da bayansa a kujeran yana mai lumshe idanunsa, a hankali ya furta, “Wannan shine dalilin zamanmu anan, dan inaji a raina wannan ƙiyayyar da sukaso nuna mata tawuce naƙin son aurenta da Qaseem kawai, akwai wani abu da bamu saniba, dan haka inason sanin anahinma alaƙarta da mutanen gidan”.
Jabeer ya ajiye cokali yana faɗin, “Kamar ta taɓa gayamin Dad yayan mahaifiyartane ubansu ɗaya, kaga kuwa bazai wuce Momy ta ƙitaba akan ƴan ubancin dake tsakanin Dad da mamata, sai dai kuma zata iya yiwuwa ɗin akwai wani abu a ƙasa damu bamu saniba harsai mun bincika tukunna”.
“Kai lamarinfa akwai ɗaurekai, sannan akwai lauje cikin naɗi, aganina tunda basa sonta da ɗansu su rabasu kawai basai sun zalinceta sun haɗata aure da wanda bata saniba”. Hafiz yay maganar cikin takaici.
Aliyu yace, “Kai dai bar son zuciya Hafiz, amma harma nawa Mami take da za’a mata irin wannan muguntar? Yanzu dai boss mikace kai akan batun? Tunda dai ALLAH yasa ta fita daga tarkonsu, yanzu aikin farko dake gabanmu shine Qaseem da Shahudah, baƙaramin yaƙi zasuyi a kankaba da Mami tunda. Shin Ka sanar musu kaine ka canja sunayen ne?”.
Jawaad da duk yake saurarensu cike da nazari yace, “Eh na sanarma Alhaji baba ɗazun, na nuna masa nine na canja, nakuma saka masa zancen Azeema ciki, na tabbatar zuwa safiya zai nema su Uncles da maganar, mukuma sai muyi amfani da wannan damar”.
“Amma Boss baka ganin ka ɗaure kanka da yawa? Taya za’ai ka amshi laifin kai tsaye bayan bamusan mike a ransuba game da batun?”. .
Muryarsa cike da damuwa yace, “Jabeer hakan shine kawai hanya mai sauƙi da zamu bama koma waye ƙafa, sannan Bazaka ganeba, rikicin tsohon nan ya wuce dukkan tunaninka, gara nafito na faɗa masa gaskiyar maganar, harfa ya kafamin sharaɗin saina saki Miemaa, yanzu dai nagama da matsalarsa”.
Dariya sukayi a tare, cike da tsokana Jabeer yace, “To tsakani da ALLAH gaskiya Alhaji baba ya faɗa, ka bama Qaseem matarsa”. Banza yayma Jabeer ɗin, ya miƙe yana kallon agogon hanunsa, “Kunga ɗaya harta wuce, mu tsaida maganar iya haka, zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu nasan Alhaji baba zaisa ai zama akan batun, anan zan fahimci yaren kowa, daga nan saimu ɗora da abinda ya dace kawai”.
Duk sunyi na’am da jawabinsa, kowa ya miƙe yana tattare kayansa kafin su fito, Jawaad tare suka tafi da Hafiz zai ajiyeshi gidan Alhaji baba saboda hanyarsa ce shi, su kuma su Aliyu kowa ya shiga motarsa.
4
STORY CONTINUES BELOW

★★★★★
Da sanɗa Jawaad ya shigo bedroom ɗin duk dan karyay motsin da zai tada Alhaji baba, a bazata yaji yace, “Daga ina?”. Tsam Jawaad yay ya kasa ƙarasawa, cikin sauke ajiyar zuciya yace, “Nafita akan wani aikine”. Alhaji baba baice komaiba, hakan yasa Jawaad nufar toilet dan ya watsa ruwa.
_____________________________________
A asibiti kam daƙyar mama ta kwantarma Batool hankali, Cikin sarƙewar numfashi da tsananin tsoro tai mata bayanin abinda ta gani a toilet, shiru maman Amina tai tana nazari da haɗa komai a mizanin daya dace, a fili kuma sai tayi murmushi tana mai girgiza kanta, cikin bama Batool ƙwarin gwiwa ta umarceta akan ta tashi tai sallarta koma minene ALLAH zaiyi maganinsa. Jiki a sanyaye Batool tabi umarnin Mama.
Haka suka kusan kwana akan abin salla suna gayama UBANGIJI damuwarsu, gabannin asuba bilkisu ta farka tana ambaton a bata ruwa. Fita Batool tai ta kira Doctor’n daya kwana duty, babu jimawa suka dawo tare. saida ya tabbatar babu wata matsala tare da Bilkisun sannan yace su bata ruwan tasha.
Tunda ta kafa kai a babban goran ruwan da Batool ta saka mata a baki sai da ta shanyesa tas sannan ta ɗauke kanta, dukansu kallon mamaki suke mata hatta da Doctor ɗin kansa, sai dai babu wanda yace komai.
murya a sanyaye tace, “Mama zanyi sallah”.
Taimaka mata batool tai ta sakko a gadon, mama ta rakasu har toilet ɗin ta sirkama bilkisu ruwan wanka da ruwan dake cikin flask, fita batool tai, mama ta taimakama bilkisu tai waka da gasa jikinta dukda tana ta noƙewa saboda kunya. Itako mama sai tayi kamarma bata gantaba. Bikisu taji daɗin wankan sosai, takumaji karifin jikinta, sallolin dake kanta ta shiga ramawa harda sallar zuhur ɗin jiya data tabbatar batayita cikin nutsuwaba.
★★★★★★
Zuwa 10:30am na safe dukkan mai alhakin tofa albarkacin baki akan wannan matsalar ya hallara a gidan Dady, bisa umarnin Alhaji baba daya buƙaci hakan, dan yanason jin gaskiyar magan akan abinda Jawaad ya faɗa masa gameda zancen Azeema da yace sunsani. Jawaad yana jerin waɗanda sukazo a farko-farko dan tare yake da Alhaji baba, hakan kuwa yaso bama kowa mamaki dan sunsan halinsa sarai da iya ƙin zuwa wajen meeting akan lokaci saiya gama shanya jama’a, amma yau abin mamaki sai gashi cikin masu sakkon zuwa.
Bayan isowar Imam da wasu daga cikin manyan massallacin da aka ɗaura auren Salman da Qaseem daya rame sosai tamkar wanda ya kwana biyu yana jiyya suka shigo suma, ya ƙara haske da tsayi abin tausayi, Jawaad dai baiko kalli inda Qaseem yakeba, amma shi Qaseem sai binsa yake da wani irin mugun kallo tunda suka shigo.
Imam ne ya buɗe taro da addu’a, a kuma dai-dai lokacinne Shahudah da Mom da suka taho daga asibiti bisa matsawar Shahudahn suka shigo suma, wajen zama suka samu idon Shahudah akan Jawaad tana mai kwarar da hawaye, itama harta rame kwana ɗaya kacal. Bayan imam ya kammala addu’oi ya ɗaura bayani da cewar, “Nasan kowa dake nan yana neman amsar tambayarsane a gareni, wadda yinin jiya har zuwa dare na ɓata lokacine wajen nemota nima amma har safiyar yau ban samo amsarba, narasa wannan wane irin cuɗaɗɗen al’amarine mai sarƙaƙiya, a hasashena har junnu saida na kawo dukda bani da tabbacin haka balle hujja, ban saniba shin ko a cikinku wani nada amsar da nima nake cikin ruɗani da bulayin nemanta?”.
Shiru falon yayi babu wanda ya iyayin koda tari, sai shashshekar kukan Shahudah kawai ke tashi. Uncle Nasir ne yay ƙarfin halin bama Shahudah umarni akan ta tashi ta fita. kafaɗa ta maƙe alamar bazata tashinba, ta koma jikin Momy ta lafe tana masa kallon harara dukda kasancewarsa wan uwarta. Babu wanda ya iya sake cewa komai game da tashin Shahudah, dan kuwa anga iyayenta basu tankaba alamar basu da damuwa da zaman nata su. Jawaad yay gyaran muryar da kowa ya maida hankali kansa, batare da ya kalli kowaba yace, “Imam kayi haƙuri, babu ta inda zaka iya samo amsar sarƙaƙiyar jiya kaida duk wanda keda alhakin sanin sirrin massallacin nan. Ni dasu Momy mune kawai masu wannan amsar, dukda inada tabbaci da yaƙinin bayanmu wasu sunsan komai koda ba duka ba”. kaf falon babu wanda bai sagade yana kallon Jawaad ba, yayinda Momy ta miƙe zumbur tana nunashi, “Amma kai dai Jawaad anyi shaiɗanin yaro, a gidan ubanwa nake da amsar? Ni dama tun jiya da akace an nemeka an rasa nasan kaine shaiɗanin daya dace a nema dukkan amsoshinnan a wajenka…….”
Murmushi Jay yayi, sai dai baice komaiba, hasalima kansa a duƙe yake bai kalli kowaba har yanzun. Alhaji baba ne ya tsaida Momy jin tanata aibanta masa jika, “A’ishatu, inaga mubashi dama muji ina maganganunsa suka dosa kafin mu yanke hukunci koda na furucin bakine, mudukanmu nan a ƙage muke dason jin amsa, yakamata muji yaya akai aka kwana a ragaya bayan munsan shirinmu a tandun mai ne”. Magana Momy zata sakeyi Qaseem yace, “Momy Please ki zauna miji munafurcin dazai faɗa”. Ƙwafa Momy tayi ta koma ta zauna saboda gargaɗin da Uncle Uwaisu yay mata da idanu.
Shirun da akaine ya saka Jawaad ɗagowa, yace, “Inaga kafin warware dukkan sarƙaƙiyar massallaci yakama musan wacece Azeema da aka ɗaurama Qaseem aure da ita? Domin wannan shine kawai zai zama mabuɗin buɗe mana gaskiyar abinda muke son sani baki ɗaya”. Tsit falon yay saboda bugawar da zukatansu sukai a lokaci ɗaya babu zato ko tsammani da zuwa furucin Jawaad ɗin a garesu. Alhaji baba ya katse shirun da cewar, “Banda abunka Muhammad Jawaad muma ai duk amsar da muke nema kenan akan Habib da Azeema?”.
Jawaad yace, “Hakane Alhaji baba, amma ina ganin karmu jata da nisa, domin su Uncle duk sunsan wacece Azeema da Habib, idan ka cire Imam da jama’arsa, kai da Uncle Sulaiman, Uncle Sadiq, Qaseem, kune kaɗai kuke neman ƙarin bayani”. Uncle Sulaiman yace, “To mukam saiku amsa mana kunata sake dilmiyar damu a hasashe”. Fuskar Uncle Nasir a matuƙar ɗaure cikin kafe Jawaad da idanu yace, “Mikake nufi da waɗanan kalaman naka?”.
Jawaad yace, “Babu abinda nake nufi Uncle, kawai dai ina son kowa ya fahimci daga ina matsalar take harshi Qaseem ɗin da aka ɗaurama aure…….”
Cike da masifa Momy ta sake katse Jawaad da faɗin, “Inma wani munafurci ka ƙulla kai zai ƙaremawa, inace dai sokake kace mune muka haɗa auren Azeema da Qaseem batare daya saniba, to ai mun isane, yarinyar da ya kawo yanason zai aura batai manaba, tayaya idan shi baisan ciwon kansaba mu zamu biye masa duk muzama mahaukatan?”.
Cikin ɓacin rai Jay yace, “Amma miyasa ni da nazo neman a bani na aura kukace Qaseem shi zai aureta?”. Yanzukam tamkar Momy zata mari Jawaad ta bashi amsa a matuƙar zafafe “Saboda Shahudah tafi ƙarfin yin kishi da ita, bandama rashin mutunci da raini irin naka Jawaad, bakaji kunyar zuwa a gaban idanunmuba kace mu haɗa maka ƴar cikinmu da wadda mukema alfarma mu aura maka”. Sosai zuciyar Jawaad take sake hasala, sai dai ƙoƙarin dannewa yake dan koba komai Momy yayar mahaifinsa ce ita, cikin ƙoƙarin danne fushinsa yace, “Amma Momy dan kawai baƙwa ɓuƙatar marainiyar ALLAH ta jingini da jininku sai kuje ku biya wani kuɗi dan ya aureta bayan kunsan shiɗin ba mutumin kirki baneba? Wai shin nawa ita wannan duniyar take da har muke tunanin wanda muka tseramawa bazai taɓa taddomu ba? Baƙwason ta auri ɗanku, baƙwason tayi kishi da ƴarku, tominene fa’idar biyan wani ya aureta? Saiku barta ALLAH ya kawo mata wani mijin, shi kuma Qaseem ku sanar masa bakwason alaƙarsa da ita bawai saikun cutar da itaba ta hanyar da batajiba bata ganiba…….”
Qaseem ya miƙe a fusace zaiyi magana Uncle Sulaiman da baƙin ciki ya lulluɓe yay saurin katseshi daga shi har Jawaad ɗin, yace “Kai Qaseem kaga zauna, ku kuma Kunga kudaina mana magana a cuɗe daga kai har Humaira, shin minene ya faru?”.
Sosai zuwa yanzu fushin Jawaad ya kasa dannuwa, cikin zafin zuciya da kowa yasanshi da ita idan aka kaisa bango yace, “Wato Uncle yarinyace suke riƙo a gidansu, har takai maganar aure ya shiga tsakaninta da Qaseem, kuma sune suka amince masa, amma kuma sai suka koma ta bayan fage suka nema masa auren Azeemar gwaggo Hajarah. Bayan kuma Alhaji baba yaje akan su bani auren yarinyar amma suka nuna min cewar shi Qaseem ɗinne zai aureta. Abinda kuma zai baka mamaki ita kuma yarinyar suka samu wani da sam ba mutumin kirki bane suka biyashi akan zasu aura masa ita yarinyar batare datasan da shirinsu ba, kuma sun nuna masa duk badaƙalar da za’ayi karya sake ya saketa, wannan shine dalilin dayasa na koma nima ta hanyar da sukabi na canja nasu shirin da nawa, tabbas nine na canja takardar da akaba Imam da tawa a lokacin da yake ƙoƙarin shiga massallaci.. Bayan duk an kawomin bayanai akan shirin da sukai na cutar da yarinyar saina shiga nazarin neman hanyar daya dace na hana faruwar mummunan ƙudirinsu, a kaf hanyar danake gani zata zama yarinyar za’a sake cutarwa, dan haka daga ƙarshe sai na yanke shawarar bin hanyar da suma sukabi, wato ta ƙarƙashin ƙasa. Imam idan har baka mantaba bayan isowarka massallaci wani yazo ya sameka akan batun wani aure, har ya roƙi afuwa akan rashin kawowa da wuri, kaikuma ka amshi uzirinsa tare da bashi takardar list ɗin sunayen waɗanda za’a ɗaurama aure a ranar kace ya rubuta sunayen waɗanda yazo dasu a gurin, to ba kowa bane face ni, da wannan damar nai amfani na canja takardarma baki ɗaya bayan na kwafe sunayen dake can nakuma canja namu a yanda naso”.
Salati manyan suka sanya da wannan al’amari, yayinda Cikin ƙaraji Qaseem yace, “ Momy!!!, mikuke nufi da hakan da kukayi to? Minai muku da zafi haka kuka zaɓi zalintata ni da Bilkisu?!, to wlhy, na rantse da ALLAH, ku kwana da sanin………..” da sauri Momy ta rufe masa baki, sauran ƙarfinsa da wanda ɓacinrai ya kawo masa yanzu ya tattara ya hankaɗe Momy gefe ta faɗi. Jawaad ne yay saurin miƙewa yana faɗin, “Qaseem minene haka? Baka da hankaline?”.
“Eh bani dashi kaikuma? Idan kai haƙuri kaima ina tafe kanka, garama kayi gaggawar sakarmin mata kafin kanema numfashinka a ƙirji ka rasa”.
Wani banzan kallo Jawaad yay masa, kafin ya bashi amsa Shahudah ta katsesu da jehoma duk wanda ke falon tambaya cike da rashin kunya. “Kai broth kamaji munafukan da suka ƙulla maka naka makircin, nikuma saiku faɗamin wanene Habib yake koma wane oho muku, kaikuma Bb kai gaggawar sakin waccan ƴar iskar yarinyar tamaje ta auri Uban Qaseem a yanzu wannan bai dameniba dan kaina kawai na sani, gwarama kowa yasan abinda zanyi sai yafi naka ɗaga hankalin kowa dake gidanan wlhy”.
Jin komai ya warware Imam da tawagarsa suka miƙe domin tafiya, a ganinsu wannan matsalace ta cikin gida, sukam tunda sun fita gara su kama gabansu. Godiya su Alhaji baba sukai musu sannan suka fice.
A take falon ya kaure da hayaniya har babu maijin maganar ɗan uwansa, Jawaad na shirin ficewarsa Shahudah dake kuka tana zubama mutane rashin kunya tai saurin riƙoshi, “Wlhy bazaka fitaba saika saki tsinanniyarnan bb”. Bai tanka mataba, sannan kuma bai juyoba, sai ƙoƙarin fisgar jikinsa da yay zai fice abinsa. Ƙara Shahudah ta ƙwalla wadda ta dawo da duk hankalin ƴan falon kansu, sosai ran Jawaad ke tafasa, ji yake badan wani daliliba da sai yayma Hudah dukan mutuwa yau, saida kuma shi a tsarinsa babu bugun mace. Alhaji babane yace, “Jawaad dawo ka zauna”. Umarnin Alhaji baba yabi, ya juyo tare da zubama Shahudah wani mugun kallo daya sakata sakar masa riga ta durƙushe a wajen tana kuka, kota kanta baibi ba ya koma inda ya taso ya zauna. Ran Alhaji baba a ɓace yace, “Wanene Habib ɗin to dakasa ya aurar musu yarinya?”.
Shima Jawaad ɗin ran nasa a ɓace yake, amma dai sai ya danne cikin ladabtaccen harshe ya bama kakan nasa amsa, “Alhaji baba shine wanda suka biya ya auri yarinyar”.
Kuka Momy ta saka mai ƙarfima kuwa tana zagin Jawaad da ja masa ALLAH ya isa.
Cikin rawar baki Uncle Nasir ke faɗin, “Yanzu nan Jawaad ɗan fir’auna ka aurama Shahudahr?………”
Uncle Sadiq yace, “Wane irin sunane haka kuma Yayah?”. Kasa magana Uncle Nasir.
Dad kam ai hawaye kawai yakeyi kashirɓan, saboda wani irin ruɗani da wautarsa akan sakarma Momy ragamar gidansa yake hangowa. Falon yay tsit kowa na jiran ƙarin bayani daga garesu, yayinda Shahudah dake jikin Momy keta ribzar kuka. Qaseem kansa kawai ya dafe saboda tafasar da zuciyarsa ke masa da matsananciyar ƙuna.
Kowa dai ya fahimci su Mom sune suka gina ramin mugunta wa marainiyar ALLAH daga ƙarshe ya rufta dasu batare dasun fargaba, Alhaji baba ya katse shirun da faɗin, “Bin ƙwaƙwƙwafin komai a yanda yake baida amfani, tunda su bamusan manufarsu ba, a ganina yanzu mafita kawai ya dace mu nema kamardai….”
Qaseem ya ɗago kai, cikin ɗacin rai yace, “Mafita itace wannan yaron ya sakarmin mata tunkafin rayuka suyi ɓacin da yafi na yanzu”.
Miƙewa Jawaad yay cike da takun ƙasaita ya ƙarasa gaban Qaseem sunama juna kalon kallo tamkar wasu zakuna, baki ya taɓe yana binsa da wani banzan kallo, cikin kakkausan furuci yace, “Gurɓataccen tunani kenan Qaseem, domin kuwa wannan shine abinda bazai taɓa faruwaba koda a cikin mafarki, kayi wani tunanin amma ba wannanba” Yaƙare maganar da ɗan buga kafaɗar Qaseem ya raɓashi ya fice daga falon.13
Babu wanda ya iya yunƙurin hana Jawaad ɗin fita har Alhaji baba, dan a ganinsu garama ya tafi kar abin ya kuma ƙwaɓewa tsakaninsa da Qaseem. Asibiti Jawaad ya nufa domin ganin yaya su Bilkisu suka tashi. Saida ya tsaya ya sai abubuwa a hanya dukda yasan za’a kai abinci daga gidan Ummah, mintuna kaɗan ya shigo asibitin, da Nabeelah yaci karo ta fito sayama Ummah kati, ta amshi kayan hannunsa tana masa sannu da zuwa da gaishesa. Bai amsaba saboda waya yakeyi, hannu kawai ya ɗaga mata yay gaba, tabi bayansa tana gulmarsa a zuciya batare daya saniba, hardasu kwaikwayon tafiyarsa.
A ƙofar ɗakin ya tsaya yayma Nabeelah nuni akan ta shiga domin sanar dasu. Da “to” ta amsa, shikuma ya cigaba da wayarsa a nutse, baifi minti biyu da shigartaba tafito tace ya shigo………….✍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.27
Page 25
………….Na daɗe banji irin wannan matsanancin bugun zuciyarba idan na samu kusanci dashi.
Tunda Nabeelah ta sanar da shigowarsa duk sai na nema nutsuwata na rasa, farfesun da Ummah ma ta tsareni naci sai naji ya fitarmin a rai, ƙasa-ƙasa nake kallon ƙofar ta gefen ido harya shigo da sallama, Sanye yake cikin ƙananun kayan nasa na fama, sai dai sun masa ƙyau kamar ko yaushe. Da hannu yake amsama kowa sannun da yake masa saboda waya yakeyi. Ummah ta tura masa kujerar da take zaune a kai ita kuma ta koma kusa dani a bakin gado.
Gaba ɗaya na kasa cigaba da shan farfesun har sai da Ummah taimin magana, “Saifa kin cinye abincin nan tas dota, garama ki dage kafin nasa a riƙeminke namiki ɗura”. Murmushi nai ina satar kallon boss da ƙamshin turarensa ya addabi hancinanmu, kasancewar turaren maza yafi na mata ƙarfi duk sai ya danne namu. A bazata muka haɗa ido, saurin janye nawa nayi dan banyi tunanin kallona yakeba. Farfesun na cigaba da tsakura kaɗan-kaɗan, har yanzu inajin idanunsa na yawo a kaina ko kunyar su Ummah bayaji.
Kusan mintuna biyar ya ɗauka kafin ya ajiye wayar yana faɗin, “Am sorry Ummana nazo ina waya”. Murmushi Ummah tai masa, tace, “Babu komai Son”. Guntun murmushi yayi yana mai risinar da kansa ya gaisheta ita da Mama, kafin ya ɗorama mama da godiya. Mama tace, “Babu komai Jawaad, ai yima kaine, Bilkisu ta cancanci ai mata abindama yafi haka dan yarinyar kirkice mai tarbiyya, mu saidai muce ALLAH ya sanya alkairi a wannan al’amari ya kuma baku zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba”.
Gaba ɗaya ban fahimci kalaman mamaba, dan dama Nabeelah ta shigo ɗazu tana cemin amaryar yayansu, kallonsa naɗan sata sai naga ya amsa da “Amin” akan laɓɓansa. Tunanin ko da aunty Shahudah aka ɗaura masa aurene yasa naɗanji nutsuwa. Ganin ya gama gaisawa da aunty Batool nima nace, “Ina kwana sir”.
Amsamin yay da “Lafiya, ya jikin naki?”. “Alhmdllh naji sauƙi”. Bai sake cemin komaiba ya juya sukai magana da Ummah, sai naga sun miƙe sun fita. Numfashi na sauke a hankali ina rumtse idona, dan fitar tasa yasa naji kamar an saukemin kaya. Babu abinda nake buƙata a halin yanzu kamar ƙarin bayani akan abinda ya faru jiya tsakanina da ƴan gidanmu, banga kowa a cikinsu ba kuma yau tunda na farka, sannan kuma miya faru har aunty Shahudah ta nemi jimin ciwo su aunty Aamilah kuma sukaimin wannan bugun da gashi ya kaini da kwana a asibiti?……..
Ring ɗin wayatane da Ummie ta kawo ɗazun ya katsemin tunani, Nabeelah dake kusa da wayar ta miƙomin tana ƴar dariya, “Matar Yayanmu waye kuma masarauta?”. Wayar na amsa dan karta tsinke batare dana bata amsaba, bayan mun gaisa daga can Amaturrahman ke tambayata a ɗakin da nake?. Mamaki ne ya kamani sosai, ta yaya akai sukasan banda lafiya to? Kodai jiya sunzo ana wannan rikicin da bansan tshensa ba? Tunanin ƙila Ummie ce ta sanar musu ya sakani amsa mata da cewar bara na turo a shigo dasu. Da ga haka muka ajiye wayar, Nabeelah na kalla cikin marairaicewa nace, “Sorry dear, dan ALLAH ki shigo da baƙi wai suna waje”. Cikin dariya tace, “Karki damu matar yayanmu, girmankine ai”. Kasa haƙuri nayi nace mata, “Wai nikam wannan sunan daga ina haka?”. Sosai ta kwashe da dariya tana nufar hanyar fita da faɗin, “A wannan ba hurumina bane, yayanmu zai baki bayani”.
Aunty Batool ce tace, “Fitsararriya ALLAH yasa ya jiki dai”. “Ba amin ba” ta faɗa tana ficewa fuska a kumbure.
Murmushi mukai ni da mama, danni taɓarar Nabeelah dariya take bani, na lura gatane kawai yay mata yawa, ga uwa ga uba ga yayu ga dangi gata auta kuma. Mintuna baifi goma ba sai ga Nabeelah ta shigo dasu Amaturrahman bakinta fal magana da ganin jama’ar kamar jinin sarauta, dan tare suke da hadimai mata uku tare da wani dattijo, sai hadimai maza suma guda biyu.
Tun a waje Jawaad da Ummah dake zaune suna magana akan yanda za’ai da bilkisu kafin lokacin tarewar sukaga Nabeelah dasu Amaturrahman, cike da mamaki suka bisu da kallo, ganin da gaske ɗakin da bily take suka shiga yasasu tasowa suka biyo bayansu.
A waje suka iske hadiman su duka biyar, basuce dasu komaiba suka shiga.
Amaturrahman na zaune a bakin gadon da babu kowa a kai tare da aunty Batool, Marwah tsaye kusa da mama dake a ɗayar farar kujerar ta wancan gadon. sai dattijon kuma a kujerar da Jawaad ya tashi, , sai Safah data ɗane gadon kusa da bily tana taɓa kumburin fuskarta kamar zatai kuka, Bilkisu dai murmushi take mata, dan har cikin ranta takejin ƙaunar yarinyar da wannan shine haɗuwarsu ta biyu.
Jawaad ya ƙaraso suka gaisa da dattijon cikin mutuntawa, fuskar dattijo da murmushi yace, “Ina fatan kaine mijin nata?”.
Wani irin muguwar bugawa ƙirjina yayi, babu shiri na zubama boss ido dan naji amsar da zai bada, saiko naji yace, “Eh nine ranka ya daɗe”. Idanun mamaki na zaro dan nama manta akwai mutane a ɗakin, wata ƴar harara naga ya zubamin ya ɗauke kansa, yayinda shi kuma dattijon ke faɗin yazo zasuyi magana a waje. Binsa yay suka fita. Cikin dawo dani hankalina Safah tace, “Aunty B mijinki mai ƙyau, zaki yarda na zauna gidanku?”. Dariya duk ƴan ɗakin sukayi, bandani dana kasa koda motsi, sai ɗan kaɗama Safah kai nayi kaɗan dan nikaɗai nasan a kalar ruɗanin da nake ciki. Buɗe ƙofar da aka sakeyine yasa duk muka kalli can, shine ya leƙo yay kiran mama da Ummah.
Suna fita naji hawaye sun silalomin, da sauri nai ƙoƙarin gogewa dan banason kowa ya gani, sai dai na makaro dan Safah tarigada ta gani, da sauri tace, “Aunty B miyasaki kuka?”. “Ba kuka nakeba Safah, abune ya shigarmin ido” nai maganar da sauri. Tace, “Aunty B wai kema kina ɗaukata ƴar yarinyane? Nafasan kuka”. Tsawa Amaturrahman ta daka mata da faɗin, “Safah wai miye haka? Ke duk inda kika zauna saikin takurama mutane ne?……..” Aunty Batool ce tai saurin katse Amaturrahman ɗin da faɗin, “Minene abin takura anan ɗin? Ai kulawama take bata”.
Marwah datun ɗazun bayan gaisuwa bata sake maganaba ta harari Safah ɗin da faɗin, “Aunty bakin yarinyarnan ne kamar bai gasuba”. Itama Safah ɗin harar Marwah tayi, tace, “Halan tarene ba’a gasa manaba, manya na magana kina wani tsoma musu baki mtsoww!”. Ƙwafa Marwah tai ta ɗauke kanta bata sake maganaba. Nai murmushi da riƙo hanun Safah nace, “A’a banda faɗa to, Marwah kema zo”. Babu musu ta bufoni, na kamo hanunta na zauna da ita ɗayan ɓangaren itama suka sakani tsakkiya.+
STORY CONTINUES BELOW

A waje kuwa dattijo ya miƙama Jawaad takarda yana faɗin, “Saƙone daga Sarauniyar gagara badau, tace na miƙa wannan takardar ga mijin Bilkisu Adam makaho, ka karanta sannan ka bada amsar da za’a koma mata dashi”. Cike da mamaki Jawaad ya amshi takardar dake nannaɗe an ɗaureta da zare ruwan gwal, yace, “Sarauniyar gagara badau kuma? Ni kaina ya sake kullewa”. Dattijo dai baice komaiba sai murmushi da yayi. Jawaad ya buɗe takarda tareda karantawa a fili domin Ummah da Mama suji abinda ta ƙunsa.
Saida yakai har ƙarshe sannan suka shiga kallon-kallo, dan tayi bayanine a taƙaice gameda sanin Bilkisu da sukai har zuwan su Amaturrahman jiya da sukai tsozali da ruguntsumin da ya faru, a ƙarshe ta nuna buƙatar ganin shi Jawaad a yau zuwa masarauta domin suyi magana.
Jawaad ya kasa cewa komai, sai kallon inda dattijon ya koma gefe danya basu damar tattaunawa yayi, mamace ta katsesa da faɗin, “Jawaad nikam ina ganin kaje ɗin sai kaji minene takeson ji ɗin”. A sanyaye Jawaad yace, “Shikenan Mama zanje, bara na kira Alhaji babba shima na sanar masa”. “Hakan yayi” cewar mama, Ummah dai tama kasa cewa komai dan mamaki, saida mama tace, “Hajiya Mariya bakice komaiba”. Murmushi Ummah tayi, tace, “Abinne aini ya ɗauremin kai, daga tsintar Cards sai kusanci har irin haka ya shigo? Lamarin manyan nanne baka musu gaggawa, amma nima nagoyi bayan maganarki akan yajeɗin sai muji mitakeson su tattauna ɗin”. shidai Jawaad gefe ya koma yayma Alhaji baba bayani ta waya, shi kansa saida ya jinjina abin a ransa, kafin yace to Jawaad ɗin ya jirasa gasunan zuwa asibitin shi dasu Dad zasu duba Bilkisu.
Ciki Ummah da mama suka koma akabar Jawaad tare da dattijo anan waje suna tsumayen zuwansu Alhaji baba.
★★★★★★★
Kasancewar su Alhaji baba a hanya suke lokacin da Jay ya kira sai gasu babu jimawa sun iso, gaisuwa sukai da dattijon da babu wanda yasan daga ina yake sai Alhaji baba, da ido yayma Jawaad nuni dasu jirashi. Jawaad ya ɗaga kansa alamar amsawa. Shikuma yabi bayansu Uncle Sulaiman ciki domin duba Bilkisu.
Dole su Ummah suka fito waje suka bama su Alhaji baba ɗakin dan yamusu kaɗan, Safah da Marwah kaɗai aka bari tare da Bilkisu daketa faman gaishesu kanta a duƙe, dan bata yarda ta kalli kowaba sai da Dad yake matsawa kusa da ita ya ɗago fuskarta yana duba kumburin daya fara sauka da jera mata kalamun ban haƙuri tamkar zai ari baki sannan ne ta ɗago tana ɗan murmushi. “Dan ALLAH Dad kabar damuwa, wlhy ni kawai na ɗauki hakan matsayin ƙaddara da kuskure kawai, kuma nama yafe musu”. Babu wanda bily bata birgeba da kalamanta, wata irin faɗuwar gabace ta riski Alhaji baba lokacin da yay tozali da fuskar Bilkisu, ya kafeta da ido ko ƙyaftawa bayayi, dukda kuwa a kumbure take kaɗan ta gefen haggu saboda duka hakan bai hanashi hango wani abu tattare da itaba. Sam yama daina fahimtar sauran maganar data biyo baya tsakanin Bily dasu Dad, haka kawai ya tafi wani bahagon tunani da shi kansa yasan akwai kuskure a cikinsa. Saurin ture abin yay a ransa suka fito, saida ya kuma waiwayawa ya kalli Bilkisu da batasan yanayiba sannan ya fice.
Dad wajen likita ya nufa dan yaji yaya ake ciki? Su Uncle Sulaiman kuma suka fita domin tafiya gida, a wajen su Jawaad suka bar Alhaji baba shima.
Takardar Jay ya bama Alhaji baba, bayan ya karanta ya kalli dattijon, “Ƙanina zance ko ɗana yaushene akesan ganin nasa?”. Dattijo yay murmuahi da faɗin, “Baba yanzuma zamu iya tafiya, dan zanbar yaran anan muje mu dawo”. Kallon Jay baba yayi, yace, “Shikenan kabisa Muhammad”. Jawaad ya kaɗa kansa da faɗin, “To baba, amma zan koma gida na canja kaya tukunna”. Alhaji baba yace, “Ato ai maganinku kenan, ƙiri-ƙiri kun ajiye suturar mutunci kun biyema ta yahudu, saboda irin haka muke muku faɗa akan kuna tunawa da naku suturar kuma, dan sune kayan da zakuje gaban ko wanene batare da kunji nauyin hakanba”. Shidai Jawaad baice komaiba, sai dattijon masarautane keta murmushi da faɗin, “Wannan gaskiyane baba”.10
★★★★★★
Sosai nake a cikin ruɗani da neman mai min ƙarin bayani akan wannan rikiɗaɗɗen al’amari, ina Yah Qaseem ɗina ya shiga da har ake jinginani matsayin matar boss?, shin wai mike faruwa hakane ni bilkisu? Mizaisa aitamin magana a curkuɗe?, a rasa maimin bayanin dazan fahimta. Koda su Oga Hafiz ma sukazo dubani harda matansu, matan sai faman yimin addu’ar fatan alkairi suke da faɗin, wai boss ya dace da matar da suka dace da juna, hakama da Ummie ta dawo tare da ƴan gidansu Momynta da Dady sunata min addu’ar ALLAH yasa hakan shine mafi alkairi, musamman ma Daddyn Ummie danaga tsantsar farin cikin hakan a garesa har suka tafi. Amina ma da Yayansu sunzo sunyi nasu kalar farin cikin, hakama Ummah ƙarama da naji suna faɗi da yaranta da tazo, sai murna suke da kasancewata wai matar ɗan uwansu. ‘Oh ALLAH! wannn wane irin ruɗanine haka?; Ina ƴan gidanmu suke? Dad kawai na gani, amma ko Yah Qaseem ban ganiba, shin ina ya shigane??. Haka naita juya wannan tunanin a raina, yawan jama’a da keta shiga da fici ya hanani sakat ɗin dazan samu na tambaya. A gefe kuma inajin daɗin ganin nima ashe mai mutanece? Ashe inada gatan dazan kwanta ciwo har mutane irin haka suyita tururuwar dubani?. ban sake ganin boss ba har sai bayan sallar zuhur.
STORY CONTINUES BELOW

★★★★★★
A ɓangaren Jawaad kam kamar yanda ya roƙa alfarma ga dattijo saida suka biya ta gida ya shiga ya sauya kayansa da ɗanyar shadda fara tas da tasha ɗinkin zamani, yaukam hardasu hularsa zannah ainahin nutsatstsiyar saƙar barnawa ta asali sai ƙyalli take, duk wanda ya gansa yaga sabon ango dukda bai shiga daga cikiba😂, shi kansa dattijon tunda Jawaad yafito daga gate ɗin gidan kasa ɗauke ido yay daga kallonsa, a fili ya furta ‘Masha ALLAH ’. Drivern dake jan motarma bai iya ɗauke idanunsaba har Jawaad ya shigo.
Sun isa katafariyar masarauta mai daɗaɗɗen tarihi da gininta na ɗaya daga cikin manyan gine-ginen da ake lissafasu a sahun farko na yankin masarautun afirika baki ɗaya saboda ƙawatuwarsa da gini mai nagarta data samu, gashi a koda yaushe cikin sake fidda masa wasu tsare-tsaren akeyi masu matuƙar sake ƙawatata. Wannan shine zuwa na biyu da Jawaad yayi cikinta, dan sun taɓa zuwa gaisuwar salla wa sarki Sameer tare da tawagar Gwamna a shekaru uku kenan da suka shuɗe. Sai dai a wannan karon sosai yaga sabbin tsare-tsare da tarin cigaban da yafi na wancan lokacin, bayi sai zubewa suke suna gaisuwa a garesu saboda wanda suke tare, shi kansa Jawaad ɗin kallon wani jinin sarauta suke masa saboda kama yake dasu ta siffofi da dama.
Jawaad mutumne shi mai nutsuwa da aji, sanan yanada tsari, bai damu da abinda babu ruwansaba komai ƙawarsa da abubuwan kallon cikinsa, wannan halin nasa na yima abu kallon ko in kula yasa sam bai zama ya rikice wajen kalle-jalleba a masarautar dukda ta cancanci a tsaya ƙare mata kallo harda son yin hotunama a cikinta. Tafiyarsa yake kai tsaye tamkar ko yaushe a kuma ko ina ya tainci kansa, bajinta, nutsuwa, da tarin ƙasaita kawai zaka hanga a takun nasa, waɗanda basu da fahimta akan halayyarsa harma zasu iya haɗawa da Izza da girman kai, sai dai kuma sam ba haka baneba, tun asali haka ALLAH yayisa tamkar wani jinin mulki wajen girmama nutsuwa a dukkanin al’amuransa koda akwai ruɗarwa a cikinsu kuwa.
An saukesa a katafaren falo mai cike da abubuwan ƙawa da birgewa, cikin mintuna ƙalilan aka cika masa gabansa da kayan ciye-ciye da har yake tsogumi a ransa wai ‘Kamar wani mai cikin zani’ (😂kujifa daga abun arziƙi. Lol🤣)
Bai taɓa komaiba bayan ruwa a kayan da aka jibge masa, dan shi ba ko ina yake sakin jiki yaci abuba (Yau naga mai irin halin babana a iya fulako😍, ALLAH ya gafarta maka baba😥🙏🏻). Cikin nutsuwa yake ɗanbin falon da kallo da jinjina daular dake ciki tamkar babu talaka mai buƙatar abinci da rigar sawa da kuɗin magani a duniya, yaɗan taɓe baki yana gyara zamansa, sam shi fariyya bata birgesa, dukda kasancewarsa mutum mai tarin dukiya bai taɓa sha’awar yin abinda ya fice hankaliba a hidimar rayuwarsa, dai-dai da motar hawansa guda biyuce kacal a duniya, hakama suturar sakawarsa akwai adadin da yake ajiyewa, ya gwammace duk sanda zai ɗinka wasu kayan ko ya saya to ya fidda tsoffin ya bada kafin ya ajiye wasu, baya sha’awar tsube sutura a drawer harya mance randa ya sake maimaita wata………
Tunaninsane ya katse saboda sallamar da akayi a ƙofar falon, ya amsa yana gyara zama da tsumewa cike da kame kai. Hadimai mata guda biyune suka shigo, cikin girmama suka gaidashi kafin su sanar masa zai iya tasowa gimbiya ta fito.
Kansa kawai ya iya jinjina musu, ya miƙe tare da jefa wayarsa cikin aljihu yabi bayansu. Ƙaramin falone madaidaici, sai daifa ya haɗu harma ya gaji da haɗuwar, Hamshaƙiyar mace mai cike da tarin kamala da kwarjini da bazata gaza shekaru arba’in da biyar ba a duniya tana zaune, sai ƙamshi da walwali take cikin alƙyabbar da kallo ɗaya zakai mata kasan an sayeta da kuɗaɗe masu daraja. Gimbiya Munaya Awwal fharok kenan, sarauniyar gagara badau mai lokaci da amfani da damarta tana damawa yanda ya kamata, matar sarki Sameer saifudden Abubakar adalin sarki mai mulkin dake tafiya da koyarwar addinin islama da zamani, cikakken sarki mai iko da ƙasaita, adali mai tarin ilimin addini dana zamani, wanda yasha gwagwarmayar rayuwa tunkan rayuwar tagama sanin shiɗin wanene.
Da hannu gimbiya munaya taima matashin saurayi Jawaad nuni da wajen zama, bata haifi kamarsaba, amma kuma ta girmesa a shekarun haihuwa. Cike da nutsuwarsa ya zauna, kafin ya risina cikin girmamawa ya shiga gaidata. Gimbiya munaya tai murmushi mai ƙayatarwa dan Jawaad ya birgeta ainun, daganinsa zakasan yajiƙu da tarbiyya tsaftatacciya. Cike da ƙasaita tace, “Kana lafiya?”.
Jawaad ya amsa da “Alhmdllh ranki ya daɗe”. Murmushin ta sakeyi, kafin ta cigaba da faɗin, “Kana tare da Uwargidan Sakin gagara badau Sameer Saifudden, nasan kana cikin ɗunbin mamakin kiran gaggawa da nai maka wanda ni kaina bansan dalilin hakanba, kawai dai ina danganta lamarinne da tsantsar ƙaunar danaga gudan jinina tanama wadda banmma taɓa ganiba mai suna Bilkisu da a jiya nake samun labarin an ɗaura maka aure da ita, hakan kuma yazo da rikicin da ita Bilkisun ke buƙatar taimako”.
Jin tayi shiru Jawaad ya jinjina mata kai, cike da girmamawa yace, “Hakane ranki ya daɗe”. “Idan ban shiga hurumin daba nawaba inasonjin wani abu koda zan iya bada gudunmawa ta, dan a yanda yarana suka bani labarin abinda ya faru da Bilkisu hakan ya matuƙar tsayamin a zuciya a daren jiya”.
Murmushi Jawaad yayi, dan haka kawai yaji ƙaunar gimbiya munaya har cikin ransa, batare da tunanin komaiba ya buɗe mata cikinsa gameda abinda ya faru akan auren nashi da Bilkisu. Shiru gimbiya munaya tai tana nazarin maganganun nasa kafin ta sauke numfashi, cike da ƙasaitarta tace, “Jawaad!, a ɗan guntun hangena na fahimci akwai matsala babba dai dake a ƙasa wadda kaima kanka kakeson bincikowa? Hakan ya birgeni, dan inason jarumin namiji mara tsoro mai ƙwazo tamkar mai martaba na, zan baka gudunmawa akan dukkanin shirinka ɗari bisa ɗari, dan bansan mi UBANGIJI ke nufi da wannan haɗin namuba ta dalilin Safah da kullum bakinta bai gajiyawa da ambaton Aunty B”.
“Godiya muke ranki ya daɗe da wannan karamci, ALLAH ya ƙara lafiya da nisan kwana mai amfani”. Murmushi gimbaya Munaya tai tana maijin daɗin karamarwar Jawaad a gareta, sannan ɗabi’unsa sunyi matuƙar birgeta, idan badan ya faɗaba babu yanda za’ai kai tunanin yafitone daga tsatson tsohon shugaban ƙasa Marigayi Abdul-aziz yusif tafida, adalin shugaba da su kansu masarautarsu tayi ƙyaƙyƙyawar alaƙa dashi a lokacin mulkinsa na shekara huɗu a gwamna ɗaya a shugaban ƙasa, a yanzu haka kuma dukkan kayan itatuwa da kaji dawasu abubuwan da suka shafi gona ana kawomusu shine daga gidan gonarsa……… Kauda tunanin nata tai Tace, “Shikenan Jawaad, yanzu mataki na farko da zamu farabi shine ina buƙatar Bilkisu ta dawo masarauta da zama, dan komawarta gidansu bazai haifar da ɗa mai idoba kodan dalilin ita tsohuwar matar taka da tsohon saurayinta da kuma mahaifiyarsu, zata zaunane na gajeran lokaci daganan zuwa bayan sallar kamar yanda kuka tsaida tarewarta, dan itama tana buƙatar ai mata auren gata tamkar kowane mace mai iyaye kodan hakan yazama izina ga masu irin halin Gwaggonka dake tunanin su kaɗaine a sama babu mai taddosu, inason susan babu wani bawa ƙasƙantacce sai wanda ya ƙasƙantar da kansa ga barin bautar ALLAH saboda son zuciya…………..✍40
Ina godiya gareku akan addu’oin da akaita zubami harda masu kira da masu turo saƙo, naji sauƙi Alhmdllh sai dai inajinran manyan ledojin kayan dubiya😆😋.15
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻21
Page 26
BARKA DA JUMA’A
…………..Jawaad da yay ɗan jim fuskarsa ɗauke da murmushi yana juya maganar gimbiya ta ƙarshe a ransa, koba komai ya sakejin kimarta, domin ta nuna tanada ƙyaƙyƙyawan tsari da tausayi akan talakawa. yace, “Shikenan ranki ya daɗe, ke uwace, kinada damar yanke duk hukunci daya dace a kanmu koda babu saninmu, sai dai ina neman alfarmar zuwa na sanarma kakana da kuma ƙannen mahaifiyata, zuwa gobe insha ALLAH zan dawo na sanar miki yanda mukayi”.
“Wannan tunanin naka shine ƙyaƙyƙyawan tunani da yakamata ya fito daga bakin jajirtaccen ɗa mai riƙo da tarbiyyar magabatansa, kaje ka sanar musu ɗin babu damuwa, sai dai zan baka shawarar koda likita yace zai sallami bilkisu kace ya jinkirta zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu, dan nafison da an sallameta kawai nan za’a wuto da ita”.
Kansa ya jinjina mata. Ta ɗauki ɗaya daga cikin wayoyinta masu azabar ƙyau ta miƙa masa, “Kasaka Number ka anan, saika ɗauki tawa yanda idan sun amince ɗin zakai kirana ka sanarmin basai kayi wahalar zuwa ka koma kawomin bilkisu ba kuma”.
Tasowa jay yay ya amshi wayar, Number sa ta musamman da wanda ya yarda kawai kuma yakeda kusanci dashi matuƙa kawaine ke da ita ya saka mata, sanan yay kira yaga tata, saving yay mata da Jawaad A yusif ya maida mata yana godiya.+
___________________________________
Tare Jawaad suka dawo da dattijon nan dan zai juya dasu Amaturrahman masarauta.
Shi kaɗai ya shigo ɗakin da sallama ciki-ciki kamar yanda ɗabi’arsa take ta rashin son hayaniya, babu kowa a ɗakin, Safah kaɗaice kwance tana barci a gadon da Bilkisu ke jiyya, mamaki ya kamashi da tunanin ina suke har ita Bilyn?. kafin yay yunƙurin yin wani abu aka buɗe ƙofar toilet, Bilkisu ce ta fito ɗaure da zani, ta yafa ƙaramin towel a kafaɗarta da alama wanka tayo saboda yanda ruwa ke jiƙe da fuskarta, duk tsefaffen gashinta ya kwanto goshinta da gefen kumatu.
Wani faɗuwa gabana yayi dan banyi tunanin iske kowaba tunda su Nabeelah sunce zasuje sallah, Mama kuma tunda ta gasamin jiki ta fita akan zata ɗauraye kwankikan da akaci abinci, bawani ƙwarin jikin nakejiba dama, dan dukan da sukaimin yasa jikina yin tsami ko ina ciwo yakemin, wai danma Doctor ya bani maganin ciwon jiki nasha. Nakasa koda ɗaga ƙafata da sunan juyawa baya, sai kawai na duƙe a wajen inaji tamkar ƙasa ta tsage na shiga ciki dan matsananciyar kunyar data riskeni, nice yau tsaye gaban boss babu riga? Dagani sai zani da ƙaramin towel ɗin dana yafo a kafaɗa, kaina sanye da hular wanka, dukda nasan fuskata kawai zai iya gani da hannayena zuwa gwiwa, sai ƙafafuna suma iya rabin ƙwairi dan zanin ya sauka min ƙasa sosai duk da ɗaurin ƙirji nai dashi, hakan ba ƙaramin abun kunya bane a gareni.
Ɗauke kai Jawaad yay daga kallon daya kafeta dashi yana mai lumshe idanu a hankali da furzar da sassanyar iska daga bakinsa, baice da ita komaiba ya juya ya fita zuciyarsa na gudu da sauri-sauri.
Hawaye nake kashirɓan da bansan dalilinsuba sam, dukda naji ƙarar buɗe ƙofa da rufewa alamar ya fita na kasa miƙewa tsaye bare na tashi. “Bilkisu lafiya kuwa? Ko jiri kike ganine?”. Muryar mama ta dawo dani hankalina. Saurin ɗago kaina nai ina share hawayen da suka jiƙen fuska, ganin dagani sai ita a ɗakin yasani sauke numfashi ina mai ɗaga mata kai alamar juwarce. Kwanikan hannunta ta ajiye tazo ta taimakamin na tashi tsaye, da taimakonta muka ƙarisa bakin hadon dan a gaske yanzun saima nakejin tamkar juwarce tazomin, ita ta taimakamin na shirya, ina kammala shiryawa su Nabeelah da Amaturrahman da Marwah na shigowa. Sannu suka yimin kafin Amaturrahman ta shiga tada Safah tana faɗin Su zasu wuce gida, jinai kamar nace su zauna, amma banda wannan ikon, ga Safah ta sanya kukan shagwaɓa akan itafa anan zata zauna tare dani. Ina mamakin wannan irin ƙauna da Safah ke nunamin.
Kafin kowa yace wani Abu boss ya shigo ɗakin da sallama. Nidai ƙasa nai da kaina ban yarda nako saci kallonsaba, tambayar da yakema Safah akan mitakema kuka kawai naji, Nabeelah ce ta bashi amsa da cewar tace bazata tafiba anan zata zauna wajena. Banji ya bata amsaba, sai saukar hannunsa naji akan nawa dake riƙe dana Safah, a take tsigar jikina ta tashi, gashi har yanzu akwai damshin ruwa jikina dama, ya cire hannunta batare da yace uffan ba, binsu da kallo nai ta ƙasan ido har sukaje gab da ƙofa. Ranƙwafawa yay yaymata maganar da duk bamujiba a cikin kunne, ta ƙyalƙyale da dariya tana tsalle, shima wani shegen murmushi ya saki maiban mamaki, Safah tace, “Amma Yayanmu (Yanda taji Nabeelah na faɗa) kafin goben zaka rama mata dukanta ko? Inba hakaba saina saka Abbu ya turo sarkin tsabga na masarauta ya musu dukan mutuwa da dorinarsa”.
Janyeta yay daga jikinsa da take neman shigewa yana lumshe idanu, a hankali yace, “Karki damu zan rama mata da kaina”. Sosai ta shiga daka tsallen murna Nabeelah da Mama na dariya harma da Amaturrahman, Marwah ce dai tai murmushi kawai tana rakuɓewa a jikina, juyowa yay muka haɗa ido nai saurin janye nawa, da hannu ya yafito Marwah alamar taje itama. Da sauri kam ta nufesa cike da ɗoki harda murmushin daya bama kowa mamaki, dan tunda tazo taƙi sakin jiki da kowa. Hannunsu ya kam suka fita, Amaturrahman taimin sallama tabi bayansu tare da Nabeelah da zatai musu rakkiya, mama kuma ta bisu da kalaman godiya dana addu’a. Nima haka godiyar nake musu har suka fice.
STORY CONTINUES BELOW

Bayan wucewar su Amaturrahman Jawaad bai koma cikiba, mota ya shiga yabar asibitin. Kai tsaye gidan Alhaji baba ya nufa, harya zauna kusa da Alhaji baba baisan ya shigoba, saida Jawaad ya kwanta tare da ɗora kansa a cinyar kakan nasa sannan ya kawo numfashi. Cike da mamaki jay yace, “Tunanin mikake haka da zurfi sofo?.”
Shafa kan Jawaad yay cikin ƙoƙarin danne damuwarsa yace, “Kaima zaka tsufan wataran ai, ango mai rinton mata, yaya kukayi dasu a masarautan?”.
Dariya Jay ya ƙyalƙyale da ita yana faɗin, “Ashe dai ni jarumine tunda gashi na ƙwace kuma dole a barmin. Ka fara gayamin damuwarka Baba sai na faɗa maka nima”. Jay yay maganar cike da kulawa ga kakan nasa abin ƙaunarsa. Sosai Alhaji babba ya sake danne halin da yake ciki ya nunama Jawaad bashi da wata damuwa, badan Jawaad ya aminceba ya haƙura, sannan ya zayyane masa duk yanda sukai da gimbiya Munaya. Alhaji babba yace, “Banƙi ta tataba, sai dai kuma kai kana ganin babu damuwa?”.
Zaune Jawaad ya tashi sosai, yace, “Amincewarka ni itace kawai tawa baba, dan kaine zaka hangomin abinda ya dace da wanda yake kuskure saboda kana gaba dani, dalilan data kawo na komawarta gidan Dad abin dubawane, nikuma gashima ban shiryama maganar tarewar tataba saboda akwai ayyukan da gidan da zan ajiyeta yake buƙata, tunanin da nake dai bai wuce dama ta koma gidan Ummah babba ba, dan dama ni ban tsara zata koma can gidanba saboda haɗarin dake tattare da hakan koda Qaseem da Hudah da Momynsu.
Alhaji baba yace, “Lallai kayi tunani mai ƙyau, yanzu dai ka bata dama, dan kowa yanama Uwargidan sarki ƙyaƙyƙyawan sheda akan adalci da shiga matsalar talakawa da ƙarfinta da dukiyarta, to akanku wannan ba sabon abu bane, bakuma yauta faraba, shiyyasa banajin wani ɗar balle tunanin akwai wani manufa a lamarinata”
Jawaad yace, “Shikenan Alhajin ALLAH zanyi yanda kace”. Daga haka hira sukaɗan taɓa zuwa sallar la’asar, daga nan Jawaad yay masa sallama ya wuce gida, dan a matuƙar gajiye yake, rabonsa daya huta tun daren alhamis ranar laraba kenan, gabaɗaya bai hutaba, a hankali ya furta, ‘Dukta cinyemin lokaci ta gajiyar dani’ ya ƙare maganar daɗan lumshe idanu ya buɗe akan titi.
iske gidan nasu yay kaca-kaca anata hayaniya, dai-dai sashensa yay fakin inda ya saba, ya fito fuska ɗaure batare da ya kalli kowaba a cikinsu ya shige abinsa, dan ya fahimci cecekucen maganar aurence suke har yanzu, shikam a tsarinsa duk abinda ya gama da matsalarsa to yagama kenan baya sake waiwayensa sai dai kuma sabo idan ya taso.
Yanda suka ganshi a tsume yasa aka rasa mai tunkararsa da magana dukda kuwa shigowar tasa suke jira dama, Hatta da Momy da Shahudah duk suna gidan sunzo saboda mama Atika data buƙaci ganin Momy, ga kukan da Shahudah keta dirja tunda Jawaad ya baro gidan. (Kaike musu yanda kaso ace ɓarnar motace, inba kaiba saiwa ɗan Abdul’aziz😂, kaikeyi kayi kuma kamar bakaiba dole a ganka a ƙyale🤣🤣).
Yana shiga falonsa ya dannama ƙofar key yana jan wani wawan tsaki, a kwanakinnan ko shara sashen baya samu saboda yaraba hankalinsa biyu, ga matsalar aiki ga matsalar cikin gida, duk ƙura ta kwanta bisa kayayyakin falon, haka ya tsallake yanzunma ya haye sama, canɗinma dai yay ƙurar sosai, bai kulaba ya ƙarasa bedroom, shi daɗan sauƙi saboda ana zama, gadonma a gyare yake, ga mayen ƙamshinsa daya kama ɗakin na nan, kayan jikinsa kawai ya rage, dagashi sai boxer ya haye gadonsa yana lullumshe idanu. Cikin ƙanƙanin lokaci barci mai nauyi yay awon gaba dashi (Barcin bayan la’asar baida ƙyau Jay🤦🏻). A hankali numfashin Jawaad ya ƙara nauyi alamar barcinsa yayi nisa, mafarki mai sarƙaƙiya, wanda a cikinsa aka sake maimaita masa kalmar “(Ƙaddarar haɗuwar Jini a cikin jini da zai zama jini a yanzu ta zama tabbatacciyar alaƙa da zata zama sanadin buɗe ma’anar jini a cikin jini, takuma warware sirrin ɓoye, Kuzama masu addu’a, dan lokacin da ƙullalliyar sarƙaƙiya mai cike dacin amana zai bayyana yayi, dolene maciya amana, amana tacisu suma, dolene waɗanda sukai shuka su girbe abarsu dai-dai da abinda suka shukaɗin tun a duniya kafin aje babbar kotu kowa ya amshi sakamakonsa, dolene gorar da azzalumai suka fafe dan tafiya ta buɗe a yanzun da suke gab da kaiwa ƙarshen tafiyar tasu, ɗan zaki ya girma, kaine jagoran fidda ƘWAI CIKIN ƘAYA, karkuyi wasa da addu’a!! dan itace babban takobinku na yaƙar wata riundina ta azzalumai masu son zuciya, gaggawarku zaizama sanadin tonuwar wasu jinane da aka kwarayar. wannan itace ƙaddararku, ƙaddara mai sarƙaƙiyar data saƙa jini a cikin jini, karku manta! Addu’a!! Karku manta!! Karku manta!!)”. Cike da firgici Jawaad ya farka, ya jiƙe sharkaf da gumi dukda kasancewar yammace mai cike da ni’ima canjawar iskar farkon damuna, ɗan zafi-zafin dake garin bashida gallazawar da zatakai mutum da irin wannan zufar da yakeyi, gaba ɗaya jiyay ɗakin na juya masa tamkar hajijiya, ya dafe kansa da hannu yana karanto addu’oin da duk sukazo masa kan harshe. Ya ɗauki tsahon mintuna zaune kafin yaji ɗakin ya tsaya dai-dai, ya sauke hannunsa yana furzar da iska zazzafa, idanunsa sunyi wani irin kaɗawa sunyi jazur, wannan wane irin mafarkine haka? miyasa yaketa maimaita kansa garesa? Akan wa ake masa wannan nunin?; ‘Ya ALLAH ka warwaremin abinda banida ilimin saninsa, ka haskamin abinda ya kasance duhu a gareni, ka jagoranci tunanina akan abinda kakemin ishara dashi acikin barcina’. Idanunsa ya sauke akan wayarsa dake haske, kamar zai share sai kuma dai ya ɗauka, ashe yayi barci mai tsaho, ga magrib harta gabatoma, saƙon da’aka turo masa ya buɗe, sanin muhimmancin wanda ya turo masa saƙonne yasashi nutsuwa ya karanta abida ya rubuto.
“Oga na shirya faɗa maka komai a yanda yake, ina kuma buƙatar a bani matata itama, amma akan farashin kuɗaɗe, kabani address ɗin inda zamu haɗu, sannan kazo da naira miliyan hamsin, nikuma zan baka labari mai matuƙar tsada akan kai kanka bayan nata itama”.
Naka ɗan fir’auna.
Ƙaramin tsaki Jawaad yaja yana mai dafe goshinsa da hannun damarsa tare da murzashi da ƙarfi, da ace ya iya kuka akan komai da a yau zama zai kawai yayta kuka har sai ya ƙoshi dan kansa yay shiru, to amma a tsarin wannan harƙallar kuka a garesa kasawace. Miyasa ɗan fir’auna yace yanada labari a kansa? Kenan shima su…. Ya haɗiye abunda ke neman toshe masa numfashi da sauri yana girgiza kai da faɗim, ‘No…’ bazai kasance hakaba. Komawa yay baya ya sake zubewa a gadon, ƴar ƙarar da agogon ɗakin yayce ta sakashi miƙewa kuma zumbur. Toilet ya nufa, ya sakarma kansa ruwa na tsahon lokaci kafin yay wanka ya fito ɗaure da alwala yay gaggawar shiryawa ya fita.
STORY CONTINUES BELOW

_________________________________
Ganin mutane sun sassauta zuwa dagani sai Mama a ɗakin da Ummie yasa nai dauriyar tattaro dukkan abinda ke raina ina mai kallonsu, “Mama!”. “Na’am Bilkisu ya akai?”. Tafaɗa tana ɗago kanta ta kalleni, Ummie ma daina latsa wayar tai ta maido hankali kanmu. Cikin bama kaina ƙwarin gwiwa nace, “Mama dan ALLAH mi yake faruwa? Gaba ɗaya tunanina ya kulle bana fahimtar komai daga kalaman mutane wanzu daga safiyar yau har kawo yanzun?”.
Murmushi maman Amina tayi, sai kuma ta taso zuwa inda nake ta zauna a bakin gadon, hannunta ta saka ta kamo nawa, har yanzu fuskarta da murmushi, “Bilkisu ya kamata dama kisan miya farun kodan kiyaye girman nauyin dake kanki a halin yanzun, danke ɗin matar aurece da haƙƙinta ya koma kan wani”. Banji komai dangane da kalamantaba face wani mummunan faɗuwar gaba da harbawar zuciya, ta cigaba da faɗin……………….
Wani irin mazarin rawa jikina ya shigayi hawaye na rige-rigen sakkowa akan kumatuna, cikin matuƙar rawar leɓe dana harshe nace, “Mama! Ki..k…kina nu..fin ni aka ɗaurama aure da BOSSS!!!?”. Mama tace, “Bafa bos nace mikiba, Jawaad! Nace”. “Innalillahi….” Na shiga ambata, yayinda Ummie ke ma mama ƙarin bayanin cewar Boss ɗin ai Jawaad nake nufi nima, haka muke cemasa a wajen aiki. Mama tace, “Ayyo, aiban fahimta bane ƴannan”.
Komai nama daina fahimta, wani irin zazzafan zazzaɓi nakeji yana saukarmin, cikin lokaci ƙanƙani nafara rawar sanyi, tunani kalma ɗaya acikin abinda mama taimin bayani na kasa nutsuwar yi, ni Bilkisu Adam makaho ce aka ɗaurama aure da Boss ɗinmu, JAWAAD ABDUL-AZIZ YUSIF!!? dama na jima zuciyata na kokwanto akan rashin damuwar da bangani a tattare da Momy ba akan aurena da Yah Qaseem, miyasa Momy ta zaɓi rabani da masoyina wanda na ɗauka dukkan yardata na bashi? Bazan ɓoyeba ina ƙaunar Yah Qaseem sosai, sannan ban tsani Boss ba dan yanada nagartar da dukkan macen ƙwarai zataso mallakarsa matsayin mijin aurenta, to amma yaya zanyi da aunty Shahudah da dukkanma ahalina? Wannan kuwa bai zama cin amanaba ga Dad da halaccinsa a gareni?. ‘To ai bake kika ce a ɗaura miki aure da boss ɗinba ko’ wata zuciya ta ayyana min daga can gefe kuma wata tace, ‘Bakuma kowa zai fahimci bakida hannu a cikiba kamar yanda mama ta faɗa miki dangin Momy na ambata hatta da Yah Qaseem dayasha gargaɗinki akan mu’amularki da Boss ɗin’. Sharr na matso wasu hawaye masu zafi da suka cikan ido. A fili na furta, ‘Innata miyasa rayuwa takemin hakane? Miyasa duk yanda naso ƙoƙarin raɓar duniya saita goce mani? Tunda na rasaki keda Abba ban sake hawa dokin da yay daidai da cikar dukkan burukanaba, dana hau matakin nasara sai ƙaddara ta sake zuwa ta datse zaren da nake tafiya da ƙwarin gwiwata a kansa, kune kuka sanarmin duniya ba komai bace face wani filin gwagwarmaya na ƙwanji da zuciya, kune kuka tabbatarmin jajircewa na iya zama babban ƙawance da duniya koda duniyar bata buƙatar hakan, miyasa ni tawa jajircwwar a kullum nisantani take da tawa duniyar, shin gaggawa nake a cikin al’amarina shiyyasa nake durƙushewa kafin nakai kokuwa tawa ƙaddarar kenan kullum a curkuɗe?….”
“Wannan ai itace tabbatarciyar nasara kuwa Bilkisu, duk ɗan adam ɗin dakeji a zuciyarsa shine kaɗai wane, shine kaɗai za’aita kira wane daga farkon ƙarni har ƙarshensa to ya tabbata akwai ganganci da tarin wauta a al’amuransa, nasarar mai nasara itace ƙalubale, kadingaji kamar baka kaiba, baka cancanci kaiwaba, bazaka ka kaiba, sai kaga watarana ka kai harma ka wuce, lokacin da wani yake ganin ya rigaka ɗauka baka da damar ƙwata babu zato saiya suɓuce masa wajen hura hanci da gadara kai ka tsinta a ƙasa amatsayin shara kaci kai nagartar da har abadan bashi da damar hangokama, wannan rubutacciyar ƙaddarace ga mafi yawan mutane marasa gata, duk wanda ake ganin bai kaiba ko bazai kaiba shike wucewa wataran bilkisu, Jawaad shine mijin da yafi cancanta da nasararki, UBANGIJI kuma yafiki sanin miyasa ya zaɓa miki shiɗin, karki damu da adawa ko tunin kinci amana, a sannu duhun da kike ganin yana binki zai yaye yazama haske, a sannu waɗanda suke ganin keɗin baki cancantaba zaki zame musu hasken da zai mamaye rayukansu, ba’a cika baki da nasara, ba’a cika baki da farawa, ba’a cika baki da iyawa, ba’a cika baki da cancanta, ba’a gadara da abinda baka da ikon dawwamar dashi a hanunka tunda kaima a wajen wani aka amsa aka baka, dagaske duniya rigar aro ce bilkisu, duk taƙamarka da ita da alfahari wataran saika tuɓeta da mutunci koda ƙasƙanci, duk abinda kaga kayi a duniya koka tsinci kanka kafin kai anyi dubunka masu ninkin banikin ɗinsa, bayanka kuma wasune zasu amsa su dama ko kaƙi ko kaso. Dan haka ki godema ALLAH da ni’imar da yay miki na mallakar miji mutumin kirki da bai ɗau duniya komaiba matsayin, dukda tarin dukiya da ALLAH ya bashi tun yana ƙanƙaninsa, shiba duniyar bace a gabansa, dan da itace bazai taɓa rabuwa da ƙyaƙyƙyawa irin Shahudah ba data haɗa komai na gata da nasaba ya ɗaukeki a matsayin ƴar riƙo a gidansu, wadda suke kallo ƙasƙantacciya a cikinsu. Akwai hikima mai yawa a al’amuran UBANGIJI bilkisu da jahili baya ganinsu ta fuskar data dace kinji”.
Kaina na gyaɗa mata a hankali, dan kalamanta sun sakani jin sanyi a raina, sai dai ina jinjina yanda zan rayu da mutum murɗaɗɗe mai wulaƙanci da ƙasaita irin Boss, aɗan zaman danai dashi na fahimci abinda ba’a sakashiba sam baya burgesa balle ya tsoma kansa. To miya kawosa cikin nawa lamarin ni kuma?.
Wannan itace tambayar data tsayamin a rai har dare.2
___________________________________
Zaune yake a ɗaɗɗaure, an ɗaure masa idanu da jan ƙyalle, bakinsa ma a liƙe yake, shi kansa baisan a ina yakeba, abinda kawai ya sani da zai iya tunawa shine.
Ranar juma’ar da aka ɗaura auren su boss, lokacin da ake tsaka da wannan dambarwa ta neman sanin wanda ya rikita tsarin auren, yabi sahun masu gani da ido babu damar tofa albarkacin baki, har aka gama rikicin massallaci aka nufi gida, baiga boss ɗinsaba, dama baisa ran ganin nasanba a wannan lokacin, ganin su dad sun ɗunguma gida shima saiya hau napep domin komawa gidan ya ɗau jikkarsa ta tafiya gida weekend kamar yanda ya saba, dama sunyi sallama da boss tun a daren jiya, hakan yasa bai damu daya kirasaba koya jirasa. Shiru gidansu boss yake babu wata hayaniya, dan duk suna gidansu Shahudah, Mama Atika da mama badiyya dake fama da jiyyane kawai a gidan sai hadimai da samari waɗanda baza’a rasaba da suka dawo daga wajen ɗaurin aure. Jikkar kayansa ya ɗauka ya fito bayan sunyi sallama da baba mai gadi, cike yake da nishaɗi akan yanda auren ya kasance, Boss ya samu wadda yake masa fata tun sanda ya fara ganinsa tare da ita, yana gab da barin layin wayarsa tai ring, cirowa yay ya duba, gani mamansace yay murmushi tare da ɗagawa yana waige-waige, saida ya tabbatar babu kowa ama kusa dashi balle yay tunanin za’a jisa kafin ya fara maganarsa kai tsaye cikin zaurence kamar yanda suka sabayi. “Mamana albishirinki?”…………..✍22
Karku rikice, muje zuwa page 27, danjin ina aka dosa, nasan dai dayanku sun fahimci kowanene ma kafin akai ƙarshen zance😉🤫👌🏼.25
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu. 09032345899 sai kunzo😍😍😍😘.2
masu buƙatar link ɗin telegram kuyi haƙuri baya nunawa anan, amma insha ALLAH a page ɗin dazaiyi yawo a watsap da facebook zan saka saiku ɗauka acan.
Musha weekend lafiya, maybe kuma ku ganni lahadi koma gobe idan ALLAH ya kaimu.😍😍😍😍.34
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭28
Page 27
……………..Daga can akace “goro yaron alkairi”. Ya cigaba da faɗin, “Da alamafa damunar bana zatai ɓarna, dan na hangi ɗakunan mutane da yawa sun buɗe ta sama batare da sun fargaba, kuma lallai bular zata zubda yoyon ruwan da zai iya haifar da ambaliya”. dariya ta tuntsure dashi daga can, tace, “Ɗan alkairi kana nufin dai dara zataci gida kenan, ɗan zaki yafara buɗe idanunsa ga rundunar kuraye masu gudun tseren neman abinci koda bai kasance halalinsu ba?”. “Ƙwaraima kuwa mamana, bana sanar miki wani ƙwai dake cikin ƙaya ya bayyana ba kwanakin baya, kuma duk haɗarin maciji ya gama shawaginsa ya barsa dan ya gagara haɗiya”. “ƙwaraima kuwa ka sanar min da wannan, a farautar zaki yaci karo dashi kenan matsayin abinci?”. “Hhhhh mamana kina birgeni da saurin ramfo zance, to wlhy ina mai tabbatar miki da hakaɗinne ta kasance, tsagerun dawa na tunanin Zaki yafi ƙarfin ruwan ƙwai sai gashi harma yana ƙoƙarin damƙosa cikin ƙayoyi”. “Kai ɗan alheri karka sa farin ciki ya karni yau ɗinan ban kalmashe bakin buhun dana farama ɗureba, yanzu dai ina fatan kana hanyar gidane?”. “Hasashenki baya zama kuskure mamana, mu haɗu acan na baki sauran bayani, dan kuwa garin bita da ƙullin ƴaƴan kura sun rufta damisa da ƴaƴan fadarta a ramin ɗan zaki, shiko ya afka musu ƙasa yasa ƙafa yatake harma da share wajen kwanciya domin buƙatar hutu”. Wata irin dariya ta shigayi mai cike da nuna tsantsar farincikinta data daɗe da mantawa da samunsa, yau ɗan nata ya biyata da daddaɗan labari. tace, “Ɗan albarka wannan zinaran kalamai naka sunfi ƙarfin saurare a salula, garzaya gida nima ina gab da iskoka, dan tun safe na nema alfarma ga Uwargida sarautar mata akan zuwa na duba mai babban suna”.
“Babu damuwa mamana ina tsumayenki acan, alkairin ALLAH ya cigaba da baibayeki tare da nasarar cigaba dayin haƙo a ramin azzalumai batare dasun fargaba har sai kinkai musu wuya lokacin sungama shiga tarko”.
Murmushi tayi daga can tana faɗin “Amin ɗan albarka” kafin ta yanke wayar, shima ya tura tasa a aljihun yana murmushi. Cigaba yay da tafiya harya fito titi, napep ya tara takaisa inda motocin ƙauyensu ke tsayawa, duk da garinsu ba ƙauye bane sosai dole muce dashi ƙauye, dan kuwa a ƙarƙashin wata ƙaramar hukuma yake, saidai yamafi l.g ɗin dukkan abubuwan cigaba, gashi a bakin titi kuma babu nisa da babban birin jiharsu. A mamakinsa ana saukesa falletsetsiyar mota na cin birki a gabansa, baiyi mamakin hakanba, dan kasancewarsa drivern boss yanada alaƙa da sanin mutane manya sosai ta fannoni da dama, lokaci-lokaci kuma yakanci karo da wasunsu koda ace shi ya mantasu dan dama dalilin shige da ficin boss na aiki yake sanin nasu. Wanda ke ciki ya sauke gilashi yana murmushi, sosai gimba ya zaro ido irin na bazatar ganin wanda bai zatoba, “Lah Ɓaleru! Dama rai kanga rai? wane mai gangancine yay kasadar baka idanunsa kaketa haska hanya dasu cike da ɗaukar faɗi?”. Dariya na cikin motar yay har yana bugun sitiyari, yace, “Gimba kaidai baka rabo da shaƙiyanci, kasan ɓalerun naka da shige-shige, ko iska ta shafamin lafiya. Daga ina haka zuwa ina?”. Gimba yace, “Wlhy gida nai, zamuje hutun ƙarshen mako domin ganawa da iyali”. Ɓaleru yay ƴar dariya da faɗin, “Mutumina baka wasa da gona, shiyyasa kullum gatanan cikin yabanya take, banga laifinkaba, yi birgimarka ka more mata sune jin daɗin duniyar ai dama. Shigo mu haura dan nima dai can na nufa ɗin”. Babu musu Gimba ya shiga yana maida masa murtanin shaƙiyancinsa, saida suka ɗauki hanya ɓaleru yace, “Nifa mamaki oganka ke bani, gashi jinin manya, ɗan tsohon shugaban ƙasa mai tarin dukiya, shi kansa ƙwaron kansane dan ya tara bayan wanda aka tara masa, amma abin mamaki kamar shima baya mora balleku ƴan muna jira ALLAH ya baka mu samu”. Murmushi gimba yayi, cikin son kare boss ɗinsa yace, “Ai abin nagartace, sai dai irinku ƴan ƙwanta ka mutu mu haye basa ganewa, komai boss yake da tsari a cikinsa, shi bai ɗauki wannan dukiyar da ta tsolema kowa idanu wata tsiyaba, marasa nasaba da itama amfanuwa suke da tagomashinta amma ta ƙyaƙyƙyawar hanya, bai yarda da almubazzaranci ba, amma shi kogine maiba na kusa harma dana nesa, alkairinsa dake jiƙe dani ALLAH kaɗai yasan iyakarsa, sai dai ba’a iya ganinsa da idon gani saina zuciya”. Wata irin mahaukaciyar dariya ɓaleru ya kece da ita wadda harta bama gimba mamaki, kafin yabi ba’asinta ɓaleru ya jefa masa handkherchief a fuska, daga haka bai sake banbance fari ko baƙiba sai a washe garin safiyar yau daya jisa a ɗaure, idanu a rufe, bakima a ɓame. A zuciyarsa ya ayyana, ‘GADAR ZARE akaimin da wanda na sani kenan?’. Murmushi yay na takaici wanda a zuciya ya kasance dan babu bakin yinsa. Da ƙarfin masifa aka fincike abinda aka sa masa a baki, azaba ta sakashi sakin wani irin gurnani sai dai jarumta ta hanashi nuna gazawa. Yace, “Suwanene ku? Miyasa kuka kawoni nan? Minai muku?”. Banza akai masa babu amsa, yasan akwai mutum tare dashi, dan yana jin hucin numfashi kasancewarsa mutum mai basira da wata ɓoyayyir baiwa. Yay ɗan yi murmushin ƙarfin hali yana mai motsa jikinsa kaɗan, ɗauri akai masa bana wasaba, hakan yasa daƙyar yake iya motsawa. Kusan minti biyir yana jiran tsammani kafin a saka masa abu akan kunne.
Wata mahaukaciyar dariya aka sanya mai dogon zango daga cikin abinda basirarsa ta ankarar dashi wayace, daƙyar mai dariyar ya tsagaita daga can, kafin ya fara magana a kausashe. “Yaro ashe kaima tsagerane ban saniba, kai wanene daka isa tono abinda ke ɓoye? Ƙaramin naman daji abincin karnuka dakai har kakejin kakai zarra wajen yimana kutse a al’amuranmu? Banida lokacin doguwar magana dakai, yanzu za’a sakeka kai gudun mutuwarka kafin jininka ya zama halattacce ga bakandamiyarmu, wanda kakema aikinma bai isaba balle kai direbansa hhhhhhhhhhhhhh!!!!!”.
Wata dariya gimba ya kwashe da ita shima, a kausashe yace, “Faɗan sunƙuru alamace tamai tsoro, idan kuncika maza kufito filin yaƙi mai nasara saiya ɗauki kambu, boss kainuwane dashen ALLAH, zakine mai yagalgala mazan da suke kiran kansu mazanma balle ku mata maza masu ɓuya a rumfar……….
Kafin Gimba yakai ƙarshen zancensa an cire wayar daga kunnensa, taune leɓensa yay da ƙarfi. Kafin a maida masa baki a rufe, Bai sake jin motsin kowaba har yammaci, yana nan ɗaure babuci babu sha tun safiyar jiya rabonsa da abinci, garama ruwa yasha bayan fitowarsu massallacin juma’a, tun yana samun garkuwa daga yawu har shima yay tifƙewar da harshe bai iya juyashi ya zama abun mai gudana, ƙishirwa abune dake saurin illata mafi yawan halitta mai rai, balle irinshi mutum mai matuƙar son ruwa. Alamun duhun magriba da hasashe ne nashi yaji ya sake ɗaure garin, a wannan lokaci yaji an fara kuncesa, har aka gama tas bai motsaba bai kumace ƙalaba. Jansa aka shigayi keeeyyyy har zuwa waje, bashi da ƙarfin kare kansa dan haka ya salama bakinsa ɗauke da addu’a, tafiyar kusan mintuna uku kafin ai wurgi dashi.
Numfarfashi ya shiga saukewa a gwame, yakai hannunsa da ƙyar ya janye ƙyallen da aka ɗaura masa a fuska, baya ganin komai da ƙyau saboda idanunsa sun kwana sun yini a rufe, ga duhun magriba, saidai ya fahimci dajine yake. Da sauri ya shiga laluban wayarsa dake aljihu wadda suka gaza gani bisa kariyar ALLAH, ya kasance mai saka waya silent saboda baison takurama Boss ɗinsa da shigowar kira, a hankali ya saba da hakan har takai bayama buɗeta koda basa tare, tun ɗazun yakejin sautin shigowar kira dama, daƙyar ya iya ganin Number boss saboda idanunsa basa gani sosai sun masa nauyi ainun. Kai tsaye WhatsApp ya shiga, yay azamar danna recording ya fara magana a galabaice.
“Boss banjin zankai labari, dan basu kamani dansu barniba, akwai babbar ƙura a gabanka da bazan iya buɗe maka haske a kantaba yanzu saboda ƙarancin lokacin daya ragemin a duya, itace musabbabin shigowata rayuwarka tun fil’azal ka gafarceni da ɓoyewa, dama nabari ka fita daga wannan matsalar rikicin aurenne idan nadawo muyi magana, saidai ALLAH bai ƙaddara hakanba, amma nagodema ALLAH da wadda zata baka abinda yafi nawa tana raye, kai ƙoƙarin zuwa gidan Alh al..alhaji………… Ya kasa ƙarasawa saboda rawar da jikinsa ya fara na tunkarowar wata muguwar halitta garesa maiban tsoro. Jifa yay da wayar bayan ya ɗaga ɗanyatsansa saƙon ya tafi kasancewar baya rufe data shi dama can. Baya ya fara jan jikinsa yana karanto duk addu’ar data zo masa, yayinda shikuma wannan halitta ke biyosa danƙyas-danƙyas tana buɗe baki da lashewa alamar dai taga abinci. Babu zato gimba yaji yay baya, ashe wajen gaccine mai zurfin gaske dan akan tsauni suke. Wata irin wahalalliyar ƙara ya saki data bada amsa kuwwa a dajin yay ƙasa…….
Wata irin mahaukaciyar dariya dahar saukarta ke kamar ƙasar dajin na girgiza ce ta fara ratsa tsaunika, anyita da tsayi kusan na mintuna biyar kafin ta lafa wani irin yare ya biyo baya da muryoyin mutane masu yawa. Duk wanda zai iya nutsuwar saurarar yaren zai fahimci kalaman cikinsa shirkace kawai ake ambato. (Wa’iyazubillah 😭ya ALLAH kasa mufi ƙarfin zukatanmu, ya rabbi ka saka duniya a tafukan hannayenmu karka sata a zukatanmu, kaiconmu, kaicon burikanmu kaicon son duniyarmu).37
STORY CONTINUES BELOW

_____________________________________
Ana sallar magriba su Momy suka koma gida akan su Uncle Nasir zasu zauna da Jawaad domin yasa ɗan-fir’auna ya saki hudah.
Momy da Shahudah ciki suka shige sukabar Aamilah na waya a barandar shiga falonsu.
Da mamaki Aamilah ke kallon akwatinan da aka jibge a harabar gidan gaban motar Qaseem, ƙiyyy!! Sautin jawo abu ya karate kunnuwanta, kallon wajen da ƙarar ke zuwa tayi, Qaseem ne jaye da jikkan gana must go irin ƙatuwarnan sabuwa dal, amma tsabar yanda yasa ƙarfi wajen janta har hannu ɗaya ya fincike yana lililo, duk dai ya ganta yiyai tamkar basan da zamantaba, baba maigadi dai tun ɗazun yana hangen Qaseem ɗin daga ɗakinsa, tsabar baison yafito ya gansa ya sakashi aikin tayashine ya sakashi maƙalewa cikin ɗakin yana leƙensa ta Window. Jikkar ya dangwarar ya sake juyawa zuwa sashensu, daga shi sai gajeren wamdo da baƙar singlet datai mugun fidda masa siffarsa ta ƙaƙƙarfan namijin dake cin ƙarfe. Saida taga ya shige kafin ta juya da gudu gulma na cinta har saura kaɗan ta faɗi, ALLAH dai ya ara mata damar dafe ƙarfen da aka ƙawata barandar ƙofar falon nasu dashi, ƙara kwasa tai a gujen ta shiga tana ƙwala kiran Momy dake sama abin duniya ya isheta ga Shahudah tsaye kanta tana ribzar kuka da mata fitsara. Sosai kiran da Aamilah ke mata ya firgitata, ta miƙe zumbur ta fito tanabi matakalar benan da gudu-gudu. “Haba auta wannan wane irin kirane haka kamar wata baƙauya, miya farune shin kikemin kiran mafarauta?”. Baki Aamilah ta cuno bayan ta murguɗama Momy kamar wata sa’arta, kafin cikin taɓara tace, “Kajimin Momyn nan, dama kika samu na taimakeki na kawo miki labarin da ɗuminsa, toga ɗankican yana haɗa kaya da alama barin gidan zaiyi”. Sosai gaban mom ya faɗi, batama tsaya saurararta wanne a cikiba ta fice daga falon da sauri, dafa mata baya Aamila tayi tare da Shahudah data fito idanu a kumbure.
Qaseem dake ta faman lodama ƙatuwar motarsa kayan yayma momy dake masa magana kallo ɗaya ya ɗauke kai batare da yace da ita ko ci kanki ba. Muryarta har zuga take na alamun ɓacin rai tace, “Qaseem wai badakai nake maganaba? Shin mikukeson maidanine a gidannan kai da Shahudah? shin bazaka nutsu kai ka fahimci uzirinmuba, Na shiga uku ni Aysha, wane irin mugun asiri wannan yarinyar ta haɗaku da shine kaida yaronan Jawaad da kuke ɗaukar kowa ɗan iska akan lamarinta?”. Cikin zafin murya Qaseem yace, “Nifa kin bala’in cikani da surutu hajiya, Please ki barni nai aikin gabana Mtsooww!!”. Ya ƙare maganar dajan wani wawan tsaki yana ɗauke kansa ya cigaba da loda kayansa a motar. Mutuwar tsaye kawai Momy tai tana kallonsa, Aamilah ta kwashe da dariya tana kallonsu, “Faɗan Uwa da ɗa abin birgewa, kucigaba da gashi guys”. Baki Shahudah ta taɓe tana mai juya manyan idanunta alamar zubama Qaseem harara, tace, “Ɗan jaraba duk bakai kaja manaba, wani iyayi da ƙwala kai a farantinne ya kaika nacema banzar yarinyarnan ƙazamiya mara gata, idan da baka maƙale matanba ta gidan uwarwa aurena da naka zasu haɗu ballema har bb ya aikata haka, asararre kawai mai baƙar zuciyar tsiy…..”
Jikake tasss!! Qaseem da babu wanda ya lura da isowarsa gaban Shahudah ya sauke mata wani wawan mari, ƙasa ta zube tana garsheƙar kuka daja masa ALLAH ya isa, to daman zuciyar ƴan mazan a kusa take, neman wanda zai amayarwa yakeyi, gashi ya samu cikin sauƙi, dan haka ya shigar tamkar an aikosa. Duk ihun da Aamilah keyi da Momy bai sauraresuba, sai ma tsarabar mari Aamilah ta samu itama, Momy kuwa ya hankaɗeta. Qaseem yanada Masifaffiyar zuciya irin wadda idan ta yunƙuro ɗinan sam bayajin bari, dan tamjar zugasama yake, sannan shifa cinnakane baisan na gidaba. Wanna. mugun zuciyan da ALLAH ya basu shida Jawaad itace ta hanasu zama ƙarƙashin inuwa ɗaya, dan kowa yanaji da kalar tasa, kawai shi Qaseem yafi Jawaad saurin fushine, dan Jawaad na dannewa yay kawaici har saika kaisa ƙarshe, amma ga Qaseem sam ba haka bane, sha yanzu magani yanzu, ga kuma ɗanbanzan riƙo saikace dangin kutare🤦🏻.
Iya gwargwadon iko babu algus Shahudah ta daku harma da Aamilah daya koma haɗawa daga ƙarshe, dama yanajin haushinsu akan abu biyu, dukan Bilkisu da jimata ciwo, saikuma gudunmawar da suka bada akan ai masa aure da Azeema. Daƙyar da suɗin goshi baba mai gadi da kuku suka amshi Shahudah da Aamilah a hannunsa, dan yay musu kaca-kaca abinka da farar fata, Shahudah harda fasa mata baki akai jini sai ɗiga yake. Yace, “ƙananun marasa kunya, daga yau idan harku kun cika tsagerune dan ALLAH kusake shiga cikin al’amurana”. Kuka kawai suke daga su har Momy, babu wanda ya iya tanka masa har kuku da baba mai gadi suka gama loda masa kayansa a motar, sashensu ya koma ya ɗakko sauran tarkacensa ya shige mota ya fice batare da ya sakebi takantaba.11
STORY CONTINUES BELOW

Kai tsaye gidansa ya zarce, dama harya ajiye mai gadi tun jiya, kodaga waje kasan gidan ya haɗu, ya mugun ƙawatuwa da shukoki masu ƙamshi da daɗi, ga ƙamshin sabon fentima na tashi. Dakansa yayta shiga da kayan, da yake ALLAH yayisa mutum mai hanzari da zafin nama sai gashi ya gama sakasu ciki tas.
★★★★★
Bayan barin Qaseem gidan babu jimawa Dad ya dawo, iske Momy yay zaune ta zabga tagumi, Shahudah na kwance barcin wahala yay gaba da ita ta ɗora kanta a cinyar momyn. sai Salman da Aamilah dake lido a d/table. duk sannu sukai masa, ya amsa yana zama kusa da momy tare da kamo hannunta cikin nashi. “Humairah mike faruwane?”. Muryarta na rawa tace, “Qaseem ne ya tafi?”. “Ya tafi? Ina ya tafi to?”. “Muma bamu saniba, ya kwashe duk kayansa na gidannan”. Cikin taune leɓe Dad yace, “Bari dai zamuyi magana, yanzu tare nake dasu Alhaji Nasir suna falon baƙi, mun kira yaronan ne da aka ɗaura aurensa da mamana zaizo”. Zumbur Momy ta miƙe jikinta har rawa yake ta ture kan Shahudah batare data tuna tana jikinta tana barciba, tace, “Ya yarda ɗin zaizo Dadynsu?”. Fuskarsa ɗauke da murmushi yace, “Eh ya amince, drivern Alhaji Nasir ma yaje ɗakkosa”.1
____________________________________
Bayan Jawaad ya dawo daga sallar magriba shiryawa yay ya amsa kiran da Alhaji babba yay masa, kansa ciwo yake masa, amma bashi da ikon bijirema kiran kakan nasa, ballema yaji muryarsa wani iri kamar yana tare da damuwa, tun da ranama ya fahimci hakan, ya haƙurane kawai ya barsa da yace masa babu komai..
Fitowa yay yanata baza ƙamshi, sai dai fuskarnan a cinkushe babu walwala. ya tsaya suka gaisa da mai-gadi har yake tambayarsa gimba bai shigo bane?. mai-gadi yace, “Aiko bai isoba Oga, ni harma na fara tunanin ko lafiya? Dan tunda ya tafi bamuyi wayaba kuma kaga har lokacin daya saba dawowa ya shige amma shiru”. Jimm Jawaad yay alamar tunani, dan shima dai tunda gimba ya tafi basuyi wayarba kam, to wannan hargitsicinne ya ɗauke masa hankali gaba ɗaya har bai ɗauki hakan komaiba. Ya ɗan sauke numfashi yana kallon mai-gadin. baba bara dai naje na dawo, idan har lokacin bai shigeba saina nemesa naji mike faruwa?”. Mai gadi yace, “To to ba laifi oga, ALLAH ya maidoka lafiya”. “Amin” Jawaad ya faɗa yana ficewa, sai dai acan ƙasan zuciyar tasa maganar gimba taƙi gushewa.
A ƙofar gida ya iske Alhaji babba zai shiga massallaci, dan haka yay fakin anan waje ya fito suka shiga tare, bayan sun fito Alhaji baba yay sallama da mutane maƙwaftansa da ragowar ƴan anguwa masu salla anan kamar yanda ya saba, kafin ya kama hannun Jawaad dake masa shagwaɓan shifa fura zaisha, Alhaji babba ya bada a siyo masa. Alhaji babba dake murmushi ya tsaya yana dungure masa kai, “Kai miyasa idan rikicinka ya motsa babu wanda ka raina saini? Kaje kaima su Mariya mana”. Fuska Jawaad ya yatsine saboda ciwon da kansa ke masa yace, “Nidai ka daina sawa gaban mamana na faɗuwa a darenan, kabama Tanimu ya sayo mani inba hakaba bazan sake zuwa kwana gidanka ba”. Dariya Alhaji babba yay da jan hannunsa suka cigaba da tafiya, yace, “Yoni ALLAH na tuba aina yayeka da zuwa kwanarmin gida, matarka ta jajiba nima na huta da rigimarka hakanan”. Jawaad yace, “Basai na ɗakkota muke kwana anan ɗin tareba”. “Bana gayya, ku zauna gidanku nima aure zanyo”. Ciki dauriya Jawaad ya ƙyalƙyale da dariya, koba komai yarage nauyin da zuciyarsa tayi da tattaunawa da kakan nasa, shi kansa Alhaji baba sai yaji damuwarsa ta sassauta.
Bayan sun zauna Alhaji baba ya zubama Jawaad fura mai ƙyau da daɗin gaske da bai rabo da ita ya dubesa, cike da jin daɗi yake shan furan sanyinta na ratsa masa zuciya da ƙirji. “Muhammad kasan miyasa na kiraka kuwa?”. Kallonsa Jay yayi ya girgiza kansa batare da yace komaiba. Alhaji baba ya ɗan sauke numfashi, murya a sanyaye yace, “Akan matarkane” Saida Jawaad ya haɗiye furan daya sha kafin yace, “Matata kuma?”……………✍1
Ƙyan alƙawari cikawa, sai dai wanda na ɗauka ni ya gagara cikar dalilin birkicewar wattpad, harna fara canja page ɗinma sai ALLAH ya taimakeni ya dai-dai ta🤦🏻, page ɗinnan kaɗai gareni babu nagobe saboda matsalar wattpad ɗinan ta ɗauki hankalina banyi typing ba, ƴan telegram sunce a turo muku kawai, amma da wuya kujini gobe idan ALLAH ya kaimu zan samu nayi typing ɗin jibi idan munada rabon kaiwa. Gaisuwa ga kowa da fatan alkairi😍😍😘😘.25
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻9
Page 281
…………….Alhaji babba ya gyaɗama Jawaad kai alamar eh ita. Cike da mamaki Jay ya ajiye kofin hannunsa yana tsatstsare kakan nasa da idanunsa cike da sonjin ƙarin bayani.
Murmushi Alhaji Babba yay masa tare da kamo hanunsa, “Daina tsareni da waɗanan idanun naka ba wani abu bameba, kawai inason sanin dangin mahaifinta ne”. Sassanyar ajiyar zuciya Jawaad ya ɗan sauke, kafin shima ya riƙe hanun Alhaji Babba da ƙyau a cikin nashi, “Baba nima inason saninsu, sonake kawai wannan ƙurar ta lafa itama ta sakejin sauƙine”. Alhaji babba yace, “Kayi tunani mai ƙyau, inason kayi ƙoƙari ka bincika, sannan yaya maganarka da mutanen gidanku? Da kuma maganar shi wanda kasa ya auri yarinyarnan ta wajen Ali?”.
Murmushi Jawaad ya ɗanyi ya ɗauki furarsa zai cigaba da sha, ganin zai basar da zance Alhaji babba yace, “Nasanfa ka jini”. Ƴar dariya Jay yayi yakai kofin bakinsa, “ALLAH ka iya rigima kaima tsohon nan, karka damu ina sane da komai”. “Nasan kana sane da komai Muhammad, sai dai hankalina ya tashi matuƙa jin ba mutumin kirki bane habibun, kajifa wani suna da Nasiru ya kirashi dashi ranar”.
Jay yay murmushi kawai batare da yace komaiba.
Sun cigaba da hirarsu har zuwa ƙarfe tara ya fita, yaso zuwa asibiti, amma ganin dare yayi sai ya haƙura ya nufi gida abinsa. A gate ya tsaya ya tambayi mai-gadi ko gimban ya dawo?. mai-gadi ya tabbatar masa da bai dawoba, ya kira wayarsa kuma gashi tana ring amma ba’a ɗagaba.
Sosai abin ya ɗaurema Jawaad kai, daga baya kuma ya ajiye tunaninsa akan inhar da safe bai dawoba zaisa abi bayansa garin nasu aga ko lafiya?. Da wannan tunanin yay shirin barci ya kwanta.+
_____________________________________
Su Dady sun karɓi baƙuncin surikinsu habib, duk yanda Dad yaso su Momy su zauna basai sunzo falon baƙiba hakan ya gagara, dole ya barsu sukabi bayansa, ba ƙaramin tashin hankali Shahudah ta shigaba da ganin wanda ake kira wai matsayin mijinta, daka gansa kaga cikakken tantiri marajin magana, cike da isa ya zauna a kujerar da aka nuna masa sai wani cika yake da batsewa.
Ya kafe Aamilah da Shahudah da kallo yana wani lasar laɓɓa tamkar tsohon maye, ko kunyar su Dad bayaji, dama daya shigo babu wanda ya gaida, bama su ishesa kallon arziƙiba.
“Wace cikar tawa anan?” yay maganar cike da gadara. Babu wanda ya tanka masa a cikinsu, sai Shahudah da Aamilah da suka zuba masa wata shegiyar harara. Ya bushe da dariyarsa mara daɗin ji yana faɗin, “Dama ace ana auren yaya da ƙanwa wlhy da duk haɗawa zanyi hhhhh! Dana kwashi gara aradu…” cike da tsiwa Aamilah da tafi Shahudah jin hausa tace, “Uwarkane garan shege mai suffan aljanu…..” wata wuta data gitta ta idanunta mai stars ce ta hanata kaiwa ƙarshe, lokaci ɗaya jinta da ganinta ya ɗauke baki ɗaya ta zube a jikin Dad daya tarota. Babu wanda yaga sanda Ɗan-fir’auna ya ƙarasa gaban Aamilah sai ƙarar maruka sukaji kawai.
A fusace Dad yace, “Kai ƙaramin ɗan tsagera, wanene ubanka da har zaka mararmin yarinya a gabana?”. Kallon dad ɗan fir’auna yay ya watsar, kafin cike da gadara yace, “Sanin ubana a gareka dattijo ai tamkar yankewar numfashinka ne, dama kun kiranine domin kuci zarafina komi? kunga dalla malamai ku bani matata na wuce na fasa zaman….” da sauri Uncle Uwaisu ya taresa cikin lallashi yana bashi haƙuri, amma fir ƴaki sauraren kowa, Aamilah dai ta farfaɗo da ƙyar bayan an zuba mata ruwa, Shahudah na rakuɓe lungun kujera sai tsiyayar da hawaye takeyi jiki na rawa, harga ALLAH tsoronsa takeji, a ranta kuwa ayyanawa take ashe Bilkisu baturiyace, dan ɗan-fir’auna ALLAH ya bashi baƙi, wanda daga gani kasan shaye-shaye ya sake taka rawar gani wajen ƙara masa shi. Da ƙyar suka samu ɗan-fir’auna ya zauna bayan an saka Shahudah da Aamilah sunbar falon, Salman kam yay laƙe kamar baya falon (hege yaga maza🤣😜).
Duk yanda su Uncle Nasir sukaso lallaɓa ɗan-fir’auna akan ya saki Shahudah yace shifa sam baisan wannan zanceba, dan yanzuma da shirin ɗaukar matarsa yazo yana buƙatar abinsa, tunda yana zamansa aka kawo masa tallansu. Har ƙasa Momy ta duƙa tana kuka da roƙonsa amma sai dariyar wulaƙanci da cusa haushi yake musu.
“Kungafa kubar ɓata lokacinku akan roƙonama, tayaya kuke tunanin zanyi sake da wannan babbar kaddarar ne haka, yo ko shugaban ƙasa ai nafishi hura hanci yanzu akan wannan cikar tawa, ku manta kawai a saimin royal bed zan kama hayar gida aje aimin jere gobe, babu damuwa idanma kunkai sati danshi shiri wuyane dashi, ko a hotel mayi amarcin satin guda kafin ku kammala surukai..” ya ƙare maganar da miƙewa yay salute nasu zai fice. Da sauri Dad yace, “Nawa kake buƙata a biyaka ka sakarmin yarinya?”.
Tsayawa ɗan-fir’auna yayi, ya juyo yanama Dad wani matsiyacin kallo maiban tsoro, sai kuma ya bushe da dariya tare da dawowa da baya. Yace, “Zan iya amsar kuɗi na saketa pale, tunda yanzu na auri ƴarka ka zama pale ɗina nima, ammafa kasani saina ɗanɗana kona sati ɗayane dan yawuna ya biya, a shiryata da safe nazo na amshi kayata, nanda sati biyu saiku cakemin naira miliyan hansin na baku ƴarku, idan haka bai mukuba kuma banida matsala, iyakaci inta mata ciki duk bayan wata tara ta ringa juyen jajayen ƴan dugwi-dugwi irinta, koba komai na samu surukai masu kuɗi nima nan gaba tunda naga jar fatar ake yayi yanzun” ya wani ɗage musu gira cike da barikanci yay ficewarsa.
Babu wanda bai jiƙe da zufaba a falon, tun fitar ɗan-fir’auna babu wanda ya iya magana sai kuka Momy dake tashi. Salman ya miƙe cikin raɗa-raɗa yace, “Wlhy kuyi ƙoƙari ku biyashi, dan wannan dagani zai iya take mutum ya yanka tamkar ya yanka kazar gidan gona, ku rufa mana asiri dad dan kuwa su momy sun kwaso mana bala’i, wlhy barin ƙasarnan zanyi idan an gama watandarku na dawo zaman gaisuwa”. Ya ƙare maganar da ɗai-ɗai yana kallon ƙofa, da gani kasan a tsorace yake (Kana bani yaji Salman🤣, lusarin banza😠).7
STORY CONTINUES BELOW

WASHE GARI.
Dad na zaune a harabar gidansa abin duniya ya taru ya masa yawa, tunda ya dawo sallar asuba bai iya shiga cikiba, a daren jiya da ƙyar suka samu Shahudah tai barci, dukta gama fita hayyacinta.
Baƙon da aka turo daga masarautane ya samu isowa, ya ƙwanƙwasa gate mai gadi ya leƙa, sai da suka gaisa sannan yace, “Magatakarda ne daga masarautar gagara badau, an aikoni domin isar da saƙo ga Alhaji Ali ko yana nan?”. Mai-gadi yace, “Ƙwarai yana nan, sannu da zuwa bara a sanar masa”.
Sai da baba mai-gadi yay sallama sau kusan uku sannan Dad ya jisa, bai amsaba sai zuba masa idanu da yayi. Baba mai-gadi yace, “Alhaji baƙone wai daga masarauta”. “Masarauta kuma? Ni miya haɗani da masarauta malam Amiru?”. “To Alhaji wlhy ban saniba, yadaice daga can yake”. Da hannu kawai Dad yay nuni alamar baƙon ya shigo. Baba mai-gadi ya koma domin shigo dashi.
Sai da baƙo ya zauna a kujerar robar da baba maigadi shima ya ajiye masa sannan suka gaisa da Dad, cikin nutsuwa magatakarda ya korama Dad bayani akan gimbiya ta bada umarnin Bilkisu zata koma masarauta da zama har sai ranar tarewarta gidan mijinta. rasa abinda ma zaice Dad yayi, sai tsurama magatakarda ido yay kamar zai haɗiyeshi dasu. Har magatakarda yaymasa sallama ya tafi bai dawo hayyacinsa ba, sai faman juya takardar hannunsa da magatakarda ya kawo yakeyi, shi yanzu abin tambayarsa anan Bilkisu ce takai ƙararsa masarauta kokuwa Jawaad? Kai yasan halin Jawaad da shegen taurin kai, bazai taɓa kai magana masarauta ba dan tsaurin idonsa bazai barsa ganin ya gaza ba. To amma bai zaton Bilkisu nada irin wannan wayon, kuma itada takema kwance a asibiti. Gaba ɗaya ransa ya kuma jagulewa, cike da sassarfa ya tashi ya shige ciki.1
★★★★★★
Jawaad kam koda ya gama shirinsa na office ya fito sai ya iske Gimba bai dawo ba, mamaki ya kuma cikashi, dan jiya bayan ya dawo ya kira Number gimba har sau biyu kafin ya kwanta amma ba’a ɗagaba, yanzu kam yafara tunanin babu lafiya, akwai wani saurayi a gidan da aikinsa kawai kula da flowers ɗin gidanne, garinsu kusada garinsu gimba yake, hakan yasa Jawaad ya kirashi yanama tsaka da aikinsa na bayin fulawar. Durƙusawa yay yana gaida Jawaad, Jawaad ya amsa da masa nuni ya tashi. “Banace ka dainamin irin wannan gaisuwarba Balarabe, kadaina min wannan durƙuson kamar wani mai neman gafara kaji”. fuskar balarabe ɗauke da murmushi yace, “Alhaji nagode sosai, amma nariga na sabane, koba aiki nake ƙarƙashin kuba aika girmeni nesa”. Girgiza kai kawai Jawaad yayi, ya ciro kuɗi a aljihunsa ya miƙa masa 3k, “Balarabe ajiye aikinnan naka zakai dan ALLAH kaje garinsu Gimba ka ganomin ko lafiya yake? aikasan garin ko?”. Da sauri balarabe yace, “Eh Alhaji, ai daga garinsu zuwa namu da ƙafama muke zuwa, kuma har gidansa na sani tunda naje sunan yaronsa da aka haifa masa na ƙarshenan mai sunanka”. “Okey Alhmdllh, kayi ƙoƙari kaje yanda zaka dawo da wuri, bani number ka na kira kaga tawa, daka isa kasan halin da yake ciki ka kirani na sani kafin ka juyo”. Cike da girmamawa balarabe yake sauraren number da Jay yake faɗo masa yana sakawa a wayarsa nokia, bayan ta cika ya kira shima jay yaga tashi.1
Mota Jawaad ya shiga, yau da kansa yay driving, kai tsaye asibiti ya nufa, sai da yaje suka gama magana da likita sannan ya nufo ɗakin da Bilkisu ke jiyya. Sallama yay suka amsa, kafin ya tura ƙofar ya shiga.
Kasa ɗagowa nai in kallesa, dan wata matsananciyar kunyarsa nakeji a raina, cikin girmamawa ya gaida mama, aunty Batool ma ta gaidashi da tsokanarsa, gaisuwarta kawai ya amsa bai maida mata magana akan tsokanarsa da takeba, na ɗago ido kaɗan nai masa kallo ɗaya na janye da faɗin, “Ina kwana”. shiru kamar bazai amsaba, sai da ya ajiye kwalin maganina daya ɗauka yana dubawa sannan yace, “Lafiya ya jikin?”. Ahankali nace, “Naji sauƙi”.
Jawaad ya ɗauke kansa daga Bilkisu ya maida ga mama, “Mama Doctor ya sallameta, saiku haɗa kayanku, zanje office yanzu, nanda awa ɗaya zuwa biyu zan dawo sannan ai kun kimtsa”. Mama tace, “To to Alhmdllh, ALLAH yasa haka shiyafi alkairi, to amma kayanta fa? Kasan komai yana can gidan”. Ɗan jimm Jay yayi idonsa akan Bilkisun, ya sauke numfashi kaɗan yana ɗauke idanunsa, “Inaga mu manta da zancan zuwa gidansu yazu, bara naje na samo mata wasu kayan kawai”.
Jin abinda yake faɗama mama yasa na ɗago da mamaki na kallesa, hakan yay dai-dai da shima ya juyo gareni, idanunmu ne suka shige cikin na juna, nai azamar janye nawa da fargabar ina kuma zan koma? Badai gidan nasaba? yanzu har rashin gatana yakai irin haka da…….
Katsemin tunani yay da cewar, “Dami-dami kike buƙata?”. Idanuna cike da ƙwalla na ɗago na kallesa, ganin har yanzu ni yake kallo saina maida kaina ƙasa, muryata cike da tahowar kukan da nake dannewa nace, “Miyasa bazan koma can ɗinba?”. Banza yay bai amsa minba, hakan yasa hawaye masu zafi suka silalomin akan kumatu. Sautin siririn tsakinsa kawai naji, cikin faɗa-faɗa yace, “Haka na gadama dole kuma hakan za’ayi, idan kuma kika nema dagulan lissafi ALLAH yau ɗinan zaki tare”. Babu shiri na ɗago kai da sauri, wata uwar harara ya zubamin. Dole na maida kaina ƙasa. Wata ƴar ƙwafa yayi, sai takunsa ya biyo baya, kafin naji buɗe ƙofa da rufewa alamar ya fice abinsa. Koda na ɗago sai naga ashe daga ni sai shine ma a ɗakin, sam banji sanda su mama suka fitaba, dukda inajin motsin ruwa a bayi alamar ɗaya na ciki ɗayane ya fita.
Gaba ɗaya zuciyar Jawaad a jagule take, sai dai jarumtarsa ta ɓoye hakan, shi mutumne tamkar kowa, yana farin ciki yana baƙin ciki, yana shiga matsala yana shiga tashin hankali, kawai dai ALLAH yayisa mai zuciyar dakiyane kamar yanda ALLAH yay mafi yawan maza da juriya akan abu komin zafin da sukeji akan al’amari. Tafiyar da bata wuce mintuna goma ba ya isa wani haɗaɗɗen boutique, yanda suka tarbesa zai tabbatar maka da an masa farin sani a waje, sai gaidashi suke cike da girmamawa. Wani mai tsananin kama da Jabeer ne ya fito daga wani lungu, ganin Jay ya sashi faɗin, “Yah Jay barka da zuwa”. Kallonsa Jay yay daɗan murmushi yace, “Yauwa Kabeer, ya kasuwar?”. “Alhmdllh Yayah, kanason wani abune?”. Kai kawai Jay ya kaɗa masa kafin ya miƙe a kujerar da yake zaune. Yana gaba Kabeer na biye dashi har wajen da kayan mata suke, tsala-tsalan jallabiya da ƙananun kaya harma da ɗinkakkun atanfofi da shadda duk sunda. Ahankali yake binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya, karon farko a rayuwarsa da yazo saima mace kaya shi ɗaya, ko sanda suna tare da Shahudah hakan bai taɓa faruwaba, dan ita a tsarinta bata sayen kaya anan saina ƙasashen ƙetare, hakan yasa koda yaga abu ya burgesa baima taɓa wahal da kansa wajen saya matanba.
Ganin ya kasa ɗaukar komai kabeer yace, “Yah Jay aida ka kira ka faɗi duk abinda kake buƙata bama saika zoba”. Guntun murmushi jay yay masa kawai daɗan taɓa kafaɗarsa, kafin ya fara nuna masa duk abinda yay masa wanda ya ƙiyasta a ransa zaiyi dai-dai da jikinta, saida ya ɗauka kaya kusan kala goma sha biyar, sannan ya ɗauka takalma uku da hijjabai huɗu ya zaɓi akwatin da za’a zubasu. Yasan dolene ƴa mace budurwa kamarta ta buƙaci kayan ciki, to amma shi ta ina zai fara tunda ba sanin seize ɗinta yayba. Kallon sashen da kayan suke yay, gasunan kala-kala kuma duk seize ɗin da kake buƙata zaka samesu, yaɗan yatsina fuska kafin ya nufi wajen, amfani yay kawai da yanda yake hasasota cikin idanunsa ya ɗauka matasu aka haɗesu da waɗancan. Card ɗinsa ya bama Kabeer, ganin kabeer na wani noƙewa akan baza amshi kuɗinba dan harya kira Jabeer ya sanar masa ga Jawaad ɗin a wajen yace karsu amshi kuɗi su rubuta su aje idan yazo zai biya. (Wajen na Jabeer ne, ƙaninsa kabeer ke kula dashi sai sauran ma’aikata). Cikin sosa ƙeya Kabeer yace, “Yah Jabeer yace karna amsa”. Sosai Jay ya kafesa da idanunsa da yau gaba ɗaya babu haske a cikinsu saboda damuwa. “Kiransa kai ka faɗa masa nazo?”. Kasa cewa komai Kabeer yay sai faman susar ƙeya yake, Jay yay gaba a binsa zuwa mazaunin kabeer ɗin da yake shine mai amsar kuɗi. Ɗaya daga cikin yaran wajen ya kira ya duba masa kuɗaɗen duka kayan aka zubasu a akwati, shikuma ya saka card ɗinsa ya cire adadin kuɗin yay ficewarsa aka bisa da kayan.
STORY CONTINUES BELOW

★★★★★
Fitar jay babu jimawa a asibiti Qaseem yazo, cike da mamaki Bilkisu ke kallonsa jikinta sai rawa yake dan tunda ta kwanta a asibitin nan sai yau ta gansa, baiko kalli mama ba balle ta samu darajar gaisuwarsa ya finciki hannun Bilkisu dake zaune bayan ta kimtsa suna jiran dawowar Jawaad, da sauri mama ta riƙe Bilkisun da faɗin, “Lafiya kuwa Qaseem? Ina zaka kaita?”. Wani banzan kallo ya mata yana figar bilkisu batare daya tankaba, itako kuka take iya ƙarfinta da roƙonsa ya sake mata hannu karya jimata ciwo, amma sam yaƙi sauraren kowa. Tun suna ɗaukar abin wasa har yanema fin ƙarfinsu, dan Doctor ma yazo ya basu sauran maganin bilkisun shima ta ritata dashi. Rikici bana wasaba ake kwasa da Qaseem har ALLAH ya maido Jawaad asibitin. Tunda ya gabato wajen yakejin hayaniya, cike da mamaki ya shiga dan ƙofar a buɗema take. Idanun sane suka fara sauka akan hannun Qaseem dake riƙe dana Bilkisu, tuni idon ƴan mazan ya rufe, a wata irin matsananciyar tsawa yace, “Qaseem sake mata hannu!!”. shi Qaseem ma sai yanzu yaga Jawaad ɗin, shima a fusace yace, “Anƙi a saki ɗin, koka saketa, koma karka saketa zan wuce da itane”. Saukar wani bahagon bugu kawai Qaseem yaji akan damtsen hannunsa, ai baimasan ya saki hannun Bilkisu ba saboda gaba ɗaya jijiyar hannunsa ta saki lokaci guda saboda azaba, kafin ya gama dawowa hayyacinsa Jay yaja hannun Bilkisu dake kuka sun fice daga ɗakin. Ganin haka yasa Doctor saurin rufe ƙofar ya kulle danya bama jay damar barin asibitin gaba ɗaya.
Kuka bily take cin ƙarfinta har suka hau titi, jin ta cika masa kunne yasashi taka wani wawan birki da batasan sanda tai tsale ta koma jikinsa ba. Sai jinta kawai tayi zaune ɗare-ɗare bisa cinyarsa ta cusa kanta a ƙirjinsa tare da ƙanƙamesa. ALLAH ne yaso Jawaad ya tsaida motar, da babu abinda zai hana su kife a hanyarnan. Gaba ɗayama sai ya kasa cemata uffan, sai rumtse idanunsa da yay yana mai cije leɓensa na ƙasa da masifar ƙarfi kamar zai hudashi.
Jin shiru mun tsaya ga ƙamshin turarensa yay mugun addabar hancina haryazama shine iskar da nake shaƙa ya sani ɗagowa, sosai na zabura ganina a jikin boss ɗare-ɗare, innalillahi…. Na shiga ambata ina rawar jikin sauka, harna koma inda na baro bai motsaba, nikuma ban iya kallon fuskarsa ba saboda tashin hankali da matsananciyar kunyar dana tsinta kaina a ciki. Jin tsahon mintuna biyar yaƙi cewa komai yaƙi kuma ya cigaba da tafiya yasani satar kallonsa ta gefen ido ina share hawayena da sukaƙi tsayawa. A kife yake kan sitiyari bana ganin fuskarsa, tsorone ya sake kamani, murya na rawa nace, “Dan ALLAH kayi haƙuri, wlhy tsorata nayi”. A fusace ya ɗago yana watsamin wani irin harara, yanda idanunsa sukai matuƙar jazur fiye da farkone ya kuma ɗagamin hankali. A kausashe yace, “Idan baki rufemin bakiba saina canja miki kamannin fuska! Saboda na raboki dashi kikemin wani kukan banza da wofi?!!”. Da sauri na shiga girgiza masa kai ina mannewa da ƙofa, dan yanda yay maganar tamkar zai haɗiyeni ɗanyane, ni tun lokacin da naga fushinsa nake tsoron cigaba da ganin hakan. Yay ƙwafa da ƙara zubamin harara, “Share waɗanan banzayen hawayen”. Saurin saka ƙasan hijjab ɗina nai na goge tas kamar yanda ya buƙata, sake ɗauke kansa yay daga gareni Batare da yace komaiba ya tada motar da fusgarta muka cigaba da tafiya.8
Duk da hankalina a tashe yake da yanda yake zuba gudu a titi ban sake gigin yin wani abuba, sai kaina dana tusa a cikin cinyoyina ina addu’ar ALLAH ya kaimu lafiya dukma inda muka nufa.
A halin da yake ciki yanzu bazai iya shiga masarauta hakaba, hakan yasa yay fakin daga waje, fita yay da waya a hannu, bayason kiran gimbiya dan haka ya maida akalar kiransa ga dattijon nan, bugu biyu kuwa ya ɗaga suka gaisa, Jawaad yay masa bayani a taƙaice. Dattijo ya amsa masa da sujirasa gashi nan zuwa. Babu jimawa kuwa yazo tare da Amaturrahman data rikice da murnar ganin Bilkisu. Basu wani ja zanceba ya basu Bilkisun batare da yace mata uffanba akan hakan, saida ya juya zai shiga motarne ya dubeta sau ɗaya ya ɗauke kansa da faɗin, “Ki shirya gobe zaki koma aiki, zan biyo na ɗaukeki” daga haka yay tafiyarsa. binsa tai da kallo har saida ya tada motar yabar wajen itama suka shiga motar dasu Amaturrahman suka fito da ita.15
______
Asibiti Jawaad yay niyar komawa dan yayma Qaseem dogon gargaɗi, sai dai tunanin barinsa ya samesa har gida ya sakashi sharewa, juya kan motar yay zuwa station zuciyarsa fal tunane-tunane, ga aiki jibge a gabansa da baisan iyakaba, ga kuma matsaloli kala-kala da yarasa makamar dazai kama domin fara warwaresu. Saƙon ɗan fi’auna ne yazo masa arai, har ya shiga office ɗinsa yana juya zancen a ransa, ‘Mi ɗan fir’aunan ya sani a kansa da haryake iƙirarin ya basa har naira miliyan hamsin domin ya sanar masa? Shin waishi yaron nanma wanene shi? Kuma a ina su Momy suka samosa?’. Wannan tunanin da yazo masa a raine ya sakashi dakatawa daga ƙoƙarin kunna Computer gabansa da ya kai hannu zaiyi, komawa yay jikin kujera ya kwanta yana lumshe idanunsa.
A haka Aliyu ya shigo ya samesa, sai da yay masa sallama har biyu sannan ya farga da shi, ya buɗe idanunsa da tashi zaune sosai, tie ɗin wuyansa ya sassauto ƙasa yana kallon Aliyu daya zauna. “Boss lafiya dai?”. Aliyu ya faɗa idonsa akan Jawaad, sassanyan numfashi jay ya sauke da cewa, “Lafiya lau Aliy”. Badan Aliyu ya yardaba ya ƙyalesa, saima takardun hanunsa ya miƙa masa yana masa bayani. Jawaad ya amsa ya duba ya sake miƙama Aliyun, magana suka ɗanyi Aliyu ya tashi ya fita.
Koda Aliyu ya fita Jay kasa haƙuri yay ya ɗauka waya ya shiga neman ɗan-Fir’auna, tana gab da katsewa aka ɗaga, daga can wanda ya ɗaga ɗin ko sallama baiyiba balle batun gaisuwa yace, “Mai wayar yayi Accident yana asibiti”. “…Accident?” jay ya maimaita da maɗaukakin mamaki tare da sake kiran wayar dan har an katse………….✍
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻4
Page 31
……………“Muje”. Ya faɗa a hankali. Babu shiri nai azamar ɗago idanuna na kallesa, duk da ni yake kallo ban janyeba, cikin harɗewar harshe nace, “Anan zan… zan kwana?”. Tamkar baiji abinda naceba ya ɗauke kansa, dubansa yakai ga sararin samaniya daketa sake caƙuɗewa da duhu, batare da yace min uffanba ya raɓani ya nufi gate. Hawayen da nake maƙalewa suka silalomin a kumatu, a fili nace, ‘Dan ALLAH kar kaimin haka nidai’. Kamar yasan mi nake faɗe ya juyo yayinda ya buɗe ƙofar gate ɗin zai shige, “Karki bari na dawo na sameki a nan gurin”. Yafaɗa yana nunoni da ɗanyatsa alamar gargaɗi. Hannu nasa na share hawayen fuskar tawa kafin na taka nima zuwa gate ɗin. Maigadine kawai ke bin jam’i a bakin gate ɗin da yake anaji daga cikin gida. Ganin yayi tsaye yana kallon maigadin ne yasa nima naja na tsaya, sai da aka sallame sallar da dama zaman tahiyar ƙarshe suke. Kamar jira, ana yin sallama maigadi na miƙewa ya nufosa. Fuska a haɗe Jay ke kallon maigadi, baiko amsa gaisuwar da yake masaba da sannu dazuwa yace, “Ka bautama UBANGIJI tamkar kana ganinsa, dan idan kai baka ganinsa shi yana ganinka, MANZON ALLAH ya horemu da zuwa masallaci muyi sallah cikin jam’i, miyasa kai kafi zaɓar yinta kai kaɗai a cikin gida? Shin tsaron gate dan kar wani ya shigo yafi maka muhimmanci akan zuwa ka samo cikakkiyar ladar da mahaliccinka kaɗai ke badata? Daga yau ina mai baka shawara a kowanne lokacin salla ka kulle gate ɗin nan idan yazama dole saika zama mai tsaron mutanen cikin gidan kaje kai sallah cikin jam’i”. Kan maigadi a ƙasa yace, “Nagode sosai Alhaji, ALLAH ya saka da alkairi ya kareka kaima, ya ƙarin haƙuri?”. Cikin lumshe ido Jay yace, “Alhmdllh, abokinku ya tafi ya barmu”. Hawayene suka ziraro a fuskar maigadi, hakan yasa Jay yin gaba shima yana haɗiye abinda ya tokare maƙoshinsa.
Jiki a saɓule nabi bayansa mukabar maigadi na kuka, sai naji nima hawayen nawa na sake gangarowa, dukda bawani sanin gimba nai sosai ba mutuwarsa ta taɓani ainun, mutum mai fara’a dason mutane.
Yana gama buɗe ƙofar da keys ɗin daya ciro a aljihu iskar na tasowa, hakan yasa muka shige da sauri saboda irin mai ƙasarnan ce sosai, da sauri na maida ƙofar na rufe na jingina jikinta ina sauke numfashi da share fuskata da hijjab ɗin gudun kar wadda ta hau ta shigarmin ido.
Boss kam ya kunna fitilar falon saboda an kunna Gen…, a take haske ya gauraye ko ina, baice dani komaiba ya nufi sama abinsa. Tafiyarsa kawai zaka kalla zaka fuskanci yana cikin damuwa, dan a sanyaye yakeyinta. da kallo na bisa har saida ya ɓacemin, na sauke ajiyar zuciya ina lumshe idanuna, a ƙasan raina addu’a nake ALLAH yasa idan iskarnan ta lafa yace zai maidani Masarauta.
Tunda ya shiga bedroom ɗin sai ya shiga yatsina fuska, shaf yama manta ko gadonsa bai samu arziƙin gyaraba yau, duk yanda yake jinsa a matuƙar gajiye haka ya daure ya shiga kakkaɓe gadon, ya gyarashi tsaf kamar ba yanzu za’a kwanta a kansaba, fitowa yay ɗaukar tsintsiya, duk da sarai yaga Bilkisu dake tsaye jikin ƙofa har yanzu yay tamkar bai gantaba yaje ya ɗakko kwandon da kayan sharan ke ciki yazo ya sake hayewa sama.+
Da kallo na bisa, haka kawai sai naga kamar bai daceba, dan da alama shara zaiyi da kansa, bayansa nabi jikina duk a saɓule, ga kaina namin wani irin ciwo ƙasa-ƙasa, ga yunwa dan rabona da abincin kirki tun breakfast ɗin safe, a garinsu marigayi fura kawai nasha rabin kofi itama sai da aka takuramin. Duk da sallamar da nayi bai ɗago daga abinda yakeba, nasan salon amsa sallamarsa a ciki-cikine hakan yasan ban damuba dan nasan dai ya amsani, nace, “Bara in share”. Kamar bazai kulani ba, sai kuma ya miƙamin tsintsiyar ya fice.
Ajiyar zuciya na sauke na cigaba da sharan a sake ganin ya fita saini kaɗai. Tsaf na kammala sannan na nufi toilet, shima dai yana buƙatar wankin dukda bawani datti yayba na tashin hankali, tsaf na gyarashi cike da ƙarfin hali. Ina fitowa daga bayin shima yana shigowa ɗakin, saurin ɗauke kaina nayi daga garesa saboda ganinsa a tuɓe babu riga sai dogon wando kawai da farar singlet yana waya, ya zauna a bakin gadon yana cigaba da wayarsa, kusan mintuna biyu ya juyo inda nake tsaye, yatsunsa biyu ya murza sukai ƙara, hakan yasa na ɗago kaina garesa, alamar nazo yaymin. Ahankali na taka zuwa garesa, ya miƙamin wayar batare da yace komaiba ya bar wajen. Duk da bansan ko waneneba haka nai sallama, muryar Ummah naji ta amsamin, hakan yasa na gaisheta cike da girmamawa, itama daga can da kulawa ta amsamin tare da min ta’aziyya. Nai mata godiya Nabeelah ma ta amsa muka gaisa, sai aunty Batool itama, daga nan mukai sallama. Wayar na ajiye masa bakin gado na fita falo, Zama nai a kujera ina jiran ya fito naji hanlin da nake ciki, harga ALLAH bana fatan kwana a gidannan. Nai zurfi a tunani da jiran fitowarsa kira ya shigo wayata, gyara zama nai na cirota a aljihu, Amaturrahman ce, dan haka na ɗaga muka gaisa, daga can tace, “Mun jiki shirune, ca muke tun biyar zaki dawo?”. Ɗan murmushin ƙarfin hali nayi, kafin nai mata bayanin yanda zata iya fahimta, nakuma nuna mata cewar bamu dawoba muna ƙauyen su gimban sai dai gamu nan a hanyar dawowa” addu’ar isowa lafiya tai mana kafin mu yanke wayar. Na faɗama Amaturrahman hakane da tunanin idan boss ya fito zaiji tausayina ya maidani can a daren nan.
STORY CONTINUES BELOW

Jawaad daya samu yay wanka da ruwa mai ɗumi sosai sai yaɗanji daɗi da sauƙin nauyin jikinsa sai dai na zuciya, yay alwala ya fito, ƴan dube-dube ya hauyi sai dai babu ko alamarta a ɗakin, guntun tsaki yaja yana lumshe idanunsa, dan shi kaɗai yasan ya yakeji, ga yunwa ga gajiya ga damuwa, dan shi babuma abinda ya sakama cikin nasa bayan coffee da yasha a office sai ruwa da yayta sha a garin su Gimba. ita kanta tausayinta yakeji gashi bawani ƙarfine da itaba ta tashi daga ciwo shekaranjiya jiya. Wadrobe ɗinsa ya buɗe ya ɗauki jallabiya fara tas ya saka mata turare sannan yasa a jiki, harya shinfiɗa abin salla sai kuma ya kalli ƙofa, koya kirata bazai yuwu tajiba saboda iskar da ake a waje abun babu sauƙi, tamƙar zata ɗauke rufin kwano, danma duk Windows ɗin sashen a rufe suke shiyyasa sukejinta da sauƙi su.
“Ki taso kiyi wanka”. Ya faɗa kawai daga ƙofar ɗaki ya juya abinsa dan yasan zata iya jinsa daga inda take. Ba ƙaramin wintsilawa kayan cikina sukaiba lokacin da furucinsa ya isomin cikin dodon kunne, sai dai koda na ɗago tuni ya juya sai ƙamshinsa daya barmin. Rasama wane tunani zanyi nai, mi yake nufi da nazo nai wanka? ‘A toilet ɗinsa?’ na faɗa a fili kamar zanyi kuka. saukar ruwan sama babu zato ya sakani miƙewa zumbur dan naji tsoro wlhy, gashi da ƙarfi ya sauka dukda p.o.p hakan bai hanani jin ƙararsaba akan rufin, to nidai dama can akwai tsoro idan ana ruwa, nafi buƙatar naga mutane a kusa dani hankalina yafi kwanciya, balle wannan da ruwan ya kasance kaso biyu a cikin uku iskace ma, wani wal garin yayi na walƙiya, labulen Window’n da ba’a sakiba sai glass ɗin kawai aka rufe yasa naga tamkar inuwar mutum a wajen, jikina har rawa yake na tashi na nufi ɗakin boss da ɗan gudu-gudu sauri-sauri har ina neman faɗuwa, wayatama anan na barta saman kujera. Na maida ƙofar da ƙarfi na rufe ina rumtse idanu da sakin nishi mai ƙarfi, har yanzu ƙirjina sai wani ɓal-ɓal yake badawa.
Shidai Jay salla yake, amm duk da haka ya jiyo yanda Bilkisu ta rufe ƙofa da ƙarfi, koda ya idar bai juyi ya kalleta ba, ya miƙe domin kawo isha’i da yaga lokacinta yayi. “Sallarce bazakiyi ba komi kike nufi?”. Da sauri na buɗe ido ina kallon bayansa daya juyamin. Murya a raunane nace, “Ai idan naje gida duk zanyi fa?”. Cikin takaici Jay yace, “Ainan ɗin jejine ko? Karki bari na ɓata miki rai a darenan Miemaa, ƙyaƙy! tom”. Daga haka ya kabbara sallarsa.
Jin yanda yay maganar a kausashe na tabbar zai aikata duk abinda ya faɗa ɗin, haka na nufi toilet ɗin ina ƙunƙuni a raina, wannan wane irin abune haka, miyasa tunda anga hadarin baza’a kaini inda nakeba sai a wuto dani nan, nidai komai dare saina bar gidanan ehe. Da wannan ƙunƙunan a cikin rai na shiga bayin, ruwa mai zafi na haɗa dan jikina bala’in ciwo yakemin sosai, banga wani soso ba bayan nasa a bayin, haka na ɗauka nai wankan da shi ina maijin daɗin ruwan, sai da na kammala nai alwala sai kuma naji ƙyanƙyamin maida kayan dana cire, to amma idan ba su ɗinba mizan saka? Nida bazan fita da tawul ba gaskiya, to idanma na ɗaura tawul inada kayan dazan saka ɗinne a ɗakin………?
Wata irin ƙara na saki jikina na masifar rawa saboda ɗaga kan da zanyi idanuna sukai tozali da wata iriyar mummunar halitta baƙa ƙirin da jajayen idanu, jikinta dai zam maciji, amma kan bana maciji baneba…
A rikice Jawaad dake addu’a ya miƙe saboda jiyo ƙarar Bilkisu dake bayi, ALLAH ya sosa bata kulle ƙofarba, ya tura da ƙarfi babu ko neman izini ya shige, dai-dai bily tai baya zata faɗi saboda numfashinta daya ɗauke dan firgici, tallafota yay ta faɗo jikinsa, yayinda idanunsa kebin halittar dake silalawa ta Window zata fice da kallo. Sai da ta gama ficewa tsaf sannan ya maido kallonsa kan Bilkisu, saurin kauda idanunsa yayi dan babu komai a jikinta, ya jawo tawul dake ciƙin ƴar drawern glass na toilet ɗin ya yafa mata sanann ya ɗaukata cak batare da yace komaiba ya fita da ita. Saman gadonsa ya shimfiɗeta, dukda ya yafa mata tawul sai da ya sake jan bargo ya rufa mata har saman ƙirjinta, tsaye yay yana ƙarema fuskarta kallo tamkar maison gano amsar tambayoyin zuciyarsa akan fuskartata, tsahon mintuna kusan goma kafin yabar wajen ya koma toilet ɗin yana dube-dube, babu komai kam, sannan a mamakinsa Windown kaɗan ya ɗaga, hanyar da yabi baikai faɗin da halittarnan zata iya shiga da fitaba, ‘mikenan?’ ya tambayi kansa, dagacan gefen zuciyarsa ta bashi amsa da (Aljanu). “Aljanu!” ya maimaita akan laɓɓansa har sau biyu. “Hummm!” ya sake faɗa a fili yana ɗibar ruwa kaɗan a ƴar roba dake toilet ɗin ya fita. Iskar hadarin ta fara lafawa, sai ruwa da ake yaf-yaf na farkon damuna, dan daya fara da ƙarfi sai kuma ya koma ɗaf, sai kuma ɗan yaf-yaf, sai dai walƙiya da aketa faman yi harda cida mai ƙarfi lokaci-lokaci. Zama yay a gefen gadon kusa da cikin bilkisu tare da ajiye robar ruwan a ƙasa batare da ya shafa mataba ya faɗa tunani. Abinda ya faru a jeji ɗazun, kalaman baba ƙaura, kalaman abokan ɗan fir’auna, ainahin abinda Gimba ya gani har yazo ya faɗa masa a randa aka shirya juya ɗaurin auren Qaseem da bilkisu zuwa Azeema da Qaseem bilkisu da ɗan fir’auna, Accident ɗin ɗan-fir’auna, mafarkinsa, sai abinda ya gani yanzu wanda ya firgita bily. Ya shiga saƙa waɗanan abubuwan dake gogayya da juna daki-daki a muhalli guda. Yay murmushi mai ciwo saboda amsar data zo masa a zuciya lokaci ɗaya. Cikin zafin nama ya miƙe, Ranƙwafawa yay kan bilkisu ya shafa mata ruwan daya dumtso a hannu, a take ta kawo numfashi mai ƙarfi.
A hankali na buɗe idanuna, sai kawai a bazata naci karo da fuskar boss dake ranƙwafe kaina daf da tawa, dan har inajin saukar numfashinsa akan tawa fuskar, gabana ya faɗi, nai saurin fara waige-waige danson kauda fuskata. Saukar tattausan tafin hannunsa naji saman fuskar ya sake juyo dani garesa. Duk yanda naso janye idanuna da suka shige cikin nasa na kasa, kallon ido cikin ido mukema juna karon farko, wani irin abu mai wuyar fassara ke fitowa daga ƙwayoyin idanunsa masu girma da sirkin jaa suna shiga cikin nawa, atake naji tsigar jikina na tashi, ƙofofin gashina na buɗewa gashin na miƙewa, jinina dukya tsinke lokaci guda yana wani irin gudu a cikin jijiyoyi, sai kawai na saki kuka a hankali.
Jawaad da har yanzu idanunsa ke kafe a cikin na bilkisu yaɗan murza babban yatsansa daga jikin hancinta har zuwa ƙasan idonta ya kwashe hawayen dake fitowar ya maida yatsan baya jikin ƴan uwansa, dan har yanzun tafin hannunsa na tallafe da kuncinta na haggu. Ahankali ya furta, “Tabbas ƙaddararki da tawa a haɗe take Miemaa, zan bada ƙarfina da lokacina wajen binciko abinda ya ƙullemu ƙarƙashin inuwa ɗaya insha ALLAH”. Yana gama faɗar hakan ya saka ɗayan hannunma a gefen kumatuna na haggu ya ɗauke duk hawayen dake zuba a idanuna guda biyu, sannan yaja baya tare da miƙewa tsaye yabar wajen.
Lumshe idanuna nai a hankali kalamansa namin kaikawo tsakanin zuciya da ƙwaƙwalwa, a hankali nima kalaman baba ƙaura da abinda ya faru yau a jejin suka shiga dawomin daki-daki. Jin an ruƙo hannuna nai saurin buɗe idanuna, boss ne riƙe da riga a hannu, batare da yayimin maganaba ya ɗaga kaina a hankali ya ziramin wuyan, sannan ya kamo hannuna ya taimakamin na saka, ɗayanma haka. Juyawa yay yana faɗin, “Ki tashi kiyi alwala ki sauke nauyin sallolin dake kanki”. Daga haka ya fice a ɗakin. Dukda tsoron dake a raina haka na miƙe dan nima rashin yin sallar cizon raina yake sosai, sauka nai daga gadon, rigarsa ce t-shirt mai guntun hannu, dukda a ido bata da girma sai gashi takai min har kusan quarter ɗin cinyata, na ɗauki wandon dana gani gefena, a raina nake raya ‘Ni balki, nice kuma da saka kayan boss yau?’. Sauƙina wandon irin mai taushin nanne da roba acan ƙasansa, sannan a sama ma robace harda zariya. zariyar naa ɗaure sannan a tsoro-tsoro na nufi bayin ina addu’a a cikin raina, saida na leƙa na tabbatar babu komai sannan na shiga batare dana rufeba na ɗauro alwalar na fito. Nayi namakin ganin hijjab a ajiye, da alama tun ɗazunma ya ajiyeshi, haka na ɗauka na saka na fara sallolin da suka shigemin.
STORY CONTINUES BELOW

Jawaad kam koda ya fita sashen Uncle Nasir ya nufa, a falo ya iske yaran harda mamansu suna kallo, duk gaidashi suka shigayi da masa ta’aziyyar Gimba, ya gaisa da Ammi ma, sannan ya zubama Ameera harara da faɗin, “Wannan banzar shigan fa? Ko ɗan kwali babu kanki”. Cike da taoro Ameera ta miƙe tana faɗin, “Dan ALLAH kayi haƙuri Yah Jay”. Bai sake tanka mataba, amma kallon da yake mata ya isheta shiga uku, da gudu tai ɗakinsu domin suturta jikinta, dan dama ya hanasu shigar banza tun yana zaune a sashen (karku manta bayan rasuwar mama Maryam Uncle Nasir shine ya cigaba da riƙon Jay har yay aure). Baya musu wasa idan yaga kan mutum yana rawa, shiyyasa suke masifar shakkarsa, gashi dama baya shiga shirgin ƴammatan gidan saboda gudun raini, samarinma kansu ba kowa ke ganin fuska daga garesa ba sai sa’anninsa dana sama dashi, suma ɗin bai maida kansa sakarai a garesuba ana dai mutunta juna. Raihana da itama ta nutsu waje guda ya kalla, “Tashi ki samo min abincin mutum biyu”. Tashi tai da sauri ta nufi kitchen, itadai Ammi batace komaiba, dan macece mai mutunci da sanin ya kamata, yanda Jawaad ke tsaye kan ƴaƴansu ita daɗi yake mata, dan shakkarsa na hanasu aikata abubuwa masu yawan gaske, har ranta kuma ƙaunar Jay take dan ita dai halayyarsa birgeta yake sosai.
Suna ɗan taɓa hira da Ammi akan rasuwar gimba Raihana ta fito ɗauke da ƙaramin basket na kaba mai ƙyau a hannu, tace, “Yah Jay gashi, ko nakai can?”. Batare da ya bata amsaba ya miƙa mata hannu alamar ta bashi, kawo masa tayi tana godema ALLAH a ranta, dan dama bason kaiwar takeba kar taje can ya sakata wani aikin kuma, dan hankalinta nakan film ɗin da suke kallo. Yana amsa ya miƙe yayma Ammi sallama ya fita.
Bayan na kammala sallolin sai kawai na ɗauki Alƙur’anin dana gani a ɗakin na shiga karatu cikin sanyin murya da rauni, dan inayi hawaye na zirara tamkar an buɗe fanfo.
Wani irin sanyi Jay yaji a ransa, ya ƙaraso cikin ɗakin sautin muryar bilkisu na ratsa zuciyarsa, sai yaji wata nutsuwa mai daɗi na saukar masa har cikin gaɓɓai. Bai dakatar da itaba ya ajiye basket ɗin ya fita, mintuna kaɗan ya dawo ɗauke da kifuna biyu sunata turiri alamar tea ya haɗo musu. Motsinsa ya sani rufe alkur’anin saboda nakai inda zan iya tsayawa, sonake na roƙesa ya maidani masarauta tunda har yanzu da sauran dare, ƙarfe goma da mintuna Uku.
Ido muka haɗa dan shima kallona yake, na maida kaina ƙasa ina juya abinda zan faɗaɗin da lanƙwasa yatsun hannuna madaidaita, “Dan ALLAH Yayah dare baiyiba, tunda ruwan ya ɗauke ka kaini can koka kaini gidan Dad na kwana”. Jin shiru bai tanka minba na saci kallonsa, shayinsa ma yake sha tamkar bai jiniba, kuma tsabar wulaƙanci kallona yakeyi. Kusan mintuna uku yace, “Taso kici abinci”.
‘Yah ALLAH, wai da wane yare zan fahimtar dashi ya fahimtane?’. Na faɗa a zuciya idanuna na cika da ƙwalla, Ban karaya ba dai, duk dan ya barni nafi nabi umarninsa, babu musu na miƙe zuwa garesa, batare dana cire hijjab ɗinba nai yunƙurin zama ƙasa. Gadon ya nunamin da hannu yana sake tamke fuska. Yanzunma dai Umarni nabi na zauna dukda ba haka nasoba, ya miƙomin kofin shayi kawai. Ƙananun kofunane dan basu wuci rabin kofi ba, tea ɗin ma kuma bai cikaba, cikin dauriya da fatan maidani masarauta na hau sha, sosai yayi daɗi abin mamaki, bansan na shanyeba balle dama yunwa nakeji.
Kofin da yasha nashi tea ɗin ya ajiye, ya buɗe kular dake cikin basket ɗin ya ɗiba abinci dai-dai misali, nidai kallonsa nake ƙasa-ƙasa, tashi yay ɗauke da filet ɗin a hannu ya koma saman kujerar ɗakin, “Ga abinci nan” yay maganar batare da ya kalleniba. Duk da inajin kunyarsa yunwa nakeji sosai, idanma nace bazanciba zan cutar da kaina matuƙa. Kofin na ajiye na ɗiba dai-dai misali. Koda wasa ban ɗago kainaba harna kammala, na miƙe na tattare har filet ɗin daya gama shima na fita dasu duk da a tsorace nake.
Jay ya bita da kallo harta fice, a ransa yake faɗin, ‘Ahaka sai ka ganta kamar wata saliha, sai dai shegen taurin kaine da ita da tsoro ko farar kura ta shafa mata lafiya’. (Jay a rage sa ido dai. Lol😂).1
Babu jimawa na dawo ɗakin, zuciyata na sake tunzurani akan na sake roƙonsa dai. Yana zaune inda na barsa ya baza takardu a table ɗin gaban kujerar yanata rubutu, na ƙaraso bakina ɗauke da addu’ar neman nasara a kansa, jikin hannun kujerar na duƙa ina mai narke murya dan yaji tausayina. “Amaturrahman ta kirani akan sunga ban dawoba, ni kuma na sanar mata muna hanyar dawowa, kuma zan koma masarauta, nasan sunacan suna jirana”. Aikin gabansa kawai yake kamar bai jiniba, na kuma raunana murya da faɗin, “Boss Please, idan na kwana a gidannan da safe wace amsa zanba mutanen gidan dasu Amaturrahman ɗin?”.
Karon farko Jawaad ya saki lallausan murmushin da har haƙoransa suka bayyana, dukda yana cikin halin damuwa da alhinin rasuwar gimba sai ta bashi dariya, fuskarsa ɗauke da murmushin har yanzun ya ɗago yana kallonta.
Wani irin daɗi naji ganin yana murmushi, a tunanina naci nasara, sai gani nai ya ɗauke kansa ya maida ga abinda yakeyi batare da yace komaiba, “In faɗa miki amsar da zaki basu idan sun ganki kin kwana anan da safe?”. Ya faɗa tamkar bashine yay maganarba. Ganin bance komaiba ya ɗago yana kallona, “Ko bakiso na riƙe kayata? Dan ƙyautace, idan ta ƙara wasu mintuna zata zama ta kuɗi”. Baki na tura masa dan haushi, nace, “Inaso”.
Jay dake kallonta har yanzu yakai yatsansa dab da bakinta ya ɗallah yana faɗin, “K kullum bazaki daina bani ciwon kaiba yarinyarnan?”.
Saurin ɗaura hannuna nai saman bakina dan zafi, idanuna har sun cika da ƙwalla, saurin rufesu nayi dan karsu zubo, boss mugune yasin, ina tausayinsa ashe bama abin tausayi baneba……..
Ture takardun gabansa yay ya miƙe, a gaban bily dake durƙushe jikin kujerar da yake zaune yaje yay wani ɗan dirƙuso da kowa yasan maza da iya salonsa, da sauri-sauri zuciyarsa ke gudu, lumsassun idanunsa nakan fuskarta datai fayau saboda ramar da taɗanyi.
Saukar numfashinsa a saman fuskata da mayen ƙamshin turarensa ya sakani ware idanu dan mamaki, ko kaɗan ban san sanda yazo daf daniba, a take jikina ya fara tsuma, ya saka hannunsa akan haɓata ya ɗago fuskata da ƙyau, saurin lumshe idanuna na sakeyi ina ambatar sunan ALLAH a raina, dan wannan al’amari nasa yafi ƙarfina da wayona. Cikin taushin muryar da bansan yanada itaba, yay magana a hankali “Na maida amsata bakiso?”.
Da ƙyar na iya haɗiye yawu ina jinjina masa kaina alamar “eh” banason, dan burina kawai ya tashi wlhy.
Jay da shima baisan mike damun kansaba ya kuma matsar da fuskarsa daf data Bilkisu, a hankali ya busa mata iska saman idanunta dake rufe, mar-mar ta farayi da idanun saboda iskar da yake busa matan.
hancinsa ya ɗora saman nata yana gogawa, cikin magana raɗa-raɗa da ko kana kusa dasu da wahala ka jinsa yace, “Duk masu suna Bilkisu jarumaine, miyasa ke kike matsoraciya?”………………✍2
(😂😂Saura naji wani yace maganar Jay ba gashkiya bane, kowa yasan mu jarumawane masu Suna Balkisu. Lol🚴🏼😜).
16
BARKANMU DA JUMA’A.
Kunata jira ko😑, ALLAH ina fara editing barci ya ɗaukeni, saida na tashi na tsinta wayar a gehe🤣.
Asha weekend lahiya🚴🏼🚴🏼🚴🏼😍😍😍😍🤗
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.10
SURPRISE💁🏻35
Wannan page sadaukarwa ne ga iyayen yaran da suka kuɓuta, gaskiya ina tayaku murna matuƙa gaya, mungodema UBANGIJI daya maido mana dasu garemu da gaggawa cikin ƙoshin lafiya kuma, ƴan uwa wannan yana sake nuna mana mu duƙufa addu’a wa ƙasarmu, aikin bana shugabanni bane kaɗai, dan idanma munƙi addu’ar mune zamusha wahala, shugabanninmu mutanene tamkarmu, suma basu isa tsaremu ba sai wanda ya haliccemu, aduk yanda rayuwa tazo mana mu amsheta matsayin jarabawa mu godema ALLAH, UBANGIJI yafi kowa sanin halin da muke ciki, muyi ƙoƙarin cinye jarabawa sai muzama masu nasara, zage-zage marasa amfani nakasace irin ta zuciya, ALLAH yay mana ni’imomi masu yawa miyasa bazamu gode masaba sai ƙoƙarin aibanta waɗanda suke mutane kamarmu da hangen gazawarsu, sai dai taimakon addu’oinmu zamu samu tsaron da muke buƙata a yankinmu, muyi haƙuri mu duƙufa wajen faɗama ALLAH kukanmu, mu gyara mu’amulanmu ga junanmu mu kanmu, dan bazamu kasance azzaluman junaba sannan muce zamu samu shugabanni adalai, mugyara sai ALLAH shima ya gyara mana danshi mai rahamane. ALLAH ya kawo mana haske da kwanciyar hankali, ya dafama shugabanninmu suma akan ƙyawawan ayyukansu, saɓanin haka ALLAH ka magance mana badan halinmu ba😭🙏🏻.26
Page 32
……………..Ganin yanda ta tsume sai ta bashi dariya da tausayi, ya dungure mata kai yana miƙewa da faɗin, “Yarinyarnan ki rage tsoro”.
Ni kaina bansan na sauke wani kakkauran numfashiba tare da komawa na zauna daɓar, nai azamar cusa kaina tsakanin cinyoyina ina mai godema ALLAH daya tashi. A raina sai ayyana rashin kunya irin na maza nakeyi, suyi abu kuma su fuske abinsu tamkar basuyiba.
Jay da tuni ya koma kan aikinsa yaɗan kalleta ya maida kansa ga rubutun da yakeyi, haka kawai yanaso ya ganta a yanayin tsoro dan ƙyau take masa. Bai sakebi takantaba ya cigaba da haɗa bayanai akan case ɗin mutuwar Gimba, ya ɗaukama kansa alwashi sai yabi kadin jininsa, duk masu hannu a cikin wannan al’amarin kosu ubanwaye saiya soya musu gyaɗa bisa tafin hannu. Ganin lokaci yaja sosai Bily na a yanda take tun ɗazun ya sashi sake kallonta, muryarsa babu alamun wasa yace, “Miemaa!”.
Gajiyar dake tattare dani tasa har barci ya saceni a haka ban fargaba, a bazata naji ya kira sunana, na ɗago da sauri na kallesa, shima ni yake kallo, sai dai fuskarsa babu walwala sam. “Tashi kije ki kwanta” ya faɗa yana nunamin gado da idanu. Yanda ya tsuke fuska babu sauƙi yasa na miƙe babu musu dan nasan dai kwana anan dole ya tabbata, zuwa nai na kwanta a bakin gadon sosai, naja bargon na rufama jikina batare dana cire hijjab.
Jay daya kuma maida hankalinsa ga aikinsa yace, “Kicire wannan hijjabin tunda ba cinyeki za’ai a ɗakinba”. ‘Boss matsala’ na ayyana a cikin raina ina zame hijjab ɗin naja bargon har saman wuyana.
Duk da azabar ciwon kai da ya keji haka ya jure yana cigaba da haɗa bayanan, sai kusan ƙarfe ɗaya saura ya miƙe, kallo ɗaya yayma sashin da Bilkisu take kwance ya fahimci har yanzu idonta biyu, baice komaiba ya cire jallabiyar jikinsa yasa t-shirt fara akan boxer ɗinsa ya haye gadon shima, sai dai ba kwanciya yayba, zama yay ya jingina bayansa jikin fuskar gadon ya kashe fitilar ɗakin yabar iya ta gefen gado. Bargon yaja ya lulluɓe iya ƙafafunsa zuwa cinya, ya lumshe idanunsa yana maijin zafi da ƙirjinsa ke masa wanda yaketa ƙoƙarin dannewa, tunɗazun dannewa kawai yake dan bayason ya ƙuntata zuciyar yarinyarnan da laifin daba nataba, yana buƙatar jin wasu abubuwa daga garetane shiyyasa ya kawota nan dama. Rayuwarsa da gimba ta shiga kokawar dawo masa cikin zuciya, yarone mai mutunci da sanin mutuncin duk wanda zama ya haɗashi dashi, yasha saka Gimba manyan ayyuka masu haɗari akan aikinsa kuma yay masasu cikin ƙwazo, gimba na ɗaukarsa tamkar yayansa da suka fito ciki guda, tabbas yayi rashi wanda yasan bazai taɓa maye gurbinsaba har abada, danshi tuni yabar ɗaukar gimba matsayin drivern sa kawai jinsa yake a jininsa tamkar ɗan uwansa abokin farin ciki da baƙin ciki. Wata ƴar ƙwalla ta taru mai akan fatar idanu kaɗan, hannu yasa ya shareta yana mai jero masa addu’oin neman gafara a cikin zuciyarsa. Ya ɗau tsayin mintuna goma a haka kafin ya juya ya kalli Bilkisu, ɗauke kansa yayi murya cike da ɗaci yace, “Miyasa kika dawo gidan su Hudah da zama?”.
Banyi tunanin ya fahimci idona biyu ba har yanzun, na rumtse idanuna da ƙarfi ina sauke ajiyar zuciya, batare dana motsaba nace, “Ƙaddarar maraici”.
Idanu Jay ya tsurama bayanta, tsawon sakanni ya ɗauka a haka kafin ya sake ɗauke kansa daga gareta, “Ina dangin mahaifinki suke? Misa basa cikin rayuwarki?”.
Hawayene masu zafi suka silalomin, dan yau kan Boss ya taɓomin inda yafi ko’ina ciwo a zuciyata, zaune na tashi na jingina da fuskar gadon nima, hawaye na ƴar tseren fitowa na shiga bashi amsa kai tsaye, dan na fahimci so yake kawai yasan wacece niɗin kafin zuwana gidan su aunty Shahudah, batare dana kallesaba nace, “Har iyayena suka bar duniya su dukansu basu taɓa sanar dani wata matsala dake tsakaninsu da duk danginsu ba, dukda nasha musu tambaya sai dai babu wanda ya taɓa bani amsa ƙwaƙwƙwara a cikinsu, kullum amsarsu a gareni itace, (komai da lokacinsa, idan lokacin yayi zan sani) tun ina damuwa da abun harma na ciresa a zuciya, dama ba komai ke sakani kwaɗayin son jiba sai yanda nake ganin sauran yara ƴan uwana sukan shirya a ranakun juma’a da Sallah suje gidajen danginsu, sai dai ni daga gareni ba haka baneba, tunda na girma nai wayo a gidan haya mai ɗauke da ɗakuna kusan arba’in na buɗi ido na ganmu, bara dai na maka gwari-gwari zakafi farimtata.
Ni dai sunana Bilkeesu ɗiya ga malam Ado makaho, ƙwarai mahafina makahone da ko tafiya baya iya yi sai da ɗan jagora, Sai mahaifiyata Asiya.
A shekarun baya can mahaifina yana ɗan gani da ido ɗaya, amma da ga baya wahalhalun rayuwa suka ida rufe ɗayan idon yazam gaba ɗaya, mahaifiyata ma tana da nakasar ƙafa, dan kuwa gurguwace bata ma iya tafiya sai dai jan jiki. A matsayin da iyayena suke kawai zai nuna muku ni ba kowan kowa bace ba, dan kuwa muɗin talakawane irin tiɓis ɗinan da a kullum sai an nemo za’aci. Abin da zai matuƙar birgeka a rayuwar iyayena shine sam mahaifina baya bara balle aje kan mahaifiyata, duk da baba baya gani bai yarda zama maroƙi ba, dan a ganinsa UBANGIJI ya masa dukkan gata da ya bashi rai da lafiya, idaniyar ganice kawai bashi da ita. Sana’ar mahaifina itace sai da kayan ɗinki irinsu zare, allura, almakashi da dai sauran kayan nau’in ɗinki tsiraru dai-dai arziƙinsa, a gaba ɗaya jarin idan zaka dinƙuleshi waje ɗaya bazai wuce na naira dubu goma sha biyarba, wataƙil ma na zurma da yawa. Dalilin kamewarsa na janye kansa da ga ƙasƙancin bara ne ya ja hankalin mafi yawan telolin anguwarmu zuwa sayayyar kayan ɗinki a wajensa. Sai mahaifiyata da ke saida kayan kuka, kuɓewa busashshe, kayan ƙamshi harda daddawa domin kare mana mutunci itama. Gidan da muke gidan hayane mai ɗauke da ɗakuna kusan arba’in, dan irin dogon gidannan ne da akan jeranta ɗakuna reras da ga farkon baranda zuwa ƙarshe tamkar gidan karuwai, ba wani faɗine da gidan ba, amma kowa iyakar mu’amularsa a ƙofar ɗakinsa ne da bazata gaza taku goma ba, babban kicinne guda ɗaya a gidanmu dake a farkon shigowa gidan wanda ya gama cuɗewar baƙi saboda mafi yawancinmu girkin icce mukeyi, masu arziƙin cikinmu ne keda lasisin dahuwar abinci saman gawayi, can da ga ƙarshen gidan kuwa banɗakine guda biyu, na kashi da wanka, wanda suka ɗaine duk yawan mutanen gidan ke shiga, shiyyasa mafi yawanmu zaki samu kowa da fo ɗinsa na kashi a ɗaki ko ƙaramin botikin fenti, da safe idan bakai azamar tashi kai wanka ba to fa ka tabbata ƙila sai dare ko goshin magriba zaka samu damar yinsa, shiyyasa da yawanmu mukan jera kwana biyu babu wanka.
Tunda na taso a gidan na ganmu, hakama mafi yawan waɗanda suke gidan haka na tashi na gansu, dan har takai mun wuce ƴan zaman haya sai dai ƴan uwa. mahaifina da mahaifiyata duk haifaffun garinne, kuma dukkan danginsu suna ciki suna rayuwa, hasalima akwai masu arziƙi a ciki. Sai dai kowa yasan halin zuciya irin ta wannan zamanin, inhar baka da shi to kaida banza duk ɗaya kuke, kai tsaye ma ake mantawa da kai a cikin dangi. To ballema irin iyayena da suka kasance nakasassu, inhar za’a iya mantawa da mai ƙafafu da hannu da idanu saboda talauci ya masa katutu ta yaya kake tunanin ba za’a manta da musakan iyayena da bayan rauni da ALLAH ya jarabcesu da shi na halittar jiki harda talauci ba?. Ni kaɗai iyayena suka haifa a duniya, nima an jima ba’a sameninba, sai da ga baya ALLAH ya azurtasu da samuna matsayin ƴa ɗaya tilo a garesu, duk da talaucin iyayena da kasantuwarsu nakasassu ni ƴar gatace, dan gwargwadon iko iyayena tsaye suke a kan bani tarbiya, nakanje makarantar gwamnati kamar yanda sauran ƴaƴan gidanmu ke zuwa, hakama ina zuwa islamiyya. Sai dai aduk lokacin da aka buƙaci wani abu da ga makaranta da yafi ƙarfin ƙarfinmu hankalin iyayena kan tashi da ni kaina, wannan yasa da yawan lokuta karatun nawa ke kwan gaba kwan baya, dan kuwa ƴan ajinmu sunsha tsallakewa gaba su banni da maimaita aji saboda rashin kuɗin abu idan an buƙata tamkar ba makarantar gwamnati ba. Badan bani da ƙoƙari bane, a wannan ɓangaren ma ina sahun farko na gwarzayen yara masu ƙwaƙwalwar karatu da fahimtarsa, sai dai rashin kuɗi ke daƙileni a kulum……………………..
STORY CONTINUES BELOW

Tunda Bilkisu ta fara bama Jay labarin rayuwarta idanu kawai ya kafeta dashi ko ƙyaftawa bayayi, ko sau ɗaya bai katseta ba har saida takai aya, fuskarta shaɓe-shaɓe da haye ta juyo tana kallonsa. “Wannan itace asalin Bilkisu da take gabanka, mai rawa da bazar Dad, badan shi ba babu mai sanin wannan BILKEESUN bare ya bibiyi tarihinta, Yah Jawaad, bazan bijirema aurenkaba, dan har yanzun bansan asalin ƙullashi ba, sai dai kasani rashin auren Yah Qaseem tamkar butulcine daga alkairan Dad a gareni, ya ɗaukeni a lokacin da kowa ke ƙyamata, ya mini gata a lokacinda masu gata ke gudun raɓata, ya tsaftace rayuwata a lokacin da datti mai ciwo ke lulluɓe da ita, shin baka ganin ya cancanci fiye da auren jininsa a gareni koda kuwa matarsa bata ƙaunata?”.
Jawaad dake kallonta idanu jazur ya ɗauke kansa daga gareta a karo na farko, murya a dakushe yace, “Bazan musa miki cancantar Dad da abinda yafima haka daga garekiba, sai dai ni Jawaad Abdul-Aziz Yusif nace bai cancanci samun sadaukarwar komai daga gareki ba”.
Sosai nai masifar waro idanu ina ture bargon da naketa faman rufe jikina dashi da, nama manta boss ne a gabana, dan haka cikin zafin rai nace, “Kai wanene da kake tunin Dad bai cancantaba? Yaushe ka sanni harda zaka iya aza mizanin cancantarsa da kalaman son sakamin shakku da baƙantasa a gareni, y…….”
“Yah isheki!!”. Ya faɗa cikin daka tsawa yana ɗaga hannu tamkar zai makeni. Baya nai da sauri ina mai rumtse idanu dan nama sadaƙar mazgenu zaiyi.
Jawaad ya rintse hannun da yakai zai maketa yana lumshe idanunsa tare da danne lip ɗinsa na ƙasa da haƙori tamkar zai hudashi, kusan sakan ashirin suna a haka kafin shi ya fara buɗe nasa idon da hannun yaja goran ruwa dake bed side drawer yasha, ahankali abinda ya tokare masa maƙoshi ya faɗa, ya maida jikinsa ya jingina da gadon yana ƙoƙarin dai-daita nutsuwarsa.
Nima jin bai makeninba yasa na buɗe idanuna, karan farko a rayuwata da nakejin zafinsa, miyasa yakeson aibantamin Dad ɗina bayan shine yaymin gatan da har shiɗin ya shiga cikin jerin masu sanina….?
Jay daya ji ƴar nutsuwa tazo masa ya sauke numfashi daɗan ƙarfi, batare da ya juyo ga bily ba yace, “Ina su Firdausi da iyayenta?”. Kamar bazan tanka masaba sai dai nace, “Tun randa na baro gidan bayan kwaɗama Jazuga abu ban sake waiwayarsa ba saboda inajin tsoro, Nima babban burina a yanzu sanin halin da suke ciki, musamman dana yawaita mafarkinsu a kwanakinan”.
“Miya hanaki waiwayarsu bayan lafawar abubuwa?”.
Kallonsa nai da mamaki, nace, “Taya za’ai batun kisan kai ya iya lafawa? Kasheshifa nayi da wannan hanun nawa”. Nai maganar ina mai fashewa da kuka da nuna masa hanun nawa.
Murmushi naga yayi, dukda dagani kasan na takaicine hakan bai hanani jin ciwoba. Ya juyo sosai yana kallon hannuna da nake nuna masa, sai kuma ya ɗauke kansa. “Wace anguwa su Uwargida suke?”.
“Harna baro gidan bansan anguwarba nima”. Baice komaiba ya sauka daga gadon, saurin ɗauke idona nai daga garesa ganin gajeren wandone a jikinsa wanda iyakarsa rabin cinyarsa. Bai sake cemin komaiba tsahon lokaci yanata safa da marwa a ɗakin, nidai gittawarsa kawai nake iya hangowa ban yarda na ɗago na sake kallonsa ba. Yazo gabana ya tsaya, hakan yasani ɗagowa na kallesa a tsorace, “Wa bincikenki ya nuna yayma Amina fyaɗe?”. Wani irin muguwar bugawa ƙirjina yayi akan wannan tambaya batare da nasan dalilin hakanba, maimakon na bashi amsa sai kawai na fashe da kuka.
Tsura mata idanu kawai Jay yayi cike da mamaki? Yanzufa ta bashi labarin komai tiryan-tiryan, amma ya mata tambaya ta saka masa kuka. A dake yace, “Qaseem ne?”. Kasa bashi amsa nai saboda wani irin juyawa da kaina keyi tamkar ana bugamin guduma, da sauri nakai hannu biyu na riƙesa ina faɗin, “Ya ALLAH kaina”.
Babu shiri Jawaad ya durƙusa a gaban gadon ya tarota ganin zata faɗi, saurin kwantar da ita yay ya kama kan ya riƙe cikin hannunsa yana janye nata hannun, addu’a ya shiga yimata jin kan ya ɗauki wani mugun zafi maiban mamaki, ga jikinta ya ɗauki wani irin rawa. Cikin matuƙar sarƙewar halshe take faɗin, “Kamin addu’a, kamin addu’a dan ALLAH, kaina zai fashe, wayyo kaina”.
Tsahon lokaci yana mata addu’a har tai shiru, jikinma ya daina rawar da yakeyi, bai dainaba cigaba yay da mata har saida yaji zafin kan ya ragu sosai barci ya ɗauketa kafin ya miƙe, alwala yaje ya ɗauro yazo ya saka dogon wando ya kabbara salla.
Kusan ƙarfe uku da rabn ta farka, nama manta a ina nake sai dana gansa a zaune da alkur’ani a hannu sannan na tuna. Yunƙurawa nai na tashi da ƙyar dan jikinna kam ciwo yake min, nima alwalar na ɗauro nazo bayansa na saka wani abin sallar na tada.
Jay duk yanajin motsinta, sai dai baiyi maganaba saboda karatun da yakeyi.2
STORY CONTINUES BELOW

UBANGIJI mai rahama da jinƙai sai ya bama Bilkisu da Jawaad damar raya wannan dare da ibada har akai kiran sallar asubahi.
★★★★★★★
Tunkafin ya dawo sallar asuba na gyara ɗakin na wanke har toilet, ina cikin gyaran falon saman ya shigo, dauriya kawai nakeyi dan wani irin barci nakeji fiye da zato, batare dana kallesa ba nace, “Ina kwana”. “Lafiya, waya saki wannan aikin?”. Kaina a ƙasa har yanzu nace, “Babu kowa”. Gaba yay yana faɗin, “Ki barsa iya nan kizo ki shirya na ajiyeki inada ayyuka da yawa yau”. ban iya cewa komaiba harya shige, dubana na maida ga agogon falon, ƙarfe shida da minti talatin da huɗu. Ƙarasa mopping ɗin nayi da sauri-sauri.
Yanda tai gyaran gadon sai ya kasa daina kallonsa, da ƙyar ya iya ɗauke idanunsa, abu ya ɗauka ya fita daga sashen gaba ɗaya yana jaddadama Bilkisu tai wanka kafin ya dawo.
Kayan sharan naje na ajiye na nufi ɗakin, a gaggauce nai wankan dan banason yazo ya iskeni, babban tawul da yafi kowanne girma na ɗauro na maida hijjabi jikina na fito, ina isa gaban mirror yana shigowa da sallama, ALLAH ya soni ban cire hijjabinba, na amsa masa kaina a ƙasa. Ledar hannunsa kawai ya ajiye saman gado ya nufi toilet yana faɗin, “Ga kayan da zaki sakanan”.
Sauri-sauri na shirya cikin doguwar rigar dake cikin ledar ruwan sararin samaniya, sai sabon hijjab har ƙasa fari tamkar wata matar liman, na fita dan bana fatan ya fito ya samini a ɗakin.
_______________________
Misalin ƙarfe bakwai da mintuna arba’in Bilkisu da Jawaad suka fito daga sashensa.
Addu’a naketayi a raina ALLAH yasa karmu haɗu da kowa, ALLAH kuwa ya amsa min ma muna fitowa ashe motar da zamu fita na a kusa. Da kansa ya buɗemin na shiga, sannan ya maida ya rufe ya zagaya mazaunin driver. Bazan ɓoye mukuba banason tuƙinsa, dan na kula ya iya zuga gudun tsiya a hanya. To amma babu yanda na iya.
Haka muka tafi babu mai cema wani uffan a cikinmu, sai dai naji daɗi sosai yanda naga mun nufi masarauta kai tsaye. Yauma kamar ranar a ƙofar farko ya tsaya, waya ya ɗauka yay kira. bayan ya ajiye wayar ya juyo yana kallona.
“Ya sunan anguwar da kuka zauna?”. kaina a ƙasa nace, “Bankaura”. “Zaki zauna a gida yau sai gobe idan ALLAH ya kaimu zaki koma aiki, ki dage da addu’a, kina dai ganin duk abinda ke faruwa”. Kaina na jinjina masa nace, “Insha ALLAH, amma dan ALLAH miyasa jiya kace ban cancanci nai sadaukarwa ga Dad ba?”.
Shiru kamar bazai tankaba, kusan sakan biyar sannan ya juyo yana kallona, “Lokaci zai nuna mana komai, babu abinda zaki iya fahimta a yanzu sai ruɗani, kije idan lokaci yay zaki sani”. Kafin nace wani abu su Amaturrahman da Amintacciyar baiwar gimbiya sun fito a mota. Gaishesa sukai cikin girmamawa, ya amsa shima fuska aɗan sake yana faɗin, “Kucema Ummu ga amanarta nan ban ciba”. Dariya Amintacciyar baiwar gimbiya tayi tana faɗin, “Jiya kam ai tayi faɗa tamkar ta ari baki anƙi maido mata ƴarta”. Murmushi Jay yayi kawai yana ɗan kallon gefen da Bily take suna magana da Amaturrahman kafin ya ɗauke kansa.
Sallama yay mana ya tafi, Muna shiga daga ni har Amaturrahman barci muka kwanta dan shi nakeji fiye da komai a yanzun.
______________________________
Jay yana ajiye Bilkisu Office ya nufa, ayyukane fal kansa har baisan da ina zai faraba, yana zama abinda ya farayi shine bige-bigen waya, a kiran farko Umarni ya bada a nemo masa gidan da Bilkisu ta sanar masa sun zauna da iyayenta a Anguwar Bankaura, tare da ainahin maigidan da halin da gidan yake ciki yanzun. Kira na biyu kuwa Ainahin gidansu Baba makaho inda aka haufesa yasa a binciko masa shikuma a Anguwar Tudin Jarƙasa.
Sunyi zaman awa biyu shida su Aliyu, duk da yaga ɗacin ran da Rose takeyi baibi takanta ba, bayan sun kammala ta buƙaci yin magana dashi, ca yay mata bashi da lokaci yanzun kam saita bari wani lokacin. Cike da takaici ta riga kowa fita. Haka ya cigaba da rage akainin gabansa.
Misalin sha biyu yabar station zuwa Barrack ɗin sojoji da suka fara zuwa jiya kafin su tai jejin nan, ya samu ganawa da Lieutenant General a tsaitsaye dan ya iskesa yana shirin fita, ya sanarmasa wajen baba ƙaura yazo. Lieut G ya saka wani soja yayma Jay rakkiya har gidan da baba ƙaura yake zaune a cikin Barrack ɗin.
Baba ƙaura ya tarbi Jay da murmushinsa mai tsayawa mutum a rai, bayan sun gaisa ya sake yima Jawaad ta’aziyya. Jawaad yay masa godiya akan gudunmawar da ya basu jiya. Fuska ɗauke da murmushi baba ƙaura yace, “Yaro bani nayiba ALLAH ne yayi”. “Hakane baba” Jawaad ya faɗa cikin sake tabbatarwa. shiru suka ɗanyi na wasu sakanni, baba ƙaura yace, “Mike tafe da kai?”. Ɗagowa Jay yay ya kallesa da ƙyau, ya tsufa sosai sai dai yana tare da ƙarfinsa, bashi da tsaho sosai sannan shiba wada bane, ya risinar da idanunsa yana faɗin, “Maganganunka na jiya baba na kwana juyasu a rai, sai dai har safiyar yau ban iya samo amsar ko guda ba, baba mika sani a kanmu?”. Murmushi baba ƙaura yay idonsa akan Jawaad, yace, “Yaro bansan komai a kanku ba, hasalima jiya na fara ganinku a iya tsahon rayuwata, kowane irin mutum a duniya yanada baiwarsa, ni tawa baiwar kenan, fahimtar wasu abubuwa daga mutane, akwai mutane masu irin wannan baiwar tawa da yawa a duniya, sai dai mafi yawansu sunfi zaɓar aikata saɓon ALLAH da tasu damar, sai kaga mutum ya zama ɗan tsubbu ko naɗama kansa wani girman da zai halakar da mutane daga barin ALLAH, ko ya maida baiwar tasa ga zalunci da neman duniya. wlhy kaji na rantse maka bansan komai daya shafekuba face abinda UBANGIJI ya bama idanuna ikon gani tattare daku jiya…..”
Cikin jinjina al’amarin baba ƙaura Jay yace, “baba ko zamu iya sanin abinda ka fahimta ɗin?”
Murmushi Baba yay da faɗin, “Yaro minene sunanka?”. Jay yace, “Jawaad”. “Masha ALLAH, malam Jawaad bawani abune na gani a rayuwar kuba, domin kuwa ƙaddarar da duk ke cikin rayuwar kowanne ɗan adam wannan ɓoyayyen sirrine daga taskar ALLAH, abinda ALLAH ya bani ikon gani tattare daku kawai shine rayuwarku na ɗaure da wani al’amari mai girma, sannan kunada taurari masu ƙarfin haske da suka hana duhun dake zagaye daku tasiri, dan har na waccan yarinyar sunfi nakama haske, abinda nazarina ya bani bayan faruwar abubuwa a dajin nan shine akwai sihiri mai ƙarfin gaske jingine da jininku, su wanene sukai muku? Miye dalili? Saboda mi? Daga yaushe ne? Shine ban saniba sai abunda ALLAH yasio sanar daku nan gaba”.
Cikin ɗaurewar kai Jawaad yace, “Amma miyasa kanema sanin sunan mahaifinta?”. “Saboda duhun dana gani biye da bayanta yafi naka rintsi”. “Duhu kuma baba?”. “Ƙwarai duhu ɗana, amma da sannu zai yaye insha ALLAHU bisa rahamar ALLAH, shawarar dazan baku shine ku dage da addu’a da sadaka musamman a cikin wannan watan mai albarka na Ramadhan da zamu shiga nanda kwanaki uku idan munada rabon kaiwa. Kunika ciyar da bayin ALLAH fiye da yanda kukeyi a baya, ku saka dubunnan marayu farin ciki fiye da yanda kukeyi a baya, ku kaima UBANGIJI kukanku fiye da yanda kukeyi a baya, sannan a daren jiya naga wani haske dake nesa da kai na tunkaroka, sai dai yana nesa dakaine, bansan tayaya zakaje garesaba koshi yazo gareka”. Da sauri Jay ya kalli baba ƙaura, “Baba ko hakan nada nasaba da mafarkin da nake mai sarƙaƙiya?”. “ALLAH kaɗai yasan gaibu Jawaad, amma tun yaushe ka fara mafarkin?”. Jimmm Jay yay alamar tunanin, yace, “Baba idan har ban mantaba na farayinsa a daren da muka dawo daga wata horaswa daga ƙasar America ne, shekara kusa ɗaya kenan, sai da danayi sau ɗaya ban sakeba sai a watanan nan naketa maimaitawa, bayan ɗaurin aurena da ita sai kuma ya canja salo”. “Ikon ALLAH,to shidai mafarki sirrine yaro, sannan akwai abinda yake ishara daga UBANGIJI a cikinsa, akwai wanda shaiɗanu ke jinginuwa a cikinsa, akwai wanda keda alaƙa da saka abu a rai, to amma kozan iya jin wani abu daga mafarkinka?”. Babu musu Jay ya faɗa masa na farko da wanda yay a ƙarshe washe garin ɗaurin aurensa da Bilkisu bayan sallar la’asar. Baba ƙaura ya daɗe baice komaiba, yanata juya abun a ransa amma bai samu wani hasken da yake buƙataba, ya ɗago ido ya zubama Jay na tsahon lokaci kafin ya janye, “Alƙar jini a cikin jini yanada nasaba da kamar kun haɗa jini kenan nidai a nawa ɗan sanin da UBANGIJI ya banifa, amma sanin gaibu sai ALLAH”. Sam Jawaad bai fahimci komai daga kalaman baba ƙauraba, dan a iya saninsa babu ta inda yakeda dangantaka da Bilkisu sai ta wajen su Hudah….. Baba ƙaura ya katse masa tunani da cewar, “Sarƙaƙiyar dake ɗaure da rayuwarku tanada nasaba da wani zalincin mai tushe daga wasu jininku, UBANGIJI shikaɗai yasan sirrin dake ɓoye dai, amma a mafarkinka mutum kake gani yana sanar dakai kokuwa?”.
“Da farko dai bana ganin kowa, amma daga bayan nan mace nake gani, gashi na santa a mafarkin, sai dai dana tashi fuskarta saita ɓacemin, duk iya hasashena bana tunota”.
“To UBANGIJI shi kaɗai yasan dalilin sirranta maka ita a zahirin taswurar zuciya, kuje kucigaba da addu’a, ALLAH bai manta da al’amarinku ba. Ga wannan gadalin (maganin), karkaji komai sanine daga abinda ALLAH ya sanar dani nima, saboda bibiyarta da ake ana tsoratar da ita dalilin abinda ke hannunta nasu ALLAH bazai basu damaba insha ALLAH, a zubashi a Abu mai tsafta, a karanta Ayatul kursiyyu (itace aya ta 255 a suratul baƙara), suratul Yunus aya ta 79~82, Suratul Ɗaha aya ta 65~70, Suratul Kafirun, Al-Ikhlas, Al-Falaq, An-Nas, a tofa ciki, A shafe jiki da shi akuma ringa sha safe da yamma, sannan ai turare da wannan. Insha ALLAHU duk wani baƙin aljani da aka haɗata dashi zai gusa, zaku samu haske mai yawa akan al’amarin cikin amincin ALLAH, sihirin dake jikinku zai warware da izinin UBANGIJIN al’arshi.
Ada Jawaad ya tsani irin waɗanan abubuwan, amma jin baba ƙaura ya ambata harda ayoyin ALLAH saiya amsa yay godiya, sunɗan ƙara tattaunawa yay masa sallama ya tafi.
Daga Barrack ɗinan tasha ya nufa inda gimba ke hawa motar garinsu idan zaije gida weekend……………..✍2
😉🤫👍🏻😘.
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.10
Page 33
……………A ɓangaren gidan Dad komai ya ƙara caƙuɗewa, yakasa barin ƙasar koda kuwa zuwa Niger ne, komai Shahudah batayi yanzu banda aikin kuka da kiran Jawaad, ta tabbatar musu indai basu rabata da Habib sun maidata gidan Jawaad ba saita kashe kanta, kullum cikin lallaɓata suke da mata alƙawarin samun Jawaad duk rintsi kuma har ƙarshen rayuwa, zakuma su rabashi da bily koda tsiya dan ita kaɗai ta mallakesa, acewarsu tabari ya gama hayaƙin rashin mutuncinsa yanzun sunada hanyar maganinsa ne.
Qaseem kan tun bayan barin Jay asibiti da Bilkisu ya shiga wankama Doctor mari akan ya buɗe masa ƙofa, cikin gigitar azaba Doctor ya buɗemasa ƙofar ya fita, koda ya fito sai bai iske su Jawaad ba, cike da mahaukacin gudu ya ɗauka motarsa ya fice daga asibitin. Marukan da yayma Doctor ne yasaka sauran Doctors ɗin asibitin alwashin ɗaukar mataki, atake suka kira police, ko jinin dake fita ta hancin Doctor basu tsaida masaba saida ƴan-sandan sukazo suka gani.
Qaseem daya fita yana can yana bilayin neman su Jawaad titi-titi bayan yaje gidansu ance Jay baizo nanba, ya nufi gidan Jay na A.Y street ne ƴan-sandan da aka tura kamashi da yawun hukumar lafiya ta ƙasa sukai ram dashi, duk yanda yaso musu taurin kai da nuna musu shiɗin wanene ɗan wanene sunƙi saurarensa. Dan kuwa dai shima Doctor ɗin da ya mara ɗan wani ƙusane a ƙasar, gashi ma’aikaci a asibitin gwamnati, shiyyasa kamun Qaseem ya taho tun daga sama.
Yau tsahon kwanakin Qaseem biyu kenan a police station batare dasu Dad sunma saniba, su duk tunaninsu Qaseem na gidansa ne tunda fushi yake dasu bazasu ganshi a yanzuba.
Salman ma dai daƙyar suka lallashesa ya haƙura da batun barin ƙasar, dan yacefa shi lokacin mutuwarsa baiyiba da zai tsaya ɗan-fir’auna ya sakashi cikin jerin waɗanda zai watandarsu kamar kajin salla, da farko Mom masifa ta fara masa, da dai taga babu ci sai ta koma lallaɓashi har Dad ɗinma, da ƙyar ya haƙura akan shifa da yaga wani motsi zai ware abinsa, da wannan ajandar tasa suka yarda, ba komai yasa basason yay nesa dasuba sai sanin halinsa musamman akan shaye-shaye, shiyyasa basason yay nesa dasu, ALLAH dai yasosu abin bai nisaba suka tsaya kansa ya haƙura.
Momy dake haɗama Dad tea takai dubanta garesa, yay shiru tamkar babushi a d/table ɗin, gaba ɗaya rikicewar da gidan yayi yasa sun fita hayyacinsu daga ita harshi, wani irin jin ƙarin tsanar Bilkisu tai a ranta, dan kuwa a ganinta duk itace sanadin komai, shigowarta rayuwarsu ne ya tarwatsa musu gida, da Dad bai jajubo musu itaba da yanzu suna zaune cikin kwanciyar hankalinsu, siririn tsaki taja tana mai dangwarar masa da kofin tea ɗin gabansa. Kallonta yay da mamaki, yace, “Lafiya kike tsaki? Bayan kinsan abinda nafi tsana kenan a rayuwata?”.
Momy ta kuma jan wani tsakin tana cigaba da zuba masa farfesun bindin sa ɗin da takeyi, “Bakai nakema tsakiba nikan Dadynsu, sanadin tarwatsewar gidana na tuna, lokacin da zaka ɗako yarinyarnan dana nuna ɓacin raina fushi kaitayi dani, ka ringa nunamin batada maraba da ƴaƴanmu jininmu a wajenka, gashi kaga sakamakon daya biyo baya ai, ka ɗakkota daga inuwa ita ta turamu rana, ranarma mafi munin zafi da ƙuna, nikam dai wannan zuminci naku ai ALLAH ya tsine mar (Wa’iyazubillah, Mom zuminci ya wuce tsinuwa, dan yana ɗaya daga cikin hanyoyin shiga aljannah🙄).
Dad yace, “Humm, wlhy kuma kingafa Aysha duk da wannan abun daya faru sai ban daina jinta a rainaba, a ganina yarinyarnan bata da laifi akan rikicinan, daga gidanku aka harɗa komai, kekuma gashi bakison laifin danginki sai nawane sakarkaru ko?!”. Yanda yay maganar da zafi-zafi ya saka Momy kallonsa da mamaki fuska a yatsine tace, “Ikon ALLAH, kaifa nagama sammun yarinyarnan yafi cinka fiye da kowa a gidannan kai da wannan shashashan Qaseem, to wlhy inma ban ɗauki matakin ƙarshe akan yarinyarnanba kuce ba sunana Aysha Humaira ba Mtsowww!!” ta ƙare maganar da buge table ɗin ta tashi tabar wajen.
Duk wannan abu dake faruwafa tsakanin Dad da Mom Shahudah da Aamilah na zaune a D/table ɗin suma, Aamilah dai earpiece ne a kunnenta tanajin waƙa, shiyyasa batasan mi tsoffin nata je tattaunawa ba, Shahudah kam cikin damuwa take mai gusar da hankali, zuciyarta gaba ɗaya tana ga Jawaad da tunanin ina Bilkisu?, dan a yanzu dai wannan matsalar tafi cin zuciyarta fiye da komai, ɗan-fir’auna tasan ko kotune Dad sai ya kaisa ya saketa, inmafa bai saketanba ita ahaka zatai aurenta tunda ai bada soyayya tsakaninsu aka ɗauraba, a ganinta tunda babu soyayya ai auren bai ɗauruba kenan (Hudah Kai a tukunya😖😂 lol).
Buga table ɗin da Mom tayine ya maido hankalinsu kansu, duk suka bita da kallo kafin su kalli Dad da shima kallon Momyn nasu yake rai a matuƙar ɓace.
Aamilah dai baki ta taɓe ta cigaba da sauraren waƙarta dacin abinci, Shahudah ce dai ta kalli Dad ɗin bayan ɓacewar Mom a idanunsu. “Dad wai faɗa kukeyi ne?”. Huda tai maganar tana mai tsatstsare Dad da manyan idanunta da suka koma ƙanana a yanzun saboda tsabar yawan kuka. Kansa ya girgiza mata yaja bowl ɗin data saka masa farfesun ya fara shan romon kawai dan kauda hankalin Shahudah daga abinda take zargin.7
STORY CONTINUES BELOW

___________________________________
Jawaad kam daga wajen baba ƙaura tashar da Gimba ke shiga mota idan zai tafi gida ya nufa. Wajen bawani babban tsasha baneba, dan motocin garin su Gimban ne kawai sai masu ƙarisawa cikin ƙauyikan dake maƙwaftaka dasu. Kowa na sabgar gabansa daga masu talla har matafiya da masu sauka, sai ƴan mashinan Napep dake ɗaukar masu shiga cikin gari idan an saukesu a tashar. Sai da ya gama ƙarema wajen kallo daga cikin motarsa kafin ya ɗauki glasess ɗinsa baƙi ya toshe idanunsa dashi, baya wani cikin mood ɗin farin ciki, hakan yasa sam fuskar babu alamun sauƙi balle rangwame. Tamkar zakin dake taƙama bayan yaci ya ƙoshi haka ya fito daga motar, dama tun fakawarsa mafi yawan jama’ar dake kai kawo a wajen suka zubama motar ido da tsumayen waye zai fito daga cikinta, dan kuwa dai taci ta ƙoshi ita kanta motar balle kuma mamallakinta a ganinsu dole ya zama abin kallo. Yako zama abin kallon dan shi kansa saida ya takura dajin yanda idanu ke yawo a kansa har jinin jikinsa na tsitstsinkewa. Guntun tsaki yay yana sake ɗaure fuska, ya fara taku a hankali yana tunkarosu kansa tsaye.
Tuni da masu kallon nasa da masu gulma suka nutsu, aka shiga gaishesa da tambayarsa ko akwai abinda yake buƙata?. Ta cikin glasess ɗinsa yake ƙare musu kallo ɗai-ɗai, sukam sam basa ganin idanun nasa, sai ƙyawun da glass ɗin yayma fuskarsa ba ƙaramin ɗaukar hankalinsu yayba. Jawaad ya shiga ƙarema saurayin dake gabansa tamkar zai duƙa kallo, nuni yay masa da hannu alamar ya miƙe da ƙyau. Babu musu kuwa ya miƙe. “Inason ganin shugaban wajen nan naku ne”. Jay yay maganar yana maida hannunsa guda cikin aljihun wandonsa. Kafinma saurayin yace wani abu wani dattijo da kallo ɗaya zakai masa ka fahimci wahalace ba tsufaba ya ƙaraso wajen yana mai amsa maganar Jay data shiga kunnensa. “Gani nan Alhaji, barka da zuwa, naɗan zagayane kama ruwa shiyyasa”.
Shi dai jay kallonsa kawai yake harya dasa aya. Dattijon ya kuma faɗin, “Muje daga cikin runfa Alhaji nan kaga rana na dukanka”. Babu musu Jay ya bisa suka shiga rumfar da ƙuda keta faman bi saboda sanyinta, ga robobin abinci da sukaci harda na fura duk ƙudan ya baibaye, gefe kuma masu saida abincinne ƴammata da yara ƙanana abin gwanin ban tausayi. Shi kallonsu yake da tausayawa sukuma suna kallonsa da birgewa da sha’awa. Duk da Jay yaji ƙyanƙyamin tebiran dake wajen matsayin abun zama haka yay shirin zaunawa akai da farin wandonsa tas daketa ɗaukar ido. Da sauri dattijon nan ya dakatar dashi, abin sallar dake can kan babbar tabarma shimfiɗe ya ɗakko bayan ya bugata ƙura ta tashi, yazo ya saka masa kan bench ɗin. Jay baice komaiba ya zauna duk da itama dai sallayan sai a hankali.
Dattijo yace, “Alhaji bara a kawo maka ruwa ko fura”. Da sauri Jay yace, “A’a nagode karka damu, tambaya nazo yi”. Dattijo yace, “ALLAH yasa na sani to Alhaji. Jay yaɗan gyara zamansa, idanunsa dake cikin glass kafe akan Dattijo, yace, “Akwai wani yaro saurayi da bazai wuce shekaru talatin da ɗaya ba mai suna Gimba, duk ƙarshen mako yake zuwa nan ya shiga mota ko kun sanshi?”. Cike da jimami Dattijo yace, “Tabbas munsan Gimba, ai a wajenan kaf Alhaji babu wani driver da zai ce maka baisan marigayiba, danshi mutum ne na mutane ga barkwanci ga alkairi”. Jay Cikin nuna alamun kamar bai sani gimban ba yace, “Naji kace marigayi; kana nufin ya rasu ne?”. Zama Dattijo ya gyara yana matsar ƴan ƙwalla, “Alhaji ashe bakasan ya rasuba? Ai jiya-jiya akai zana’idarsa ma, muma yau labari yake zuwa mana akan duk yanda abun ya faru, ance ogansa da yakema aikine yajasa cikin ƙungiyar asiri, dama anata ƙananun magana akan yanda Gimban kema mutane ɓarin abin arziƙi a garin musamman a irin wannan watan na Ramadhan dazai kama, to dai kasan mutanenmu da kwaɗayi, dukda anajin tsoro dai haka ake amsa a lashe, sai ya gusa kaji anayi dashi, saifa yanzunne da suka tsotse jinsa zance keta fitowa abubuwa gasu nandai barkatai babu daɗin ji”. Tunda Dattijo ya fara magana jikin Jay ke wani yaamm na mamaki, haka kuma aka maida zancen rasuwar gimban ahi baida labari?, kai ɗan adam sai dai ka gansa ka barsa da halinsa kawai, baiji komai a ransaba tunda yasan ba hakan bane, abinda kawai ya ɗauka jahilci ne ke aiki cikin ƙwaƙwalen kansu. Ya gyara zamansa cike da ƙwarewa cikin salon aiki yace, “Ai nima akan batun mai gidan nasa nazo daman, yanzu haka mun kamashi a hannu bincike mukeyi, idan ka bamu haɗinkai kaima kanada naira dubu hamsin sabbi ƙar a takarda. Jimm Dattijo yayi yana ninƙaya a nazari, mikuma ya tuna sai ya kalli Jay yace, “Nikuwa mina sani akan wannan zance Alhaji?”. A karan farkio Jay yay murmushi, “Ba canai ka saniba daman ai, sonake dai naji abinda ka sani ɗin, ranar juma’a Gimba yazo tashar nan taku?”. Dattijo yace, “Eh to kamar dai yazo”. Jay daketa dannewa bayason ya tsoratashi yace, “Banason ƙwana-ƙwana a magana, ka fitomin a mutum mu wanye lafiya”. Ya ƙare maganar da zare glass ɗin idonsa sukai ido huɗu da Dattijo. Sosai kwarjinin Jawaad ya sake cikama Dattijo idanu dama wajen baki ɗaya. kasa jurar kallon idon da Jay ke masa yayi ya duƙar da kansa. Jawaad yay wani munafukin murmushi yana ɗauke kansa shima, “Yaya zan samu amsar gaskiya?”. Kai Dattijo ya ɗaga batare da ya yarda ya sake kallon Jay ɗinba. “Tabbas yazo nan ranar juma’a nayan an sakko masallaci”. “A motar wa ya tafi gida?”. “Bai shiga motar kowaba ranar a tashar nan”. Cikin ƴar fusata Jay yace, “To motar wa ya shiga?!”. “Ni…ni bansanshi ba Alhaji”. Murmushi Jay ya sakeyi irin na zan lailaya kanka a titi ɗinan ya ɗaga jacket ɗinsa ƙaɗan yace, “Kalli nan”. Koda Dattijo ya ɗago yauy arba da bindiga sai ya waro idanu waje, kafin kace kwabo zufa ta gama jiƙesa. Jawaad yace, “Saika zaɓa, amsata ta gaskiya kokuma rasa numfashi?”. “ALLAH ya baka haƙuri oga, wlhy inada iyali da ƙananun yara a gida, abinne wuya garesa shiyyasa”. “Kai kake ganin wuyarsa”. Cewar Jay yana haɗe fuska fiye da farko. Cikin kakkausan murya yasake faɗin, “A wace mota gimba ya tafi gida ranar juma’a?”. “Tare da ɓaleru” Dattijo ya faɗa da sauri kamar zai haɗiye harshensa.
Jay ya sake zare glass ɗin idonsa a karo na biyu, sun sake kaɗawa sunyi ja da ɓacin rai, “Wanene Ɓaleru?”. Ya faɗa yana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya da harɗe hannayensa saman ƙafar yanaɗan juya glasess ɗin hannunsa idanunsa kafe akan dattijon. Kan Dattijo a ƙasa yace, “Shima ɗan garinmu ne, zanma a iya ce maka kamar abokai suke da marigayi gimban, dan duk sa’anni ne kuma unguwarsu ma kusan ɗayane”. “Ina zan samesa yanzun?”. “Wlhy oga ban saniba, kawai dai nasan yana anan birni shima yana aikin drivernci a wani gida”. Miƙewa Jay yayi tsaye da cewar, “Koma ina yake ni zan memosa, ba’a cin kuɗina a matsayin cin hanci, amma ina biya idan na saka aiki, zan baka aiki nakuma biyaka yanzunan, ya rage naka kaimin da gaskiya kokaci amanata idan anzo an biyaka abinda yafi nawa, biyoni”.
Jiki a saɓule dattijo yabi bayan Jay har zuwa isa inda ya faka motarsa. Jawaad ya buɗe motar ya shiga ya zauna batare daya rufeba, ƙafafunsa duka a waje, takarda ya ciro da pen ya kalli Dattijo dake tsaye, “Ka iya karatu ne?”. Da sauri Dattijo yace, “Eh nayi sakandire Oga”. Jay baice komaiba ya maida kansa yay rubutu da hausa a takardan sannan ya miƙa dattijon tare da kuɗi bandir ɗin ɗari biyar. “Wannan aikin zakaimin, ga kuɗin aikinka nan”. Daga haka ya shige motar sosai ya rufe abinsa yaymata key tare dayin reverse yabar wajen.1
STORY CONTINUES BELOW

Ganin lokacin sallar zuhur yayi sai ya tsaya yay sallah kafin ya ƙarisa station, tunkan ya shiga office ɗinsa ya samu kira daga sir Ahmad, fasa shiga nasa office ɗin yay ya nufi na Sir Ahmad ɗin. Ba’a masa iso dan zai shiga office ɗin sir Ahmad, knocking kawai yakeyi a bashi iznin shiga. Yanzunma kansa tsaye ya isa yay knocking ɗin, daga ciki sir Ahmad ya bashi izinin shiga dan yana kallonsa.
Cikin girmama ya gaishesa, Sir Ahmad ya rufe file ɗin gabansa yana kallon Jay ɗin dake zaune, “Ina ka shige hakane tun ɗazun nake aike a kiramin kai?”. “Am sorry sir na fitane”. “Okey to ya ƙarin haƙuri?”. “Alhmdllh sir”. “To ALLAH ya gafarta masa, ya raya abinda ya bari. Na kiraka ne dama akan Qaseem, wai yau kwana biyu yana hannun police”. Cike da mamaki Jay yace, “Police kuma? Basusan shiɗin wanene ba?”. Murmushi Sir Ahmad yayi yana kwantar da bayansa jikin kujera, “Sun sani sarai, gabace da gabanta, ya mari wani Doctor ne a General hospital shekaranjiya lahadi harya fidda masa jini, to Doctor ɗin ɗan Alhaji ɗan-iya warzu ne, shinefa yakai maganar hukumar lafiya ta ƙasa baki ɗaya, sukuma suka saka aka kama Qaseem ɗin”. Huci Jawaad ya furzar , shi shaf yama manta yabar Qaseem ranar a asibiti, yaso ya koma amma sai aka samu akasi, ya tabbata dalilin abinda ya faru ranarne Qaseem ya mazge Doctor, shi baisan yaushe Qaseem zai daina halin ƴan danbe ba ya rage baƙar zuciya. Yace, “Yanzu miya faru to Sir?”. Sir Ahmad yace, “I.G ne ya kirani da safen nan yake sanar min cewar shi Warzu yace sai anje kotu, shikuma yaga ɗaya daga cikin yaranane shiyyasa ya kira ya sanarmin dan anrma lauya, kuma ko babansa ma bai saniba”. Murmushi ne ya kufcema Jay, dan kuwa dai yasan lallai da Dad yaji da ba’a zauna lafiyaba, dan inma ɓakin son ƴaƴane Dad yatake Warzun ya shanye. “Miya baka dariya?” Sir Ahmad ya faɗa yana tsatstsare Jay da idanu. Kai Jawaad ya shafa yana ƙara sakin wani murmushin, “Sir abinne nasu ne ai, ni nasan Dad da yasan Qaseem na cell da yanzu garinan ya fara yawo a gajimare dan rikicinsa, kafaɗamin wane station ne? zanje na fiddosa yanzun insha ALLAH”. “To aini banƙi in baka damar cirosanba, kaima rikicin naka nake tsoro ai, dan baka da maraba da Dadyn naku, ta wani wajenma ka fisa zama ɗan ƙunar baƙin wake, nikuma banason ka haɗa harƙalla da Warzu dan shaiɗanin mutumne da kake ganinsa kullum cikin manyan kaya”. “Karka damu Sir salin alin zamu dawo”. “To shikenan gashi, saika nema lauyan Qaseem ɗin kuje tare”.
Sallama Jay yaymasa ya fita.1
Bai koma office ba ya sake ficewa, harga ALLAH bazai iya jurar tuƙiba, haka yake shi baison tuƙi saita kama dole, dolene yasan mafita, to amma shikam ‘Wane driver ne zai iya maye masa gurbin Ginbansa?’ yay maganar cikin rai zuciyarsa na masa zafi. Office ɗin Jabeer ya shiga, babu jimawa suka fito tare. Jabeer ɗinne ya jasu, sai da suka fara tafiya yaɗan dubi Jay ɗin daketa faman danne-danne a tab ya ɗauke kansa ya maida ga titi “Na zatafa wajen rasuwarnan ka koma?”. Jay da bai ɗagoba bai kuma fasa abinda yakeba yace, “A’a, dama sonake sai gobe idan ALLAH ya kaimu mu koma mu duka”. “Okey ALLAH ya kaimu” cewar Jabeer yana maida hankalinsa ga tuƙin.
Asibiti suka fara zuwa wajen Doctor Ballo Warzu, cikin girmama ya tarisu yana tambayar jikin Bilkisu?, mafi yawan amsarsa Jabeer ne ya bashi ita, sai da suka gama gaishe-gaishensu sannan Jay yay masa magana akan abinda ya kawosu, da tambayar miya faru bayan tafiyarsa?. Labarin komai Dr Bello ya basu, Jay ya dafe kai cikin takaici.
Shi dai Dr Bello haka kawai komai Jay yayi ƙyau yake masa da burgesa, haka ALLAH ke sakama bawa ƙaunar wani batare da wata manufa ba, yay murmushi yana kallonsa, “Karka damu abokina na haƙura indai nine, bansan ɗan uwanka bane dana barsa tun a ranarma baza’a kai hakaba saboda kai, naga rashin hankalin nasa ne yayi yawa shiyyasa naga gara aɗau mataki, amma yanzu kam yaci darajar mai daraja”.
Fuskar Jay ɗauke da guntun murmushi yace, “Nagode Doctor ALLAH yabar zuminci”. Shima Doctor godiya yaymusu, ya kuma rakosu har inda motarsu take, sai da yaga fitarsu sannan ya koma office yana kiran babansa a waya.1
★★★★★
Tunda suka shigo police station ɗin aketa basu girma, kai tsaye office ɗin d.p.o suka nufa, inda acan ɗinma dai suka tarbi juna da girmamawa kafin a ɗaura da gaisuwar mutunci. Jay da kansa yayma d.p.o bayanin abinda ya kawosa, ya kuma nuna masa lawyer’n Qaseem ɗin da ya shigo a bayansu dan shi isowarsa kenan. A take anan aka kashe magana babu zancen zuwa kotu sannan aka kawo musu Qaseem. Babu abinda akai masa, dan ko hararsa babu wanda yayi tunda aka kawosa gurin saima girmamawa, ko kayansa ba’a cire masaba, sannan ba’a haɗashi da kowaba a cell.
Kallon ido cikin ido sukaima juna shi da Jay, kowa ya ɗauke nasa fuska a tamke, Jay ya fara miƙewa ya fice abinsa, hakan yasa Qaseem jan tsaki, rai a ɓace ya kalli d.p.o yace su maidashi cikin cell ɗin. Duk kallon mamaki suke masa, Jabeer da yasan wasan ya dafa Qaseem ɗin yana magana a hankali, kamar Qaseem ɗin bazai yardaba sai kuma miya tuna oho masa ya nufi hanyar fita Jabeer da lawyer ɗinsa suka take masa baya.
A jikin mota suka iske Jay tsaye yana magana da Engineer ɗin da zai masa gyaran gidansa da Bilkisu zata zauna. Suna isowa yana ajiye wayar dan sungama. Sake ma juna kallon ido cikin ido sukai shi da Qaseem, cikin ɗacin rai Qaseem yace, “Miyasa ka cironi? Minene haɗina da kai?”. Murmushin rainin wayeo Jay yay masa yana lasar lip ɗinsa na ƙasa, yaɗan ɗage gira cike da salo dukda idanunsa na cikin glass ne, hannayensa duka cikin aljihun wandonsa suke, Yace, “Inada business da kaine shiyyasa”. Wani kallon banza Qaseem yayma Jay shima, yace, “A kasuwa ka ganni?”. Jay ya sake murmusawa tare da ciro hannunsa yaɗan sosa gefen girarsa da ɗan yatsa yana karyar da wuya, “Karkai taurin kai, akwai tagomashi mai yawa da riba”. Qaseem yaja tsaki ya motsa zaibar wajen yana faɗin, “Zanyi maganin tsagerancinka ne yaro kwanan nan”. Cike da rainin hankali Jay yace, “Ai zuru batacin zuru, sai dai a haɗu ai zuru-zuru. Nabaka nanda kwanaki bakwai kacal zaka nemeni da kuɗinka ma”. Qaseem yay wata dariyar kai banzane ya wuce motar lawyer ɗinsa batare da yabama Jay amsaba….
Jawaad yay wani lalataccen murmushi yana zare gilashin idonsa, sai da Qaseem ya shiga motar sannan ya maida glasess ɗinsa yay salute ɗin motar da faɗin, “YANZUN MUKA FARA”. (Bari na ƙarasa maka jikan Yusufa🤣. WASAN😉).
____________________________________
Ƙarfe sha biyu da wasu mintuna na farka, ni kaɗaice a ɗakin, na sauka daga gadon ina addu’a da miƙa, naji daɗin jikina sosai gaskiya, rashin barci ai masifane. Wanka na shigayi, amma abin mamaki sai nai karo da Jini, cikin mamaki nace, “Jini kuma? To duka yaushe ma nai wankan tsarki? Kofa sati biyu banyiba”. Mamaki tamkar zai kasheni nai wanka na fito. Ina shiri ina juya al’amarin cikin raina. Shigowar Amaturrahman ne ya sakani juyawa na kalleta. Tai murmushi da faɗin, “Amarya saifa wani Shining kikeyi miye sirrin ne?”. Murmushin yaƙe na mata kawai bance komaiba, itama tai dariya kaɗan, “Kefa tuni na lura irin Marwah ce, muskilanci ya muku yawa, idanma an zauna hira daku daga eh sai uhm sai a’a kuka ƙware yi, badai haka za’aje anama Yayan namu dunɗun dunkum ba kamar hadarin maraice?”. Bansan sanda na ƙyalƙyale da dariya ba babu shiri, dan harga ALLAH taban dariya musamman yanda tayi da fuska sanda zatai maganar. Ta ɗagamin gira da cewar, “Ko kefa, gashi na sakaki kin dara, ki shirya muje Ummu na jiranki, yau dai tace sai taga ƴarta”. Naji daɗi a raina, sai dai ina ɗanjin tsoro-tsoro, nice yau zan gamu da Sarauniyar gagara badau gaba ɗaya, ni Bilkisu ɗiyar baba makaho da Asiya gurguwa, ALLAH sarki duniya, duk abinda kaga ba’a gani saboda ƙanƙantarsa wataran zai fito kowa ya gansa saboda girmansa, wataran kuma sai tsufa ya sakayashi, a ƙarshe mutuwa ta ɓoyesa. Tsaf na shirya da taimakon Amaturrahman cikin siket da riga na atanfa da sukaimin ɗas a jiki, dukda dai basu kama jikina ba, duk yanda tasi hanani na saka gyale kasawa nai saida na saka sannan muka fito……………..✍
Barkanmu da dawowa, ina fatan kunyi weekend cikin ƙoshin lafiya😉😘😘😍😍😍😍.3
Masu kira akan zasu sayi ƘWAI CIKIN ƘAYA!! bafa shi ake tallaba, muna tallar buks ɗinmune guda goma na zafafa gasunan, duk wanda bai sayaba ya motso ya saya karya bari romon daɗi ya wucesa🤗🤗🚴🏼
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.14
Page 34
……………….Katafaren falone daya amsa sunansa falo, komai yaji iyakar ji fiye da tunanin mai hasashe, ga wani sassanyan ƙamshi mai kashe lakkar jiki da tsaida gudun jini na tashi, lallai wannan baiwa ta isa a kirata sarauniya, ta haɗu tama gaji da haɗuwar, ga kwarjini irin wanda kowa yasan masu mulki dashi. Tana kishingiɗe ne amintacciyar baiwarta na gefenta da alama hira sukeyi, dan fuskokinsu dukansu ɗauke suke da murmushi, sai bayi biyu kawai a falon, ɗaya na tausa mata ƙafafu ɗaya na yanka mata tufa a ƙaramin filet. Sallamarmu ta sakata maido fararen idanunta kanmu, da sauri Amaturrahman ta tareni tana faɗin, “Gaskiya Ummu sai kin biya”. Murmushi Gimbiya Munaya tayi mai ƙayatarwa, cikin nutsatstsiyar muryarta tace, “Amaturrahman kin maidani kakarki a gidannan, nakula kema auren kikeso”. Da sauri Amaturrahman ta matsa gefe tana tura baki gaba da faɗin, “Ni ALLAH banason aure ina tare dake da Abbu da Mommah”. Dariya hadiman sukayi, nima dai murmushi nike, dan saita tunomin da Nabeelah. Gimbiya Munaya dake murmushi ta miƙomin hannunta da yasha adon jan lalle, “Kinga ɗiyata manta da wannan zo naji ɗuminki kinji”. Jikina har rawa yake saboda yanda tamin tamkar mahaifiya, na taka a sannu cikin nutsuwa gareta, durƙusawa nai kaina a ƙasa, ina faɗin, “Barka da rana Ummu”. Ina jiyo fitar sautin murmushinta, ta ɗora yatsunta saman haɓata ta ɗago kaina, “Nagode da wannan girmama ɗiyata, ALLAH yay miki albarka kinji, kiyi haƙuri da rashin ganina tun zuwanki”. Murmushi na mata ina ƙasa-ƙasa da idanu, dan bazan iya kallonta kamar yanda take kallona ba, nace, “Babu komai Ummu”. Murmushi ta sake yi, tare da zaunar dani sosai, ta sallami bayinta guda biyu, daga ni sai Amintacciyar baiwarta da kuma Amaturrahman data koma can cikin kujera tana kumbura wai ance za’a mata aure. itafa ta rantse bazatai aure tabar Ummu da Abbu ba. (Kujimin ƴa, to itama munayar ai sunƙumota Galadima yay daga gabansu hajiya innaro😂).
Cikin nutsuwa da hikima Gimbiya Munaya kejan Bilkisu da hira, abin gwanin sha’awa, babu wani nuna ƙyara ko izzar mulkin kasancewarta ƙasan ƙasa da ita, haka gimbiya Munaya take, bata yarda ƙasƙantar da waniba a rayuwarta, tace tasan ciwon ƙasƙanci, bazataso yima waniba, ita tasan wahalar da zuciyarta tasha lokacin da suke ƙarƙashin mulkin mallakar Innaro a gidansu. (hajiya innaronmu ta mutumci kwanciyarki lafiya cikin ƙasa matar Faruku😂🤗, karkimin fatalwa da daddare kuma yasin😤).
Yanda Sarauniya ta iya hira har bansan sanda nake bata duk amsar data buƙata daga gareni ba, har takai munyi zurfi sosai a hirar fiye dazaton mai hasashe, kiran sallar zuhur ne ya tashemu, muka koma ɗakinmu domin yi, nidai banyi yunƙurin yiba tunda naga jini a jikina dukda dai kaina a ƙulle yake.
Muna cin abinci kira ya shigo wayar Amaturrahman, ɗaukata cike da zumuɗi tana faɗin “Meenal kun tahone?” bansan mi akace mata daga canba naji cike da murna ta sake cewa, “Wlhy da gaske nake tana nan har sai lokacin tarewarta”. Daga inda nake ina jiyo ihunsu, itama ta miƙe tana rawa da ihu. Nikam mamaki suke ban, Amaturrahman irin tsagwaron izza da mulkinan na ƴaƴan sarakuna sam batayi, ko kiga tana wulaƙanta bayi tana takasu yanda takeso, abinda kawai na fahimta tarbiyyace daga iyayensu hakan, An nuna musu bayin gidansu mutanene tamkarsu masu daraja da mutunci, shiyyasa sam basa tozartasu.
Ban tambayeta su wayeba muka cigaba da ƴar hirarmu, dukda nifa dauriya kawai nake hankalina ya rabune kashi-kashi. Ba’afi mintuna talatinba saiga ƴammatan ranar da muka taɓa haɗuwa a Saloon tare da su Amaturrahman ɗin, Meenal da Amatullah, ashe tafiya sukayi shiyyasa ban gansuba tunda nazo. Suka rungumeni cike da murna, ni harma mamaki suka bani, gasu suma da shegen kauɗi, aiko yinin yau dai kaina har ciwo yake saboda surutunsu, amma zamana dasu ya ɗeben kewa sosai, sai nake ganinsu kamar su Ummie. Muna tare Zuhrah ta kira waya, yanda sukaji muna waya da ita tana tsokanata Amatullah ɗiyar Buzaye mai cike da sirrin ƙyau ta fige wayar ta saka a hansfree kowa yanaji, a cewarta suma yanzu ai ƙawayen Zuhrah ne, duk ƙawayena sun zama nasu suma.
Abin mamaki da daddare saina nema jini na rasa, baƙaramin ɗaure kaina al’amarin ya sake yiba, ni a ƴan kwanakinnan sam bama na ganema kaina, daga wannan al’amari ya wuce sai wannan, ALLAH na gode maka da wannan jarabawa, ya rabbi ka bani ikon cinyeta, ka ƙaramin haƙuri da juriya.3
STORY CONTINUES BELOW

(Amin Sakwara🚴🏼)1
____________________________________
“Nifa wannan wasan naku dariya yake bani kaida Qaseem Boss, gashi yanzu Mami ta sake tunzura komai ya ɗau zafi, shi bazai yarda da ƙaddara bane ba?”. Murmushi Jay yayi baice komaiba, sai ƙoƙarin saka waya da yake a kunne. Daga can Abbati yay sallama. Amsawa Jay yay suka gaisa. Yace, “Ina fatan yau zaka tashi aiki da wuri dan inason ganinka, banason kuma a wuce yau saboda muhimmancin zaman”. Daga can Abbati yace, “Babu damuwa, ai kama yanka akan gaɓa, dan inason na shigo namaka ta’aziyya dama, zan shigo bayan magriba da safe sai na wuce”. Jay yace, “Kai malam nifa yanzun ƙattai sun daina kwanarmin a gida inada iyali”. Ba Abbati ba hatta da Jabeer dariya ya kwashe da ita harda ƙyaƙyƙyewa, Jay ya mangarema Jabeer kai tareda ranƙwashi mai zafi, yace, “Kaima ɗan iska na wayar zan kamaka ne, masu zuwa lahira da ido ɗai-ɗai”. Bai jira amsar abbati ba ya yanke wayarsa. Jabeer dake sosa inda Jay ya ranƙwashesa yana tuƙi yace, “Oho dai, ai sa idon namu mai lasisi ne, ni nama taɓa ganin munafukin soyayya irinka?, ALLAH zan cema sarauniya karta bar Mami ta tare har sai kazo da kanka ka furta kana SO da hawaye”. Taɓe baki Jay yayi da kwantar da kansa jikin sit ya lumshe idanunsa, a hankali yace, “Idan namata ciki a waje saiku barta ta tare ɗin, koku bari saita haihu kukaita da ƴar ko ɗan”.
Jabeer dake ƙumshe dariya yace, “Ainasan kai waliyyine bazakai hakanba”.
Shiru Jay yay tamkar bazai tankaba. Sai kuma zuwa can ya zubama Jabeer ɗin harara ya ɗauke kansa.
Kasa daurewa Jabeer yay ya kwashe da dariya yana dukan sitiyari. Jawaad yay guntun tsaki da faɗin, “Kaifa wani lokacin baka da man kai, ka isheni fa”. Jabeer dake dariya yace, “Baka da amsa yanzu, sai mun isa inda zan saida wannan jaridar tukunna”. Banza Jay yay masa bai sake magana ba, saima kansa daya sake kwantarwa jikin kujerar yay luf.1
Gaba ɗaya a wannan yinin Jay yayisa cikin aiyuka, Baibar Office ba sai bayan sallar isha’i, haka ya tashi a gajiye, gida ya wuce kai tsaye dan Abbati harya kirasa ya sanar masa ya iso, ada idan zasu haɗu A.Y street suke haɗuwa, yakan daɗe bai kawo aboki family house ɗinsuba sai idan ta kama dole, to a yanzu wancan gidan a hargitse yake dan amma fidda komai na cikinsa aiki akeyi tuƙuru da sauya fasalin abubuwa.
Tare suka shigo da Abbati dake ɗauke da jikkar Jay ɗin a hannu, basu zauna falon ƙasaba saboda yay datti sosai, suka haye sama, anan yabar Abbati shikuma ya shige bedroom dan yaɗan watsa ruwa. Ya sauke idanunsa akan gadonsa ya lumshesu yana maijin wani iri, jiya iyanzu suna nan tare. Wasu abubuwan data dingayi ya tuna, babu shiri murmushi ya suɓuce masa, aransa mamaki ma yake yanda take matsoraciya ya akai ta shiga aikin nan? Bashi da mai bashi amsa dan haka ya nufi bayi, bai wani jimaba saboda yanaso su tattauna da Abbati ya kwanta da wuri, yay shiri cikin kayan barcinsa farare tas masu taushi wandon har ƙasa. Dama ya sayo musu abinda zasuci a hanya, hakan yasa yana fitowa ƙasa ya sauka ya ɗakko filets ya dawo inda Abbati ke zaune yana kallo. Sake gaisawa sukai, Abbati na juye kajin a filet Jay kuwa na daga can wajen D/table yana haɗoma kansa Shayin da shansa ya zame masa jiki yanzun, takai har idan baima shaba bayajin daɗi.
“Ni ina nawa shayin?” cewar Abbati. Hararsa Jay yayi ya ɗauke kansa ya maida ga tv, “Sai kazauna tunda ni matarkane na kawo maka”. Abbati ya miƙe yana faɗin, “Kazama matata aiban moreba Yasin, ina zani da gabjejen ƙato kamarka”. Murmushi kawai Jay yayi ban sake tankawaba, saima shayinsa da yakesha hankali kwance har Abbati shima ya dawo ɗauke da nasa.
Bayan sun sake gaisawa sukai jimamin rasuwar Gimba sosai sannan Jay ya ɗora da faɗin, “Bana babu Gimba, dama shike tsaye akan rabon kayannan na azumi Abbati, narasa wazan ɗauka yay aikinan, gashi ya kamata ace tun jiyama aka fara rabonsu kamar yanda marigayi yakeyi”. Abbati yace, “ALLAH sarki rayuwa kenan, ALLAH ya gafarta masa, lamarine na mutane sai addu’a, sam bama tsoron ALLAH, wanda ya bada baiji ƙyashiba sai kaga masu rabawa sun zama azzalumai, amma kuma wai da an tashi zagin shugabbani suma sunada bakin jefa nasu”. Jay yace, “Humm, ai Abbati ɗan adam barshi yanda ka ganshi kaji, lokacin daka bashi zuma ya lasa zai sanar maka da daɗi yama gode maka, amma da saɓanin hakan ya gitta kafi kowa muni a idonsa. Manta da wannan maganar muyi wadda ta fita muhimmanci. Yanzu dai kafinma akai ga mahanar fidda kayan, kayan abincinmu da zamu saida sunada yawane?”.
“ALLAH na tuba boss ai suma ɗin dai kamar ƙyautarne, tunda ana saida musu ne bisa farashi mai matuƙar sauƙi, duka stores ɗinmu cike suke da kayan abinci kamar kowacce shekara, idanma munada ƙarancin wani abu to manja ne gaskiya”.
“Karka damu, batun manja nayi magana da Jessica ɗazun, insha ALLAH zuwa jibi zai iso, inason linka kayan da ake rabawarne, to da nayi tunanin sayen waɗanda muke dasu a ƙasa, sai dai ɗazun kuma wani tunani yazo mani, gara mu saya hannun ƴan kasuwa, shikuma namun mu saida musu akan farashin da aka saba ɗin bisa ƙaramar riba”.
“Banƙi ta takaba Jay, amma kaima idan ka sayi namun ai zaka samu sauƙi, dan naga wannan karon abubuwan sun taso da yawa, ga maganar gyaran gida naga ka saka, hidimar aure ta wuce wasa ai”. Ɗan lumshe idanu Jay yay yace, “ALLAH zai rufa asiri Abbati, muyi hakan kawai, inason zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu a kammala siyayyar, dukda guri ya ƙure zuwa jibi sai a fidda kayan, kayanmu kuma da za’a saida yakamata kuma ku fiddasu ai”.
“Eh dama munyi dasu Labaran gobe idan ALLAH ya kaimu za’ai baja koli, shiyyasama nace zanzo na sameka yau ɗin, zan ɗauki hutun sati guda wajen aiki insha ALLAH muga an raba kayan yanda ya kamata mabuƙata sun samu”.
“Nagode sosai Abbati, nayi magana da Alhaji Garba yadi, amma Jabeer ne zai tsaya nan ɓangaren shi da su Aliyu dan aikin yamaku yawa kuma, inason wannan shekarar insha ALLAH muhaɗa da tufafi wa ƙananun yara suma, ni kuma inason hankalina ya tsaya wajen gyaran gidannan ne”.
Cikin jin daɗi Abbati yace, “ALLAH ya saka maka da alkairi ya ƙara buɗi, ALLAH yasa baɗi iwar haka muna nan muna shagalin sunan babys ɗinmu. Murmushi kawai Jay yayi baice komaiba. Sun cigaba da tattaunawa har kusan 12 sannan suka kwanta, Abbati a ɗakin baƙi da Jay ya shiga ya taimaka masa suka gyara, shikuma ya koma ɗakinsa ya kwanta.
STORY CONTINUES BELOW

WASHE GARI.
Washe gari Jay suka koma garin su Gimba, ta’azziya suka sakeyi, shima kuma aka sake masa dukda wasu harda munafunci dan sun dasa ƙananun magana akan Jay ɗan ƙungiyar asirine, shine yakai Gimba ma aka shanye nasa. Kasancewar shi mutumne mai saurin fahimtar abu kafin su baro garin ya karanci abubuwa masu yawa daga mutane, ya kuma saka an bincika masa inda ɓaleru yake ta hanyar iyayensa da basusan dawan garinba. Zuwa Azhar suka baro garin.
Tunda suka dawo daga garin su gimba aiki yake babu hutu, kiran sallar la’asar ne kawai ya tadashi, bayan an idar office ya dawo ya ɗora daga inda ya tsaya. Zamansa baifi da mintuna goma ba Hafiz dake ɗauke da takardu a hannu ya shigo office ɗin da sallama..
Batare da Jay ya ɗagoba ya amsa masa. Hafiz ya zauna a ɗaya daga kujerun gaban tebirin yana faɗin, “Yauwa boss ga file ɗinan na gama tattare komai, abinda ya rage mana kawai yanzun shine bin sawunsa kawai, kaga dai dukkan abinda muke buƙata mun riga mun gama samunshi”.
Jawaad ya ɗago yana ɗan bubbuga pen ɗin hannunsa akan laɓɓa, takardun da Hafiz ya ajiye ya ɗauka, sai da ya gama dubawa sannan ya sake ɗagowa ga Hafiz ɗin, “Kamar ba komai ne anan ba ai Hafiz, Rose ta baka dukkan bayanan dake hannunta ne? akwai kuma bayanan Restaurant ɗinan shima ban gansaba anan?”. Hafiz yace, “Oh sorry, wlhy nama shafa’a sosai, na gidan cin abincin nan kamar suna hannun Mami ne fa, jiya naso amsa, sai kuma na iske batazoba, bara na amsosu, saina haɗo dana hannun Rose ɗin”. Dakatar dashi Jay yayi ta hanyar ɗaga masa hannu. “Rose ta fita ita da Aliyu, Miemaa Kirata ta kawo, nima akwai aikin dana sakata ma ita da Dawood shi ya kawo nasa ita shiru kakeji”. Miƙewa Hafiz yay zuwa gaban landline ɗin office ɗin yana faɗin, “Bara muji to kota kammala duka”. Jay baice komaiba ya cigaba da aikinsa, yayinda Hafiz yay waya department ɗin su Bilkisun. Baifi mintuna goma da ajiye wayarba akai knocking ƙofar.
★★★
Tunda nazo office ban gansaba, ban kuma je inda yakeba, ina namu office ɗin na duƙufa dukkan ayyukan dake gabana, sai hirarmu da bata ƙarewa ni da Ummie.
Kasancewar jinin dana gani jiya tun a daren na nemesa na rasa yasa dukkan sallolina yau nayisu batare dana sake ganinsa ba kuma. Mun fito sallar la’asar kowa ya koma kan aikinsa. Nayi nisa sosai akan aikin da nakeyi saƙon kira daga office ɗin Boss ya sameni. Dukda nasan dalilin kiran sai da gabana ya faɗi, dama tun ɗazun Dawood ya sanarmin ya kai masa aikin daya sakamu tare saura ni yake jira. Miƙewa nai na tattare files ɗin guda biyu na fita.
Da sallama na shiga office ɗin bayan nayi knocking an bani izinin shiga, naɗanji sanyi ganin akwai Oga Hafiz a office ɗin, shinema ya amsan sallamata, dodon nawa kam bai ko ɗagoba, gaba ɗaya hankalinsa nakan Computer, inama shigowa ƙarar danna keyboard ɗinsa ce ta fara tarata, yanda yake dannawar da sauri-sauri yasa akejin ƙararsu sosai. Da fara’a oga Hafiz ya tarbeni, na gaishesa ina miƙa masa file ɗaya a cikin biyun dana shigo dashi tunda nasan dama shine wanda zan baiwa. Ɗayan kuma na matsa tebirin boss na ajiye, murya a sanyaya nace, “Barka da yamma”. Batare daya ɗagoba yace, “Barka” ya cigaba da aikinsa. Duk da yanda yaymin ɗin haka na sake dannewa nace, “Gashi na kammala, sai dai result ɗin sayin hannun nasa ɗin bai fitaba”. Dakatawa yay daga abinda yakeyi ya ɗago min manyan idanunsa da a yau suke farare tas, sai dai sunɗan kumburo alamar cike suke da gajiya, sauri janye nawa nai lokacin da sautin muryarsa ta fara isowa cikin kunnena. “Wakika kaimawa?”. Yay maganar har yanzu idanunsa a kaina dan inajin yanda suke shiga ɓargona. Cikin nutsuwa ta nace, “Sir danaje office ɗin Umar bayanan saina gamu da Hashim”. Cikin kaushin murya yace, “Hashim! Kina nufin shi kika bamawa!?”. Yanda yay maganar ya sani ɗagowa na dubesa da sauri. Dan masifa har fararen idanun nan dana gani yanzu sun sirka da ɗan ja, na kula da yashiga ɓacinrai zakaga idanunsa sun sauya kala. A ɗarare na ɗaga masa kai kawai. Uffan bai sake cewaba ya ɗauki wayar landline yay kira.
Hafiz da duk yana zaune yana kallonsu ya kalli Bilkisu, “Mami garin yaya kika bama Hashim bayan bashi akace ki bamawa ba?”. Kaina a ƙasa nace, “Wlhy ni bansan akwai matsalaba ne, na fito shikuma zai shiga office ɗin shine yake tambayata ko lafiya? Nikuma nace masa wajen Umar nazo, shine yace bara ya ajiye masa anjima saina dawo na amsa, to kafin na koma ɗinne kuma mukai fitar ranar, jiya kuma banzo office ba, ɗazun nakoma amsowa danna tattare komai shine Umar ɗin ya sanarmin bai bashiba, amma ya fita idan ya dawo zai tambayesa koya mantane”
Hafiz ya ɗan girgiza kansa da faɗin, “Ki ringa kula kinji, duk wanda ba’ace kibama abububa kidaina bashi, wannan aikin namu da kike gani kowa takansa yakeyi, shiyyasa zakiga a komai ana taka tsantsan, bara ni naje wajen Hashim ɗin da kaina Boss”.
Jawaad ya dangwarar da kan wayar a ƙasa saboda yakasa samun Umar ɗinma, bai cema Hafiz komaiba harya fice.
Kansa ya dafe cike da takaici, ya miƙe tare da tura kujerarsa baya da ɗan ƙarfi ni harma na tsorata, yay taku ɗaya biyu kafin ya juyo yana kallona, yanda ya matso daf dani yasani maida kaina ƙasa, yaɗan buga tebirin da faɗin, “Wai sai yaushene zaki daina bani ciwon kai ne yarinyarnan? Wataran saina sauya miki kamannin fuskarnan taki maikama data mage idan baki dawo hankalinki ba” yay maganar da yunƙurowa kamar zai makeni. Baya nai da sauri, cikin zafin nama na tura kujerar na miƙe tsaye, dan yanda ya fusato ɗinan nasan iya makeni zaiyi ɗin.
Jay da takaici yake neman shaƙema numfashi yace, “Zonan, idan kuma kika bari ni nazo saina karya ƙasusuwanki”. Idanuna cike da ƙwalla na kallesa ina tura baki, kafin na samu damar bashi haƙuri yace.
“Ni kike murguɗama baki?!”.
Saurin ɗagowa nai ina ƙwalalo idanu waje, kujimin sabon sharri, ni yaushe na murguɗa baki dan ALLAH jama’a?. ganinfa da gaske ni yake nufowa fuska a ɗaure sai na fara ja baya, bai fasa biyoni ba kamar yanda ban fasa tafiya da bayaba ina yarfe hannu, jinai tamkar na saki fitsari, yayi bala’in ɗaure fuska yanda na tabbatar yau idan ya kamani sai ya karyanin da yake faɗa. cikin sarƙewar harshe nace, “Ni wlhy ban murguɗa maka baki ba fa Sir, kuma ALLAH bani da lafiya ma”. Nai maganar dai-dai na dangane da bango, shikuma ya iso daf dani.
Ina rufe baki ana turo ƙofar, ido huɗu mukai da Rose, kafin bakina ya iya sake furta wani abu naji an fisgoni na faɗo saman ƙirjin mutum………….✍
22
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
15
Page 35
……………..Rintse idanuna nai da azabar ƙarfi, a duk lokacin da jikinsa ya taɓa nawa nakanji tamkar na taɓa wuta, daga randa mukaje ɗakko gawar Gimba kuma sai na rage jin hakan, sai dai sam banason yace zai taɓani, amma a mamakina yau sai naji tamkar an azani bisa wutar. A take jikina ya fara karkarwa saboda azabar da nakeji, cikin gangarowar hawaye bisa idanuna nace, “Boss dan ALLAH ka matsa, wlhy jikinka tamkar wuta nake jinsa”.
Yanda ta ƙare maganar da fashewa da kuka tana neman silalewa ƙasa yasaka Jay ja baya cikin ɓacin rai, dan shi kalamanta zafi sukai masa a zuciya, cikin kaushin murya yace, “Qaseem ne kawai idan ya taɓaki baƙyajin zafi tunda shi kikeso?”. Idanuna na shiga lumshewa ga zufa sai karyomin take a jiki saboda azabar da nakeji, na shiga girgiza masa kawai, “Kaimin addu’a, fatar jikina jinake tamkar ana ɗayemin itane”. Yanzu kam da mamaki yake kallonta, dan yanda jikinta ke wani irin karkarwa da zufar da takeyi ta cancanci a fahimceta, kalaman baba ƙaurane suka faɗo masa cikin rai, addu’ar ya shiga karantowa yana tofa mata, idanunsa harsun ƙaɗa sunyi jazur saboda yanda yakeji a cikin ransa, gaba ɗaya yakan rasa wane tunani zaiyi akan lamarinnan, idan ya zurfafa tunaninma sai kiji kansa ya fara matsanancin ciwo, dole yake ajiye batun ya shiga wata sabgar badan kuma al’amarin baya cikin ransa baneba. Ahankali Bilkisu ta shiga sauke numfashi, zufar na tsafewa sanyin ac na ratsata, kusan mintuna goma suna a haka.+
Rose da tunɗazun tai sumar tsaye tai Luuuu zata faɗi saboda wata hajijiya data rufe ganinta. Da sauri Hafiz da isowarsa kenan dasu Jabeer ya tarota. tai ƙoƙarin ƙwacewa jikinta na rawa zata sake danna kai cikin office ɗin idanunta na zubar hawaye Hafiz yay saurin sake fusgota, cikin tsawa-tsawa yace, “Rose! Minene kikeyi hakane?”. Wasu irin zafafan hawayene suka shiga rige-rigen sake gangaro mata saman kumatu, ta tsare Hafiz da kallo, hannu na rawa ta nuna ƙofar office ɗin Jay, “Boss fa rungume da yarinyar nan”. Cikin takaici Hafiz yace, “Idan ya rungumeta sai akai me? Ba matarsa bace! matarsa ce ita halalinsa, ke kanki shedace akansa, inda Jay yana harkar mata ke zai fara lalatawa ai” ya ƙare maganar da balla mata harara yaja tsaki ya juya yabar wajen.
Da sauri Rose ta maida kallonta ga Jabeer da Aliyu. Tace, “Kunajinfa miyace, miyasa Hafiz baya ƙaunata?”. Ɗan murmushi Jabeer yay yana girgiza kansa, “Hafiz ba ƙaunarkine bayayi ba, gaskiya ya faɗa miki, Mami matar Jay ce yanzun”. Daɓar Rose ta zauna ƙasa tana faɗin, “Jesus, shikenan na mutu Jabeer, yaushe akai musu auren?”. Duƙawa Aliyu yay gabanta cikin taushin murya yace, “Baki mutuba Rose, kisama ranki haƙuri dan ALLAH karki tada hankalinki kinji, ALLAH ya rubuta itace matarsa, kema naki mijin nanan zuw…….” “Aliy daina faɗamin maganar banza kaji, ni boss zai yaudara, dama tunda naga yarinyarnan na shige masa nasan zatai abinda yafi haka, nasan asiri tai masa kawai”. Ƴar Dariya Jabeer yay shima ya duƙa gabansu, “Rose na faɗa miki gaskiyar magana? Boss shike bin Mami ba ita ke binsa ba, tunda muke da ita bata taɓa nuna wanima a cikinmu ya taɓa koda birgetaba, shi kansa farautar soyayyarta yake amma sam taƙi bada ƙofar hakan, kullum ma nunawa take ita batama taɓa fahimtarsa ba, itaɗin mace ce mai AJI!, shine babban maganin asirinta akan zuciyar Boss, yakamata ki fahimci yana son mace mai suna mace, ma’ana mai Ajiiii!!”. ya ƙare maganar cike da salon iskanci yana salute ɗinta, miƙewa yay tare da mata nuni ta miƙe dan tayi sagafene tana kallonsa da fassara maganganunsa sala-sala.6
Sam Jay baiga Rose ba, Bily kanta data ganta halin data shiga yasa tama manta da ganin nata, ruwa ya ɗakko ya bata, babu musu ta amsa, yanda tasha ruwan sosai har mamaki ta bashi, ta miƙa masa kofin tana godiya, baice mata komaiba sai nuni da yay mata data tashi takoma kan kujera.
Nima ina buƙatar hutawar, dan haka na tashi na koma saman kujerar na zauna tare da lumshe idanuna.
Sosai nakeji a jikina kallona ake, ina buɗe idanu muka haɗa ido dashi, ɗauke kansa yay tamkar baniɗin yake kallonba, nima na janye nawa a raina ina jinjina yanda ya ƙware a iya kallon mutum.
Babu wanda ya sake shigowa office ɗin har aka kira sallar la’asar, shine ya fara shiga ya ɗaura alwala sannan yace naje nayi nima, lokacin dana fito tsaye na gansa, bance komaiba na nufi hanyar fita yana biye dani.
STORY CONTINUES BELOW

Daƙyar Aliyu ya lallaɓa rose suka bar ƙofar office ɗin Jay, kuka take rurus cin ƙarfinta, a zuciyarta tana ayyana matakin gaggawa da zata ɗauka akan Bilkisu nan bada jimawa ba, bazai yuwu tazo jiya-jiya ta samu abinda ita ta kashe shekaru masu yawa tana bibiyaba, dolene kodai ita ta samu, kokima su rasa gaba ɗaya. Da wannan ƙudirin tabar office yau.
Yau tare dashi mukabar office, a ƙasan raina cike nake da tuhumar ina Yah Qaseem ya shiga? Sam bana ganinsa a office tunda na dawo, mike faruwa dashi ne? Inason tambayar boss inajin tsoron buyaginsa. Munyi nisa a tafiya batare daya kalleniba yace, “Jazuga bai mutuba”. Da wani irin matsanancin sauri na juyo na kallesa, harma na manta dawa nake na kafesa da idanu ko ƙyaftawa banayi”. “Malama idanun nan sunmin yawafa”. Kumbura fuska nai na ɗauke kaina jin abinda yace, sai kuma na kasa haƙuri naɗan sake kallonsa na risinar da kaina, cikin zumuɗi nace, “Dan ALLAH da gaske boss?”. yace, “Mun fara ƴar wasane dake?” kaina na girgiza masa dukda nasan bani yake kalloba. Shiru bai sake cewa komaiba, har muka isa masarauta, dukda inason jin ƙarin bayani haka na daure na danne a raina, idan taƙamarsa jan aji gidan ya taras.
A cikin ran Jay wani irin haushine ke cinsa, mamaki da takaicin miskilancinta yake, yayi shirune yaji kozata tambayesa cigaba labarin amma yanda yay shiru itama ta tsuke baki, shikuma inhar ba ita tanema jin yanda akaiba bazai faɗa mataba. Babu wanda ya sake yin magana tsakanina da shi har yasamu guri yay fakin gab da sashen gimbiya, dan yanzu shi babu shamaki an bashi damar shigowa cikin masarauta a duk sanda yaso. Yunƙurin buɗe motar nai ya riƙo hannuna. Daƙyar na iya danne abinda nakeji na kallesa, ganin ni yake kallo sai nai ƙasa da kaina, sakarmin hannu yay yana faɗin, “Saiki jira na gama tunda ba tauneki zanyi ba”. Nidai bance komaiba, ya miƙa hannu sit ɗin baya ya ɗakko leda viva sabuwa. “ga wannan, duk yanda zakiyi amfani dasu na rubuta miki, Karkiyi wasa Miemaa, dan ina buƙatar matata a kusa dani” yay maganar ahankali yana kafeni da idanu, saurin sadda kaina nai dan naji wata irin bahaguwar kunya ne. Jay dake kallonta yay wani lallausan murmushi da cigaba da faɗin, “dolene ta hanyarki zan gano bakin zaren matsalarmu, hakan kuma bazai yuwuba kai tsaye sai da taimakon UBANGIJI”. Kaina a ƙasa nace, “Insha ALLAHU zanyi Sir”. “ALLAH ya tabbatar”. Ya faɗa batare da ya da ɗauke kansa daga gareni.
Nima saina fita a motar ɗauke da ledar da bag ɗina, ta sashensa na zagaya na sake masa godiya sannan na shige, tuni an amshi kayan hannuna tun fitowata a motar.
Jay daya kafeta da kallo ta cikin mota yaɗan lumshe idanunsa yana sauke ajiyar zuciya lokacin data shige. Shima fitowar yayi. Masallacin masarauta yay salla har isha’i, kafin ya samu damar ganawa da gimbiya a tsaitsaye. Yamata bayanin abubuwa da dama a gurguje, itama ta sanar masa ƴar firar da sukai da Bily da abinda ta fahimta. Duk yanda taso yaci abinci ƙinci yay yauma yaymata sallama ya wuce.
__________________________
Tun daga wannan ranar gimbiya ta sake jan Bilkisu jikinta, riritata take tamkar uwa da ƴa, gefe ɗaya tana koya mata dabarun rayuwar aure cikin hikima kamar yanda itama Mommah tai mata gata, sannan a hankali take fahitar wasu abubuwa daga Bilkisu ta cikin hira. Magungunan da Jay ya kawo mata Amintacciyar baiwar gambiya tsaye take akan Bilkisu dan ganin tayisu kamar yanda ake buƙata, ga maganin sanyi shima da ake bata acewar gimbiya shine matakin farko.
Kullum da safe driver zai kaita office da yamma idan an tashi Jawaad ya ɗakkota ya maidota, dukda babu wata hirar arziƙi a ciki, yakuma daina raɓarta koda wasa, yanzu sam basama haɗuwa sosai a station ɗin saboda baya zama aiki yaymasa yawa, su kansu yana wajigasu da ayyukan sosai.
A haka aka shiga wata mai albarka na ramadhana, manya da ƙananun yara harma da tsaffi kowa ya tashi da wannan ibada a baki cike da ɗoki da fatan kammalawa lafiya. Yayinda Bilkisu ke kallon ikon ALLAH wajensu gambiya dangane da alkairin da ake fita dashi domin talakawa. Abin sai ya birgeta, a cikin ranta tana fatan kwatantawa taji idan zata iya watanara, sannan har yau da take nufar sati na biyu a masarautar bata taɓa gamo da Sarki Sameer ba, Safah ta sanar mata yaje saudia hutawa shida amaryarsa da suke kira Ammi, sai azumi yaje tsakkiya zai dawo sukuma su tafi Umarah
STORY CONTINUES BELOW

★★★★
Jay da muƙarrabansa sunyi busy matuƙa, ga aiki ga aikin sa kai gana hidimar bayin ALLAH duk ya haɗama kansa, burinsa ya kammala abubuwa da yawa cikin watannan, baya neman Bilkisu ne dan yana tausayinta sosai, ga azumi ga rana dan ruwa bai zaunaba sosai, gani yay ta rame masa a kwanakinan sosai sai tai haske kuma.
Abin mamaki Rose kuma saita shiga ja baya dasu, har takai saida Jay yamata magana da kasa, ranar kam dai yaga taɓara da iyayi, gashi yanaji da azuminsa. Shidai ya lalaɓata kawai dan yana buƙatar nutsuwa baison hayaniya.
Tuni yasa ana bibiyar masa bayan Ɓaleru duk inda ya sanya ƙafa batare da shi ya saniba, bayason kamasa a cikin watannan mai albarka shiyyasa yay tamkar ya manta da al’amarinsa, ga jikin ɗan-fir’auna da har gidan su Shahudah suka ɗauka ya mutu na nata sauƙi da warwarewa.
__________________________
Kwanci tashi babu wahala wajen UBANGIJI azumi yakai tsakkiya, a daren sha bakwai sarki Sameer da Amaryarsa suka dawo, anyi murna da dawowar tasu sosai, dan ranar kam kowa ya shaida hakan a masarautar gagara badau, ranar gimbiya da kanta taima Takawa abincin buɗa baki a kicin ɗinta na sirri da babu mai shiga sai ita saiko Amintacciyar baiwarta. Tunda ta tafi ɓangarensa su bily basu sake jin ɗuriyartaba sai washe gari, sai a randa za’a ɗau azumi na sha takwas ne suka ganta, shima dan tasaka a kira mata bily ne.
Cikin girmamawa na gaisheta kamar yanda na saba, fuskarta ɗauke da murmushi ta amsa min tare da kamo hannayena cikin nata. “Ɗiyata dama nasa a kiramin kene saboda zaku wuce Umrah gobe idan ALLAH ya kaimu ke da su Amaturrahman, an kammala miki komai insha ALLAH” Dama Boss ya sanarmin tun shekaranjiya, sai dai na nuna mata farin cikina sosai akan hakan itama tamkar bansan da tafiyarba, nakuma mata godiya. Ta cigaba da faɗin, “Naso ace tun farkon azumi kika tafi, sai dai mijinki ya sanarmin hakan bazai yuwuba saboda aikinki, dan akwai wata auntyna matar yayan abokin Takawa tanada makaranta ta musamman domin koyar da amare, ana gyaran jiki da komai a ciki, koya girki da dukkan dabarun zaman aure, itama ƴar nan ƙasarmu ce, dalilin ƙaddara ta shigo rayuwarmu, mun kaita domin neman magani sai yayan abokin Takawa yace shifa yayi mata, wannan shine dalilin zamanta a can itama”. Fuskata ɗauke da murmushi nace, “ALLAH sarki”. Itama murmushi tayi, “Yanzu dai yayi dukkan cuku-cukun daya dace a wajen aikinku insha ALLAH keda nan sai saura kwana biyar tarewarki, inason naga kin zama cikakkiyar mace mai amsa suna mace a fadar mijinta, mijinki babban mutumne sannan yanada wasu sirrika dake kaɗai zaki fahimci kayanki anan gaba, shiyyasa nakeso a gyaramin ke yanda ya kamata domin zukatan maƙiya su girgiza, waɗanda suke ganin baki kaiba su fahimci kin musu zarrah ta har abada kinji”. Hawayen dake ziraromin na share, bansan irin godiyar da zanma wannan baiwaba a rayuwata, itaɗin ta musamman ce a cikin jerin abubuwa masu muhimmanci da suka shigo rayuwata, ALLAH ya biyata da aljannarsa.13
Washe garima naje wajen aiki, sai dai yau bashi ya maidoni ba sawa yay sabon direbansa ya maidoni, gobe idan ALLAH ya kaimu kuma bazanje aikiba, dan ƙarfe huɗu zamu wuce, share hawayen dake zubomin nake akan abinda ya faru tsakanina dashi yanzu a office ɗinsa. Na roƙesane akan zanje gidan Dad nai masa sallama, dama tun farkon azuminan naketa masa magiyar ya kaini na gaishesa, bai taɓa kulaniba sai yau da yanema marina a office, yajamin dogon gargaɗi akan inhar na sake masa maganar Dad ALLAH sai ya fasan baki. Sake share hawayen nai zuciyata namin zafi da takaucinsa, ni bansan mi Dad yaymasaba haka da zafi shi da ahalinsa, inason ganin koda mutum ɗayane a cikinsu amma abin ya gagara, sam yanzu bana ganin Yah Qaseem, narasa ina ya shiga baya zuwa Office, mike damunsa? Minene matsalarsa? Haka kawai bazai bar zuwa office ba ai?. Zafin boss yayi yawa, nikuma har zuwa yanzun ban taɓa jin sonsa a rainaba, nasan dai zan iya haƙurin zaman aure dashi amma badan inajinsa a raina da kalmar soyayya ba, bansan miyasa hakanba, har zuwa yanzu Yah Qaseem ne kaɗai a zuciyata, shi nakeso, shi na fara so, sai dai shikuma banajin sha’awar zama dashi matsayin miji, bansan miyasa hakanba shima. Ya ALLAH ka kawomin ɗauki bisa ruɗaɗɗen tunanina daya banbanta dana sauran mutane a yanzu.
STORY CONTINUES BELOW

Har muka bar ƙasar bana cikin walwala sam, sai wata irin matsananciyar damuwa da na tsinci zuciyata a ciki, wannan dalilin yasa har jirginma ya tashi ban tuna shine hawana na farkoba, Safah na lafe a jikina tana barci har muka sauka. mun sami tarba ta musamman daga wasu manyan mutane da bansan matsayinsu ba, sai dai ina tunanin waɗanda Gimbiya taban taƙaitaccen labarinsu ne ranar, sai dai wannan nafi ƙyautata zaton abokin takawane da iyalansa ba waccan mai makarantar bace da naji nafi ɗokin gani. Ƴan uwa abu mafi ɗaure kaina shine, maimakon najini cikin farin ciki da zuwa ƙasa mai tsarki a karo na farko a rayuwata sai saɓanin hakan ya biyo baya, kallonsu nike kawai tamkar wata sakarai, ƙirjina na wani irin zafi, sai can ƙasan zuciyata kuma nakejin wani irin sanyi dake kawomin sassauci a cikin ƙirjina kaɗan-kaɗan. Darene sosai, dan haka makwanci kawai aka bamu da abinci, nikam bammaciba na kwanta.
______________________________
Yau tunda ya tashi aiki wanka kawai yaje yay a gida ya kimtsa, sabon drivernsa mai suna Sadiq ya ɗaukesa sai gidan Alhaji Babba dan acan yake buɗa baki yanzun kullum, wataran kuma gidan Ummah babba, kokuma gidan Ummah ƙarama idan ta ishesa da ƙorafi. Haka kawai yau yakejin tamkar wani abu dake nesa dashi yana tunkarosa, minene? A ina yake? Itace amsar dakanzo masa akai-akai cikin shauƙinsa.
Shi dai Alhaji babba kallonsa kawai yake amma baice komaiba, sai da suka dawo salla sukai zaman buɗa baki sannan, ya kai dubansa ga Jay da keta juya cokali cikin kofin kuni yana ɗan murmushi. “Wai nikam gwauron nan yau miya saka farin ciki haka?”. Kallonsa Jay yay fuskarsa ɗauke da murmushin har yanzun, yace, “Babu komai Baba, kawai dai”. Murmushi shima Alhaji baban yayi, “Kawai dai haka ka tsinci kanka kaima ko?”. Kai Jay ya jinjina masa yana lumshe ido. Alhaji babba yace, “Nima haka na tashi da farin ciki, sai nakeji tamkar wani abu dana daɗe da rasawa zai dawo gareni, sai nakeji kamar wani abuna mai muhimmanci ya haɗu da abuna mai muhimmanci, sai nakeji kamar wani abun da na daɗe ina neman amsarsane lokacin sanin amsar yayi, a daren jiya nayi mafarkin ƴaƴana guda biyu cikin farin ciki, tabbas Jawaad inaji a raina wani abu mai daraja da haske na matsowa zuwa garemu”. Jawaad sauraren Alhaji babba kawai yake yana murmushi irin wanda ya kasance mai tsada a garesa, ya ɗora kansa a kafaɗar kakansa yana sake ƙawata murmushinsa, “Ya ALLAH ya tabbatar da wannan hasashe naka ya zama alkairi kakana”. Shafa kansa Alhaji babba yay yana murmushi da faɗin, “Amin ya rabbi jikallena, amma yakama ka dawo nan kwanaki goman nan na ƙarshe muyisu tare cikin ƙololuwar ibada, ka ajiye duk wani aiki gefe”. Jay ya tashi zaune sosai yana kallon kakan nasa, yace, “Nima nayi wannan tunanin, sai dai banason takura maka da yawa”. Ranƙwashi Alhaji babba ya kai masa bisa kai, Jay yay saurin kaucewa yana dariya da haɗe hannayensa waje guda alamar na tuba.1
Bayan sun dawo daga salla suka iske Ummah babba da ƙarama sunzo, dama sunce yau zasuzo. Jay ya zauna tsakkiyarsu yana dariya da faɗin, “Saini ɗan gatan ALLAH, Ummahs ɗina duka tare dani”. Atare sukai dariya da riƙe hannayensa, Ummah babba tace, “Ja’iri kamar ya wani damu damu?”. Karyar da kai Jay yayi ya ɗora saman kafaɗarta, murya a sanyaye yace, “Idan ban damu da kuba dawa zan damu Ummah?, kuɗin duniyatace, sannan haskena, aikine kawai ke hanani rawar gaban hantsi”. Guntuwar dariya tayi da shafa kansa, ta sumbaci hannunsa tana mai saka masa albarka.
Kasancewar basu da ishashen lokaci suka fara tattaunawa akan maganar lefe da dama shine ya kawosu. Da farko Jawaad yace su barsa zaiyi, amma sukace sam bazai yuwuba, na farkoma dan an nuna musu fin ƙarfine Uncles ɗinsa sukace zasuyi, to wannan kam suma sune zasuyi insha ALLAH.
Jawaad yay shiru yana murmushi dajin ƙaunarsu mai narkar da zuciya na ratsasa, zamansa ya gyara a kujerar daya koma shi kaɗai yana kallonsu, “Nagode sosai iyayena, kun sharemin hawayen maraici tuni, bani da abin biyanku sai dai naita muku addu’oin gamawa da rauwa lafiya, idan na ganku saina manta bani da Uwa, idan kuka kalleni sai nake ganin Mah-mah har yanzu tana tare dani, ida har tabar duniya ina roƙon UBANGIJI yasa ana nuna mata dukkan alkairanku ga gudan jininta, idan tana duniya ina fatan ganinta na bata labarin alkairanku ga gudan jininta, ku……” “Ya isa haka kaji Muhammadu, insha ALLAH inaji a jikina BILKEESU tana raye, insha ALLAH kafin nabar duniya saina ganta” Alhaji babba yay maganar yana share hawayen da suka ɗan zubo masa. Ummah da Ummah ƙarama ma kuka suke, Jay gwanin dakiya babu hawayen zahiri saina zuci kawai.
STORY CONTINUES BELOW

________________________________
Kasancewar nazo babu tsarki sai yau nake fatan samu lokacin da zamuyi sahur saina duba, naji wani nishaɗi ganin ya ɗauke harda tsallena a bayi, wanka nayo da brush na fito, cikin tsokana Meenal tace, “Gandiya halan yau kin musulunta ne? Naga wanka da asubar fari”. Murmushi nai mata ina zama domin busar da kaina da hand drayer ɗin dana gani saman mirror ɗakin, nace, “Oh da kafira kike kallona?”. Dariya sukayi ita da Amaturrahman dake ƙoƙarin shiga yin brush itama, tace, “Ai kima godema ALLAH ke kina zuwa yana ɗaukewa, ita tana shigowa yana zuwa”. Cikin ɗan zaro idanu na kalli Meenal ɗin, sai kuma na langaɓe kai nace, “Kai harfa kin bani tausayi babie”. Filo ta ɗauka ta jehomin ɗaya ta jefama Amaturrahman. Da gudu Amaturrahman ta shige bayi tana dariya, nikuma na cafe wanda ta tillomin. “ALLAH karkiji wasa meenal tausayi kika bani” nai maganar da ɗan mata gwalo. Ƙwafa tayi da faɗin, “Wlhy duk zan rama, ke saurama ƙiris na raman ai, zaki gane kurankine”. Murmushi nai mata bance komaiba na cigaba da busar da kaina.
Bayan munyi sahur salla mukai muka sake kwanciya barci, mune bamu tashiba sai sha ɗaya, shima tadamu akazo akayi. shiri mukai a gaggauce na tafiya massallaci, nidai Kasa daurewa nai na tambayi Amaturrahman Auntyn da Ummu tace tanada makaranta gidansu kuma na kusa da inda zamu sauka?.
“Lah Bily ai yanzu bazakiga Umm-Anum ba, sun shiga ittifaqi, kinga gidansu nan, duk Ramdhan idan mukazo bama ganinsu muma sai ranar sallah”. Da mamaki nace, “Basu da yara?”. Tace, “Sunada yara biyu mana, mace da namiji, namijin ya girmemu da kusan shekara biyar, sunansa Anwar, sai macen Anum, tare suke shiga ittifaqi. Tunkan na gansu naji sun matuƙar burgeni har ina zumuɗin ganin nasu mai ban mamaki, dan tunda Ummu taban labarin matar a taƙaice saita kasa barin zuciyata. Yanda na iso da ƙuncin zuciya a yanzu sai ba hakaba, fes nakejin raina cike da nishaɗi da farin ciki da shauƙin ganina a ƙasa mai tsarki, santin da banyi a daren jiyaba sai gashi a yau inayinsa, dan har muka isa massallaci bakina bai hutaba, Safah kam bata gajiya damin bayanin komai dalla-dalla. Lokacin dana ganni gaban ɗakin ka’aba sai kawai nakejina tamkar wata sabuwar Bilkisu ce tsaye ba wadda tazo da ƙunci ba, hawaye masu ɗumi na ziraromin bisa kumatu, abinda ban taɓa tunaniba koda a mafarki, wani nauyin zuciya da ƙunci da damuwar da natsinci kaina a gaba ɗaya cikin shekarunan sai naji tamkar an yayesu an zubar tare da ruwan wankan dana samu tsarki ɗazun da asuba. UBANGIJI mai rahama, UBANGIJI mai ni’ima.
Muna zaune a wajen mutanen kirki, larabawan usul masu ƙyawawan zuciyoyi, bamu rasa komaiba, ibada muke babu wasa dansu Amaturrahman sun horu sosai, sannan sunada ilimin addini suna kuma aiki dashi, Umm-Aban koda yaushe cikin kulawa take damu sosai, nasamu sauyi iri-iri da haske a rayuwata a cikin kwanakinan goma da mukai na Umrah, babu abinda mukeyi banda ibada, duk wata shiririta mun ajiyeta gefe, a kullum safiya bayan sahur muna waya da gimbiya, hakama su Ummie duk saina kirasu, Boss kam ko filashin bai taɓa haɗamu ba, sannan dukkan numbers ɗin ƴan gidanmu bana ganinsu a wayata yanzun, bansan yaya akai hakan ta kasanceba tunda nidai ban gogeba.
Yau take salla, sosai massalacin ke cike, bayan an idar da sallah sai na dingajin juwa, duk yanda naso dannewa hakan ya gagara, bandai sanarma su Amaturrahman ba dan karsu tada hankalinsu, miƙewa nai da nufin na ɗan samu waje inda babu yawan mutane na huta ko zanji nutsuwa sai kawai hajijiya ta kwasheni. Sama-sama na jiyo wata nutsatstsiyar muryar ta ambaci “Yah ALLAH”. Sai jina nai a jikinta. Cikin ɗan larabcin da nakeji kaɗan-kaɗan na tsinci tanama wani wanda bansan ko waneneba magana akan ya bata ruwan zam-zam dake hannunsa. Gabana yay wata masifar faɗuwa jin muryar data amsa mata, murya irin wadda wajan mutum ɗaya na santa, muryar dake sakani bugun zuciya, muryar dake saka jinina gudu cikin jijiyoyi, da ƙyar nai ƙoƙarin ɗaga idanuna dake neman rufewa na sauke a kansa dai-dai ya miƙo ƙaramar goran ruwa wa matar da har yanzu nike a jikinta………….✍
39
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
14Page 36
……………..Tabbas muryar iri ɗayace, kamanin ma ɗayane, sai dai wannan farine tas, shekarunsa kuma basu kai nasa ba, sannan muryarsa bata kai tasa kauriba, na sake lunshe idanu a hankali na sake buɗewa da tunanin kodai mafarki nake?, saukar goran ruwa a saman bakina ya sakani fahimtar komai yana faruwane a zahiri ba’a gaibun mafarki ba. Ruwan nasha sosai kozan samu sauƙin nauyin da ƙirjina yayi, matashiyar budurwar da bazamu wuce sa’anniba fara tas itama balarabiyar usul ta duƙa gabana tare da kamo hannuna cikin nata, ta narke fuska sosai tamkar zatai kuka, magana take cikin harshen larabcina da ban fahimta saboda tanada ɗan saurin baki, na kafeta da kallo, itakuma idanuntane kawai irin na Boss, amma kamaninta daban. Juyawa nai a hankali domin son ganin fuskar wadda nake a jikinata, sai akai sa’a itama niɗin take kallo. Wani irin faɗuwar gaba naji. Na lumshe idanu na sake buɗewa a kanta, kallona take babu ko ƙyaftawa itama tamkar mai ƙoƙarin gano wani abu akan fuskata.
A tare muka sauke ajiyar zuciya ni da ita, kafin nai yunƙurin tashi zaune tsigar jikina na wani irin tashi. Na sake kallon saurayin da sam hankalinsa baya kanmu yanata latsa waya abinsa, gabana ya sake faɗuwa dan kuwa yanda yake tsaye iri ɗayane da yanda Boss ke tsayuwarsa, sosai ruɗani ya sake bayyana a gareni, na kuma juyowa ga matar dattijuwa sosai mai tarin kamala, doguwar rigar jikinta mai adon fari tai masifar yima fatarta ƙyau, murmushi ta sakarmin, cikin harshen turanci tace, “Sannu, kiringa kula kinji?”. Nima murmushin nai mata na gyaɗa mata kaina. Miƙewa tai tsaye ta miƙomin lallausan hannunta da alamun girma ya bayyana a fatar, babu musu na miƙa mata nawa ta taimakamin na miƙe, budurwar ta miƙomin ƴar ƙaramar bag ɗina itama tana murmushin da sakemin sannu. Godiya nai musu, na juya zanbar wajan, taku biyu na juyo na sake kallonsu, sai naga suma duk niɗin suke kallo harda saurayin yanzuma, murmushi mukaima juna na sake juyawa na ciga da tafiya.
Naɗan ƙara juyawa na kallesu sai naga still suma dai idonsu na kaina har yanzun……..
Riƙo hannuna da akai ya sakani saurin juyawa, lip ɗina daya bushe na ɗan lasa zuciyata na wata irin tsitstsinkewa.
Amaturrahman ta girgiza hanun Bilkisu data kula sam bata cikin hayyacinta, “Bily lafiya kuwa? Ina kika shiga munata nemanki?”.
Nannauyan numfashi na sake saukewa ina haɗiye abinda yaymin tsaye a maƙoshi tare da tattaro murmushin ƙarfin hali nace, “Babu komai Amaturrahman, kawai jinai inajin jiri shine naɗan samu waje na huta fa, inasu Safah?”. Cikin sauke ajiyar zuciya Amaturrahman tace, “Gasu can ke muketa nema dama mu wuce, muje ko”.
Hira suke tayi a motar amma nifa nakasa cewa ko uffan, abinda na gani ya kasa barin raina, shin da gaske dama akan samu mutum mai kama da wani koda basu da alaƙa kamar yanda ake faɗa? Wacece wannan mai kama da Boss haka? Shin mamansa ba rasuwa tayi ba dama kokuwa minene ke faruwa?… Da wannan tunanin a raina har muka iso gida, hankalin kowa nakan abinci.
Kowa na ƙoƙarin cin abincin da aka barbaje kala-kala domin farin cikin bikin salla amma bandani, kallonsu kawai nake tamkar wata sokuwa, Meenal dake kusa dani taɗan zungureni da hannu, “Wai nikam mike damunkine? Kodai kewar yayanmu kike ne?”. Harara na dalla mata nace, “Ashe…” dariya suka sanya min, shiru nai musu kamar bansan sunaiba.+
A gaba ɗayan wannan yinin nayi sane zuciyata cike da tunanin waɗanan bayin ALLAH da ganinsu ya kasa barin raina, a dukkan motsina sai sun faɗomin a rai, munsha yawo sosai, an kaini wajaje daban-daban na tarihi da wajen hutawa, bamu dawo gidaba sai dare, a gajiye muke liɓis, dan haka wanka kawai mukai kowa ya nema makwancinsa.
Haƙurin dana kasayine ya sakani kallon Amaturrahman da keta lumshe idanun alamar barci nace, “Amaturrahman wai su Umm-Anum ɗin basu dawo daga ittiqafin bane?”. Kaɗan ta buɗe idanu ta kalleni ta maida ta lumshe tana murmushi, “Hajiyata kin ƙagarane a fara gyarama yayanmu ke ko? Kwantar da hankalinki nasan sun dawo, dan bama gidane shiyyasa bamu shigaba, Umm-Anum saita maidake zinariya a idanun yayanmu saboda gyara”. Juya kwanciyata nai ina faɗin, “Masheranciya kawai, daga tambaya zakimin banzan fassara saida safe”. Ina jiyo ƴar dariyarta naƙi kulata, Meenal dama tana wankane.
STORY CONTINUES BELOW

★★★★★★★
Washe gari tunda safe saiga kira daga Ummu, bayan duk mun gaisa da ita tace a bani wayar. Daga can tace, “Yauwa ɗiyata ki shirya komai naki danke yau zaki koma wajen Aunty da zama, tun jiya da daddare ma taso shigowa ta ɗaukeki, ki nutsu ki kwantarmin da hankalinki ki fahimci dukkan abinda akeson ki fahimta kinji, kinga lokaci ya ƙure sosai, inason kidawo ƙasarnan da cikakken sunanki BILKEESU MAI GADON ZINARI ba Bilkisu kawai ba kinji”. Cike da jin nauyinta nace, “Insha ALLAHU Ummu zanyi duk yanda kikeso”. “Yauwa ƴar albarka ALLAH ya bada sa’a kinji, jibi su Amaturrahman zasu taho su saboda makaranta, ranar litinin su Safah zasu koma hutu”. Kamar zanyi kuka nace, “Wayyo Ummu ni kaɗai za’a bari anan kenan?”. Murmushi tayi har ina jiyo sautinsa, tace, “Ohni Munaya, anya kuwa randa zan miƙaki gidan miji baza’a sha daruba? Karki damu itama Anum ɗinta zakuyi sa’anni, nasan zata ɗauke miki kewarsu, kuma kedama zaki maida hankali ga abinda za’ai miki ai baƙya buƙatarsu Amaturrahman kusa dake, koma sun zauna na ganin juna zakuyiba, inason suzo domin shirye-shiye, ki basu duka numbers ɗin ƙawayenki karki manta”. Godiya nai mata mukai sallama.
Kamar yanda ta umarceni haka na shirya dukkan abinda yake nawa, duk ji nake babu daɗi, banso ace batare zamu koma dasu Safah ba, to amma yaya zanyi tunda haka Ummu ta tsara.
Atare muka fito cikin shiga ta kamala, Marwah jaye da ɗan ƙaramin akwatina. Gida baifi huɗu bane a tsakaninsu, dan haka tafiyar mintuna ƙalilan muka iso gidan, Aunty Mahfuzah tai knocking haɗaɗɗiyar ƙofar falon, babu jimawa akazo aka buɗe mana, wani irin tsammm naji jikina ya bada saboda cin karo da fuskar budurwar jiya. Ta rungume Aunty Mahfuzah tana magana cikin harshen larabci, kafin ta saketa ta rungume Amaturrahman da Meenal cikin tsalle irin na nayi kewarku, sai dariya suke da faɗin yanda sukai missing ɗin junansu. Ta sake rungume su Safah suma kafin ta juyi gareni, idanu taɗan waro tana nunani da faɗin, “Lah kece?” murmushi nai mata kawai dan nikaɗai nasan mi nakeji, rungumeni tayi nima, sannan muka ƙarasa falon daya gama jin kayan more rayuwa, ga sanyin AC da wani ƙamshi mai kashe zuciya, tuni ɗan gumin da mukai harya tsane, labarin haɗuwarmu ta jiya taketa bamasu Amaturrahman saboda tambayar da sukai na ina muka san juna?.
Fitowar matar gidan ya sakasu Safah miƙewa gaba ɗayansu harsu Amaturrahman sukai kanta suka rungume, ba kowa bace face matar jiya data taimakeni, bayan sun zauna ta gaisa da aunty Mahfuzah cikin salon gaisuwar larabawa, nima gaidata nai kamar yanda na iya a nawa al’adar da tarbiyyar, kallon mamaki tai min dan da’alama sai yanzune ta lura dani ma, da turanci take tambayata wai dama tare muke dasu Safah?. Amaturrahman ce ta bata amsar da take buƙata harma da ƙara mata wadda bata tambayaba. Murmushi taita saki da ƙaremin kallon da kowa yaketa mamakinsa, tana ta maimaita sunana tamkar karatu a bakinta, bansaniba daɗi yaymatane kokuwa yaya oho, dan nasan suna Bilkisu dai sunane sananne da zaka iya jinsa a kowacce duniyar musulmai balle tace yaune ta fara jinsa sabo.
Ranar dai anan muka yini, har yamma su Amaturrahman basu koma can gidanba, danni dai an tabbatarmin da nazo kenan bazan koma canba, acewartama a daren zata kaini can makarantar da Ummu ta faɗamin. Banga saurayin nanba sai yamma lis ya shigo sanye da farar jallabiya sol da mayafi irin wanda larabawa kansa akai su saka baƙin abunnan a sama tamkar gammo, fara’ar da bangansa da itaba jiya sai gata yau a fuskarsa yanamasu Amaturrahman magana da kulawa kamar yanda suma suke masa, shima dai sai da ya nuna mamakin sake ganin nawa anan, su Amaturrahman da basa hutawa sukai masa bayani dai-dai fahimtarsa, shima dai murmushin yayta saki kafin ya nufi ɗakinsa wai zaiyi wanka.
Ban tashi shiga damuwaba sai da su Amaturrahman zasu koma gidan aunty Mahfuzah su barni anan, hakan kuma na nufin munyi sallama kenan dasu, sai naji ƙwalla ta cikamin idanu, sabo kenan turken wawa. Suma kansu na lura basuso hakanba, amma sai suketa dariyar ƙaramin ƙwarin gwiwa da tsokana. Haka mukai musu rakkiya har gidan sannan muka sake dawowa ni da Anwar da Anum mai shegen surutu, yanayin rawan kanta sai yakemin kamanceceniya da Nabeelah, gata da saurin magana saina nutsu sosai nake fahimtar magana idan tayi, dama dai maganar tamu sai da turanci. A falo muka sake zama, cikin son fidda abinda kecin raina na tambayi Anum da Anuwar da naga shima ya saki jiki dani yanzu kosun taɓa zuwa ƙasarmu?. Anuwar ne kaɗai yace ya taɓa zuwa shima sau ɗaya tare dasu Abdur-rahman, sunzo hajji wata shekara zasu koma ya bisu sukaje tare, satinsa biyu acan ya dawo daga nan bai sake komawaba har yanzun, amma yanada burin sake zuwa saboda ƙasar tai masa daɗi sosai.
Murmushin jin daɗi nayi sai dai a ƙasan raina ina mamakin to Mamansu fa? Ita bata taɓa kaisu wajen nata danginba kenan kokuwa?, da ƙyar na ture tunanin a raina muka cigaba da hira har sanda Umm-Anum ta fito cikin shiri, sanin inda zamuje ya saka duk muka miƙe, tana gaba muna biye da ita har inda Anuwar ya ajiye motar da zamu fita. Ni da ita baya muka shiga, Anuwar da Anum na gaba, dukda darene garin zirga-zirga aketayi tamkar rana, gashi ko’ina ƙwanyar da wuta abin birgewa.
Mun iso wani haɗaɗɗen gini babba da nake ƙyautata zaton makarantarce, Anuwar yay fakin duk muka fito, jin kamar ana kallona yasa na ɗago, Anuwar na kama idanunsa tsaye a kaina ƙyam, saida gabana ya faɗin dan wlhy sai naga tamkar Boss, murmushi yaymin. ɗauke kaina nai batare dana maida masa murtani ba, Umm-Anum dana fahimci tana kallonmu ta hararesa da kama hannuna mukai gaba. Ina jiyo dariyarsa shi da Anum, sai dai banajin mi suke faɗa cikin harshen larabci. Gaskiya ina sake jinjina wannan tsananin kama a cikin raina, kai gaskiya inason sanin wani abu dangane da mutanen nan, wannan kamar ta wuce kama kawai, anya kuwa babu wata alaƙa tsakanin………..
Shigarmu wajenne ya katsemin tunanina, Bansan yanda zan fasalta muku haɗuwar wannan makarantaba da tsarinta, na bama kowa dama ya ƙiyasta a cikin ransa kawai, dan idan nace zan lissafo komai shafin yau da gobe duk anan zamu ƙare. Tuni na zama baƙauya wajen kallon abubuwan birgewa, to lallai da ace munada irin waɗanan makarantun da mace-macen aure ya ragu muma a yankunanmu, da ansamu sauƙin rikin aurarraki a gidajenmu. Sashe na musamman aka buɗe mana mai madaidaicin falo guda da ɗakuna biyu a ciki.
Fuskar Umm-Anum ɗauke da murmushi ta kalleni, “Ɗiyata anan zaki zauna, dan da kaina zan miki aikinnan saboda ƙurewar lokaci, ga mamanki ɗinan sotake ta ganki tamkar zinare”. Murmushi nai mata kaina a ƙasa dan haka kawai nakejin nauyinta, nai mata godiya tare da addu’ar fatan alkairi. Batace komaiba sai murmushinta dake kasheni taketa sakarmin.
Ɗaya daga cikin ɗakunan muka shiga, kayayyakine ajiye da ban fahimci kona mineneba, ta umarceni dana cire kayana gaba ɗaya na shiga wani madaidaicin kwami dake cike da ruwa da bazamu kirashi normal ruwa ba, ita kuma ta fita. Dukkanin yanda ta umarceni nayi haka nayi babu musu, inayi ina ɗan waige-waige tamkar mai tsoron wani ya shigo, saida na cire komaina kafin na fara saka ƙafa cikin kwamin, ajiyar zuciya na sauke a hankali saboda ɗan ɗumi-ɗumin ruwan mai warware gajiyar jiki, na ida saka ɗayar ƙafar sannan na shige gaba ɗayana, sihirtaccen ƙamshin da ruwan keyine ya sakani lumshe idanu ina karanto addu’ar godiya ga ALLAH da ni’imominsa masu yalwata ta fuskoki da dama ga ɗan adam. Sai da nai kusan mintuna uku da zama sannan ta shigo da sallama, ta canja kayanta da wata doguwar riga mai kama da leda, hannayenta sanye da safar hannu ta leda itama, murmushi taimin ta tako inda nake. Ɗan kwalina daban cireba ta zame daga kaina, ta warware gashina da Alhmdllh yanzu ya cika sosai kuma yanada tsayi gwargwado saboda kulawar da naita bashi bisa koyarwar su Ummie tun muna boarding, wani ɗumi mai daɗi naji ya ratsa kan nawa, hakan yasani kallon madubin dake gabana da nake iya hango kaina da ita kanta.
Tace, “A cikin ruwannan zaki kwana, babu abinda zai sameki insha ALLAH karkiji tsoro, ruwane mai ɗauke da sirrika kala-kala da duk macen da aka gyara dasu dolene mijinta yasan ta isa mace, sirrikane na ƙamshi masu daraja a jikin ƴa mace, ƙa’idar makarantarmu watanni ukune domin mace ta samu damar koyon abubuwa masu yawa, ba sirrin gyaran jiki bane kawai mace tafi buƙata a rayuwar aure ɗiyata, zakiga wata macen komai ta iya ta kuma ƙware, amma idan batasan yanda zataima miji maganaba kawai sai ya rusa mata komai, dan wani namijin shi abinda ke ƙololuwar birgesa ga mace shine iya magana, wani kuma a kallo kawai zaki gama dashi, wani tafiya, wani girki, wani ƙamshi, wani shagwaɓa, wani kwalliya, wani kwanciya. Karki sakama ranki cewa tarayya da miji a gado shine kawai farin cikin aure ko shikaɗaine auren, hakan kuskurene, wani namijin ƙanƙanin abun da kika raina shike sakashi farin ciki. Karkiyi tunanin gyara kanki yana nufin kin mallaki namiji ya zama naki ke kaɗaine, macen data isa mace bata shakkar zama da kishiya ɗiyata, dan wani lokacin zama da kishiya nasake bayyana darajar macene a wajen mijinta. Karkuma kiyi tunanin babu wata mace data isa raɓar mijinki dan yana sonki ko kin iya komai, wani namijin badan baya sonki yake miki kishiyaba ko yake budurwa, a’a halayyar san mace fiye da ɗaya a jinin maza yake, ko bazasu ƙara aureba saisun kalla. kizama mai gyara aurenki ta kowanne ɓangare, idan nace kowane ɓangare ina nufin kowanne fanni hatta da ƴan uwansa da duk abinda ya shafesa. Inason ki cire komai a cikin ranki ki nutsu ki bani dukkanin hankalinki a kwanakinan goma sha biyu da zamuyi tare, sonake komai na cikinsa ya zama tamkar rubutu bisa dutse a cikin ƙwaƙwalwarki, ki ɗaukeni tamkar mahaifiyarki, kuma ƙawarki aminiya wadda zaki iya magana kowacce iri da ita batare da kinji kunya ba, inhar kika riƙe duk abinda zaki koya a kwanakinan ina mai tabbatar miki bazaki taɓa goguwa a zuciyat mijinki ba koda zai auri mata uku ku zama huɗu bayan ke”.
Idona a risine na ɗaga mata kai alamar to, inajiyo sautun murmushinta itama. Abu ta fara shafamin a fuska tana cigaba da min magana cikin nutsuwa, sosai kunya ta lulluɓeni, dan abubuwane masu matuƙar nauyi a gareni take faɗa a buɗe, ta haɗe fuska a yanzu babu wasa tattare da ita ko kaɗan. Saida ta gama tsaf sannan ta fita suka sake dawowa da wata mata. Matar ta nunamin da faɗin, “zata zauna dake anan, ni zan koma gida sai da safe idan ALLAH ya kaimu zan dawo”. Kaina na jinjina mata dan ta hanani magana tunda ta shafamin abin fuskarnan.
Duk yanda zan baku labarin abinda ya gudana a kwanakinan da wahala ku iya fahimtata, abubuwan dana koya kam ba’a magana, sam Umm-Anum bata wasa dani idan akazo ɓangaren abinda zan iya jin kunyarta balle naga fuskar yin sakaci da abinda ake koyamin, tsaye take kaina ɗari bisa ɗari, komai buɗemin shi take babu hijjabi, aduk lokacin da takemin bayani aka abinda yafi ƙarfin kaina tamke fuska take tamau babu wasa, kai jama’a hatta da salon tafiya ba’a barniba sai da aka koyan, komai a tsare yake. Matar da take bari ta kwana dani kasa haƙuri tayi ranar dai take tambayata wai kodai ni ƴar uwar Umm-Anum ce? Dan ita yanda take ganin tanamin ya ninka yanda takema ɗalibanta fiye da zato. An kawoni ɗaki na musamman, sannan komai ba’a sakani cikin ɗalibai ni kaɗai ake koyamashi a nutse, daɗin daɗawa da kanta take min komai bata yadda kowa yayminba sai abubuwan da ba’a rasaba, dan takance kowa a rayuwa da irin basirar da ALLAH yay masa, abinda suma sauran malaman makarantar suke koyamin zai amfanar dani ta fannoni da dama. Murmushi nayi nidai bance komaiba, dan nikaɗai nasan mi nakeji game da matar nan, ita kanta lokuta da dama nakan kamata ta shagala da kallona, kallo maiban mamaki, kallo irin na shagala da zurfi ason tunano wani abu, idan tai irin wannan zurfin kuma zakaga daga ƙarshe ta dafe kanta tamkar zata fita cikin hayyacinta. Akwai randa naga kallon har yaso yimin yawa, sannan ni kaina yanda takemin ɗin nasan ba kamar yanda takema kowa baneba, tana sakin jiki dani fiye da hasashen mai hasashe. Akwai randa tazo tana koyamin girki sai muke ɗan hira kaɗan-kaɗan, cikin dabara nake tambayarta ko zasuje ƙasarmu nan kusa?. Shiru tai bata bani amsaba, na kasa daurewa dai na sake mata tambayar cike da ladabi. Yanda ta juyo ta kalleni fuska a haɗe saida naso firgita. Kaina na duƙar ƙasa ina faɗin, “Kiyi haƙuri dan ALLAH Ummu, bansan tambayar zata ɓata ranki ba”. Sautin murmushinta na jiyo, hakan yasa na ɗan ɗago na kalleta, ta ajiye cokalin hannunta tazo ta kama hannayena, murya a sanyaye tace, “Ɗiyata ba laifi kikayiminba, ƙasar takuma ni ban taɓa zuwantaba ai, duk amintakar dakika gani tsakanina da ƙanwata Gimbiya Munaya ban taɓa ziyartarta ba, sai dai ita idan tazo nan mu haɗu, duk lokacin danai yunƙurin zuwa nakan tsinci kainane a wani mummunan hali da baida fassara”. Tana gama faɗa ta saki hannuna ta juyamin baya, aikin da mukeyi ta cigaba dayi batare da ta sake min maganarba.
Ajiyar zuciya na ɗan sauke hawaye na ziraromin, haka kawai yanda tayi maganar sai naji abun daban, to amma ai Ummu ta sanarmin itaɗin ƴar ƙasarmu ce, sanadin neman magani ya kawota nan hartai aure, itakuma gashi yanzun tace bama ta taɓa zuwa canba, anya kuwa babu wani sirrin dake ɓoye?…….
Ajiyar zuciya na sauke da saurin kallonta jin ta taɓanu, tace, “Kinama fahimtar abinda nakeyi kuwa?”. Da sauri na ɗaga mata kai alamar eh na tattara hankalina gareta baki ɗaya.
________________________________
A ɓangaren Jawaad ma dai shirye-shirye sun kankama, an gama gyaran gida tsaf, ya canja kamanni gaba ɗaya tamkar bashiba, amarya kawai yake jira ta shigo cikinsa. Gaba ɗaya a tsakaninan a busy yake matuƙa, ga aiki ga shirye-shiryen biki dasu Jabeer ketayi naban mamaki, dan gayya suke ta gaske da gayya tamkar wannan shine auren farko da Jawaad ɗin zaiyi. Shidai ya zuba musu idone kawai yana kallon ikon ALLAH, dan dayay magana ca sukai babu ruwansa, kawai dai yama shirya dan bai isa cewa bazaije wajen abinda suke shiryawanba ehe. Bai sake musu maganarba kuwa ya cigaba da nasa harkokin, maganar kayan da za’a saka a gidan kuwa gimbiya Munaya tace Takawa yace zaiyi komai, kayan kicin kuwa itace zatayi. Da yay mata maganar lefe tace masa ya dakata, zasu nema Dady suyi magana, sai ana saura kwana biyu tarewar za’a kaisu can gidan Dad ɗin dan sune sukafi cancanta da amsar lefen, koyayane zasu bashi matsayinsa na uba kodan ɗawainiyar da yay da Bilkisun. Jawaad baice komaiba shi dai sai ALLAH ya kaimu.
A yau tunda safe Su Amaturrahman suka shirya yima Mami (Munubiya) rakkiya gidan kamar yanda Gimbiya da Takawa suka buƙata, zataje su haɗu da kamfanin da zasu shirya gidan. bayan sun duba saisu zaɓa mata kalar data dace a tsara komai yanda ya dace…………..✍
Bara dai na baku hakanan, inata ƙoƙarin typing ɗin bayan tafiyar baƙi amma kiraye-kirayen waya ya hanani nutsuwar yi da yawa, takaima harna daina ɗaga wayoyin mutane wlhy🤦🏻😑😓.
9BARKA DA JUMA’A
10
Page 37
………………Sosai su Amaturrahman ke santin gidan Jawaad na A.Y Street, badan yafi kowane gidaba, bakuma dan an cikasa da ƙawa ba, ginine dai tamkar kowanne gini da kowa yasani, sai dai yanda akai tsarin gyaran sai ya kuma fiddo da ƙyawun gidan fiye da yanda yake a da, (masu karatu karku manta wannan shine gidan da aka haifa Jawaad, a cikinsa iyayensa suka rayu, dan shine gidannan da turawannan suka bama Abba Abdul-aziz, shine kuma sanadin wannan arziƙi daya tsolema mutane ido). Sai da suka shiga ko’ina da ina dan babu komai cikinsa sai ƙamshin sabon fenti.
Suna tsaka da dubawa Jay ya iso gidan, zaune yake a bayan motar sai Sadiq sabon drivern sa dake tuƙi cikin nutsuwa, dan shima dai baida matsala, amma hakan bai hana Jay tuna Gimba ba a kowacce daƙiƙa ta rayuwarsa, yasan gimba bazai mantu a zuciyarsa ba, dan yawuce duk tunanin mai hasashe a zuciyar tasa. Yauma kamar kullum yana cikin gayunsa da ƙyamshi, sai dai ya ɗan rame, hakan yasakashi yin wani fayau dashi, (bamu saniba azumin da aka shane kokuma ɗokin amaryarne. lol😂).
waya yakeyi, hakan yasa har Sadiq ya fito ya buɗe masa bai fitoba, sai da yaja kusan mintuna huɗu sannan ya fito bayan ya ajiye wayar, Safah data dage sai anzo da ita da gudu tayo kansa, fuskarsa ɗauke da murmushi harta iso garesa, hannunsa ta kama tana gaishesa. Shidai kallonta yake kawai, dan sosai ƙiriniyarta ke bashi mamaki, ko gajiya batayi, girma take amma abun tamkar ƙaruwar mata yakeyi. (Hhhhh tunda Jinin Munaya na yawo a jikin Safah ai kaga abinda yafi hakama, sarki Sameer ne zai baka labari dalla-dalla😂🤐). Cikin ɗoki tace, “Yayanmu gidanka kaida aunty B ya haɗu sosai, nima harna zaɓi ɗakina dan kasanfa nan zan dawo. Murmushi yay mata mai sanyi ya jinjina mata kai amma baice komaiba.
Sosai mamaki ya kama Jay lokacin da suka shiga ciki shi da Safah yay arba da Munubiya, shi tunaninsa Gimbiyace da kanta, itama ɗindai kallon mamaki take masan sai dai ita bamusan kona minene ba. Su Amaturrahman ne suka katse tunaninsa da gaisuwar da suke masa, ya amsa musu da kulawa kafin shima ya gaida Munubiya cikin girmamawa. Kasa haƙuri yay dai yace, “Ummu da kanki? Su Amaturrahman ma aisun isa basai ke kinzoba”. Munubiya tai murmushinta mai kama dana Munaya, kafin ta bashi amsa Safah tace, “Lah Yayanmu bafa Ummu bace, wannan Mami ce sweetheart ɗin Ummu”. Cikin rashin fahimta yake kallon Safah amma baice komaiba. Amaturrahman tace, “Yayanmu ai Ummu ƴan biyune, Mami itace hassanarta”. Ɗan waro idanu Jay yayi waje sai kuma ya shafa kansa, “Sorry Mami ai wlhy ni duk ɗaukata Ummu ce, bansan ita ƴan biyu baneba nasan dai tanada yaya mace”. “Karka damu ƙanina, Gida yay ƙyau masha ALLAH, ALLAH yasa rai akaimawa, ALLAH yasa a cika manashi taf da ƴaƴa ko jikoki zance”. Cikin murna su Safah suka shiga faɗin, “Amin”. Shidai a saman laɓɓa ya amsa nasa amin ɗin.
Kasa jurewa Mami Munubiya tai ta koma gefe tai kiran Munaya, tana ɗagawa tace, “Sweetheart kingako mina gani ga angon nan?”. Daga can murmushi gimbiya Munaya tai tana gyara kanta a kafaɗar takawa, tace, “Nasan ina kika dosa sweetheart, tun randa na fara ganinsa nima naga abinda kika gani, wannan ne dalilin tura matarsa can ta ɗan zauna, sai dai bamu da tabbas, amma muna fatan ALLAH yasa ta kasance hakanne”. “Kai to amin kuwa, al’amarin akwai ruɗarwa, amma gaskiya bana tantamar alaƙa a tsakaninsa da Umm-Anum Sweetheart, nifa da farko na zata Anuwar ne wlhy, sai da nai masa kallon nutsuwa na fahimci yafi Anuwar cikar zati, Anuwar kuma ya fisa haske, hatta da maganarsu kumafa babu banbanci, bara sai dai mun dawo ma tattauna”. Daga haka Mami Munubiya ta yanke wayar ta koma ciki dan baƙin da suke jira har sun iso.
Sai da suka gama zagaye gidan tsaf kafin su basu hotunan kayan ɗakin da zasu dace da tsarin gidan akan su zaɓa. Shi dai Jawaad bai saka musu bakiba, Mami dai ta tambayesa kalar da yafi so, ya sanar musu, daga haka ya cigaba da danne-dannen waya Safah na gefensa tana zuba masa surutu, shidai nasa saurarenta dayin murmushi, sai jefi-jefi yake bata amsar wani abun koyay mata tambaya.
Kusan awa guda suka kammala komai dangane da zaɓin kayan, a take Mami ta kira Ummu ta sanar mata kuɗin da suka cajesu. Kafin kuwa subar gidan har ƙuɗaɗensu sun shiga accaunt. daga haka suka bar gidan akan sai zuwa jibi idan ALLAH ya kaimu zasu dawo suga yanda kamfanin suka shirya gidan. Jay yaymusu rakkiya har mota yanama Mami godiya, sai da suka wuce sannan shima ya shiga mota suka bar gidan.68
STORY CONTINUES BELOW

Office Jay ya koma domin cigaba da tarin ayyukan dake gabansa, dama yana tsaka da aikinne Ummu ta kirasa akan yaje can gidan yanada baƙi, dole ya ajiye ya tashi ya tafi. Fatansa ya rage ayyukan sosai, gashi yanason ɗaukar hutu kona sati ɗayane, duk da dai Sir Ahmad yace bai isaba na sati biyu zai ɗauka shima yaje yasha angwanci da ƙyau.
Zamansa baifi da mintuna talatinba baƙon da yake jira ya iso, sai da akai masa iso sannan ya bada izinin a shigo dashi, ba kowa bane baƙon face Sulaiman yayan Amina, Jay ya ɗago daga abinda yake fuskarsa a sake dukda dai ba murmushi yake ba. hannu ya bashi suka gaisa kafin ya miƙe ya kawo masa abinsha baya. ya nuna masa wajen zama, yah Sule yay godiya. Ɗan murmushi kawai Jay yayi baice komaiba. Sai da ya ɗan sha ruwa sannan Jay yace, “Yaya ake ciki Sulaiman? ka gano ina yake?”. Numfashi yaya sule ya sauke yana gyara zama, “Wato ni abin nasu yanzu ya fara ruɗar dani oga, nama rasa wanene mara gaskiyar tsakanin Alhaji Alin da Hajiya Humairan? A yanda bincikena ya nunafa Qaseem baya ƙasarnan”. “Baya ƙasar kuma?” Jawaad ya faɗa yana tamke fuska cike da ɗunbin mamaki kuma. “Ƙwarai kuwa wannan itace magana ta gaskiya, saura kwana ɗaya a ɗauki azumi ya tafi, kuma abinda na fahimta lafiyarsa ƙalau ba kamar yanda ku anan office yace zaiyi zaman ganin likita a gidaba”. Shiru Jay yayi yana juya al’amarin a ransa, tun randa ya fiddo Qaseem a cell bai sake ganinsa ba, sai ana gobe za’a fara azumi, ya shigo station amma baifi awa uku ba ya tafi, Jawaad bai kawo komai a ransaba sai da aka sake ɗaukar tsahon sati ɗaya baiga yazo aikiba, shinefa yay bincike ya fahimci Qaseem ɗin hutu ya ɗauka akan baida lafiya zaiyi zaman ganin likita a gida. Aranar bai ƙasa a gwiwa ba ya nufi gidan Qaseem, amma sai ya iske bayanan daga bakin maigadinsa, yayi tunanin yana gidansu ne, saiya saka a bincika masa can, nanma an tabbatar masa baya nan, tunda yayma gidan yajin aiki ma bai sake waiwayensa ba. Shinefa yasa yaya Sule ya bincika masa.
Huci mai zafi Jay ya furzar daga bakinsa yana danna ƙasan pen ɗin hannunsa da ƙarfin gaske, ya ɗan kalli yaya Sule ya ɗauke kansa daɗan duka table ɗin, “Tabbas yanzu na sake fahimtar akwai abinda suke ɓoyewa, in babu rami miya kawo maganar rami? Sun fahimci ina bibiyar Qaseem shiyyasa suka turashi can, ammafa sunyi abanza, sugama zagaye-zagayensu saina gano komai, da izinin ALLAH sai na bankaɗo komai, idan nace ina nufin komaima Sulaiman!!”. Ya ƙare maganar cikin fushi da dukan tebirin da masifar ƙarfi. Shidai Yaya Sule har sai da yaɗan rumtse ido. Jay yace, “Wace ƙasa suka kaisa?”. Yaya Sule da yay ɗan shiru alamar tunani yace, “Idan dai ban mantaba China naji”. Karan farko Jay ya saki murmushi mai ma’anoni da dama, yaɗan ɗage kafaɗarsa da taɓe baki.
★★★★★
Da daddare bayan Jawaad ya koma gida ya samu kira daga su Uncle Nasir, saida ya kammala shirin barcinsa sannan ya nufi sashen mama Atika inda suke jiransa. Bai wani nuna mamakin ganinsuba gaba ɗaya ya gaishesu cikin girmamawa kamar yanda ya saba.
Uncle Nasir yace, “Alhaji Ali ya kirani jiya akan ankirashi daga gidan sarki za’a kai lefenka gidansa, Jawaad kana ganin kuwa wannan hanyar daka biyo mai ɓillewace? Karfa ka manta a yanda kasa akai ɗaurin aurannan?”. Shidai Jay baice komaiba kuma bai ɗago ya kallesa ba. Cikin fushi Uncle Uwaisu yace, “Wato ga ƴan iska na magana kayi kunnen uwar shegu damu ko?” Murmushi Jawaad yayi yaɗan girgiza kansa batare daya ɗago ɗinba, yace, “Uncle to nikam mi kukeso nace, idan maganar yanda aure ta kasancene tun a wancan karon na bada amsar da duk ake buƙata, a tunanina yanzun mun wuce wannan wajen, kai lefe kuwa daga can masarauta ne sukai tunain akai lefen can saboda koba komai ubane shi ga yarinyar shine kuma mariƙinta har a yanzun……….”
“A wannan ganganne Jawaad, Shine mariƙinta ko kai daka ɗauketa ka maida gidan sarki saboda ka isa, karkuma a taɓa maka ƴar gwal?”. Uncle Bashir ne yay maganar a fusace. Jawaad da har yanzu yaƙi kallon kowa a cikinsu yace, “Nidai duk abinda kuke ganin na mukushi ba daidaiba akan wannan aure kuyi haƙuri ku kuma gafarceni”. Uncle Sulaiman da tun ɗazun baice komaiba yace, “Nima dai a ganina maimaita maganar baida amfani tunda abinda ya faru ya rigada ya faru, haka kuma ALLAH ya tsara dama zata kasance, kunga kenan bamu isa canja wannan ƙaddarar ba. Yanzu Jawaad ina zaka ajiye matarka? Dan bamuga kana ƙoƙarin gyara ɓangaren nakaba”. Karon farko Jay ya ɗago daɗan murmushi ya kalli Uncle Sulaiman, “Uncle ba anan zan ajiyeta ba, A.Y street zata zauna har an kammala gyaran”. Uncle Nasir yace, “A.Y kuma? Saboda karmu cinyeta anan?”. Jay da keta ƙoƙarin danne fushinsa yace, “Ba haka bane Uncle………..”
Da sauri Mama Atika ta ƙatseshi da faɗin, “Inma haka ɗinne kaidai ka sani fitsararre mai shegen taurin kai da raini, hakan dakai ni bai dameniba, dan ko kaƙi ko kaso dolene a maida aurenka da Sabira, dama shirin maka tsinannen mijin daka aura mata muke a kotu, sai gashi ya matu kuɗinmu sun huta, to wlhy kama tabbata aure kamar mun maidashi ne kai da Sabira”. Cikin fushi Jay ya kalleta zaiyi magana Uncle Sulaiman ya girgiza masa kai. Shiru yay ya maida kansa ƙasa, har sukaci jarabarsu suka tsire bai sake tankawaba, taron dai ya watse da sharaɗin sai ya maida aurensa da Shahudah.
Shidai bai tanka musuba tunda yasan ɗan fir’auna bai mutuba.
STORY CONTINUES BELOW

__________________________________
SAUDIA
Gaba ɗaya wannan yinin na yau Umm-Anum ta yisane cikin yimin nasihohi da haɗamin kayan gyaran jiki da wasu littatafai masu muhimmanci kamar yanda tace, sai faifan cds da tace na kasance cikin kallonsu duk randa nake da lokaci zasumin amfani.
Gaba ɗaya raina a ɓace yake banason tafiya, basan yanda zan musalta muku yanda nakejinta a rainaba, tunda tafiyarnan ta gabato har kuka nakeyi idan na tuna zan tafi, baƙaramar shaƙuwace ta shiga tsakaninmu ba a kwanaki sha biyun nan, kodan ta jani jikintane oho.7
A ɓangaren Umm-Anum ma dai cike take da damuwa, haka kawai takejin batason Bilkisu ta tafi, yinin yau komanta sukuku zaka gansa, da daddare tare suka dawo gida da bilkisu, anan zata kwana yau gobe idan ALLAH ya kaimu zasu wuce ita da Aunty Mahfuzah da Anum sai Anuwar daya dage shima zaije, da farko Umm-Anum catai bazaijeba, sai da Abie yasa baki sannan da ƙyar ta amince, dan haka kawai takeji batason suje da ga shi har Anum ɗin.
Abie bai taɓa ganin bilkisu ba sai yau bayan sun dawo, itama kuma yauɗin ta taɓa ganinsa, amma yanda ya karɓeta abin har mamaki ya bata, shikansa mamakin yanda yarinyar ta shiga ransa yakeyi, sannan badan kar ace yay ƙaryaba wasu abubuwa nata suna ɗan masa kama dana Umm-Anum ɗin, musamman tafiya da dai wasu ƙananun abubuwa da saika nutsu sosai kake fahimtarsu.
Sai da su Bilkisu suka shige suka kwanta sannan ya fuskanci matarsa, dan yanda take komai rai ɓace ne ya sakashi jinsa shima a damuwa. cike da kulawa yake tambayarta mike damunta?. Hawayen da taketa riƙewane suka zubo mata. Sake rikicewa yay ya jawota jikinsa, dan yanason wannan baiwar ALLAH shidai a rayuwarsa, dukda ba ita kaɗaice matarsaba kuwa, amma yanda take ƙyautata masa yasa tazama tauraruwa a garesa. Yanda yaketa jero mata tambaya wata kan watane ya sakata sakin murmushin ƙarfin hali, idonta a kansa tace, “Bafa komai baneba, yarinyarnan banason ta tafi wlhy, jinta nake cikin jinina fiye da yanda kake zato, ina mata ƙauna maiban mamaki har a ƙarƙashin zuciya, sannan sunanta duk sanda na ambacesa ko wani ya ambata sai naji matsananciyar faɗuwar gaba, bansan miya saba”. Abie dai kallonta ya keyi cike da nazari, sai da tagama ya sauke ajiyar zuciya tare da sake rungumeta, maganganunta na buƙatar ayi musu zama na musamman domin yin nazari, amma duk da haka bara ya gwadata ya gani, ko lokacin da suke fatane yazo. “To kodai zamu shirya muma muje bikin nata ne?”. da sauri Umm-Anum ta tashi daga jikin mijin nata tana girgiza kanta, fuskarta harta nuna ɓacin rai, tace, “Babu inda zani Annur, badanma ka takuraba kosu Anum bazasu jeba”. Da kallo shidai kawai yake binta, amma baice komaiba, baikuma sake cewa uffanba game da tafiyar har gari ya waye su Bilkisu suka tashi da shiri.
★★★★
Yau ta kasance ranar da zan koma ƙasata ta haihuwa tare da tarin alkairan Umm-Anum da mijinta da Aunty Mahfuzah, sai su Anum da nakejin ƙololuwar farin cikin tafiya tare da su, gefe guda kuma na zuciyata najin ɗacin rabuwa da Umm-Anum tare da matsananciyar kewa. Munfi awa uku zaune da ita tana sake tisamin abubuwa masu dama, daga ƙarshe ta roƙeni akan karna manta da ita, zata kuma ringa kirana akai-akai, idan kuma nasamu lokaci na daure muzo gareta wataran tare da mijina, haka kawai takeji a ranta tanason ganin mijin ƴarta. Murmushi kawai na iyayi ina share hawayena kaina a risine, ta rungumeni a jikinta tana jeromin addu’oin fatan alkairi da zaman lafiya a gidan aurena. Da ƙyar ta barni na fito, tana kuka nima inayi tamkar zan shiɗe, da ƙyar Aunty Mahfuzah taja hannuna ita da Anum.
Har jirginmu ya ɗaga ban daina kukan kewar Umm-Anum ba, ina ƙaunar matarnan matuƙa a cikin jinina da tsokar zuciya harma da ruhi.
Kasancewar tafiyar yamma mukayo dukda ba time ɗinmu ɗaya da nanba munyi saukar dare ne, inda mukaci karo dasu Amaturrahman ƴan tarba, sosai muke murnar ganin juna, sai santi suke wai na canja matuƙa, sunata zubamin shaƙiyanci nadaiƙi kulasu, dan bana cikin mood ɗin farin ciki sam.
Koda muka isa masarauta Ummu ma rungumeni tayi, sai taɓani take tana jerama Umm-Anum addu’oi na musamman, ga daɗin da taji na barin su Anuwar da akai suka biyomu. A ƙasan raina inata mamakin ganin yanda suketa shirye-shiryen bikin tamkar zasu aurar da ƴarsu ne ta cikinsu ko ƴar uwa ta jini, kai waɗanan mutane sun cancanci zama shugabbani, domin duk mai fuskantar al’umma da maida al’amarinsu nasa to lallai shine shugaban da yafi cancantar zama shugaba.
Ɗaki guda aka waremin dan Ummu tace bazan zauna ɗakinsu Amaturrahman ba wannan karon, akwaima sauran kayan gyara da Umm-Anum ta bayar a ƙarasa min a kwanaki biyun da suka rage mana. Babu wanda yaymin maganar Boss nima kuma bamma kowa ba, da yake darene bayan anɗan gaggaisa duk muka kwanta.
STORY CONTINUES BELOW

WASHE GARI.
A safiyar yau nakejin wai za’a kai lefena gidan Dad ne, haka kawai naji gabana ya faɗi, amma sai na danne zuciyata na cigaba da addu’oi, har yanzu Yah Qaseem na ƙasan raina, inason nasan halin da ya ke ciki shi da Dad fiye da kowa a gidanmu, sai dai hakan ta gagara dan boss ya toshe ko ina da ina da zan iya jinsu. Su Amaturrahman sunata shirin tafiya can gidan domin amsar lefen suma, sai a yau naga sauran manyan ƴaƴan Ummu ƴan uwan tagwaicin Amaturrahman. Abdul-Raheem da Abdur-rahman, sai Ameen ɗan uwan tagwaicin Meenal, sai Uncles ɗinsu huɗu, Sauban da matarsa ƙyaƙyƙyawa mai kirki da yaransu huɗu masha ALLAH, sai Aryaan shima da matarsa da yara biyu, Aiyaan ma matarsa da yarinyarsu ɗaya sai ciki ƙarami da matarsa keda shi, sai Khalil shima da tasa matar da yara biyu, dukansu suma a jiya suka iso daga India. Gida ya cika yanda akeso tamkar bikine daya shafesu na jini, washe gari sai ga wadda naji suna kira Aunty Samha itama da nata ƴaƴan, sai kuma babbar mace suna kiranta Aunty Mimi. Wlhy bansan sanda hawaye suka faramin gudu a kumatuba, duk wani kewar ahali sun toshemin ita ta ko ina, sun mayemin gurbin dangin da suka nisanceni.
A wajen Amaturrahman nakejin wai Boss yazo masarauta wajen Ummu yau da safe, bai nemi inda nakeba har ya wuce, banji komai a rainaba game da hakan, sai daga baya suke bani labarin Ummu ce tace an daina ganina har da shi kansa bazai ganniba. Ni saida abinma yaso bani dariya amma na kanne.3
___________________
A gidan Dad kam shirye-shiryen karɓar lefe suke, duk da dai ran Momy a ɓace yake matuƙa tana dai ƙoƙarin dannewane, shi dai Dad baka gane yanayinsa, dan yamafi maida hankali ga lallashin ƴar lelensa da suka cikama zuciya da alƙawarin komawarta gidan Jay nan bada jimawaba.
Kusan sha biyun rana su Amaturrahman suka iso gidansu Hudah, Hudah dai bata fitoba zamanta tai cikin ɗakinta, Aamilah kuma an fito ayi rainin wayo saita iske waɗanan sunci uwarta aduk iskancin da take taƙamar ta tara kota iya. Dole fa ta nutsu waje guda ta kama kanta, harta je ta ƙwanƙwasama Shahudah dake ɗaki gulma da cewar lallai Bily ta shahara a asirin nata har ƴan gidan sarki taimawa. Cikin takaici Shahudah tace, “Tsinanniya jikar matsafa, ai nayi alƙawarin randa na koma gidan Bb wlhy bazata kwana a gidanba, shi kansa saina sakashi yin nadama wlhy, kuma a banza zata shiga ta fito Hajiya (mama Atika) tamin alƙawarin ko hannunta bazai riƙeba dan Uban da ya haifeta”. Dariya Aamilah ta sanya da sake tunzurata akan hakan da zatai shine dai-dai, kuma taji daɗin matakin da mama Atika tace zata ɗauka akan kar Bilkisu ta raɓu Jawaad, (dan sufa har iyanzu tunaninsu nakan asiri Bilkisu taima Jay bawai sonta yakeba😂). “Mtsooww kamar kin manta da aikin matsafa kenan” cewar Shahudah cike da takaici. Haka dai sukaita aikin zagin Bilkisu da Alhaji Babba harda su Ummah basu tsiraba, kai gidan sarki ma saida suka samu rabonsu😂.
Oho su bama susan da zaman wata Hudah ba a duniya balle a cikin gidan, sun ɓararraje abinsu sunata harkokinsu tamkar gidansu (😂Wani aiki saisu Samha) hankalinsu kwancefa yake a gidan Dad dukda sunga cika da batsewar da Momy keyi basu nuna ta damesuba.
Ƙarfe biyu da wasu mintuna na rana matan Uncles ɗin Jawaad dasu Ummah suka iso da lefen Bilkisu. Kayane gwargwadon iko na gani na faɗa babu fariyya a ciki balle nuna anfi kowa. Sai dai fa tsarin kayan da nagartarsu dolene ta girgiza zukatan mahassada da masu ganin wadda akai dominta bata cancancesu ba. Inna zainabu sai haɗiyar zuciya akeyi, hatta da Lawisa da ayanzun basa faɗa da bilkisun kuma itama mijinta Alhmdllh sun sami sauyi saida taji ɗaci a ranta, hakama sauran dangin kowa dai ta ciki na ciki, su kansu matan Uncles ɗin Jawaad da suka kawo kayan kowa dai sai murmushin saman fuska tunda suma sai yaune suke ganin kayan tunda su Ummah ne suka haɗa abinsu. To kowa dai ya danne an gama komai lafiya, an kuma bar kayan anan sai Dad ya gani sai a kaisu masarauta zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu suma su Gimbiya su gani.
Tukuyci mai tsoka ƴan masarauta suka saukema su Ummah, wanda ya girgiza kowa hatta momy da take ganin wanda Dad ya bada a bayar yayi yawa da.
Aikam tunda su Safah suka koma masarauta babu abinda suke sai labarin lefe, suka addabama Bilkisu da tsokana musamman su Amaturrahman da matansu Aryaan da suke biye musu suma dayake mashiriritan ne. Sai da gimbiya ta fito da kanta ta korasu daga kan Bilkisu sannan suka sama mata lafiya.
STORY CONTINUES BELOW

_________________
Gayya taban mamaki su Jabeer sukayo a wannan biki, al’amarin har ba’a cewa komai, tun a yau baƙin nesa kuwa suka fara sauka, irin su Abbati ma duk yau suka kawo matansu gidan Ummah babba, su kuma suka yada zango a masaukin da su Hafiz suka tanada musu.
Ango kuwa yau alhamis yana zuwa office Sir Ahmad ya korosa akan ya tafi sun bashi hutu, karya ƙara ganin ƙafarsa sai nan da sati biyu ciff, shidai murmushi kawai yayi baice komaiba. Ƴan station ɗinsu ma dai zuwa yanzu sunsan boss ya auri Bilkisu, masu gulmar dama soyayya yake da ita sai bakuna suka buɗe aka samu nayi, yayinda masu goyama Rose baya suketa angizata da maganganun ɓatanci ga Bilkisu da Jay ɗin kansa, masoyansu na ƙwarai kuwa murna suke tayasu da ganin sun dace da juna.
MASARAUTA
Tunda garin ALLAH ya waye an tashine cikin shirye-shiryen kamu da aka haɗashi da Hausa fulani day baki ɗaya, su Ummie, Nazifa, Zuhrah, Rebecca, Amina, Nabeelah, duk suna can suma tare dasu Amaturrahman, abin birgewa kuma duk ƙawayensu na Boarding skull sai da su Ummie suka gayyatosu suma duk sunata isowa masarauta a safiyar yau, hakan saiya saka Bilkisu hawaye da tuno iyayenta, inama da ransu wannan rana tazo mata, inama suna jingine da ita har zuwa yau ɗinta, ina firdausin ta, ƙawar amana ko tace ƴar uwa rabin jiki, kullum addu’arta ALLAH yasadata da Firdausi da iyayenta kafin tabar duniya.
Tunda safe dama mai ƙunshi tazo muka shige cikin ɗaki daga ni sai ita ta shiga zanamin na nutsuwa, zuwa azhar ya bushe yay shar kamar ka cinye dan baƙi da jaa aka ɗaɗara mani, kasancewar fashin salla nike dama sai kawai aka shigamin gyaran kai a nan gida dan Gimbiya nada dukkan kayan gyaran kai a gida da takema kanta, bayan an kammala nai wanka lokacin ƙarfe kusan uku.
Kasancewar ba sallah zanyi ba sai ban damu da kwalliyar da ake shirin tsaramin ba, ni kaina basai an faɗaba nasan ina tsaruwa dai-dai gwargwadon iko, duk da ba’aimin kwalliyar dana canja kamanni baneba amma nayi ƙyau fiye da zato. Bayan an kammala kwalliyar aka shiryani cikin atamfa lass ƴar ubansu datasha stones work ɗan gaske, sket da riga akai da suka fidda ainahin tsarin jikina dukda basu matseni tsam ba, sundai zaunamin a jiki ɗas har ni kaina ban gaji da kallon kaina ba. An min naɗin ɗan kwali mai tsari aka ƙawata adon nawa da sauran kayan ƙawata kwalliya irinsu sarƙa da sauransu. Ƙamshina kam ai har hawa kan mutane yakeyi, daka ganni kaga cikakkaiyar bahaushiya jinin Fulani, tabbas a yau na sake yarda da babu mummuna a duniya sai wanda ya munana kansa, idan har zaka tashi ka gyara kanka tofa ka wuce a kiraka mai muni, dama can rashin gata da kulawane suka dadushe sihirtaccen ƙyawuna mai cike da kwarjini.
Taron iya matane, dan acikin masarauta ma za’a yisa, su Ummah da danginsu duk sun iso masarautar, hakama danginna na ɓangaren Uwa su Inna Zainabu dasu Momy harda Aamilah, Aunty Shahudah dai ban gantaba, ƴan gidansu Boss ma kam inada tabbacin ƙwai da kwarkwata ne a wajen nan. Babu abinda da dai za’a cema UBANGIJI sai godiya a wannan al’amari, amma tabbas Bilkisu tazo da farin jini mai ban mamaki da tarin alkairi. Iyayen ƙawayenta su Ummie, matansu Aliyu, abokan aikinsu ƴan station ɗinsu, ƙawayenta na makaranta harma da waɗanda sukazo dalilin wane da wane duk suna a wajen. Sai ƙarfe huɗu da rabi Gimbiya Sarauniyar gagara badau Munayatul-muna ta fito riƙe da hannun amarya Bilkisu mai gadon zinari.
Ai a take wajen ya ɗauki ƙannan magana musamman ma ƴan gidansu Jawaad da ada suke ɗaukar Bilkisu ba komaiba saboda yanda su Momy ke munanata da ƙasƙantar da ita a garesu. Wasu sunɗan santa sama-sama wasuko sai a yau suke ganinta.
Ganin yanda ɗunbin mutane suka taru danni sai kawai naji hawaye sun zubomin a kumatu, Zuhrah ce ta duƙa gabana inda ya kasance mazaunina ta shareminsu da handkherchief tana murmushi, “Haba amarsu ai lokacin kuka baiyiba kinji, sai gobe idan ALLAH ya kaimu kina kusa da Boss, da sun zubo ya lashe kayansa”. ta ƙare maganar da kashemin ido. Hararta nayi ban iya cewa komaiba, sai dai fa maganar datai sai da naji gabana yaɗan faɗi, dana tuna kuma ma ina period saina ɗanji sauƙi a raina.
Ba’a ɓata lokaci wajen fara gudanar da abinda ya tara mutane ba, komai kuma a nutse babu wata hayaniya, koda aka fara kiɗan ƙwarya ma a nutse ƴammata da matan aurenma masu jini a jika keyin rawa, ina tsakkiya nikam anata zubamin liƙi, Anum na liƙe dani wai tana gwagwaɗamin wai itama idan ta tashi aure zamuje Saudiyya da masu kiɗan su mat. Murmushi kawai nayi mata dan ta bani dariya.
komai ya tafi cikin burgewa da kwanciyar hankali, kafin a koma yin hotuna da kowa ke fatan yi da amarya da gimbiyar gagara badau. Zuwa magriba aka tashi.
Ni dai tunma kafin magriban muka bar wajen tare da Ummu da akoda yaushe tana kusa dani idanunta akan kowa da zai iya raɓata. Dan tace itafa bata wani yarda da kowa dake wajenba.
______________________
A ɓangaren su Jay suma sunacan suna nasu shagalin, sai dai su nasu sai bayan sallar isha’i suka fara, suma iyasune maza zalla a wajen abokansa, su Aryaan duk suna can dan kuwa dai sa’annine, sudai su Abdur-raheem, dasu Anuwar basu jeba kasancewar su Jay yayunsune wannan shigar ba tasu bace, suna buƙatar sakewa kuma, sunama can gidan Mami Munubiya suna shan shaftarsu hankali kwance.
Dauriya kawai Jay keyi, dan kansa ciwo yake masa matsanancin ciwo ma kuwa, amma kasancewar yasan duk ɗunbin mutanennan dan shi suka taru sai ya daure har zuwa goma na dare kafin ya gudu ɗakin da zai kwana a hotel ɗin ya barsu, ko wanka baiyiba dan bai jima da yiba, kayansa kawai ya zame ya faɗa saman gadon ya kwanta yana sauke tagwayen ajiyar zuciya, cikin ransa ko mamakin Bilkisu ya keyi, ƙaramar yarinya da ita sai shegen jan aji da miskilanci, tunda ta tafi bata nemsaba, ta dawo ma haka. Wani ɓangare na zuciyarsa yace, ‘Kaida haƙƙin sanin lafiyarta ke a kanka ka nemeta ne?’. Kansa ya dafe kawai da lumshe idanu, kafin ya buɗe a hankali ya jawo wayarsa dan tunawa da saƙwanin da yasa a turo masa.
Kasancewar datarsa a buɗe take duk sunma buɗe kansu da kansu, harda videos. Ya sauki wani lallausan murmushi maiban mamaki daya sakani tunanin wai shin mi yake kallo hakane?…………….✍55
Jiya kun haɗan zafi yasin, waɗanda ban ɗaga kiransu ba suyi haƙuri man kaina ne ya tsiyaye😂🚴🏼.5
BARKA DA JUMA’A.
4
Musha weekend lafiya
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭😭🙏🏻31Page 38
………………Shagulgulan biki sun cigaba da gudana a washe gari tamkar yanda aka tsara, su Ummah babba sunyi yinin biki suma matsayin iyayen ango, kafin zuwa la’asar su ɗunguma zuwa masarauta domin halartar walima da gimbiya ta shirya itama. Walima kam ta ƙayatar fiye da zato, amarya tasha ƙyau cikin shadda pink mai duhu. Inda malamai magada annabawa suka gudanar da wa’azi mai kashe jiki da ɓargo, bilkisu kam dai ansha kuka, idanu sun ƙara girma. Tun su Zuhrah dake zaune kusa da ita suna mata dariya har dai suka koma lallashinta suma suna sharar hawayen dan jikinsu duk sai yay sanyi ƙalau. An tashine gab da magriba, dan haka kowa yana yin salla shirin tafiya dinner ya fara. Amarya ma wanka aka sakata ta shiga.
Gaba ɗaya jikina a sanyaye yake, tunani da fargaba duk sun cika zuciyata, yau ni Bilkisu nice za’a ɗauka akai gidan boss matsayin matarsa ta aure, aure ba yawo ba, idan naje shike nan natafi din din din, duk da nasan ba sonsa nakeba, shima kuma bason nawa ya keba na ɗaura ɗammarar masa biyyayya insha ALLAH, zanyi haƙuri tamkar yanda kowa ke faɗamin zaman aure haƙurine, zanyi biyayya a garesa matsayinsa na mijina shugabana, zanyi aiki da dukkan dabarun Umm-Anum da gambiya suka ɗorani akai domin samun zaman lafiya a gidana koda ace bazai soni ba. tausayinsa nakeji har cikin raina yanzun, dan a daren jiya munyi zama na musamman da Ummu inda muka tattauna game da kamanninsa da Anuwar harma da Umm-Anum ta abubuwa da dama. Ta tabbatar min nice ya dace nai wannan aikin na bincikar abinda ya shafesa ko tanan zasu iya fahimtar idan akwai alaƙar da duk muke zargi dan kamannin sun wuce kama akwai dangantakar jini dole, bansan komai na abinda ya shafi family nasa ba, sai ɗan abinda ba’a rasaba shima iyakarsa daga wajen su Mom ne da da rashin jituwa tsakaninsa da Yah Qaseem, amma a raina nima tunda muka haɗu da Umm-Anum nakeji abubuwa da dama nazomin a rai game da shi……… Da wannan tunane-tunanen na tsaftace jikina na fito, kasancewar ba salla zanyiba zaman min kwalliya akayi.
Tun ina jiyo hayaniyar ƙawayena dake ɗakin su Amaturrahman suna shiryawa har naji tsit, alamar dai sun fice dan zuwa yanzu har anyi sallar isha’i. Basan yaya zan musalta muku irin ƙyawun da nayiba yauma, amma na bama kowa damar ya hasasoni cikin zuciyarsa, kwalliyata ta yau ta kasance harda alƙyabar da Mommah ta bani matsayin ƙyautarta, basai an faɗaba, a gani da ido kaɗai ya isa amsa ga mai kallo cewar an sayeta da kuɗaɗe masu nauyi da darajar gaske. Suna cikin gyaramin alƙyabbar da santin ƙyawun da nayi aunty Samha ta shigo.
“Wow, masha ALLAH amaryar ƙamshi” ta faɗa tana rungumeni, ta ɗagoni tana kallona da cigaba da faɗin, “Wannan ai saiki rikita angon yace an fasa dinner ɗin”. Dariya waɗanda sukaimin kwalliyar sukayi, ni dai kaina a ƙasa ban yarda na kalleta bama dan tasa naji kunya, gashi kukane keta ƙoƙarin tasomin ina dannewa. Itace ta kama hannuna muka fice, ganin ba’a kaini wajen Ummu ba sai nayi tunanin za’a sake dawo dani nan kenan, ƙilama sai gobe idan ALLAH ya kaimu. A take naji farin ciki ya wani lulluɓeni. Ko ina ƙwanyar yake da haske a masarauta shiyyasa koda muka fito dukda kaina a ƙasa yake ina kallon inda muka nufa.
Mun tsaya dai-dai motar da na hango Oga Jabeer jingine yana waya tun fitowarmu, yana sanye da shadda ƴar ubansu ruwan madara. Yana ganin mun ƙaraso ya ajiye wayar yana murmushi da faɗin, “Aunty Samha aini da har ina shirin bin bayanku, dan naga baƙwa son bamu amaryarnan kamar”.
Murmushi tayi mai sauti tana gyaramin hular alƙyabar, “To gaskiya badan munasoba zamu baku, dan bamu gaji da ɗiyarmu ba, amma yaya muka iya, wannan shine girman”. Oga Jabeer na ƴar dariya ya buɗe ƙofar motar da cewa, “Aure yaƙin mata”. Tace, “Har mazan ma”.
Daddaɗan ƙamshin turarensa da na sani daine ya fara tarbata da sallama, na shaƙa na lumshe idanu ina ƙoƙarin dai-daita bugun zuciyata da kalato yawun da zan jiƙa maƙoshina da ya bushe, sai da na zauna da ƙyau Mah-mah ta gyaramin alƙyabar sannan na tsinkayi muryarsa yana gaisheta cike da mutun tawa, sai da suka gama gaisuwar sannan Oga Jabeer ya rufe motar ya shigo shima, itama motar da zasu tafi a ciki ta nufa ta shiga.
“Ina yini?”. Na faɗa a hankali har banyi zaton zaima jini ba. Shiru banji ya amsaba, kuma tabbas inaji a jikina idonsa a kaina suke, dan ina jinsu har cikin ɓargona. kaɗan juya na kalli sashen da yake dan in tabbatar da bai jinin ba kokuwa ƴan wulaƙancinne a kusa…..
Ina ɗagowa idanuna na shigewa cikin nasa, saurin maida kaina ƙasa nai ina ɗan ƙunƙuni a cikin raina batare da nasan bakina naɗan motsawaba ashe, ‘mutum babu abinda ya iya sai kallo, har sai an hango maka muni’.
Jawaad dake kallon yanda bakinta dake ta shining na ɗan lipstick ɗin da aka sanya mata ya lumshe idanu a hankali yana sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya, maida kansa yay jikin sit ya kwantar yana maijin takaicin yarda da yay da zuwan wannan dinner ɗin banzar, yanzufa kowa sai yaga wannan ƙyawun da tai ko?. Ware idanunsa ya sakeyi a kanta yana binta da wani irin sassanyar kallo, gaba ɗaya ƙamshin turarenta ya saukarma gaɓɓansa da kasala………
“Ehhgy egeehhmm!”. Jabeer yay gyaran murya. Haɗe fuska jay yayi ya balla masa harara tare da ɗauke kansa ya maida gefe bai dai ce komaiba. Jabeer ya haɗiye dariyar dake cinsa daƙyar sannan ya tada motar suka fice.
Shiru motar tayi bakajin motsin komai sai na ac da ƙamshin turarukanmu, tunda na gaida Oga Jabeer nima ban sake ko ɗaga kai na kalli inda sukeba, dodon nawa kam tun gaisuwarsa da aunty Samha ban sakejin ya firta komai ba shima, anata kiran wayarsama yayi kunnen uwar shegu tamkar ba yaji ana kiran. Mintuna ƙalilan muka iso wajen taron, inda muka taras da abokansa dasu Ummie tsaitsaye alamar isowarmu suke jira.
Jabeer da yay fakin ya juyo ya kalli Jay. “ku zama cikin shiri boss, bara na musu magana”. Kai kawai ya ɗaga masa, shi kuma ya fice. Kusan sakanni ashirin da fitar Oga Jabeer babu wanda ya motsa a cikinmu daga ni har shi, inata ɗan juya zoben yatsana ne dan gaba ɗaya a takure nakejin zaman namu kusa da juna.
“Bana son rawa” na tsinkayi muryarsa ƙasa-ƙasa saitin kunnena, da sauri na juya garesa dan a bazata maganar tazomin. A karo na biyu muka sake haɗa ido, sai dai yanzun duk yanda naso janye nawa kamar ɗazun hakan ya gagara, kallo yakemin irin na tsakkiyar idonnan tamkar zai haɗiyeni dasu, bazan iya jurewa ba, amma na kasa janyewa dan tamkar yamin ɗaurin goro ne da mayun idanun nasa da a yau suke farare tas babu sirkin ja alamar dai baya tattare da ɓacin rai. Da ƙyar na samu nai ƙoƙarin yin ƙasa da kaina zuciyata na wani tsitstsinkewa tare da jinin jikina. Amma a bazata saijin tattausan hannunsa nai ya taro haɓata ya sake ɗago fuskar, tuni zuciyata ta sake wani zallo tamjar zata faso ƙirji ta fito, Farfar na farayi da idanuna da suka cika taf da ƙwalla lokacin da ya matso da fuskarsa daf da tawa har munajin saukar numfashin juna, lumshe idanun kawai nayi ganin bani da wata mafita kuma, ya kawo bakinsa daf da nawa.
Yanda jikina ke tsuma zai tabbatar maka a matsanancin tsoro nake da yanayin, tsigar jikina duk ta miƙe.
Jay dake kallon yanda bily ta rikice ya saki lallausan murmushi tare da goga hancinsa kan nata, murya can ƙasan maƙoshi yace, “Matsoraciya kawai, darajar matata tafi ƙarfin nayi kissing ɗinta anan wajen yariya, hakan bazai taɓa yuwuba sai a fadata insha ALLAH. badan girman alƙawari ba da bazan taɓa bari ki shiga wajen nanba, ni kaɗai yafi cancanta na shaida wannan ƙyawu naki a cikin gidana. Ina ƙara maimaita miki bana son rawa”. Ya ƙare maganar da ɗaura yatsansa babba saman lips ɗina ya kwashe ɗan lipstick ɗin da aka samin.
Wata irin kunya naji ta lulluɓeni mai haɗe da tsoro da ɗan haushin gogen lipstick da yayi, nai ƙasa da kaina ina ɗan kumbura da faɗin, “Toni nama iya rawan ne ma………”
Saukar ɗalli kawai naji a saman laɓɓana mai azabar zafin, na ɗago idanuna da suka cika da ƙwalla a kansa. sassanyan murmushin mugunta ya sakarmin har dimples ɗinsa duka biyu na loɓawa, ya ɗage kafaɗunsa yana ɗage gira ɗaya da taɓe baki alamar ni naja.
Kafin wani ya ƙara magana a cikinmu akai knocking glass ɗin motar, sauke gilas ɗin yayi, oga Hafiz ne yay masa magana akan mu fito. Banji amsar da ya bashiba, baice min komaiba nima ya fice, ina ƙoƙarin gyara alƙyabata nima na fita naji an buɗe ƙofar ɓangarena, na ɗago dan ganin wanene muka haɗa ido ashe shine ya zagayo tanan, hannunsa na dama ya miƙomin yana wani ɓata fuska da kallona ƙasa-ƙasa, a kunyace na ɗora nawa ya taimakamin na fita nima, hannunsa na haggu yasa yaja hular alƙyabar ya sake rufemin fuska da ƙyau.
Ina jiyo wani cikin baƙin abokansa na faɗin, “Sarakin kishi muma ba kalla zamuyiba ai bar wahalar rurrufe mata fuska”. banji ya bashi amsaba sai dariyar da sauran sukayi. Inajin irin zafin da nakeji a duk lokacin da ya raɓu jikina, sai dai yau kaɗan nakejinsa cikin amincin ALLAH, dan haka nai jarumtar daurewa tamkar banajin komai ina addu’a cikin raina har muka shige abokansa da ƙawayena na biye damu a baya cikin ƙyaƙyƙyawan tsari babu wata hayaniya.
Muna shiga da aunty Batool dake ƙofar tsaye tana jiranmu muka fara cin karo, ta shiga feso mana wani farin abu mai ƙyalƙyali da ƙamshi, masu hotuna kuwa nata ƙyalla mu.+
STORY CONTINUES BELOW

Sauran mutanen duk suka miƙe idanun kowa na kan amarya da ango dake cike da birgewa, yayinda ƴanmatan family ɗin su Jay sukejin zafi a zukatansu dajin takaicin bilkisu da tazo daga sama tai musu wuf da shi, sai irinsu Rose da kallo ɗaya zakai musu ka hango tsagwaron kishi da tsanar bilkisun a cikin idanunsu. MC kuwa na zubama amarya da ango kirari. yayinda Ali jita ya sake gyara maƙogwaron nan nasa na zinari ya fara baitocin girma ga amaryar ƙamshi bilkisu mai gadon zinari cikin waƙarsa mai taken Bilkisu gimbiya.
(Bara naɗan raira muku kaɗan saura wani yace ban iyaba😣😚. lol)
🎸🎸🎶🎶BILKEESU zan faɗa dan ALLAH, mata ku bani dama duka.
bilkisu gimbiya.
BILKEESU mai gadon zinari waƙarki ta fita haka.🎸🎶🎶
BILKEESU sai gani sai nuni, kowa ya tabbata duka.🎸🎸🎸🎺🎺
BILKEESU gimbiya an baki, mata su dakata duka.🎸🎸🎺
BILKEESU sanya alƙyabar ki kaya mayalwata haka.🎸
Bilkisu gimbiya.
BILKEESU za’a yiwa fada, ai mata fifita haka. 🎸
Jita kaja muje nai waƙar Bilkisu masu girma haka.🎸
Mata ku rausaya Ali jita nine na baku dama haka🎸🎶🎶
Komai yanada rana a gane dama tanada dama haka, Bilkisu gimbiya.
Giwa ki rausaya BILKEESU ALLAH ya ƙara baiwa haka.🎸🎷🎷
Komai yaje ya dawo BILKEESU ku za’a tabbatarwa haka🎸
Ganga irin ta girma a miki waccan a mata garwa haka.🎸
BILKEESU za’a baiwa Number komai daren daɗewa duka
Bilkisu gimbiya
BILKEESU sannu mata irin na zamanin ɗebe kewa duka.🎸🎸
Kinsha aradu kinsha yasin, kin samu arziƙi duka.🎸🎷🎸🎷
Kin tsallakema tarkon maƙiya, ga ɗan abin biki haka.🎸
Kinzam sarauniya a cikin mata bar munafuka haka.
Bilkisu gimbiya🎸
Ga zamani da daɗi wannan al’amarinkine duka🎸🎸🎸
Tsarki na zuciya bilkisu ya baki ɗaukaka haka.
Kinsa kara a hanya BILKEESU wazata tsallakane🎸
Komai kina tunani Bilkisu baƙya abu daka haka🎸
Bilkisu gimbiya
Ga ilimi da halin girma, ALLAH ya ɗaukaka haka………🎸🎷🎸🎷🎸🎺🎺🎺🎺1
(Kunema sauran kuji na gaji😂😜)1
“Mawaƙin nan dolene yaci ƙyautar mota”. Oga Aliyu dake bayanmu shida matarsa ya faɗa yana ƴar dariya.
Murmushi naga boss yayi a hankali lokacin da yake kama kafaɗuna yana zaunar da ni a ɗaya daga kujerar guda biyu da aka tanada danmu. Ni kaina waƙar tamin daɗi sosai, hakan ya sakani sakin murmushi da banyi niyyaba. Jay yaɗan lumshe idanu ya sake buɗewa a kanta sannan ya zauna a nashi mazaunin shima.
Babu ɓata lokaci aka fara gudanar da abinda ya tara mutane, an buɗe taro da addu’a kafin ai kiran Ummie tazo ta bada tarihin amarya a taƙaice, Hafiz ma ya bada tarihin ango tare da ɗorawa da shaƙiyancin randa suka fara gane Jawaad ya kamu da son amaryar tasa. Yanda yake faɗar wajen dole ya saka mutane dariya, masu baƙin ciki kuwa suka shiga zuba tsaki suna haɗiyar zuciya. Bily kanta sai da ta murmusa dukda tasan ba haka bane tunda ita dai bai taɓa ce mata yana son nata ba, ɗagowa tai da nufin satar kallonsa sai suka haɗa ido, dan shima kallonta yake ƙasa-ƙasa idanu a narke.
Cike da salo ya wani ɗagemin girarsa ɗaya, maida kaina nai ƙasa zuciyata na motsawa. Ban sake gigin kallon sashen da yakeba nima na maida hankalina ga kallon mawaƙa da suketa baje fasaharsu cikin daɗaɗan waƙoƙi da duk an raira baitocinsune da sunayenmu. Umar m shariff, Ado gwanja, Nura m inuwa, Naziru Ahmad, Hamisu breaker, Isa ayagi, Abdul D one, kai abunfa ba’a magana, ƴan uwa da ƙawaye da abokan ango nata casar rawa, duk yanda mc keta magiya da roƙon amarya da ango su fito filin rawa ya hanani ko motsi, duk wanda ke buƙatar mana liƙi sai daifa yazo nan inda muke zaune ya liƙa mana ɗin, amma ko sau ɗaya bamu shiga filin rawarba.
Lokacin da Anum da Nabeelah suka hawo domin yima su Jay liƙi ba ƙaramin faɗuwa gabansa yayiba, itama ɗin dai sai da ta ɗora hannunta a ƙirji alamar gaban nata faɗuwar ya keyi, dama tun sanda su bilkisu suka shigo saida gabanta ya faɗi, jikinta a sanyaye ta liƙa masa kuɗin shi da bilyn suka sauka ko jin surutun da Nabeelah keyi bataiba. Duk bilkisu na kula da yanayin da boss da Anum ɗin suka shiga, dan harta sauka yana binta da kallone.
Tun ɗazun nake wuwwula idanu ko zanga Yah Anuwar, haka kawai nakeji a raina bana son su haɗu da boss yanzu anan, to bammaga su Abdur-raheem bama. Da hannu na yafito Anum, ta taso zuwa gareni. Cikin magana ƙasa-ƙasa nace, “Ina Yah Anuwar?”. Tace, “Tab aishi bayason bidi’a, da wahala idan zaizo wajen nan, amma bakiga yanda mijinki ke kama da Yah Anuwar ba? Nifa dana kallesa gabana sai ya faɗi wlhy bilkisu”. Murmushi na mata da cewa, “Karki damu zamuyi magana amma ba anan ba”. Kanta ta ɗagamin ta koma wajen zamanta. Ina kallon irin kallon tuhumar da boss kemin nai kamar ban ganiba, dan rashin zuwar Anuwat ɗin yasa naji hankalina ya kwanta.
An buƙaci mu fito domin yanka cake. Ganin bai motsaba nima nai zamana, Ina jiyo fitar guntun tsakinsa alamar bayason yi, ni kaina bason nakeba, dan duk a takure nake matuƙa. Sai da Jabeer yazo yayta roƙonsa da ƙyar ya amince muka miƙe zuwa gaban cake ɗin da yay masifar ƙyau.
Mun yanka cake tamkar yanda tsarin yake, ni na fara cira ɗan guntu da zan saka masa a baki cike da jin matsananciyar kunya, dan da ƙyar na iya control ɗin tsumar da jikina keyi nakai hannuna bakinsa, hannun nawa ya riƙe shima muka saka masa gaba ɗaya wanda na ciroɗin kasancewar ɗan ƙaramine a baki. Ina ƙoƙarin janye hannun ya maidashi cikin bakinsa ya tsotse yatsun biyu dana ɗauki cake ɗin dasu suka ɗan ɓaci kaɗan. tafi hall ɗin ya ɗauka. Jinai tamkar na nutse dan kunya.
Shi kam Maimakon ya ciro ya bani kamar yanda nai masa sai ya lakato ya samin a saman hanci kawai dan wulaƙanci, ban gama fita daga takaicin salon nasaba naji saukar numfashinsa kan fuskata, kafin na sami damar magana ya lashe wanda ya lakatamin ɗin da bakinsa. tafin yanzun kam har yafi na ɗazu, dan yanzu harda waƙar Ali jita aka sake saki ta Bilkisu gimbiya. Ƙasa nai niyyar duƙewa dan kunya yay azamar riƙoni jikinsa, sai kawai na ɗora kaina saman ƙirjinsa ina sakin murmushin jin kunya, shima ya ɗaura hannunsa ɗaya saman bayana yana ɗan bubbugawa.
Da ƙyar mc ya samu hayaniyar ta lafa, zamu koma wajen zamanmu aka dakatar damu. Jabeer ya fara bayani kamar haka….
“To jama’a kowa sai ya buɗe idanu domin dai zamuga wasan manya ne, kunsan daga amaryar har angon jarumaine a filin daga”. Ya nuna bindigu guda biyu dake saman wani table duk an buɗesu, “Kuna dai ganin bindiga guda biyu ajiye ko? To munason ango da amarya su haɗasu cikin minti ɗaya yanda suke, wanda ya fara gamawa yana da ƙyauta ta musamman”.
Ni abinma dariya ya bani, hakan yasa naɗan murmusa, batare da tunanin zanyi nasaraba muka ƙarasa, sai da oga Jabeer ya irga uku sannan duk muka fara ƙoƙarin haɗawar cikin hanzari, ina kammalawa nai saurin ɗagowa na nunasa da bindigar fuskata a ɗaure, dai-dai da shima ya nunani data hannunsa fusakarsa babu wasa. .
Wani irin ihu hall ɗin ya ɗauka da tafi. Murmushi ya saki tare da tanƙwaɓe hannuna bindigar tai ƙasa ya caɓe cikin hannunsa, nai ƙasa da kaina ina murmushin nima dan naji kunya.
Duk da kusan tare muka gama ni aka bama ƙyautar dai dan nina fara nunasa da bindigar, wajen zamanmu muka koma, muna zama mc ya fara sanar da babban saƙo daga ƙannen ango na musamman Princes, sunce a basu wannan filin su kaɗai, dan ga waƙa ta musamman daga garesu da suka tanada domin amarya da ango. tsit hall ɗin yayi kowa ya buɗe kunne yaji ya kuma ga waɗanan ƙannen ango na musman da kowa ke ƙyautata zaton ƴaƴane daga masarauta.
Matasan samari masu ji da jini a jika da wautar ƙuruciya, Abdul-Raheem, Abdur-rahman, Ameen, suka miƙe, dan da gaske Anuwar bai zoba (su ustazu🤐 lol). sunsha ƙyau harsun gaji cikin shadda kalar sararin samaniya, kansu tsaye mazaunin ango da amarya suka nufa, yayinda Hamisu breaker ya miƙe ya fara raira musu waƙar……..
Ashe da rai yake sanki jaruma bada zuciyatai ba, komai ruwa da iska akanki jay baza ya daina kewa ba, tunda dai ya samu zarrar samunki baza ya tanka kowaba, shi baiga mai hararaba, balle ya waiwaya baya. Indai a kankine zaya jure wahalar zuwa garin nisa, da an taɓaki ajirasa danko tilas yazo ya ɗau fansa……….9
(Man kaina ya tsiyaye dole mukoma wajen breaker ya ƙarisa🚶🏻😫)
Breaker na fara raira waka sukuma suka farke ƴan dubu-dubu suka fara zubama Jay da bily liƙi, gaba ɗaya hall ɗin ya yamutse da hayaniya, masu ɗaukar video nayi a waya masu hotuna nayi, masu yima breaker liƙi nayi masu yima ango da amarya dasu Abdur-raheem nayi. Daga hakafa aka tafi casun ƙarshe.
Alhmdllh taro ya tashi lafiya kowa cikin farin ciki, anci ansha kowa yayi haniƙan banda amarya da ango, dan ko ruwa bily batasha a wajen nanba har aka tashi, haka shima Jay ɗin.
★★★★★
Ana tashi aka fice dani daga wajen, ganin mun barsa acan ba’a mota ɗaya zamu tafiba kuma farin ciki ya kamani, dan nazata dai masarauta za’a maidani. Sai dai ana sakani mota naji suna faɗin daga nan gidan amarya za’a nufa, idan anje ana kaita mutane su fito dan ba zama za’aiba dare yayi shabiyu saura.
A take zuciyata ta shiga tsitstsinkewa, hawaye suka fara gudu a kumatuna, dan nama manta da wata kwalliyar fuskata, ALLAH bansan wannan shirin suka shirya ba, duk zatona sai gobe idan ALLAH ya kaimu ganin bamuyi sallama da Ummu ba a masarauta. Tun ina kuka a hankali har ya bayyana fili. Lallashina Mah-mah take tayi da sakemin nasiha ƙasa-ƙasa har muka isa, dazan fita a motarma sai da ta sakani nai addu’a, hakama da zan saka ƙafata a falon, kaina lulluɓe yake da alƙyabba banajin komai sai ƙamshin fenta da ya haɗe dana turare dana sabon kaya ya bada yanayi na musamman.
An miƙa amarya Bilkisu ɗakin mijinta, inda basu wani ɓata lokaciba dan basufi mintuna ashirinba aka saka kowa ya fita ya shiga mota, dama wasu sun wuce gida daga wajen dinner, acewarsu zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu sazo suga gidan amarya da ƙyau.
Cikin mintuna ƙalilan gidan yay tsit, motocin duk sun juya, Aunty Batool kawai aka bari, itama zata ɗan zaunane kar abar Bilkisu ita kaɗai kafin Jay ya shigo. Bayi ta shiga ta haɗa ruwan ɗumi da turaruka masu ƙamshi tazo ta tada bily da har yanzu take kuka. “Kukan ya isa haka amarsu, tashi ki daure ki watsa ruwa dan wannan kukan naki nasan ya ɓata kwalliyar”. Ban musa mataba dan inada buƙatar yin wankan kasancewar a yanayin da nake ciki. Alƙyabar ta taimakamin na cire kawai ta fita ta barni, ban zauna jan jikiba dan tace nai sauri boss zai iya shigowa koda yaushe, bai kuma dace ya iskeni a haka ba. Wanka na shiga nayo sauri-sauri na kimtsa jikina na fito, harta kwashe kayan dana cire ta ajiye min riga da zani na atanfa. Shiryawa nai a gurguje, ina kammala saka kayan tana shigowa. Tace, “Yauwa kinga ai hakan yafi, bara aɗan gyara fuskar”. Bance komaiba nidai taɗan shafamin fauda da lipsgloss a baki kaɗan sai turarurruka data fesheni dasu ta bani babban gyale na yafa tare da sake feshe ɗakin da Air Fresheners masu daɗin ƙamshi.
Inda ta zaunar dani ta matso tana murmushi, “To Amarsu angonki ya shigo, bara naje hasu Aliyu can na jirana zasu saukeni a gida, mu kwana lafiya ALLAH ya huta gajiya”. Hawayen da suka ziraromin na share, nace, “Aunty Batool dan ALLAH ki kwana anan mana, kingafa dare yayi”. Murmushi tayi tana riƙe haɓa, “Inani ina kwana gidan amarya, kinga nayi nan”. Hawaye masu ɗumi ne suka sake gangaromin, na zame na kwanta inayin kayana dan jinake ma duk haushin kowa nakeji, ni banason auren a maidani gidan Dad kawai na cigaba da zamana hankalina kwance.
______________________________
Lokacin da shagali ke gudana a gidan Dad tashin hankali suke fuskanta, dan kuwa dai Salman ne ya gano hotunan biki na yawo a yanar gizo waɗanda ke wajen dinner nata ɗorawa, kunsan mutane da waya a hannu tamkar abu na cizonsune idan suka gani, tun fara dinner ɗin suketa ɗakar hotuna suna ɗorawa wasuma harda videos. Aiko Salman yaci karo da su, shigowa gida yay ya kunna tv dan son ganin wainar da ake toyawa a wajen kasancwwar babu wanda yaje a cikinsu Momy ta hana. Yana zama Aamilah na fitowa, zama tayi suna kallo tare da zagin Bilkisu da Jawaad, hayaniyarsu ta saka Shahudah dake kwance a ɗaki zazzaɓi ya rufe fitowa, aiko tai mummunan gani, dan kuwa dai-dai wajen da Jay ya lashe cake ɗinan daya saka a hancin Bilkisu taci karo dashi, idan ba kallon tsaf kaima wajenba zaka ɗauka kissing ɗin Bilkisu ya keyi. Ƙara kawai ta ƙwalla ta yanke jiki ta faɗi.
Duk kanta sukayi da ihu har Momy Da Dad dake sakkowa daga sama. Girgizawar duniya da sakama Shahudah ruwa taƙi koda motsi, a take hankalinsu ya ƙara kaiwa ƙololuwar tashi suka kwasheta zuwa asibiti likitoci suka rufu a kanta. Har zuwa yanzun dai babu wani bayanin farfaɗowarta kuma………….🤦🏻✍
15
Duk wanda suka kirani jiya ban ɗagaba suyi haƙuri, ngd sosai kuma da addu’oinku gareni na samu lafiya🤦🏻.
24
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭30
Page 39
……………..Tsaye kawai Jawaad daya shigo yay yana kallon Bilkisu da keta faman shashashar kuka, ya ɗan sauke ajiyar zuciya yana girgiza kansa. Sai ya tuna da randa aka kai masa Shahudah, cikin kayan barci ya shiga ya sameta zaune hankalinta a kwance tana buga game a waya, amma ita jiba duk da ba daga ainahin iyayenta aka rabotaba ta kasa barin kuka. Idanunsa ya lumshe a hankali da ƙara sauke ajiyar zuciya. Ya cire hular da babbar rigan, daga shi sai wando da ƴar cikin da iyakarta rafin cinyarsa. Ƙarasawa yay gaban gadon ya zauna kusa da ita, dauriya kawai yake dan kansa ciwo yake masa shima, hannunta ya kamo batare da yayi magana ba.
Gaba na ne ya faɗi dan banji motsin shigowar kowa ba, gyalen dana rufe har fuskata da shi nai saurin janyewa dan naji tsoro, ya murza hannuna dake cikin nashi yana faɗin, “Tashi zaune, K baƙya gajiya da kukane?”. Yay maganar da kamoni sosai ya miƙar. Koda na tashi zaunen ban yarda na kallesa ba, ya sake murza hannuna da har yanzu yake a cikin nashin. Idanuna naɗan rumtse ina ƙoƙarin danne abinda nakeji.
Jay dake kallonta ya girgiza kansa kawai tare da kai hannu ya janye gyalen data rufe fuska “Jiba yanda wannan kukan ya saka miki zazzaɓi, amma bazaki tausayima kankiba ki barsa haka, indai danni akeyi a ya isa haka na yafe”. Kamar jira take yay magana wasu hawayen suka sake zubowa sharrr. Kai Jawaad ya dafe kawai yana lumshe ido da sake buɗewa a kanta, shi kukan natama ya fara bashi dariya, sudai mata a duniya suyi kuka shine jin daɗinsu, ya sauke numfashi kaɗan yana ƙoƙarin danne dariyarsa. “Tashi muje kici abinci kisha magani sai mu dawo ki cigaba da kukan kamar ƙyafi samun ruwan hawayen sosai ai”. Mamakin maganarsa yasa na ɗago na kallesa. Yace, “To miye na kallon nawa? Ba daɗi kukan yake miki ba?”. Ɓata fuska nayi nasa hannu na goge hawayen. Bai sake cewa komaiba ya miƙar dani tsaye, kunyace ta kamani nai azamar ɗaukar gyalena daya zame zan maida, amma sai ya riƙe, yana nunamin hanya alamar muje. Cikin rawar murya nai magana a karo na farko tun shigiwarsa, “To ka bani gyalen”. Matsowa yay gab dani sosai, hakan yasa naja baya idanuna na sake tara ƙwalla, Hannuna kawai ya kama batare da ya bani gyalenba bai kuma cemin komaiba muka fito falo.
Dukda kaina a ƙasa yake nasan falon nan ya haɗu, ga wani ƙamshi mai kwantar da zuciya na tashi a cikinsa. Cikin kujera ya zaunar dani shima ya zauna kusa dani, ya buɗe filet ɗin dake akan centre table ɗin falon, ƙamshi mai daɗi ya daki hancina, kajine guda biyu da suka sami gashi mai ƙyau da tsafta. Yace, “Kici abinci kisha magani jikinki yayi zafi da yawa”. “Nifa na ƙoshi”. Na faɗa murya na rawa. Banza yaymin ya ɗebo naman da hannunsa ya kawo min a baki. matsar da fuskata nai ina girgiza kaina da sake faɗin, “ALLAH da gaske nake na ƙoshi”.
Shiru yay na wasu sakanni baice komaiba yana kallona, kafin ya ajiye wanda ya ɗebo ɗin ya matsoni sosai, Hannunsa kawai naji saman haɓata ya ɗago fuskata, muryarsa babu alamar wasa yace, “Iyayi zakimin danma kinga zan baki kazan ƙyauta, ALLAH garama kici da arziƙi, bar ganin period kikeyi inada hanyoyin da zan sakaki kukan da kike sha’awar yi mai dalili, idan kuma kinji ƙarya kar kici na nuna miki ainahin kalata da baki saniba”. Tunda ya fara maganar idona ya cika da ƙwalla, na fara ƙyaƙyƙyaftasu.
Fuska Jawaad ya haɗe sosai, dan ya kula sai ya buɗe mata wuta zasu dai-daita, a ɗan kausashe yace, “Miemaa!”. Da sauri na ɗago na kallesa jin yanda ya kira sunan a daƙile. Ya tsatstsareni da idanunsa dake tattare da ɗumbin gajiya, duk yanda naso janye nawa ya hanani. “Na miki kama da abin wasanki?”. Kaina na girgiza masa da sauri. “Inhar kika bari waɗanan hawayen suka zubo ALLAH saikin gane kurenki”.
“Dan ALLAH kayi haƙuri, wlhy nima bada sona suke zubowa ba, wani irin tsoro nakeji a raina, saina dinga ganin kamar gilmawar inuwa kuma idanuna, sannan a ƙasan zuciyata wani irin zafi nakeji, kamin addu’a a cikin ruwa”. Kafeta yay kawai da idanu na wasu sakanni, ya ɗan ciza leɓensa na ƙasa yana jawota jikinsa ya rungume. “Ki daure kinji, ki dinga ƙarfafa zuciyarki, insha ALLAHU babu abinda zai faru ALLAH na tare damu da duk al’amuranmu, kefa jarumace na sani, ko kinaso suci galaba a kanki?”. A hankali na girgiza masa kaina hawayen da nake maƙalewa na sauka masa saman ƙirji, nace, “Insha ALLAH zanyi kamar yanda kace”. Yace, “Yauwa my sweet princess, tashi kici abinci ki manta da komai dake zo miki a rai kinji”.
Munkai tsahon mintuna uku a haka kafin ya ɗagoni, addu’ar yaymin a cikin ruwa kamar yanda na buƙata ya bani na sha, a take na fara zufa duk da kuwa falon fanka na aiki, wata nutsuwace ta fara saukarmin a hankali har naji nauyin da kaina yayi ya ragu sosai, sai ajiyar zuciya kawai naketa saukewa. Da kansa ya bani naman, duk da a kunyace nake matuƙa haka na daure naci, sai dai banci da yawaba nace na ƙoshi, amma ƙin saurarena yayi ya cigaba damin ɗurar dole. Daƙyar na samu ya barni, tashi yay babu jimawa ya dawo ɗauke da ɗan box a hannu, ni dai harma na ɗan fara gyangyaɗi dan sosai naji nutsuwa a daga ruɗanin dana fara shiga ɗazun, dama ga yunwa kuma. magani ya bani na sha.
“Tashi kije ki kwanta dare na sake yi”. Kaina dake a ƙasa na ɗaga masa na miƙe, rashin gyalenan a jiki duk jina nake a matuƙar takure.
Jay ya bita da kallo harta shige, ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana jingina da kujerar tare da lumshe idanunsa, tausayi take bashi sosai, kallo ɗaya zakai mata ka fahimci tanada damuwa sosai, yasan zafin rashin iyaye, dan haka yake tausayin duk wanda bai dasu, balle mace ma mai rauni irinta dake zagaye da ruɓaɓɓun dangi gaba ɗaya, garashi dangin uwa na ɗauke masa kewa da damuwa ma. Yanzukam ya samu kwanciyar hankali duk wani motsinta zai kasance a kan idanunsa, a yanzune zai binciko abinda ke binne da iznin ALLAH.
Da wannan tunanin ya tashi ya shiga ɗakinsa, wanka yayi da ruwa mai zafi yay shafa’i da wutiri, maganin shima yasha dan kansa ciwo yake masa sosai dauriya kawai yakeyi.7
STORY CONTINUES BELOW

★★★★★★
Kasancewar maganin da ya bata harda na barci tuni barcin yay awan gaba da ita, kayantane a jikinta bata canjaba, hakan ya saka Jawaad daya shigo tsura mata idanu, komanta ya ƙara canjawa, musamman ma fatarta tai wani irin gogewa sai ƙyalli takeyi, a fuskarta kawai zaka karanci bata da son hayaniya, komai nata tsaka tsakine, hakan yasa ƙyawunta ya kasance mai sanyi, a kallo ɗaya bazaka taɓa ganin sirrin ƙyawunta ba dan batada cika ido irin na Shahudah, yanda take nutsatstsiya haka ƙyawuntama a hankali yake bayyana ga mai kallonta. Tanada kwarjini da cikar haiba na isassun mata masu kamun kai. Yaɗan lumshe ido ya sake buɗewa a kanta, a fili ya furta, ‘Sai jan ajin tsiya da miskilanci ga tsoro kuma ba’. Yay maganar yana nufar akwatinta da aka jiye alamar kayantane a ciki, buɗewa yay, a sama yaci karo da kayan barci har kala uku, doguwar riga da bazata wuce rabin cinyaba, sai riga da wando kala biyu. Riga da wandon ya ɗauka dan sun ɗanfi kauri da mutunci, yasan dai saka matasu akayi daga gani. Zama yay bakin gadon kusa da ita, ya janye bargon data rufama ƙafafunta zuwa ƙugu, zif ɗin rigar ya janye ƙasa bayan ya zame ɗan kwalinta gashinta da yasha gyara yanata ƙamshi ya bayyana.
Cikin barci naji ana ƙoƙarin ciremin kaya, da ƙyar na buɗe idanuna sai naci karo da shi, ai babu shiri na miƙe zaune duk da jikina babu wani ƙarfi, na dafe rigar da har ya ciren hannu guda batare da na yarda mun haɗa ido ba.
Kayan daya ɗakko mata ya ajiye saman cinyarta yana miƙewa, “Ki canja waɗanan kayan dan zasu takuraki sunyi nauyi da kwanciya barci”.
Da kallo kawai na iya bin bayansa ina haɗiye tsoron da saura kaɗan ya hudan zuciya, gaba ɗaya mamaki al’amarinsa ke bani, wai dama haka yake boss ɗinan ashe, yanzu daban farkaba nufinsa shine zai sauyan kayan? Tabɗi wlhy daya gama dani kuwa. Saida yaje ƙofa zai fita sannan ya juyo yana kallona, “Idan kika bari mintunan dana ɗiba miki ya cika baki tashi kin sauya kayan nanba, hummm..” yay maganar murya ƙasa-ƙasa amma daɗan karsashi sannan ya fice.
Kamar nayi kuka haka naji, na kalli kayan barcin da ya ajiyemin tare da ɗagasu, riga ce ƙarama dan ko ɗuwawuna bazata saukaba, hannunta ɗan siriri sai wando da nasan iyakar gwiwa zai tsaya min. Sanin halinsa ya sakani miƙewa ina sauke ajiyar zuciya, dan nasan zaiyi duk abinda yace ɗin, canja kayan nai ina addu’ar ALLAH yasa bazai dawo ba dai. Ina kammalawa na kwanta. sallamarsa ta daki dodon kunnena.
Sosai na waro idanu waje naja bargo na rufe duk jikina, ganin ya zagaya ya kwanta ta ɗayan gefen Cikin in ina nace, “A a..nan za.. ka kwanta?”. Ba tare daya kalleniba yace, “Uhmm”. Baki na tura ina lullumshe idanu, Cikin ɗan haushi-haushi nace “Ammafa kowa ance da ɗakinsa ai”. Ganin ya juyo yana kallona, nai saurin jan bargon na rufe har saman kaina da shi. Murmushin da baiyi niyyar yi bane ya suɓuce masa, ya matso inda take sosai tare da ɗaga bargon ya shiga shima, saka hannu yay ya yaye na saman fuskartata tare da ɗora kansa saman filon data kwanta suna fuskantar juna, tuni jikinta ya fara tsuma, ta kuma rumtse ido kam, fuskarta duk ta bayyana tsoronta a fili. Hannunsa ya ɗora saman kanta ya shafa gashinta dake kwance luf yasha gyara tun daga goshinta har inda yake ɗaure da ribbon, a hankali ya zame ribbon ɗin gashin ya warware. Ƙoƙarin danne dariyar dake neman kufce masa ya keyi. Tsabar yanda take a tsorace har bugun zuciyarta yanaji dan suna gab da junane sosai, hannunta data sakane ta matse ƙirjinta yay musu kantanga. Da biyu ya tura yatsun hannunsa cikin gashin nata da wani irin salo.
“Na shiga uku ni balki”. Ta faɗa babu shiri muryarta na rawa tamkar zata fashe da kuka tare da ware idanunta gaba ɗaya kansa. Jay daya kasa riƙe dariyarsa yanzun kam ya saki lallausan murmushi da ɗora goshinsa saman nata, “Kinsan baki da ƙarfi miyasa kika nemi faɗan?”. “To yi haƙuri dan ALLAH” ta faɗa tana son jan jikinta baya. “Daga baya kenan yarinya” ya bata amsa shima da sake matsota jikinsa sosai ya matse yanda tilas ta janye hannunta data kare ƙirji da shi dan taji numfashinta na neman barin ƙirjinta. Jawaad kam da yasan da biyu ya matsetan dama ya sake sakin murmushi da manna dukan fuskarsa akan tata har labbansa na gogar nasa. Cikin raɗa-raɗa yace, “Nifa idan aka takaloni faɗa banajin bari saina maida raddi”. Hawayen da bily ke maƙalewane suka zubo mata a kumatu, tace, “To ai na baka haƙuri ko”. “Ni kuma sai ban haƙura ba ai hajjaju” yay maganar da manne laɓɓansu yanda babu damar sake magana ma. Duk yanda take mutsu-mutsu ya hanata kowacce irin damar da take buƙata, karan farko a rayuwarta da hakan ta faru da ita, abinda takema kallon ƙazanta idan ta gani a film yau shine ake mata a zahiri, ba kowa ke matanba kuma sai boss, innalillahi…… itakam taga takanta dama haka mutuminnan yake…….?9
STORY CONTINUES BELOW

(To nima dai bansan hakan yakeba bily sai yanzun, duk zatona waliyyine fa kamar yanda Jabeer ya faɗa😂🚴🏼🚴🏼😜).4
★★★★★★★★★
Barcin da suka gaza samunyi da wurine ya ja musu makara, Jay ya janye bilkisu daga jikinsa da ƙyar ya tashi zaune bayan ya kunna fitilar ɗakin, hannunsa dafe da kansa da har yanzu yake jingim alamar ciwon bai saukaba gaba ɗaya, bargon ya gyara mata yana kallon fuskarta da duk hawayen da tai suka bushe, idanunsa yaɗan lumshe yana mai tunanin yanda zasu kwashe da wannan uwar tsoron randa yace mai gaba ɗaya zaiyi, a daren jiyanma ba wani abun kirki yay mataba amma tabi ta ishesa da kuka. Numfashi ya sauke da sauka a gadon. Yasan tilas ne yay wanka kafin yace zaiyi salla, dan haka ya fita zuwa ɗakinsa a gaggauce kafin a tada sallar.
A hankali na buɗe idanuna dake jingim da barci nabi bayansa da kallo harya fice, tunda ya motsa nima na farka, sai dai matsananciyar kunyarsa da nakeji bazata barni na nuna masa na farka ɗinba, abinda ya faru daren jiya ya shiga rige-rigen dawomin a zuciya, hannuna na ɗora saman laɓɓana da sukasha gurza a hannunsa, da wanine ya cemin abinda yay a daren jiya zai iya wlhy sai na ƙaryata, kamar ba boss ɗin nanba na office gwanin hayaƙi da mazurai, sai yaso kaga walwalarsa balle akai ga dariya, yanda yake mara hayaniya a zahiri haka yake a komaima nasa babu hayaniyar, ajiyar zuciya na sauke murmushi na suɓuce mani, tashi nai nima dan ina buƙatar gyara jikina dukda barcin da nakeji na fitar hankali. Gadon na gyara sannan na nufi bayi, wanka nai da ruwa mai zafi ina addu’a a raina ALLAH yasa kar jinin nan ya ɗauke yau, dan nasan a ƙa’idar kwanakin da nakeyi zuwa rana zai ɗauke, dama yanzun kaɗanma na gani a jikin pad ɗin amma bai ɗaukeba, to na tabbata zuwa azhar bazan gansaba. Ina fitowa doguwar riga na zura na koma gadon dan har wani jiri-jiri nake gani saboda barci, yau ko azkar na kasayi, aiko kafin na farga na lula.
Ɓangaren Jawaad ma ana idar da salla da ƙyar ya daure yay azkar ɗin, yana kammalawa ya nufo gida, sama-sama suka gaisa da maigadi ya shigo gidan, yasan Bilkisu barci take tunda dai ba salla zata tashi yiba. Ɗakinsa ya shige, jallabiyar jikinsa kawai ya zare ya haye gadonsa shima sai barci.
_____________________________________
Da ƙyar likitoci suka samu Shahudah ta farfaɗo kusan ƙarfe biyun dare, ba ita kanta dake cikin mawuyacin halinba harsu kansu sunyi matuƙar jigata, gasu Dad duk sunbi sun ruɗa musu asibiti sai kace ran ƴar tasu a hannunsu yake. Aiko koda ta farfaɗo allurar barci kawai sukai mata ta sake komawa, suna fitowa su Momy dake wujiga-wujiga suka yo musu caa da tambaya. A yanzu bazasu iya wani zaman musu bayaniba dan haka sukace kawai ta farfaɗo.
Koba komai su Dad sun sami kwanciyar hankali, dan shi kansa ɗazun harda hawaye yayi, baisan irin ƙaunar da yakema Shahudah ba a rayuwarsa, musamman ma a rin wannan lokacin da wani gagarumin abu mai taɓa zuciya da tashin hankali keson faruwa da ita, sam zuciyarsa bazata iya ɗaukaba gaskiya, bama zai yuwuba, dolene ya nema mafita kafin lokaci ya ƙure. Shahudah sa, ɗiya mafi soyuwa a zuciyarsa, kai ina bazai yuwuba, dolene yasan mai yuwuwa, ya yarda ya rasa komai akan Shahudah wlhy.
Haka suka kwana a asibiti hankalinsu tashe har ALLAH ya wayi gari lafiya.12
Misalin takwas na safe Shahudah ta farfaɗo bakinta na kiran sunan Jawaad, kuka take rurus da roƙon a kira mata Jawaad ya saki Bilkisu inba hakaba zata kashe kanta.
Kasancewar har mama Atika da bama lafiyar ƙafane da itaba tazo asibitin itama tunda safe suka rufu kanta suna lallashi da bata baki akan cewar ai Bilkisu bata tareba wai, kuma ta kwantar da hankalin Jawaad zaizo anjima kaɗan. Sam taƙi sauraren kowa, daga ƙarshe dai dole Doctor ya sake zuwa yay mata allurar barci mai ƙarfi dan jininta yay masifar hawa.1
Doctor ya kalli Dad da Momy dake zaune a gabansa bayan ya gama rubuce-rubuce a takarda. Momy ta sake share hawayen da tun ɗazu ke mata ambaliya a saman kumatunta, “Doctor ka sakamu a duhu, kace muzo kuma kaƙi kace mana komai, mike faruwa ne da yarinyarmu?”. Numfashi Doctor ya saki yana goga biron hannunsa saman gira, kafin ya sake ɗagowa ya kallesu. “Maganar gaskiya bazan ɓoye mukuba yarinyarku na cikin haɗari, jininta ya hau ƙololuwa kasancewar tana ɗaukar abu da girma fiye da kima, wannan shine karo na biyu datai irin faɗuwar da ba’ason duk mai hawan jini irin nata da yi, dan kai tsaye take kaisu ga paralysis, yakamata ku daure ku sama mata abinda ta keso koku ɗauki ɗammarar ƙwantar mata da hankali ta hanyar data dace. sannan akwai wani ciwo da muka gano tana dashi wanda ita kanta da wahala ace tasan a kwashi, dan baikai lokacin da har yanzu zai fara ciwon da zatajisa a jikinta ba”. Cikin matsanancin ruɗani Dad da Mom ke tambayarsa wane ciwo ne?. Kafaɗunsa yaɗan ɗage yana sauke numfashi, “Karku damu bamai ɗaga hankali bane can sosai, domin ko babu ciwon ai sai ALLAH ya ƙaddara mutum zai haihu a duniya dama. Alamu sun nuna yarinyarku ta taɓa cire ciki, bincikenmu da hasashenmu ya nuna mana kuma kamar wata allura tayi yayin zubarwar, a zahiri wannan allurar tana aiki fiye da zato ga mace mai son zubda ciki, dan a ƙanƙanin lokaci take rugurguje ɗan tayin dake mahaifa ta kuma ɓarosa waje, sai dai idan akai rashin sa’a da yanayin jinin mutum takan haifar da matsala a mahaifa daga baya musamman idan anyita babu ƙa’ida, sai bayan wasu shekaru kuma ake gani illar da taima mace, wata macen haihuwace bata sakewa kwata-kwata, wata kuwa ruɓarmata da mahaifar takeyi har sai an cire mata, to Alhmdllh ita duk hakan basu kasance a gareta ba”. Ajiyar zuciyar Dad da Mom suka sauke lokaci guda, Doctor ya cigaba da faɗin, “Sai dai wani ƙari ya fito a bakin mahaifar, a hankali kuma zai rinƙa girma inhar ba’ai mata aiki ba, zaita girmane cikinta na girma kamar mai ciki, idan tsautsayi yasa ya fashe kuma sai ta ringa zubar da ruwa mai wari”. Idanu a waje cike da tsoro su Dad suke kalon Doctor, cikin rawar baki Dad yace, “Likita amma ai kace ana cirewa?”. “ƙwarai Alhaji ana cirewa, sai dai itamafa cirewar nada nata haɗarin, dan zaku iya rasata a dalilin cirewar, idan kuma an dace za’a cire lafiya ta tashi”. Kuka Mom ta fashe dashi iya ƙarfinta, shi kansa Dad dauriya kawai yakeyi, amma kallo ɗaya zakai masa ka fahimci tsagwaron tashin hankalinsa. Murya a sanyaye yace, “Wannan itace kaɗai mafitar Doctor?”. Doctor yace, “Eh to akwai wata mafitar bayan wannan”. Cikin rawar jiki Mom tace, “Wacece Doctor faɗa mana ita dan ALLAH”. “Hajiya mafitar ƙarshe itace shan magani, zamu iya bata maganin da zata shashi a sati sau ɗaya, ya kama a wata guda sau huɗu kenan, sai dai yanada matuƙar tsada, sannan zata cigaba da shansane har illa masha ALLAH, amfanin shansa anan bazai bar wannan ƙarin ya cigaba da girmaba, sannan bazata sake samun cikiba sai abinda ALLAH ya ƙaddara wannan ikonsane da rahamarsa idan yaso, nidai iya hasashena na faɗa sanin gaibu kuma sai ALLAH”.
____________________________________
Knocking ƙofa da akeyine ya saka Jawaad farkawa, guntun tsaki yaja yana buɗe idanunsa akan agogon ɗakin nasa, ƙarfe goma harda mintuna sha bakwai, ya ɗan lumshe idanu ya sake buɗewa kafin ya tashi zaune da ƙyar. Lallai yasha barci sosai ashe. Sauka yay daga gadon ya nufi toilet, fuska ya wanko ya kuskure baki ya fito, jallabiyar da yaje masallaci ya ɗauka ya zira.
A falo suka haɗu da Bilkisu wadda itama bugun ƙofarne ya tasheta, nbatare da ita tama gansaba ta buɗe ƙofar. Nabeelah ce ɗauke da basket.
Murmushi nai mata ina matsawa na bata hanya ta shigo tana ƴar dariya damin shaƙiyanci. “Ta wajena naga duk kinyi wani laushi, ko Yayanmu ya angwanc……….”
Jin tayi shiru tare da jan biriki bata ƙarasaba ya sani maida ƙofar na rufe na juyo. zaune yake saman kujera ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya yay bala’in ɗaure fuska da tsatstsareta da idanunsa masu ban tsoro ga marajin magana. Ba itaba hatta ni saida na tsume, dan a bazata na gansa tunda sanda na wuce ban ganshi a wajenba.
Yaƙi cewa komai kuma yaƙi daina kallonta, a hankali takai ƙasa ta durƙusa kamar wata munafuka, muryarta har rawa take wajen faɗin, “Yayanmu ina kwana”. Bai amsa mataba, sai sake ɗaure fuska da yay yace, “Ƙarasa abinda kika fara”………………✍
3
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.1
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
15
Page 402
……………Sosai Nabeelah ta waro idanunta da suka cika da hawaye tana haɗe hannayenta waje guda alamar roƙo, “ALLAH yayanmu ni babu abinda zan faɗa, dan ALLAH kayi haƙuri”.
“Kinsan ALLAH idan kika bari harna miƙe kanki sai jikinki yay masifar yin tsami”. Yay maganar muryarsa babu alamun wasa. A mamakina sai naga Nabeelah ta fashe da kuka tana ɗanja baya, na kallesa da nufin bashi haƙuri duk da nima a tsoracen nake sai na ga ya miƙe, ai kafinma nace wani abu sai hango Nabeelah nai ta kwasa da gudu ta fice. Yanda yaja birki tare da riƙe ƙugu yana kallontane ya sakani kasa danne dariyata, hannu nasaka na toshe bakina tare da saurin kauda idanuna ganin ya kalloni.
Jawaad yay ƙwafa yanabin Bilkisu da kallo, “Ke kuma dariyan na miye to?”. Kallonsa nai da sauri ina ƙoƙarin haɗiye kayata amma na kasan, dan fuskata kawai zaka kalla kasan dariyar taƙi haɗiyu wa, harar daya ballo mince tasa nai niyyar barin masa falon naje nai dariyata a ciki. Caraf naji an cafkomin hannu da faɗin, “Dariya ko? To bara na huce a kanki”. Tsaf na haɗiye dariyar na koma zare idanu, cikin marairaice fuska nace, “Nifa ba dariya nayiba”. “To mi kikayi?”. Yay maganar da tsatstsareni da mayun idanunsa. Sosai kunya ta lulluɓeni nai ƙasa da kaina ina ɗan waige-waige, nima na Nabeelah nake tsarawa na fece kawai. Kamar ya fahimci abinda nake tsarawa a raina yace, “Kema guduwar zakiyi? Itama ɗin ba ƙyaleta naiba zan sameta har gida sai naci ƙaniyarta na gasa mata baki tunda ita magananniyace”. Murmushin da ban shiryaba ne ya suɓucemin, nace, “Yi haƙuri to niba baƙuwar zafi bace wlhy”. Kafin yace wani abu wayarsa ta shiga ring, kallon wayar duk mukai da mamaki, da alama ma anan ya mantata ta kwana ko?, hannuna dake cikin nasa na janye na ɗakko masa wayar da rabinta ya shige ƙasan filon kujera. Ban tsaya kallon ko wanene ba na kawo masa cikin.
Amsa yayi yana zama, ni kuma na juya na ɗauki basket ɗin da Nabeelah ta kawo wanda ko ba’a faɗaba kasan breakfast ne a ciki. Harna nufi D/table naji ya kirayi sunana, juyowa nai ina amsawa da “Na’am”. Dai-dai zai saka wayar a kunnensa alamar wancan kiran ya katse shi ya sake kira. Yace, “Kawomin tea, karki saka suga da yawa”. Da “to” na amsa kawai na ƙarisa na ajiye basket ɗin saman dani. Kicin ɗin na nufa ina ɗan murmushi da yaba ƙoƙari da sadaukarwa irin ta waɗanan bayin ALLAH, babu dangin iya babu na baba suka kashemin waɗanan kuɗin? Ba ƙaramin mutsuwar tsaye naiba da ganin yanda kicin ɗinan yay mugu-mugun haɗuwa, ni balki ɗiyar baba makaho ce da wannan gidan matsayin matar cikinsa? Sai kawai naji ƙwalla sun cikamin idanu, na shiga maimaita kalomin Alhmdllh a zuciyata ina hawayen zuci. Fasalta muku yanda kicin ɗinan yake ai ɓata lokacine, abin mamaki da al’ajab harda kayan abinci da malam bahaushe ke kira da gara, dai-dai da magi wannan sakarai an ajiye min shi. Sai dai kuma babu kayan tea ɗin da yace na haɗa masa, iya dubana banga koda lipton ba sai kayan ƙamshi kawai da abinda ba a rasaba, komawa nai da niyyar faɗa masa ban ganiba amma na iske yana waya da ransa a ɓace. “Uncle Please ka ƙyalesu ni babu abinda zanzo na musu, ina ƙoƙarin danne duk abinda suke son takalata dashi kawai amma na kula neman kaini maƙura sukeyi akan shirmensu”. Yaɗanyi shiru alamar saurare, hakan yasa na juya zan koma dan na bashi damar gamawa amma sai naji takunsa a bayana, baimin maganaba yazo ya wuceni, ganin hakan yasani bin bayansa, drawer saitin fridge ya buɗe ya nunamin. Kaina na jinjina masa na ida shiga ciki shi kuma ya fice yana cigaba da wayarsa. Bani da matsala da kayan ƙamshi dan duk gasunan a robobi harma da ganyan shayi masu daɗi da Umm-Aban dama tace zata haɗa min saboda ta lura inason shayi. Tukunya na ciro da dama an fiddata a kwalinta na ɗauraye na zuba duk abinda zan buƙata na ɗora saman gas da dama an haɗashi shima. Komawa nai na ɗauki plate da flask da kofi na ɗaurayesu tsaf, cikin mintuna ƙalilan na kammala na fito da komai na ajiye a dani ɗin, sannan na koma na ɗakko tea ɗin dana haɗa a kofi na ɗaura saman ƙaramin tire na kai masa falon dan har yanzu wayar yakeyi. Yanda yake kallona harna ajiye tiren a centre table duk sai naji na takura, nuni yaymin da in bashi, ɗauka nai na miƙa masa, ya ɗan lumshemin idanu alamar “thanks”. Bance komaiba nabar wajen dan sonake nai wanka.
Saida na gyara gadon yay tsaf sannan na shiga wankan, wanka nai haɗe da wankan tsarki dan mai jar motama ya ɗauke tunkan azhar ɗin da nake hasashen, zaton babu mai shigominne ya sakani fitowa daga ni sai guntun towel ga gashi a jiƙe, sai dai inata ƙoƙarin tsanesa da ƙaramin towel dake a hannuna. Ina ƙarasawa gaban mirror yana shigowa da sallama ciki-ciki alamar ransa a ɓace yake har yanzun, saida naji tamkar na ƙwala ihu, na ɗan wawwaiga banga wani abu dazan iya ja na rufe jikina da shiba, haƙura nai kawai na ɗan ɗago na kallesa cikin dauriya ina faɗin, “Nazo na baka abincin ɗinne?”. Shirun da naji yayi bai amsaba yasa na ɗago kaina na dubesa, idanunsa nakan gashina ko ƙyaftawa bayayi. Sake maimaita masa tambayar nayi. Ya janye idonun nasa da juyawa zai fita yana faɗin, “Ki gama nima zanyi wankan ne”. Binsa kawai nayi da kallo dan na lura ransa a ɓace yake, ‘Komi akai masa kuma?’ na faɗa a fili batare da inada mai bani amsata ba. Gudun karya sake shigomin yasa nai shiri a gaggauce cikin sket da riga na shadda orange color. Ni kaina nasan sunyimin ƙyau dan kamar an haliccesune a jikina sunmin ɗam dan telan ya iya ɗinki, kaina nakeson busarwa amma abin haushi babu wuta, a haka na gyarashi bayan na tsanesa sosai babu ruwa, ɗauresa nai da tunanin ƙila su kawo wutar anjima tunda naga anguwar kamar suna samunta sosai. Bawata kwalliya nai da yawaba amma fuskata tayi fayau, na saka ƙaramar sarka sannan na feshe jikina da turare sosai, kowa ya ganni yaga amarya da gaske, farin gyale na ɗauka shima na saka turare sannan na yafa na fito falon. Gidan tsaf yake babu wani datti, hakan yasa kawai na ɗauki fresheners da turare mai ƙamshi haɗin gida na fesa iya falon nan kawai. Ina cikin fesawar ya fito.
Jin Motsinsa a bayana ya sakani waigawa, kwalliyar tasa ta sakani shagala a kallonsa batare dana fargaba, shaddace ƴar ubansu golden color ya saka, sai maiƙo take da ɗaukar ido, ta samu nutsatstsen ɗinki na zamani da ya fiddo cikar zatinsa mai tabbatar dashi jinin hausawan usul harda su hula……
Saukar iskar da naji a cikin idanuna da ƙamshi Mouth freshener ɗin da ya saka ya sani dawowa hayyacina daga sakin layin da nayi, nai ƙasa da kaina dan naji kunya.
“Gulmammiya kinaso kina kaiwa kasuwa, na miki ƙyaune?”.
Ɗan kallonsa nai na juya ƙeya nace, “Kaɗan”. Murmushi ya saki har inajin sautinsa, ya ɗaura hannunsa saman haɓata ya maido fuskata inda yake, “In har da gaske kike ki kaleni cikin ido kice kaɗan nai ƙyau”. Hannu nasa na rufe fusa da sake juya masa baya ina murmushi. “Baki da gaskiya kenan”. Yay maganar kusa da kunnena yana zame gyalen dana yafa. “Malama niba surukinki bane ai, muje kiga gidanki”.
Shine yaymin rakkiya lungu da saƙo na cikin gidan har ɗakinsa da harabar gidan, gaba ɗaya gidan ya canjamin tamkar ba wanda na taɓa zuwa ɗin nanba, an gyarashi sosai ya canja kamanni. Sai da muka gama zagaye ko ina muka yada zango a wajen cin abinci. Nidai kasa sakewa nai naci saboda yanda yay mugun tsatstsareni da idanu, duk sanda zan ɗago sai naga idonsa a kaina. Da dai na gaji saina kumbura masa fuska, “Nifa wlhy ba television bace ba”. Bakinsa ya taɓe baice dani komaiba bai kuma bar kallon nawaba har muka gama. Ɗakinsa ya koma nikuma na tattarr wajen, na fito masa da abincin maigadi da tunkan mu fara cin namu ya sakani na zuba shima ya fito, agogonsa da links ya miƙomin tare da miƙamin hannunsa. Dukda inajin kunya haka na saka masa links ɗin sannan na saka masa agogon. “Thanks” ya faɗa a hankali yana ɗagemin gira ɗaya.
Kafin nace wani abu maigadi ya doka sallama a ƙofa, kallon ƙofar mukai gaba ɗaya amma shi ya amsa masa, ya amshi kular hannuna tare da nufar ƙofar ya buɗe.
Maigadi ya gaidasa da faɗin, “Alhaji kanada baƙone”. Da ɗan mamaki Jawaad yace, “baƙo kuma malam gambo?”. “Eh Alhaji, harzan masa ƙaryar baka tashiba saina fahimci amatse yake da son ganinka gaskiya, kuma kamar baƙon mai muhimmanci ne”. “Okey, to ga abincinka ina zuwa”. Amsar kular yay dayi godiya ya koma, Jay kuma ya maida ƙofar ya rufe ya dawo inda yabar Bily tsaye tana kallonsu. Wuceta yay ya ɗauka key ɗin motar dake kan centre table, “Bara naje na gaida Alhaji Babba daga nan na leƙa asibi wai Hudah aka kwantar”. “Ya salam” na faɗa cikin damuwa, “Miya sameta kuma? Dan ALLAH kaje dani”. Kaɗan ya kalleni ya ɗauke kansa, “Kimata addu’a daga nan ya isa, kokin taɓa ganin amarya ta fita”. Cikin shagwaɓar da bansan inada itaba nace, “Toni tsoro nakeji wlhy”. “Tsoro kuma?” ya faɗa yana kallona. kaina na ɗaga masa batare dana yarda mun haɗa ido ba. Jin yaƙi magana yasa na sake kallonsa, sai naga niɗin yake kallo ashe shima. “ALLAH na kula kinma rainani” yay maganar yana matsoni, baya nai saurin ja, amma duk da haka saida ya riƙoni. Cikin magana raɗa-raɗa yace, “Ke komai abin tsorone a wajenki halan?”. Nace, “To inason naje naga aunty Shahudah ne”. “Uhhyim shine zakimin ƙarya? to babu inda zakije, ki jira ƙawayenki na nan zuwa zan dawo bazan jimaba dan zanyi magana da ku”. Saurin kallonsa nai da mamaki nace, “Su Ummie?”. Kansa ya ɗagamin. “Miya faru?”. “dan na dawo zakiji ai, ana jirana yanzun”. Ya ƙare maganar da ɗaura bakinsa saman nawa babu zato. ‘Ya salam’ na ambata a zuciyata tsigar jikina na tashi ga yanayin da nakeji na neman tasomin dukda dai yanzuma da sauƙi sosai ba kamar da ba. Sai da yaja kusan minti biyu kafin ya saki bakin ya sumbaci goshina. “Saina dawo”. Kaina kawai na jinjina masa dan na kasa kallonsa. A hankali na furta, ”ALLAH ya tsare”. Inajin yana murmushi. Nidai ban kallesanba har ya fice.
Sassanyar ajiyar zuciya na sauke tare zubewa a kujera daɓar na dafe kaina, wlhy abun mamaki yake ban, boss fa! Kai rayuwa bata rabo da abubuwan al’ajabi. Naja kusan mintuna biyar a haka kafin na miƙe naje ɗakinsa dan na gyara. Sosai ɗakin yake ƙamshin turarensa daya fesa yanzun, tsaf na gyarashi na saka fresheners sannan na koma kicin na ɗauraye kwankina da mukaci abinci shima naɗan gyara abinda bai minba.+
STORY CONTINUES BELOW

Koda Jawaad ya fito sai ya iske baƙonsa cikin rumfar bunun dake harabar gidan maigadi ya kawosa, ƙarasawa yay yana faɗin, “Ai bammayi tunanin kai bane Munkaila”. Baƙo mai suna Munkaila daya miƙe domin girmamawa ga Jay yay murmushi, “Nine wlhy Oga barka da fitowa”. “Yauwa sannunka da zuwa” Jay ya faɗa yana zama tare da masa nuni daya zauna shima. Cikin girmamawa Munkaila ya gaishe da Jay kasancewarsa ogansa, file ɗin gabansa ya miƙa masa yana faɗin, “Oga dukkan abinda kake buƙata gashi, harma da abinda bakaceba dukna haɗo maka”. Kai Jay ya jinjina masa da faɗi, “Sannu da ƙoƙari” yana buɗe file ɗin. Da hotuna ya fara cin karo waɗanda sukai masifar ɗaure kansa dan harda Alhaji baba tare da mata biyu wadda ɗaya a ciki takasance kakarsace mahaifiyar su Ummah da shima a hoto ya santa, kallon Munkaila yay kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya maida file ɗin ya rufe.
Munkaila yace, “Oga akwai matsala ne?”. Kai Jay ya girgiza masa, “Babu matsalan komai, yaya maganar wancan aikin?”. “Shima ina gab da kammalawa oga, saboda naga ka matsu da wannan ma shiyyasa na dakata da wancan”. “Shikenan kayi ƙoƙari shima ka haɗamin shi a satin nan, ga wannan ka saka mai nima nayi aljihun nawa yay ƙasa”. Godiya Munkaila yayi sosai sannan suka fito a rumfar. Jay ya shiga mota shikuma ya fice dan mashin ɗinsa na daga waje bai shigo da shiba.
★★★★★
Fitar jawad babu jimawa su Ummie suka isa gidan amarya Bilkisu, Ummie, Zuhrah, Rebecca, Nazifa. Duk da jiya suka rabu da juna tuni suka haukace da ihun murnar ganin juna, suka saka bily tsakkiya da tsokana kala-kala, tun tana musu shiru dai harta koma ramawa itama dan taga shirun nata bazai sa su barta ba.
_________________________
Asibiti yay niyyar fara zuwa saboda Uncle Sulaiman daya tilasta masa yaje, to amma wannan bayanan da Munkaila ya kawo masa yanzun sun ruguza komai, burinsa kawai ya dangane da gidan Alhaji Babba. A waje yay fakin motarsa ya shiga shi kaɗai, Alhaji babba na zaune a falo hannunsa riƙe da Jarida Jay ya shiga da sallama. Ɗagowa yay yana kallonsa fuska ɗauke da murmushi, cikin tsokana yace, “A lallai wannan angon da gaske bahausa ya aura, ashe ba gidan jiya ya komaba”. Jay dake murmushi ya girgiza kai kawai yana zama, “Wannan itace tarbar da zakamin ma na baro matata na taho ganinka da farar safiyar nan”. Alhaji babba yay dariya irin tasu ta manya yana faɗin, “Ja’iri kenan bakifa ya buɗe”. Gaidashi Jay yayi yana murmushin tsokanar da kakan nasa ke masa. Sai da suka kammala gaisuwar da tambayar lafiyar juna da amarya Bilkisu kafin jay ya buɗe file ɗin da Munkaila ya kawo masa, hotunan ciki ya fiddo gaba ɗaya ya miƙama Alhaji Babba shi kuma ya maida hankali ga duba bayanan cikin file ɗin.
“Sa’adatu! kuma?”. Alhaji babba ya faɗa da alamun bazata. Kallonsa Jay yayi amma baice komaiba. Alhaji babba yace, “Jawaad kana nufin matarka nada alaƙa da wannan ta hoton?”. Zama Jawaad ya gyara sosai yana maida dukkan hankalinsa ga kakan nasa, “Baba abinda bincike ya nuna min kenan, sai dai nima kaina a kulle yake musamman da ganin hotonka a tsakkiyar mata biyu bayan mata ɗaya nasan kanada ita kafin Mama Maryam”. Shiru Alhaji babba yay na wasu mintuna kafin ya sauke ajiyar zuciya, yace, “minene sunan mahaifin nata?”. “Adam makaho” Jay ya bashi amsa a taƙaice. Nanma shiru Alhaji babba yay na wani ɗan lokaci yanata faman jinjina kai da murmushi a fuskarsa kafin yace, “Abin akwai ɗaure kai da ban al’ajabi”. Jawaad yace, “Miyasa zai ɗaure maka kai bayan na fahimci kasan wani abu”. Murmushi Alhaji babba yayi mai ciwo da sake maida hankalinsa ga hotunan guda biyar, ɗaya shine da mata biyu a jiki sai jaririn yaro da alamu suka nuna ranar sunansa aka ɗauki hoton ma ƙila, ɗaya kuma matane da miji matar gurguwa sai mijin da alamu suka nuna makaho ne, sai hoto na uku jaririyace nannaɗe cikin farin showal da gani kaga sabuwar haihuwa, hoto na huɗu, mata da minjin nan ne da jaririyar, na ƙarshema dai mata da mijinne sai bilkisu a tsakkiyarsu da bazata wuce shekaru goma sha biyarba. Ya ajiye hotunan yana kallon Jawaad da ƙyau. “Akwai abinda ku baku saniba Jawaad, mahaifiyarka cema kawai zata iya sanin wani abu itama ba duka ba dan a labari ta sani. Ba Amina da Maryam kawai na taɓa aureba, na taɓa auren wata matar mai suna Sa’adatu. Kafin aurena da Amina Sa’adatu itace yarinyar da naso aura dan itace muke soyayya amma iyayena suka ƙi, bakomai ne ya sakasu ƙinba sai kasancewar Sa’adatu batajin magana, duk da yarinyace da bata wuce shekaru goma sha biyarba a lokacin mutane kan jefeta da kalmar ƙarancin tarbiyya, Sa’adatu ta tashi a gidansu bata da uwa a hannun kakarta ta tashi, hakan yasa ta tashi sangartacciya da batajin ƙwaɓa, a dalilin ɗan karatun da aka sakata na boko wanda a wancan lokacin iyakamu maza kawai keyinsa yasa idanunta buɗewa dan ita kaɗaice mace a cikinmu, Sa’adatu ji take tafi kowa a ƴammatan yankinmu dama gata ƴar gata kuma babanta shine maigari, ALLAH ya jarabceni da sonta fiye da yanda kake tunani har takai naima iyayena maganar aurenta. Amma sai mahaiyata tace sam batasan wannan zanceba tama rigada tamin mata Amina, na ɗaga hankalina matuƙa a lokacin amma dole na haƙura muka rabu da Sa’a ina kuka tanayi. Hakan ya zafi kakarta har tayi alwashin sai nayi nadamar yaudarar jikarta da nayi. Babu wanda ya ɗauki alwashinta wani abu aka ɗauramin aure da Amina ta tare. Banason Amina amma ita tana sona kuma mace ce mai haƙuri da kawaici, a zamanmu tasha wahala kafin na ɗan fara fuskantarta, aurenmu da Amina yakai shekara shida amma bata taɓa ko ɓariba, a wancan lokacin dan mace takai shekara goma ma bata haihuba babu mai damuwa da hakan balle ya zama abin magana shiyyasa nima ban taɓa damuwaba. Zuwa lokacin Sa’a itama tayi aure amma ba a wannan garin namu ba, wani ɗan uwanta mai kuɗi aka aura mata, sai dai kuma hankalinta na kaina dan haka shekararta uku ta kashe auren ta fito da yarinyarta guda safara’u, a lokacinfa na tsaya kai da fata saina auri Sa’a dan sonta na nan daram a raina. Zakasha mamaki idan nace maka Amina itace taita kai kawo ga iyayena har mahaifiyata ta amince na auri Sa’a. A farkon shigowar Sa’a gidana ta kwantar da kanta tanama Amina biyayya kamar gaske, amma tunda muka wayi gari ta samu ciki sai abubuwa suka fara canja salo, raini da wulaƙanci babu wanda take ragewa bataima Amina shi ba a bayan idona, amma a gabana babu abinda ya sauya na ladabin da take mata da. Sam ban fahimci zaman kisan mummuƙen da akeyi a gidana ba dan Amina ko a fuska bata taɓa nunaminba har ALLAH ya sauki Sa’a lafiya ta haifi ɗa namiji wanda yaci sunan kakana Adamu. Bayan haihuwar Adamu ne na fara fuskantar akwai matsala a zaman nasu, dan wataran na shigo a bazata na iske Sa’a nama Amina gorin haihuwa. Ranar nayi tamkar bansan Sa’a ba saboda biji-biji nai mata tare da dogon gargaɗi na saki ɗaya. Kamar Sa’a ta nutsu bayan wani lokaci saita dawo da halinta na rashin arziƙi har ƙawaye take kawowa suna haɗuwa cin zarafin Amina. Cikin amincin ALLAH Sa’a bata yaye Adamu ba saiga Amina da ciki. Munyi murna sosai fiye da zato, ganin Amina itama ta samu cikin da ake mata gori sai Sa’a ta sake sabon salon iskanci, Amina dai bata kulata dan ta bama banza ajiyartane. Cikin ikon ALLAH itama cikinta yakai haihuwa ta haifi mace wadda taci suna Bilkisu (mamanka kenan) dariya Sa’a taitayi alokacin da faɗin ai dai itace a sama tunda namiji gareta, Amina dai bata kulatan, bata yaye Bilkisu ba sai ga wani ciki, Sa’a kuma shiru, hankalin Sa’a ya kuma tashi ainun da wannan ciki na Amina harta sake haihuwa bata barta ta hutaba, a wannan haihuwarma dai mace ta samu itace Wasila (Ummah babba). dukda Sa’a ta nuna bata damuba tunda Amina mace ta sake haihuwa saita kasa daurewa, tashiga ƙananun magana Amina tai mata asiri haihuwarta ta tsaya, tun ina tsawatarwa har al’amari yafi ƙarfina na saki Sa’a saki biyu ya zama uku dan al’amarinta ya isheni. Wannan saki yama dangina daɗi yama nata zafi dan dangina dama babu mai sonta sai ƙalilan a cikinsu. Nayi ƙoƙarin na amshi Adamu amma kakar Sa’a tace ban isaba, duk hanyar data dace nabi suka hanani ɗana, acewarsu kishiya bazata riƙe musu yaroba wataran ta kashesa. Rabuwarmu da Sa’a da shekara guda Amina ta sake haihuwar mace dai again, wadda taci sunan Rahamah (ɗiyar Alhaji babba wadda ta rasu) haihuwar Rahama babu jimawa kakar Sa’a ta rasu, alokacinne na shirya amshe yarona dan banaso ya tashi da kalar tarbiyyar gidansu, sai dai a randa naje nai magana da mahaifinta washe gari aka nema Sa’a aka rasa ta gudu da Adamu. Neman duniya anyi babu wanda yaga Sa’a, munɗauki tsahon lokaci muna nemanta amma babu Sa’a babu labarinta. Har kuma ALLAH yayma Amina rasuwa ta barni da ƴaƴa huɗu duk mata ban sakejin ko labarin Sa’a ba balle yarona, kullum yana a raina, dan harda Maryam mun taɓa yin labarinsa”.
Ajiyar zuciya Jawaad ya sauke yana mai jinjina al’amarin a ransa, yace, “to Amma baba miya nisantaka da danginta harmu bamu taɓa saninsu ba ballema shi labarin Uncle ɗin? Tunda gashi dai alamu sun nuna shi Uncle ɗin ya dawo gida har yay aurema kenan ya haifi Miemaa”.
“Kasan na faɗa maka dama akwai damuwa tun hanani aurenta da akai a farko, sannan koda mukai aure danginta sunajin zafin mahaifiyata dani kaina, badanma sunso Sa’a ta dawo ta aureni ba, bayan guduwarta kuma sai abubuwa suka sake ƙwaɓewa suka ɗaura laifin akan Amina ce tai mata kurciya tabar gari saboda ita ƴaƴanta matane Adamu kuma namijine, dalilin wannan sheɗancin nasu nema yasa nayo nesa dasu na dawo nan dan lokacin garin bai haɗe ya zama babba ba gaba ɗaya kamar yanzun, ahankali abubuwa sukaita canjawa dangi makusanta sunata ƙarewa, shiyyasa kusancin namu ya sake taɓarɓarewa ma baki ɗaya tunda wanda za’aiyi dominsa babu shi tare dasu”.
Kai kawai Jawaad ke iya jinjinawa amma ya kasa magana, Alhaji babba ya katse shirun nasu da faɗin, “Duk da na daɗe banga Adamu ba tun yana yaro amma ƴarsa sai ta ɗakko kamanin Rahamah sosai musamman tana yarinya fiye da nasa kamannin, dan ni randa na farama ganinta a asibiti kamannin Rahamah na gani tattare da ita bana Adamu kawai ba, hikimar UBANGIJI kenan mai tsara yanda yaso a lokacin da yaso, Jawaad yanzu kenan Adamu baya raye?”. Cikin damuwa Jay ya jinjinama Alhaji babba kai, “Ta faɗamin mahaifinta ya rasu bayan rasuwar mamanta kusan shekara bakwai kenan ana cikin na takwas, kuma a yanda bayanai suka nunama kenan anan ɗin ya rasu, to amma abinda yama ɗauremin kai sufa danginsa ma suna nuna tamkar bashi da wata alaƙa da ɗiyar tasane fa, wannanne dalilin daya raunana zumincinsu ya dawo gefe yana rayuwarsa shi da matarsa kawai da yarinyar, kuma ko bayan rasuwarsa abinda yasa sukai watsi da ita kenan sai dai batasaniba ita”.
“Jawaad ban gane basu da alaƙa ba, duk wanda ya kalli matarka aiko yaga jinin Adamu ai”. “Gaskiya ne Baba, a hoton dai kam daka gani kasan jinsa ce, nima inason zuwa da kaina garesu naji miyasa suke nisantashi da abinda alamomi suka nuna nasa ne?”. “Bakai kaɗai zakajeba Jawaad, tare zamuje ai, dan nima ina buƙatar amsoshi da yawa a garesun”. Sun daɗe suna tattaunawa akan batun kafin jay yayma Alhaji babb sallama ya tafi asibiti.
★★★★★★
Tunda ya shiga asibitin sukai masa caa da idanu, shiko ya fuske abinsa fuska a ɗaure ya gaidasu da tambayar jikin Shahudah, kafin ya shiga ya dubata tana barci har yanzun, dan data farka suke sake mata wata allurar barcin tunda taƙi kwantar da hankalinta ta saurari kowa, ta dage sai an kira mata Jay.
fitowa yay daga ɗakin ya dawo wajensu da nufin yimusu sallama ya kama gabansa, amma sai mama Atika ta dubesa cikin gadara fuska babu wasa tace, “Mun gama magana da ƙannen ubanka yau bayan sallar azhar za’a maida aurenka da Sabira, kuma gobe idan ALLAH ya kaimu zata tare koda ba’a sallameta daga asibitin ba”.
Wani lallausan murmushi Jay ya saki da ya bama kowa al’ajab da mamaki, dan ba murmushin sukai tunanin gani daga garesa ba. Ya kalli mama Atika da ƙyau yana tura hannayensa cikin aljihun wandon shaddarsa da gyara tsaiwa yace, “Shi kuma mijinta yaya zakuyi dashi”. Yay maganar da maida kallonsa ga ƙofar shigowa.
Gaba ɗaya suka maida kallonsu ga ƙofar inda ɗan-fir’auna ke tsaye akan ƙafafunsa ya warke sarai sai tabbunan raunikan da yaji waɗanda basu gama bajewa da ƙyauba………….✍8
(Kana basu pepe da ginger ɗan bilkisu da Abdul-Aziz mijin bilkisu🤣😂🚴🏼)31
______________________
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
19
Page 41
……………..A firgice Mama Atika, Dad, Mom, Uncle Nasir, Uncle Uwaisu, Aamilah, Salman duk suka miƙe baki hangame. Uncle Sulaiman da Uncle Sadiq da basusan komaiba illa cewar ɗan fir’auna ya mutu suka bisu da kallo dansu basusan ɗan fir’aunan ba a zahiri har yanzun. Cikin tsananin firgici da suɓutar baki Mama Atika tace, “Nasiru ba kunce sheɗanin nan ya mutu ba wai?”. Rasa mai bata amsa akai a cikinsu.
Ƙyalƙyalewa da dariya ɗan-fir’auna yay irin ta asalin tsagerun nan da suka gama gawurta a fitsara, ya nuna Mama Atika yana tsuke fuskar tamkar ba shine ya gama dariyar ba, “Ke dai tsohuwarnan anyi ƴar buƙulu, to idanma na mutu ban kwashi garaba ashe kanwa na kawo duniya, koda yake ashefa shirya kasheni akai ko? To anyi tabanza dan shegen taurin raine dani zanyi dogon zamani fiye da naki, a nunamin inda matata take malamai”. Jikin Aamilah na rawa tace, “Brother ga shi nan”. Harara ya zabga mata, “K dan tsohuwarki waye Brother ɗin? Yayah zaki ringa cemin dan gyatuminki hausa zakimin, kujimin faratun banza mai suffar yahudawan farkon ƙarni”. “Kayi haƙuri dan ALLAH yaya bazan sakeba” tai magana tana komawa bayan Jay da yay kunnen uwar shegu dasu kamar baisan wainar da ake toyawaba ta maƙale, Jay wayama yake latsawa abinsa hankali kwance kamar baya wajen. Dariya ɗan-fir’auna ya sake kecewa da ita yana faɗin, “Kaji bayani, da kikace ke tsagerace? Hegiya nifa bar ganinki ƙanwar matata billahillazi jinake kamarfa nai miki eyane dan zaki bada kala a garin maji daɗi. Amma kinci arziƙin musulunci ba’a wannan haɗin. Oga bara na shige daga ciki duk da fa inajin nauyinka fuska kawai zanyi aradun ALLAH na siɗaɗa”. Yay maganar da wani ɗora hannu ɗaya kan ɗaya irin salon nan na gaisuwar gayu ga na gaba dasu. (ALLAH ya daidaita sahunka akan lokaci habibullah😂🤣)
Jawaad da baiko ɗagoba ya jinjina masa kai kawai yana cigaba da aikin latsa wayarsa. Sai da ɗan fir’auna ya shige ɗakin da Shahudah ke kwance sannan Jay ya ɗago yana kallon Dad da yay sagade kamar wani gunkin hanya yana kallon ƙofar, firgigit ya dawo hayyacinsa saboda bugo ƙofar da ɗan-fir’auna yayi da masifar ƙarfi.
Inda Jay yake ya nufa da sauri-sauri yana baza babbar riga, Muryarsa da zafi ya furta, “Inason muyi magana”. Kallonsa kawai Jay yayi baice komaiba, sai dai fuskarsa shima a haɗen take, da ya kai maƙurar da ayanzu zai ɗauki matakin da bai ɗaukaba ada akan kowa. Guntun Murmushi yay da miƙewa yana ɗan kallonsu Uncle Nasir da suka zubo musu idanu. Rai a ɓace Dady yace, “Jawaad!!….” saurin ɗaga masa hannu Jay yayi batare daya kallesa ba. “Karkai saurin harzuƙa, muje waje muyi maganar”. Ɗauke kai Dady yayi kamar bazai sake tankawa ba sai kuma miya tuna oho ya nufi ƙofar fita yana jiyo kukan Momy dake sukar masa zuciya. Tashi Jay yay shima ya fice baiko kalli inda ƴan gidan nasu sukeba balle ya nuna yaji ihun kukan Momy dana Mama Atika.
A can gefe inda babu mutane ya hango Dad nata kai kawo ransa a ƙololuwar ɓace, Jay yay ɗan murmushi ya ƙarisa. Kallonsa Dad yay ya ɗauke kansa, “Jawaad!! Tun muna ƴar kunyar juna ka saka wannan ɗan iskan yaron ya sakarmin yarinya ta”. Murmushi Jay yayi da tura hannunsa ɗaya aljihu ɗaya kuma ya shafi kumatunsa da gashin saje ke kwance kaɗan saboda yana askewa, “Miyasa kukai tunanin kashesa ne zai baku mafita domin farin cikin ƴarku?. Irin wannan raɗaɗin da kakeji a yanzun, ita kuka shiryama taji mafiyisa Dad, Miye dalilinku na janta jikinku bayan baƙwa buƙatar ta raɓu jininku?……..”
Dady ya kallesa da ɓacin rai sosai ya katsesa da faɗin, “Ya ina maka magana akan Mamana kanamin wata banzar magana taka mara tushe?”. Haɗe fuska Jawaad yayi da tura ɗayan hannunsa aljihu cikin ƙoƙarin danne nasa fushin yace, “Banason mu bama juna wahala, dan inhar muka kai ga haka komaima zan bankaɗo babu ruwana, dan haka mu tsaya iya haka ɗin kamar zaifi sauƙi. Batun Hudah na riga na gama da wannan matsalar yanzu tsakanin kune ku da sirikinku. Lokaci yayi da zaku nuna gajiyawar da baƙwaso a gareta na bakomai zaku iya bata ba, ALLAH shike bada komai ga wanda yaso a lokacin da yaso ba mutum mai barci, mai mutuwa, mai mantuwa ba. Koda yake, wannan bashi bane matsalata. Minene Ya kai Qaseem China kuma?!”.
“Kai Jawaad!! Tsagerancin naka da su Alhaji Nasiru ke faɗa har yazo kaina nima kenan? Minene matsalarka ko alaƙarka kuma da barin Qaseem ƙasar nan?, Qaseem fa ɗanane, babu kuma wanda ya isa ya sakani koya hanani a kansa, itama bilkisun ba tsoro yasa na bar maka itaba dan inada ikon hanaka auren nata tunda ɗiyar ƴar uwa tace, a hannuna kuma ka ganta. Niba sa’an yinka bane, ka kama kanka kajiki”. Ya ƙare maganar da fara tafiya zai bar wajen.
Jay dake binsa da kallo yay murmushi, “Tabbas kanada iko da ita fiyema da hakan, kuma har gobe ita kallon uba take maka dan ta baka dukkan yarda kai da ahalinka, babu wani laifinku da take kallo laifi sai dai kuskure. Haka take komai nata irin na masu ƙyaƙyƙyawar zuciya ne, tana ƙyautatama kowa zato musamman wanda ya nuna tausayinta saboda a irin rayuwar data tsinci kanta ciki, Dady ka daina tunanin har yanzu al’amarin a rufe yake, na tanadi hanyoyi masu yawa dazan bankaɗo komai harda na Qaseem da kukai ƙoƙarin rufewa dan ina bibiyarsa kuka turasa China”.
Juyowa Dad yay daga tsayuwar da yay tun fara maganar Jay. Idanu suka zubama juna na kusan mintuna biyu kafin Dady yay wani murmushi yana girgiza kansa. Batare da yace komaiba ya juya ya tafi.
Da kallo kawai Jay ya bisa har ya shige, ya lumshe idanu da furzar da huci mai zafi daga bakinsa, batare da yay ƙoƙarin sake komawa cikiba ya nufi motarsa ya bar asibitin5
STORY CONTINUES BELOW

A ciki kuwa tunda ɗan fir’auna ya shiga da maida ƙofar ya rufe babu wanda ya sake jin ɗuriyarsa balle sanin mi yayi a ciki har saida Dad ya koma ciki da kusan mintuna biyar sannan ya fito yana wani ɗan iskan washe baki kamar gonar audiga. tsayuwa yay ya gama kallesu a ɗage sannan ya wuce batare da yacema kowa komaiba, sai wani rangaji yake irin na tsageru tamkar wani bishiyar giginya.
Babu wanda ya iya cewa uffan dan har ransu tsoronsa sukeji, sai da ya kai ƙofa sai kuma ya juyi da sauri, “Af kunga nayi mantuwa zan wuce, Surukina inafa da magana da kai a ina zamu haɗu mu tattauna ta?”. Kafin Dad yay magana Uncle Sulaiman yace, “Haba yarona, hakan duk bai kamataba kaji, koba k…….” Da sauri ɗan-fir’auna ya katse Uncle Sulaiman cikin ɗaga masa hannu da faɗin, “Nifa ka ganninan duk tsagerancina ina girmama masu mutunci, kai Uncle ɗin Ogane mai daraja babba, dan ALLAH na roƙeka ka zama ɗan kallo, dan ko takalmin Oga bazan so na takaba balle kai Uncle ɗinsa”. Uncle Sulaiman ya jinjina kansa kawai batare daya ƙarasa abinda ya faroba, sai dai a ransa yana mamaki. Juyawa ɗan fir’auna yay yana faɗin, “Duk da ni mutumne mai kunya da baya son yawan shiga gidan surukai Zanzo gida na sameka surukina”.
Kallo kawai suka iya binsa dashi harya fice tamkar wasu wawaye babu wanda ya iya sake tanka masa. 8
_______________________________
Ɓangaren su Bilkisu kam sunsha firarsu cike da nishaɗi kasancewar sun daɗe basu sami damar irin wannan haɗuwar ba, abincin da driver ya kawo daga gidan Ummah babba suka ci, dan Nabeelah ƙin biyosa tayi dan tazata Jawaad na gidan. Sai dai batasanma yana tafe zuwa gidan nasu ba, dan bayan sallar azhar can ya nufa. Tana falo zaune tana kumburin fushin Ummah tace taje tai kitso yay sallama. Ai da wani shegen gudu ta kwasa sai ɗakinta ta garƙame ƙofa. Hakan datai ya saka kowa fahimtar laifi tai masa.
Zama yay suka gaisa da Ummah tare da musu godiyar hidima da gajiyar taro, Aunty Batool ma ta gaidashi da tambayarsa bilkisu. Anan yaci abincin rana suka ɗan tattauna da Ummah akan abinda ke faruwa, kuka rurus Ummah keyi na farin ciki da al’ajabi, kai ita kanta tana mamakin irin yanda takejin Bilkisu har cikin jinin jikinta da ɓargo, san nan tana hango abubuwa da yawa dake mata kamanceceniya da jininta tattare da Bilkisun amma tarasa wacece?, wato jini ya wuce gaban wasa duk inda yake. Tace, “Jawaad bazan iya haƙuri ba gobe idan ALLAH ya kaimu zaka ganni a gidanku”. Murmushi Jay yayi, “To ai Ummah itama bata saniba, bamason ta san komai yanzun har sai mun bincika sauran abinda ke faruwar tukunna, dan kinga al’amarin yazo da ruɗani a ciki”. Shiru Ummah tai na wasu sakanni, cikin sauke ajiyar zuciya tace, “Hakane kuma Jawaad, rashin faɗa matan yanzu yanada amfani, dan ko ƴan gidanku karmu bari su sani yanzun sai mun gama sanin komai mu kanmu”. Jay yace, “Insha ALLAHU Ummah bazasu sani ba”.
Baibar gidan Ummah ba sai kusan ƙarfe uku na rana. Daga nan gida Ummah ƙarama yaje itama, itakam harma tafi Ummah Babba shiga ruɗani, saboda ita mutumce mai ƙarancin juriya akan farin ciki ko ɓacin rai, duk wanda ta tsinci kanta a ciki saika ganesa tattare da ita. itama dai ya jima anan suna tattaunawa, dan saida akai sallar la’asar sannan ya baro gidan.
Gida ya nufa dan a gajiye yake ga barci yanaji sosai cikin idanunsa. Dai-dai traffic light ta tsayar dashi idonsa ya hango masa ɓaleru cikin mota, wanda ke a bayan motar ya kalla ya ɗauke kansa, sai kuma yay saurin sake kallon motar. Abinda ya faɗo masa a raine ya sakashi saurin ɗaukar wayarsa ya shiga WhatsApp, saƙon gimba da har yanzu yana nan ya kunna, ya maimaita dai-dai inda gimba yake sanar masa sunan Alh…Alh..k……
Ganin an basu hanya ya harba motar gaba hankalinsa nakan motar su ɓalerun, gefen titi ya gangara yabi motar da kallo harta ɓacema ganinsa, a fili ya furta ‘Tabbas Alhaji Kokino Gimba kake nufi’ yay maganar da ɗan dukan sitiyarin motar yana cije lip ɗinsa na ƙasa da ƙarfi, kafin ya furzar da huci mai ƙarfi ya kife kansa a sitiyarin na kusan tsahon mintuna bakwai. Tabbas inhar tunaninsa nakan dai-dai matarnan ce, to minene alaƙarta da Gimba?. Bashi da mai bashi amsa, dan haka wayarsa ya ɗauka yay kira, bugu biyu kuwa aka ɗaga daga can cike da girmamawa. Bai tsaya sauraren gaisuwarba yace, “Hameed kana tare da ɓaleru ne yanzu haka?”. Daga can aka amsa masa da, “Yes Sir, ai da naga ma irin sabuwar motarka a traffic yanzu har na ɗauka kaine”. “Kaga manta da wannan, wa yake ja a motar?”. “Alhaji Sadi Kokino ne sir” “Ka tabbata shine?”. “Wlhy shine Sir”. Shiru Jay yayi yana murza goshinsa, ya sauke zazzafan numfashi da faɗin, “Amma kacemin Drivern Mr Gebrail ne ai?”. “Wlhy Sir tunda na fara aikin nan tare da shi nake ganinsa, ni kaina yau da naga ya ɗauki Alhaji Kokinon nasha mamaki, shiyyasa ban gazaba wajen bibiyarsu”. Sitiyari Jay ya sake daka da ƙarfi, “Hameed akwai matsala, kodai sun shirya bada ƙafane dama dankar a bibiyesu, kokuma sunada tabbacin akwai mai bibiyarsu, yanzu haka suna ina?”. “To Sir nikam ka sakani a ruɗani, amma gamu a anguwar Sanni zasu shiga wani gida mai farin gate”. “Maza kabar wajennan Hameed, kuma duk abinda ka gani bai makaba ka tabbatar ka kirani, gobe idan ALLAH ya kaimu kazo ka sameni a A.Y street”. Cikin mamakin da babu damar tambaya Hameed yace, “Okey Sire”. Yanke wayar Jay yayi ya maida akalar kiran ga Jabeer, yana ɗagawa shima bai saurari tsokanar da yake masaba ta ango ango yace, “Jabeer kuna Office ne?”. “Eh muna Office, lafiya naji muryarka haka?”. “Jabeer inason yanzun nan ku bincikamin Number da Gimba yay wayar ƙarshe da ita a randa aka ɗaukesa, a ina mai ita yake yanzu haka? Sannan macece ko namiji?”. “Okey boss ina zuwa”. Yanke kiran Jawaad yayi ya tada motarsa yabar wajen, kansa tsaye tashar da ake hawan motar garin su Gimba ya nufa. Nesa da wajen yay fakin tare da kiran Dattijon nan a waya. Mintuna uku kuwa basu cikaba sai gashi. Motar ya buɗe masa ya shiga sannan ya maida ya rufe. Saida suka gaisa Jay yace, “Ka tabbatar yarinyarnan tana mana aikin da muke buƙata?” “Sosai kuwa Alhaji, ai itama kanta batasan aiki take manaba a kansa, yanzu haka ɗazun take sanarmin wai yau zasuje wani gidan dirama wani mawaƙi zaiyi wasa na musamman akan soyayyarsu da ɓalerun”. Murmushi Jay dake ɗan wasa da yatsun hannunsa saman sitiyari yayi, “Address ɗin wajen, sunan mawaƙin, time ɗin da zai shiga wajen da tashinsa?”. Dattijo yay ƴar dariya da faɗin, “Ai Alhaji kamar dama nasan zaka tambaya duk sai da na samo waɗanan amsoshin kaf, gasu a rubuce”. Amasar takardar Jay yayi yana jinjina kai, ya ciro kuɗi ya miƙa masa yana faɗin, “Ga cikon kuɗin aikinka nagode”. Baki a washe dattijo yace, “Nine da godiya ai Alhaji, ALLAH ya ƙara buɗi na alkairi, idan wani aikinma ya taso wlhy a kawo zanyi”. Jawaad baice komaiba sai murmushi kawai.
Dattijo na fita kiran Jabeer na shigowa, ɗagawa yay yasa a kunne batare da yayi magana ba. Daga can Jabeer yace, “Tabbas Boss mace ce, sunan da tai register layin dashi shine Safara’u Hashimu, kakanta Bala, sunan mahaifiyarta Indo, kakaninta na wajen uwa Hassan da Baraka, shekarunta sittin da huɗu a duniya, asalinta ƴar garin Tsamiya ce, yanzu haka alama ta nuna ana amfani da layin a anguwar Habbun………” Jay ya katsesa da faɗin, “Habbun kuma? Ba garin nan bafa kenan?”. “Kwarai hakane”. Baya Jay yay ya jingina da kujerar yana furzar da huci, kafin yace, “Hasashena ba dai-dai bane kenan?”. Daga can Jabeer yace, “Kai minene hasashen naka da?”. “Jabeer akwai wata mata lokacin case ɗin nan na Alhaji kokino mun haɗu da ita a gidansa idan baka mantaba itace ta taimakemu sosai har muka ɗauke mata yaro mai suna Yazeed, da ina zargin itace Gimba ke magana a gidan Alhajin nan da bai ƙarisa faɗaba”. “Tabbas Boss hasashenka ba kuskure bane, tun a wancan lokacin naso nace muku kodai Alhaji Kokino Gimba ke nufi, dan na taɓa ganinsa a ƙofar gidan farkon fara maka aiki lokacin bikinmu da Surayya, kasan matar Alhaji kokino ƙanwar maman tace, yanzu abinda za’ai shine kabani daga nan zuwa safiya insha ALLAHU zan bincika komai”. “Okey babu damuwa, shima yaron nan yau insha ALLAHU zan kamashi dan na kula akwai wani abu damu bamu saniba”. “A’a haba boss, ka bari wani a cikinmu ya kamashi mana, karka shigarma Mami lokacinta, amma mika hasaso mana”. “Da kaina zan kamashi Jabeer, dan akwai saƙon da nakeson bari a kamun nasa, abinda na hasaso kuma sai mun haɗu zamu tattauna”. Ya kashe ƙittt batare da ya jira amsar Jabeer ɗinba.
Wayar Bilkisu ya kira, sai da ta kusa tsinkewa ta ɗaga dan bata kawo a ranta shi bane, ba Number data sani bace. Shiru tai taƙi magana, dan haka shi yay sallama. Yanda ta amsa sallamar ne yasashi fahimtar ta gane wanene yanzun, zamansa ya gyara da ƙoƙarin dai-daita muryarsa dake cike da ɓacin rai, “Am sorry kicema ƙawayenki suje kawai zan haɗu dasu zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu, wani uziri yane ya riƙeni gaba ɗaya shiyyasa ban dawo ba”. Murya a sanyaye bily tace, “To zan faɗa musu, amma bakaci abinciba fa, haka kake yawo da yunwa?”. Idanun Jawaad ya lumshe yana murmushi, ji yay duk ɓacin ran da ya tarar masa a ƙirji yana guduwa, yace, “Karki damu da anyi magriba zan dawo isha ALLAH, jin muryarki kawai tasa nama ƙoshi, ke dai ki shirya amsar angonki kawai ƙanwar Jay…….” ƙittt ta yanke wayar daga can.
Jawaad ya girgiza kansa yana murmushi har kumatunsa na loɓawa, motar ya tada yay gaba har lokacin murmushi ya gaza barin fuskarsa.6
STORY CONTINUES BELOW

_______________________________
Tunda su Zuhrah suka wuce sai naji gidan duk babu daɗi, ga wani motse-motse da naketa famanji amma narasa takamaimai a ina nake jinsan, nai jarumtar dakewa dan bana son na ruɗar da kaina, sai kuma na koma ganin tamkar gittawar inuwoyi ta jikin Windows, da farko dai naso fita na leƙa waje, sai kuma wata zuciya ta gargaɗeni dayin hakan, yanda kaina ya farayin nauyine yasa na jawo wayata na kunna karatun Al-Qur’ani mai girma, a hankali nutsuwa ta fara saukarmin, naji kaina ya saki na koma normal, gidan kuma yay wani irin yin tsitt mai ban mamaki, babu motsin nan sam, ko ƙarar na’urorin dake aiki da wutar dake a kwai duk bakajin ƙararsu, ban ɗauki hakan komaiba na cigaba da zama a falon har aka fara kiraye-kirayen sallar magriba, Miƙewa nai da shirin sake wanka, dan ɗazun lokacin sallar azhar da zanyi salla ganin ɗingon jini yasa banyi ba, amma yanzu dana duba gab da su Ummie zasu wuce kuma ya sake ɗaukewa, dama nasan ɗazun nayi gaggawar yin wanka dan ƙa’idane sai bayan sallar azhar nake wanka ko la’asar duk da lokaci kan ɗan canja min wani watan.
Wayar na ɗauka na shige bedroom, Kayan da zan saka na fara cirowa a drawer na ajiye, dan waɗan nan dazan cire ɗin jini yaɗan ɗiga a sket ɗin kaɗan sai yanzu na kula ma. Batare dana kashe karatunba nabar wayar a saman gado na cire kayan na shiga bayin, ban jimaba na fito gudun kar lokacin salla ya ƙwace min. Saida na farayin sallar magriba sannan. Saboda wutar dake akwai sai na jona hand dryer a soket kawai, nai zaman fara busar da gashina.
Karatun Al-Qur’anin dana sakane yasa sam banji motsin shigowarsa ɗakin ba, sai da yay sallama, da sauri na juyo dan banyi tunanin ganinsa ba.
Jay da tun ɗazun yaketa faman sallama ya ɗan tsura mata idanu, daya shigo baiga kowa a falo ba, har yay tunanin nufar nasa ɗakin sai kuma ya nufo nan saboda jiyo sautin karatu.
Towel ɗin dana tsane kai na ɗauka na ɗaura a kafaɗa ta ya ɗan rufemin ƙirji, wanda na ɗaura ɗin kuma sai faman jansa nake ƙasa dan cinyoyina duk a waje suƙe. Ganin ya ɗauke kansa tamkar baiga abinda nakeyinba ya sakani saurin cemasa, “Sannu da zuwa”. “Yauwa sannunki kema”. Ya faɗa yana ƙarasowa cikin ɗakin sosai. Zama yay a bakin gadon yana sauke numfashi alamar gajiya. Daurewa nai na tashi, na raɓa ta gefensa na ɗauka kayana dake saman gadon zan nufi bayi dan na saka sannan na dawo ɗauka masa ruwa da zaman busar da kan.
“Da miye na saurin yin wankan tunda kinsan bai tafiba?”. Maganarsa tazomin a bazata. Cak na tsaya tare dayin ƙasa da kaina dan ni bansan wace amsa zan bashi ba nikam, yaushe yasan nayi wankan to? Anya boss bai gani har hanji kuwa?.
Ganin yanda ta wani tsume waje guda ya sakashi miƙewa yana girgiza kansa, zare rigarsa yayi ya raɓata ya wuce batare da ya sake cewa komai ba.
Ganin ya shige bayi nai azamar saka kayan sauri-sauri sannan na fita na ɗaukko masa ruwa, zaman busar da kan na sakeyi yanzun kam hankalina kwance, saukar laimar ruwa da naji a kan hannuna ya sakani saurin ɗagowa na kalli mirror’n, shine tsaye a bayana, sakar masa hand dryern da yake ƙoƙarin amsa a hannuna nayi ina rumtse idanu, dan wani irin masifaffen harbawa zuciyata tayi, karan farko da naga namiji a tuɓe kamar haka a gabana bayan jazuga da baida wani fasalin kirki irin na zaratan maza. a raina rayawa nake, ‘Wai miyasa maza sam basu da kunya ne? Daga shi fa sai towel iya ƙugu zuwa gwiwa amma ya iya fitowa gabana ya tsaya’.
Jay da duk yana kallon yanda ta rikice ta cikin mirror’n yay guntun murmushi kawai yana ƙarasa busar mata da kan, sai da ya gama tsaf ya ɗauki ribbon ɗin da yaga ta ajiye ya ɗaure matashi tsaf fiyema da yanda zatayi, harda su mata wani ɗan style da brush. Kujerar ya juya ya maido fuskarta inda yake kafin ya miƙar da ita tsaye ya ɗaura duka hannayenta saman ƙirjinsa daketa raɓar ruwan wanka. “Buɗe idonki” ya faɗa babu wasa.
Hannunta dake ɗan rawa tai ƙoƙarin zamewa tana maƙe kafaɗa alamar “Ah-ah”. hannun nata ya maida da ƙyau, yana bin fuskarta da kallo. A bazata ya sumbaci inda batai zatoba duk da akwai riga a jikinta. A take ta waro idanu waje da masifar sauri tare da buɗe baki. Babu shiri Jay ya ƙyalƙyale da dariyar da bai niyyaba, dan yaga tsoron nata fiyye da yanda yake son gani.
Bilkisu tai saurin duƙewa tana matse hannayenta duka biyu a ƙirjinta tare da cusa kanta duka a cikin cinyoyinta tana murmushi, dan ita kanta tabama kanta dariyar abinda tayin. Ga kunya mai tsanani akan abinda yayi ta lulluɓeta. Kafaɗunta ya kama ya ɗagota yana murmushi, duk yanda yaso su haɗa ido taƙi, daga ƙarshema saita ɗora kanta a ƙirjinsa ta ɓoye fuskar. Rungumeta yay da duka hannayensa yana murmushi tare da shaƙar ƙamshin da gashinta keyi da jikinma nata ya lumshe idanu. Kusan mintuna biyu suna a haka sannan ya zauna a bakin gadon ya ɗaurata saman cinyarsa. Fuskarta ya ɗago yanda zata kallesa duk da dai tanata faman yin ƙasa da idanu amma tana ganin fuskar tashi. Laɓɓansa ya nuna mata da ɗan yatsa yana wani ƙanƙance idanunsa. Kafaɗa ta maƙe da sake maida kanta a ƙirjinsa.
“Ni ai sai nayi” yay maganar yana yin baya dasu a kan gadon ya birkiceta ta koma ƙasa. A take idanun bily sukayo waje, hanata dukkannin dama yay ya shiga yin yanda yaso da ita.
Kiran sallar isha’i ne ya ƙwaci Bilkisu a hannun Boss, shima da ƙyar, dan daga kiss sai salon ya nema canjawa. Tunda ta samu ya barta ta cusa kanta cikin filos. Baice da ita komaiba shima ya fice yana murmushi. Ɗakinsa ya nufa ya sake ɗaura alwala da canja kayansa zuwa blue jeans da t-shirt itama Blue, ya saka turare kaɗan da ɗaukar wata ƴar ƙaramar bindiga ya saka a gefen ƙugunsa sannan ya fito. Ɗakin Bilkisu ya koma. isketa yay ta fito daga toilet fuska a jiƙe alamar alwala tayo. Ruwan data ajiye masa ɗazun ya ɗauka yana sha idonsa a kanta. Kofin ya ajiye yana kallon agogon hannunsa, “Bara naje za’a shiga salla, idan an idar zan ɗan ƙarasa wani waje insha ALLAH kafin goma zan dawo.
Da sauri Bilkisu ta kallesa idanu cike da ƙwalla, “Dan ALLAH mu tafi tare, nidai tsoro nakeji”. Yanda ta kumbura baki taso bashi dariya, amma sai ya danne abinsa ya taka zuwa inda take tsaye, fuskarta data duƙar yasa hannu ya ɗago, acan ƙasan maƙoshi yace, “Kin taɓa ganin amaryar kwana ɗaya a gidan miji ta fita?”. “To ai babu wanda zaisan na fita tunda dare ne”. Fuskar tata ya saki yana ɗan ɗage kafaɗa, “Okey, ki shirya kafin na dawo salla saimu je”. Cike da murna ta amsa masa da to. Goshinta ya sumbata ya juya ya fice yana murmushi dan wayo kawai yay mata ba dawowa zaiyi ba.5
Ana idar da salla Jay ya fito daga massallaci, motarsa da dama ya bari a waje bai shiga da ita gida ba ya shiga ya bar anguwar, kai tsaye address ɗin da dattijon nan ya bashi ya nufa, anguwace irin sabuwar anguwarnan da uncompleted buildings sukama fi yawa, sai dai inda gidan drama’n yake anɗan gaggama wasu gidajen dan wajen harya fidda santa ɗoɗar, bakajin hayaniyar komai saina Genretor ɗin da suka kunna da ƴar hayaniyarsu alamar basu gama zuwa ba, akwai ƙwayayen wuta a waje da suka haska kusan rabin layin, sai mai Nama daketa faman haɗa wuta, gefensa mutum biyune ɗaya mai ruwa ɗa kayan drinks, sai saurayi da budurwa dake can gefe suna hira, sai kuma masu shiga da fita cikin gidan ɗai-ɗai dan yanzu suke kan zuwa. Waya ya ɗauka yay kiran wani abokinsa da ya kasance ainahin police, saida suka gaisa ya gama tsokanarsa da ango-ango, sannan Jay yace, “Auwal kuna garin nan amma tsageru har suke da lasisin buɗe wuraren iskanci irin haka?”. Daga can Auwal yace, “Haba dai Jay, kaima kasan hakan bazai kasanceba”. “Gashi kuwa na gani da idona, akwai wani gidan Drama a sabuwar anguwar nan data kusa haɗewa da jan-ɓauna, inason ƙarfe goma da rabi kuzo wajen kuyi kamen kan mai uwa da wabi”. Bai jira cewar Auwal ba yace, “Mu kwana lafiya” ya yanke wayar. facemask ya ɗauka ya saka tare da facing cap, kallon kasan yayi a madubi ya tabbatar komai yayi kafin ya fito bayan ya kashe motar. Sai da ya tabbatar babu wanda yaga fitowarsa sannan ya nufi gidan.
★★★★★★
Ina idar da salla na koma bakin gado nai zaman jiransa, ganin shiru-shiru sai kawai nahau yin game a waya, hamma na farayi ɗai-ɗai alamun inajin barci, nayi guntun tsaki da kallon agogon ɗakin, tara saura minti ashirin, zamewa nai na kwanta tare da jan filo na ɗaura kaina na cigaba da game ɗin, tun ina ƙoƙarin damƙe wayar dake neman suɓuce min harna yaddata batare dana saniba.
A firgice na farka jikina na wani irin ƙyarma, ‘innalillahi wa’inna ilaihirraji’un’ na shiga ambata ganin ɗakin dunɗum da duhu bayan kuma nasan fitilar a kunne take, dariyar da aka tuntsure da ita ta sakani sake firgicewa nahau laluben gadon…..
“Bilkisu! Kenan mai gadon zinari, wato ke amarya ko? Azatonki zaki iya tsere minne? Ke da kina tunanin na barki? Wannan gurɓataccen tunanine bilkisa, na rantse miki yau saina amshi abinda ya kasance cikar burina dan bazan rasa komai a dalilinki ba wannan gangan ne hhhhhhhhhh!!!!!!!!……………..✍45
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.15
Page 42
………………Inda mai naman nan yake ya tsaya, batare da yayi magana ba ya miƙama mai-naman 1k tare da nuna masa naman. Kallonsa yay a ƙufule, “Haba malam, ya zakazo waje babu ko sallama ka miƙomin dubu wai na baka nama? An faɗa maka ni irin sakarkarun masu saida naman nan ne da kuke rainama hankali, nibanma taɓa ganinka a gidannan ba, kai wane?”. Jay ya danne takaicinsa cikin salon maganar kurame yay masa nuni wai shi bebe ne”. Mai nama yace, “Oh to yanzu naji batu, kasan rainin tsagerun gidannan ne bazan iya ɗaukaba shiyyasa kaima nai zaton kalarsu ne, na duka kake so?”. Kai Jay ya jinjina masa. Mai nama ya fara yankowa yana sawa a takarda da raira ƴar waƙarsa ta shata mai taken “Natsaya ga annabi Muhammadu…….” Jay dai kallonsa yake da nazarin wajen harya kammala yanka masa, amsa yay da masa godiya ya juya zai tafi, sai kuma ya juyo da sauri irin kamar yayi mantuwar nan. Ƴar takarda ya ciro a aljihun wandonsa ya miƙama mai nama. Mai nama ya amsa da faɗin, “Miye kuma wannan? Nifa kunsan ba wani boko nayiba amma kuyitamin wani lagude-laguden jaraba. Kai Hamusu zo duba mi ya keso kuma?”. Wanda aka kira Hamisu dake gaban lemuka ya amsa da “To baba”. Takardar ya amsa ya duba sannan ya kalli mai naman, “Baba wai gidan Ɗan Alhaji ya keson a nuna masa”. Shiru mai naman yay yana kallon Jawaad, mikuma ya tuna oho masa sai ya washe baki, “Af to inaga irin abokansa ne daya ɗan gayyato, kasan yau zaiyi ajo”. Jinjina da hannu Jay yayma Mai nama irin ka gane ɗinan. Mai-nama ya sake washe baki da nunama Jawaad wani gida dake can kusan ƙarshen layin. Cikin alamar maganar kurame yayma Jay yay masa godiya da nufar inda aka nuna masan.
Rufe gidan yake dan haka ya ƙwanƙwasa, sai da yay sau kusan baƙwai sannan akazo aka ɓuɗe cike da masifa.
“Wai wane shegene yake bugama mutane gida haka? Sai kace ya bada ajiya ko an ci masa bashi, idan akai haƙuri dai ai zan fito ba sai ansama lokacina ido b…..” hankaɗa shin da Jawaad yay ya koma baya ya hanashi ƙarasa maganar, zai sake magana Jay ya ɗaura hannunsa saman baki yace, “Shiiiiii”. yana ɗaga rigarsa bindiga ta bayyana, jiki na rawa ɓaleru ya saka hannu ya toshe bakinsa yana faman zare idanu. Ƙofar Jay ya maida ya kulle bayan yay wurgi da ledar naman daya shigo da ita, ya sake kaima ɓaleru wani bahagon bugu tare da damƙo wuyan rigarsa ya miƙar dashi tsaye. Batare da yay magana ba ya nuna masa hanyar cikin gidan. Jikin ɓaleru na rawa ya shiga kaɗa kai tamkar wani ƙadangare.
Gidane madaidai ci yasha tiles har a jikin bango, ga hasken wutar Genretor da alamu suka nuna na gidan drama ɗinne aka jawo masa har nan, ƙofar dake buɗe suka shiga, budurwar dake kwance saman katifa tsirara ta miƙe da sauri zaune tana jan bedsheet ɗin saman katifar ta ƙudundune kanta ciki zata zabga ihu…….
“Idan baki rufemin shegen bakin kiba saina ragargaza ƙasusuwanki wlhy!!”. Jay yay magana cikin kaushin muryar da ta saka budurwar cusama bakinta bedsheet ɗin tana zare idanu hawaye na ƙwarara, jikinta sai rawa yake.
Jawaad ya maida kallonsa ga ɓaleru da duk hankalinsa ke kan wayoyinsu dake zube a ɗan table na glass ƙarami dake gefe. Ƙafa Jawaad yasa ya taɗesa ya faɗi ƙasa tim, cikin zafin nama ya shiga sauke masa maruka a fuska da hannu bibbiyu. A take ji da ganin ɓaleru suka gushe, gashi babu damar yin ihu yana tsoron bindiga. Sai da Jay ya jigatashi da maruka ya tabbatar ya fita hayyacinsa sannan ya barshi. Budurwar daketa gunjun kuka da faman ɓoye fuska ya kalla, “K zoki kashemin duk wayoyin nan….”. Kafinma yakai ƙarshe harta miƙe zaram tana damƙe bedsheet ɗin da ƙyau jikinta na rawa, wayoyin uku manya ta kashe sai ƙarama ɗaya. Yace, “Ina taki?”. Nuna masa ɗaya daga cikin manyan tayi, ukun kuma tace, “N..na nashi ne sauran”. Ɗauke kai Jay yay batare da ya sake cemata uffan ba, ya ɗauki Coc dake ajiye yanata raɓar sanyi ya ɓalle murfin, saman fuskar ɓaleru daya suma ya juyeshi, a take ɓaleru ya kawo numfashi. Wani marin Jay ya sake sauke masa a fuska. Take ya dawo hayyacinsa ya fashe da kuka yana share jinin da yake fita daga hancinsa yana sauka masa kan baki, “Dan ALLAH malam minai maka kake min irin wannan dukan? Idan kuɗi kakeso ko nawane zan baka, nidai karka kasheni dan girman ALLAH, kag…..” sake wanka masa wani marin Jawaad ya ƙarayi tare da ɗora ƙafarsa ɗaya kan katifar ya ranƙwafo kansa da nuna masa fuskar wayarsa. “Wanene wannan?”. Ɓaleru da jikinsa ke rawa ga jini nata fita masa ta hanci da gefen baki yace, “Ni…ni ban sanshi ba wlhy”. “Baka sanshi ba! Kace baka sanshi ba?!!”. “Eh wlhy oga bamma taɓa ganinsa ba”. “Yayi ƙyau” Jay ya faɗa yana miƙewa da tattare hannun rigarsa sosai yay sama. Har Ɓaleru ya fara murna an barsa sai kawai ji yay Jay ya cakumo masa wuya ya miƙar dashi tsaye da ƙyau. Mahaukacin duka ya shiga masa da babu algus, yanda yake bugun nasa zai tabbatar maka zuciyar ƴan mazan a wuya take. Sam baya sauraren roƙon da ɓaleru ke masa da kukan karuwarsa. Saida yay masa lilis sannan ya hankaɗashi ya faɗa saman katifar kansa ya daki bango Ƙummm!!!!. Dafe kan Ɓaleru yay da sakin wata wahalalliyar ƙara, saiga jini sharrrr. Jay ya sake cakumo wuyansa ya shaƙesa da ƙyau da hannu guda, ɗayan kuma ya sake nuna masa hoton Gimba dake tare dashi da suka ɗauka a gidan gonarsa wani zuwa da suka taɓayi tare. Yace, “Har yanzu dai baka sanshin ba?!”. “Dan ALLAH ka tausayamin oga ka daina dukana karka halakani na sanshi, Abokina ne sunanasa Gimba garinmu ɗaya”. Ɗauke fuskarsa Jay ya sakeyi da mari yana faɗin, “Ɗan iska kake son maidanine da?”. “Na tuba dan ALLAH kayi haƙuri bazan sake maka ƙarya ba”. Miƙewa Jay yay tsaye ya kaima Ɓaleru harbi a ƙafa da tofa masa yawu, sai faman huci yake, jiyake tamkar ya kashe banzan nan ko zaiji sauƙin raɗaɗin da zuciyarsa ke masa.5
STORY CONTINUES BELOW

________________________
Bilkisu! Kenan mai gadon zinari, wato ke amarya ko? Azatonki zaki iya tsere min ne? Ke da kina tunanin na barki? Wannan gurɓataccen tunanine bilkisa, na rantse miki yau saina amshi abinda ya kasance cikar burina dan bazan rasa komai a dalilinki ba wannan gangan ne hhhhhhhhhh!!!!!!!!.
Hannu nasa na toshe kunnuwana domin nisanta jina daga shaiɗaniyar dariyarsa, na fashe da kuka ina jan jikina baya, “Kaji tsoron ALLAH bawan ALLAH, koda kai aljanine na tabbata kasan akwai hisabi tsakaninmu ƴan adam da ku, minai maka ne kakeson ganin bayana? Ka tunafa ni matar aurrece yanzun, dan ALLAH na roƙeka karka wulaƙantani, ka barni da mutuncina………….”
“Kima daina ɓata yawun bakinki madam, babu wani roƙonki dazan taɓa saurara, keɗin kaddarace mai girma a gareni, makullin cikar dukkanin burkana. Kinsan illa nawa kikaimin ne?!!” yay ƙare maganar a tsawace da cafke wuyana ya shaƙe. A take jikina ya fara rawa na fara ƙoƙarin fisgo numfashi cikin kakari. Hankaɗani yay na bigi fuskar gadon. Azaba ta sakani fashewa da kuka na riƙe wuyana da duka hannu biyu. Wani irin matsanancin fushine ya tasomin jin dariyar da yake sake ɓaɓɓakawa yanzu ma, nace, “Ƙarya kake azzalumi, idan ka isa ka daina ɓoyemin kanka, matsoracin banza da wofi kawai, Bazan sake roƙoka ka barni ba koda hakan na nufin zakai nasara a kaina ɗin, sai dai na ɗauki alwashin in ALLAH ya yarda, inhar ƙazamin jikinka ya kasance shine ƙaddarata, nima nice zan zama ƙaddarar mutuwarka, dan da hannuna zan kasheka a ɗakin nan, a wannan daren la’ananne ALLAH fasiƙi kawai!!!”.
“Hhhhhhh!!” ya shiga sake ɓaɓɓaka dariyarsa mara daɗin ji da tafa hannayensa. Gaba ɗaya ɗakin ya ɗauki sauti hakan yasa na kasa fahimtar taka maimai inda yake. “Da ƙyau Bilkisu, da ƙyau!, ashe kema kin fara koyon jarumtar mijin naki?, nine zaki kashe, ni ni ninan kikejin zaki iya ki kashe…..?!!!” naji an sake damƙar wuyana an shaƙe.
A take jikina ya fara rawa, nasa hannu na daki cikinsa cikin gushewar hankali, dukda alamu sun nuna yaji zafi bai sakeni ba, sai ma dannani da yay baya ya maƙureni jikin fuskar gadon ya haye kaina. “Zanyi abinda ya kawonin, ada nayi niyyar barinki a raye tamkar sauran kicigaba da rayuwa kema, to amma tunda kince ke tsagerace saina shayar dake gidauniyar azabar mutuwa, k har wacece? Nawa kike? Da zaki zamewa rayuwata matsala…….”
Yanda naima Jazuga ne ya shiga dawomin a rai, duk da shaƙar da yaymin cikin rahamar UBANGIJI na samu damar lalubar bed side drawer da naji a kusa da hannuna, kofin da boss yasha ruwa ban fiddaba yana a kai na jiyo, ALLAH ya bani sa’a fisgosa na ɗaga hannuna dake rawa da ƙyar na maka masa a gefen kunnensa. A take ya sakarmin wuya yana huci na shigar zafi….. Kafin ya dawo hayyacinsa na caka masa sauran kofin dake riƙe a hannun nawa, sai dai bansa a inane ba dan a kwai duhu a ɗakin har yanzun. ƙara ya saki yana sake kaimin wawura sai dai na zille harma na dire a gadon. Cafkoni yay cikin zafin nama ya maidoni baya kan gadon har saida nai ƙara dan azaba nima. Na gallama hannunsa cizo tare da halbinsa da ƙafa cikin salon trianing ɗin da muka samu duk da ba ganinsa nake ba. kokawa ce ta kaure a tsakanina da shi dukda yafi ƙarfina nesa ba kusaba. Amma kasancewar akwai taimakon UBANGIJI da kuma kowa yasan mata ALLAH kan bamu ƙarfi a irin wannan yanayin koda ace bazamu iya ƙwatar kanmuba kuwa. Kokawa muke bil haƙƙi da gaskiya dukda nice keshan wahala ban yarda ya kaini ƙasa ba. Cikin sa’a na kama ɗan yatsan hannunsa da yake neman sake kaiwa wuyana na murɗesa da azabar ƙarfi nai baya dashi. Jikake ƙaraƙassss ƙasss ƙasss ƙashin na bada sauti. Wahalalliyar ƙarar daya saki yay baya ta bani damar jan hannuna baya nima, sai na saɓulo da zoben dake jikin yatsan.
A take Ɗakin ya ɗauki sautin wata murya mai ban tsoro da saka firgici, aka shiga faman faɗin, “Barmata shine kuskure mafi girma, ka karɓa maza ka fita karka tsaya akwai matsala!!”.
Wani irin ɗagowa yay a zabure ya fisgoni muka tafi ƙasa tare ya murɗe hannuna da zoben ke a ciki zai ƙwace. Hakan yasa na shiga ambaton,
حَسْبُنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ.
Hasbunal-lahu wani’mal-wakeel.
(ALLAH ne mai isar mana, kuma madalla da shi abin dogaro).
اَللَّهُمَّ اكْفِنِيهِمْ بِمَا شِئْتَ.
Allahummak finihim bima shi’ita.
(Ya ALLAH! Ka isar mini su da abin da Ka so).
اَللَّهُمَّ لاَ سَهْلَ إِلاَّ مَا جَعَلْتَهُ سَهْلاً وَأَنْتَ تَجْعَلُ الْحَزْنَ إِذَا شِئْتَ سَهْلاً.
Allahumma la sahla illa ma ja’altahu sahlan, wa anta taj’alu-l-hzana idha shi’ta sahlan.
(Ya ALLAH! Babu wani abu mai sauki sai abin da Ka sanya shi ya zama mai sauki, kuma Kai kana sanya tsanani idan Ka so ya zama sauki).
Ƙarar da aka ƙwallah ta sakashi Hankaɗani kaina ya daki gadon, ya fita da gudu, na fasa wani irin gigitaccen ihu jikina na ɗaukar wani irin rawa, a take komai yay min ɗifff…….
Fasa ƙarar Bilkisu tai dai-dai da ƙarasowar Jay jikin ƙofar falon zai buɗe dan isowarsa gidan kenan bayan yakai Ɓaleru ya ajiye a wani ɓoyayyen waje. cikin zafin nama ya faɗa falon batare da ya rufe ƙofar ba. Ledar dake hannunsa ma sakinta yay a falon. A gigice ya danna makunnar fitilar ɗakin ta kawo haske. Ya daka wani uban tsalle sai gashi gaban Bilkisu data sume. Da ƙarfi ya ƙwala kiran sunanta jikinsa na rawa dan har yanzu yana tattare da fushin ɓaleru ne, yay saurin maidata ya kwantar jin kamar gudun mutum ta bayan Windown ɗakin. Fita yay da gudu yana ƙwalama maigadi kira cikin matsanancin hargagi akan ya rufe masa gate. sosai maigadi dahar ya shiga ɗakinsa zai kwanta ya fito a gigice shima jin wannan mafaraucin kira, baƙaramin tashin hankali ya shigaba ganin yanda Jawaad yake nufosa tamkar mahaukacin zakin dake a yunwace. Ɗaukesa Jay yay da mahaukacin mari, “Waye ya shigomin gida? Ka gayamin wa kabama damar ya shigomin gida!!?”.
Maigadi daya gama ruɗewa da marin da yasha yace, “Wlhy oga babu wanda ya shigo gidannan tunda ka fita, narantse maka babu wanda ya shig……..” bai gama saurarensaba ya bar wajen, ta bayan Windows ɗinsu ya nufa kasancewar akwai wuta ko ina da haske. Take masa baya mai gadi yay da sauri shima dan bai fahimci abinda ke faruwa ba. Jay yaja wani mahaukacin birki yana kallon tsanin dake tsaye jikin katanga alamar koma wanene tanan ya shigo, kuma tanan ya fita. Naushi ya kaima bango da azabar ƙarfi yana faɗin, “Noooo!!”. Da sauri maigadi dake cikin tsoro ya riƙe masa hannu, “Oga dan ALLAH karka jima kanka ciwo”. Fisge hannunsa yayi dayin wani Uban tsalle ya ɗane katangar cikin ƙwarewar training da suka samu batare da ya kalli inda tsanin ya keba. Dirarsa can baya kawai maigadin yaji. “Na shiga uku ni gambo, mike faruwa a gidan wai?” mai gadi ya faɗa hankali tashe.
Babu abinda Jay ya gani sai sayin takalmi kawai da wani tsanin a baya, wajen siririyar hanyace data fita ɗoɗar har babban titi, hanyar tana taimakawa ƴan anguwarne wajen fita titi basai sunbi ta titin layinba dake da nisa da babban titi, ya dafe kansa dake wani irin masifar sara masa. Halin daya bar bilkisu a cikine ya faɗo masa a rai. Ya fiddo wayarsa a aljihu ya shiga haske-haske harya zagaya ta ƙofar gate yay knocking. Koda aka buɗe baiko kalli maigadi dake neman ƙarin bayani ba ya nufi cikin gidan.
Yanda ya barta haka ya Koma ya sameta babu alamar numfashi tattare da ita. Tsugunnawa yay gabanta ya Rungumota da ƙarfi cikin ƙirjinsa jikinsa na wani irin tsuma na tsananin ɓacin rai, “Ubanwaye ya shigomin gida? Miyay miki?”. Yay maganar cikin raunin murya da ɗaci, jijiyoyin kansa na miƙewa ruɗu-ruɗu, zafafan hawayene ke kwarara a cikin zuciyarsa, a zahiri kam babu ko ɗigonsu sai idonsa daya kaɗa yay jazur. Ɗagata yay gaba ɗayanta ya ɗaura a kujerar dake ɗakin guda ɗaya ƴar doguwa, sai da ya gama bin ɗakin da kallo tsaf, ɗigon jini har a kan gadon ya gani, sai fasashen glass aƙasa zuwa gadon dake a yamutse alamar ansha dabbe a kansa. Kauda kansa yay yana rumtse ido da danne abinda ke yinƙuro masa tamkar zai faso ƙirjinsa ya fito mai alaƙa da Masifaffen kishi, sauran ruwan daya bari dake yashe a ƙasa ya ɗauka, a hannu ya zuba ya shafa mata a fuska. A take ta kawo wani nannauyan numfashi tare da miƙewa zumbur cikin zafin nama tana faɗin, “Saina kasheka, bazan barkaba yau, kasheka zanyi wlhy……” Saurin riƙe hannunta da take ƙoƙarin kaiwa wuyansa yayi da ƙarfi ya mannata jikinsa yana faɗin, “Kwantar da hankalinki ki nutsu nine”.
Ƙamshin turarensa da naji ya sakani fashewa da kuka na ƙanƙamesa, “Boss shine, wlhy shine ke bibiyata tun a gidan Dad wai sai yamin fyaɗe, ya ɗau alwashin saiya ketamin mutuncina, yace nice cikar burinsa, saiya yimin yanda yayma su Amina, na shiga y……” ɗagota yay da sauri jikinsa na kakkarwa ya manne bakinsa da nata, sam baya buƙatar ji, bayason yaji komai a yanzu, zuciyarsa zata iya tarwatsewa idan ta cigaba da faɗa bazai iya ɗauka ba, yanada kishi mai tsanani akan dukkan abunda ya kasance nasa. hawayen da tun ɗazun yake fatan yinsu sunƙi suka shiga silalo masa a kumatu yanzun, yanda yake matan kawai zai baka tabbacin ba’a hayyacinsa yake ba. Yaja kusan mintuna biyar yana kissing ɗinta, tun tana ƙoƙarin son ƙwacewa harta nutsu ta miƙa wuya, dan ta kula da fushi yake sumbatarta. hawayensu ne masu ɗumi ke sauka bisa fuskokin juna. Saida yaga tayi laƙwasa sannan ya zare bakinsa cikin nata da sake rungumeta yana haɗiyar zuciya tamkar numfashinsa zaibar ƙirjinsa. Yanda ƙirjinsa ke sama da ƙasa sosai ya firgita Bilkisu, sai dai tai luf a jikinsa tana kuka dan dukkan abinda ya faru a waɗancan ranakun a yanzu tsaf suke dawo mata tamkar yanzune komai ke faruwa. Ɗaukarta yay gaba ɗayanta ya nufa ɗakinsa da ita, kai tsaye bayi ya zarce. Tanason tai magana sai dai babu fuska, dan haka ta nutsu shiru tanata share hawaye da sauke ajiyar zuciya. Ruwa ya haɗa mai ɗumi sosai ya nuna mata alamar tai wanka ya fice.
Binsa nai da kallo harya fice sannan na maida idona ga hannuna dake a rumtse, zobene mai azabar ƙyau da ɗaukar ido dana samu zamewa hannun tsinannen nan. Na maida hannun na rumtse ina cigaba da zubar da hawayen, mamaki nake a raina miyasa wancan zuwan da yaymin a gidan Dad ban taɓa tunawabama balle na sanarma wani? Nida sam bani da mantuwa amma gashi wannan ban taɓa tunawaba sai yau? Ko yaya akai hakan ta faru?. Da wannan zoben rumtse cikin hannuna nai wankan, da gasa jikina kawai nayi da ruwan daya haɗamin kafin nai amfani da sosonsa sama-sama dan wani irin ƙyanƙyami da takaicin raɓar jikina da la’anannen can yayi nakeji.
Jay Ɗakinta ya sake komawa. Bai taɓa komaiba bayan kayan barci daya ɗauka mata ya kashe fitar ya rufo ɗakin. Ledar daya yasar a fali ya ɗauka ya koma ɗakinsa.
ina kammala wankan yana shigowa, nai saurin komawa na duƙe dan bankai ga ɗaura towel ba, bai fasa shigowa cikin toilet ɗinba, sai dai kuma bani yake kallo ba, bathrobe dake ajiye ya ɗauka ya juyo inda nake, kafaɗuna kawai naji ya kamo ya miƙar dani, nai azamar rumtse idanuna dake cika da ƙwalla hannuna na naɗe a ƙirjina gaba ɗaya, ban buɗeba harya gama sakamin ya ɗaure igiyar sannan ya kama hannuna daga cikin bathtub ɗin ya fitar dani. Muryarsa a dakushe yace, “Yi alwala”. Juyawa nai naɗan kallesa, ganin shima ni yake kallo nai saurin maida kaina ƙasa tare da miƙa masa hannuna dake a dunƙule rumtse da zoben. A hankali ya tako inda nake ya kama hannun ya buɗe, jin bai ɗaukaba baikuma yi maganaba yasa na kallesa. Zoben ya kafe da idanu tamkar mai nazari, hakan ya bani damar ƙarema fuskrsa kallo dake a matuƙar ɗauren da ban taɓa ganiba nima. Ya ɗago jajayen idanunsa masu tsananin saka firgici ya kalleni. “Nashi ne?”. Kaina na ɗaga masa. Bai sake cewa komaiba ya ɗauke zoben yana sake nunamin nayi alwala. Nima ɗin bance komanba na barsa tsaye yana jujjuya zoben a hannunsa. Ina alwalar ya fita, babu jimawa ya dawo lokacin na kammala, fita nai na barsa, sai yanzuma nake tunawa banyi sallar isha’i ba ashe balle shafa’i da wutiri. Riga da hijjab dana gani a saman gadon na ɗauka na saka, na ɗauki abin salla dake ɗakin na shinfiɗa na tada sallar isha’i na miƙe nai shafa’i, bayan na idar na miƙe zan sake kawo shafa’i da wutiri na tsinkayi muryarsa yana dakatar dani. Dukda nayi mamaki haka nabi umarninsa, wani abin sallar ya shimfiɗa a gabana. Munyi salla raka’a biyu sannan mukai shafa’i da wutir. Juyowa yay ya dafa goshina bayan mun idar, a fili ya shiga karanto addu’arnan ga mai sabon aure,
اَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ خَيْرَهَا، وَخَيْرَ مَا جَبَلْتَهَا عَلَيْهِ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّهَا، وَشَرِّ مَا جَبَلْتَهَا عَلَيْهِ.
Allahumma innee as-aluka khayraha wakhayra ma jabaltaha ‘alayh, wa-a’oothu bika min sharriha washarri ma jabaltaha ‘alayh.
(Ya ALLAH ina rokon Ka laherinta da alhrin da Ka dabi’antar da ita a kansa, kuma ina neman tsarinka daga sharrinta da shaarrin Da ka dabi’antar da ita a kansa).
Ya saki goshin nawa ya juya tare da ɗaga hannu yay doguwar addu’ar da banaji, dan haka nima nai tawa tareda yima iyayena addu’a da sauran musulmai baki ɗaya.
Batare da yace dani komaiba ya miƙe, ficewa yay, babu jimawa sai gashi da kofi a hannu da filet, ina a inda ya barni zaune nidai banko motsaba, ledar ya buɗe ya juye gasashen naman rago daketa tashin ƙamshi saboda yanda aka sarrafashi cikin filet ɗin, kofin kuma ya saka fresh milk a ciki. “Taso kici abinci” ya faɗa yana zama akan sofa. Duk da bazan cinba ban musaba na tashi zuwa garesa jikina duk babu ƙwari ga ciwo yanamin ta ko ina saboda damben da mukaci da azzalumin can, ƙasa naso zama amma sai ya riƙoni na zauna kusa da shi, murya a sanyaye nace, “Naƙoshi, da yamma mukaci abincin da Ummah ta aiko dashi da rana”. Baice dani komaiba ya miƙamin fresh milk ɗin cikin kofin, amsa nai ita na kafa kai na shanye gaba ɗaya badan tanamin daɗiba sai dan buƙatar samun sanyi a cikin ƙirjina da yaymin nauyi. Jikina ko ina ciwo yay tsamu ga barci dama inaji. Amsar kofin yayi ya sake zubawa ya miƙomin, kaina na girgiza masa cikin marairaicewa dan kar yace saina shaɗin tilas. shanyewa yay ya miƙe ɗauke da filet ɗin naman da kofin. “Ga kaya nan ki canja ki kwanta”. Kaina a ƙasa nace, “To”. Juyawa yay ya fita, harna kammala saka kayan bai dawoba, na zauna bakin gadon ina ƙara tariyo abinda ya faru awanni biyu da suka shuɗe tamkar film ko mafarki. Gittawar da akai ta gabana ya sakani saurin ɗagowa, ganin shine sai na sauke ajiyar zuciya a hankali. Kwantawa nai da sauri ganin zai cire jallabiyar jikinsa na juya masa baya. Kusan mintuna goma sannan ya hawo gadon shima ya kwanta bayan ya kashe fitilar yabar ta gefen gadon kawai. na lumshe idanuna hawayen da suka taru min na silalowa, ni kaɗai nasan irin raɗaɗin da nakeji a raina da ruɗanin abinda ya hanani tuna waɗancan kwanakin da wannan shaiɗanin yazomin. saukar tattausan hannunsa akan kumatuna ya sakani buɗe ido a hankali kansa, fuskarsa gab take da tawa har muna shaƙar numfashin juna, dan akan filon danake kwance ya ɗora kansa shima, idanunsa dake kallon fuskata ya lumshe a hankali cikin salon lallashi yana mai sharemin hawayen da hannunsa dake akan fuskar tawa, cikin muryar raɗa yace. “Miyasa baƙya gajiya da kuka?”. Wasu hawayen ne suka sake silalo min, nace, “Na tsaneshi ne fiye da yanda kowa zai iya tunani”. Murmushi naji yayi mai sauti, hakan yasa na buɗe idanuna ina kallonsa, kallona yake shima,, “Kinsan minene?” kaina na girgiza masa alamar a’a, yace, “Na fiki tsanarsa Miema”. Murmushin da ban niyya bane ya suɓuce min a bazata. Gani nai shima yay murmushin idanunsa da suka rine jaa na wani irin ƙyalli kamar hawaye ya taru a cikinsu. nai ƙoƙarin jan fuskata baya dan kusancinmu yayi yawa, sai yay saurin maidoni gab fiyema da farko, yace, “Faɗamin miya faru? Kozan sami nutsuwa”. Hawayen ne suka sake silalowa, na maida idanuna na lumshe inajin yanda yake murza yatsansa babba saman fuskata, sauran huɗun kuwa kan gashina daga ƙeyya zuwa gefen kunne “A wani daren daya shuɗe, wanda tunani ko hasashe bai sake dawo dashi ba gareni, ranar da ya fara zuwa gareni…………………….”.
Na ƙare faɗa masa dukkan abinda ya faru har zuwa yau da fashewa da kuka mai cin rai, da ƙarfi ya jawoni jikinsa ya rungumeni tsam, jikinsa na wani irin rawar ɓacin rai, nima saina sake fashewa da kukan, dan koba komai na fahimci shima yanajin irin zafin da nakeji a cikin raina, nace, “Na rasa miyasa ban taɓa tunawa ba sai yau?, Inason nasan ko wanene shi? Miyasa duk waɗanan kalaman nasa a kaina? saina kasheshi, da hannuna zan kasheshi azzalummi maƙiyin ALLAH, sainai gunduwa gunduw………”
Jawaad daya saki murmushin takaici mai ciwo ya ɗagota daga jikinsa, babban ɗan yatsansa da yake share mata hawaye ya ɗaura akan laɓɓanta da faɗin, “Shiiii!!. kisa a ranki zaki sanshi, bana buƙatar sake ganin kukanki, Ni Jawaad Abdul-aziz yusif insha ALLAHU zan gurfanar miki da shi a gabanki kan gwiyoyinsa, abinda yake bibiyar kuma zan tabbatar masa da yafi ƙarfinsa har abada a wannan daren”. Ya ƙare maganar da manna bakinsa saman nata batare da ya sake bata damar magana ba. Duk da yana tausayinta bazai iya barintaba, wani irin shauƙi da zumuɗin kasancewa da ita yakeji, ji yake tamkar ana ingiza zuciyarsane akanta, jiyake idan bai kasance da itaba a wannan daren kamar zai rasa komai ciki harda ita kanta, tun yana sarrafata da tunanin iya ƙaramin wasa ya barta har hakan yaji bazai yuwuba, zuciyarsa ingizashi kawai take na kaiwa ga ƙololuwar martabarta…………….✍11
😜Saura kuma naji wani yay gulmar Jay ehe😣🤐🤣🚶🏻.23
Barkanmu da dawowa.
A ranar asabar an samu kuskuren ɗakko page daga telegram zuwa WhatsApp, wadda tayo copy ɗinsa daga can bata ɗauka a jereba kamar yanda page ɗin yake, shiyyasa tallan zafafa goma ya koma tsakkiyar page, wasu sai sukai tunanin ƙwai cikin ƙaya ake talla wai. To ba haka baneba, dan ranar kam masu sai da zafafa goma saida kuka tsiyayar musu da man kansu tas🤦🏻😑 saboda kira. Waɗanan buks ɗin goma namu sune nake talla gasu ga mai buƙata dan karku bari a baku labari inhar kasan baka karantanba dan duk sunyi lagwadar daɗi aradu🚴🏼👇🏾 .11
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI…
GUDU DA WAIWAYE….
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za’a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.13