MIJIN BUZUWA CHAPTER B KARSHE

 MIJIN BUZUWA CHAPTER B KARSHE

Yau take son ta gwada abubuwan da aikin boka dan Ondo wanda ya ja mata kunne da gujewa aikata kuskure tace zata tsare in sha Allahu.

   Ya shigo bai jima da dawowa ba ya fada wanka Nafisa ta shigo dakon kai tsaye tasamu yana ban dakin gurin wanka nan ta zauna a bakin gadon cike da jiran mijin nata.

  Ya fito daga ban dakin ta taso ta karbi duk wani abinda yake ma jikin shi tana mai gama daga goge jiki da shafan mai da saka turare da sauran su.

   Shidai ido kawai ya saka ma ta yaga iya gudunta don zuwa yanzu ya fara gano shirin ta sam bai yarda da wanan abinda take mashi ba .

  Ya gane sai tana son abu take mashi ladabin shegu a lokacin yake miji da zaran ta samu abinda take so shike nan ta koma ma halinta na I don’t care da ta saba dashi.

  Zama yayi a bakin gado yana jiran yaji ta inda zata bullo mashi ta dan yi dariya tare da karasowa wurin shi ta zauna itama.

  Sai bayan ta zauna ne tace samad a ranshi yace nasan da wanan kan tace wai yaushe ne zamu tafi shopping ga ciki ya fara girma haka ?

  Yayi mata kyar da ido sai kuma ya sake guntun murmushi a fuskan shi yace ban san da wanan maganan ba ai.

   Ita ko tayine don tana ganin shi ne zai fi saka shi farin ciki har ta samu ta sake da ita ta aiwatar da nufinta gare shi sai kuma taji sabanin hakan a bakin shi.

  Sai ta dan tsuke fuska tare da fadin gaskiya ya kamata ace ka shirya wa tafiyan mu zuwa yanzu don kada nazo nayi nauyi da yawa kace ba zan fita ba.

   Abdulsamad ya tsura mata ido yana mamakin rigimar Nafisa yanzu bata aje kanta a kusa ba shi kayan bany ko a nan gida Nageria za a samau su ai.

  Ya cikin daure fuska kin fi kowa sani komai nake so zan iya odan shi a dan kan kanin lokaci ya iso gare ni ballanta na babu dan da aka haifa a gidan nan da na fita waje na sayo mashi kaya.

  Ranta ne taji ya baci don may zaya danganta sauran diyan shi da abinda ke cikin ta a yanzu da ta san tafi karfin kowa ma nashi.

  Shikan gado ya hau yana gyara kwanciyan shi don yasan ba tayin abinci zai samu a gurinta ba duk dako yana son saka wani a bakin shi yanzu.

  Nafisa kuma bataji dadin haka ba don tana gani idan ta kyale shi bazata samu yadda take son komai ya tafi ba har ya sadu da ita don ta riga ta shafa maganin da boka ya bata tayi amfani dashi.

  Tabo shi tayi tana kwantawa a jikin shi da sauri ya juyo gareta yana fadin barni banda lokacin aiwatar da wani abu yau a tsakanin mu.

   Tace aiko tunda ni ina da bukatan ka tare dani dole zaka daure ka biya min bukatana haka nan yasan ta da son ya kusance ta akai akai wanda a baya yakan biye mata.

   Kara kwanto mashi tayi ya kara daga ta ajikin shi karo na biyu yace ki barni please na fada maki ina bukatan kasancewa ni kadai ne duk iya nacin ta dole ta barshi tafita kamar zatayi hauka take jin kanta a lokacin.

  Ta jefeshi da harara ya karkace kai yana mamakin tace ba laifin ka bane tunda kai kana fita waje yanzu kana samun inda ke sauke nauyin ka acan.

   Sheri zaki min yau kuma Nafisa tace amma kasan baka kyauta mi ba nima idan kai min haka yau don ina bukace dakai a yanzu yace ki hakkuri nace yau ba zaki samu ba ya gyara kwanciya yana fadin hakan.

  A yadda ta rude sai ta bashi tausayi amma bai iya aiwatar da komai a yadda yake jin gabanshi yana faduwa mai.

  Jin fitan ta a fusace bayan ta gama mashi mita ta fice daga dakin ya girgiza kanshi ya gyara kwanciyan shi sai barci acikin barcin ne yayi mafalkin mara dadi da Nafisa wanda ya tayar mashi da hankali.

   Tunda ya falka bai koma barci ba tunanen mafalkin da yayi ne ya tsaya mashi a rai mikewa yayi ya dauro alwala ya gabatar da sallah tare da samun sauki alamura a gare shi kamar yadda mahaifan shi ke koyar dashi ko wani lokaci.

   Washe gari ta tashi gaban ta yana fitar da wani irin kaikayi dake damun ta sam bata kawo cewa aikin boka da ta sakane ya jawo mata hakan ba.

   Tunda ya watsa ruwa ya fito yana shiri zuciyar shi cike da tunanen abubuwan da suke faruwa dashi ya yanzu din.

   Sai da ya biya dakin ta ya dubata kamar yadda yayi mafalkin a haka ya samay ta tana ta faman da soshe soshe don kaikayin dake damun ta.

  Yace may ke damuwan ki haka ne kike wanan soshe soshen haka cikin bacin rai tace dama ai haka kake so dani tunda na bukace ka kashere ni.

  Banga dalilin da zaka daukoni karabo ni da kasata ba kazo yanzu kana nuna min gazawanka a kaina inda take shiga banan take fita baya ya ciki da irin kalaman da take fada mai.

  Hannu ya daga mata tare da fadin ya isheki haka na kada kine me ki fada min maganan banza an fada maki ni banda abinyi ne sai na kwanciya da mace kullun  , ?

   Kallon shi take da mamaki don bata dauka zai fada mata wanan magana haka ba yace kinje kinyi biye biyen ki kin dauko wa kanki cuta kiike son aza min.

  Kuka ta saka mai tan

, aza mai  kururuwa bai kulata ba ya fice daga gidan kai tsaye kukan ta ne ya jawo hankalin yan uwanta gare ta suka shigo dakin.

  Har yaje office bai iya tsinana komai ba da yamma koda ya dawo ya samay ta a hargitse ya dawo har ya dade ta bishi dakin shi ta samu ya fito wanka yana daure da dan karamin tawul a jikin shi.

 Tunda ta shigo mai daki ya dago ido ya kalleta ya kawar da kan shi gefe daya yaci gaba da abinda yake yi din tazo gaban shi tace.

  Allah kuwa sai ka fada min abinda yasa ka tsiro yimin wullakanci haka ko dan kaga ina dauke da ciki ne a jikina yanzu yasa har kake guda na.

  Ya jefeta da wani muggun harara har sai da taji tsoro ta dan ja bays kadan yace look Nafisa idan dan dai kina son mu zauna lafiya dake sai kin aje kanki a matsayin da na dauko ki a gidan nan na mata.

   Macen kwarai itace wace ta san damuwar mijin ta da cin shi da shan shi da gyara mai makwacin sa da sauran su.

  Amma duk ke baki san yin wanan ba sai dai kici arziki ki wadatar da yan uwan ki ba tare dani kin dubi nawa da komai daya shafe ni ba.

  Don haka kodai ki gyara halin ki ko kuma in karo wata a gidan nan ku zauna tare wacce zata dinga kyautata min.

 Ya na kaiwa nan yaja dogon tsukiy ya dauki key din motar shi ya fice dakin ya barta tsaye tana kurma ihun bakin ciki.

   Wanan halin da Nafisa keyi wani lokaci kamar zautata sai daga baya kuma idan ta samu abinda take wa haukan ta dawo ta gyagije kamar ba ita ba.

   Iyanzu ya fahince ta idan tana bukatan abu bai mata shi ba babu sauran zaman lafiya a gidan tsakanin ta dashi shiyasa da zaran ta bijiro da bukatatun ta yake saurin biya mata akan lokacin.

  Wanda ita kuma take ganin aikin bokayen tane da mahaukacin son da yake mata yasa yake biya mata bukatanta a haukace kamar ba gobe.

   Wanda tayi believing da  baka da malamai ta ne aikin su yake ci a gareshi da kuma kyau da zati wanda take gani dashi take rudan shi ba zai taba samun mace kamar ta a cikin matan hausawan Nigeria ba sai dai kalan matan mu na nan.

  Burin mazan Nigeria ne su malki mace mai kyau koda bata da hali na gari adai ce matar shi ta gwada wa tsara ne a gari.

   Bata san Nigeria akwai wanan akwai kuma la,akari da ilimi tare da wayen mace da tarbiya ga mazan da suka san kan su.

   Yau ma kamar jiya tashigo mai tana bukatan su kasance tare amma fir yaki amincewa ya biya mata bukatan ta kamar jiya haka ta wahala da wanan dan banzan kaikayin na gaba da tadamay ta.

  Yanzu kan ya gama sakankancewa a ranshi mafalkin shi gaskiya ne inda ya ganta dauke da wani mugun abu tana goga ma gabanta.

   Washe gari har ya shirya bata tashi ba daga barci tana ramuwar barcin da bata samu tayi ba a daren shiya tsaya ya tayar da ita cike da tsanar halin ta na rashin son yin ibada.

   Idonta da sauran magagin barci bai gama watsakewa ba tace har ka shirya fita ke nan yace idan ma ban fita ba wani abin zaki min ne tunda ba abin kari zaki hada min ba.

  Cikin bacin rai ga maganan shi tace ba muyi wanan alkawarin da kai ba na cewa nice zan dafa ma abincin da zakaci na dauko masu dafa ma kace basu iya ba don haka banda matsala ga wanan.

  Yace yana daukan jakar Laptop din shi tare da sabawa a kafadan shi Nafisa zakiyi nadaman wanan maganan da kike fada min don ya zama dole idan baki canza ba in dauko wace zata bani kulawan da nake so a gidana.

   Maganan shi Ya bata mamaki kwarai don bata zaton zai iya fadin wanan magana a gabanta ba kai tsaye  sai gashi yau yana fada mata da bakin shi wai zai dauko mai kula dashi a gidan.

  Wai ina kudin da take narkawa malaman ta yake shiga ne haka gashi ta dalilin bin bokaye da malamai dasa gaba yanzu ta daina kai kudin da suke kaiwa gida duk wata ana amfani dashi.

  Ya bata mamaki kwarai ta samu ta danne zuciyar ta don ta san yanzu akwai sauyi a tare dashi ta dago ta kalleshi yana shirin fita daga dakin.

  Fuskan shi a daure yake har lokacin gabata ne ya kara faduwa sosai dole sai ta hada da kissa da kisisinan mata yanzu.

  Tace kayi hakkuri don naga yanzu magana kadan sai ka dauki zafi dani haka yace ai kece zan bawa hakkuri keda ban san na dauko ki kawai ne gidana don ki ji dadi ba.

  Ta sada kai kasa tace ba laifina bane ka sani don ba girki zan iya yi yadda kake so ba bai sake yin magana ba yaci gaba da shirin shi bayan ya gama ne ya dago ya kalle ta yana fadin ki tashi ki sallah don lokaci ya gama kure maki ko.

  Ya fice daga dakin bayan ya gama fadin haka bishin shi tayi da kallo har ya bacd ma ganin ta sai lokacin ta saukar da ajiyan zuciya.

  Tace lalai da sake ya zama dole ta canza halin ta idan ba haka ba wankin hula zai iya kai ta dare wanan wani irin mutum ne da magani bai saurin kamashi.

   Shin shi ba kamar sauran mazaje yake bane da take jin mata na hiran yadda suke samun kan maza je nasu suke juyasu ne ?

  Yazama dole duk wani abu da zatayi taga ta samu ya sauko kamar yadda malam yace ta bi komai a sannu kada alamarin ya juye mata gashi ko taga abubuwa na shirin juyewa da ita.

  Wai shin ko da gaskiya ne asiri baya kama mutum idan mace nada ciki ko ta haihu dole ne ta jirkinta har ta haihu ta bishi a yadda yake so ta nuna mashi ta kwanta yanzu.

   Alaadan shine idan ya fita office zai mata kira uku ko sama da haka amma sai take ganin sabanin haka yanzu tun yana mata kira daya har yakai yau ya bai kirata ba ki daya.

   Haka yasa ta fara zargin dama dalili yake nema da ita ai sunsha yin fiye da haka dashi amma bai sa ya daina kulata ba sai wanan kawai zai dauka da zafi haka.

  Har tayi wanka ta fito falo wurin yan uwanta da ta samu suna shayen shayin su bata daina tunanen halin da take ciki da mijin ta ba.

  Gaida ita suka farayi ciki harshen buzaci tana karba masu da kyat yanayin ta ya nuna ba ta cikin dadin rai.

  Yar dattijuwa daga cikin su ne tace yau ba zaki fita bake nan ta amsa tare da yamutse fuska tana fadin ba inda zanje yau suko sunfi sin tana fita a gidan don sun fi sake jiki suyi yadda ransu ke so idan bata gidan.

   Matar tace yanzu ya kamata ace kin fara natsuwa guri daya saboda cikin ki da ya fara girma don kina bukatan hutu.

  Ta dan lumshe ido tare da jan tsoki ta dafe kan ta tace wani irin hutu Yanyala,  ni da abubuwa suke son rikewa a gidan nan yanzu.

  A lokaci daya suka zaro ido tare da mayar da hankalinsu gare ta suna sauraren ta tace ya zama dole dukkan ku ku gyara a gidan nan.

   Yace mun bata mashi gida bamu gyara ba ai mai girkin da na dauko ku da sunan masu aiki a gidan saboda haka nake son kowa ta dan fara aikin ta.

  Yanyala ta fidda idanuwa waje tana mamaki tace garin yaya har kika bari haka ya faru a tsakanin ku tace wallahi ke ma shedace ina iya kokarina don ganin haka bai faru ba amma hakan bai samu a gare ni.

  Yanyala tace gaskiya ya kamata ki fara tura kaya gida tun yanzu ko za a watse dai kin riga da kin debi rabin ki ko ke.

  Dama bazan Nigeria ai basu da tabbas ba kowane ke kamuwa yadda ake so ba don haka muke daukan su kamar wurin cin kasuwa a gare mu.

  Don ko da kasuwa zata watse dan koli yakasa ya kwashe rabon shi nan dai sukai ta shawaran abinda zasu yi akan sauyin da ta ke gani ga mijin nata yanzu.

   

 Idan da sabo na saba izuwa yanzu haka kawai zai zo ya dauke ni a mota sai dai mu zagaya gari ya dawo dani ya aje ya wuce makaranta.

  Yau ma da yai kwana biyu bai zo inda nake ba komai na tafiya a guri na normal sai dai zan iya cewa haduwa na dasu ya bude min wani sabon babi na rayuwane.

  Duk da nake yarinya kuma mace ban yarda na fara hurda dasu ba sai da na karanci rayuwan su nagane zama dasu ba yana nufin jefa ni a gurbataciyar rayuwa bane.

  Yauma ina daki kwance ni kadai ina nazarin wani littafi don sabon da nayi da yawan karatu sai dai ance sabo turken wawa ne don har na dan fara shiga damuwan rashin ji daga gare shi kwana biyu.

  Waya na da yai ringing na juya ina kallon mai kirana a lokacin ganin sunan shi a screen din wayan yasa na dan sake murmushi sai da naja mai aji na dauki wayan.

  Da sallama na fara magana ya amsa min yace kina hostel ko kina cikin makaranta ne nace ina hostel yanzu fito ina waje yace ya kashe wayan shi.

  Na shirya cikin wani dogon riga mai dan hannu shara shara riga yana dan matse kadan daga saman shi kasan shi a bude.

  Kai tsaye daga inda yake zaune a motar yana sana,an shi na hango shi cikin motar ya mayar da hankalin shi sosai ga abinda yake yi.

  Tun da ya dago kai ya hangoni tafe ya daina abinda yake yi ya tsura min idanuwan shi masu kashe min jiki da zuciya haka ya sake min su tankar wanda ya samu tv har na iso gare shi.

  Daga waje na gaida shi kamar wanda baiji ni ba yayi sai bude min motar yayi da alaman in shiga kai na daga na kalle shi carab muka hada ido dashi.

  Nan nace dashi karatu nake fa yallabai ka kirani yanzu  yace shiga mu tafi na sani ai.

  Tambayan shi nayi da ina zamu tafi tare da kashe shi da idanuwana dasu ke rikitashi idan ya kalla.

  Sayar dake zanyi yace murmushi nayi nace ai dako kayi babban kamu yau galleliyar yarinya kamata ba karamin kudi zaka samu ba ko.

  Nace yanzu ya kamata ace kana wurin aiki ka ko gida kana hutawa dan murmushi ya sauke tare da fadin.

         Bazan iya zama gida ba ne yanzu.

   To ka koma office yanzu mana tunda lokacin aiki bai kare ba don nima karatu nake yi yace don Allah ki shigo mu tafi kona fito na daukeki in sa a mota.

  Nayi saurin nuna kaina nace ka dauke ni sai kace wata yar tsana ko matar ka can da zaka dauke ni.

  Don Allah shigo mu tafi kin sa mutane suna kallon mu na dan juya naga wasu yan mata dake gefen mu sun kura muna ido.

  Dole na bude motar na shiga ya tayar da motar muka bar gurin sai da mukai nisa ne naji yace may yasa duka mata wani lokaci halin ku daya ne wai ?

  Na bata fuska tare da dan kallon shi nace haba mijin buzuwa da alama yau baka cikin dadin rai kake hango matsalan gidan ka ga kowa.

  Kada ka danganta abinda ya hada ka da matar ka dani don bai shafeni ba ko kadan yanzu ma banga abinda nayi da zaka fadi haka ba.

  Yace nima ban san dalili  kawai dai ina hango hakane gun ko wace mace kamar halinku duk dayane wani lokaci.

  Nace baka canka da kyau ba malam ai kaji ance mata suna suka tara .

   Ya kalle ni ya girgiza kai yace bazan iya tabbatar da haka ba sai na gwada don naga biyu halin su daya basu damu da damuwan mutum ba kansu kawai suka sani da son abinduniya.

             Wow i am impress dama haka ka dauki mata a ranka ashe ?

 Yes sai dai ban sani ba ko kamar yadda kika fada inke din ta daban ce  don na dan ga alama haka.

   Shiru mukayi duka a motar sai can yace cikin langabar da kai please khadija kiyi hakkuri ki fahince ni don yanzu bani da zabi sai wanan tunanen.

  But sai dai ban san may yasa ba nake yawan son in kasance a tare dake muna irin wanan tafiya tare da shammatan junar mu.

   What na fada cikin mamaki da rashin fahintar maganan shi tare da fadin me ye maanar hakan a gare ka may yasa sai nice zaka ji dadin fada dani ranka yai maka dadi.

  Don haka kaje ka dauko ni a lokacin da nake a tsakiyan karatuna don kawai son fitina kace wai kana son muyi ta shammatan juna kana jin dadi.

  Murmushi yayi yana fadin bazaki gane ba ne khadija hakane kawai farin ciki na a yanzu a take na daure fuska tare da fadin maidani inda ka dauko ni don Allah.

  Haba mana khadija may kike fadi haka ke nan baki bukatan ganin farin ciki na ne komay yanzu fa kika gama fadin mata suna suka tara da bakin nan naki.

   Nace da ban dauka farin ciki kaka samu daga yin haka da nake maka ba ai na dauka bacin rai nake sakaka.

  Hummm yace sai ya juyo ya kalle ni yace to indai ina da wani matsayi a gare ki yanzu dai ki zauna mu tafi.

  Ba yadda na iya haka na koma na zauna tare da kawar da kaina gefe daya yace yanzu na fara sanin ashe suna kuka tara.

 Tunda gashi na roki alfarma a gurin ki kin yi min abu biyu ke nan na fahinta a gare ki yanzu zaman mu tare da ke.

  Nace wanan bata min lokaci na kawai kake son yi a banza bayan kasan ina da abinyi a gaba na yanzu.

  May yasa zan so bata maki lokacin ki haka bayan nafi kowa sanin amfanin abinda kike yi yanzu.

  Yanzun dai mubar wanan magana may kadauko ni yi a yanzu ne don Allah na tambaye shi tare da kura mai ido ina son jin amsa na.

  Wanan lokacin da wanan yanayin yafi min ko wani lokaci jin dadi a rayuwa na yanzu matukar ina tare da ke khadija.

  Kece mace ta farko da nafi jin natsuwa idan ina tare da ita khadija ya juyo ya kalle ni tare da fadin kin san may yasa nace haka ?

  Kai na girgiza mai cikin sanyin jiki alaman ban sani ba sai ya fada dai zan sani daga gare shi.

   Yayi murmushi ya kalleni yace kin san yadda zakisa zuciyar mutum ya sake ba tare da an rabu cikin bacin rai ba khadija.

   Ina jin dadin hakan da kike min ke ta daban ce da sauran matan zan iya yarda a yanzu saboda wasu dalili da na kafa akan ki.

  Wani dalili ne haka na tambaya da sauri tare da kallon shi yace baki taba rokona wani abuba khadija alhali nasan kina da bukatan abubuwa da dama tunda kin san ina da halin shi.

   Na nuna kaina nace ni in rokeka kuma akan may zan roke ka bayan nasan rabo ne idan rabona ya ratsa a kan ka zaka bani ko ban roka ba.

  Good girl tafiya zatai dadi a tare dake kuwa tunda kin san haka she nayi saurin fadin ashe kai marowaci ne ke nan ga mata ?

  Ya dan lumshe ido yace ko daya wallahi na dai fi son inyi abinda ba sai an roke ni bane sai dai ina haduwa da matan da basu da hakkuri ne khadija.

  Ban san lokacin da baki na ya bude ba nace kana nufin har da anty Fati haka take yaushe ma ta samu gurin roko a wurin ka kai ?

   Ya na tukin shi hankali kwance ya murmusa yace kin ga yanzu ma kin fada da bakin ki yaushe na kula ta balle ta samu tambaya na ?

   Haka kowa ke gani khadija shiyasa manya sukace tsakanin miji da mata sai Allah wanan abin na bar wa kaina sani kawai.

  Daga ya mayar da kanshi ga titi yana ta tuki a hankali tare da shakan isakan dake kadawa a lokacin may hade da kamshi kasa wanda ke nuna dama na son sauka a lokacin.

   Ba wani guri mukaje ba sai yawata garin da mukayi kawai ya dawo dani hostel ya aje ba tare da na tsaya ba na shige kai tsaye yaja motar shi ya tafi.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

          SEENABU

Mommy wayayir mace mai haba haba da jamma irin matan nan ne masu fara,a a fuskan su kuma ita har cikin zuciyar ta haka take da kowa sai dai bata daukan raini.

   Abin ta bai rufe mata ido ba tana da ilimi na boko wadattace don duk matan na Abban su Abdulsamad suna da ilimin su ya aure su in ka debe ummi wace iyakarta secondary kadai tayi har hajiya mama mahaifiyar Abdulsamad a gidan shi ta hada karatun ta na NCE wanda dama koyarwa take koda ya aure ta.

  Ita anty amarya ma da aikin ta ya auro ta wanda yanzu ta daina duk ya hana matan nasa aiki ya tsaya ga bukatun su kuma.

  Mommy ne zaune tare da Abban yana karyawa hajiya mama wadda yaranta ke kira da hajiyan mu ko hajiya mama ta shigo falon.

   Akan maganan tafiyan mommy da Abdul din ya bugo yana mata tuni a daren jiya don sun fara tatauna maganan sai Abban bai bada goyon baya akan haka ba.

  Yanzu shine ta shigo ayita akaare idan zai yarda shigowan mama yayi daidai da shigowan hajiya ummi da anty Amarya data kira kaffinta shigo.

  Sun sami wurin sun zauna tare da fuskantar shi yasa yasan da magana sukazo mai ummi ce ta fara maganan amma sai anty amarya ta dan saka larin kishi a ciki tace ni naga ai ba sai taje ba ya mayar da matar shi mana zaifi sauki.

  Ummi da wanan kkaron bata goyi bayan maganan anty amaryan ba tace a a Sadiya tunda har kika ji wanan yaron ya bukaci hakan ai sai mu gode ma Allah da har wanan tunanen yazo mashi a rai.

   Ko ba komai ya kamata  ace sanin halin ita Nafisa  ya kamata wani daga cikin mu yaje ya zauna kamar yadda ya bukata din don ace mai daki shiyasan ida ruwa ke yoyo a dakin.

  Nidai kunsan ba lafiya ke gareni ba ba zan iya zuwa ba ita dai suwaiba din ya dace ta tafi don ita dai zainab din ya dace taje ta zauna dasu ta saka ido tunda da iyan bawa zasuyi tafiyan.

   Murmushi Abban yayi yace ke nan dai kun gama magana kuna goyon bayan dan ku ko ummi tace ba hakana bane Alhaji.

  Ganin dai dacewan hakan mukayi yasa muka goya baya ga maganan shi da kan shi babangidan ya fara tuntubana da wanan zancen da yazo na bashi goyon baya akan haka.

  Sai anty amarya ta kalle ta ta rausaya da kanta gefe daya bata kara magana ba har lokacin da Abba ya gama ja ma mommy kunne akan zaman da zatayi a gidan dan nasu.

   Suka bar mommy dashi a falon kowa ya kama gaban shi tun wanan ranan mommy ta fara shirin tafiya Abuja gidan Abdulsamad wanda suke kira da babangida kasancewa sunan mahaifin maigidan su ke gare shi.

   

   Abdulsamad bai fada ma Nafisa zuwan mommy ba gidan sai cin karen su ba babbaka suke ita da yan uwanta a gidan banza ta fadi masu kasa gasasa dama haka aladansu yake yar su ta auri mai arziki dangi su kwaso a taru aci arzikin ta.

   Mommy bata boye ma Anty Fati zancen tafiyan ta ba inda ta kirata ta fada mata da bakin ta tare da cewa zatayi iya kokarin ta taga ta shirya tsakanin ta da mijin ta kafin ta bar Abuja din.

  Allah ya kiyaye hanya Fati tai mata tare da cewa mommy amma fa sai kin hada da hakkuri don kun san Nafisa bata kaunar taga kowa ya rabi yaya Abdulsamad.

   Abinda yakai ni shi zanyi idan tayi ba daidai ba dole ne in fada mata gaskiya koda kuwa bata so dariya tayi don sanin halin Nafisa da tayi kamar yunwar cikin ta.

    Tsaye yake tsakar falon inda yake umartan masu aikin da ya shigo dasu da su gyara part din Fati yana masu kwatance yadda yake son gyaran.

   Nafisa da ke barci a dakin ta Yanyala ta shiga mata da maganar cewa may ke faruwa ne taga ana gyaran dayan part din da tace na uwar gidan ta ne.

  Kamar ba cikine a jikin ta ba ta diro saman gadon ta fito inda masu aikin su nan ta hausu da fada wayasa su aiki a gidan ta ba a fada mata ba.

  Daga bayan ta ya bata amsa yana saukowa daga sama yace nine nan maigidan na basu aiki suyi in biya su wani irin kallo mai kama da kai asuwa ta aika mashi.

  Bai tsaya kulata ba sai kokarin shiga dakin da yake yi tasha gaban shi da sauri ta tsare shi may kake nufi ne samad da wanan gyaran da akeyi ?

   Yace abinda kika gani Nafisa shi nake nufi don gida nawa ne ba naki ba kamar yadda kika fadi yanzu.

  Nan hankalin ta ya tashi sai ta fara surutu ita may yake nufi da ita da zai mata haka yace don yaga zata haihu zai dawo da fati da yaranta gidan shi.

  Tace nasan dama kule kulen da ake shiryama ke nan kake yawan zuwa kaduna akai akai yanzu dama ba so na yan uwanka keyi dani ba .

  Shi dai bai mata magana ba don mazan dake gidan suna aiki ya fita batunta basu raba hali a gaban su ba.

   Hankali tashe ta kira madam tana fada mata abinda ke faruwa madam tace kika sani ko watace zai dauko ya saka a dakin ba Fati ba ?

  Nan hankalin ta ya kara tashi sosai tace Nafisa dam wanan tunanen baizo min ba sai da kika tunatar dani haka yanzu.

  Madam tace to zauna nan kina fada akan fati wata tazo ta shige dakin kina gani saboda sakaci irin naki in zaki mike ki mike tun yaushe muka gama da wata fati can.

   Wacce hudi daya mukai mata muka fitar da ita a gidan har diyan ta sai tarihin su yanzu har kike tunanen ita zai mayar dakin ta.

  Ke kasar ku fa zaki koma aiki kaifi sai Niger nan kusa kafin ma mu dawo aiki ya kankama ko  mu huta da ko wacece ma ke son muna kutse haka cikin ruwan sanyi.

   Nafisa tace madam kin san ba zuwan ba kuma ba kudin nake jiwa ba don zan iya saida da duk wani kaddara da nake da akan wanan aikin tunda yanzu na rasa gane kan shi.

  Matsala daya ne shine mutumin nawa yanzu kin san matsi yake min tun wanan tafiyan da mukayi ondo ya kara burge min a gidan nan baya sake min har yanzu ga kuma lalurar cikin nan dake jikina yanzu.

  Madam tace ke dai kawai tawa ki nemi kudi in ma bai barki ba sai ni inje maki manene amfanin zaman mu tare da ba zan iya maki komai ba.

  Ai kawai ki daina damun kan ki mu za a gwadawa hanyar boka ko malam kuma ko latsandan ne gaba da lahira indai ana zuwa zamuje shi.

   Sai lokacin Nafisa tayi ajiyan zuciya taji dadi a ranta tana ganin aduniya bata da kamar su madam dake tsaye a kan ta yanzu.

   Tace uwar dakina Allah dai yaja muna nisan kwana tare ni nasan banda kamar ki a duniyan nan yanzu.

  Da wanan shawaran hankalin Nafisa ya kwanta nan ta shiga buga waya gida Niger ko an samu wani bakon boka ko malami mai tashe a kasan.

   Sai da ya ga komai ya kankama yadda yake so ya bar gidan bayan ya sallami mutanen da sukai mashi aiki duk da yawan samari yan uwan Nafisa a gidan ba wanda zaiyi bugun gaba dashi yayi mashi aiki alhalin biyansu yake duk wata dasunan aiki suke mai a gida.

   Bayan kwana biyu su mommy sun gama shirin su tsab ya tura Yusuf ya dauko su zuwa garin Abujan mommy a gutin hajiya mama ta bar yaran ta tazo ita kadai sai iyan Bawa da suka zo tare da wata yar mai masu shara budurwa don taimaka masu da wani abin.

    Mommy sunyi waya da Ya Amina tana sallaman ta tace zata gidan Abdulsamad wanda matar shi watan haihuwan ta ya kama zasu dan kwana biyu acan .

  Ya Amina sai sulbul da baka tayi tace mommy ashe zaku hadu da Khadija na ke nan mummy tace banda abinki khadija dake makaranta ina zan ganta ni ?

  Sai dai idan sawa zanyi a dauko min ita ko akaini in gano maki lafiyan ta idan na samu lokaci dariya kawai ta Amina tayi don ta san gidan su Abdulsamad basu san komai ba a tsakanin mu dashi.

   Tafiyan rana sukayi don haka sai da yamma lis suka shigo garin Abuja din direct gidan shi suka nufa yana gida a lokacin don yana dakon zuwan su.

   Nafisa wace ke falo tana shan iska ga yan uwanta a kewaye da ita kowa na shaanin gaban shi sai sallaman su mommy da su iyan bawa suka ji .

   Gaban tane ya fadi da ganin su mommy din gidan don bata taba zaton zuwan su ba don a wautan Nafisa ta gama da kowa nashi yanzu babu mai marmarin zuwa inda yake.

   Zuwan su mommy ba karamin faduwan gaba yasa ta ba sai take ganin ai zancen auren da take zato ko dawowan Fati gidan gaskiya ne.

  Shiya fito daga daki bayan sunyi waya da Yusuf ya sheda mai sun iso ya fito da yar fara, a a fuskan shi yayin da ko kallo su mommy basu ishi Nafisa da yan uwanta dake falon ba .

  Shi da kanshiyayi masu iso dakin da zasu sauka din bayan dun gaisa sun mashi yaya gida ya fito tare da Yusuf da ya shigo da kayan su ciki da taimakon wani saurayi.

   Falon ya dawo inda suka samu Nafisa da yan uwanta sun juye harshe cikin yaren su na buzanci suna maganan zuwan su.

   Fuska a daure ya kalle ta yace Nafisa baki san mommy bane da gwago na iyan bawa da baki tare su da zuwa ba ?

  Tace a yatsune na san su mana ba matar mahaifin ka bane ita yace OK cikin wani irin kallo har ya fara tafiya sai ya juyo yace tunda kin san ta kin san kuma matar mahaifina ne baki iya taron su ba nima haka ban son in fita yanzu in dawo in samu wa yan nan yan uwan naki a gidan nan yanzu.

  Yana fadar haka ya juya ya fara tafiya tace wallahi baka isa ba don zuwan su zakace yan uwana su bar maka gidan ka yanzu yace zaki san na isa idan yan sanda dun shigo sun fitar min dasu.

  Idan akwai abin da yan Niger sukaki jini shine dan kakin Nigeria don basu yi masu da wasa idan sun farmake su.

  Nan Yanyala ta fara magana tace haba Allaji ai bin baikai can ba daga dan wanan magana har zaikai ka kira muna polizawa kawai dai jira muke su huta mu mika masu gaisuwan mu.

   Ya fice zuwa nemo ma su mommy abinda zasu ci a gidan don yasan ba zasu iya taba cin abincin da suka dafa ba.

   Bai dauki lokaci ba ya dawo dauke da ledoji iri na restaurant dauke abinci dasu ruwa a ciki ya bayar aka shigo masu dashi har dakin.

   Mommy ta idar da sallah sai ga yaron shi isyaka yana shigo da kayan ciki tare da gaba tar masu da abincin.

  Sunka ce har da dawai niya zuwa sayo abinci kuma nan dai iyan bawa ta kasa hakkuri tace zainabu may kika fahinta ga wanan zaman ?

  Murmushi mommy tayi tace ke dai iyan bawa ai ayi shani kawai wai ancuci na kauye wanan matar bata da hali ko kadan.

  Kin dai fara ganin makasudin zuwan mu garin nan ke nan don fitar shi kunyan abokan shi nasan halin matar nan tashi dakilace na gani a fada.

  Ba zamu sakar mata fuskan da zata kawo muna raini ko wulakanci ba don nasan tun zuwan mu batayi farin ciki da ganin mu ba.

  Sunci abinci sun huta sai ga Nafisa ta shigo tayi wanka ta saka sutura a jikin ta yan uwan ta suna mara mata baya suka shigo dakin.

   A falo suka samay su nan ta ja ta tsaya bata zauna ba tana fadin kunzo lafiya ya hanya da mutanen gida ?

  Mommy tace lafiya duk suna gaida ku yaya nauyi Allah ya rabaku lafiya tace amin sauran suka shiga gaida su da yi masu ya hanya suka fice daga dakin ba wanda ya zauna.

    Shiko bayan ya mika sakon wuri na ya nufa kamar yadda ya saba zuwa man  koda ya kirani muna tare da maryam da zarah a dakina kiranshi ya shigo min.

   Mutumin ki ne halan yazo maryam take tambayana nace cikin tabe baki shine ai kin san bai tashi zuwa min sai wanan lokaci.

   Maryam tace ai kuna daidai dashi in kin isa ki fadi a gaban shi yana da amsan baki indai wanan yaya in love din kine.

  Kai maryam kina da wuyan sha,ani wallahi na fada maki ba soyayya a tsakani na dashi sai amin taka kawai na damuwa.

  Zarah ta dago kai tace min wani guy kuke magana muje in gani idan ya min in saka shi a layi mu shiga sha,ani dashi.

   Zarah wai ke baki jin kunyan fadin fitsrane haka tace in banda abinki wake ta wani wasa da so yanzu khadija bari kiyi wasa da daman ki yanzu yan jami,an nan suyi maki wuf dashi.

  Idan banda abinki an fada maki kowane yan matan jamia ke iya wuf dashi kai daya zarah wanan ya wuce sanin ki wallahi.

   Dariya tayi tace muje inga guy din nan dai da kuke wani zuzutawa haka dai murmushi nayi kawai don ba zan so a ganni da ita ba.

  Duk da ba wani shiga na yi ba amma suna ta yaba kyau da nayi wai na hadu zarah na fadin ashe zaki zama yar hannu haka khadija.

  Tare muka fito dasu sun zo su gaida shi tunda muka tunkare shi zarah ta tsunke da ganin motar da yazo da ita tana fadin tun ban ga guy din ba wallahi nasan zai hadu ko don motar nan da nagani how lucky you are da kika iya canko wanan zukeken guy haka.

   Mun iso yana ta faman ansa call a wayan shi sai da zarah ta kare mai kallo ta dago bayan ya gama wayan suna gaida shi bai wani sake fuska ba ya amsa gaisuwan.

   Tare da kawar da kanshi gefe daya zarah tace dama na sani sai irin wanan guy din khadija wanan jan ajin naki yayi yawa wallahi har ta gama ta wuce bai yi magana ba suna shiga maryam ta nufi dakin ta.

  Maganar shi ta farko bayan wucewar su shine ina kika samo wanan kawar kuma ?

   Nace a inda ka gan mu yanzu yace No ba girman ki bane da mutuncin ki yawo da irin wayan nan nace kawatace fa tare mukazo karatu daga gida.

   Na fada maki bana son in kara ganin ki tare da ita please na juyo ina kallon shi ido cikin ido nace tana da aibu ne komay ?

   Au ke baki ga aibu ta ba wanan bata da kamun kai ba girman ki bane yawo da ita nace ka taba ganin mu a tare ne ko yanzu ma daurowa tayi ka gan mu da ita.

  Har ya bude baki zaiyi magana sai kuma yayi shiru nima shirun nayi ba wanda yayi magana daga cikin mu.

      

 Can naji yace idan na fada maki wani abu zaki yarda dani ?

             Zaki yarda gaskiya nake fadi.

   Murmushi nayi nace idan maganar ta kama gaskiya mai zai hana nayarda tunda nasan gaskiya ka fada.

  Kin yarda dani khadija ?

    Nace na yarda dakai mana yaya Abdul fati da mijin buzuwa ina fadi ina mashi dariyan shakiyanci cikin gatse.

  Shima murmishin ya dan yi wanda sai wanda ya sanshi zai iya fahintar hakan daga gare shi yace  kin san kamun kan ki yasa muke tare da ke har wanan lokacin.

    Kasan ni ne da zaka wani ce ina da kamun kai    bayan iyakar mu dan wanan haduwan da muke yi.

   Na tsinci muryan shi yana fadin niko na sanki khadija you are classic baby da na taba haduwa da ita a rayuwana.

  Katse shi nayi da fadin may ke faruwa daksi haka ne wai ke irin wanan magana yanzu a kai na ko last zuwa da kayi haka ka dinga min wanan maganganun.

  Ya girgiza min kai tare da fadin ba komai cikin lumshe idanuwa shi sai kuma ya bude su ya sani gaba yana kallo na.

   Shirun motar na kawar da fadin yau ba fita ke nan yace ina kike son muje nace inda ka saba zuwa mana mu zaga gari kawai kana barnan man motar ka.

  Haka kika dauki fitan namu dama nace hakane mana tunda ba wani guri muke zuwa ba.

  Ke ce baki fahinci muhinmancin fitar namu ba kila amma ni yana da ma,ana masu yawa a gare ni matuka khadija.

  Don kasan cewan mu a tare you have change me  now na fahinci su abubuwa da dama da ban taba fuskantar su ba a baya.

  Maganan gaskiya yau kin dawo min da farin ciki rayuwana har iyayyena sun zo gida da sunan kwana biyu a wuri na.

  Da sauri nace cikin murna wai da gaske kake yi yace kwarai kuwa deeda don yanzu haka mommy da gwagona iyan bawa na gida maganan nan da muke yi dake.

  Taya kike ganin bazan maki godiya a wanan kangin da nake ganin kin fitar dani wanda a da nake dauka da shirmay irin naki na yara kike yi.

   Sun kuyar da kai nayi kasa ina tunane hankalina yayi nisa bani jin abinda yake fadi tsoro na daya ne kada mommy tasan ina tare dashi ta fasara haduwan mu a wata manufa.

   Ban sauri maganan shi ba na katse shi da fadin zan roke don Allah kada ka bari mommy tasan kana zuwa inda nake don bansan da wani ido zan kallesu ba har hajiyan ka.

  Ya lura da irin rudewan da na shiga sai dai baice min komai ba ganin bai yi magana ba yasa nace please yaya Abdulsamad ka boye wanan a matsayin siri a tsakanin mu don Allah.

   Kallo na yayi ya sauke murmushi yace saboda may kike son kada su san ina tare dake nace dashi wayyo Allah kana son su dauke ni yar cin amana ne ko may ?

   Cikin sanyi  murya nace kasan su ba zasu gane mutunci ke tsakanin mu ba sai su dauka muna tare da wani manufan da bashi ba.

  Hakan kuma yana nufi na ci amanan su ke nan gama yadda suke son Fatin ka a gidan yanzu kuma sai su gan mu tare yaya kake ganin zasu dauki abin.

  Kai tsaye yace zasufi kowa farin cikin da hakan na sani tunda sun san ki sun san halin ki zasu yi farin ciki da hakan.

   Daga yau magana ya kare ba sauran wani abu a tsakanin mu tunda bukatar mu ya biya ka shirya tsakanin ka da yan uwan ka.

  Mamaki magana na ya bashi yace juyo yana kallo na sai can yace ai deal namu bai kare ba tukun ko kin manta baki karasa aikin ki ba akan fati ?

   Na amsa da fafin kwarai bamu kai nan ba cikin takaici nace wana  kuma yanzu ya rage gare ka sai kasan yadda ka shirya da matarka.

   Ba wani sauran magana yanzu a tsakanin mu kuma na fada cikin tsiwa ya juyo da kyau ya kalle ni yace don mommy tazo duk kike fadan wanan magana ko may.

  No ba don tazo ba in ma don tazo din ne haka ne bana son su dauki abinda wani fassarane kawai.

  Ya zura min idon sa yana kallin yadda duk na rude yace a ranshi ashe karyan rashi  kunya nakeyi a da gashi yanzu daga jin mommy tazo duk na bi na birkice lokaci daya.

    Motar tayi tsit kowa da abinda yake tunane a ran shi sai da ya shafa kan shi naji yace relax deeda wace dake mommy zata san da wanan maganan dake tsakani  mu wai ?

  Wata zuciyane ta bashi shawaran ya min wayau kawai don yadda na rikece din nan daga jin mommy tazo zai iya sa komai ya faru idan ya biye min.

  Kawar da zancen yayi da fadin zuwa nayi ki ban shawara yaya zan yi da Nafisa don batai farin ciki da zuwan nasu ba yanzu haka.

  Da sauri na dago kai na kalle shi da idona da suka sauya kala nace baka fada mata zancen zuwan su bane dama , ?

  Kai ya girgiza min yace ban fada mata zasu zo ba tunda ba itace ta aje ni ba yan uwan ta dake zuwa ai ba fada min take yi ba itama.

  Kada kaga laifinta a yanzu don kai kai sake har haka ya kasance tun farko saboda tsoron ta da kake nuna kanayi da farko.

  Ba tsoran ta nake yi ba deeda kaunane kawai na tsakanin miji da mata wanda ita ta dauka tsoron tane yasa nake mata hakan.

  Sai yanzun kasan da wanan yana iya faruwa ka manta a lokacin da take saka abu kana mata  shi koda kuwa baka son abin ?

   Ya gyara zama yana fadin shine babban kuskure dana tabka a farko wanda nake nadaman yi  shi a yanzu haka.

   Duk abinda zakayi ko zatayi kada ka bari rainin matarka yakai ga iyayyen ka don ko zaka iya canza mata amma ba zamu iya canza iyayye ba.

  Wai ke wake koya maki wanan hikimar haka nr ya tambaya cikin son in bashi amsa nace baka son maganan ke nan.

  Yace No idan ban so ai ba zan fada maki zuciyana na ba a yanzu don da zuwan su abinda tayi masu yaci min rai sosai ba zan boye maki ba don yanzu ke ce abokiyar shawarata shiyasa nazo maki da zancen.

  Yaya zanyi khadija ina son in fita daga cikin dana shiga a bayane gida na yanzu bana son su mommy su fahinci sakaci na a gida na.

  Nace na yaushe kuma saidai kada a kara muma makwabta ku mun sanni balle su mommy dake gidan tare ku.

  Ina son mata na khadija shiyasa har haka ya faru da ni kallon shi nake cikin mamakin kalamin shi na wai yana son matan shi da yace.

  Shin shi wani iriin mutum ne wai nace nafisa dai kake so amma baka son fati kowa ma yasan da hakan ?

   Haka kuke tunane ya fadi cikin zafin zuciya amma ita ai tasan ina sonta halin ta ne kawai baizo daya da nawa ba shine matsalan mu.

  Kalon shi nake sororo kamar na samu tv da alama yarasa yaya zaiyi da damywar shi ne ya tsinci kanshi cikin fada min sirin zuciyar a matsayi  shi na mutum mai shekaru kamar shi.

  Tausayi ya bani don na fuskanci bayan Yusuf da suke tare baida wani wanda zai fada ma zuciyan shi ya fahince shi shiyasa yazo gare ni.

  Nace wallahi rayuwan ka na cikin hadari ya kamata ka koma ga Allah kayi abinda Allah yace shine kawai mafita a gare ka.

   Lokaci ya duba yace zai tafi lokacin sallah ya gabato zai dawo gobe tunda ba school mu karasa tataunawa mukai sallama ya tafi ya barni cike da tausayi  shi.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

            SEENABU

2️⃣4️⃣Gidan ya nufa kai tsaye tare da sayayyan da yayiwa bakin shi na abubuwan bukatun su ya nufi part din fati dashi.

   Babu kowa a falon sai yake mamaki yau ina mutanen gidan su shiga haka duk da basu ciki hakan bai hana falon nashi jin tashin yanayin da jikin su ke dashi ba a falon.

   Hakana har ya isa gurin su mommy zuciyar shi cike da tambaya da tunane ya samay su a zaune suna hira yarinyar da suka zo da ita tana cin abinci.

  Sai da ya aje kayan a gaban mommy ya zauna lokacin ya fara gaida su suna kara mashi yaya sula samay su yace mummy lafiya sai hamdala.

  Nan dai ya zauna dasu suka dan taba hira har wani lokaci sai ga Nafisa ta biyu shi har dakin dags kofa ta tsaya ta kira sunan shi.

  Bayan ya amsa kamar ba zai tashi ba sai kuma ya mike ya tafi sude su mommy kala basu ce ba suna kallon ikon Allah kawai.

  Ya fito ya samay ta zaune falo tana ganin shi ta mike da kyat ta fara fadin muje sama ina da magana dakai ne ta juya ta fara tafiya yana biye da ita a bayan shi.

   Ko da suka hau sama bai tsaya bin ta nata ba don har ta juyo da nufin tayi mai abinda ta kulla a ranta sai hango shi tayi yana bude kofan dakin shi kai tsaye.

   Ido ta bishi dashi tana fadin samad maganar nakira ka muyi zaka shige kuma yace baki san dakina bane ko a kan hanya kike son maganan da ni ?

   Sai lokacin ta dan juya ta dubu wurin da suke tsaye din sai kuma tayi shiru don ita bata ga komai a nan ba don sunyi magana ai gidan su ne.

   Dakin ta samay shi tsaye yana rage kaya a jikin shi ta fado dakin babu ko sallama ya dan juyo ta kalle ta ya kawar da kanshi gefe yaci gaba da abinda yake yi.

  Bayan shi ta tsaya tana kama baya tare da fadin Samad wai may wanan mutane suka zo yi ne a gidan nan ?

   Yaushe zasu koma don ban son sa ido da takura a gida na sai da ya gama cire kayan ya rage daga shi sai boxes a jikin shi yace cikin duban ta ina fatan wa yan nan mutanen da nace su bar min gida na yau sun bari ?

   Tsaye tayi sororo tans kallon shi ta shige ban daki ya barta a wuri tsaye tana mamakin yau wai itace samad ke ba amsa haka daidai da nata tambayan.

   Da dane da yanzu ya fara matairaice mata yana bata hakkuri akan zuwan su mommy din itako tana cika tana batsewa tare da kafa mashi sharudda dole ya bi ya juye mata makudden kudi yana lalashin ta.

  Yanzu ko da yake kokarin kwato kanshi daga sherin ta sai take ganin wasu ne suke kokarin bata mata aikin ta ta baya.

   Tunda ya shiga bayin taja kafanta ta zuwa bakin gadon dakin ta zauna tare da tin tagumi don ta fahinci ba maganar da zatai sanyi bane dashi sai da yanzu cikas din ta shine cikin da ke jikin ta don bai bari tayi yadda take so sam.

  Da mamaki samun ta wurin yake kallon ta da ya fito daga ban dakin don yayi zaton tuni ta tafi dakin ta ta kwanta sai ganin ta yayi zaune cikin damuwa.

  Samad wai may kake nufi danine yanzu da ke tsiro da wasu halaiya na daban da ban san ka da su ba a da don may zakace sai na sallami yan uwa na gidan nan ?

   Yace saboda ba gidan yar uwasu bace su bari idan kin kaiga naki gidan sai su kwaso gaba dayan su su dawo inda kike ba dai nan gida na ba.

  Da bakin ka kake fada min haka Samad yaushe ka tashi ga samad din da na sani mai so na da tausayina da son duk wani abinda nake so a rayuwa na.

   Da ke nan Nafisa a lokacin da ban fahinci koke wacece ba amma yanzu da na fahinta yasa kike ganin sauyi daga gare ni haka .

   Ban taba yarda da halin ki ba sai yau Nafisa da har mahaifa na zasu zo gida na ki tsare ni kina tambaya na wai yaushe ne zasu koma ?

   Alhalin ke ga yan uwan ki nan a gidan sun hana ni shakat dani da gida na ba daman in huta in samu natsuwa a ciki ga dan banzan kazanta da kuka bata min gida dashi ya koma wani iri.

   Samad mune kazamai dani da yan uwana kake nufi ko may yanzu ne kasan da kazantan mu din ko may yace da na dauka idan idon ki ya bude zaki daina Nafisa ashe abin ba haka yake ba a gun ki.

   Komai ai zaka iya fada a kaina tunda kaga yanzu banda moriya a gareka yadda kake so a da, da kake yawan naci a kaina da banda komai.

   Wanan ne tunanen ki ashe kike min yadda kikaga dama bakin ce in dauki matakin da zan dauka ki gani ba ranan to matakin ne yanzu na fara daukar wa kaina.

   Su mommy kuma da kika gani nan sun zo gidan nan ke nan harsai kin haihu kinyi arbain zasu koma gida.

   Ido ta zaro waje tace ina zasu zauna din yace a inda kika gan su and bari kiji idan naji wani rashin mutunci ya fito daga gare ki zan baki mamaki sosai a gidan nan.

  Mamaki ne ko rudewa ya kamata a wanan daren na Abdulsamad wanda take gani karfin haline irin nashi daya iya fada mata wanan magana haka babu ko dar a idon shi.

  Bai kara kulata ba ya shiga gyaran jikin shi ya barta zaune a gurin cike da mamakin shi fita yayi ya duba ko an rufe gidan ya samu ko ba a rufe ba shi da kansa yaja kofa ya rufe yasa mashi key.

   Washegari mommy da wanan yarinyar da suka zo mai suna Aisha bayan sunyi sallah basu kara kwantawa ba suka fito falon gidan suka gyara tas ta saka turaren wuta dana tsunke a ko ina na gidan.

  Take gidan ya dauki kamshi  da sanyin Ac kitchen suka koma sai da gaban mommy ya fadi ganin yadda kitchen din yake kamar ba mata ke amfani dashi ba.

   Nan kuma suka shiga aiki a kitchen din gyara can gyara nan take kitchen din ya koma na macen da tasan kan ta girki suka dora na abinda zasu ci a gidan.

   Sai da suka kusa gamawa ne matan dake gidan jin kamshin girki yasa suka fara fitowa daga dakunan kwanan su daya bayan daya.

Suna lekawa kitchen din suna masu ina kwana don tsaron mutuncin su ga maigidan.

   Bayan sun gama girki mommy ta zuba masu nasu taba Aisha nasu ta shige masu dashi ciki tabar saura da mutanen dake gidan zasu ci.

   Yanyala ce ta shiga dakin Nafisa take kwarmata mata abinda ke faruwa a gidan da fushi Nafisa ta sauko kasa zuwa kitchen din don taga abinda ke wakana mata a gida.

   Komai na gidan neat yake yau ya samu gyaran da ya dace daga bakin su ta shiga kitchen din taga yadda suka gyara komai suka jera shi a inda ya dace.

  Fita tayi zuwa sama ta samu Abdulsamad ya gama shirin fita tsab ta fado dakin da fushi tana fadin ban san may kuke nufi ba kaida wa yanda kake fadi wai iyayyen ka ne ?

   Ya juyo yana fafin kamar ya fa tace don may zasu zo min gida suna min abinda suka ga dama a ciki suna matsayin baki a gare ni.

   May sukai maki ya tambaya cikin bata lokacin shi yana sauraren amsa daga bakin ta tace a hasale yanzu ya dace ace sun shiga kitchen sunyi abinda suke so haka ?

   Sai da ya dubeta dakyau yace kada ki manta gidan dan su suka zo suna da ikon yin komai da suke so a gidan nan.

   Dansu ko dan ta da sauri ya kalleta yace may kike nufi da wanan maganan naki tace dashi gani nayi itama arziki tazo ci kawai a gidan nan do  ba itace ta haife ka ba.

  Au dama wanan ne tunanen ki ke nan dama raba daya biyu a gida to bari kiji mommy tankar hajiya mu take gare ni don matar mahaifina ne ita ma kamar hajiyan mu don haka nake daukan su daya.

  Yanzu ke baki jin kunya baki tashi kin tare su da abin karyawa ba sun tashi sunyiwa kansu har kike fadan akan haka don baki da kunya ?

   Tace ba zan yarda da wanan wuce wurin ba irin nata dama na dade da sanin halin ta tun shigowa na cikin ku do haka kayi saurin taka mata burki a hakan.

   You’re very stupid ya fada da karfi sai data razana yace kada ki fara kice zaki saka masu ido a gidan nan ko bayan fitana ne don zan saba maki sosai kuwa.

  Fita yayi daga dakin ya barta cike da mamaki tana ganin wankin hula zai kai ta dare wai itace samad din ta keyi wa abubuwa haka yanzu.

   Lalai duniya na shirin juya mata baya idan batayi da gaske ba tin yanzu dakin ta ta koma ta jawo wayan ta cikin tashin hankali take fada wa madam abinda ke faru da ita.

  Sai da ta gama sauraron ta tace Nafisa sai kin hada da hakkuri fa yanzu don ni a gani na akwai ida aiki ki ya samu matsala ko kuma don cikin dake jikin ki ne asiri ya daina kama mijin ki yanzu.

   Ina cikin wani hali walahi haka na nufin yan uwan samad zasu dawo gare shi suyi yadda suke so gidan nan ke nan wanda ba zan taba yarda ba sai dai duk abinda zai faru sai dai ta faru.

   Madam tace Nafisa kibi sannu fa ba kullun ne ya zama dole mutum yayi nasara ga abinda yake so ba kowa kika gani sai yanayi yana hadawa da hakkuri da kuma kissa bawai ga magani kawai muka dogara ba.

  Madam ni abin ne yazo min a bazata wallahi tace yanzun dai ki kwantar da hankalin ki mubi komai a sannu.

  Tace na ji amma duk da haka zan nuna masu gidana suka zo ba zan bari suyi min abu gaba gadi ba haka tace kiyi a sannu dai na fada maki.

   

    Shiko yana fita tun a falo ya fara ganin sauyin da gidan nashi ya samu da zuwan su mommy din ga gida ya koma neat a lokaci daya a falo ya hango su hadiye suna kuskus a cikin yare suna ganin shi suka shiga gaida shi.

   Fuska a daure take amsa masu ya wuce part din su mommy din wanda anan fati da take zaune da yaran ta ganin haka yasa ya tuna da abubuwa da dama na rayuwan su a baya a gidan.

  Kagin zuwa yanzu da komai ya hargitse mashi haka wanda kan shi yanzu ya dorawa laifin kasancewar haka kamar yadda na fada mai.

   Ya samu su mommy sun yi wanka suna karyawa a cikin tsanaki ya shigo da sallama ya gaidasu tare da masu ya gajiyan hanya.

  Mommy tace gajiya ai yabi lafiya don mun zama yan gari yanzu ko yace mommy duk ku kukai wanan gyaran haka a gidan nan ?

  Tace ba dole ba babangida gida ya koma kamar ba mata a cikin sa  kasan mu mun saba mijin mu baya son ganin kazanta ko kadan.

  Iya bawa tace mai ni ina mamaki gida da mata haka ace bai samun gyaran da yadace mace ta yi a gidan ta wanan matar taka akwai bakin son jiki ne da ita.

  Ciki ai bai hana ka gyara muhalin ka sai dai dama idan gyaran bai damay ka ba can amma yaushe ne mace kirki zata bar gidan ta haka ?

   Mommy tace ga abin kari can a kitchen idan ta fito sai ta raba maku ka karya kafin ka fita yace mommy zuba min zanci anan gurin ku don bata fito ba ko ina sauri ne.

  Anan ya zauna ya karya tare dasu yana mai jin dadi a ranshi yaushe rabon da ya karya a gidan shi haka cikin dadin rai.

  Bayan ya gama yayi masu sallama tare da tambayan ko akwai wani abinda suke bukata a gidan ya sayo masu idan ya fita.

  Mommy tace sai kayan kitchen din da taga sun soma lalacewa saboda rashin amfani dasu da ba a yi akai akai yanzu dole a sayo wasu yaje matar shi tai mashi lissafi don gudun su shiga mata hakkin ta.

  Bai koma takan Nafisa ba ya fice gidan inda ya samu Sani driver yana jiran shi a waje suka dauki hanyar zuwa office din su.

   

   Barci nake a dakina tun dawowana class wayan shi ne ya tayar dani daga barcin da nakeyi nayi mamakin kirana a wanan lokacin da yayi.

  Bayan na karba mun gaisa ne yake tambayana idan maryam tana nan don Allah zai aiko Sani driver shi mu taimaka mu sayo mai abin girki a gidan shi.

   Da sauri nace mai kaga malam bafa zaman ka nake a garin nan ba da zaka dora min nauyi irin haka a kaina ina matar ka kaje ka tura ta ta sayo ma mana  .

  Don Allah kiyi hakkuri ku taimaka min for today only naji nace na kalli maryam dake barci nace yanzu yau friady muna hutawan mu ya dauko wahala ya dora muna kuma.

   Ban sake komawa barci ba motsina ya tayar da maryam nan nake fada mata abinda ya bukata da mu tace to may ye a hakan khadija ?

   Ai taimako ne kin san matar shi ba wani wayewan kaine da ita ba kuma kin san gata da ciki baki yanzu nace wanan ai ba excuse bane.

  Son dorawa mutane wahala kawai yake yi don kada a zauna lafiya muna zaune kalau zai dauko wahalan gidan shi ya dora muna.

   Kin san may khadija nace aa cikin kada kaina tace walahi sai nake ganin wanan Abduldin yana bukatan taimako a rayuwan shi.

  Bai samu macen da ta dace da irin halin shi bane har yanzu yasa komai yanzu yake bukatan taimakon ki ban san yaya zaiyi ba ranan da zaku rabu dashi tunda kince ba soyayya bane a tsakanin ku.

  Nace ai ke kin fi kowa sanin hakan shiya san yadda zaiyi don ni bashi ne a gabana ba karatuna ne ya damay ni inga na kammala Allah yaban sa,a in samu aiki da wuri.

   Duk da haka khadija akwai matsala ranan rabuwan ku kan inda ran mu zamu sha kallo nace in babu sai abaku labari ai.

  Tace labarin taimako ya juye ya zama soyayya haushi maganan ta yabani ban samu bata amsa ba naso ta biye min kada muje ko ina ya karata can da halin shi shiya sani.

   Karfe uku bayan an fito sallah jumma,a sai ga malam sani driver yazo daukan mu nan yaban kudin yace wai zamuyi waya dashi.

  Muna hanya ya bugo min yana fada min duk wani abinda muka sani ana amfani dashi a fannin girki har nama da kaji da sauran su mu sayo mommy ne ke bukata a gidan.

   Kai dama duk wanan abin ba a saya a gidan ka may kuke ci a gidan silly girl ya fada ya kashe wayan shi naja tsuki.

  Mun shiga kasuwa maryam tayi kaca kaca da kudin komai mun hada sai yamma lis muka baro cikin kasuwan inda ya fara sauke mu a hostel ya wuce bayan hilux din su acike muka bashi sauran kudin shi ya kai mashi canji.

   Wanka nayi tea kawai nasha da nai sallah muka samu wuri muka kwanta don gajiyan da muka debo a kasuwan bamai taimaka wa wani a cikin mu duk a aikin sa kai da mukayi.

   Barci yana batun dauka na wayan shi ya shigo min jin murya na yasa yace har kin fara barci ne ko may ?

  Nace ba dole ba yau an samu wahalan da ba namu ba lada ba zunubi sai tarin gajiya khadija ke wace irin yarinya ne wai da ba tsoron fadin magana a bakin ki ?

   Yanzu dai ba wanan ba don may kuka ba sani ragowan kudin da ya rage yakawo min kuma ya fada min komai baku sayo wa kan ku ba ku.

  Saboda ba hakkin mu bane yasa muka bashi yakai ma kudin ka don Allah barni na huta malam gara da kai kana da madafa.

   Murmushi naji yayi yace ina dashi tunda ina da matar da zan runguma inji sanyi ke ko sai dai ki kama filon ki ko ?

   Kaidai ka sani nace mai sai da safe yace ba zaki tsaya nayi maku godiya ba zaki kashe min waya ?nace ai ba don ka gode muna muka taimaka maka ba na kashe wayan gaba daya.

  

A gidan shi ya iso da kayan akai ta shiga dasu ciki shi kanshi yayi mamakin yawan kayan da muka sayo din ya kira Nafisa kafin ta sauko ya kira mommy da kanshi kan tazo idan akwai abinda babu sai a sayo gobe.

   Nafisa na zuwa mommy tana fitowa tare dashi yake tambayan ta ta duba ta gani ranta a bace tace komai yayi sai mommy tace komai an sayo sayayya haka kamar na mace.

  Nafisa da ta juya zata tafine ta juyo da sauri ta kara kura ma kayan ido tana kallo kayan da bata kalla ba da farko saboda idon ta ya rufe da masifa a lokacin.

  Maganan mommy ne ya tsaya mata a rai da tace sayayya kamar mace tayi komai an saya yadda ya kamata ta kira hadiye da yanyala wai su kawar da kayan wurin tana daure fuska gata mai gida.

   A daki ta samay shi zaune lokacin muna waya tace gurin ka nazo ya aje wayan da na kashe yana kallon ta ta samu guri ta zauna da kyat.

 Tausayi  ta yaji ya dirka mai a zuciya tace may kake nufi da baka shawarce ni ba ka sayo wanan kayan haka sai da  kasayo abinka zaka kirani.

   Yace saboda baki damu da asaya din bane yasa na sa a sayo min tace wace yar iska ce ta sayo ma cikin kura mashi ido da son jin amsa daga gare shi.

   Wanan ba matsalsn ki ba ne ke dai kiji da kanki ya fada mata yana kokarin mikewa tsaye samad mai kake nufi dani ne wai ?

   Da akayi may kuma yanzu tace ban fa gane inda ka dosa ba gaskiya da irin wanan halin naka yace saboda baki son gaskiya ne yasa na canza nima.

   Kana nufi nice mai laifi yanzu aike ma kin sani idan kina son mu shirya dake to ki canzs ke ma yaushe rabon da na karya a gida na in ba yau ba da mommy tazo.

   Dama nasan abinda ya kawo su ke nan ai hadin fada a tsakanin mu in bashi ba may zai sa su kwaso kafan su suzo nan wai sai na haihu.

  Yace saboda ina dan su kuma ni na bukaci haka a gare su tunda ke baki san komai ba sai bakin yawo da lalaci kawai da kashin kudi.

  Nice mai kashin kudi murushi yai mata yace ko yanzu ma nasan amsan kudin ne ya kawo ki ai ba wani abu ba tunda baki damu da damuwa na ba.

  Kaine dai ai naga kamar kana gudana yanzu nan dai suka shirya ranan ace tsakani  miji da mata sai Allah suka manta da komai a ransu.

  Washe gari mommy ta sake hada masu break fast mai rai da lafiya tasa Aisha ta gyara dining din aka jera kkmai a yadda ya dace ta aikawa su hadiye da nasu.

  Tare suka sauko suka karya a tare sai hadiyan abincin take ba kunya ko wani nauyi a tare da ita bayan sun gama ya fita zuwa wurin aiki.

  Sai lokacin Nafisa ta kalle gefen dakin da su mommy ke ciki ta kira hadiya ta rufe mata kofan kitchen da store din gidan gaba daya.

   Da rana mommy ta turo Aisha ta gyara mata kitchen din sai ta samu gurin a rufe ta koma ta fada ma mommy.

  Mamaki ne ya kama mommy ta kira hajiya mama tana fada mata abinda Nafisa tayi masu ita kuma mama ta kirashi inda take shiga ba nan take fita ba tace maza ya dawo dasu gida tunda yasan gidan shu ba a hannun shi yake ba ya dauke su.

  Hakkuri ya fara bata yace zai dauki mata hakan tace ya yake son yi idan Abban su ya samu wanan baki  labarin  dama abinda yake ma gudu ke nan ya hana su zuwa tu  farko.

  Hakkuri ya dinga bata har ta saurara mai tace tana jiran taji matakin da ya dauka a gidan idan ba haka ba zata fada ma Abban su abinda ke faruwa kada yaji a gurin wasu.

  Yusuf yana zaune yana sauraren su yana kashe waya  ya dago idon shi da suka kade sukai ja yace wai may Nafisa take nufi da nine ?

  Guri ta samu take wanan abin mana Yusuf ya bashi amsa yace in bashi ba rashin mutuncin nata har yakai ga su mommy kuma yanzu.

  Mommy ne zata rufewa dakin girki bata girka ta basu ba basu damu ba suna yi kowa kuma yaci har zata rufe kada suci su kwana da yunwa komay ?

  Tasan yadda Abba yake ji da iyalin shi kana zaton da ba mommy bace in anty amarya ce Abban zata kira da kan shi ta fada mai kasan ko yau ba zata kwana gidan ka ba.

  Wallahi idan zaka kara aure ka kara shine kawai mafita ga wanan shu,umar mace da ka dauko wai mata bazata taba ganin darajan ka ba idan ba ta bude ido tagan ka da wata mace ba a gidan.

  Idan tana zama ta zauna in bata zama kuma ta kara gaba dama ba akirata ba kutse ne da sa kai irin su ta kallamay kada dadin baki da komai ta aure ka.

   Kai yace tare da bugun tabur din gaban shi ya mike cikin fushi Yusuf yace ina zaka kuma yanzu ?

  Gida yace cikin wani irin murya kamar mau zazzabi shima mikewa yayi ya bishi a baya tare suka fita daga office din shiya jasu don Abdul din bai da karfin haka a yanzu.

   Suna tafiya yana dafe da kanshi ba tare da ya kalle shi ba Yusuf din yace ba irin ku masu sanyin hali ne ya kamata ya auri irin Nafisa ba.

  Sun fi daidai da irisu wa yanda zasu caja junan su a zauna lafiya amma ai dama ita haka suke so su samu wanda suke juyawa son ran su.

  Yanzu ai ta fara koya min iya magana ita da wanan yar matsalan khadijan din nasan idan an auna ni za a samu VP dina ya hau wallahi Yusuf damay Nafisa take son inji ne wai ?

Suna shiga gidan su Nafisa ne zaune a falo da yan uwanta sai wata bukuwa da tazo mata a lokacin wace bai san ko wacece ba.

   Sun fara gaida shi sai dai ita bata dago kai ta dube su ba ganin su tare da Yusuf da taki jini da tayi don a cewan ta Yusuf ne ke kulla mashi duk wani shawara a gamay da ita.

  Shima Yusuf din bai tsaya ta kan su ba ya wuce dakin da su mommy suka sauka dauke da ledan take away da suka sayo masu a hanya.

   Nafisa may ne hujjan ki na rufe kitchen da kikayi yau tace saboda gida nane yasa na rufe don ina da ikon yin hakan ko ?

   Idan abinci yayi saurin karewa wa zaka tambaya yadda akayi dashi ai naga da kawo abincin sai da ka kirani ai in gani ko ba haka na bane ?

   Nafisa lalai wuyan ki ya yi kauri a gidan nan har da zaki iya rufe ma iyayyena wuri kada su dafa abinda zasu ci ko suyi amfani dashi.

  Amma ba laifin ki bane laifina ne da na sakar maki wan har kike ganin kin isa kike son wuce gona da iri a gidan nan da rayuwa na.

  Baki dafa kin basu ba sun dafa ma kansu kuma kinyi bakin ciki da haka da suke yi ko kin mata nan din gidan dasu ne halal malal suna da iko da komai yadda suke su.

   Ai ban sani ba sai yanzu da ka fada a gaban kowa nasan yan uwanka sun fini muhinmanci a gare ka yace da may kike daukan kanki ne.

  Tace ai sai su fito mu zuba dasu a gidan bansan ka kawo su nan bane don su kara dani tsawa ya daka mata cikin kiran sunan ta da karfi.

   Mikewa tayi da kyat itama tana fadin ban san sun isa da kai ba sai naga muna raba kwana a gidan nan dasu.

   Haka kike ce tace an fada din yace bada su zan raba maki kwana ba amma ki sani zan kawo wace ta dace in raba maku kwana gidan nan wace zakuyi daidai da fitsaran ki.

  Su wa yan nan iyayye nane yanzu na kawo amma mai zuwa in raba maku kwana tana tafe kwanan nan.

  Madam ne dake zaune ta mike tana fadin Nafisa kina da hankali kuwa kin san may kike shirin aikata ma kan ki yanzu ?

  Ta figi jakkanta dake aje gefen kujeran da ta zauna tana fadin ni na tafi tunda baki da wayo yace bata san bata da wayo ba yanzu ne zata sani.

   Waya ya ciro daga aljihun shi ya fara fadin hello inspector kana jina wasu froriners nake son kazo ka kwashe a gida na yanzu don Allah.

  Jin haka duk suka mike tsaye don da a zaune suke gefen guda sun zuba masu ido suna sauraren su madam ce ta fara bashi hakkuri da fadin.

  Assha Alhaji ai a bin bai kai haka ba basai ka kira hukuma a cikin zancen iyalin ka ba anan akayi sai a sasanta shi a nan Nafisa kin yi kuskure ki bashi hakkuri ke kuma.

  Bani taiwa laifi ba su da ta bari da yunwa tun safe ne za ta ba hakkuri tace ni ban masu komai ba balle in basu hakkuri.

   Yace da kyau mommy da suke daki da Yusuf suka ji hayaniya yai yawa a gidan yasa suka fito daga dakin gaba dayan su.

   Sun fito daidai lokacin da take fadin batai masu laifi ba bazata basu hakkuri ba mommy tace Nafisa kinyi kuskuren ki ba mijin ki hakkuri mu namu mai sauki ne.

  Don shi muka zo gidan nan kuma da bakin shi yasa muzo ba wai haka kawai muka kwaso kafan mu zuwa nan ba tunda mun san baki son wani nashi ya rabe shi yasa kowa ya sallama maki shi yanzu.

  Shigowan inspector din da wasu polisawa uku ne ya ruda Nafisa da da ta dauki abin da burgan maza yake mata sun gaisa ya nuna su Yanyala da su hadiye yace gasu nan .

  Yar uwar su na aure suka zo suka tare min a gida ban san dalilin su nayin haka ba sai ku tambaye su hankalin kowa a falon ya tashi ya juya gurin su mommy ya fara basu hakkuri.

  Mommy tace mu bakai muna komai ba don wurin ka mukazo dama ba wurin wani ba macen police din ne ta fara ingiza keyan su hadiye gaba.

   Samad kayi hakkuri don Allah ba sai ka wulakanta min yan uwa ba don ni suka zo gidan nan sai ka hada dani duka kace a kwashe mu.

  Bissimila yace idan haka yafi maki yan uwa na daine dole na a yanzu gidan nan na kuma gwada maki haka kina iya binsu ga hanya nan a bude ya juya gurin police din yace ku tafi dasu duka.

   Samad ni zakai wa haka ni zaka fada a kwashe mu a tafi damu babu ko nauyin haka a bakin ka kake fada.

  Ke uwata ce ko may ko ajeni kika yi a gidan mara mutunci kawai ya juya zai fara tafiya da sauri tasha gaban shi tana fadin kuskure ne nasan nayi ba daidai ba don Allah kayi hakkuri.

   Madam tace tun farko da haka kikayi da abin baikai haka ba ya nuna su mommy yace su zaki ba hakkuri bani ba ai.

  Mommy kiyi hakkuri kisa baki a maganan nan don Allah mommy tace naji zan bashi hakkuri amma haka ya zama ishara a gare ki gaba.

   Nan Abdul din ya dage sai idan ta basu hakkuri zai jaye maganan tace cikin dukawa mommy kuyi hakkuri nayi kuskure don Allah.

  Iyan bawa tace amma ke kan anyi mutumiyar banza a nan yanzu baki ji kunya ba don Allah ga yan uwan ki ko ina a gidan baki bakin ciki da cin su ba sai mu da mukazo zama daku na dan lokaci.

  Dan mune fa mai dukiyan da kike kadagi dashi din har kike ganin kowa ba kowa bane a gurin shi sai ke da yan uwan ki keda iko komai dashi.

  Nan suka kaita fada mata abinda suke so a cikin nasiha tace ayi hakkuri zata gyara yusuf ne ya sallami yan sanda suka wuce.

   Ranan dai anyi ta ba dadi a gidan tayi nadama tayi bakin ciki abinda Abdulsamad din yayi mata a gaban kowa ya nuna bata da wani power a gare shi yanzu ga madam ma tayi fushi da ita ta tafi tana fadin ta bashe su a idon duniya.

  Ta kula wanan ta kwance wancan haka na ta wuni da sake sake a ranta a kan sai ta rama abinda yayi mata akan su mommy din da suka zo gidan don ganin bayan ta.

  Ita sam bata dauka don dan su da taimakon ta suka zo ba har yanzu don idon ta ya rufe da son bata kaunar taga wani wanda ba nata ba ya rabe shi saboda tsananin kishi da take dashi irin na buzaye.

   Ta kira madam ta bata hakkuri har suka shirya take anan kuma suka fara sabon shirin da zasu aiwatar a kan kowa ma daga bangaren shi.

  Shiko a bangare shi ranan daki ya shige bai son yawan hayaniya da kowa don haka ya ke be kan shi a daki ba abinda yake sai tunanen hanyar da zai samu mafita ga alamarin Nafisa.

  Saboda yasan ba canza halin ta zatayi ba kwanto kawai tayi a yanzu tana nazarin ta idan zata biyo mashi ne.

   Allah ya gani yana son ya kara aure kamar yadda Yusuf yasha fada mai shine kawai mafita gare shi akan Nafisa to amma wa zai aure din da zasuyi daidai da Nafisa a zauna lafiya.

  Khadija ina khadija karama ne sosai ga Nafisa da halinta ba zai dauko yar mutane ya jefa a matsala ba ya cuta mata don yanzu yana jin yarinyar a wani bangare na rayuwan shi .

  Don haka ba zai cuta mata ba ta wanan hanya na hada aure a tsakanin su wani abu yazo ya samu yar mutane a hannun shi.

  Ga mahaifin ta ko yaushe sukai waya yana mashi godiya akan kyautatawan da yake ba yarsu wace kamar kauna take a gareshi.

  To amma kuma ga shakuwan da sukayi taya zai iya rabuwa da khadija a yanzu nan tunanen irin rayuwan da suke yi da khadija din ya fado mashi a rai abinda ya sa shi dan murmushi ke nan kadan ya gyara kwaciya yana lumshe idanuwan shi.

   Wayan shi ne ya yi tsuwa alaman kira na shigo mai ya dan juya ya daga wayan Queen of matsala ya gani da sauri ya daga kiran nawa.

                      Tambayan shi nayi lafiya kake kuwa yau ?

   May kika gani ya bani amsa dashi sai na rasa abinda zan fada mashi karya na samu kaina da yi nace kawai dai sai nake tunanen hakan .

   Fada min kewa na kikayi ko may kika kirani a cikin wanan daren haka baki san ina da mata bane ni Family man ne idan kika hadani fada da mata na fa ?

   Wayan na kashe ina ci gaba da tunanen mafalkin da nayi dashi a yanzu daga dan barci ya dauke ni sai wanan mafalkin yazo min gaba daya na saka waya na a off na gyara kwanciya cike da zullumi ina tunanen mafalkin.

   Can dai barci ya dauke ni na manta da zancen mafalkin koda na tashi naci gaba da alamura na shima kuma bai kira ba don haka na kara share shi.

  Nafisa ko hankalinta bai kwanta ba gida Niger ta kira mai mata aike a can da kukan ta wiwi matar tace may ke faruwa Nafisa ko sakin ki mijin ki yayi ?

  Tace bai sake ni ba serah sai dai gaba daya ya canza min yanzu nan dai ta koro mata bayanin abinda ke faruwa cikin kuka.

   Serah tace share hawayen ki Nafy murde dan iska zamuyi ya koma  sai yadda kika ce a gidan ki bai isa ba wallahi yanzu dai ki daure kibi yan iska yan da suke so daga yau zan shiga in fita zaki gannin nan da kwana uku kedai turo min da kudi kiga aiki da cikawa.

  Tace serah har kin kwantar min da hankali na wallahi don yanzu ni damuwa na bai wuce cikin nan dake jikina ba don cewa ake wai idan mace nada ciki ko jinin haihuwa wai komai nata baici.

  Serah ta katse ta da fadin da ke nan wanan zancen yanzu may ye kudi baiyi Nafy ina nan shigowa nan da kwana uku kada kiji komai.

  Bayan sun gama wayan ta zauna ta zabga ta gumi ta rasa ta ina zata fara da shi zata fara ko da iyayyen ko wanan mugun abokin nasa da ta tsana.

   Zaman gidan yanzu haka ake yin shi ba ruwan wani da wani sai gaisuwa a tsakanin su dasu mommy kowa na harkan gaban shi.

   Shiko yana tsananin basu mommy girma da kulawan da ya dace a gidan wanda hakan keyi wa Nafisa ciwo matuka ta rasa yadda zatayi dasu a gidan.

   Kunci cikin zuciyar ta ba a maganan shi har yakai bata iya boyewa hakan yasa ma ta daina yawan saukowa kasa inda zata gan su ko wani  abinda sukeyi shiko sam bai kula da halin da ta jefa kanta a ciki ba yanzu.

   Kamar yadda serah tayi alkawari haka ya faru tazo da kule kule da sihiri kala kala tun a ranan suka fara aiwatar da komai kamar yadda suke so ya tafi.

   Nafisa sai gani take har aiki ya fara ci saboda yarda da tayi da maganin don irin labarin da Serah ta bata yadda ta shiga kungurumin dajin kasan su wurin samo mata wanan asirin mai amfani da ci da sauri ga wanda akaiwa.

  Haka kawai yake ji kwana biyu yana jin haushin kowa a gidan inbanda Nafisa da yanzu yake jin wani irin so da kaunar ta yana shigan shi.

   Mommy dake da kaifin basira ta fahinci abubuwa suna sauyawa a gidan don haka ta fara tuntubar Iyan bawa akan abinda da ta fara hangowa ga dan nasu don tun zuwan Serah mommy tasha jinin jikin ta da ita don tsarin ta da zubin ta yafi kama dana yan duniya ta irin mutanen su.

  Batai kasa a gwiwa ba ta sanar da mahaifiyar shi hasashen ta amma tace kada ta bari kowa ya fahinci abinda ta fada mata ta dai taimaka mashi da addua.

   Hajiya mama tayiwa mommy godiya bayan sun gama tataunawa akan zancen sukai wa juna sallama aka aje wayan.

  Sosai hankalin hajiya mama ya tashi da maganan mommy haka yasa ta kira yayan ta da suke uwa daya uba daya a zaria tana neman shawaran shi.

  Yace ta bari zai ga wani malamin shi a nan cikin garin zaria da zancen don rayuwar Abdulsamad da wanan matar tashi yana bukatan addua sosai.

  Haka suka bar zancen akan zai kira ta taji duk yadda sukayi da malamin nashi idan ya dawo daga wurin shi.

  

   Ban san mun shaku da shi ba sai wanan karon ga jerabawa ya na gaba to muna ga zancen zuci dake damuna haka ya dan sani rama kadan.

   Karshe nabawa kaina shawaran abinda ka fisheni na watsar da komai na rugumi karatu na gadangadan ina yi tare da share zancen su gaba daya a raina.

  Ranan muna zaune da Maryam a dakin ta tsifar kaina na ke da ya kitso ya tsufa min zan je in wanke kai na wayana yayi tsuwa na duba Yusuf ne a kan layin.

  Nayi mamaki kwarai da ganin kiran shi a wanan lokacin na dauka da sallama tare da gaida shi ya amsa yana fadin kanwa ta ina kika shige haka ?

  Kai yaya Yusuf ina nan inda nafi karfi mana na bashi amsa yace ko dai mutumin nawa ya boye muna ke ne ban sani ba ?

   Wa ke nan kake magana nima na tambayeshi yace abokina mana kuma ogana a wurin aiki nace wai mijin buzuwa kake magana ?

   Dariya ya kyalkyale dashi yace kai khadija baki da dama wallahi har yanzu dai mijin buzuwa aiko zaku kwasa dashi idan ya jiki.

               Nace ina ruwa na dashi balle balle ya jini .

  Yace ke ko keda ruwa dashi khadija yar mama amma dai baki da kirki Abdul din ne zaki ce yau ina ruwan ki dashi da bakin ki kike fadin haka .

  Tsuki naja na tabe baki kamar yana gani na a lokacin nace ni na fita batun shi yanzu banda lokacin shi.

   Yace subbahanallahi may yai zafi haka ne a tsakanin ku kuma keda mutumin naki khadija ?

   Mutumi na ko naka yaya na kai nifa ko wancan lokacin da nake kula shi albarkacin ku ya samu a gare ni har na biye mashi amma ba don shi ba.

   Kai haba yar mama bai dace ki fadi haka ba tsakanin ki dashi yanzu ai kunyi nisa sosai bai kamata aji wanan maganan ba a bakin ki.

  Taimako fa kikace zakiyi sai da abu ya kusa kai karshe zaki ce ba ruwan ki dashi yanzu ai ko kece mai ruwa har da tsaki akan shi yanzu.

   Mu dai bar wanan zancen nace dashi da sauri yace akan may zamu bari idan na tambaye ki zaki fada min gaskiya ?

  Nace akan may ke nan yace akan mutumin naki mana nace idan na sani may zai sa na boye maka kuma ?

  Yace Yaushe rabon da yazo gurin ki ko kuyi waya dashi when last kukayi koda waya ne please kada ki boye min komai just feel free with me khadija?

  Dan jin nayi sai can nace gaskiya mun kwana biyu dashi don ba zan iya tuna zuwan shi gurina ba na karshe ko wayan shi a yanzu.

  Yace abinda nake son ji ke nan daga bakin ki sai dai zan ari bakin aboki na inci mashi albasa Abdulsamad yayi tafiya two weeks ago amma dai yanzu ya dawo.

  Sai dai ko a yanzu da bukata nazo maki a kan shi don gaba daya khadija ba zan boye maki ba Abdulsamad ya canza ga komai cikin yan kwana kin nan.

  Gashi matar shi na shirin haihuwa watan ta ya tsaya tun last month sai dai har yanzu bata haihu ba yana gida ko wani lokaci tunda ya dawo like da ita.

  Katse shi nayi da fadin ni may ye nawa a cikin zancen nan kuma can su karata shi da ita tunda shi ba tsayayyen namiji bane ko yaushe.

   Namiji ne mana khadija   ai shiyasa na kiraki don ki sheda mai cikin wanan wasan da kuke yi don ya farga ga abinda yake yi din.

  Ni tsoro na shine kada su mommy daya dauko gidan shi su fahinci susucewar shi a kan wanan shuumar matar tashi sugane gazawan shi a gaban kowa.

   Shiya sani mana tunda shi ke ji a jikin shi ba wani ba yayi saurin fadin a a khadija ba haka zamu yi ba daurewa zakiyi mu fitar dashi daga wanan kangin don Allah.

  Ni haba yaya Yusuf ni may zan mai kuma shiya sani don Allah khadija dakata ki saurare ni don Allah nace ina jin ka ai.

   Zaki iya hakkuri ki daure ki kirashi a waya ki fada mai magana daya wanda zai shi ya natsu ya dawo cikin hankalin shi yanzu don ke ce kawai mafitar da nake dashi bayan Allah.

  Ni kuma why sai nice mafita akan haka yace saboda ban taba ganin wani ko wata dake fada mai magana yadda kike fada ba azauna lafiya kuma yai amfani da abin da kika da mai a zauna lafiya.

   Dan jin nayi ina tunane yace kada ki karaya khadija don nasan zaki iya ki taimaka muna please wanan taimako ne indan kin yarda.

   Yaya Yusuf wanan ya zama na karshe da zan ma wani alfarma akan wanan mutumin don gaskiya baida niyar canza halin shi nake gani  .

    Khadija ba laifin shi bane shu,umar mace ya hadu da ita take juya shi yadda take so nace har da halin shi a haka.

   Kin yarda zaki taimaka muna ke nan nace naji zan gwada don Allah don kai amma da ba haka ba babu abinda zai kara damuna da rayuwan shi.

  Nagode kwarai da hakan da zaki min don wanan ne kadai hope din da nake dashi yanzu akan wanan matar tashi.

   Ina aje wayan maryam dake zaune ta kura min ido tana sauraren maganan da muke yi din tace kai wasu maza suna haduwa da shu,uman mata wallahi.

  Koda yake ba abin mamaki bane ga wanda yasan mazajen da ke auren irin yan yaren buzaye zai san mazan ne a kasa matan suna sama.

   Sai abinda sukace komai su mamaye na miji yazama nasu su raba shi kuma da kowa nasa sai su da yan uwan su zasu dinga bushasha da shi da dukiyan shi.

   Sai dai kima sam basu son auren mazan yaren su don irin bakar wahalan da suke sha wurin su amma namu mazajen su ke kwadayin matan buzaye saboda bakar jaraban da suka iya.

   Yanzu dai kira shi muji yadda zaku kwashe a tsakanin ku don nasan akwai drama nace ni wanan daure ni suke son yi maryam.

   Ban san may yasa suke cewa wai sai nice zan iya masu haka ba bayan yana da kanne mata da yan uwa da zasu iya.

  Su iya may khadija ai abin sai da hikima ke fa ba yar uwan su bace kin ga yadda kuke moved dashi kamar saurayi da budurwa ne.

  Ke komai zaki iya fada mashi a zauna lafiya wani dan uwa idan yafa da sai inda karfin shi ya kare ke ko sai ki fada mai a wasa bai dauki abin da zafi ba.

   Wayan ta na karba ta hanyan yi mata karya wayana ba kudi a ciki tace ai bai san layi na ba don haka ba lale bane ya dauki kiran .

  Bari dai mu gwada mu gani idan bai dauka kiran har ya kusa karewa ya daga tare da fadin hello nace dole zama da yan haure ya kowa ma wani akidar banza.

   Wake magana please ya tambaya nace wata buzuwa ce ko kana son kari su zama biyu a gidan ka murmushi yayi yace khadija nace ba ita bace.

   Kina zaton muryan ki nan zai bace min ne nace marya na yana kama da na buzaye ne ?

   Yace ai kamar ma ta baci baki ganin zubin ku daya dasu sai dai yaren da baki ji nasu kai malam ni kiran ka nayi naji ko mommy ta koma ne?

  Don nasan ba lale bane buzuwan gidan ka ta barsu su dade a gidan yace idan kina son sani kije gidan ki duba mana.

   Ban tashi ba ne da zanje yace ya kike nace ina nan yarda ka sanin a baya ke ba a maganar girma da arziki dake ne ?

   Nace banson don ba gaisuwa na kira ka muyi ba ko tambayana yaya ni yace ai kogi ba ki dadi ba ko nace .

  Wani kogin ke nan dai wani ko wani ruwa ne ya shige shi in ba nasa bane amansa yake yi don haka ba gaisuwan ka nake nema ba.

   Yace becareful nace a nan ko sai kaga mutum har mutum amma a gidan shi sai ka rena mai wayo idan kaga abinda yake yi.

  Ta yaya bakin haure har zasu shigo su samu mutum a gidan shi in ba samun wuri ba suce sai abinda suke so zasu mai ni wallahi na dade da raina aya don tsakuwar ta.

  Yau hausa kike ji ke nan nace daurowa ne hakan adai ji tsoron Allah kada mutum ya zauna mace ta mayar dashi saniyar tatsan ta .

  Ba mai ci sai ita da yan uwan ta kadai yace kina son wani abu ke nan nayi saurin fadin haram wallahi adai ci lafiya.

   Ga yan ketare nan suna taya ka ci idan ka wawuro su kuma sai su cafke ranan na zuwa da zan maka irin ku kotu masu ba bakin haure makafa suyi yadda suke so da dukiyar kasan mu.

  Yace magana kike ji ke nan dai nace ba wani magana sai fadin gaskiyan da na saba kulun idan naga anyi ba daidai ba.

   Ya Abdul ace mutum baiwa kansa adalci kulun   sai abinda mace ta dora shi a kai yake bi yace wai may kike nufine don na rasa gane ida maganar ki ya doso har yanzu.

   Mafalki nayi naga ka susuce kazama bawan mata sai goyon su kake yi a bayan ka ka manta da kowa na naka sai masu jajayen kunne kasa a gaba.

   Murmushi yayi yace ki fito fili kice kin yi kewa na kawai kin tsaya kina dora wa wani laifi kuma ko na kulata ba mata na na kula ba na kula matar wani ne ?

  Mata wai mata matar namu duka dai inji manya mata kan tana kaduna ka barota can wanan ai ta bugi ne  .

   Khadija you are very stupid matar nawa kike aiban tawa a gaba na nace ko a idon ka sai na fada don gaskiya ake fadi.

    Namiji kamar mace baida say a gidan shi sai na mace macen ma abin kyamatar mu gaskiya ka gyara halin ka sai anjima nayi saurin kashe wayan batare da najira amsan da zai fada min ba.

   Wanan yarinyar ta ci uban rainin wayo wallahi yace Yusuf da ke zaune gefen shi yana murmushi yace khadija ce halan ?

   Wa kasan zai min wanan idan ba ita ba ban san mayeatsalar ta da Nafisa ba ko da yake su mata haka suke dama ko Nafisan da tasan da zancen khadijan Allah kadai yasan iya boren da zatai min.

  Kana zuwa gurin ta ke nan har yanzu ya danja tsuki yana fadin wallahi na dade ban ganta ba tunkan naje Lesvegan rabo da na ji daga gare ta.

   Yusuf yace ai gashi yau ta kiraka ita yace ta kirani taci min mutunci ba sai nayi maganin yarinyar nan wallahi ta raina ni da yawa I don’t know why take min abinda taga dama haka ?

   Kun fi kusa ai bani shiga tsakanin ku yanzu ai wani kallo yaiwa Yusuf din yace tunda ka gama hadawa ba ai ka fadi haka yanzu ?

   Au ni ma hada ke nan ashe wa ya manna min wanan chewing gun din idan ba kai ba ina zaune kalau abina.

            Amma ai tayi muna rana ba kadan ba kasan da hakan dai ?

   Tsuki yaja yace ban san ya nakoma ba wallahi yar karamar yarinya ta shige min na kasa yin komai akan hakan ?

   Kun dai shige ma junan ku yanzun ne kuma kake neman maraba da ita ko why zaka so ka rabu da khadija bayan kasan tana da amfani a gare ka ?

  Amfani fa kace Yusuf yana kallon shi da idon shi da ya kafa mashi sai da Yusuf ya rausaya kai yace kafini sanin haka malam.

  Kada ka bari shedan ya rudeka kaiwa kan ka hasara zukekiyar yarinya kamar khadija may kake fadi ne wai Yusuf ?

  Kiran kawun shine ya katse masu magana da mamaki a fuskan shi ya furta kawu habu yau lafiya kawu ya kirani haka ?

  Ya dauka suka fara gaisawa da kawun nashi wan mahaifiyar shi cikin kunya da nauyin kawun nashi yake amsa mai gaisuwan.

  Don ya manta yaushe rabon shi daya kira shi ya gaida shi a matsayin shi na wan mahaifiyar shi da take ji dashi a cikin yan uwanta.

  Bayan sun gama gaisawa ne kawun nasa yace dama na kiraka ne idan da hali ina son ka shigo kaduna a cikin wanan satin .

   Da mamaki ya tambayi kawun nasa yace kawu lafiya ko yace a, a lafiya kalau sai alheri akwai abinda nake son kayi ne idan kazo amma fa idan ba takura.

  Haba kawu ba komai in sha Allahu satin nan zan shigo ranan jumma, a asabar zan karaso zaria in gan ka kawun nashi yace nagode Allah yayi maku albarka ya kara tsare muna ku.

  Ya amsa da amin kawu na gode ya aje wayan yana mamakin maganan da kawun nashi ke dashi akan shi Yusuf dake gefen shi ne ya tambaye shi ko lafiya.

   Yana mai da kan shi bayan kujeran da yake zaune sama yake fadin wallahi ban san abinda yasa yake nema na ba a yanzu.

  Zamu tafi karshen satin nan don haka sai ka shirya muna tafiyan yadda ya kama sai dai ban so tafiya yanzu ba a yadda Nafisa take haka haihuwa yau ko gobe.

  Zamu iya zuwa muyi kwana daya idan hakane sai mu juyo idan ka gama ganawa da kawun.

  Yace hakan za ayi Allah ya kaimu lafiya gaba daya har ya manta da zancen wata khadija ko don mantuwan da yake fama dashi a yanzu.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

          SEENABU

 Tunda mukai waya da Ya Amina tace min bata da lafiya sosai sai naji hankalina bai kwanta min ba ina bukatan zuwa kaduna weekend in dubata.

   Kwatsam aka wayi gari inace wa maryam kaduna zan tafi yau in duba jikin Ya Amina da bata da lafiya tace shine baki fada min zaki tafi ba muje tare .

  Nace kada ki damu watarana mu tafi tunda muna tare ai har bakin titi ta rako ni na shiga mota ta koma ita.

   Da wuri na isa don sammakon da nayi na samu jikin nata da sauki sosai na fahinci ciki ne ta samu ashe yana bata matsala dama haka take ciki da wahala ita.

  Gidan da bai samun gyara saboda laulayin da takeyi yasa gidan yayi datti da yawa sai da nayi wa gidan tas na yi wanka na kwanta don in huta.

  

 

Tunda ya fara shiri Nafisa take tsaye a kansa tana fada dashi akan may zaiyi tafiya yanzu bayan yasan halin da take ciki zata iya haihuwa ko yau ko gobe.

   Ya dago yana ce mata tafiyan ya kama shi ne dole don haka na fada maki gobe zan dawo insha Allahu may nene kuma na fada yanzu.

 Tace yanzun dai baka damu dani bane ban san may kake yawan zuwa yi gida ba akai akai haka ?

   Au ke da kike zuwa gida wani abu kike zuwa yi a can tace zaka hada kaina da kaine nifa kasan ba nan iyayyena suke ba ya zama dole in rika duba su a kai akai.

   Da kyat ya samu ta barshi zai tafi koshi don yace aikin shine zai sa ya tafi yasa Nafisan ta daga mai kafa.

  Da suka isa kaduna zaria suka wuce kai tsaye don ganawa da kawun nashi dake neman shi ida sukai saa sun samu kawon a gida wanda ya nuna jin dadin shi da amsa mai kiran da yake mai din.

  Bayan gaisuwa sun natsu ne kasun ke fadin ba wani abune yasa na kiraka ba sai yar wata magana da ta taso daga mahaifiyar ka a gamay da kai.

  Zama ya gyara don ya saurari may mahaufiyar nashi hajiya mama tazo ma kawun nashi dashi duk sunyi tsit suna sauraron kawun.

  Yace tazo nan ta samay  hankali a tashe take fada min abinda ke faruwa dakai na rayuwa musanman da kai da iyalin ka.

   Dama yasan maganan ba zai wuce wanan ba ai yace cikin karfin hali kawu wani abin tace nayi kuma yanzu ?

  Yace eh to tace bata ce ba kasan dai tsakanin da da mahaifi akwai wani kulawa da damuwa na musanman shiyasa tazo min akai ya kamata a taimaka ma da addua da wani taimako.

  Shine na kwantar mata da hankali nace zan yi wani abu akai don kasan naka sai naka a yadda naga damuwa a tare da mahaifiyar taka.

  Yasa bayan mun rabu naje wurin wanj malami tsohone aminin mahaifin mu tun yana raye nakai mashi wanan matsalar taka.

  To Alhamdullahi ya karbi maganan namu sosai da muhinmanci ida ya ce in bashi sati hudu zaiyi istihara sai a san abinda za a yi bayan satin hudun dana koma sai yace dani yana bukatsn ganin ka sai kazo da kanka zakuyi magana dashi.

  Wanan ne yasa na kiraka don kazo ku samu ganawa dashi kaji may zai fada maka sai musan mafita ga zancen.

   Zama Abdulsamad din ya gyara acikin ranshi yana fafin ikon Allah ita kuma mama tanan ta bullo min kuma yanzu bayan tasan ban son irin abubuwan nan tun farko.

   Amma a fili cewa yayi to kawu ba matsala amma dai sai dai ina fata aikin shi ba na kaucewa Allah bane dai ?

   Murmushi kawun nashi yayi yace haram haram kana ganin munyi kama da masu kaucewa alamarin Allah ne ya kamata ka shedi mahaifiyar ka kasan halin ta.

   Yanzu haka ma bata san komai ba tukun a wanan zance nafi son muyi magana ta maza da maza kafin ta samu labarin komai.

  Yace hakan na dakyau kawu don nima ban isa can gurin su ba tukun nan muka fara zuwa yanzu sai mun koma zan isa gidan.

  Tashi sukayi zuwa gidan tsoho malam illu don su gana dashi sun samu yana ganawa da wani babban mutum don haka suka zau a motar su suna jiran fitowan mutumin.

  Bayan mutumin ya fito ne kawun nashi ya ce su taso su shiga daga ciki suka fito daga motar zuwa ciki amma sai Yusuf yace zai jira shi a waje.

  Ya juyo yana fadin haba haba Yusuf ya zakace haka kuma mushiga don Allah zai fi akwai abin da baka sani bane nawa.

   Kawun yace mu shiga mana ai ba komai bane wanan mushiga daga ciki kawai mugan shi.

   Cikin suka shiga tsohon yana kishingide saman farin buzu irin na dabbobi da malaman da ke zama a sama.

  Yana ganin su ya dan dago daga kwanciyan manya da yayi nan suka zube don girmamawa suka fara gaida tsohon yace salihu kune tafe yanzu ?

   Yace eh baba yaron da kace yazo ne dan wurin ita kanwar tawa hafsat yazo yau daga can abuja inda yake aiki don amsa kiran da kai mashi din.

  Tsohon ya daga kai yana kallon su Abdul din yana jijiga kai yace Allahu Akbar yanzu wanan jikan mahaifi  ku ne Allah ya jikan malam shaibu suka amsa da amin .

   Ya dauko wani tasbaha ya rike a hannun shi ya dan murza ya mikawa Abdul din baya ya ce shine wanan din ko kawu salihu yace shine baba.

   Yace canki daya a nan yana mika mashi tasbahan dake a hannun shi Abdulsamad din ya mika ya zabi dayan dan tasbahan tsohon ta girgiza kai yana murmushi.

   Ya dago kai yace Abdul yake ko yace eh Abdulsamad yake sunnan kakan shi yaci na wurin mahaifin shi yace to kamar yadda na fada ma zanyi istihara akan jikan nawa Allah ya bani iko nayi.

   Sai dai naga abubuwa da dama da suke faruwa da jikan nawa wanda da farko zan iya cewa akwai sakaci aciki alamarin jikan nawa.

   Abdulsamad yaya akayi kabar gida haka kana dan musulmai jikan malamai kamar mu kabar abubuwa suka cabe haka a lokaci daya gare ka.

   Zama Abdul din ya gyara yana sauraron shi maganar da ta fara zuwa bakin tsohon shi ne na fitar da yayi zuwa kasan waje satin da ya wuce zuwa wasan da suke yi acan na milloners in world.

   Zufa ne ya tartso mashi a goshi yadda tsohon ke bashi labarin abinda ya faru acan har ya fadi a wasan ya dai san babu wanda yasan wanan abin don ko Yusuf baida labarin abinda ya faru can sai ga wanan tsohon na bashi labari tiryan tiryan.

   Bayan ya kare mai wanan bayanin ya dago ya kalli Abdul din wanda kanshi ke kasa yana tunane yace sai kuma maganan da ya shafi iyalin ka yanzu.

  Malam ya danyi shiru na wani lokaci ya sunkuyar da kan shi kasa kamar mai nazarin wani abu yana kada kafan shi jefe jefi yace.

  Yace gaskiya nayi istihara a kan ka sai dai abinda zan fada ma ba lale bane ka yarda zaka iya zuwa wurin wani yai maka ko kai kayi da kan ka don zaka iya istihara ba abu bane mai wuya idan mutum yasa kansa yi.

  Yusuf ne yace malam ba matsala ai zaka iya muna bayanin abinda ke nan yanzu don musan abinda ke nan.

  Malam yayi baiyananen murmushi ya na gyara zama yace bani hankalin ka nan ka saurare ni da sauri suka dago suna sauraren bayanin shi.

  Yace abinda nagani a satin farko shine kana tsare a karshin wata mace fara doguwa sai kayi kamar zaka kubce daga sherin ta sai ta sake sabon shiri a kan ka ta kara daure ka.

   Sai dai dana sake yi naga wata yarinya fara itama a cikin rayuwan ka ban sani ba ko kasan da ita ko baka sani ba tana nan dai yar matashiya ce haka da ita.

Sai dai ina ganin itace kamar warakan matsalan ka watarana amma dai ban sani ba Allah masani.

  Sai wanda nayi a karshen nan ya nuna min cewa zaka kara aure wanda haduwan ka da yarinya alheri ne sosai sai dai akwai matsala daga wurin wanan matar taka .

  Zaka kara aure nan bada dadewa ba zai zams maka alheri dan yarinyar mai biyaya gare ka ta kawo karshen komai a gare ka don arzikin ku yazo daya da ita sosai.

  Duk zauren akai shiru ana sauraren tsohon sai Abdulsamad wanda ke shatan zufa daga goshi  shi.

  Malam yaci gaba da fadin sai kayi da gaske ka zama namiji zaka samu mafita don yanzun haka matar da zaka aure ban debe tsamanin ba ayau ko gobe zaku iya haduwa da ita.

   Yace wanan ke nan bansan abinda yasa yaran yanzu kuke sakaci da ibada ba bayan kuna da sanin da Allah ya baku wanda idan mutum ya rike yanayin sa ba wani shedanin da zai iya tunkarasa.

   Ya dauko wani abu yace amshi rika nan ya mika hannu da sauri yana karban abinda yake miko mashi din yace yau nake son kayi amfani da wanan abin idan ka isa gida.

  Zaka shaye shi duka sai ka rage kadan ka wanke fuska da hannayen ka kamar dai yadda kake alwala zakayi dashi sai ka kwanta insha Allahu zaka kubta daga sherin su da yardan Allah.

  Yace har in kayi yadda nace kayi da yardan Allah  ba wani sihirin da zai shige ka koda kuwa sun hada da jinnu da sauran su don kamar ka dafe wani kafa na jikin ka ne da wanan tsarin Allah ya tsare ya kare yace dasu.

  Yusuf ne ya ce da tsohon malam batun yarinyar da kace fa tana nan kusa tsohon yayi murmushi yace gaskiya tana nan kusa damu a yadda nagani yanzu.

  Kuma ina sa ran haduwan ku ko yau ko gobe idan Allah ya kaimu sai dai mu bar ma Allah sanin shi.

  Gaban Abdulsamad din ne ya fadi a ranshi yana tunanen don yana tunane wacece wanan yarinyar da zai hadu da ita yaji har yana so  ta.

  Godiya sukai ma malamin suka kawo kudi suka bashi kai ya kada masu yace ba wanan a tsakanin mu aikai jika nane bazan karbi ko kwandala a gare ka ba.

   Sukai mashi godiya suka mike zasu tafi sai tsohon yace akwai tafiyan da zai taso maja gashi na gani a gabana kayi kokari kayi wanan tafiyan don zaka samu alheri mai yawa a cikin shi.

   Ya kara godiya suka fita sai da suka sauke kawu salihu suka kama hanyar kaduna a lokacin yamma yayi sosai.

   Ba mai magana a cikin su kowa da abinda zuciyar shi ke saka mashi a lokacin don shi da farko bai yarda wai nafisa tana mashi sihiri bane.

  Ya dauka so ne kawai yake mata na tsakani da Allah mutane ke ganin wai sihirce shi tayi baida ta cewa akan ta sai abinda taga dama takeyi.

  Amma yanzu sai gashi dan tsohon nan ya jefo zancen ta a cikin maganan shi shi bawai ya yarda bane to amma kuma abinda ya daure mashi kai shine zancen tafiyan da yayi tsohon ya sani.

   Zai gwada abinda yace don ba a kin ta maya koma maye zai gwada maganin ya gani zai kuma bi a hankali yaga maganan tsohon ko gaskiya ne.

  Muryan Yusuf ne yaji yana fadin wallahi na dauka khadija ce tsohon nan ya gani a tasbahan shi ashe ma watace.

  Sai dai wallahi naso ka auri khadija ashe abin ba haka bane muna namu Allah na nasa ne.

   A tunanen ka ke nan kai ni ban kawo komai ba har yanzu don ba wata mace a gaba na yanzun haka abinda ya damay ni ya damay ni.

   Koda suka isa dare yayi don haka suka bari sai da safe idan zasu wuce su shiga su gaisa da su hajiya mama.

   Barci nake bayan na gama mata komai sai na koma in huta can cikin barcin naji muryan Y Amina a kaina tana fadin khadija don Allah tashi ki shiga gidan su mommy ki karbo min lemun tsami.

   Na dago idona cike da barci nace haba ya Amina nifa ban son shiga gidan nan har in koma tunda ba dadewa zanyi ba.

   Khadija magani zan hada dashi don Allah daure ki shiga ki karbo min dole na daure na mike ta fita daga dakin ta koma falo ta zauna.

  Na fito sai take cewa dani wurin hajiya mama zaki karbo min don mommy bata nan tana Abuja gidan Abdulsamad takai wata can an dauka matar shi zata haihu a lokacin suka tafi gashi har yanzu bata haihu ba.

  A raina nace ai nafiki sani na fita ina ce mata sai na dawo a gidan sunyi mamakin ganina don basu san da zuwa na ba .

  Sai da nabi kowa na gidan na gaida su na nufi dakin hajiya mama nan falon ta na samay ta na zube kasa ina gaida ita take cewa hadija yaushe a garin ?

  Nace jiya da safe na shigo nazo duba Ya Amina ce da jiki  tace ayyah ai amina taji jiki wallahi haka take cikin ta ita.

   Nayi murmushi nace tace in karbo mata lemun tsami a gurin ki ne tace to barin in tashi in duba maki ko akwai saura.

   Sallaman su ne ya katse muna magana ta amsawa tare da fadin yaushe kuka shigo garin nan kuma ba labari don da gani anan kuka kwana.

   Hajiya jiya muka shigo munje zaria ne gurin kawu salihu sai dare yai muna a can kafin mu dawo cikin fadada murmushi tace toh daga wurin yaya din kuke ashe.

  Wuri suka samu suka zauna suka fara gaisawa dasu kaina na duke a kasa na somay da gani  du sai bayan sun gama gaisawa ne hajiya ta tuno dani tace Aff.

  Kinga khadija na manta dake wallahi zuwan wa yan nan na bazata da sukai muna da sauri suka kallo ni kowan su na mamakin ganina a dakin mahaifiyar tasu.

   Mikewa tayi tana fadin khadija ga yayan ku nan wanda ya taba rage maki hanya kwanaki ashe suna hanya suma da kin sani ai dasu kika biyo koda yake kin ce ke shigan safe kikayi.

   Ina wuni nace dasu cikin jin kunya ban ko saurari amsar su ba na kawar da kaina gefe ina wasa da yan yatsun hannu na.

  Fita tayi zuwa wurin fridge din ta dake waje fitan ta naji muryan Yusuf yana fadin khadija yaushe kika zo garin nan ne ?

   Nace don Allah malam ban saku ba ku bari in rabu lafiya da hajiya don kunyar ta nake ji sosai na fada ma wanan aljanna ce wallahi.

  Inba ba wanda ya saba dashi ba ba zai dauka shi yayi maganan ba alokacin  ban basu amsa ba don na hango hajiya tafe da bakar leda a hannun ta.

   Miko min tayi tana zama tana fadin ki gaida min ita da jiki in na samu lokaci zan kara shigowa in duba ta.

  Nace to mama an gode na mike da sauri ina barin dakin naji tace yaushe ne zaki koma Abuja ke.

   Nace gobe zan koma mama tace ku yaushe ne zaku koma tana tambayan su suka amsa mata da yau insha Allahu.

    Ai na dauka sai goben zaku tafi sai ku rage mata hanya nidai na wuce na barsu nan ina sauri in fice gabana na faduwa da ganin su.

  Har nayi nisa naji muryan Yusuf a bayana yana fadin yar gidan mama gani fa na biyo bayan ki.

   Tsayawa nayi ina jiran karasowan shi inda nake ya iso yana fadin surprise to see you dama ashe kema zaki shigo kaduna baki fada muna ba ?

  Yaya tace bata da lafiya nazo duba ta yace gaskiya naji dadi da na ganki nan nace namay fa   baka san ina zuwa nan bane dama ?

  Yace na sani amma banyi tunanen zuwan ki nan a wanan lokacin bane sai abin ya ban mamaki matuka.

  Nace zai shige sai mun hadu idan mun koma yace shike nan amma da wata mota kika zo ne nace motar haya mana ina wucewa nake bashi amsa.

   Naba da baya naji yana fadin zamu biyo mu gaida yayar tamu nace basai kun zo ba an gode na shige gidan ya tsaya yana kallon gidan da na shiga.

  Abdul ya fito ya samay shi waje yake fadin dama kasan zata zo garin nan ne ita ma ko ta san da zuwan mu ne ta biyo mu.

  Murmushi yayi mai yace haka dai Allah ya tsara abinsa nima yanzu na ganta wallahi.

   Ina shiga nace dana sani wallahi da ban shiga gidan nan ba yanzu wallahi ina mika mata ledan nake maganan tace saboda may?

  Nace wai fa mutanen nan nagani a gida da sauri tace suwa nace su Yusuf da Abdulsamad mana tayi murmushi ta fara bude ledan tace a haka da yawa aiko na gode.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

           SEENABU

Ido Ya Amina ta bini dashi kaawai na shige daki iya yanzu haushin su su duka nake ji shiru shiru basu zo ba yasa na saki jiki na koma normal life dina a gidan.

  Kwana hudu nayi a kaduna na juya na dawo Abuja ban tsaya na sallami kowa ba don dama banda gidan su mommy ban shiga ko ina ba .

  Tafiyan marance nayi don ban da kaya a tare dani ba zansha wahalan zuwa hostel ba daga inda na sauka.

   Maryam ta tare ni da murna tana fadin wallahi har hankalina ya tashi da naga yau ma har dare baki dawo ba nace na tsaya ne inga yadda jikin nata ya kara sauki.

   Ban mata hiran haduwan mu dasu ba itama din bata tambaye ni ba don batayi tsamanin zamu hadu dasu ba a can.

  

   Suna gaisawa da Abba shine Nafisa ta kira shi tana fadin bata jin dadin jikin ta yau tun da ta tashi yace subbahanallahi yanzu zamu taso.

   Sun iso sun samu taje asibiti ance haihuwa da sauran lokaci suka dawo gida duk wanan abin su mommy dake gidan basu san wainar da ake toyawa ba a gidan.

  Don dama sai taga dama take gaida su da kwana bayan nan zasu wuni basu ganta ba a gidan.

   Ga A,A sun ga sauyi a gare shi sosai tun bayan zuwan wanan matar a gidan komai da yake masu na kulawa ya rage a yanzu wani lokaci har fita yake bai gasa dasu ba.

   Ya dawo duk da yadda yake ji ya rage jin shi yau direct gurin su mommy ya fara zuwa ya gaisa dasu sukai mai sannu da zuwa tare da tambayan shi mutanen gida.

  Ya amsa da suna lafiya suna gaida su ya fito ya nufi part din su kwance ya samu Nafisa tana barci ya dan dade a tsaye kanta yana dubata ya juya zai fita ta falka.

   Shima juyowa yayi yana fadin kin tashi tare da zama a kusa da ita yana tambayan ta jikin ta tana wani yamutse fuska take fadin da sauki.

  Taje asibiti an dubata ance ba haihuwa bane da sauran lokaci Allah ya sauwaka yayi mata ya mike zai fita tace samad yanzu ya dace katafi kai zaman ka ka kyale ni.

  Haba Nafisa jiyane fa nayi tafiyan nan kwana daya nayi a can kawai shine kike fadin na tafi na kyale ki haka ?

   Nasan wurin wanan yar iskan matar taka fati kaje ka fake ga wai aiki ne zai kai ka can barin fada maka wallahi baka isa kace zaka wullakantani ba ka dawo da Fati a gidan ba.

  Kallon mamaki yake mata yace idan baki yarda Fati ta dawo ba ai zaki yarda wata ta shigo gidan nan ta zauna ko ya fadi a hasale.

  Ke baki damuwa da abinda ke gaban ki sai bakin kishi kawai dake cin ki haka har zaki ce wai saboda fati naje kaduna.

  Idan ma naje gurin ta ai ba laifi bane don fati matanane kowa yasan ina da hakki a kansu yana fadin haka ya juya ya fice daga dakin.

  Bin shi tayi da kallo mamakin shine ya rufe lokaci guda a lokaci daya ya juye mata haka har yana da corrage din bude baki yana fada mata magana son ranshi.

   Amma sai ta basar da zance da fadin kila gajiya ne a tare dashi ita kuma ta tare shi da zancen Fati da bai kaunan ayi mashi.

  

Washe gari na idar da sallah ina zaune wayan Binta Abdulrahim kaunan  Abdul samad ya shigo ga wayana.

   Na daga in fadin B,A ya kike tace wallahi khadija Adamu baki da kirki yanzu kizo kd ko neman mutane bakya yi in ba mama da ra fada muna yanzu muna maganan ki ba wai kin zo kin shigo har gida mu baki ne may mu ba

  Dariya nayi nace Binta Abdulrahim ke nan ni da na shigo gidan ko amsan abu kuma ban dade ba wanan miskilin yayan naku mai jin kai ya shigo na fita.

   Ashe kwana biyu kika yi kawai nace hudu dai don jiya na dawo Abuja da dare tace baki da kirki naji nace da ita.

   Zamu shigo Abuja idan matar yayan mu ta haihu zan nemay ki ai idan mun shigo kin san mommy na garin gurin shi ai.

   Nace Ya Amina ta fada min da nazo kd ai tace kin san yanzu mun dan fara samun kan shi yana dan kula mutane sai dai ba can ba.

   Nace da san nu zai kula ku ai watarana tace ai shi nace ma hajiyan mu da ta tayar da hankali kin san shegiyar matace buzuwan nan.

  Don su mommy sun je gidan kawai sai ta kule kitchen wai ba zasuyi mata girki a gida ba ki san muguwa wai da yunwa zata hore su kuma ?

  Don kawai su bar mata gida tunda bata kaunar ta bude ido taga yan uwan shi sun rabe shi ko kadan nace wanan yayan naku kamar soko yake ai mutum ya zauna haka mace tana juya shi.

   Khadija kin fa san buzayen nan yadda suke wurin mallake maza ai ke da gani kin san ba banza tabar shi ba idan munzo dai ai zamu sha kallo don nasan sai an kwasa da ita.

   Nace idan haka ne may zai kawo ku kuma ba sai ku zauna gida abinku ba tunda ba dole bane sai anzo din tace kindan haihuwar ta ke nan na farko a gidan shekara shidda da aure sai yanzu ta samu ciki dashi ana ta cin duniya.

  Wani abu da ban sani bane na ji ya tsaya min arai nace ku kuka sani ni dai idan kin samu lokaci don Allah ki shiga ki duba min jikin yar uwata don in san halin da take ciki.

  Tace insha Allahu zan shiga in duba maki ita nace halan ina Z,A take ko ta fita ne tace gata zaune tana jin mu wai fushi take da ke .

  Dariya nayi nace su zainab manya fushi akan may idan batai hankali ba sai na hada ta da buzuwa matar yayan ku ta latsa min ita da kyau.

 Tace ai kawar ki ce gaku kuma zaune a gari guda waya sani ma ko kun kulane da ita dariya ne ya kamani sai naji wayan ya mutu nasan kudin ta sun kare ne.

   Ita Binta bata jin ta kiraka ta dade kuna hira har sai kudin ta sun kare zata kyale mutum sai kuma tunanen buzuwa ya fado min a rai .

   Tsuki naja ina fadin lalle wanan takai shu,uma nan nake ba maryam labari muka zauna nan muka rage mata zunubin ta wurin cin naman ta.

   Bayan kwana hudu da dawo wan shi cikin dare ana ruwan sama sosai na kuda ya taso ma Nafisa gadan gadan da kyat ta iya saukowa falo hayaniyar su ne ya tayar da su mommy inda mijin duk ya rude saboda bai taba ganin mace tana labour haka ba sai wanan karon don anty fati haihuwan da tayi duk a gida take haihuwan ta bai nan.

   Ganin ga haihuwa yazo mata gadan gadan bata ko iya daga kafa yasa mommu tazo da sauri gurin tana fadin ta duka anan shiko duk ya rude sai fafin yake mommy ku kamata mu kaita mota muje asibiti.

 Tace bata iya tafiya Iyan bawa ne tace don Allah mazan su fice su barsu zasu kamata zuwa waje su Yanyala ko komai sun kasa iya sai yare suke sun rude .

   Da taimakon Iyan bawa da mommy ta samu ta haifi yarta a gurin kukan yarinyar da ya karade falon ya dawo da hankali wa yanda ke waje suna jiran a fito da ita.

   Sai da suka gama komai ne suka ce a shigo daga ciki mommy ta kamata zuwa sama dakin ta ta zaunar da ita a ciki tace tayi wanka sai suje asibiti a dubata.

   Shine ya shigo dakin yana gaida ita da yima mommy sannu da fama iyan bawa kuma tayiwa yar wanka bayan an yake ci bi.

   Ta fito wanka ya kara dawowa dubata tana zaune ta dubar yar ta da tasha kayan sanyi a jikin ta tana barci don ruwan zafin da iyan bawa ta gasa ta dashi .

  Da murmushi dauke a fuskan shi yake fadin baki kwanta kin huta ba har anyi sallah fa tace yanzu dai zan kwanta.

  Yace ki dan kwanta idan mommy ta dan huta gari yayi haske sai muje asibiti a duba ku tace ai ko bamuje da mommy ba ga Yanyala nan sai mu tafi da ita.

  Mommy dai zamu da ita itada tasan kan komai yanyala mai ta sani yanzu ai kinga ranan dauko su danayi suzo su zauna damu ko ?

   Tace ko basu zo ba ai haihuwa dai zanyi yau balle ni kadai na sha wahala na ai ba da wani ba yace yanzu zaki fadi haka amma da kike son taimako ai sunan ta kike kira ta taimaka maki.

  Fuska ta daure da alaman bata son magana ya mike yana fadin yanzu dai sai ki huta kafin gari ya kara wayewa mu tafi ya fice daga dakin.

   Ranta ne taji ya baci bata so su sa mata hannu ga alamarin ta ba sai gashi haihuwan ma a hannu su mommy tayi shi taja tsuki tana jin haushin yan uwan ta da suka kasa taimaka mata a wanan lokacin.  

   Taja dogon tsuki tana kwanciya tare da tsurawa yar baby ta idanu tana son gano inda tayi kama da uban ta sai dai don kankantan yarinyar bata gane komai ba a gare ta illa yawan kaman da yarinyar keyi da ita na zubin buzaye.

   Shiko yana shiga ya fara kiran yan uwa da abokan arziki yana fada masu karuwan da ya samu .

   A ban gare na Binta ce ta fara kirana tana sheda min zancen haihuwan wanda yayi masu daidai don a karshen sati ta haihu don haka zasu samu daman shigowa wurin suna.

   Bayan mun gama waya da ita ne na shiga tunane   a raina maryam na shigowa nake fada mata zancen haihuwan matar A,A din addua tayi ga yarinyar sai cewa tayi saura muje barka ko ?

  Da sauri nace wa ai ni nan da kika ganin ba abu kadan zai kaini gidan nan ba sai ya kama dole balle idan bai kira ya fada min ba ko barka ba zan mai ba, .

  Dariya ta dinga yi wai ko ina kishine zai sa ba zan tafi ba nace yanzu idan nace zan tafi gidan shi ke ba zaki min fada ba maryam.

  In dai ya samu nayi masa a waya ya gode a watse taro lafiya dai indai wanan yar barikin mata nashi ne in ba a watse da tsiya ba da yan uwan shi.

  Nan nake bata labarin da binta ta bani na hana ma su mommy dafa abinci a gidan da sauri tace abincin da muka sayo masu ke nan fa khadija ?

   Nace wa ya sanar mata mara mutuncin mata kawai wai kamar mommy zataiwa rashin mutunci irin haka saboda ta samu guri a wurin shi.

   Dariyan mumuke maryam take yi nace wanan dariyan fa haka kamar wace taga an cuci wani ?

   Ganin bata da niyar dainawa ne yasa nayi banza da ita har tayi ta gaji ita kadai sai bayan kwana biyu ne Yusuf ya kirani yana fada min wai an masu haihuwa.

  Nace nako taya ku murna Allah ya raya yasa dadin musulmi ne aka samu yace amin sai dai baki tambaye ni ko wa ya haihu ba koda yake bazaki rasa ji ba a wan gurin.

  Wa yasan na san ku da zai fada min an maku haihuwa ni yanzu nake ji a wurin ka Allah ya dada sa albarka ga abinda aka samu .

  Amin yace tare da godiya kamar shi akaiwa haihuwan ya tambaye ni jikin anty na nace da sauki na gode mukayi sallama ya kashe wayan.

  Wurin gi nayi da wayan gefe na naci gaba da karatun da nakeyi sai dai ban gane komai ba a cikin karatun yi dai nake yi kawai.

   Maryam ta shigo dawowan ta ke ban daga cikin makaranta gaida ita nayi ina fadi  kin dawo ta amsa min da eh tana cire   kayan jikin tace yanzu naga abin mamaki a waje zan shigo.

   May kika gani na tambaya ba tare da na dago na kalle ta ba tace zarah ki na gani yanzu ko kallo na batayi ba ta shige Napep.

   Zarah fa kika ce yaushe  rabon da nasa ta a idona nima yanzu ina ganin ta watsar da zancen karatu  ne tana abinda taga zai fishe ta.

   Maryam tace amma gaskiya tayiwa kanta tana ganin wanan rayuwan da ta zaba shi zai fida rayuwan ta watarana.

  Ba ace mutum kada yayi yadda yake so ba amma idan zakayi sai kayi yadda ya dace don kada gaba kazo kayi daka sani.

 Don maza mayaudara ne idan ka hadu da wanda baida tsoron Allah kin ga kamar wanan mutumin ki din yasan ciwon kan sa sosai haka nima MS yasan mutunci na amma kawai don kazo karatu sai ka biye wa maza suna bata ma lokaci bayan su sun gama gina tasu rayuwan a baya.

  Idan da basu tsaya sunyi karatun ba yaushe ne zasu zama haka har su samu kudin da take kwadiyi a wurin su.

  Wanan tunanen nake yi kika ga ina son rage hurda da kowa yanzu tace khadija Allah ya raba mu da wanan halin ita fa mace batayi sai da namiji haka namiji bai yi sai da mace.

  Abinda yasa nace maki haka don rayuwa ne na taimakawa juna a tsakanin mu dasu to amma idan zakayi kada kayi haramtaciya wanda Allah ya hanna yanzu rayuwan ne yazo da haka.

  Sai dai mutum kada ya shagala da ruden duniya ya biyewa shedanun maza sukai shi su baro tun farko a yadda na sanki da mutymin ki dan iska ne na tabbatar tafiyan ku ba zai yi nisa haka ba.

   Mu godewa Allah da ya dube mu ya hada mu da natsatsun mutane sai kuma muyi adduan Allah ya kara kauda shedan a tsakanin mu ko wani lokaci.

  Nikan har ta bar maganan amma abin ya tsaya min a rai sosai sai nake ganin may ma zai hana in watsar da kowa yanzu har sai na gama karatuna in fara dating.

   

   Yau tunda ya fita office ya rasa gane kan shi sai ta fara aiki yaji bai iya karasawa ya aje, a haka Yusuf ya shigo ya samay shi zaune ya tas files a gaba sai kallo yake yi.

  Kallon shi yake tun daga kofa har ya karaso tun bai kai zaune ba yake fadin lafiya dai ko naga yanayin ka ya canza a lokaci daya.

  Dan gyara zama yayi yana kama goshin shi yace wallahi haka kawai naji jikina ya mutu yaki fada mai gaskiyan maganan yadda yake jin gaban shi na yawan faduwa haka kawai.

   Kallon shi Yusuf yayi yace muje in sauke ka gida ka dan huta kila yawan jigila da baki ne ya jawo maka haka tunda baka saba ba.

   Shi ya sauke shi gidan shi don haka ba a san dawowan shi gidan ba babu kowa a falon sai tv dake aiki don haka ya wuce kai tsaye sama inda dakunan barcin su yake.

   Tun yana hawa yake jin hayaniya na tashi a saman sai ya dauka yan barka ne har saman suka hau a step din karshe ya fahinci dariyan wani abu suke sai yaji yana son zuwa ya duba baby shi kafin ya kwanta.

  Haba Nafisa kina bani mamaki namiji kamar mijin ki zai gagare ki kin kasa juya shi yadda kike so a hannnun ki.

  Itako Nafisa sai tace ba na kasa juya shi bane dama vikin nan dake jikina ne ya hanani aiwatar da sauran aiki na amma yanzu tunda na haihu lafiya may za a fasa sai in dora a inda na tsaya kawai.

   Sai na kama shi na mayar dashi marayan dole sai abinda nace kamar mahaifiyar shi zan koma duk wa yan nan dagin kala dake ganin dun samu kan shi har zasu zo gidan shi suyi yadda ran su ke so ba za su ga kafan sake gigin zuwa ba kuma.

  Don kafin su wuce sai na samu sherin da na kula masu gidan nan sun tafi ta baibai ai ni kowa yaci tuwo dani ya san miya kawai yasha.

  Da baya baya ya koma dakin shi ya koma ya bude a hankali ya shiga ya kwanta bai taba yarda Nafisa zata iya fadin magana ba haka duk da yasan halin ta amma bai dauka takai haka ba.

   Sai zuwa can ta raka madam ko may ta shigo dauka dakin taji shi a bude ta sa kai ta shiga kwance ta hango shi rigingine ya na tunane.

  Da sauri ta karasa wurin shi tana fadin lafiya kadawo a wanan lokaci yace ban jin dadin jikina ne na dawo in huta.

   Tace tun dazu ka dawo ke nan yace shigowa na ke nan kika shigo sai ta sauke ajiyan zuciya yana lura da ita.

  Zata zauna yace ki barni in huta please ko zan samu barci jikin nawa ya sake haka yasa ta mike ta fita daga dakin yabita da kallon mamaki yana fadin Allah ya kara kare shi daga kaidin ta.

  Ranan yayi tunane iri iri a ranshi barcin da yake son yi gaba daya ji yayi ya fice mashi a idon shi.

  Shiryawa yayi ya fice daga gidan ya rasa inda zai nufa yaji sanyi sai tunane na yazo mashi a da in yana cikin wanan yanayin guri na yake zuwa muka shi rikici dashi har yaji ya manta da komai a ranshi.

  Sai da yakusa kaiwa ne tunane yazo mai a rai yaushe rabon da yazo guri na ya dubani yanzu zai iya kai wata hudu fa tun cikin wancan hutu kafin muje gida.

   Gaskiya dole ya hakkura da zuwa sai kuma wata zuciya yace mai ya tafi kawai yasan abinda zai fada min uzurin rashin zuwan shi din.

   Waya ya dauka bayan ya iso ya kira ni ina ganin wayan shi gaba na sai da ya fadi nayi saurin kashe wa ya sake kira ba kashe don yasan naga kiran nashi kai ya girgiza ya kara danna kiran na sake kashewa.

  Tsaki yaja ya kira Yusuf yace kace ma wanan yarinyar ta dauki wayana na kirata ta kashe min waya Yusuf yace wata yarinya ke nan.

  Kai tsaye yace khadija a takaice Yusuf yace ko tana class ne yanzu bata don yanzu sun rufe ya kashe wayan nashi.

   Yusuf din ne ya kirani shima ban dauka ba har kiran ya katse  ban daga ba karshe ma da naga zasu damay ni sai na kashe wayan gaba daya.

  Kiran shi tayi ya fada mai abinda ke faruwa yace bata dauki wayan nawa ba sai dai barin kira kawar ta maryam in ji.

  Maryam din ya kira yana tambayan ta ni ko ina ciki ne tace mai eh ina nan bari ta duba dakina ta gani sai zuwa can sai gata tace na duba bata dakin ashe tayi mai karya.

  Yace mata ya gode ya tayar da motar shi ya wuce badon ya yarda ba do  yadda yaga maryam din ta da farko ranta a bace ta dai kare ni ne kawai kada ya dauki wani abu.

   Bakin cikin da yake ciki yaji ya karu mashi kai tsaye gidan Yusuf ya nufa yana aje mota ya fada ciki yana huci tare da fadin ni za a kawo wa iskan ci don ta samu na zubar da ajina ina kulata take daukan kanta wata mace can.

  Kaida waye kuma Yusuf dake zaune yana kallon shi yake fadin haka cikin kafa mashi idanun shi yana so  ji ko shidawa ke fada.

  Sai cewa yayi duk haka suke dama irin daya mata basu da banbanci wurin karamin kwakwalwa wallahi ko wace taga kana kokari sata a inuwa sai tayi kokari kai ka rana kai.

  Wai may ke faruwa ne haka duk ka hargitsa kan ka haka yace Nida wanan yarinyar ne mana khadija don kawai yau na tuna da ita naje gurin ta shine har zata nemi ta wullakanra ni.

 Kai mutumi na cool down don Allah ka fa san khadija yarinya ce mai kaifin basira da aiki da hankalin ta kamar ba karamar yarinya ba.

                    Ke nan ka goyi bayan wulakantani da nakai kaina tayi min ke nan ko may ?

 Dole in goyi bayan ta don itama mutun ce kamar kowa don may zata yarda ka bata mata lokacin ta a banza bayan ta gama fahintar ka ba don Allah kake tare da ita ba.

               Ba don Allah ba fa kace Yusuf

   Kwarai kuwa don hakane tunane ta a yanzu tsakani da Allah yau rabon ka da zuwa wurin yarinyar nan zaka iya tunawa ?

   Waye khadija da zan ta binta koda da yaushe don banda aikin yi ko may ko yaushe zan kama hanya gurin wata can daba matana ba ko wata nawa ?

            Yusuf yace ba wanan ba yanzu in tambaye ka  may kaje yi gurin ta har tayi ma haka ?

  Wani kallo yayu mashi yace May naje yi kacs da ban kan lekata ne idan na tashi ko yanzu abinda ke kaini gurin ta ne ya kai ni ba wani abu .

   Kai mutumina kafito fili muyi magana kan yarinyar nan ni dai ba bako  ka bane ko na khadija ka sani watau kaje ka ganta ka sata wani abin sai aka samu akasin hakan kake ganin laifinta don taki.

  Yace ko gani  ta nayi ta ki daukan wayan mu na tura akira ta kuma wai ni zatace ace wa bata nan may ta dauki kanta ?

   Yace ita ce daidai da kai wallahi wace daga kai har Nafisa zakuyiwa ta tsaya ta kwatar wa kanta yan ci a gurin ku ba Fati bane ya dace tayi kishi da nafisa sai khadija ta dace da wanan.

   Kai duk mata a yau din nan daya na dauke su a guri na don may zanje gurin ta na debo baci  rai a gida nazo gurin ta don inji sauki sai ita ta zuba min nata dafin.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

          SEENABU

Yan uwa da abokan arziki ba laifi sun zo mashi karan suna sai dai taron ba wani dadi don mai jego ta tsare komai na gidan ta hana mutane suyi yadda suke so.

  Ganin haka ne tu sha biyu suka buga min waya suna tafe gurina don basu ga amfanin zama gidan da suke yi ba gara kawai su fita suga gari.

   Da waya har suka iso gidan da muke zama inda ake kira da up k na mata inda a nan nima nake da dakin na da aka kama min tun zuwa na Abuja.

  Ranan nayi mayan baki don karshen ta dole suka samu gaba wai mu zamu nuna masu gari shigan dai guda ne don ko yau wani abaya baki mai kyau ne ke saman lace din da nasa.

  Shigan yayi min kyau matuka don ya mayar dani kamar wata yar bukuwar haure dani munje wuse market mun dan leka gura re sai yamma lis muka bar SAHAD zuwa inda gidan yayan nasu yake inda suka zo suna.

  Don nace dasu ni ban sani ba can ko sai faman tambayan su ake don wata ta bar yar ta karama na barci a gidan ta biyo mu yarinyar ta tashi tana kuka sosai don haka ake tambayan ina suka je.

   Har shi kanshi maigidan da kukan yarinyar ya damay su yake tambaya akace mai suna gurina bai tsaya mamaki ba ya fara fadin may suka je yi wurin yarinyar dake makaranta.

  Mun shigo suna falo an gama rikici ke nan da buzuwa matar shi da Fauziya kanwar shi da su mommy don komai da ake shigowa dashi gidan buzuwa ta hana aba mutanen Abdulsamad sai idan kaje wurinta munafunci zata baka ko matan abokan shi haka bata ba abin sai taga dama.

  A daidai lokacin da suka gama rikici da Fauziya da tace sai an raba an basu nasu,  ranan ta murje ido tayi ma buzuwa tas a gidan abinda a da suke tsoron mata.

   Shigowan mu ne gidan ya dawo da hankalin mutane a gare mu su tambaya ina suka shige haka ne ni da zainab ce da Binta sai maryam muka shigo daga karshe gidan ina tako dadaya duk kan mu kwaliyan mu ba laifi.

  Tsaye yake yana magana a cikin fada muka shigo da sallama falon sai da ya so rudewa a lokacin da mukai arba dashi nayi saurin kawar da kai na mommy da na hango zaune na nufi gurin ta har kasa na zube ina gaida mommy ta dafa ni tana fadin khadija kina garin nan nazo na dade a nan ban ganki ba.

   Yanzu ma nasan don su Binta ne kika zo gidan nan da bamu gan ki ba na san har mu koma Nafisa dake zaune ta cika ta batse sai huci takeyi tana kokarin son tuno a inda ta san fuska na amma ta kasa ban dade ba muka ce da su zamu koma ko dakin bamu shiga ba.

   Binta na fadin ba wani abu a basu mommy shi kuma maigidan ns fadin Fauziya tashi ki hada nasu snack din nan da aka yi da drink’s lokacin har mun kai kofan fita daga katon falon nasu ko.

   Binta da zainab dake bin mu a baya ne ke fadin ku tsaya don Allah a kawo maku abin buki kutafi dashi na juyo nace da ita.

  No ku barshi kawai dama mommy muka zo gaidawa a a yan mata ashe kun samu shigowa bukin ku ma ?

  Muryan Yusuf ne dake fitowa daga cikin motar da ta parker a gaban mu yake fadin haka maryam ce ta bashi amsa da fadin wallahi fa.

   No ba buki ya kawo mu ba munzo mu gaida mommy ne tsaye Binta tayi tana kallon mu da mamaki tafiya na fara yi zan wuce wurin Binta tace don Allah ku tsaya ku karbi abin buki mana.

   Nace a barshi kaya zai muna yawa idan mun tsaya daukan wani abu kuma ke khadija wani kaya ke gare ki banda handa bag da kika rika nace shima ai kaya ne ko.

   Khadija ya kira suna na da karfi na juyo tsaya mana ku amshi kayan bukin maryam tace ya Yusuf muna sauri ne mu samu abin hawa kasan unguwar nan naku idan yamma yayi akwai matsalan abin hawa.

              You known each other ne dama ?

   Zainab ke tambaya cikin mamaki No ya dade da na san su ba irin familier din nan ba dai na fada ina yatsune fuskana.

   Barin sauke ku mana Yusuf yace da sauri nacevka barshi kawai zamu karasa ai na fadi ina ci gaba da tafiya na nufar get din zuwa waje.

   Da sauri ya shiga babban motar Abdul din yana fadin ku shigo in sauke ku nasu in ki amma Binta na ta kaudi motar yayan sune ai in shiga a kaimu hostel din .

  Zainab tace friend ku shiga don Allah bari muje tare a sauke ku sai yaya Yusuf ya dawo damu abubuwa ake fitowa dashi daga cikin gidan wai duk namu .

   Mommy ne ta fito waje lokacin da zamu shiga motan tana magana dani tace ga abin buki nan yayan su Binta yace a baku kuje dashi wai angode nace lokacin shima ya fito wajen.

   Yusuf ina zaka ne yace zan sauke su khadija ne hostel in dawo barin bi ka mu fita daga can zan tafi gidan MD dayani.

  Ga mommy tsaye ta kura muna ido dole na yarda muka shiga motar a tare dashi dasu Zainab da binta ya juyo yana fadin ku kuma ina zaku sukace zamu raka friend din mu ne yaya.

   Ba yanzu zamu dawo ba fa ku fita don Allah rike zainab nayi nace a tare zamu fita ke nan don  saboda su nazo nan din da kuma mommy.

   Sun yi mamakin jin maganan da na iya fada ma yayan nasu wanda suke matukan tsoro da girmamawa su.

  Sun dauka zai yi wani abu sai sukaji yayi shiru bai sake magana ba sai tsawan da ya daka ma Yusuf akan ya tsaya mana su sauka kokarin sauka nike yi zainab tace ki bari gobe zan shigo wurin ki da safe ai.

  Ta fice daga motar da sauri ta rufo kofan da mu a ciki yusuf ya kama hanya ya tafi daga gidan ba wanda yayi magana a cikin motar.

  Ya Yusuf ka tsaya dan Allah in sauka ko sauraro na bai yi ba sai tukin mota yake a hankali kwance abinshi.

  Tsuki na naja daga inda nake zaune muryan shi ne naji yace kibi a hankali    fa kada ki bata muna rai a nan sai kace wace aka ce za a sace ta.

  Nace ai in ma kunyi niya zaku iya hakan don iya yaudaran ku dariya sosai Yusuf yayi yace munyi kama da mayau dara ke nan khadija.

  Kasan ta iya shirme wani lokaci mu sace ki muyi may dake ai ba irin ki zamu sata ba har in muna satan yan mata.

  Yusuf yace nikan irin su zan sata don yanzu suna danyun su shar ai kaga daidai sata ke nan nace ai dama nasan zaku iya haka ba sai kun fada ba.

   Yace Yusuf ya tsaya a wani guri da ake sai da kaji ya mika mai kudi ya sayo muna da abinsha mai sanyi Yusuf ya fita ya barmu a motan tare dashi.

  Naji dadi da maryam ke cikin motar a lokacin ba a barmu mu biyu ba ko kallo gefen da yake ban yi ba maryam ne ta dan zugure ni wai in yi mai magana.

  Na kawar da kai kamar ban gane abinda take nufi ba tunane nake ta yadda zan fita motar nasu a lokacin Yusuf ne ya dawo dauke da ledoji a hannun shi ya shigo motan yana aje kayan a gefen shi ya ta da motar muka tafi.

   Ban akara ba sai gamu bakin hostel din mu da sauri nayi niyar fita daga motar amma motar tana rufe har lokacin ga sanyin A C motar daya damay ni.

  Suna zaune ba wanda yai magana a cikin su har dan wani lokaci can naji Yusuf yace daidai lokacin da nake fadin ka bude mu fita mana.

  Shikuma yana fadin gaskiya khadija ba a kyauta maki ba a kyauta maki ba da sauri ya dago kai yana kallon Yusuf din dake magana.

   Yusuf fitar masu da tsaraban sunan su su sauka don Allah zaka tsaya wani magana kuma yace ya zama dole mu bata hakkuri don bamu kyauta mata ba.

   Da akai mata may kuma ya tambayi Yusuf din cikin tsare shi da ido yace ai kaine mai lafin yaya zaka saka ta saba da kai daga baya kuma kazo ka share ta haka ba dadi wallahi irin haka kaima ka sani.

  Please ka fitar masu dashi mu tafi don ina da abinda nafito yi yanzu ba wanan ne a gabana ba zaiyi magana yace fito masu dashi nace please.

  Ai da ka barshi zuwa kawai mukayi in gaida mommy da su anty Fauziya da suka zo ya sake fafin don Allah ciro mata mu tafi ya sake maimaitawa.

   Fita Yusuf yayi daga motar ya bude bayan motar yana fitar da kayan da aka saka a bayan motar sai da nayi mamakin ganin yawan kayan da aka debo muna mu kadai.

  Haka na dake fuska daure na fita daga motan ban koyi masu godiya ba na fice fuuu a motar Yusuf ne ya tsayar dani yana fadin haba yar mama ki sasauta wanan fushin naki ku fahinci juna da mutumin ki.

  Dan Allah yaya Yusuf ka daina hadani da wanan mutumin don ba ajina bane shi mutumin da yake under control din mace macen ma yar haure ba jinsin nahiyar mu ba.

   To waima may kake son in kula shi aka in kula shi ya bata min lokaci ya hana mutanen arziki zuwa gurina ko may ?

   Subbahanalahi ina wanan maganan ya fito haka a bakin ki baki taba tunanen Abdulsamad son ki yake bane ko may ?

  Da sauri nace so so fa kace na girgiza kaina nace a,a dama kace kawai yana amfani dani ne wurin cin ma wani manufa nashi da zan yada da hakan amma ba wanan kalamin naka na so ba.

  Sam na sake girgiza kaina karo na biyu tare da fadin wanan wani sallon yaudarane kuma ka dauko yanzu.

  Yace to ko ki yarda ko kada ki yarda ni yau na fada maki son ki Abdulsamad keyi har cikin ranshi wallahi bai dai iya fitowa fili na ya fada maki ko ya nuna maki hakan.

  Wani irin kallo nayi mashi tare da girgiza kaina na juya na fara tafiya ina jin wani bacin rai a zuciya har na shige ba tare da na dauki komai nasu ba da suka aje muna.

   Kwanciya nayi ina tunane a raina maryam da wata suna shigo da kayan daki har suka gama ta debar masu ta basu daga ciki.

  Ta dawo ta zauna tana ta faman cicire kayan guda guda tace kai khadija akwai wanda ya samu abinda muka samu kuwa a wurin nan jifa wanan uban kayan da aka loda muna wai duk namu ne mu kadai ina zamu da wanan kayan haka ?

  Sai lokacin na dago kaina ina duban kayan data tara a gaban ta na maida kaina saman filo na kwanta magana Yusuf ne ke ta min yawo a zuciyana har wanan lokaci.

 Maryam ne naji tace wallahi khadija na yarda da Yusuf daya ce son ki Abdulsamad keyi har cikin ranshi ba karya ya fadi ba don ni na dade da sanin haka tun tuni.

  Ina jinta saidai ban yi mata magana ba har ta gama fadin abinda zata nace ke idan nace zan bata lokaci ga wanan mutumin ba zaki min fada ba maryam.

  May ke cikin gidan irin su Abdulsamad banda tarin rikici da tashin hankali kulun ni kwadayi bai kai idona ya rufe ga abin hannun shi ba wallahi.

  Salama nike nemawa rayuwana ko yaushe ba zan tsaya in yaudari kaina ga abin da nasan yafi karfi na tun yanzu akan matar shine fa ya daina kulani ke ma kin san da hakan.

  Tace da sauri Kin san uzurin shine da zaki yanke mai wanan hukucin haka khadaji idan yana son ki ko Allah ya kaddara akwai aure a tsakanin ku matar shi ta isa ta hana ne ko tayi kamar Allah ne.

   Sai dai in kece zaki bata kafan da zata hana din ta dauki kanta inda Allah bai kai ta ba kinatsu khadija ki san may son ki da zuciya daya.

  Ni na fahinci A,A irin mazan nan ne da furta kalman so ke wahala a bakin su sai dai suyi ta nuna ma mace alama amma basu iya furta mata da baki.

   Nace shine kike son in tsaya wahal da kaina gare shi ko may ni koda ya furta bai mun ba don ba zan so shi ba ma ban ra,ayin mijin tace a rayuwa na.

   Ban yarda ba wallahi ke ma kina son shi kishine dai ke damun ki ke ma kina ganin kamar ya mutu akan matar shi ya daina kulaki don ta.

   Haka zuciyar ki ta fada maki ashe nace mata bata ko fada maki daidai ba ke nan idan tace maki nima ina son shi.

  Tace idan baki son shi may yasa yanzu kika rage mashi tsiwa irin da don da dane da yanzu kunyi fada a motan nan yafi a kirga.

  Nace amma kin san wulakanci bai da kyau ko saboda haka ne na kyale shi badon komai ba yanzu dai ai kanku ake ji ku karaci gulman ku ku dawo hanya dai.

  Indai har kin san kina son shi ya kamata ku daina wanan shirmay tun wuri tun bazuwa bata kara kwace maki shi ba kuma.

  Ta kwace shi mana shi ya shafa bani ba nace mata cikin kunan rai tace dukkan ku dai ya shafa khadija bashi daya ba kin dai san so yanzu koda kike kirarin baki taba so ba a rayuwan ki.

  Washegari a wurina su Binta da zainab suka wuni don ba shiga school Friday ne yau sai sunday zasu koma kd.

   Don haka da yamma muka shiga gari dasu yawo sunyi mamakin sanin garin da nayi don sanin da sukayi min ba mai rigima bace ni.

    Munsha yawo sosai rana sai dare muka dawo hostel dasu bamu dade da dawowa ba wayan Binta yai kara ta dauko da sauri tana dubawa take fadin nashiga uku yayane fa ke kirana zainab.

  Zainab tace dauka mana kiji may yake kiran mu nasan dai sunga dare yayi ne bamu dawo ba suke neman mu ta dauka tana fadin hello yaya A,A yace kuna ina ne har wanan lokacin hankali mutane ya tashi.

  Tace gamu nan wurin khadija tun dazu ita ce zata rako mu mu dawo yanzu yace tana da motane tace a a yaya karatu fa take yi ina zata samu mota kuma ?

   Yace ganinan zuwa in dauke ku yanzu ku jirani in zo yace ya kashe wayan kallon ta mukayi nace yanzu ba zai bari ku kwana nan ba ke nan ?

  Tace tunda kika ga yakiramu ai haka yake nufi damu nace bari yazo ni zan fita nagan shi da sauri tace ke baki san halin shi bane bari kawai yazo din mu tafi gobe sai mu dawo muyi sallama ba shike nan ba.

  Zainab tace ni nafi sakewa a nan wallahi amma can gidan duk a tukure muke wallahi shegiyar matar nan tashi bata bari mutum ya wala a gidan.

  Dariya nayi mata sosai da take fadin haka ba a jima ba sai gashi ya kirats yana fadin su fito nace barin je in gashi tace bari dai mu tafi ban son fadan nan nasa wallahi.  Maryam tace ku bari ta fita ta gan shi mana ai zai yarda ku kwana nan idan ta roke shi baku san ko waye bane yaya AA kawai.

  Mikewa nayi na fita batare da na kula da kayan dake jikina ba a lokacin yana zaune a cikin motar shi ya fitar da kafa daya waje yana shakan iskan dake kadawa a lokacin .

  Na iso gurin sallama nayi mai ya dago kai da sauri yayi min wani irin kallo ya kawar da kan shi kuma kallon da ada in yayi min nasan na bata mashi rai ke nan.

   Sai dai yau ban san may yake nufi da hakan ba da yayi min shi nace don Allah ka barsu su kwana guna tunda gobe ne kawai haduwan zasu koma gida jibi.

   Ya sake kallo na a karo na biyu yace su ke son kwana nan din sukace maki nace suke son hakan bani ba yace to shike nan indai zaki basu kulawan da ya dace may zai hana nace mai sai yadago ya dube nayi saurin kawar da kaina gefe daya nima.

   Nace na gode na juya zan tafi naji yace khadija nayi saurin juyowa sai naga ya kada kai kawai sai kuma yace may yasa kika fito waje haka da wanan kayan ?

  Don Allah ki bar fitowa haka na roke ki please kallon kayan dake jikin nawa nayi sai lokacin na ga kayan don na cire abayan da na dora sama da muka dawo daki.

  Ki kula daga yau ban son ganin mace a waje haka gara idan mace tana cikin gidan ta zata iya amfani dashi haka ko ga mijin ta.

  Kai na rausaya cikin wani irin jan aji da ban san nayi ba nace ga matar da bata da miji fa itama sai a hanatayin yadda take so ko may.

  Yayi tsuki yace na dai fada maki ban so ki kula daga yau kada in sake ganin ki haka a waje daga yau.

  Jikina ne yayi sanyi na kasa yin wani magana kuma ya kawar da kan shi gefe bai sake magana ba sai ya mayar da kafan shi daya dake waje tare da jan kofar motar yana fadin ni na tafi sai da safen ku.

    Kin dai ji abinda nace dake ki kiyaye duk abinda nace dake ban so ban so ne ya rufe motar yai mata key gurin nake tsaye kamar wace aka kafe har ya bace ma gani na naja kafata na koma ciki.

  Ina shiga na samay su har sun shirya suna jiran shigowa na dakin nace dasu yadda na gansu a takure yace ku fito bai yarda ba wai.

  Zainab tace ai dama na sani don kada kice mun hana ki ne do  ba mu son kwana din amma ninasan ba zai yarda ba ta fada a sanyaye.

  Tare da fadin tashi muje Binta binta din taja wani tsuki tana shirin mikewa nace ya tafi fa tace don Allah ki bari nace wallahi ya tafi tun dazu na tsaya magana ne a waje.

  Wai da gaske kikeyi khadija nace wallahi ya tafi yace sai da safen ku tunda anan kuke son kwana indai kula daku naso ce mashi mudake nan wake kula damu ?

   Da sauri tace da kin muna tsiya wallahi nan dai muka sake muna ta hiran mu kayan bukin da muka dawo dashi a tare dasu mukai amfani dashi.

  Sai hiran buzuwa da Binta ke ta bamu a dakin wanda inda tasan yadda raina yake baci da ta daina bamu labarin abin haushi haka.

  Washe gari ma kusan tare dasu muka wuni a hostel din mu sai da yamma muka je gidan tare dasu yiwa sauran yan uwa sallama.

 Mommy tace khadija kice bakin naki ne dai wanan irin fresh da sukayo haka wurin ki dan kwana daya da rabi injin dai ba dan abincin naku suka cinye ba.

  Shine ya shigo nan ya gan mu kallo daya yai muna ya kawar da kanshi gare mu gaishe shi suke yi yace da alama kunji dadin zama a inda kukaje din ke nan.

  Mun dan jima tare dasu mukai masu sallama suka rako mu zamu tafi sai ga driver yace ance ida zamu koma a sauke mu .

ZAINAB IDRIS MAKAWA

            SEENABU

Tun wanan ranan ban sake ji daga gare shi ba ban kuma koma ta kan su ba ina karatuna hankali kwance don komai ina dashi a tare da ni.

   Ashe suna da kwana biyu bayan tafiyan bakin shi tafiya ya kama shi nan Nafisa ta tubure akan may zaiyi tafiya yanzu bayan yan buki basu gama tafiya ba.

   Idan na zauna may zan maki a gidan ina kudi kika sani na kashe maki wanda ni kai na ban san iyakar shi ba.

   Yan uwana sun tafi da takaicin abinda kikai masu a gidan nan bayan sun san da komai nayawa kike kadagi a gidan nan amma kika rufe ido kika hana masu komai da na kawo gidan .

  Haka suka tafi da bacin rai a tare dasu don ma mommy mace ce mai tunane da sanin ya kamata ta sa na samo masu abinda zasu koma gida dashi.

  Don baki da kunya yanzu zakice ba zan tafi neman kudi ba idan ban fita ina samo kudin nan a zaune kudin da kike kashewa zasu samay mu ko may ?

   Tunda ya fara magana bata katse shi ba sai da yakai karshen maganan shi tace ina da sunana kasai abin bukin ?

  Baka ce da wasu yan uwa naka zamu raba shi ba idan bakayi ba wa kake son yayi min da ?

  Tafiya kuma kana nufin ni kadai zaka bari da wahalan dubar yar ka ko may tare muka samay ta don haka tare dakai zamu rene ta babu inda zaka a yanzu kaji na fada maka.

   Yace tunda ke kika ajeni sai ki hanani zuwa mugani idan zaman ki nake yi ba ke ke zama na ba a gidan nan Nafisa kin dauki kanki ki  kai inda Allah bai kaiki ba fa.

   A da ana fadin ina ganin don ba a kaunar ki cikin mu ne yasa ake maki haka ashe halin ki ne hakan ban sani ba ina jiye maki ranan da reshen ki zai juye maki a gidan nan idan har baki nemi shiri da yan uwana ba.

  Tace wanan tunane kake a ranka dama akwai wani rana da zaizo min ba daidai ba gidan nan har in neme shiri da yan uwan ka to kasani babu wanan ranan a rayuwana da zan shirya da yan uwanka.

 Tunda tun farko sun iya nuna min rashin kaunar su gare ni yanzu may zai sa in dawo ina shiri da mutanen da basu so na ko kadan.

   Yace aike baki da kunyan fadin magana wani irin sone basu nuna maki ba da kika zo gidan nan musanman ma mommy amma kikai fatali da kowa don ke kan ki kawai kika sani .

  Ya ture ta gefe ya fita rai bace zuwa inda ake neman su dan bayanin tafiyan su ta tsaya tana kallon shi cikin mamaki.

  Don dai malamin ta yace da ita yanzu AA a tafin hannun ta yake saboda sun gama daure mata shi yadda take so kuma ba karamin kudi ta tura wurin yin wanan aikin ba.

   Shiko bayan ya fita daga gidan rai bace bai tsaya ko ina ba sai inda club din millonear in the world yake ya cika komai da zai cika na tafiyan shi kasan.

  Take a nan wurin suka maida mashi da amsa sakon shi ya karbu sai kudin da zaiyi tafiya da na komai suka turo mai yana barin haraban wurin ya wuce wurin Yusuf kai tsaye.

  Ya samu Yusuf wajen gidan yana shan iska taee da waya a hannun shi yana yi wuri ya samu ya zauna daga gefen shi ya tsiyaya lemon da yagani wajen yana sha.

   Yayi mamaki daya fahinci Yusuf da mace yake wayan yana kashe murya tare da zuba soyayya baki ya tabe ya kawar da kan shi gefe yana jiran ya gama wayan.

  Ya gama yana kallon shi   fuskan shi dauke da murmushi yace ya dai ina ka fito yanzu haka sai da ya dauki cup din juice din ya kara korawa yake fada mai inda ya fito.

  Yace amma kasan may wai ni yar rainin wayon nan zata raina ma hankali wai bata yarda inyi tafiya yanzu ba.

  Nafisa ke nan Yusuf ya fada yace ai kaima ka sani wazaiyi wanan haukan idan ba ita ba yusuf yace wai may matar nan ta dauki kanta ne halan ?

  Komay ta dauka zan bata mamaki ai kwanannan kuwa don sai ta rena kanta wallahi yusuf yayi saurin fadin baka iyawa ne ai shiya sa take kawo maka raini haka.

   Haka kake gani ko kamar yadda kowa yake dauka na ban iya aiwatar da komai akan nafisa yanzu kaima hakan ka dauko ke nan ?

  Yusuf yace ai haka din ne yanzu fa don haihuwa kai mata wanan irin sayayan haka bayan wanda ka din ka mata wanda zata fita dashi ga kuma sayayya kamar na hauka da ka da mata daga baya.

  Wanan ba komai bane Yusuf har in zatai amfani dashi ni mutum ne mai son in ga iyalina suna shiga suna fita a gida don haka ban jin kyashin kashe ma iyalina na kudi ko nawa ne.

   Kasan wanan halin ne ya hadani da Fati bata sawa bata kuma gyarawa amma mutane basu ganewa ida matsalan mu yake da ita.

   Mutum ko yaushe baka gane dadin ran shi kullun ya zauna kamar an mashi wani abu babu marmari ko kadan.

   Ita nafisa tana maka yadda kake so ne halan da ita da fatin duk jirgi daya ya kwasosu a gidan  banbanci dai kace ita nafisa tana sakewa da kai kawai ne.

  Yanzu badon yarinyar nan khadija da ta muka saya ma yara da ita fatin kaya ba a kwanaki ina ban dashi tunda suka tafi har yau bakai tunanen ka kara saya masu komai ba.

  Yarinya ta dauko saka ka a hanya tanayi hanyar alheri wanan bakar shu,umar ta shiga ta fita yanzu ta raba ka da ita nasan wurin shige shigenta can aka bata labarin khadija din ta sani.

   Khadija khadiji Yusuf ka fasan tafiyan mu ba zai zo daidai da wanan yarinyar da take daukan kanta wani tsiya ba.

   Yasuf yace yanzu ka gama fadi da bakin ka mace yar kwalisa da iya gyaran gida da jiki kake so a gidan ka.

  Daga cikin wanan wani khadija ta rasa a tare da ita ka fada min ya ja iska yace baka san wani abu ba wallahi ranan naje dauko su Binta da dare wurin ta.

  Kasan yarinyar nan sai da taso ta rikitani gaba daya Yusuf ya tambaya yace akan may kuma yace wallahi wani shegen shiga tayi tafito waje dashi sai da na kasa kallon ta.

  Ban san lokacin da nayi mata fadan haka na ba don wanan shigan sai ya rikita mutum a banza wallahi.

  Dariya sosai Yusuf yayi mashi har sai da yaji haushin shi yace malam na fada ma son yarinyar nan kake yi wallahi ka tsaya kana wani noke noke.

  Bari garin kallon ruwa wani ya rigaka  jefa fatsan shi kana kallo dama ya samu ka fida zuciyar ka ka tsaya kana wani izza haka.

   Shiru yayi mai yace bazan bata lokaci na ba kan wanan da yanzu ma take zama mace bata gama mallakan hankalin ta ba.

  Zaka sha mamaki wallahi khadijan ne macen da bata san wani abu ba idan bata san komai ba yanzu akan may take fushi damu.

  Badon share tan da mukayi bane kwana biyu ta dauki wanan zafin haka kana tunanen ita ma bata fada tarkkn son ka bane ko may ?

   Kallon Yusuf din yake yi yace abinda take ma fushi ke nan dama yace don may baza tayi fushi ba kuwa ?

  Kwana biyu da yin maganan su ya shirya ya tafi club din su inda zai buga game a can .

   

Banda labarin yayi tafiya sai dai ina murna a raina sun gaji sun barni ke nan tunda ban kara jin labarin su ba kuma.

   Sai dai tunanen su yana nan a zuciya na inda nayi wani sabon saurayi dan kabilar nufe koshi haduwan mu dashi a wani shago ne yana waya da yaren su na Nufe sai ya yar da dan wallet din shi kasa.

   Da yaren Nufanci da nake ji don zaman gari daya da nufawa da nakeyi nace dashi da yare kayar da wallet din ka fa.

  Ya juyo ya dauka yana min godiya a cikin yare yana fadin (Nufe wayyo ni )nace dashi a a ke yar ina ce ya tambaya a cikin yare nace ni yar Niger ce yace (kiyyo sunayo) nace dashi khadija.

   Sai yace Iam mamud by name yana aiki ne a CBN dake nan cikin garin Abuja shi mutumin garin Bidda ne dan murmushi nayi don kamar naga na gida ne da na ganshi.

   Nomber na ya tambaya na nuna bazan bashi ba ya matsa min sai na bashi da na sai turaren da nazo saye sai gashi mun hade wurin biya ya biya min nafito zan wuce sai gashi yace in zo ya sauke ni.

   Banyarda na bishi ba ashe ya biyo ni baya muna sauka shima ya tsaya yana dariya ya fito daga motar shi nan muka tsaya dashi yake fadi ashe karatu ya kawo ki,  nan ke nan.

   Murmushi nayi nace may yasa ka biyo ni har nan kuma yace don in san zahirin ki tunda kin ki yarda in dauko ki ni kuma ba zan yarda ki bace min ba ina ganin nayi babban kamun yar garin mu haka.

  Tun daga wanan ranan muka hade dashi saboda nacin shi dole nasaba dashi don mutum ne mai saurin sabo da mutane ga baa da iya magana kamar shiyayi kan shi.

   Tun ranan da suka fara haduwa da maryam tace yanzu kan kin samu daidai dake khadija haduwa da mamud yasa na manta zacen wani AA can a rai na.

  Shiko yana can yayi nasaran tafiya don shi yazo na daya ga gasan da sukayi na wanan lokacin ya samo makuden daloli a wanan tafiyan.

  Tsaraba yayo wa iyalin daga ciki Allah ya ciyar dani ya sako min a wani jakka na daban tun daga can ya ware min nawa.

   Yusuf yazo gurina inda ya samu mamud yazo sai da ya jira ya wuce yana zaune cikin motar yana kallon yadda nake kwasan dariya daga inda nake tsaye.

   Yana mamaki a ranshi yaushe har na hadu da mamud har mukai nisa haka dashi muna irin wanan hira don yaga na sake jiki sosai da mamud din.

    Mamud ya wuce sai lokacin ya kirani yana fadin gashi nan tsaye bakin hostel din mu yana jirana waige na fara yi sai dai ban ganshi ya fara fada min irin kayan dake jikina da yadda nake tsaye ina waige waige.

  Har na gano shi na iso gare shi abinda ya fara tambaya na shine waye wancan danaga ya tafi yanzu khadija ?

  Mamaki nayi da tambayan shi nace wani abu ne halan sai yace a yanda naga kuna hira dashi yasa na sha jinin jikina khadija kada fa yayiwa abokina yankan baya.

  Kai na rausaya nace wani abikin ka kuma ke nan yayana yace haba khadija tun yanzu har kina nufin kin manta damu ne.

   Nace haba dai abokin ka ai ba saurayina bane kuma bai taba cewa yana so na ba asalima shiba irin mazan da nake so bane.

  What har akwai irin mazan da mace ke so ashe sai yau naji wanan a bakin ki nace kowa da abinda ke masa kasani .

   Yace kina Nufin bai maki ba shikenan ko ko sai wanan dan kyamazon ne yayi maki da sauri nace kada muyi haka dakai yayana.

  Yace Allah ganin shi nayi kamar dan tsurut a motar bai wani cika motar tashi ba sosai nace akwai dai kishi ga maganan ka ke nan , ?

 Dole muyi kishin ki khadija don kin cancanci hakan a gare mu saboda ke mace wance ko wani namiji yake fatan ya mallaka a gidan shi.

   Nayi dariya tare da fadin kazo da wata magana ta daban ke nan idan kai nayi ma ai shi abokin naka ban mashi ba.

   Ko ya taba cewa dakai son na yake da gaskiya kaga yayana mu bar wanan zancen muyi wanda ya kawo ka yanzu yace maganan tana cikin abinda ya kawo ni ai.

  Bashi ya kawo ka ba kadai zo ne don duba kanwar ka na sani kuma gani ka ganni ai na kuma gode kwarai da gaske.

  Khadija ya kira sunana wanda ya nuna maganan da zaiyi tana da muhinmaci sosai a lokacin gare ni amsawa nayi da naam yaya na.

  Yace don Allah ki natsu kiyi abinda ya kawo ki garin nan ki bar biyewa irin mutanen nan da suke zuwa da karya.

   Nace yayana ban yarda na tsaya da mamud ba sai da nasan ko shi waye da sauri yace dani shi waye din kika sani.

  Dariya nayi nace yanzu dai mu bar maganan don Allah don naga bazaka fahince ni ba a yanzu gaba mayi idan mun hadu.

   Yace to shike nan tunda kin hada ni da Allah yanzu ina maryam ina son ganin ta nace ayyah maryam yau taje gida da yamman nan gurin yayanta.

  Kasan ita anan garin take da zama yayan nata ne tayi tafiya ta dawo shine taje mata sannu da zuwa yace ashe idan Abdulsamad ya dawo zaku zo tarun shi ke nan ?

   Da sauri nace da zai tafi ya sallamay ni ne da zanje tarun shi yace kece baki bashi dama ba don kina fushi dashi yasa bai sallamay ki ba.

  Wanan maganan kane kana kokarin gyara shi a wuri na ne kawai wanda ba zai taba gyaruwa ba kuwa.

   Murmushi yayi yace zan gano ko waye wanan dake shirin hure maki kunne haka har kike son yin wa kanki zaben tumun dare.

  Haka dai mukai ta zubawa dashi har ya kaimu wani lokaci a wurin karshe dai yayi min sallama ya tafi.

   Maryam ta dawo daga gida tana fushi dani wai naki zuwa gidan su in gaida yayanta da dawowa nace ba haka na bane maryam kina dai gani ba fita nakeyi ba amma kullun Daddy fadan da yake min ke nan in natsu.

   Kada ki damu watarana zan tafi mu gaisa da ita har ma in kwana ba shike nan ba haka yasa ta sake jiki dani tana bani labarin  yayan nata da abinda ta dawo dashi wanan tafiyan.

  Ta ciro wani dogon riga tabani tace yayan nata ne ta sayo muna ni da ita don yawan labarina da take bata ko yaushe.

  Nayi godiya tare da karban lanbata nace zan kirata inyi mata godiya tace mutumin ki baizo bane yau nace yayi tafiya ai da yanzu kin gashi nan..

  Yusuf dai yazo bakya nan ya gan mu tare da mamud yake wani maganan robish a kan sa tace saboda Allah nace wallahi ko.

  Ai dama na fada maki ina jiye maki ranan da zasu san mamud ya shigo rayuwan ki gashi wanan mamud din da alama baizo ba kamar sai da ya shirya maki .

  Nace kin jjiki da wani magana kuma ba wani shirin da yai min sone kawai wallahi ni kuma ya kwanta min sosai a raina.

  Tunda bada wasa yazo min ba ke ma kin sani idan yau zan ba mamud baki ya fito a shirye yake da yafito din.

  Allah ya zaba muna abinda yafi zama Alheri a gare nace amin yama zaba min din Allah sa albarka ya rage kice.

Kwana hudu da maganar mu na dawo daga class don yanzu karatun mu ya dau zafi sosai muyi nisa mun zama manya a cikin makarantan.

  Kwance nake ina hutawa ban cire kaysn da na dawo dasu ba wata ta shigo tana fadin wai ina da baki a wajen hostel nayi mamakin ko suwaye ?

   Sai lokacin na tuna wayana a kashe yake tunda zan shiga class na kashe wayan mikewa nayi daga kwancen ina gyara bujen jikina dakyau.

   Dinkin wasu material ne na india da mijin ya Amina ya sawo muna tsaraba nasa takalmana flats shoes na saka don ban faye sa takalma mai hill ba.

  Wani dan yalalon gyale na yafa akaina duk rabin jikina yana bude na fito don ganin wanda ke nema a wajen.

  Motar AA na hango can nesa kadan sun faka shi da Yusuf sai naji gaba na ya fadi ras don ban san may ya kawo su ba nasan kuma Yusuf ya fada mai zancen mamud yanzu haka ?

  In bashi ba may zai sa su zo gurin mutumin da bani a gabasa zai zo wurina yau kuma ?

  Haka na daure fuska na karasa inda motar tasu take aje cikin daure fuskana na isa inda suke sallama nayi masu irin na addinin musulunci.

   Tare da fadin sannun ku da zuwa Yusuf ne ya amsa min sallaman nawa don shi sai wani kallo yayi min ya kawar da kan shi gefe daya.

   Nima yi nayi kamar ban ganshi ba a wurin khadija ya kuke ya karatu nace Alhamdullahi kune tafe yanzu ashe yanzu ko na shigo hostel din ina cikin makaranta tunda safe.

   Aike ko alhudahuda ya kauce maki ga karatu yanzu kin zama ina zaki karatu,  ina kika fito karatu .

  Dariya mukayi dukan mu dashi nace sunan da na samu ke nan kuma yanzu yace sunan ki ke nan ai bakiga mutumin ki ya dawo bane banji kin tare shi ba.

 Nace ai bansan yayi tafiya balle in gaida shi da dawowa yace a a fa kada muyi haka dake nace to an dawo lafiya ya hanya ya mutanen can ?

  Saida ya sauke wani irin sayayan ajiyan zuciya yace Lafiya kalau suna gaidaku ya karatu fa nace Alhamdullahi lafiya.

   Allah bada sa a nace amin yace ya naga kin ramay haka may ke damuwan ki kuma ko duk karatun ne haka ?

  Nace kila dai idon kane ke ma gizo amma ni ban ji na ramay ba Yusuf yace yaganine ya fada halan dan banufen ki bai fada maki kin ramay ba.

   Daidai lokacin Mamud din daya fito office ya biyo ta gurina ya faka motar shi gurin idon ni da Yusuf muka bi motar dashi.

  Bai fito ba nima banje gurin shi ba don wullakanci baida kyau Yusuf yace wanan mutumin ya zama maye ana maganan shi sai gashi.

  Rai bace ya juya yana kallon shi yace waye wanan din kuma ?

   Cikin dakiya na bashi amsa da fadin wanda zan aura ne in sha Allahu  nan bada dadewa ba cikin wani yanayi yace What da mamaki nace barin kirashi ya gaida yayye na ai.

  Ban tsaya jiran abinda zasu fada ba na wuce wurin mamud nace mashi ga yayyena sun zo yazo ya gaida su da saurin shi ya fito daga motar yazo gurin su su gaisa.

  Sun dawo daga tafiya ne suka zo su duba ni ya mika masu hannu da kyat AA, ya bashi hannu suka gaisa dashi yana masu yaya hanya .

  Yace khadija zan tafi sai eight zan dawo tunda kina da baki yanzu ya juya tafi ya barmu nan dasu.

   Shiru gurin yayi na dan lokaci yusuf ne ya kawar da shirun da fadin khadija wai kina nufin da gaske wanan mutumin zaki aura ko may ?

   Kana mamaki ne da ba auren shi zan yi ba zan gabatar maku dashi ne a matsayin ku na yayyena a gaban ku.

  Yusuf don Allah ciro mata tsarabanta ka bata mu tafi kar mu bata lokacin mu anan nace ai da kun barshi ai ko ganin ka dawo lafiya yafi tsaraban da zaku kawo min .

   Don Allah ciro mata mu tafi don banda lokacin magana yanzu ban son damuwa akwai gajiya a tare dani ka sani.

  Fita Yusuf yayi ya bude bayan motar ya fito da wani jakka mai daukan ido yana miko min tare da fadin ga tsaraban ki nan aboki na ya kawo maki daga Italy.

   Nayi mamakin ganin wanan katon jakkan yadda ya dauko shi ba tare da matar shi ta gani ba godiya nayi bayan ya aje min jakka a gaba na.

  Ya koma mota ya tayar suka tafi na ja jakkan zuwa ciki ina mamaki a raina guri na samu na aje can kuryan dakina ina jiran shigowan maryam dakin.

  Sai da ta dawo tana shigowa da jakkan tayi arba tana fadin wanan kuma fa khadija ?

  Nace bari ke dai maryam wai tsaraba ne duk wanan kike gani su Yusuf ne suka zo min dashi A A ya dawo daga italy tace bakaji batun ba maye a ciki.

  Ban bude ba ina jiran ki dawo mu bude ne da sauri ta karasa wurin tare da jawo jakkan ta fara budewa tana ciro kayan dake ciki.

  Dogayen riguna ne a ciki har kala bakwai sai turare da su man shafi da jakka handa bag da sauran tarkacen mata a ciki .

  Zip din jakkan taja sai ga set din sarka da yan kune da awarwaro suma a ciki da sauri ta karasa fidowa waje.

  Sai da na gyara zama na alokaci don mamaki sai ta kara fida wani agogon hannu na mata mai ruwan gold mai daukan ido shima.

  Nauyi da kunyan kaina naji maryam ta dago kai tana kallona da mamaki fal a fuskan ta tace khadija kin ga wanan kayan kuwa ?

  Nagani maryam nace mata tare da lumshe idanuwana ni kadai nasan abinda nake ji a lokacin.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

           SEENABU

Jikina yayi sanyi sosai da kayan da naga ya sayo min musu kya dagani kasan ai kashe kudi a wurin sarkan maryam ta daga tana fadin.

   Wanan kan kizo kiji kudin shi zai kai a kala dubu dari uku fa saurin kallon ta nayi nace kai haba wanan dai kila mafa fashion ne kawai.

   Khadija wallahi gold ne haba baki ganin shi ko agogon nan ban debe tsamanin shi ma fashion bane nace a wani dalili zai sayo min kaya haka masu tsada bayan yasan iyayyena talkawane idan naje gida dasu may zan fada masu akan wanan kayan haka ?

  Rigunan ta sake tabawa tana daga su tace wallahi ko kayan nan anan zasu kai dari biyu kila koma sufi zaune nakai ina fadin shi wani irin mutum ne da baijin wuyan kashe kudi haka ?

  Maryam dariya tayi tace khadija ke nan baki san ko waye shi ba yasa kike fadin haka bafa karamin mutum bane wallahi kudi na shigo mai ta kowani hanya.

  Zasu iya sai da fili daya a wuni su samu milayan dari riba bakomai bane wanan a gare su wallahi kwanaki da mijin yaya na zai sai wani fili AA akace sai ya gani ya sa mashi hannu zai iya samun filin.

  To mutum da ke samun kudi haka don ya sayo wanan ai kamar ki jefa allura ne a cikin teku gare shi gashi nan muna ganin shi a banza amma mijin yayana yakai wata uku yana neman ganin shi bai samu ganin shi ba.

  Da sauri nace shi din tace wallahi Allah khadija wanan AA din kuwa shine don na tambayi anty na nayi mata kwatancen shi tace shine kuwa wallahi ba karamin kudi yake dashi ba ai.

  Banda abinki duk wanda kika ga ya auri buzuwa gidan shi har ta zauna haka ai ya mallaki abinda ya mallakane.

  Dubi shadda da tasa ranan da gwalagwala a hannun ta da wuya ke ko shaddan nan da zaki ji kudin shi zaki sha mamaki wallahi.

   Ido na lunshe na koma na kwanta ina tunane a raina gaskiya ya zama dole in raba dasu kada suzo su batani haka da itin kayan nan in zo gaba abin ya damay ni na saba da saka mai kyau in sha in kuma ci maikyau.

  Ranan da banda mai bani irin wanan yaya zanyi ga iyayyena tallakawa ne lis muna neman abinda zamuci a gidan mu.

 Muryan maryam ne ya dawo dani daga tunanen da nakeyi tana fadin khadija zaki iya samun fiye ma da hakan gun samari don kyauki ne ya jawo maki haka .

  Don ke din baki da maraba da yan buzaye dole ne na miji ya ganki ya rude haka sai dai shi AA nashi sallon son yazo daban da na sauran maza ne.

  Yace dake sona yake yi da kike fadin haka kawai dai mutunci ne a tsakanin mu kune dai dake da Yusuf kuke ganin haka din amma ni ba wani abu makamancin so daya taba hada ni dashi.

   Balle yanzu nasan da wuya su kara dawowa inda nake don na fada masu mamud zan aura kuma har na gabatar dashi a garesu sun gaisa dashi dazun.

  Kikayi may khadija amma wallahi baki kyauta ma kanki ba wanan wani irin cin fuskane haka kikayi masu lalle kan da wuya su dawo gurin ki kuma sai dai da yake maza ne basu fushi da abinda suke so kai tsaye.

  Mun dauki lokaci muna maganan da ita har dai nagaji na kyake ta tanayi ita kadai na bata baya.

  

Yau da wuri muka dawo dawo daga class bamu dade irin yadda mukan dade acikin makaranta ba maryam ta rigani dawowa har na samu ta gama abinci ko.

  Dafa dukan manja yaji atarudu ta hada muna sai naman datayi amfini dashi a ciki danye zaune nake ina cin don ita tace tasha tea da tadawo don maryam bata wasa da cikin ta ko kadan.

  Na kusan gama cine wata Ruth Samuel ta shigo dakin tana cewa ina da bako a waje yana jirana maryam ne ta kallo ni bayan Ruth tafita daga dakin tana fadin yanzun haka mamud ne dan kadafin tsiya ya biyo ki.

  Nace kada kiga laifin dan bawan Allah a banza don nagane ke son wanda baisan kinayi ba kike yi yasa kike ganin laifin mamud din.

  Hijjab dina karami na dauka ina sawa nake maganan na fita waje ban jira may zatace ba kada ta bata min rai.

  A zatona mamud din ne yazo amma ina fita sai banga motar shi ba a wurin fitowa Yusuf yayi daga cikin motar da yazo da ita yana min hannu.

  Zuwan Yusuf din ya bani mamaki matuka don banyi zaton zasu kara dawowa inda nake ba kuma .

Na iso inda yake tare da sallama yanayin shi kawai ya nuna min bai cikin dadin rai a lokacin yace ya karatu nace Alhamdullahi.

  Shirune ya dan biyo baya sai ido daya kura min yace dama nazo ne neman alfarma a gurin ki idan zaki iya yi min .

  Da sauri nace in zan iya may zai hana in maka tunda har kataso kazo gare ni a wanan lokacin haka.

  Ajiyan zuciya ya sauke yace ina son ki shiga ki shirya yanzu ki fito in kai ki asibiti ki gaida Abdulsamad ne yau kwanan shi biyu kwance bai da lafiya ya dawo da ciwon ciki sosai tunda ya dawo.

   Subbahanallahi na fada mace ciwon ciki kuma kodai yaci wani abin ne baku sani ba yace ciki da kai yake fadin yana mai ciwo tun kwana biyu da dawowan shi waje.

  Ko ranan da muka zo wurin ki cikin karfin hali nasa shi muka zo ke kuma sai kika bata muna rai da dan banufen ki.

  Murmushi nayi nace kuka dai bata ranku ga banza amma ni ban bata maku raiba gaskiya yace kin ko san kishin maza yafi na mata khadija ?

   Kishi akan may zaiyi kishi kuma don dan wanan magana kawai yace wallahi ba don nasan Abdul tun farko baida lafiya ba da sai in ce har da maganar dan banufen nan ya sashi ciwo haka.

  Sai dai bai karamin magana ba tun wanan lokacin a kan ki yanzu ma ni naga dacewan haka nazo daukan ki muje ki duba shi don Allah.

  Nace gaskiya ba zan iya zuwa ba da sauri yace khadija kada muyi haka dake mana na dauka zan iya saki abu kiyi don ni koma badon niba ai yaci kije ki gaida Abdulsamad din tunda akwai mutunci.

   Kai na girgiza tare da fadin Allah dai ya bashi lafiya amma ni ba zan tafi ba idan ma naje matar shi ta ganni may kake son in fada mata kuma don komai tamun tana da gaskiyan ta.

  Balle ma bazaku hadu ba don ita tana gida bata faye zuwa ba sai sa a mommy ce dai a gurin nashi take jinyan shi.

  Ko zan tafi bani kadai zan tafi ba sai inda maryam na fada yace gaskiya ne hakan yana da kyau ai wallahi ni ma kin ga na rude ban ko kawo haka ga raina ba sai yanzu.

   Don Allah ki daure kizo muje khadija yin hakan yana da kyau sosai wallahi ciki na koma na fadama maryan zuwan Yusuf din tace muje don Allah ki duba shi gaisuwa ai ladane gare shi so sai.

 Mun shirya ba laifi don zakace ba asibiti zamu tafi ba don maryam ne ta saka in shirya haka don kada muje mu hadu da buzuwa a can ta raina muna wayo.

 Nace in sha Allahu ma baza mu hadu ba har mu dawo muka fito muka kama hanya ina gaba tare dashi maryam na zaune a baya.

  Yusuf ya kawar da shirun da motar yayi a lokacin yace nasan zaiyi mamakin ganin ku yau saidai don Allah ki tuna a wani hali yake yanzu.

   Nan dai ma banyi magana ba sai murmushin da na danyi kawai yace maryam khadija ta fada maki abinda tayi muna ranan ko ?

  Wallahi ta fada min bata kyauta ba ai nayi mata magana kasan tayi nisa yanzu ga son dan banufen nan bata jin kira sai ta kai.

  Da sauri yace ehyehh tayi nisa fa kikace har ya shiga gidane bamu sani ba komay ?

   Amma khadija idan kin muna haka baki kyauta muna ba wallahi yaya zaki yi da abokina kuma idan kika fitar da wanan mamud din ?

  Nace Allah kadai yasan wa zan aura yanzu da kuke wanan magana niko mamud din ina shakku a gare shi ne don ban faye son mutum mai mata ba a rayuwana .

   Murmusgi Yusuf yayi yana kada kanshi yace yanzu dai kikai magana dama nayi zaton don ki musguna na munane kikai hakan.

   Nace a a wallahi ni gaskiya na na fada maku har cikin raina bandai son mai mata ne a rayuwana yasa nike shakkan shi.

   Tsaya yayi ya sayo kayan dubiya asibiti ya dawo ya shiga motar muka tafi dan jefi jefi yake dan jan mu da magana har muka kai inda zamu.

  Motar ta shiga cikin Turkeys hospital ya samu wuri ya faka muka fito zuwa cikin dakin da aka kwantar dashi wurin tsit yake baka cewa akwai mutane saboda natsuwan da wurin ke dashi.

   Da sallama muka shiga dakin yana gaba muna bayan shi biye har zuwa cikin dakin yana kwance rai,rai ya doran hannun shi daya saman goshin  mommy tana zaune gefe saman kujera tana duban wayan hannun ta.

  Sallaman mu yasa ta dago kan ta tana amsa muna tare da zuba muna idanu don bata sheda ko suwaye tafe don maryam ce ke bin Yusuf din.

  Sannun ku da zuwa tace muka amsa da sannu mommy muna gaida ita sai can tace khadija kune tafe kun san baida lafiya ne ashe , ?

  Yusuf ya karba da fadin wallahi sunji mommy yanzu na gansu shigowa nan din na karaso dasu ya mai jiki nace da mommy .

   Mai jiki gashi nan yaji sauki yau ai mun ga hankalin shi jiya kan da muka zo abin ai ba dama wallahi.

  Maida hannkali na nayi inda yake kwance yana saye da wandon three quarter fari sai yar riga irin na shan iskan maza din nan mara hannu amma rigar na da kauri blue colour.

   Ya jikin nace a cikin wani irin murya mai taushi da sanyin jiki tare da dan kura mai manyan idanuwa na a hankali ya sauke hannun shi saman kan shi yace da sauki.

  Shirune ya biyo dakin na dan wani lokaci Yusuf ne ya karaso zuwa bakin gadon suna magana dashi wanda ba lalai ne mu jisu ba.

   Ledan da muka shigo dashi ya mika wa mommy yana fadin mu muka zo dashi tace kai khadija ina laifin zuwan da kukayi ke da ke makaranta kikaje yin wani dawainiya kuma haka ?

   Tana nuna mashi daga inda yake kwance tare da fadin kako gane ta yarinyar nan ne kawar su Binta da suka kwana wurin ta kawar matan officer na layin mu.

   Murmushi yayi mata kawai ba tare da yace komai ba muna nan tsaye jin yace yace Deedar akwai ayaba ki bare min in ci kai na gyada mai ba tare da nasan ko akwaishi ba.

   Na bude ledan ina ciro ayaba daga ciki na fara barewa na miko mai tashi yayi zaine ya dan jingina jikin shi da filo ina mika mai a hankali yana karba dakin yayi tsit a lokacin.

   Kofan aka turo wasu mata ne suka shigo dakin hamshakai dasu idon su caraf a kaina a yadda nake tsaye wurin kan shi ina bare mai ayaban ina bashi yana ci ko mommy ido ta zuba muna tana kallon mu sai take gani kamar da can musan junane ko kuma namu daine yazo daya bata sani ba.

   Shigowan matan ya dauke mata hankali ga barin kallon mu ta maida hankalin ta gare su suna gaisawa dasu.

   Kun fara jerabawa ne ko da saura ya tambaye ni mutum ba zai iya fahintar abinda yake fadi ba saini dake kusa nake jin shi nima a hankali na mayar mashi da amsa da cewa next week zamu fara insha Allah.

  A yadda muke magana zaka dauka wani magana mai ma,ana mukeyi idon matan nan da suka shigo su uku ya dawo a kan mu suna kallon mu gashi jikina na kusa da nashi kamar dai mata da miji.

   Mommy ke fadin yaji sauki sosai yau gashi ma yana cin ayaba har mun ga idon shi ai jiya abin ba dama wallahi.

  Basu tsaya ba suka yi ma mommy sallama tare da fatan Allah ya kawo sauki suka fita muma bamu dade ba mukace zamu tafi Yusuf ya taso yana fadin barin je in sauke ku ko ?

   Sallama mukai masu muka baro asibitin Yusuf ya fito ya sauke mu tare da yi muna godiya nace ba komai ai Allah dai ya bashi lafiya.

Fitan matan kenan daga daki suna shiga motar su dayan tace nikan yau naga abu wallahi wai waye wanan yarinyar danagani tare da mijin Nafisa.

   Dayan tace aini yau imani ya kashe ni anan anya Nafisa batai sakaci ba kuwa ta yaya zata zaune gida ta bada damar wata na mata jinyar mijin ta don tsaban son jiki da sakaci irin nata.

  Wanan may ta sani banda karyan arziki da nuna son miji a baki kawai waya ta daga ta kiranta tana labarta mata abinda suka gani.

  Bata jira ta gama bayani ba ta kashe wayan tare da fitowa waje a sukwane tana zunduma ashar tare da fadin su Yanyala su biyu ta.

  A hanya take fada masu abinda ke faruwa a asibiti da mijin ta da wata sai dai kafin su zo mommy tasha ita da Yusuf da mijun nata uwa uba yarinyar da bata san ko wacece ba .

   A fusace ta turo kofan mummy dake zaune tana lazimi ta dago kai tana kallon ta da shigowan ta tace ina yar iskan yarinyar da tazo tana bare ma Ayaba ina karuwan yarinyar ta tafi ?

  Wacece ita wa ya bata dama tazo kusa da miji na haka tana magana tana zaran ido ta kalli mummy ta kalli Abdul di dake kwance yana kamllon ta.

  Nafisa you’re very stupid zaki shigo ma mutane daki ba sallama kizo kina fadin rubish haka wakika ba ajiyan yarinyar da kike tambaya ?

  Mommy tace wace yarinya wai take magana ne wani kallon wullakanci tayi ma mommy din tace ko wace yarinya ce ai kun sani ni za a munafunta kuma ?

   Dama na sani ai abinda ake kulla min ke nan ba yau ba wallahi anyi kadan aga baya na a gidan nan balle aje a dauko wata karuwa tazo tana bare ma ayaba tana baka a baki.

   Subbahanallahi wani munafuki ya fada maki haka mommy barta an bare min ayaban an bani a baki may zakiyi ?

   Au ashe ma kasan karuwan ka tazo har ta baka ke nan karuwa kema kin san nafi karfin karuwa don yar kwarai ce ba irin ki ba da tashigo duniya tabar iyayyen ta.

  Babangida kubar maganan nan don Allah tunda kai kasan gaskiya tace dole kice haka mommy tunda dake ake hada bakin yin haka.

   Samad akan karuwa kake zagi na har kake min gori na baro iyayyena gida nazo nan ni kadai.

  Ba karuwa bane yadda na aure ki haka itama zan aure ta in kawo gida ta zauna dani tafiki komai da kike tunanen kina dashi.

   Ido ta waro waje kafin tai magana security din asibitin suka shigo suna kokarin jan ta waje suna fadin ba ai masu hayaniya anan kuma ba lokacin zuwa duban marasa lafiya bane yanzu.

   Samad aure kake fada min da bakin ka zakayi aure fa kace suka tura ta waje tana masifa tana zagi mommy mamaki ne ya cika ta da jin kalamin da ya furta.

  Bayan fitar ta tace Babangida dama kuna tare da khadija ne ko dai ka fada mata hakane don ka bata mata rai.

  Mommy bar yar iskan matar nan da bata da hankali zanyi maganin ta nan bada dadewa ba.

  Lamarin Nafisa ne sai hakkuri kabar biye mata kuna sai da hali haka haka ba tarbiyan ka bane wallahi.

     Bai iya mata magana ba don ranshi a bace yake da abinda nafisa tazo tayi masu yanzu sai mommy tace wai ma a ina taji wanan abin ?

  Har take aibanta yarinyar mutane haka khadija ne take kira da karuwa wanan bata da tarbiya wallahi.

  Har ta kare bai mata magana ba tace Allah ya kyauta taja bakin ta tayi shiru zuciyar tab da sake sake a cikin shi.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

            SEENABU

Kwance nake saman katifan dakina ina karanta handout dina maryam zaune a bakin katifan tana gyara kumbar kafan ta.

   Waka take wanda take damuna dashi sai ya hanani yin karatun  tunanen mamud nakeyi wanda ya kai sati biyu yanzu bai lekoni ba kuma banji daga gareshi ba har wanan lokaci.

  Hijjab dina dake gefe na dauka na rufe jikina dashi tace sanyi kike ji ko may da zaki rufe jiki haka  nace sanyi nake ji wallahi.

  Na kara jawo handout inci gaba da karatu tace wai ni ko dazun sai naji kina waya ina son in fito in tambaya wakiraki ko mutumin naki ne naga ya dade bai zo ba kuma banji yana kiranki ba.

   Maryam kin damay ni fa karatu nake kuma kin gani a, a wani karatu yanzu inga kina tunane  ke kika ga wanan din na gyara kwanciya ina bata baya.

   Sai da ta gama abinda takeyi tace don Allah tace muje mini market mu sayo kayan miya nace ban zuwa tare da lumshe idona.

  Fada min a jiki naji tayi tana dariya tare da sake ihu daidai kunnuwa na a zabure na mike na biyo bayan ta da gudu zuwa waje.

   Dagani sai dan body hook da nake sakawa a ciki in dora abaya kaina ba dan kwali gashina dana daure ya fado min a baya don duk zuben filani na gajeshi wurin kakannin mahaifan daddy na.

   A daidai lokacin nz hango motar su tana fakin a daidai inda suke tsayawa da mota idan sunzo guri na ban dauka su bane sai da na duba da kyau don gurin na kowa da kowane masu zuwa wurin yan matan su.

  Itama maryam din ta gansu da sauri ta dawo inda nake tsaye tana fadin su yaya Yusuf ne can ko ? 

  Ba yadda zanyi don sun gama gani na gashi ko dan kwali babu akaina da sauri na koma ciki ita ce ta tafi wurin su tana gaidasu.

  Yusuf ne ya tambaye ta gudun may muke haka kamar yara tace wallahi khadija ce ta biyo ni da gudu wai ina damun ta tana karatu.

  Na fito daga ciki na dora a baya saman kayan ina hararan khadija na iso inda suke tundaga nesa ya watso min harara yi nayi kamar banganshi ba na kawar da kaina ga kallon shi  ina gaida su baki daya.

 Har muka gama gaisawa da Yusuf yana tambayana karatu da kwana biyu nace lafiya maryam taso ta bar gurin da dabara Yusuf yace ta tsaya ai .

    Munzo muyi maku sallama ne zamu tafi umura gobe idan Allah ya kaimu mukayi masu adduan adawo lafiya Allah yasa a karbi ibada.

   Daga ida yake zaune baiyi magana ba tun zuwa su yace ashe baki jin magana baki daina saka kaya irin wanan ki fito dasu waje ba ?

  Nace wasu kaya kuma ina duban kaina da shigan da nayi yace ai kema kin sani yaya kika fito waje dazun ?

  Haba yaushe zaka daina samin ido hakane aiko wanda zan aura yanzu bai isa ya zaba min kayan da zans saka ba a jikina sai idan naje gidan shi.

  Murmushi mai kama da yake ya sakar min yana fadin au haka ne fa kuma  gaskiya na faye sa ido.

  Yusuf yace kajiki da wani magana kuma akwai wanda yafishi sanin ya kamata akan ki ne yanzu dole ya nuna bacin rai ga abinda yake da iko dashi.

  Dariya nayi sosai nace sai kace nice buzuwa ko anty Fati wanan dokan yanzu ai sai daddy na yakai can.

   A bari a rabu lafiya kin ga tafiya zai yi kada a rabu kuna halin naku kuma kinga zai tafi dake a zuciya kila ba zai maki addua ba idan yaje.

  Addua kan kulun ai mahaifa na suna min shi kuma yana tasiri gare ni wanan bakin naki kuwa anya wataran bazai mutu ba khadija ?

   Dariya nayi nace yau dai kun tuna mu ke nan aka kawo muna ziyara haka yace bakin ki zuwa gida ki kara gaida shi da jiki ba ai shi baiyi fushi ba gashi yazo.

 Dan satan kallon shi nayi naga hankalin shi baya gare mu nan dai mukayi sallama dasu suka tafi.

   Da yamma ina kwance sai ga kiran shi ya shigo min a wayana nayi makai dalilin kiran shi sai cewa yayi fito gani bakin hostel din ku kai tsaye kamar yadda ya saba ya katse kiran.

  Na shirya na fito shi kadai na sama kamar yadda nayi tsamani bayan na gaidashine yake fadin dawowa nayi don dazu muna barin wurin nan Abba ya kirani.

  Yana son mommy ta koma gida kafin in wuce don haka nake son ki rakani musai masu abinda ya dace diban lokaci nayi a wayana bakwai da rabi na dare don haka akwai lokaci.

   Ciki na koma na shirya sai da na zauna ya tayar da mota nace kana dai son ka ban wahala kai da sukai ma hidima dakai da matar ka ni may ye nawa a ciki yanzu.

   Na dauka yanzu ma ai da shigan dazu zaki fito tunda ban isa in baki umarni ba ban dai ga dama bai don ba mai iko dani a yanzu.

  Allah yakaimu in dawo lafiya zanyi maganin wanan fitsaran naki lokaci daya .

  Ka fara maganin fitsariyar matar ta gida mai fita rabi tsira wace bata damu da hijjab ba balle gyale kafin kazo kafa min dokan ka .

  Sallon yaudara kawai zaka wani gama kalle min jiki kawani ce kai baka son haka na bayan sai da ka kalle ni tsab.

  Dama badon akalle ki kika saka ba idan ni kadai zan kalla ba matsala bane a gare ni wasune kawai ban son suga abinda nagani din.

   Don kanawa a gare ni zaka hana wasu su kalle ni kada ka mata ni yanzu a kasuwa nake banda hakkin kowa ai kaina amma ga masu hakki baka tsa, , , 

   Jinin hannun shi kawai nayi a jikina yana fadin barin fara gwadawa in gani ko tayi min tunda a kasuwa kike kinga idan yayi min basai kin tallata ma wasu mazan ba.

   Bugu nakai ma hannun nashi sosai da yakai ma jikina yana shafawa bai san ina yi ba sai kokarin gwaucewa nake yi ina buge hannun shi.

  Fuskan shi a daure bai fasa min abinda yakeyi ba wuri ya samu ya sauka daga titi.

  Da karfi nace bude min in fita ina kokarin bude kofar motar a gigice hannun shi naji yana cire min dan gyalen da na yafa saman dogon rigar da nasa.

   A take gashin kaina dana tufke daniyar in na samu lokaci inje gurin kitso ya bayana a fili hannu yasa yana wasa da gashin har zuwa inda ya tsaya.

  Take naji wani hawayen bakin ciki ya silalo min a fuska na haka bai sa ya daina abinda yake min ba sai ma ji danayi ta rungumay tsam a jikin shi yana sauke wani irin numfashi yana shafa na son ran shi.

  Kara sautin kuka na nayi a lokacin sai naji ya sake ni yana fadin are you crying bocouse of dis akasuwa fa kike yanzu.

  Hannun shi yakai saman fuskana yana wasa da hawayen dake zubo min din sai kuma naji ya rungumay ni zuwa jikin shi tsam na dan wani lokaci.

   Sai da ya gaji don karan kanshi naji ya sake ni ya koma saman kujeran motar ya kwanta yana maida numfashi a hankali.

  Kaina na dukar naci gaba da kukan abinda yai min din can kuma naji ya tada mota a hankali ya hau titi ba tare da yayi magana ba .

  Kofan bakin wani plaza mai girma  ya tsaya ban taba sanin akwai wuri haka a abuja ya bude motar a hankali tare da fadin fito mu shiga ki zaba masu abinda ya dace dasu kuma ki share wanan hawayen kada ace satoki nayi.

  Sai lokacin na dago kaina na dubi wurin nace ka sani har kullun Allah ba zai taba baka sa a akaina ba mayaudari kawai.

   Dariya naji yayi yana bude motar yace banda wanda Allah ya bani yanzu a kanki kuma koko kina nufin karfin ki ne ya kwace ki a kaina .

  Kuma ki daina kira da mayaudari don da yardan ki muka fito nan  ki sani banda niyar aikata komay yanzu a gare ki amma ki aje a ran ki time will soon come .

  Ko yanzu ke kikaja in maki haka da wanan bakin naki da bai taba mutuwa don ki san irin abinda zaki fada ma mutum.

   Fita yayi ya zaya ya bude min gefen da nake zaune na sauko motar a hankali na fito don girman jeep din nasa.

   Mun fara tafiya naji ya rada min a kunne anya kuwa ke ma ba buzuwan bace deedar wanan irin gashi da jiki mai dadin tabawa haka fa ?

  Hararan shi nayi idon shin kyam a kaina ya sake fadin nayi haka don ki san har gobe nafi wani banzan dake zuwa wurin ki komai.

   Banyi magana ba don mun kawo bakin shagon haka muka shiga a jera da juna sayaya nai wa mommy har da gaiya don har yaran ta na zabawa abu.

   Ya kalli kayan mai makon inji yayi korafin sunyi yawa sai ji nayi yace kina ganin wanan kayan sunyi ke nan idan kuma kin sai wa yaran mommy ita kadai su sauran yaran anty amarya fa ?

  Dole na koma na kara zaba muryan shi ne naji a bayana yana fadin ki zaba ma su ummi da su hajiyan mu kayan suma.

  Sosai ya kashe kudi bayan na mommy dana su iyan bawa gana su hajiya mama dana zaba masu super masu kyau su ma.

   Mun kai ya biya ko dar nanga yayi ba da akai mashi list din kayan aka saka ga wani katon buhu zuwa inda motar shi take tsaya nayi ban shiga ba sai da ya zauna ya leko yana fadin shigo mana mu tafi.

   Nace dashi katafi kawai zan bi taxis in koma ni da sauri naga ya bude kofan motan ban san lokacin da na bude na shiga ba muka bar wurin.

  Sai da mukayi nisa naji yace kina zaton abinda ya faru zai kara faruwa a tsakanin mu ne yanzu idan haka kike tunane kinyi kuskure.

  Don ni ko matana dake gida sai naga dama nake waiwayan mace do  ba haka nake ba kowani lokaci.

   Sai dai nayi mamakin ganin yadda kika narke min a jiki kaman dama jira kike in taba ki haka ya nuna min ke nan dama a jirace kike da hakan ya faru.

   Ban san lokacin da nace mai mugu mayaudari kawai macuci ba wanda ya taba min haka a duniyan nan sai kai kai kasan wani mace ta narke ma ajiki dan, , , , 

  Hannu yakai zai kara kamoni na gwace da zafin nama yayi murmushi yace gobe idan halin ki ne ki kara cika min baki haka.

    Ba sai ka kara ganina ba zakace in cika ma baki kaji dadin yaudaran da ka sabayi wa mata a kaina.

   Zaki bar Nigeria ne ko mutuwa zakiyi don wanan ne kadai abinda zai hana in ganki in kara kallon wanan suran da kike kasawa a kasuwa in riga kowa kwashewa.

  Haushi bai barni na sake magana dashi ba sai juya mashi baya danayi kawai shima bai sake magana ba sai da muka kusa tsayawa naji yace

   Wallahi shiyasa kike kara burge ni da wanan halin naki na dan juyo na harare shi yace yes i mean it da wata ce sai tayi nata sayayyan amma ke naga ko tsinke baki dauka a shagon ba naan kuma dole kin ga abinda zuciyar ki ke so a ciki .

  Kinga ke nan kin nuna min abin mutum baya gaban ki idan bai baki ba yana da kyau hakan keep on da wanan hali.

   Sai dai ai na biyaki ladan ki ko ina ganin ba sai an rubuta maki wani lada ba ko bani wanan lafiyan fresh body din da kika yin kin more ai ke ma.

  Ya tsaya da motar na bude najita a rufe na juyo na kalle shi nace bude min in fita hug me for d last time tunda kin ce baza mu sake haduwa irin haka ba.

  Malam ka bude min mota in fita ni ba yar iska bace ka sani wallahi ban sani ba zan dai sani nan gaba in Allah ya yarda ban fahinci abinda yake nufi ba bai kuma bude min motar ba yana jiran wai abinda yace.

   Na sake cewa da kai fa nake magana ka kyali ni yace even peck kiss yana lumshe ido kamar zan kai kiss din sai na cije shi a kumatunshi.

  Yana shafa wurin yana fadin wassh ko hakan ai na gode zan tunaki watarana na taba haduwa da wata manya yar Niger mai zubin half cas.

 Ya bude motar tare da fadin thanks ki kula da kan ki don Allah don kin bar min tarihi nace mugu kawai azzalumi mayaudari da sauri na fita do kada ya kara rufe kofan yana dariya yaja mota tare da min horn ya tafi .

  Ko da na shiga hostel na samu har martam ta kwanta ina shugowa tace kun dawo tare da duban time tana fadin ban dauka zaku dade haka ba ai.

   Zama nayi jagwal a wurin fuskana kawai zaka kalla kasan ina cikin bacin da sauri ta mike zaune tana fadin wani abu yayi maki ne.

   A takaice nace may ye bai mun ba yau maryam AA ya cuci ni ya shammace ni sosai wallahi da sauri naga ta fida ido waje.

   Nace ban taba sanin dan iska bane sai yau wai nifa AA ya ruguma maryam har da taba min kai kiji min dan iskan banza.

  Ajiyan zuciya naji ta sauke tare da fadin wallahi har kin saka gaba faduwa na fa dauka ko raping dinki yayi wallahi wani irin harara nayi mata nace ya ma isa.

   Tace cikin dariya yadda kikai maganan ai dole mutum ya tsorata yayi zaton hakan ne ya faru a tsakanin ku.

   Nace may ye marabin wanan da hakan don Allah bada hakan ake farawa ba har aje can daga magana kawai sai naji ya rungumay ni don kawai ya nuna min dan iska yake macuci kawai.

  Tace akan kayan dazu ko na kada mata kai nace ashe kin san abinda zai min kika bari nabishi ke nan tace kema kin faye baki wallahi .

  Ai gara da kika zabi law don kin iya bakin ki don Allah bani labari nikan in sha dariya don nasan yau ashe yasha zagi a gunki.

   Nace ban sani ba cikin hararan ta ina mike tace indai gulma kuka kai shi ke dashi kuna son juna kuna wani noke noke .

  May zanyi da wanan dan iskan ni bakiji ba ma wai shi ko matan shi sai yaga dama yake kara waiwayan mace idan yaga dama.

  Dariya mai karfi ta kwashe dashi tana fadin ashe akwai aiki kuwa kuma yake sha, awan kara mata fadi dai yayi wallahi.

  Toni ina ruwana da rashin kula matan shi ko ya kula ko kada ya kula duk uwar su daya a gun khadija don ba abinda ya shafe ni da hakan na fada mai.

  Nan nabarta tana min shakiyanci alwala na dauro ina son yin waka don kada ta zarge ni haka na fito na tayar da sallah na gama na kwanta banci komai ba ranan.

  Sai dai ba barci nayi ba don tunane ya hana ni shakat a zuciya na don da zaran na rufe ido abinda ya faru tsakanin mu ne yake zuwa min.

  Har dai barci yazo ya dauke ni ranan na makara da sauri na mike ina shiryawa sai ga wayan shi ya shigo min.

  Kamar ba zan daga ba kallon da maryam ke min yasa na daga wayan murmushi naji yayi tare da fadin nasan dai kamar yarda banyi barci ba kema hakan bazaki barci ba daren jiya.

  Akan may zan hana idona barci nace mai,  yace akan dan gidan mommy mana kema kin sani , nace Allah dai ya sauwaka kana ganin kayi wani abun gwanewa kenan,  mutumin da ko runguma bai iya ba sai ta hanyar karfi,  zai sa na kasa barci na kashe wayan.

  Yayi kiran duniya naki daga wayan sai ga text din shi ya shigo min kamar haka.

           Saboda kin san kin zuba min dahin ki a jiki daren jiya yasa kika fara garani ko may ?

                   Niba macijiya bace ai,  balle in zuba ma dafi

    Na tura mashi, ba a jima ba sai ga amsa shi kamar haka ,

   Kin fi macijiya dafi karfa ki manta ke mace ce,  mace ko shu,umace ko wace iri ce ita tasan sallon sheri ga da namiji.

   Kai dai ka sani da kayan sherin ka in ma dafi ne kai kazubawa kan ka bani ba ya karanta yana dariya bai san shigowar Nafisa ba dakin.

                  Sai jin muryan tana tambayan shi kaidawa ke waya haka kake dariya ?

   Dakewa yayi duk da kaduwan dayayi cikin ranshi amma a fili cewa yayi da ita nida Yusuf ne don yasan ba karatun boko ta iya ba balle ta amsa ta karanta.

  Ba don ta yarda ba ta kyaleshi kawai tana zargin shi a cikin ranta don yanzu ya fara bata tsoro gaba daya don ya daina sayin ta da yake yi a da can baya.

  Daga haka ya sauka kasa yana yana kiran yaran aikin gidan shi ya shigo mashi da buhun da ya dawo dasu jiya.

   Ya  sa akai masu dakin da su mommy suke tare dasu iyan bawa a gidan daidai lokacin Nafisa ta sauko kasa tana fadin Sabel wanan kayan haka daga ina kuma ?

   Yaro  gidan dan yaren su na buzaye yace maigida yace ya dauka yakai dakin dabakin shi suke ciki tabi buhun kayan da kallo nan ta so sanin abinda ke ciki.

  Don haka tabu shi a baya wai taje da sunan gaida mommy yau da kwana yana zaune saman kujeran dakin suna hira da iyan bawa ta shigo tana gaidasu idon ta akan buhun dake gaban shi nan ya fahinci buhun ta biyo a lokacin don ganin may ke ciki.

  Idon ta ya gano mata atamfan da ya fara fitarwa kasa yana son fitar da sauran sai gata ta daure fuska tamau idan da dane da ya shiga hankalin shi ga yadda ya ga ta daure fuskanta.

      Sai ci gaba da fitar da kayan yake yana bin sunaye su yadda na rubuta ajikin ko wani ledan kayan yana ajewa gaban mommy bai fara bayani ba ta juya ta bar dakin a fusace cikin bacin rai.

   Sai bayan fitan ta daga dakin ya fara yiwa mommy bayanin kayan tare da dora ma ko wani kudi a saman kayan yace suyi dinki sai Allah ya dawo dashi lafiya zai shigo yayi masu ban gajiya.

Kallon shi mommy tayi da kyau bayan ta gama sauraro  shi tace wanan hidimar yayi yawa haka  babangida don haka kabar kudin nan abin kuma ya koma biya , ?
   Mu da mukazo aikin lada zaka saka muna da wanan irin alherin haka mai yawa gaskiya hakan bai muna dadi ba gaba baka son inzo zama da diya ta ke nan in Allah yayi abin.
   Murmushi yayi yace ko baku zo nan ba mommy zan iya maku fiye da hakan don haka wanan ba komai bane Abba yace a tura ku gida yau kafin in wuce.
  Nasan ya kiraki ya fada maki komai ai don haka idan da sauran wani abin sai ku fada min a sayo maku kafin ku wuce na kuma gode kwarai da kokarin ku a kaina.
  Sai dai ayi hakkuri da yanayi matar gidan don Nafisa sai hakkuri nima dai kun ga shinakeyi.
  Ka dauki kudin nan ko ka rage dawainiyar yayi yawa haka abin ya zama  kamar biya mu kayi ke nan ya mike yana murmushi yana fadin ba komai iyan bawa ai yima kaine.
  Na shirya driver da  zai sauke ku idan kun gama sai aimin waya zan dan leka office don tafiyan mu sai dare zamuyi shi akwai dan sauran lokaci zuwa yanzu.
  Godiya sosai sukai mai ya fita nan dai mommy suka fara shirin tafiya don ba a ketare maganan Abba a gidan.
   Yana fitowa bai koma ciki ba ya nufi hanyar fita daga gidan muryan Nafisa yaji a bayan shi tana fadin dama nasan abinda ya zaunar da su ke nan a gidan nan tun bayan suna basu tafi ba kamar yadda kowa ya wuce.
   Suwa ke nan kike nufi wanda kasai wa kaya bada sani ba yanzu Allah ya tona ma asiri na gani do  baku so in gani ba.
  Wai nafisa kina da hankali kuwa iyayyen nawa ma bakin ciki kike dasu akan nayi masu alheri tace ai ba su kadai suka wahala a gidan ba har dasu Yanyala sun wahala .
  Don may ba zaka saya masu tare ba ka ware naka kadai watau sune ka sani ke nan kai ya girgiza cikin kunan rai yace ba laifin ki bane sai kawai yaga ta sha mai gaba ta inda zai wuce ta.
  Hayaniyar su ne ya fito dasu mommy waje ganin su mommy ba sa ta fasa ci mai mutunci ba mommy ce ta hana shi magana.
  Duk ta hade dasu mommy tana zagi tare da fadin tayi ma kowa nashi iyaka da gidan tun da ba zuwan arziki suke yi ba jifa samun wuri a gurin wanan matar ita ha gida taf da yan uwanta kullun sai kara yawan su takeyi a gidan.
  Kowa yazo da sunan ganin ta sai ya nemi wuri ya zauna ba maganan zuwa gida kuma gare su an shafe ke nan.
  Haka ya fita gidan ranshi bace ranan su mommy sun ga fitsara a gurin Nafisa inda tayi ta aiban ta su suna ji suna gani ba abinda zasu iya yi tana gani  taci gaban su.
  Ranan haka dai ya wuni cikin bacin rai halin Nafisa ya jutayin irin zaman da suke na rashin jin dadi a gare shi kuma bai jin zai iya rabuwa da ita ko kadan.
  Bayan su mommy sun gama shiri suka kirashi yace gashi nan zuwa ya samay su a shirye don haka basu bata lokaci ba suka fito da kayan su Yusuf suka loda a mota sukai sallama dasu suka tafi suna kara bashi hakkuri.
   Da yamma ya fito cikin shirin shi ya samay ta a dakin ta tana zaune tana waya ganin shi bai sa ta katse wayan ba sai data gama yake fadin su zasu tafi.
  Wani sabon lalura ta kirkiro mashi aladole kudin da take hasashen ya kashe ma iyayyen nashi sai ya kashe mata su bayan ya riga da ya sallamay ta da safe ta lissafa mai abinda take so ya bata.
  Nafisa wai may zakiyi da kudin da kike karba ne haka ya tambaye ta wani kallo tayi mashi tace idan zaka bani ka bani ba sai ka tsaya ka tambaye ni ba kuma ina sin idan ka dawo zan tafi gida inyi gyaran gidan mu na can.
  Dole ya bata daga cikin kudin da zaiyi amfani dashi don kawai su rabu lafiya da ita.

ZAINAB IDRIS MAKAWA   
             SEENABU

Tunda muka muka bar asibitin shiru nayi ban iya magana ba sai su ke dan hira jefi jefi a motan ajiyan zuciya na sauke ina fadin yanzu baku ganin kamar yawan ciwon kan nan wani abune ?
  Da sauri Yusuf ya juyo yana fadin wani abu kamar yaya sai nayi shiru kuma yace tambayan ki nake yi mana kin yi shiru kuma.
   Nace akwai ciyon kai irin wanan da yake na shihiri ne in kunyi diba ga irin matar nan nashi zai yuyu wani aike tayi mai wanda bai zauna a jikin shi ba sai ya iya haifar mai da hakan.
   Idan ba kasan da irin shi ba ba kowa ne yake gane hakan ba zaka mutum na fama da ciwon kai mai tsanani ayi ta magani kamar ba a yi.
  Nima gani nayi a makwabtar mu haka ya faru koma dai ba shi bane ya kamata ku hada da na gargajiya tunda likitoci sun ce basu ga komai ba su .
  Shiru yayi na wani lokaci ba tare da yayi magana ba abubuwa da dama yake tunane a ranshi sai can yace maganan ki na da kamar gaskiya khadija.
   Don dai a yadda yake rike kai yana kugi zakace zai iya mutuwa ne a lokacin kuma kan sai cikin dare kawai yake damun shi .
  Nace abinda ya ban mamaki ke nan nima ace ciwon kai kamar na sihiri sai dare kawai yake tashi cikin ne ma wani lokaci yake dan tashi da safe ko idan ya ci wani abu.
   Allah ya sauwaka nace maryam dashi suka amsa da amin lokaci daya maryam tace gashi har ya ci ayaba ya zauna mashi ciki lafiya abin ya ban mamaki ai.
  Nidai har muka shiga hostel ban yi magana ba sai dai ido da sauraren su da nake yi kawai.
Kwance nake tun bayan dawowan mu da nayi sallah magariba da ishai na kwanta nan iya cin komai ba na kwanta zuciya na cike da damuwa.
   Washe gari tunda safe da na tashi ina shiri jikina ba karfi a tare dani sai tunane nake na yadda na ganshi kwance jiya yana jin jiki sosai wai a haka yaji sauki ke nan.
  Waya na nadauko ba tare da na tsaya tunane ko yana barci a wanan lokacin ba na dana mai kira wayan ya shiga yana ta ringing ba a daga ba.
   Sai kusan zai katse aka daga wayan muryan shi da alaman barci a tare dashi yace hello Deedar ya kike nace ina kwana  ya amsa da lafiya nace ya jikin yace jiki da sauki nagode.
  Sai nayi shiru yace hello dayaji shirun yai yawa nace kaji sauki sosai ko yace mm a ji sauki Deedar ya kuka koma jiya nace lafiya a sanyaye.
  Can nace nagode Allah saka da alheri yace namay fa nace na tsaraban da ka kawo min ranan nagode kwarai Allah saka da alheri tsaraba haka da yawa.
   Yace ba komai nagode sai an jima na kashe wayan ajiyan zuciya na sauke ina aje wayan cikin hand bag dina tare da lumshe idona.
   Haka na shiga makaranta jiki ba karfi duk yinin ranan haka nayi shi a sukurkuce dani yau ma kamar jiya na dawo ban dade ba a cikin makaranta na dawo.
  
Yusuf tunda ya aje mu hankalin shi ya koma kan maganan mu kawu salisu ya kira yana fada mai matsalan Abdulsamad din.
  Kawu yace zai je a ga malam yayi mashi bayani komai kai tsaye asibiti ya nufo inda ya samu Nafisa na fada da security a bakin get.
  Nan ya tsaya rai bace yake masu magana abin mamaki sai ta maida fadan wurin shi tana fadin sune ai munafukan da suka ja a wullakanta ta din sun dauko karuwa sun kawo ma samad har cikin asibiti tazo tana iskanci.
  Da mamaki yace karuwa may ya hada AA da karuwa kuma tace in ba karuwa bane may zai sa tazo tana bashi ayaba a baki ?
   Kai ya girgiza yana mamakin inda maganan ya fito mata yayiwa security din magana akan su kyalesu su wuce basai sun tura ta ba.
   Ciki ya shiga fuskan su kawai da ya kalla yasan akwai damuwa a tare dasu yace mommy ya akayi har Nafisa tazo nan da fitina haka ?
   Yusuf Nafisa tana fada ne bisa ka,ida zuwa tayi nan tana hauka nasan kawayen ta ne da suka zo dazun suka fada mata don dun samu yana cin ayaban da suka shigo.
   Ya girgiza kai yana murmushi yace mun dai auna arziki bata samu su khadija a nan ba da ba karamin tashin hankali zasu yi ba don ko ita khadija ba baya ba da alama wurin fitina.
   Khadija ce kaidai zata yi daidai da gidan Abdulsamad a halin yanzu mommy don itace kadai nake ganin zata iya da Nafisa a yanzu.
   Shi babangidan yace yana son ta ne ko ya nuna wani alama na ra,ayin tane da dai zanyi hakan gaskiya da yayi dace da kamilan mace a gidan shi don ni yarinyar tanayi min wallahi.
  Don akwaita da natsuwa da girmama na gaban ta ga ilimi addini da na boko ta samu a tare da ita kaga kowa ma zaiyi kwadayin wanan mace a gidan shi ai.
   Tun farko ina ma yaran gidan mu kwadayin ta sai dai kasan yaron yanzu ba ai masa haka gara inshi yagani da kanshi yace yana yi shine za a zauna lafiya.
  Duk da nasan khadija tana da masoya ko anan kaduna din amma haka bai hanani jin wani nawa ya so ta ba.
  Amma kai da kake fadin haka akwai wani abu makamancin so ne a tsaka su dama kodai dacewan haka kaima ka hango yasa kai magana ?
   Mommy gaskiya ba zan boye maki ba akwai sai dai dan nakine miskilanci da ji da kai da izza yahana shi tsaya su fuskanji juna shi da ita kin san kuma ba a son mutum da haka.
  Shi yana ganin idan yaje mata da zancen so kamar ya zubar da kiman shi a gare ta ita kuma khadijan kallon yan uwa take muna a yadda na fahinta ni.
  Sai dai dukkan su suna boye feeling din su ga juna ne amma indan so akwai so gaskiya miskilanci shi dai ne ya hana ya nuna mata haka din.
   Murmushi mommy tayi tana fadin dana ai ba a haka yanzu matan yanzu sai da so ake saye zuciyar su bawai da kudi ba kawai don ba ko wace mace bace kudi yake gaban ta ba.
   Mommy dan nan naki in kiyi duba gare shi bai fa san so ba shi don a yadda ya auri Fati da Nafisa ba wai an tsaya anyi wani soyayya bane dasu.
  Auren fati dai kin san komai akai hadine na iyayye tun farko ita kuma Nafisa abu biyu ne nake ganin ya kai su ga aure.
  Na farko kin san akwai shi da son fararen mata dogaye sai na biyu ita din batazo mashi abanza ba sai da ta asirce shi.
  Wani kallo yayi ma Yusuf din dake magana yana kwane ya harde hannayen shi sama kirjin shi kafafuwan shi a harde yana karkada su a hankali.
   Ni kake wa sheri haka Yusuf  kuma a gabana Yusuf yace ba sheri bane abinda nagani nake fadi ni baka son khadija ne karya ne maka ?
   Ke nan ashe sun dade tare da ita mommy ta tambayi Yusuf din cikin son karin bayani gare shi.
   Don ni na dauka zuwan nan na su Binta ne kuka hadu da khadija din har kuka santa yace a,a mommy ba zuwan su bane muka santa don gaskiya dama muna tare da ita.
   Ikon Allah a mu kuka boyewa mawa dama amma yaran nan kun iya taku har karshe yanzu ashe kuna tare da yarinyar nan kuna nuna ba komai a tsakanin ku da farko ?
  Hakan na da kyau da kuka boye ba laifi bane haka yayi daidai nima zan kama baki na inja ga wanan maganan badon komai zamuyi haka ba sai don matan shi.
  Duba yadda Nafisa tazo nan tayi muna yanzu bata san da komai ba ke nan ina ga inta sani din sai idan abu ya kankama a tsakanin su lokacin da wani bai iya komai za a fitar da zancen ga kowa yaji.
   Don idan ba haka ba maganar sai yazo yabi ruwa azo ba ayi shi ba sai dai babangida ya kamata ka daina wanan halin naka don ba haka ake neman ba yanzu.
  Kamata yayi ka bata lokacin ka ka nuna mata so da kauna ta yadda zata saki jiki dakai har a cin ma abinda ake so.
   Mommy sheri Yusuf ne kawai yarinyar nan a yan uwa ta dauke mu har ta gabatar muna da wanda take so ta aura fa.
  Tayaya zaice kuma ni na kutsa kaina ga abinda ta riga tayi nisa ga wani gare shi da sauri Yusuf yace.
  Wanan magana ba gaskiya bane dakai da mamud din da tace wa yariga wa ta riga sani cikin ku biyun kai ta fara sani kasani ba wancen ta fara haduwa dashi ba kaine ta fara sani.
   Yusuf kabar wanan zancen don Allah yarinyar da kaji mommy ma ta fada tana da masu son ta akan may zan tsaya bata lokacin gun ta karamar yarinya ma da ita haka da tara maza ai babu komai sai wulkanci a gurin ta.
  Da sauri Yusuf yace ta taba yima wullakanci ne da zaka fadi haka san nan kuma kowa ai da karfin shi yake zuwa ya gwada tashi sa,an akan mace idan tai ruwa rijaya idan batayi ba masai.
   Banda wanan lokaci kai ka sani so don Allah kubar wanan zancen na Deedar please zan dai yi hakkuri ina zauna da wa yan nan da Allah ya hadani dasu.
  Munyi magana da Abba Fati zata dawo dakin ta karshen watan nan ya kuke son inyi da mata uku yanzu biyun ma yaya na iya dasu balle na kara ma kaina wani wahala can.
   Aure ne kawai mafita gare ka a yanzu saboda ta haka ne kawai zai kawo fitar da zargin da ake maka akan Nafisa ta mallake ka don ni nasan matsalan ku da Fati wanda ma kowa ya sani in ba wani aure kara yi aka gani ba, bazaka fita bakin mutane da zargi su a kan ba.
   Mommy ban damu da abinda mutane suke cewa a gare ni ba tunda nasan ina tsare kaina ga duk wani abin hani.
   Mommy tace babangida kada kace haka idan kasan kana son yarinyar nan kada ka bari wani yazo ya kwace ta daga gare ka.
  Shawaran da zanbaka shine ba,a kin shawara idan na kwarai ne ka gwada a gani ko hakan ne mafita a gare mu kaga sai a wuce wurin a manta da komai sai fatan samun zuri, a masu albarka.
   Murmushi Yusuf yayi Allah yakawo lahadi don litinin yai niss inji maza ranan nasan ni za,a kira da munafuki yafi a kirga gun Nafisa.
   Yanzun dai maganan mommy ne mubar wanan zancen a yadda yake a rufe sai munga komai ya kan kama za a ji.
  Mommy kaifin basira irin na khadija yasa nake mashi kwadayin ta a gidan shi don khadija yarinya ce mai tunane wallahi.
   Mommy ta tashi taje yin alwala lokacin ne Yusuf ke fada mashi gobe yana son ya je zaria da safe akan ciwon shi yaga malamin nan na gurin kawu salisu.
   Yace kana ganin zuwan ka wurin shi yana da wani alaka da ciwo nane ko may ko wani abin ne zai kaika wurin shi.
Sai da ya mike tsaye don zuwa sallah ya bashi amsa da cewa akan ciwon ka nake son zuwa can don yanzu wanan shawaran yazo min .
   Bai mai magana ba sai mikewan da yayi shima don zuwa yin sallah magariba data gabato a lokacin.

Da dare yana kwance na kira shi muka gaisa na ba maryam ita ma tayi mashi yaya jiki yace da sauki ya gode muka kashe wayan.
    Maryam ne tace ni har yanzu sai nake ganin kamar jikin nashi da sauki a yadda naji muryan shi a yanzu nace haka nima nake tsammani danaji.
  Daga haka ban kara cewa da ita komai ba ina kwance rigingine ta dauko waya tasa muna kira,a shine naji hankalina yana kwantawa a hankali naji damuwan da nake ciki wanda ban san dalilin shi ya fita a raina har barci ya dauke ni daga hakan.
   Washegari na tashi wasai dani wanka nayi na shirya na kama hanya zuwa cikin makaranta don ina da test a ranan gashi banyi wani karatu ba isashe.
  Ban fito ba sai yamma lis na fito daga cikin makarantan alokacin yunwa ne ya addabe sosai a sukwane na shigo dakin ina wurgar da handbag dina ina cire hijjab din dake kaina a lokacin.
  Maryam kuma bata dawo ba nake gani alokacin don haka na fara kokarin hada jeloup din taliya don ina ganin shine mafi saukin dahuwa a gare ni a wanan lokacin.
  Agurguje nake aikin daidai lokacin da na kusan gamawa ne wayana kira ya shigo min  sai da na duba abincin sama sama na dauki wayan.
   Ban tsaya duba mai kiran nawa ba naji murya shi yana fadin yau ba akira anji jikin nawa ba dan banufen naki ya dauke maki hankali ko ?
   Murmushi nayi a baiyane ta yadda har yaji a cikin wayan mommy bata nan ne daka bugo min waya ?
                   Kina tsoron taji ina waya dake ne a gaban ta komay ?
    Ina da kunya da girmama na gaba shiyasa amma ba don tsoro ko wani abuba kawai don kawaici ga manya ne .
   Gata zaune tana jin ki ko in bata wayan ku gaisa ne kana fara shi wanan ma ai fadi ne kawai nasan mommy tafita yasa ka kirani kamar yadda nake da kunya kai ma nasan zakaji kunyan waya a gaban ta ai.
  Muryan mommy ne take fadin khadija kun koma lafiya jiya ya karatun Allah ya tsare ya kare ban iya cewa komai ba sai daburcewan da nayi a lokacin.
   Hello khadija ba kya jine ina magana kin yi shiru nan ma ban iya magana ba shiru nayi mata a lokacin sai naji tayi murmushi.
   Wayan na kashe sai da na gama girkin sai kuma cin abincin ya gagare ni duk da yunwar da nake ji din da farko .
   Waya na dauko na tura mashi text kamar haka baka kyauta min ba ya zakai min haka ka san girman mommy a idona kuwa ai sai kasa ta zargi wani abu a zuciyar ta a gare mu.
   Na gama na tura mai maryam ta shigo dakin tana fadin wai yau na gaji wallahi zama tayi tana kallon yanayin da ta samay a ciki.
   May ya faru tace tana kallon fuska na cikin damuwa ga yadda ta ganni din sake tambayana tayi tana maida hankalin ta gare ni.
  Ga abinci can ki diba ina kika tsaya har yamma haka lis wallahi mugun malamin nan namu ya tsaida mu haka yau test din yayi wuta sosai tamike tana fadin har kin ci ne ke tana kallo na.
  Kaina girgiza mata tace kin ci wani abin ke nan ko naga ko karyawan kirki baki tsaya kinyi ba kika fita yau.
   Wallahi da yunwa na dawo sai da na gama kuma naji ban son cin komai ki sha wanu abu mai ruwa kila yunwa ne yai maki yawa ya hanaki cin abincin.
  Ta debo ta fara ci tayi nisa ga ci nake cewa da ita kin san may wanan mutumin yai min yau maryam.
   Da sauri ta dago kanta tana fadin wani mutumi mamud ko wa nace wani mamud kuma AA fa don ya maidani karamar yarinya wai a gaban mommy zai kirani yai waya dani.
  Maimakon inga damuwa itama a fuskan ta sai naga sabanin hakan a fuskanta dariya ta soma tana fadin lalai wanan dan barki ne .
  Ya daure tamau yanzu a gurin mommy ta gama sanin komai a tsakanin ku ke nan ?
   Komai kamar yaya ya dai daure ni wallahi tace ai maganin ki ke nan tunda bakya jin shawara ai gara da ya fito maki tanan.
   Haushin ta naji sosai a rai na don rashin nuna jin haushin hakan dayayi min da ta nuna rashin damuwan ta akaina.
   Bayan ta gama ta mike lokacin nayo alwala zanyi sallah itama ta shiga bayin ta dauro alwala muka gabatar da sallah mu.
   Zaune nake bayan na idar da sallah ban bar wurin ba sai da nayi isha,i na mike ina nade sallaya maryam ta mike ta dauki heater tare da dauko cup ta hada min shayi mai kauri saida ta gama ta miko min.
  Kamar ba zan karba sai dai na mika hannu ko ba komai nasan shan tea din zai taimaka min ga yunwa da ke ciki na.
   Tunda na kwanta ban sake bi ta kan komai ba har barci ya dauke ni a haka yadda nake cikin dare na falka na ga ta rufe min kofa itama tana kwance a kusa dani ranan a dakina ta kwana.

Zaune take a falon madam datai ma tsuke tunda safe ta isa gidan madam din a yadda ta ganta sai take tambayan ta ko lafiya haka da safe.
  Madam gaskiya yanzu samad ya rikice min tunda na haihu din nan na rasa gane kan shi gaba daya.
  Jiya fa a gaban wanan kishiyar uwar tashi yake fada min wai aure zai kara saboda kawai nace sai ya fada min wace yarinya ne tazo gaida shi har take bare mai ayyaba tana bashi ?
  Ke a ina kika ji wanan labarin ne wai waya fada maki ne shiya daure min kai tace kai tsaye su hajiya karima ne da suka je gaida shi.
  Baki ga irin wullakancin da security din asibitin nan sukai min bane suka fitar dani waje yana kallo baiyi magana ba.
  Haba Nafisa kullun ina fada maki magani fa bai ci sai da siyasa da kissa da kisisina da kutungwila na mata.
  Ya zama dole yanzu ki bishi a sannu ko banza kin zubar da jinin haihuwa a gidan ki kiga komai da kikayi na asiri yanzu ya karye.
  Ai ba karamin hikima bane aka samo na haihuwa asibiti da mata ke yi yanzu bature ya taimaka ma mata da ya fito da wanan hikimar haka na haihuwa asibiti.
  Kinga ko da za a dawo da mace gidan ta an wanke komai a asibiti kinga wanan uwar tafiyan na haihuwa yafi komai karya asiri ga mutane ba matan ba ba mazan ba.
  Shiyasa iyayyen mu na da basu wasa dashi a gida zakiga da sauri ake fitar dashi gida asamu gefe a binne shi amma mu matan yanzu sakacin mu yayi yawa ga komai wallahi.
  Yanzu ya zama dole gare ki ki lalaba shi ki kara sabon shiri sosai a kanshi dan kada yazo ya bijire maki nan gaba.
  Zancen kuma aure ni nasan ba dagaske yakeyi ba don ba abinda kika rasa da ake so gun mace yana kuma son ki tsakani da Allah.
  Zancen kuma ita yar iskan yarinyar dake dmson maki kutse a gidan ki ta dauke maki hankalin mijin ki tambaya zamu muji da gaskiya ne hakane ?
   Idan da gaske ne sai mu san ta inda zamu fito da zancen nata ga wanan irin arziki da ya taso ma mijin ki haka ina zamu bari muba wata daman da zata shigo ciki muna kallo.
   Yar iska bamu san ko wace iri bace ita tazo tafimu iyawa dashi babu yadda zamuyi ko wacece zata shigo maki kin san itama ta shirya.
  Don kishi da buzuwa ba wasa bane duk matan nahiyar nan namu sun sani shiyasa suke tsoron ku buzaye don cire ice har sayen shi komai tsufan shi ba wasa bane gare ku.
  Madam duk da haka ya zama dole gare ni in tashi tsaye in hana gaba da bayan shi motsi a gare shi ko mace ba zai iya daga ido ya kalla da sunan tausayi ba balle so.
   Yanzu dai duk ba wanan ba sai fa kin kwantar da hankalin ki ko ta siyasa zaki iya gano gaskiyar maganan gare shi idan kin kwanta amma.
  Tace a sanyaye naji zan gwada yin abinda kika ce min din tai mata godiya tare da sallama ta nufi gida tana ba kanta hakkuri.
   A ranan ya samu sallama bayan dawowan Yusuf da bayanin abinda ya girgiza shi daga malam don yace a lemon da ta tare shi dashi yasha batare da yayi bissimillah ba.
  Yayi arziki akwai tsari sosai na Allah a jikin shi da ba karamin wahala zaiyi ba don ba maganin alheri akabata tabashi ba.
   Ya iso gida zuciyar shi ba dadi wanka ya shiga don ya tsabtace jikin shi don baijin zai iyacin abinci ga yadda yake jin kanshi a lokacin.
  Yana zaune bakin gado ta shigo dakin ta saba diyar ta a kafada tana rangaji tana zuwa ta azamai yarinyar saman jikin shi itama ta samu wuri ta zauna a gefen shi.
  Yadda taga bai sake fuskan shi ba yasata fadin har yanzu abinda ya faru ne kake ma fushi haka ko jikin naka ne har yanzu.
  Kallon ta yayi yace may ya faru kamar bai fahince ta ba tace akan maganan nan na asibiti da ya faru raina ne ya baci a lokacin nayi haka ba tare da nayi tunanen komai ba.
  Wanan matsalan ki ne sai dai ki sani duk abinda zaki karbo daga yau da sunan malakana a gidan nan kada ki sake karbo wanda zai cuta min haka don ki sani nasan abinda kika zuba min a lemon da kika bani ranan.
  Kuma shiya haifa min wanan ciwon danayi ban hanaki yin abinda kike ganin shine mafita a gare ki ba don dama haka yawancin mata kuke da wanan shigeshigen din sai dai ki sani ba zaki taba mallakana ke kaidai ba domin ni din mijin mace hudu.
  Yana fadin haka ya mika mata yar tare da mikewa ya bar mata dakin nan ya barta cike da mamaki tana wasi wasin ko dai wani ya fada mai a gidan.
  To ina ma wani ya ganni nida na zuba a cikin dakina amma yaya akayi wanan maganan ya koma kunnen shi haka.
   Watau ke nan abinda ta zuba mai ne ya jawo mashi haka ba maganin kwarai aka bata ba kena  cutar ta akayi akan maganin da ta kashe makuden kudi akan shk a bazan zai tafi ba zaiyi aiki akan shi ba tunda had ya gane may ake ciki.
Ko dai shima yana irin nata ne har yaje wani ya fada mai abinda tayi mai tace kai wanda ke kwance haka ba lafiya ina zai iya zuwa ?

ZAINAB IDRIS MAKAWA
            SEENABU
Na farka cike fa far’a da kuma farincikin zuwan da Mama za tai, ban taba tabbatar da na yi missing dinta sosai na sai da na farka da kewarta. Hamma ya shirya mana abun karyawa ni kuma na gyara gidan a wauta taa na zata gidan zata fara sauka sannan ta wuce gidan Momy. Bayan na gama komai muka zauna muna karyawa sai ga Momy ta kira Hamma a waya tana labarta masa cewar Mama ta zo tana gurinta.

“Laa ba nan za ta sauka ba?”

“Shikenan sai ta sauka nan saboda ga ta ita mai ya ko?”

“Amman na dauka nan zata sauka, har ina shirye shirye girka mata wani abu”

“To an hutar da ke”

Ya fada yana jan hancina. Sai nai murmushi.

“Ita ma zan mata magana na ce tai maka maganar karatuna”

“Oh magana kika yi ma Momy tai min magana ko?”

“Aa Wallahi ita tai dan kanta,kawai dai ina son karatun ne kuma kai na ga kamar ba ka so”

“Ba wai so ne bana yi ba, yana ganin kamar karatun a yanzu zai iya zame miki matsala ko wahala”

“Wallahi ba wani Wahala bana jin komai fa kalli”

Na yafa ina daga rigar da ke jikina, sai ya kalli cikin ya kalleni yana murmushi.

“Ai a jikinki ake gani ba, nan gaba na ke miki nuna”

“Idan na ji da wahala nan gaba zan daina”

“Daman ai kin iya raki ai”

“Amman ni ai ina da kokari bana raki a komai ma”

“Ko”

Ya tambaya kamar mai magana da yar shekara uku babu dariya ko murmushi a tare da shi.

“Idan mun koma Abuja zaki fara zuwa islamiyar su da bokon da ke can, amman idan cikin ya kai wani mataki za ki saurara da zuwan har sai kin haihu, sannan ki cigaba”

Ban san lokacin da bar inda na ke zaune ba, na fada jikinsa ya rumgume shi ina murna.

“Da gaske Hamma”

“Ba na ce ki daina ce min Hamma ba?”

Ya fada yana jan lips dina.

“Ni dai amsa min da gaske?”

Ya gyada kai sai na kara rumgume shi saboda murna har da yi masa kiss a gefen fuska, shi kansa abun sai da ya bashi dariya. A ranar sai farincikina ya zame uku, na zuwan Mama da na case din Doc Asim da za ayi ga kuma zancen Karatu da Hamma yai min. Kowa ya ganni a wannan lokacin ya san ina cikin farinciki, har muka yi wanka muka shirya ban daina sake saken yadda zan fara karatun nawa ba.
  Bakar a baya na saka shi kuma ya saka wani koren yadi mai kyau mai kamar boyal kuma ba boyal ba, ya saka bakar hula da bakaken takalmi karka so ganin mijina a wannan lokacin yayi kyau sosai fuskarsa har wani annuri take kamar wani ango, ni kaina sai da na kusa shashantar da kaina gurin kallonsa.

“Ashe kai ma kana da kyau”

Ya dube ni da duba irin na wasa da kuma mamaki.

“Oh dacan ba ki taba ganin kyau na ba sai yau? Ko dan ina yawan fada miki cewar kina da kyau?”

“Aa gaskiya yau dai sai naga kamar kana da kyau”

Hannu ya kai ya rikoni ya matse min kunne.

“Na fiki kyau yarinya ni da yan mata ke hari ma, ke ma ba kyau ne ya janyo ki ba, kina ga dan yaro kyakkyawa kika lake min har da addu’ar Allah yasa na so ki, shiyasa na kasa zaune na kasa tsaye sai da na kawo ki gidana”

Ban san lokacin da dariya ta subuce min ba, duk kuwa da irin zafin rikon kunnen da yai min.

“Da zafi sosai da zafi”

Na fada a lokacin da yake jan kunne nawa zuwa gurin motarsa.

“Yau ke za ki bude min motar na shiga”

“Saboda me?”

“Saboda ni ne Sarki”

“Amman ai kai ka saba bude min”

“Lokacin da kina sarauniya ba”

“Yanzu fa”

“Ni ne sarkin”

“Taya?”

“Gashi nan ke ma kin yaba kyau na”

Dariya nai na daka tsalle na cire hular kansa na watsa da gudu gaban motar sai ya biyoni ya gudunsa.

“Ke ba ki da kai ya za ki fara gudu da ciki”

Jin hakan yasa na tsaya sai kawai ya karaso kusa da ni ya karbe hularsa ya sake rike min kunne.

“Na gane ba ki jin magana Babyna”

Haka ya janyo ni har gurin motarsa ya bude min na shiga ya rufe sannan ya zagayo ya shiga mazaunin direba ya tashi motar muka dauki hanyar gidan Momy.
   Ina shiga dakin Momy yai kan Mama da gudu na rumgumeta ina murna. Matan da ke tare da ita sai suka saka dariya suna ta kiran wai na cika kurciya, Momy ma dariya take tana fadin haka muke ni da Husna da Siyama kusan halin mu daya Amina ce kawai mai hankali, sai da muka dade a dakin muna fira ni har na manta da Hamma sai gashi ya shigo dakin da kunya ya gaishe su tare da musu fatar an zo lafiya sannan ya fita. Wani abun haushi abun mamaki Mama ta yi ma kowa tsaraba, a gidan sun daga kan Daddy har Momy da Amina Husna da Siyama kai har Hamma sai da ta siyo masa wata dakakkiyar shadda yar Agades amman ban da ni, nikan Nonon Ragumi ne kawai tai min tsaraba da shi. Misalin biyu saura na rana muka fito zuwa inda ake bukatar ganinmu, ni da Hamma a mota daya Mama kusa ta shiga wata mota da yan’uwanta maza suka zo da ita daga can inda suka sauka.
  Ko da muka isa gurin biyu daidai, wani katon gurine mai kamar ma’aikata, yan’uwan Mama maza da Hamma suka shiga gurin da aka tana da domin sallah, ni kuma da Mama da wata yar’uwarta da ake kira da Mama Lattu muka shiga wani dan fili mai kamar dakin karatu mukai na mu sallah.
Ba mu zauna a dakin ba sai uku daidai domin bayan gama sallah sai da aka jira isowar wasu daga cikin wadanda za a zauna da su. Maza da mata ne da yawa a dakin za su kai su goma a dakin, sai wasu kujeru da aka jera can dabam wadanda aka nuna mata aka ce mu zauna, duk irin kusancina da Hamma na kasancewar mijina hana shi shiga akai a gurin, da kuma yan’uwan Mama sai aka hana su shiga, wai da mu kawai suke son su fara magana.
  Inda Doc Asim yake zaune da dabam da inda muke zaune, sai kallona yake kamar be tana ganina ba, na kalleni ya kalli Mama wata kila mamakin rayuwarta ya kashe shi ko kuma mamakin kawo kararsa yake oho, sai dai a yanayin da ya ganmu daga ni da har Mama ya sam yanzu ba kamar da ba ce domin ta canja zane. Da turanci suka fara magana kamin dayan ya fara yi da hausa yadda ni da Mama za mu fahimta.

“Doc Asim ka san wannan?”

Sai ya kalleni ya gyada kai.

“Eh na santa”

“A ina ka santa?”

“Ta yi zaman jinya asibiti tare da mahaifiyarta a lokacin da ta siyar min da kodar mahaifiyarta”

“Ke kin sanshi?”

“Eh shine likitan da ya cire kodar mahaifiyata ba tare da sanina ba ko saninta”

Daga haka suka fara karanto masa abunda ake kara akansa da kuma zarginsa da ake.

“Wannan yarinyar fa karya take ita ta siyar da kodar mahaifiyarta, kuma ta kai karata a gurin police ba ta ci nasara ba suka koreta shine yanzu take kokarin ganin ta bata min suna, wasu ne suke sakata saboda aci min zarafi”

Sai da suka tambayeni sannan na bayyana komai yadda ya faru ciki har da kulleni da akai gurin police, da suka tambayi ko ina da shaidu akan hakan sai na ce shukura ce ta san komai yadda ya faru.

“Fine na yarda a nemo shukura za ta fadi gaskiya ai, and zan kawo takardar da ta saka hannu akai za ku ga komai”

Yana fadar hakan na raya a zuciyata cewar akwai abunda yake kokarin shiryawa, wata kila ita ma zai siyeta kamar yadda yai ma polisawan da suka kama ni.

“Za mu cigaba da bincike, za mu gone gaskiyar lamarin idan har ba shi da laifi za mu hukuntashi, kuma zamu mika shi kotu domin ta hanke masa hukunci daidai da abunda ya aikata, ba zamu yarda wani likita ya bata mana aiki ko suna ba, ko kuma ya taka daya daga cikin dokikinmu, idan kuma ke muka samu da laifi yin masa kazafi za mu hukunta ki babu ruwanmu da kasancewar jikan Sarkin Agadaz babu ruwanmu da kudin kakanki ko babanki za mu hukunta kuma mi mika ki kotu domin a yanke miki hukuncin daidai da abunda kika aikata”

“Na yarda”

Ina fadar hakan Doc Asim ya maida hankalina a gurina, wata kila yana mamakin yadda nake da karfin hali ne wata kila kuma yana mamakin jin alakata da wani babban mutum nw kamar sarkin Agadaz da kuma zancen kudi da sukai ko da be san waye shi ba yana ji ya san ba karamin mutum, a take yanayinsa ya canja ya koma kamar ba shi ba rama yai ko lalacewa ba, yana nan yadda yake amman hankalinsa ne a tashe, domin ya san waennan likitocin ba kamar police ba ne da zai iya siye su ba. Ninkaina a yadda na gansu na san za su adalci ko da yake abun ba a fuska ba ne, da a fuska ne da Doc Asim ba zai min haka ba.
Dukanmu da farinciki muka dawo a mota na ke labartawa Hamma yadda akai yana ta kara kin kwarin guiwar cewar za su yi adalci domin gurin ba gurina na wasa ba, kuma ya san wasu daga cikin ko dab ganin abun ya fito ta bangaren Mai Martaba dole su kwatanta adalci domin ya nuna musu hakkin yarsa yake son a bi masa, abu na biyu kuma ba za su so wani likitan mai zaman kansa ya bata musu suna ba.

A gidan Momy na wuni ni da Mama domin bayan Hamma ya aje ni sai ya shiga gari, muka wuni muna ta maganar likitan har ake dauko zancen wasu likitocin masu taimakon da gaske da kuma wasu masu halin Asim sai dai su ba su kai shi ba ba domin na shi ya yi yawa ba kowane mai imani ne zai aikata haka ba. Daga bisani Mama ta dauko min labarin yayan Ammy da wasu yayan yayyunta ke so, wai magana har ta yi nisa ta kai gurin Mai Martaba ana zancen yin baiko. Na jidadin sosai jin cewar yaran Ammy ne duk dai Mama bata rike sunansu ba, amman ina ayyana cewar Humaira ce da Anty Zee, sosai na so ganin fuskar Mama Fulani da Maryam dan na san ba zata jidadi ba, saboda ba son shiri da Ammy take ba, kuma babu wanda zai so y’ar kishiyarsa ta samu jiki ta sa bata samu ba, balle Mama Fulani dake ta falako a cikin gida da nuna isa. Lallai Allah mai yadda ya so, kuma sai ya bawa Ammy surukai a cikin jikokin Mai Martaba yayan masu arziki wanda nasan Mama Fulani ce zata fi kaunar hakan.

Sai da dare muka koma gida, bayan Mai Martaba ya sake Kiran mama ya fada mata cewar an saka wani ranar Assabar mai zuwa wato nan da kwana biyu kenan. Kamar yadda ya saba yau ma sai da siya mana dan abun tabawa a baki sannan ya muka isa gida yana rike da hannuna kamar ba zai sake ki ba.

***      ***      ***

Gaba daya al’amarin duniya ya koma mata sabo kuma ya zo mata ta inda bata zata ba, bayan daukakar da Allah yai ma Ataa akansu ya daukakata fiye da su sai kuma Allah ya kawo ma yaya Ammy miji daga cikin zuri’ar da tai kwadayin yayanta su samu, har magana ta fara karfi ga nata yayan babu wanda ya taya ban da Kamal shi ma Kamal din ma tun da akai fada da shi akan Ataa be sake kula Maryam ba. Balle Rukaiya ita ko zancen ba a ayi yadda kasan ta kasa kashi haka take, ga shi ba kyau ne babu ba amman babu mai gani ya taya kamar wanin abun amai. A yadda take so ita bata ki an hade su da auren Muhseen da za ayi ba, ita ta wanke su gaba daya ta huta ya zamana baby ce kawai ta rage mata.
 
Fitowa tai daga kitchen ta nufo inda Maryam take zaune tana lasar waya ta fara mata masifa kamar mai jin haushinta.

“Ai dole ku rasa mijin aure, ina can ina aiki kina nan kina lasa waya, idan safiya ta waye dakinku kawai kuka iya gyara kamar ku? Ace ba za ku iya aikin komai ba? Idan ma kun yi auren ai ba duka namiji ne zai dauki haka ba, dan ba ko wane namiji na kamar Aliyu ba da zai yarda da hali irin na Rahma wanda yai kama da halinku, su yayan Ammy haka suke? Indai auna nan ai su suke mata komai ku gyara ko’ina girki ne kawai nata shi ma wata rana su suke yi, gashi nan ai Allah ya basu maza a cikin waenda nai muku burin samu saboda ku ba ku san ku yi tausayina ko idan ina abu ku rika min ba, duki ki ga yarinyar Ataa haka ta zo tana aiki a gidan tai nan ta yi a can gurin Ammy duk akan mahaifiyarta kuma da Allah ya tashi bata gashi nan har Muhseen da Aliyu sai da sukai fada akanta, kuma yanzu gashi nan Aliyu take aure, mai taimakon uwa ai baya faduwa amman ku kullum kuna kan waya sa kan gado sai ka rantse kujera sai idan na gama ku taso zuwa dinning room dan ba ku da kunya”

Maryam ta kalleta cikin jin haushin fadan na ta ta ce.

“Oh Mama yau kuma duk wannan fadan a kan mu? Kamar dai kin gaji da ganinmu”

“To wace uwa ce zata so yayanta kamar ku su zauna a gida suna jera tsawo da ita? Yanzu idan an wanke Zainab da Humaira ai kubkadai kuka rage domin na ji Abbah ku na zancen har da Batula zai aurar tunda tana da mijinta amman ku ko mai sallama babu, balle mai zancen aure ko a wayar nan da ake haduwa da maza ku ban ku, ace kuma tausayina da yanzu kuma Allah ya tauyasa muku ya baku inda za ku huta ku jidadi”

“Mama kin san aikin nan fa ba mu saba ba, taya jiki irin nawa zai iya aikin wahala dan girman Allah? Kara dai a nema wata nai aikin”

“Wallahi ba zan dauko wata mai aikin ba, wato n dauko wacce Aliyu ya aure yanzu kuma na dauko wacce ubanki zai aure ko? To ba za a koma ba”

Mama Fulani na rufe bakinta Rukaiya na shigo cikin falon makkale da waya a kunnenta baki har kunne tana wasa da keys din motar hannunta, zaunawa tai kusa da Mama Fulani a lokacin da ta sauke wayar ta rumgume Mama Fulani tana murna kamar wacce akai ma albishir.

“Mama ke dai wani ne na hadu da shi, ya hadu Mama ga motarsa yar yayi”

“A’ina?”

Mama Fulani ta tambaya baki a sake Maryam kuma ta tashi zaune tana jin kamar ita ce.

“A gidan mai shi ya biya min kudin mai aka cika min motata tam, sannan ya karbi number wayata yanzu haka ina isowa yana kira wai na ji na isa lafiya, yana ta tambayar gidanmu”

“Wow Allah yasa mijin ne yanzu nan Mama take ta fada sai ka ce mu muka dorawa kan mu bakin jini”

Cewar Mama. Rukaiya ta kyalkyale da dariya tana kara rumgume Mama Fulani da ke murmushi cikin jindadi.

AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.
Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al’ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.
[11/1, 10:39 AM] Khadeejah🥰: Kwance nake saman katifan dakina ina karanta handout dina maryam zaune a bakin katifan tana gyara kumbar kafan ta.
   Waka take wanda take damuna dashi sai ya hanani yin karatun  tunanen mamud nakeyi wanda ya kai sati biyu yanzu bai lekoni ba kuma banji daga gareshi ba har wanan lokaci.
  Hijjab dina dake gefe na dauka na rufe jikina dashi tace sanyi kike ji ko may da zaki rufe jiki haka  nace sanyi nake ji wallahi.
  Na kara jawo handout inci gaba da karatu tace wai ni ko dazun sai naji kina waya ina son in fito in tambaya wakiraki ko mutumin naki ne naga ya dade bai zo ba kuma banji yana kiranki ba.
   Maryam kin damay ni fa karatu nake kuma kin gani a, a wani karatu yanzu inga kina tunane  ke kika ga wanan din na gyara kwanciya ina bata baya.
   Sai da ta gama abinda takeyi tace don Allah tace muje mini market mu sayo kayan miya nace ban zuwa tare da lumshe idona.
  Fada min a jiki naji tayi tana dariya tare da sake ihu daidai kunnuwa na a zabure na mike na biyo bayan ta da gudu zuwa waje.
   Dagani sai dan body hook da nake sakawa a ciki in dora abaya kaina ba dan kwali gashina dana daure ya fado min a baya don duk zuben filani na gajeshi wurin kakannin mahaifan daddy na.
   A daidai lokacin nz hango motar su tana fakin a daidai inda suke tsayawa da mota idan sunzo guri na ban dauka su bane sai da na duba da kyau don gurin na kowa da kowane masu zuwa wurin yan matan su.
  Itama maryam din ta gansu da sauri ta dawo inda nake tsaye tana fadin su yaya Yusuf ne can ko ?
  Ba yadda zanyi don sun gama gani na gashi ko dan kwali babu akaina da sauri na koma ciki ita ce ta tafi wurin su tana gaidasu.
  Yusuf ne ya tambaye ta gudun may muke haka kamar yara tace wallahi khadija ce ta biyo ni da gudu wai ina damun ta tana karatu.
  Na fito daga ciki na dora a baya saman kayan ina hararan khadija na iso inda suke tundaga nesa ya watso min harara yi nayi kamar banganshi ba na kawar da kaina ga kallon shi  ina gaida su baki daya.
Har muka gama gaisawa da Yusuf yana tambayana karatu da kwana biyu nace lafiya maryam taso ta bar gurin da dabara Yusuf yace ta tsaya ai .
    Munzo muyi maku sallama ne zamu tafi umura gobe idan Allah ya kaimu mukayi masu adduan adawo lafiya Allah yasa a karbi ibada.
   Daga ida yake zaune baiyi magana ba tun zuwa su yace ashe baki jin magana baki daina saka kaya irin wanan ki fito dasu waje ba ?
  Nace wasu kaya kuma ina duban kaina da shigan da nayi yace ai kema kin sani yaya kika fito waje dazun ?
  Haba yaushe zaka daina samin ido hakane aiko wanda zan aura yanzu bai isa ya zaba min kayan da zans saka ba a jikina sai idan naje gidan shi.
  Murmushi mai kama da yake ya sakar min yana fadin au haka ne fa kuma  gaskiya na faye sa ido.
  Yusuf yace kajiki da wani magana kuma akwai wanda yafishi sanin ya kamata akan ki ne yanzu dole ya nuna bacin rai ga abinda yake da iko dashi.
  Dariya nayi sosai nace sai kace nice buzuwa ko anty Fati wanan dokan yanzu ai sai daddy na yakai can.
   A bari a rabu lafiya kin ga tafiya zai yi kada a rabu kuna halin naku kuma kinga zai tafi dake a zuciya kila ba zai maki addua ba idan yaje.
  Addua kan kulun ai mahaifa na suna min shi kuma yana tasiri gare ni wanan bakin naki kuwa anya wataran bazai mutu ba khadija ?
   Dariya nayi nace yau dai kun tuna mu ke nan aka kawo muna ziyara haka yace bakin ki zuwa gida ki kara gaida shi da jiki ba ai shi baiyi fushi ba gashi yazo.
Dan satan kallon shi nayi naga hankalin shi baya gare mu nan dai mukayi sallama dasu suka tafi.
   Da yamma ina kwance sai ga kiran shi ya shigo min a wayana nayi makai dalilin kiran shi sai cewa yayi fito gani bakin hostel din ku kai tsaye kamar yadda ya saba ya katse kiran.
  Na shirya na fito shi kadai na sama kamar yadda nayi tsamani bayan na gaidashine yake fadin dawowa nayi don dazu muna barin wurin nan Abba ya kirani.
  Yana son mommy ta koma gida kafin in wuce don haka nake son ki rakani musai masu abinda ya dace diban lokaci nayi a wayana bakwai da rabi na dare don haka akwai lokaci.
   Ciki na koma na shirya sai da na zauna ya tayar da mota nace kana dai son ka ban wahala kai da sukai ma hidima dakai da matar ka ni may ye nawa a ciki yanzu.
   Na dauka yanzu ma ai da shigan dazu zaki fito tunda ban isa in baki umarni ba ban dai ga dama bai don ba mai iko dani a yanzu.
  Allah yakaimu in dawo lafiya zanyi maganin wanan fitsaran naki lokaci daya .
  Ka fara maganin fitsariyar matar ta gida mai fita rabi tsira wace bata damu da hijjab ba balle gyale kafin kazo kafa min dokan ka .
  Sallon yaudara kawai zaka wani gama kalle min jiki kawani ce kai baka son haka na bayan sai da ka kalle ni tsab.
  Dama badon akalle ki kika saka ba idan ni kadai zan kalla ba matsala bane a gare ni wasune kawai ban son suga abinda nagani din.
   Don kanawa a gare ni zaka hana wasu su kalle ni kada ka mata ni yanzu a kasuwa nake banda hakkin kowa ai kaina amma ga masu hakki baka tsa, , ,
   Jinin hannun shi kawai nayi a jikina yana fadin barin fara gwadawa in gani ko tayi min tunda a kasuwa kike kinga idan yayi min basai kin tallata ma wasu mazan ba.
   Bugu nakai ma hannun nashi sosai da yakai ma jikina yana shafawa bai san ina yi ba sai kokarin gwaucewa nake yi ina buge hannun shi.
  Fuskan shi a daure bai fasa min abinda yakeyi ba wuri ya samu ya sauka daga titi.
  Da karfi nace bude min in fita ina kokarin bude kofar motar a gigice hannun shi naji yana cire min dan gyalen da na yafa saman dogon rigar da nasa.
   A take gashin kaina dana tufke daniyar in na samu lokaci inje gurin kitso ya bayana a fili hannu yasa yana wasa da gashin har zuwa inda ya tsaya.
  Take naji wani hawayen bakin ciki ya silalo min a fuska na haka bai sa ya daina abinda yake min ba sai ma ji danayi ta rungumay tsam a jikin shi yana sauke wani irin numfashi yana shafa na son ran shi.
  Kara sautin kuka na nayi a lokacin sai naji ya sake ni yana fadin are you crying bocouse of dis akasuwa fa kike yanzu.
  Hannun shi yakai saman fuskana yana wasa da hawayen dake zubo min din sai kuma naji ya rungumay ni zuwa jikin shi tsam na dan wani lokaci.
   Sai da ya gaji don karan kanshi naji ya sake ni ya koma saman kujeran motar ya kwanta yana maida numfashi a hankali.
  Kaina na dukar naci gaba da kukan abinda yai min din can kuma naji ya tada mota a hankali ya hau titi ba tare da yayi magana ba .
  Kofan bakin wani plaza mai girma  ya tsaya ban taba sanin akwai wuri haka a abuja ya bude motar a hankali tare da fadin fito mu shiga ki zaba masu abinda ya dace dasu kuma ki share wanan hawayen kada ace satoki nayi.
  Sai lokacin na dago kaina na dubi wurin nace ka sani har kullun Allah ba zai taba baka sa a akaina ba mayaudari kawai.
   Dariya naji yayi yana bude motar yace banda wanda Allah ya bani yanzu a kanki kuma koko kina nufin karfin ki ne ya kwace ki a kaina .
  Kuma ki daina kira da mayaudari don da yardan ki muka fito nan  ki sani banda niyar aikata komay yanzu a gare ki amma ki aje a ran ki time will soon come .
  Ko yanzu ke kikaja in maki haka da wanan bakin naki da bai taba mutuwa don ki san irin abinda zaki fada ma mutum.
   Fita yayi ya zaya ya bude min gefen da nake zaune na sauko motar a hankali na fito don girman jeep din nasa.
   Mun fara tafiya naji ya rada min a kunne anya kuwa ke ma ba buzuwan bace deedar wanan irin gashi da jiki mai dadin tabawa haka fa ?
  Hararan shi nayi idon shin kyam a kaina ya sake fadin nayi haka don ki san har gobe nafi wani banzan dake zuwa wurin ki komai.
   Banyi magana ba don mun kawo bakin shagon haka muka shiga a jera da juna sayaya nai wa mommy har da gaiya don har yaran ta na zabawa abu.
   Ya kalli kayan mai makon inji yayi korafin sunyi yawa sai ji nayi yace kina ganin wanan kayan sunyi ke nan idan kuma kin sai wa yaran mommy ita kadai su sauran yaran anty amarya fa ?
  Dole na koma na kara zaba muryan shi ne naji a bayana yana fadin ki zaba ma su ummi da su hajiyan mu kayan suma.
  Sosai ya kashe kudi bayan na mommy dana su iyan bawa gana su hajiya mama dana zaba masu super masu kyau su ma.
   Mun kai ya biya ko dar nanga yayi ba da akai mashi list din kayan aka saka ga wani katon buhu zuwa inda motar shi take tsaya nayi ban shiga ba sai da ya zauna ya leko yana fadin shigo mana mu tafi.
   Nace dashi katafi kawai zan bi taxis in koma ni da sauri naga ya bude kofan motan ban san lokacin da na bude na shiga ba muka bar wurin.
  Sai da mukayi nisa naji yace kina zaton abinda ya faru zai kara faruwa a tsakanin mu ne yanzu idan haka kike tunane kinyi kuskure.
  Don ni ko matana dake gida sai naga dama nake waiwayan mace do  ba haka nake ba kowani lokaci.
   Sai dai nayi mamakin ganin yadda kika narke min a jiki kaman dama jira kike in taba ki haka ya nuna min ke nan dama a jirace kike da hakan ya faru.
   Ban san lokacin da nace mai mugu mayaudari kawai macuci ba wanda ya taba min haka a duniyan nan sai kai kai kasan wani mace ta narke ma ajiki dan, , , ,
  Hannu yakai zai kara kamoni na gwace da zafin nama yayi murmushi yace gobe idan halin ki ne ki kara cika min baki haka.
    Ba sai ka kara ganina ba zakace in cika ma baki kaji dadin yaudaran da ka sabayi wa mata a kaina.
   Zaki bar Nigeria ne ko mutuwa zakiyi don wanan ne kadai abinda zai hana in ganki in kara kallon wanan suran da kike kasawa a kasuwa in riga kowa kwashewa.
  Haushi bai barni na sake magana dashi ba sai juya mashi baya danayi kawai shima bai sake magana ba sai da muka kusa tsayawa naji yace
   Wallahi shiyasa kike kara burge ni da wanan halin naki na dan juyo na harare shi yace yes i mean it da wata ce sai tayi nata sayayyan amma ke naga ko tsinke baki dauka a shagon ba naan kuma dole kin ga abinda zuciyar ki ke so a ciki .
  Kinga ke nan kin nuna min abin mutum baya gaban ki idan bai baki ba yana da kyau hakan keep on da wanan hali.
   Sai dai ai na biyaki ladan ki ko ina ganin ba sai an rubuta maki wani lada ba ko bani wanan lafiyan fresh body din da kika yin kin more ai ke ma.
  Ya tsaya da motar na bude najita a rufe na juyo na kalle shi nace bude min in fita hug me for d last time tunda kin ce baza mu sake haduwa irin haka ba.
  Malam ka bude min mota in fita ni ba yar iska bace ka sani wallahi ban sani ba zan dai sani nan gaba in Allah ya yarda ban fahinci abinda yake nufi ba bai kuma bude min motar ba yana jiran wai abinda yace.
   Na sake cewa da kai fa nake magana ka kyali ni yace even peck kiss yana lumshe ido kamar zan kai kiss din sai na cije shi a kumatunshi.
  Yana shafa wurin yana fadin wassh ko hakan ai na gode zan tunaki watarana na taba haduwa da wata manya yar Niger mai zubin half cas.
Ya bude motar tare da fadin thanks ki kula da kan ki don Allah don kin bar min tarihi nace mugu kawai azzalumi mayaudari da sauri na fita do kada ya kara rufe kofan yana dariya yaja mota tare da min horn ya tafi .
  Ko da na shiga hostel na samu har martam ta kwanta ina shugowa tace kun dawo tare da duban time tana fadin ban dauka zaku dade haka ba ai.
   Zama nayi jagwal a wurin fuskana kawai zaka kalla kasan ina cikin bacin da sauri ta mike zaune tana fadin wani abu yayi maki ne.
   A takaice nace may ye bai mun ba yau maryam AA ya cuci ni ya shammace ni sosai wallahi da sauri naga ta fida ido waje.
   Nace ban taba sanin dan iska bane sai yau wai nifa AA ya ruguma maryam har da taba min kai kiji min dan iskan banza.
  Ajiyan zuciya naji ta sauke tare da fadin wallahi har kin saka gaba faduwa na fa dauka ko raping dinki yayi wallahi wani irin harara nayi mata nace ya ma isa.
   Tace cikin dariya yadda kikai maganan ai dole mutum ya tsorata yayi zaton hakan ne ya faru a tsakanin ku.
   Nace may ye marabin wanan da hakan don Allah bada hakan ake farawa ba har aje can daga magana kawai sai naji ya rungumay ni don kawai ya nuna min dan iska yake macuci kawai.
  Tace akan kayan dazu ko na kada mata kai nace ashe kin san abinda zai min kika bari nabishi ke nan tace kema kin faye baki wallahi .
  Ai gara da kika zabi law don kin iya bakin ki don Allah bani labari nikan in sha dariya don nasan yau ashe yasha zagi a gunki.
   Nace ban sani ba cikin hararan ta ina mike tace indai gulma kuka kai shi ke dashi kuna son juna kuna wani noke noke .
  May zanyi da wanan dan iskan ni bakiji ba ma wai shi ko matan shi sai yaga dama yake kara waiwayan mace idan yaga dama.
  Dariya mai karfi ta kwashe dashi tana fadin ashe akwai aiki kuwa kuma yake sha, awan kara mata fadi dai yayi wallahi.
  Toni ina ruwana da rashin kula matan shi ko ya kula ko kada ya kula duk uwar su daya a gun khadija don ba abinda ya shafe ni da hakan na fada mai.
  Nan nabarta tana min shakiyanci alwala na dauro ina son yin waka don kada ta zarge ni haka na fito na tayar da sallah na gama na kwanta banci komai ba ranan.
  Sai dai ba barci nayi ba don tunane ya hana ni shakat a zuciya na don da zaran na rufe ido abinda ya faru tsakanin mu ne yake zuwa min.
  Har dai barci yazo ya dauke ni ranan na makara da sauri na mike ina shiryawa sai ga wayan shi ya shigo min.
  Kamar ba zan daga ba kallon da maryam ke min yasa na daga wayan murmushi naji yayi tare da fadin nasan dai kamar yarda banyi barci ba kema hakan bazaki barci ba daren jiya.
  Akan may zan hana idona barci nace mai,  yace akan dan gidan mommy mana kema kin sani , nace Allah dai ya sauwaka kana ganin kayi wani abun gwanewa kenan,  mutumin da ko runguma bai iya ba sai ta hanyar karfi,  zai sa na kasa barci na kashe wayan.
  Yayi kiran duniya naki daga wayan sai ga text din shi ya shigo min kamar haka.
           Saboda kin san kin zuba min dahin ki a jiki daren jiya yasa kika fara garani ko may ?
                   Niba macijiya bace ai,  balle in zuba ma dafi
    Na tura mashi, ba a jima ba sai ga amsa shi kamar haka ,
   Kin fi macijiya dafi karfa ki manta ke mace ce,  mace ko shu,umace ko wace iri ce ita tasan sallon sheri ga da namiji.
   Kai dai ka sani da kayan sherin ka in ma dafi ne kai kazubawa kan ka bani ba ya karanta yana dariya bai san shigowar Nafisa ba dakin.
                  Sai jin muryan tana tambayan shi kaidawa ke waya haka kake dariya ?
   Dakewa yayi duk da kaduwan dayayi cikin ranshi amma a fili cewa yayi da ita nida Yusuf ne don yasan ba karatun boko ta iya ba balle ta amsa ta karanta.
  Ba don ta yarda ba ta kyaleshi kawai tana zargin shi a cikin ranta don yanzu ya fara bata tsoro gaba daya don ya daina sayin ta da yake yi a da can baya.
  Daga haka ya sauka kasa yana yana kiran yaran aikin gidan shi ya shigo mashi da buhun da ya dawo dasu jiya.
   Ya  sa akai masu dakin da su mommy suke tare dasu iyan bawa a gidan daidai lokacin Nafisa ta sauko kasa tana fadin Sabel wanan kayan haka daga ina kuma ?
   Yaro  gidan dan yaren su na buzaye yace maigida yace ya dauka yakai dakin dabakin shi suke ciki tabi buhun kayan da kallo nan ta so sanin abinda ke ciki.
  Don haka tabu shi a baya wai taje da sunan gaida mommy yau da kwana yana zaune saman kujeran dakin suna hira da iyan bawa ta shigo tana gaidasu idon ta akan buhun dake gaban shi nan ya fahinci buhun ta biyo a lokacin don ganin may ke ciki.
  Idon ta ya gano mata atamfan da ya fara fitarwa kasa yana son fitar da sauran sai gata ta daure fuska tamau idan da dane da ya shiga hankalin shi ga yadda ya ga ta daure fuskanta.
      Sai ci gaba da fitar da kayan yake yana bin sunaye su yadda na rubuta ajikin ko wani ledan kayan yana ajewa gaban mommy bai fara bayani ba ta juya ta bar dakin a fusace cikin bacin rai.
   Sai bayan fitan ta daga dakin ya fara yiwa mommy bayanin kayan tare da dora ma ko wani kudi a saman kayan yace suyi dinki sai Allah ya dawo dashi lafiya zai shigo yayi masu ban gajiya.
   Kallon shi mommy tayi da kyau bayan ta gama sauraro  shi tace wanan hidimar yayi yawa haka  babangida don haka kabar kudin nan abin kuma ya koma biya , ?
   Mu da mukazo aikin lada zaka saka muna da wanan irin alherin haka mai yawa gaskiya hakan bai muna dadi ba gaba baka son inzo zama da diya ta ke nan in Allah yayi abin.
   Murmushi yayi yace ko baku zo nan ba mommy zan iya maku fiye da hakan don haka wanan ba komai bane Abba yace a tura ku gida yau kafin in wuce.
  Nasan ya kiraki ya fada maki komai ai don haka idan da sauran wani abin sai ku fada min a sayo maku kafin ku wuce na kuma gode kwarai da kokarin ku a kaina.
  Sai dai ayi hakkuri da yanayi matar gidan don Nafisa sai hakkuri nima dai kun ga shinakeyi.
  Ka dauki kudin nan ko ka rage dawainiyar yayi yawa haka abin ya zama  kamar biya mu kayi ke nan ya mike yana murmushi yana fadin ba komai iyan bawa ai yima kaine.
  Na shirya driver da  zai sauke ku idan kun gama sai aimin waya zan dan leka office don tafiyan mu sai dare zamuyi shi akwai dan sauran lokaci zuwa yanzu.
  Godiya sosai sukai mai ya fita nan dai mommy suka fara shirin tafiya don ba a ketare maganan Abba a gidan.
   Yana fitowa bai koma ciki ba ya nufi hanyar fita daga gidan muryan Nafisa yaji a bayan shi tana fadin dama nasan abinda ya zaunar da su ke nan a gidan nan tun bayan suna basu tafi ba kamar yadda kowa ya wuce.
   Suwa ke nan kike nufi wanda kasai wa kaya bada sani ba yanzu Allah ya tona ma asiri na gani do  baku so in gani ba.
  Wai nafisa kina da hankali kuwa iyayyen nawa ma bakin ciki kike dasu akan nayi masu alheri tace ai ba su kadai suka wahala a gidan ba har dasu Yanyala sun wahala .
  Don may ba zaka saya masu tare ba ka ware naka kadai watau sune ka sani ke nan kai ya girgiza cikin kunan rai yace ba laifin ki bane sai kawai yaga ta sha mai gaba ta inda zai wuce ta.
  Hayaniyar su ne ya fito dasu mommy waje ganin su mommy ba sa ta fasa ci mai mutunci ba mommy ce ta hana shi magana.
  Duk ta hade dasu mommy tana zagi tare da fadin tayi ma kowa nashi iyaka da gidan tun da ba zuwan arziki suke yi ba jifa samun wuri a gurin wanan matar ita ha gida taf da yan uwanta kullun sai kara yawan su takeyi a gidan.
  Kowa yazo da sunan ganin ta sai ya nemi wuri ya zauna ba maganan zuwa gida kuma gare su an shafe ke nan.
  Haka ya fita gidan ranshi bace ranan su mommy sun ga fitsara a gurin Nafisa inda tayi ta aiban ta su suna ji suna gani ba abinda zasu iya yi tana gani  taci gaban su.
  Ranan haka dai ya wuni cikin bacin rai halin Nafisa ya jutayin irin zaman da suke na rashin jin dadi a gare shi kuma bai jin zai iya rabuwa da ita ko kadan.
  Bayan su mommy sun gama shiri suka kirashi yace gashi nan zuwa ya samay su a shirye don haka basu bata lokaci ba suka fito da kayan su Yusuf suka loda a mota sukai sallama dasu suka tafi suna kara bashi hakkuri.
   Da yamma ya fito cikin shirin shi ya samay ta a dakin ta tana zaune tana waya ganin shi bai sa ta katse wayan ba sai data gama yake fadin su zasu tafi.
  Wani sabon lalura ta kirkiro mashi aladole kudin da take hasashen ya kashe ma iyayyen nashi sai ya kashe mata su bayan ya riga da ya sallamay ta da safe ta lissafa mai abinda take so ya bata.
  Nafisa wai may zakiyi da kudin da kike karba ne haka ya tambaye ta wani kallo tayi mashi tace idan zaka bani ka bani ba sai ka tsaya ka tambaye ni ba kuma ina sin idan ka dawo zan tafi gida inyi gyaran gidan mu na can.
  Dole ya bata daga cikin kudin da zaiyi amfani dashi don kawai su rabu lafiya da ita.

ZAINAB IDRIS MAKAWA   
             SEENABU
Tun  bayan rabuwan mu dashi ban kara jin labatjn su ba haka yasa nasan sun tafi ke nan tun tafiyan su kuma ban sake ji daga gare su ba bakuma labarin mamud.
  Duk da son mamud da nake a zuciya na yanzu na fara fitar dashi a raina don na fahinci ba wani son gaskiya yake min ba .
  A cikin haka muka gama exam din mu na wanan zangon kaduna ya kamata in tafi amma don gudun haduwa da mommy a can yasa na kekeshe kasa nace ma Ya Amina ba zan tafi can ba gida nake son yin hutu dole ta kyale ni don tasan tunda nace haka ba zan zo ba.
  Tunda na dawo gida in ba islamiya ba ban fita ko ina don haka ba kowa ne yasan ina garin ba yau satina biyu da zuwa gida na shirya zuwa gidan anty mu dake aure a falamingo easthe.
   Tare da karamin kanina muka fito daga gida mun zo bakin titi inda zamu tare Napep din da zai kai mu unguwar nasu mun dan tsaya a gurin na hango wata mota daga can gefe tafe.
  Zuwa mai shi yayi roud ya dawo inda muke tsaye da kanina a hankali yazo inda muke tsaye ya tsaya ban daga kai na kalle shi ba wata taxis tazo tana tambayan inda zamu.
   Sai lokacin na cikin motar yace wai ba khadija bace wanan a hankali na dago ina kallon shi mamud ne ya kara yin fresh dashi har bakin shi na sheki.
   Ya samu wuri ya parka motar shi da kyau ya fito daga cikin motar zuwa inda muke tsaye tare da fadin hajiya khadija ke nan ashe kin shigo garin namu.
    Nadan yi murmushi nace mamud manya ashe kuna kasan na dauka baka kasan murmushi yayi yana fadin i am sorry wallahi na bar Abuja ban samu leka wuri ki ba sai yanzu gashi mun hadu.
    Mun gaisa duk da ban wani sake mai fuska ba sai kame kamay yakeyi yace ya labari nace kai za a tambaya kai dana ga sauyi a tare da kai.
  Yace sauyi gare ni ko a gare ki jifa yadda kika koma dan kwana biyun nan danayi ban ganki ba kin koma wata danya dake kamar wata diyan larabawa wai ma ko kina karatu kuwa ?
  Dariya nayi nace kai mamud bari bani dariya haka akan titi muke fa yace haka fa ina zaku naga kamar mota kuke jira nan.
  Filamingo easthe zamu na fada kai tsaye yace muje in sauke ku nace ka barshi kawai zamu samu taxi anan yanzu .
  A a khadija kada muyi dake please ai ko ba siyasa akwai daga hannu  ko dariya nayi nace ashe dai hausa ya zauna a bakin ka haka ?
  Yana dariya muka taka zuwa bakin motar shi ya bude min gaba na shiga ya bude baya mansur ya shiga ya zagayo ya shiga mazaunin driver ya fara tuki.
   Mun dau hanya yace van san yaya zan fara maki bayani ba ma sai dai da farko na gode da kika fahince ni har baki nuna min komai ba haka.
   May kake son in nuna maka gudu da kayi daga wuri na ko may yace wallahi khadija ba laifi na bane ba naki bane.
   Laifin waye na tambaye shi cikin kallon fuskan shi yace ba zaki gane bane khadija amma tunda kina gari zanzo har gida in maki bayanin komai.
  Nace kasan gidan mu ne yace zandai sani yanzu daga bakin ki idan kin bani dama can kuma yace gaskiya khadija kin kara wani itin kyau da girma a lokaci daya.
  Nace kai mamud wanda ke karatun wahala kake fadan haka gareshi dan kallo na yayi yace kin ko ga yadda kika koma kuwa ?
  Ina dariya na kalle shi nace yaya na koma kuma  ya dan bugi sitiyarin motar da hannun shi yace I don’t know how to say.
  Amma ai kema kin san kin sake gaba daya wallahi nace dama ance ku Nufawa mayu ne to kurwa na kur kada ku cinye ni.
   Dariya yayi sosai yace amma kin kusa gama karatun naki ko yanzu  dariya abin na mamud ke bani don na gane nufin shi sarai.
  Katse shi nayi da fadin ina madam din ka ya fadada murmushin shi yace yaya akayi ki san ina da aure yanzu ?
  Nace tambayan ka ai nayi suna lafiya yace lafiyan su kalau wallahi  daidai lokacin muka shigo Filamingo din da kwatance har muka iso kofan su antyn nawa.
  Godiya nayi mashi ina bude kofan motar yace khadija na juyo ina kallon shi cikin jan aji yace wani time zaki koma gida inzo in dauke ku ?
  No ka barshi kawai mun gode da hakan sai anjima nafita daga motar Mansur kanina ya kira yasa hannu a aljihun shi ya ciro kudi ya ba yaron ya tafi bayan yayi min horn.
  Gidan Ya Hauwa muka shiga da sallama na bude labule falon su da danta babba na fara cin karo zai fito yana ganin mu ya saki ihu yana fadin ga mommy khadi .
   Murmushi nayi ina kamo shi nace Lawal kaine ka girma haka ina yan uwan ka yace suna ciki jin ihun yaron yasa Ya Hauwa ta fito daga kitchen din su tana fadin sai yau kika ga daman zuwa gidan mu ?
   Haba dai ya hauwa kema kin san ba halina bane haka na dawo da gajiyan karatu ne wanan karon na dan tsaya in huta.
  Mansur ne ya gaida ita tace a a mansur tare kuke tafe da antyn naka ashe nace ai kin san mutumi nane shi nan dai muka zauna a falon shi wanda ke bukatan gyara ba halin yin hakan gare su don yanayi.
   Ranan ni na girka masu abincin rana a gidan yaran suna ta murnan kasancewa tare da mu  bayan na gama na gyara mata gida don haka take ba gwanan gyara bace ita amma idan ka ganta a waje sai ka dauka ko agidan ta haka take da tsabta.
   Ranan sai magariba muka koma koma gida na samu daddy yana fadan rashin dawowan mu da wuri gida.
  Muna shiga ya mayar da fadan da yake wa mama akan mu may yasa na bari nakai wanan lokacin ban dawo gida ba idan na fita kada in kara kai dare haka bamu dawo gida ba .
  Kaina yana sunkuye a kasa na amsa da toh daddy daga haka ya fita daga gidan rai bace buta na dauka naje na kewaya na dawo na daura alwala don har an sallamay sallah a lokacin.
  Sai da na idar da sallah na gaida mama da gida da take dakin ta zaune saman sallaya tana jan tasbaha.
  Tace khadija may yasa kuka kai wanan lokacin a waje haka kika bari har magariba yayi maku a waje haka baki san fita a wanan lokacin baida kyau ba.
   Mama kuyi hakkuri ba zan kara kai haka ba tsayawa nayi gyara ma ya hauwa gida shine yasa mukai wanan lokacin a can .
  Tsuki tayi tana kawar da kanta tare da fadin ita ke nan malalaciya bata iya gyaran gida kullun sai dai ai mata ina amfanin a ganta a waje fes amma a gidan ta baya kalluwa.
  Ban san inda ta dauko wanan hakin nata ba nidai nasan na koyar daku abinda ya dace koda kun kama dakin ku zaku iya kulawa dayi amma sai dai kayya bata dauki wanan tarbiyan dana baku ba ita.
  Wanka nashiga don inji dadin kwaciya saboda yau na aikatu a gidan yar uwar tawa bayan na fito na tayar da sallah isha,i mama ta turu yaro wai idan na gama inje in debi abinci nace a koshe nake munci abinci gidan ya hauwa kafin mu dawo gida.
   Wani yaro ne ya shigo yana sallama da bazan iya sheda muryan yaron ba yana fadin wai ana sallama da khadija a waje.
  Da mamaki daga cikin dakin da nake, nake tambayan yaron ko waye yace shima zai wuce ne ya aiko shi don haka bai san ko waye ba.
  Jekace dashi tayi barci yaron ya fita can sai gashi ya dawo yana fadi cikin daga murya wai yace kiyi hakkuri kizo minti biyu .
  Na fito daga dakin ina fadin bana ce kace dashi nayi barci bane yaron yace na fada mashi yace indawo in fada maki haka.
  Zan sake magana mama tace da yaron ya tafi ganin nan zuwa tace kije giga kowaye kin san damay yazo gurin ki wulakamci bai da kyau ina fada maku.
  Hijjab na dauko na aza saman rigar dake jikina na fita tun daga nisa na gane motar mamud ta dazun da ya dauke mu dashi.
  Mamakin abinda ya kawo shi nake yi da wanda ya nuna mashi gidan namu yazo yana ganina ya fito daga motar zuwa guri na.
  Bayan mun gaisa ne yace kin yi mamakin hani na yanzu ko nace kwarai kuwa yace to kibar mamaki don abin jiya na dawo maki dashi.
  Da sauri nace meke nan sai da yayi murmyshi yace khadija ke nan So mana da kaunar ki khadija don tun dazun dana ganki na kasa natsuwa tundazu na kasa control din kaina akan ki abin ya dawo min sabo yanzu a raina.
  Mamud ke nan abinda ya wuce ai ya riga da ya tafi don ni kuma sai naji yanzu sam baka kwanta min ba a raina.
  Da sauri yace saboda may khadija nace halinka bai mun a yanzu don ba zan kara yarda ka sa min miki a zuciya ba.
  Kasan ina son ka da farko mamud sai da ka bari na gama yarda dakai ka gudu ka barni babu bayanin komai daga gare ka Allah ya taimake ni, ni ba mai sa abu ga zuciyana bane .
  Khadija ba haka na bane wallahi don koda muke tare dake already ina da mata karawa nake son yi sai kuma naje ma iyayyena da maganan ki amma sukaki banin goyon bayan haka don basu son in auri wace ba yaren mu ba.
  Kin ga kuma bazanki maganan iyayye na ba sai naji kunyan komawa gare ki in maki bayanin halin da nake ciki .
  Katse shi nayi da fadin basu sona yanzu may kadawo yi wuri na kuma yace ina da daman yanzu in zabi wace nake so tunda ina da yaren mu mutum biyu .
  Kai na girgiza tare da fadin mamud kasan tun farko ban kika ba kai da kanka ka guje ni yanzun kuma baka da bakin cewa ka dawo gare ni.
   Ko banza na farko ba zan shiga inda ba a sona ba sai na biyu yanzu ni mai zai kaini wurin mai mata biyu in ba daukan magana ba.
  Dariya yayi a lokacin tare da fadin khadija ke nan watau kin mayar da laifin a gare ni ni daya to naji na dauka kuma ki kwantar da hankalin ki ba a gida daya zan ajeki dasu ba.
  Don haka ai min hakkuri muci gaba kamar yadda muke da don son ki yana son ya min illa a rayuwana.
  Mamud gaskiya sai dai kayi hakkuri don ba zan iya ba yanzu gidan ka yafi karfi na da sauri yace what ?
  Nace yes I mean it don bazan dauki wanan risk din ba da hankali na ina ji ina gani.
  Shiru yadan yi na dan wani lokaci kafin ya dago kai yace is ok naji amma zaki yarda ina kawo maki ziyara lokaci lokaci don ban sani ba koda rabo na ciki.
   Dadai kayi hakkurin kamar yadda nace dakai zafi kyau don ban son ka dinga wahal da kan ka yace ke kika dauke shi a wahala.
  Ni abinda nake so ne na damu dashi don haka ban hakkura ba ki sani nace wanan kuma matsalar kace ni dai na fada ma gaskiya.
  Bai dade ba mukayi sallama ya tafi na shigo gida alwala nayi na gabatar da shafa,i da wuturi na samu wuri na kwanta.
  Amma ranan sai barci ya gagari idona saboda tunanen dayayi min yawa a lokacin a raina nace ohh ni khadija haka rayuwa zai kasance kuma sai masu mata ne ke zuwa ne mana ni ban san ko may yakawo haka ba gare ni.
  Gashi ni kuma banda sha,awan auren namiji mai mata don ban son yawan fitina daga anayi a gidajen masu mata nasan da laifi nane kin kula samari amma yanzu ban san dalilin rashin samun su ba,  da haka har barci ya dauke ni ban sani ba.
 
Matafiya umurah sun sauka lafiya don haka yan uwa da abokan arziki suke shigowa gaida shi gidan shi wanda ba wasu mutane ke zuwa ba don sanin hslin matar gidan da sukayi sai wa yan da ya zama ma dole sai sun zo ke zuwa gaida shi.
  Bata san cewa Fati ta koma dakin ta ba sai a bakin wani abokin shi da yazo yana mashi sherin yaushe zai leka can kaduna yaji ance fati na gidan shi yanzu.
   Wani kallon mamaki ta aikawa AA din sai da yasha jinin jikin shi don yasan akwai rikici babba yau a tsakanin su dakewa yayi kamar bai ganta ba yaci gaba da hira da abokin shi.
   Sai dai hankalin shi yana gurin ta duk abinda yake yi din bayan tafiyan mutumin tun a falo ta fara tambayan shi Fati ta dawo gidan ka ne baka fada min ba.
   Yace ta dawo suna nan gida yanzu haka shewa tayi tare da mikewa tsaye tana fadin haukan banza ke nan yadda ta dawo haka zata koma inda ta fito.
   Wanan kuma maganan ki ne don dama ai ba wanda ya kore ta ita da kanta taga daman fita yanzu kuma ta dawo tace ashe ko zamu zuba daku mugani a gidan nan.
   Ke ban fa son haukan naki na bazan Fati bakuwa ce a gare ki ko yanzu ne na fara zama da ita zaman ki na nan Abuja ita kuma yanzu bayan shekaru ta zabi zama kaduna ita da diyan ta.
  Don haka ban son jaye jayen wani matsala kima da zai kawo muna tashin hankali ba gaira ba dalili haka,
  Yana fadin haka ya mike ya haura sama ya barta a falon cike da mamaki halin irin na Nafisa da bata iya boye kishin ta .
   Satin shi biyu abuja yana hutawa ya kama hanyan zuwa kaduna gida don ya hana kowa yazo daga can yace yana nan tafe.
  Nafisa bata yarda cewa iyayyen shi zai tafi gani ba ta shirya wai tare zasu tafi ba yadda ya iya dole a tare da ita yayi tafiyan.
   Tunda suka shiga garin ta hana komai a tsakanin shi da Fati din bayan gaisuwa bata yarda komai ya kara hada suba don ko abinci da Fati ta gama sai cewa nafisa tayi abincin yayi mai nauyi ba zai ci ba.
   Suna zaune da dare ta na kokarin hana shi shiga wurin Fati da kissa da iyayi wayan hajiya mama ya shigo mashi nasiha tayi mai sosai wanda ya kashe mai jiki inda take mai tuni da cewa ya tuna hakkin ko wace yana a kanshi do  haka ya daure yana ba kowa hakkin ta.
  Bayan sun gama waya ne da mahafiyar shi bai wani dauki lokaci taga ya mike da sauri take tambayan shi ina zai tafi kuma.
  Kai tsaye yace mata gun Fati zan tafi bata iya boye bacin ranta ba ko kadan tace bai isa ba don tare suka zo fati ta bari idan bai zo da ita ba sai ta kwana dashi.
  Yace a garin ku haka akeyi wanan dokan hakan wai Nafisa may kika dauke ni kamar wace ta haife ni zaki dinga bani umurni kai tsaye.
   Ba sake kula ta ba ya shige sashen Fatin kamar yadda yayi tsamani hakan ya samay ta sunyi barci da yaranta a saman gadon dakin ta tana saye da kayan data wuni dashi a jikin ta tunda suka zo,
   Ya dade tsaye a kansu bata san ya shigo dakin ba sai da ya dan bubuga mata kafa ta falka ina zan kwanta yace da ita kai tsaye dan watsake idon ta takeyi daga nauyin barcin da ya fara kama idon ta din.
  Sai can tace dakin ka fa yace Nafisa na cikin dakin kin sani mikewa tayi tana gyara ma yaran kwanciya tare da gyara dan wurin da ta bar mashi ya kwanta.
  Kallon ta yayi daga inda yake tsaye yana tambayan ta wai dakin su fa da kika dawo da kwanan su nan kamar ba zata bashi amsa ba sai can tace ban san anan zaka kwana ba ai tare muke kwana tunda ba kowa a gidan.
  Tsuki yayi yana hawowa gadon ya takure kan shi a guri daya kamar may kyankyamin dakin amma kin san hakan ba daidai bane nasha fada maki haka kwana da yara a daki daya.
  Banza tayi dashi ba wai banzan bane ya sani halin ta daine nakasa da kyaluwa haka take kindis da ita ko yaushe fuska ba fara, a.
Tunda ya samu barci ya dauke shi bai falka ba sai karfe hudu da rabi na asuba da bugun kofar nafisa ke masu ya tayar dashi a firgice.
   Tambaya yayi yana zura riga a jikin shi tace itace ya bude kofan ya bude da mamakon ta a fuskan shi yana tambaya lafiya take cewa dashi.
  Banan ce bata da lafiya basuyi barci ba kallon yarinyar dake sabale a kafadan ta yayi tare da fadin ta miko mashi ita.
  Sai da tayi mai wani kallo tace ka karasa fitowa daga dakin mana murmushiin gefen fuska ya sauke kafin ya fito din muryam Fatine take tambayan make damun yarinyar ne ?
  Kada ki soma ki taba min ya ta yanzu ranki ya baci a gidan nan tana fadi tare da watsa mata harara da saida taja jikin ta ta koma daga bayan shi.
   Karban yarinyar yayi ya nufi falon kasa da ita suna biye a bayan shi dukan su ruwa ya fara ba yarinyar tasha sosai tare da ajiyan zuciya ta lafe a jikin shi.
  Dakin da bai koma ba ke nan ya zauna nan falo da yarinyar data koma barci a jikin shi tana sauke ajiyan zuciya .
  Juyawa fati tayi ta koma dakin ta don ta san kadan ne daga cikin sherin Nafisa ko ba yarinya a tsakanin su haka take masu idan zai kwana a dakin Fati din tace bata da lafiya karshe a dakin ta zai kwana.
  Do  haka ta juya abinta taje ta kwanta bata kara ganin shi ba har rana breakfast din da ta hada mai baci ba wani aka kawo masu daga gidan Auta amiyar Nafisa din.
  Haka fati tayi ta hadiyan bakin ciki da wanan zuwan nasu ita da ganin miji sai dare idan zai kwanta zai lalabo ya dawo dakin ya kwanta da safe ya fice kuma ranan nafisa tace itace zatai girki .
  Dole Fati ta kyaleta tayi yadda ranta ke so tunda har mijin ma ya biye mata ita yanzu burin ta shine ta zauna a cikin yaranta kawai su girma a tare da ita.
  Nafisa bata shiga gaida sarakkanta ba balle suga yar jikan tasu data haifa da dan su sau daya ta shiga  gaidasu ana gobe zata koma bata ba kowa yar ta ba suma basu taya zasu dauka ba.
Sai kuma abin ya bata mata rai don yadda ta shirya bata samu yi ba sai taji haushin basar da ita da sukayi takoma fadin wai yanzu har kiyayyan da suke mata ya shafi yar ta jikan su.
  Haka ya sa AA yaji haushin abinda sukai mata a ranshi har ya kira mommy yana fada mata abinda sukaiwa Nafisa da yar shi baiji dadin hakan ba.
  Don ba halin ya kira mahaifiyar shi ya fada mata yasan kwanan wasa yanzu za a jisu da ita idan ta fara mai fada yasa shi kiran mommy.
    Mommy tace dashi babangida kasan halin matar ka fa ta make yarta a jikin ta bata ba kowa ba mune zamu karba tai muna wullakanci amma munyi kuskure gaba zamu gyara insha Allahu.
   Bayan kwana hudu suka nada suka koma abuja tun da suka kama hanya ta washe ranta da ya rasa gane mata da suke a kadunan.
  Yanzu ko kamar ba ita ba sai hira take jan shi a motar tana faman dariya tana kuma wasa da yar dake zaune a cinyar baban ta din.
  Tunda ya dawo ta samu kansa da kyau sai dai abinda bata sani ba yanzu asiri bai faye tasiri ya dauki lokaci a jikin shi don maganin tsarin da malam na zaria ya bashi.
   Kuma abokin shi Yusuf bai zauna ba akan shi yana tsaye da alamarin shi haka ma mahaifan shi suna tsaye da mashi addua sosai yanzu.

Yau tunda na dawo daga islamiya nake kwance ba wai don banda lafiya ba sai dai ina jin jikina ba dadi ne ko aikin gida da nake taya mama ban iya tayata yi ba.
   Barci nayi sosai a ranan can zuwa rana yaro ya shigo yana fadin ana sallama dani a waje mama ta shigo ta tadani tana fadin min wai ina da bako a waje.
  Mikewa nayi da kyar don barcin dake idona na  ban tsaya gyara fuskana ba na fita daga gidan haka na mamud ne zaune a motar shi da yaran shi biyu.
   Na iso inda suke ina gaida shi bayan motan na bude inda yaran suke zauna kafa na suna waje ina gaidasu tare da tambaya su yaya makaranta.
   Kafin yaran su bani amsa ya jefo min tambaya yaya naga fuskan ki haka kuma ko baki da lafiya ne ya tambaya ?
   Nace daga barci na tashi yanzu ba tare dana kalle shi ba hannu na mika wa yar karamar yarinya dake saye a cikin uniform din shekk lemo sai yarinyar ta noke taki zuwa.
  Tambayar ta nayi yaya sunan ta yace sadika dayan kuma nasir ina taba kafar yarinyar nace zakici biscut ta daga min kai nace to sai kinzo wurina sai ta kara makewa.
  Ina zuwa nace dashi cikina koma na hado masu kayan kwalama na yara wanda na dawo dashi muna ci da kanne na nafito rike da leda a hannuna namikawa yaran.
  Da sauri suka karba nan dai muka taba dan hira yace zai maida yaran gida daga islamiya ya dauko su mukai sallama ya tafi.
   Bayan sun isa ma sai da ya kirani muka taba hira ya kashe wayan tare da fadin zai zo amsa gudane wurina nace na hutar dakai kada ka wahal da kan ka.
  Yace to zamuyi waya nace sai najika aiki gida na taya mama ta koma folo tana kallo sai dana gama zuwa dare na shiga daki na samu wayan mamud har six miscall ya kira ban dauka ba.
  Kiran layin shi nayi aka dauka ban tsaya sauraren ba nace ina waje ne ina aiki banga kiran ka ba.
  Ban karasa magana na ba naji muryan mace tana fadin ke wacece da zaki kira lamban mijina kin san ko waye mamud kuwa ?
   To bari kiji daga yau kada ki sake shiga harkan mijina in ba haka ba zan sa ayi maganin ki a garin nan shiru nayi ina sauraren ta sai da ta gama nace.
  Ke kuma wacecd a guri  mamud din bari ki ji ki sani ba don ki ke kadai akayi shi ba daga yau ki gyara kalamin ki inzaki magana akan shi ki dinga cewa mijin mu.
   Ina fadin haka ban tsaya jin haukanta ba na kashe wayan ina dariya nace banza mahaukaciya ni mijin ki bai a gaba na yanzu da kin ga tsiya wallahi.
   Bai kirani ba nima ban kirashi ba sai bayan kwana biyu sai gashi ya aiko kirana wai ace mamud ne mace ace ban samun fitowa aiki nake yi.
  Mamace ta samin baki dole na fita naci karo da dan aiken ya dawo wai yace don Allah inyi hakkuri minti biyu kawai zanyi.
  Tare muka koma da dan sakon na samay shi zaune a cikin motar shi yana duban wayan shi karasowa na ya fito yana washe baki.
  Fuska na a daure na gaida shi magana yake na kyale shi sai ko umm ko ummumm nake bashi amsa dashi kaina a kasa ina dakilan wayana.
  Muryan shi naji yana fadin yau gimbiya  may ya faru ne naga an fito min haka a daure nace wani abu ka gani halan ?
  Yadan motsa kafan shi kadan yana murmushi tare da harde hannayen shi guri daya yace ko gimbiyar tawa mulki take jine haka ?
  Sai da nayi mashi wani irin kallo shekeke nace mulki ai mulki yana gidan ka don ko wayan ka sai an baka izinin dauka kake dauka ko zuwa gurina yanzu waya sani ko santan hanya kayi kada matan ka su gani.
   A cikin rashin kuzariya dago kai yana kallona yace wanan wani irin magana ne haka khadija kikeyi kai tsaye ba tare da tunane ba.
  Nace irin wamda matar ka tayi min jiya daga kiran wayan ka ta dauka tana zagina a wayan ta daukar min waya fa kikace nace ka duba nan ga kirana a wayana kana gani katuna ina kaje jiya a daidai wanan lokacin ?
   Look mamud na fada ma soyayya dakai a yanzu akwai matsala ka nace akan sai munyi gashi tin ba a je ko ina ba an fara kirana ana zagina daga gidan ka har da yimin iyaka dakai.
   Ya kai duban shi gare ni tare da sake dan murmushi yace mai shi tayi nasara gare ki ke nan  tunda gashi har kin karaya zaki bar mata ni.
   Haka muka kasance dashi muna musayan maganan karshe dai  yaban hakkuri nace ya wuce amma ya daina zuwa wurina.
  Yace ba da sanin shi ba amaryan shi ce ta dauka daya shiga wanka kuma da ya fito bata nuna mashi akwai wani matsala ba.
  Nace wanan kai ta shafa ni dai na gama magana kuma.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
            SEENABU
Hutun mu yana karewa na fara shirin komawa makaranta bayan na kara sati daya a sama agida ina tare da iyayyena da yan uwa na.
  Duk da ba so  daukan kaya nake yi ba hakan bai hana mama ta dan tanadar min irin abubuwan da uwayen mu mata suke tanadarwa yaro idan zai koma karanta.
  Inda mahaifina ya bani kudin da zanyi sayayya na raba kudi  biyu na mayar mai da rabi nace ina da kayan abinci da ban ci ba a daki na.
     Bayan na shirya ina shirin zuwa Abdulsalam garage da kayana inda zan shiga motar zuwa abuja na fito a cikin shiri na yan uwana suna a bayana zasuyi min rakiya bakin titi.
  Gaban daddy da mama nazo na durkusa har kasa ina fadin daddy zan tafi ya dago kai ya kalle ni tare da fadin khadija kin fito ke nan.
  Yace do  Allah khadija ki kula da kanki kamar yadda kika saba a baya ki maida hankali ga karatun ki kinga lokaci na   tafiya yanzu.
  Kaina na kasa nace in sha Allahu daddy na gode mama tace banda kai kai inda Allah bai kaika ba kawar da kanki ga komai sai kiga komai yazo maki a cikin sauki nace na gode mama na mike tsaye jiki a sanyaye.
   Ban dade ba na samu mota naba kanne na kudi su raba daga cikin wanda  daddy ya bani in rika din muka tafi tare da kanina dake bin min.
   Na isa Abuja da wuri inda na samu maryam ta rigani dawowa lokacin ranan mun jima tare muna hira ko barci bamuyi da wuri ba dan shaukin juna da mukeyi duk da muna waya kusan kullun da ita.
  Dayake muna da abinci ga kuma wanda maryanm ta karo don haka ban damu da nashiga gari in sayo komai ba don akwai shi a dakin.
  Mun samu sabbi  fuska a gidan namu don an dauki sabbin dalibai yanzu wasu sun tafi kuma koda zan dawo ban bari mamud ya sani ba  .
   Idan ya tambayeni yaushe zaki koma nakan ce dashi ba yanzu ba idan na tashi zan sanar da kai lokacin da ya samu labarin na koma school ranshi ya baci sosai dani.
  Kirana yayi ga waya yana fada wai ya fahinci gaba daya yanzu ban damu dashi ba don may zan koma school ban sanar dashi ba saida yazo gidan mu ya samu labarin na tafi.
   Nace dashi na fada maka tun farko kada ka wahal da kanka gare ni don ba auren ka zanyi ba na riga na rufe babin nan ko a raina.
  Satina biyu da dawowa sai ga mamud din ya kawo min ziyara gaskiya banji dadin zuwan shi ba don na gane yana son da karfi da yaji ya shiga raina again.
  Yadan jima a guri na muna hira dashi wanda hiran duk a kan zaman mu dashi ne anan maryam da wata Aisha da yanzu muke tare da ita suka samay mu.
  Da zasu tafi ya basu alheri sukayi mai godiya yace ma maryam ta taya shi kanfen a guri na dariya tayi tace ban maka wanan alkawarin ba don abaya ka gujemu ba wani dalilin komai.
  Haba maryam banyi zaton jin haka a gare ki ba yace tace gaskiya na fada don yanzu tace karatun tane a gaban ta doon kaga muna gab da gamawa ba wasa a gare mu.
  Kaya masu yawa yazo min dashi irin na bukatan yan makaranta na nuna mashi hakan da yake yi ba daidai bane yace yace bai son irin kalamin nan da nake mashi.
  Bayan tafiyan shi ne muka bude kayan da yazo min dasu muna kallo Aisha tace amma ni kan sai naga kun dace dashi very handsome dashi wallahi.
  Nace Aisha ba handsome bane abin damuwa abinda ke cikin gidan mamud din ne ai maryam tace da ita ai khadija haka take samun handsome guys don baki ga AA bane har kike ganin mamud a matsayin handsome a gare ta.
   Nafitar da zancen wani mamud da AA a raina karatuna kawai nake fuskanta a yanzu da ya dau zafi gare mu banda lokacin kowa a tare dani ban kuma shiga gari ko yaushe ina cikin makaranta ko hostel din mu.
 
Zaune yake a office din shi yana aiki a wani file aka turo kofan office din nashi aka shigo baidago ya kalli wanda ya shigo din ba don yasan daga Yusuf ne sai ko masinjan office din nashi.
  Muryan da yaji yana mashi sallama ne yasa ya dago a lokacin wani hamshakin Alhaji ne ya shigo office din tare da wata mata a bayan shi.
  Yana ganin su ya kara daure fuskan shi tare da amsa masu sallaman su wuri suka samu suka zauna tare da fara gaida shi hakan yasa ya aje aikin da yake a lokacin yana fuskatar su.
   Bayan sun gama gaisawa ne mutumin ya fara magana da cewa yau ma gamu mun dawo gare ka bayan wahalan da mukasha kafin mu iso gare ka.
  Cikin daga hannu ya dakatar da mutumin ga maganan da ya fara yace Alhaji na fada ma wanan business din ba zai yuyu ba tun farko.
   Ba haka muke sake fili ga mutanen da basu san darahan shi ba suna gina abinda suka ga dama a cikin gari.
  Mutumin yace ba zancen gina wancen company a yanzu gare mu ni buri na kawai a yanzu shi ne in mallaki filin nan isan yana a matsayin nawa ne.
  Zan baka ko nawa kake bukata muddin zaka yarda ka saka min hannu in malaki daga milayan daya har zuwa hamsin zan baka idan kana so don wallahi ina , , , , , 
  Table di  gaban shi ya buga tare da mikewa tsaye yace na fada maka tun farko ba haka nake aikina ba kada kayi tsamanin da cin hanci ire iren ku na dogara.
  Ina da abinda zanyi a wuni daya million dari ya shigo min a accout dina ba tare da nasha wani wahala ba nafison in ci halan dina da na tsaya amsan cin hancin ire iren mutane irin ku.
  Matar ne ra katse shi da cewa ba wai cin hanci muka kawo maka ba kanina ka sani gogi bai ki kari ba balle mutum mai lalura da jama, a irin ki ko yaushe.
   Ina son ki sani wani gogin ne ke son kari wani ko an zuba mai wani ruwan aman shi yake yi don ba wurin zaman shi yazo ba.
   Don haka na roke ki ku fita min office yanzu ina da abubuwan yi a gabana da yawa da zanyi kada ku bata min lokaci.
   Matar zatai magana don ranta ya gama baci a lokacin mutumin ya daga mata hannu yace barshi mu tafi Allah ya bashi hakkuri bata mai rai da muka.
  Ya mike yana fadin mun barka lafiya sai dai ka sanin haka ba zai sani fushi dakai ba don abinda nake so nake nema a gare ka.
  Kuma ka sani ni ma ba irin mutanen ne da kake zargin suna sayen filin gwanati su gina abinda bai dace ba dashi nima kamar yadda zuciyar ka yake fari a kan kasan ka haka nawa zuciyar yake fes ga komai.
  Do  haka mun barka lafiya matar tace bai kamata kana saurin yanke hukunci haka ba akan abinda bakai bincike akan shi ba.
  Binsu yayi da kallo har suka fice a office din nashi wani iri  tsuki yaja tare da dafe kan shi da hannu shi daya yana fadin wai may mutane yanzu suke daukan kan su ne ?
   Yana jan tsuki tare da bude file din gaban shi yana gyara zaman shi da kyau Yusuf ne ya turo kofan ya shigo da sallama ciki.
  Tun daga nesa yake kallon yanayi abokin nashi yace may kuma akayi naga yanzu yanzu ka sauya gaba daya mana ?
  Bai yi magana ba sai duban files din yaci gaba dayi wuri Yusuf din ya samu ya zauna yana fuskanta abokin nashi tare da kara maimaita tambayan shi gare shi.
  Yace wanan mutumin mai bakin nacin tsiya akan sai ta mallaki filin da yake so mu bashi ne ya sake zuwa yanzu tare da wata mace dake son karanto min hauka.
  Wai har ni zasuce zasu iya ba daga million daya zuwa dari don dun mai dani mubukaci ban san ciwon kaina ba ko may ?
    No ba haka bane wasu ne ke bata wasu ga alumma shiyasa suke daukan haka ga kowa idan da sun san ko kai waye da ba zai tunkare ka da wanan zancen ba.
  Kai din ne ka faye boyon kurwa ga jamma, a kaki fitar da kan ka fili mutane sunan kokai waye may zai hana irin mutanen bazasu dinga tunkaran ka da suna baka ci  hanci ba ko yaushe.
  Murmushi ya sake a fuskan shi yace dole ne sai na fito na nuna ma duniya ko ni waye san nan zasu sani kana ganin ko a gidana da matsalar Nafisa kawai bai isheni ba yanzu.
  Ni ba wanan ba ma gida nake son ka sama mun mai dakuna da yawa inda zan sai wa yan uwata su koma nagaji da zaman da suke min a gida na wallahi.
  Mutum da gidan shi baida halin ya huta yaji dadin gidan nashi sai a hana shi shaka wanan abin yana damun raina sosai wallahi.
  Ya zakayi abinne sai hakkuri tunda yan uwar matakar ce kaga ko don yar uwasu zasu zo gidan da son ka ko ba da son ka ba.
   Iska ya furzo daga bakin shi tare da ci gaba da aikin shi yayin da Yusuf yake dan tunane a zaune a gaban shi.
  Can ya dago kai yace ina ganin fa hutun su khadija ya kare don haka nake ganin tana garin nan duk yadda akayi yanzu ta dawo school din.
   Ummm nima abinda nake tunane ke nan do  hutun su ya kare ai ita ba zata iya neman mutane a ida take ba tana jira a nemay ta ko ?
   A, a kaiko yaya zata nemay ka kafa san halin mata da jan ajin su ko yaushe aji kawai take ja muna ita ma a matsayin ta na mace.
  Ashe ko zata tsunke idan nine ya fadi ba tare da ya dago kanshi ba ya kalli Yusuf din dariya Yusuf yayi yace idan bata tsunke ba kai ai zaka tsuke din.
  Nayi mamaki da tunda muka dawo ka daina maganan khadijan amma acan kusan kullun kana min zancen ta har ina jin dadin ta shiga ranka yanzu ashe abin ba haka yake ba a gurin ka ban sani ba ?
  Au so kake banda aikin yi sai na ta yanzu kai ni fa tunda yanzu muna lafiya da Nafisa wani batun karama kaina wahala ya kawu min a zuciya.
  Ban gane may kake nufi ba yace Yusuf amma dai kaga aiki nakeyi ko yana mikewa yake fadin nagani barin baka wuri ka taba aikin ka.
   Har ya mike yake fadin ina son ka turawa Fati kudin da ta bukata na bukin da suke dashi don jiya take fada min bukin ya gabato.
  Kallon shi Yusuf yayi yace baka fada min nawa zan tura mata ba and kuma ina ganin ya dace ka tura ma da wanda zasuyi suturan fita bukin dashi.
  Katura mata biyar dakomai da komai don saboda laluran yara idan zai ishesu dariya Yusuf yayi yace indai fati ne ko bai isa ba baka jin korafin ta akai shiya nake ganin zubin su daya da khadija wallahi a wani gu.
  Baiyi magana ba sai murmushin da yayi a baiyane tare da fadin yar matsala wai ita a dole fushi take ba a kulata ba.
   Mata idan suka samu guri sai so wuce limit din su akai ni dake da mata biyu wata mace zata tsaya jawa rai a waje yanzu ?
   Fita Yusuf yayi yana mashi dariya tare da fadin ni dai nasan yanzu akwai nadi a lauje muje zuwa dai a hakan .
Kwance nake a dakina ina so in huta don yau a gajiye nake ga test ga pratical da muka fita da rana maryam ce ta shigo dakin tana fadin malama tashi zakiyi fa mu fita.
 Don har kayan miya nake son mu sayo kin ce kuma kina son kayan make-up ke ma da sauran abubuwan bukatan ki.
   Wani kallo nayi mata nace cabdi jam a yanzu yadda nake din nan don Allah ki tafi ki dawo yau na gaji wallahi sosai maryam.
  Ke ma kin san dole zaki tashi mu tafi don yau kadai kike free kara kwantawa nayi na fita batun ta tana ta shirin ta har na fara barci sai naji takai min doka a baya.
  A zabure na mike tana fadin don Allah tashi muje khadija kada ki bata muna lokaci mana nace maryam ba zaki barni in huta ba don Allah wallahi na gaji ne yau.
  Matsa min tayi dole na mike na fara shiri ba don naso ba dogon riga na saka kaman kullun don sune kayana ko atamfa zan dinka nafi  inyi dogon riga dashi yanzu nafi sakewa a cikin shi.
  Mun fito maikon mu tsaye kusa sai da ta jamu zuwa ciki  gari a shagon da take ganin zamu samu kaya da sauki a gurin.
  Raina na bata ina fadin ni ban iya wahalan ki wallahi shiyasa nace kizo ke daya don ban iya wanan wahala saboda son banza zaki jawo mu zuwa nan.
  Dariya take min tace kin dai riga da kin fito yanzu sai yadda nayi dake kuma ai shagon babbane so sai kaya iri iri ne a cikin sa .
  Binta nake a baya kamar dole banko iya magana don gajiyan da nake ji din ta sai wanan ta dauki wancan.
  Wani set din kaya make-up na gani mai kyau na mika hannu zan dauka naga hannun wata mace ta mika itama zata dauka.
  Duk tare da ita muka dauka a lokaci guda na juyo ina kallon ta Nafisa ce a baya na ta ke daukan set din ita ma nace cikin wani irin murya sake don na rigaki dauka.
  Nawa gare ki da zaki biya wanan make up din halan ta na shirin bangajeni ta dauka na riga ta rike kit diin nace don Allah ban wuri malama.
  Baki isa ba mara kunyar banza nace marasa kunya din ke wacece da zan dauki abu kice wai na bar maki kamshin turaren shine naji a hancina yana fadin may ke faruwa ne Nafisa ke da waye kuma ?
  Yana tsaye bayan ta rungumay da yarsu a kafadan shi tana barci tace dashi cikin zafin rai wanan mara kunyar mana tana ganin ina da raayi  abu kuma zata sa wani kazamin hannun ta ta dauka.
  Bar mata mana tunda ta riga ta daukan wanan ba sai a kawo maki wani ba tunda baza su rashi ba anan din .
   Haba malam yaya zan ce ina son abu sai kace wai in bar mata ita wacece da zan bar mata murmushi nayi nace au shagon dama na gidan ku ne ashe.
    Maryam ne ta iso take tambaya ganin shi kuma sai duk ta daburce tana gaida shi tare da gaida nafisa wace ke ta kunduma ashar a bakin ta.
   Nace da maryam muje ko ban tsaya kulataba na raba su na wuce maryam ta biyo ni baya duk a tsure take bamu tsaya magana ba muka mika kayan wurin biya suma a lokacin suka iso gurin biyan kudi yace hada kudin da nasu ka cire a katina lokacin nafisa ta iso ta samay shi tace dani.
  Karya kike yarinya zanyi magananin ki a garin nan dani kike wasa wallahi nace kafin kiyi magani na ni zan fara yin naki a garin nan na watsa masu harara har mijin nata naja hannun maryam muka tafi.
   Bayan mun fito muna saman titi da maryam muna jiran abin hawa sai ga su sun fito daga cikin shagon suma suka shiga wata hadadiyar motar su a gaban mu ta leko glass din motar tana fadin matsiyaciya ko mota ashe baku da.
  Tsawa mukaji ya daga mata tare da fadin wai manene haka nafisa ya ja motar da karfi suka bar gurin tsuki naja gami da harara na raka su dashi.
  Maryam tace yau naji takacin barin mota na a gida wallahi da dashi muke wanan matar bata isa tayi muna haka ba.
   Nace au ke kin damune da maganan ta ita uban wa ya bata motar gidan su badai da namijin nata take barazana ba.
   Matar nan lallai bata da hankali khadija jifa yadda take abu kamar wata yar bariki can nace guri ta samu tayi abinta amma ni bata isa ta fada mi  in kyale ta ba.
 A can kuma cikin motar su fadi Nafisa keyi wai ni ina ma nasan wanan fuskan ne na mance ida nasan wanan yarinyar wallahi ?
  Bai mata magana ba sai tukin motan shi yake yi shi kadai yasan abinda yake ji a ranshi a lokacin wai a haka zai hada wa yan nan yan zafin rai guri guda.
   Tace wai ashe ba yarinyar nan bace kuwa sai kuma tacce ba ita bace don waccan bata waye haka ba koma waye taci bashi wallahi  in dai nice zamu hadu wata rana ai zata raina kan ta.
  Tana takama don tana da kyau da diri wa zata nunawa kyau da fari anan kai dake dani a gida tana ganin kyauta zai rude kane take wani far da idanuwan ta haka.
  Murmushi ya danyi cikin kunan rai tare da fadin ki san abinda zaki fadawa mutane don baki san ko ita din waye ba a garin nan kizo ki jawo wa kanki matsala wata rana.
   Maryam ke ta zuba a mota nace please maryam ki rabani da maganar wanan matar mara mutunci wallahi sai na gwada mata ita karamar yar iska ne daga yau .
   Ni fa laifin ki nake gani da kika bata wanan daman take ganin ita wata tsiyace da kin jaye hankalin mijin ta ai da zata gane bata da wayo.
   Nace cikin mata wani iri  kallo wani mijin kike magana badai wanan mijin da baida ta cewa ba a gaban matar shi kike nufin in sace zuciyar shi in kai ina idan na sace ga mai iko da zuciyar shi kina gani.
   Jifa yadda yau ya nuna bai sanmu ba a gaban ta kwata kwata wallahi saboda tsoron mace da yakeyi.
  Ta kada kai tana fadin wallahi ba tsoro bane mutunta matar shi ce kawai yayi kuma ko wani namiji ne ma haka zai yi ai a gaban kowa.
  Don dai kawai a zauna lafiya amma da gidan shi kike yai haka shine zakice wani abu kyale ta nayi don ina ganin don ba ita akaiwa hakan ba yasa take fadin hakan.
  Har muka isa hostel din ba wanda yayi magana da dan uwa wanka nashiga na fito da alwalana na tayar da sallah ina gamawa na kwanta tare da bata baya .
   Muryan ta naji tana fadin bazaki ci komai ba ke na kike nufi zaki kwanta yanzu banjin cin komai murmushi tayi tare da fadin .
  Ai ba haka ya kamata ki bullo mata ba da fushi da abinci don ita ko shi basu ma san kina yi ba ai yanzu wallahi khadija lokaci yayi da zaki falka daga barcin da kike yi.
   Kamar yaya na katse ta tare da juyowa ina fuskantan ta nace may kike son in yi mata tace wallahi ki cusa kanki ga A A shine mafita a gareki.
   Kaina girgiza nace haba maryam wanan zubar da ajin kike son inyi komay kuma ni nasha fada maki ban ra, ayin wanan A A din sam.
    Tace ko baki son shi ki girgiza buzuwan nan don Allah tasan shayi ma ruwa ne ba ita kadai bace mace a duniya har duniya ta kare akwai mata kyawawa a duniya.
  Nasan wallahi kyau ki da zatin ki kadai ya ishe ta ballw uwa uba karatu da kike dashi wanda nasan ko bokon primary ita batayi ba kila acan .
  Dama na farko da zaki fara nuna mata kai tsaye shine gorin motar da taimaki kona kwana gudane kice mashi mota kike so anan zamu gane idan yana son ki sai muci gaba da aiwatar da shirin mu akanta sannu a hankali.
  Kallon ta nayi wani iri nace mota fa kika ce maryam ina zankai mota tace baki zaiyi kai tsaye akace maki balle ki damu.
  Fada mai hakan kawai zakiyi don mu gani kina da tasiri a gurin shi ko baki dashi ajiyan zuciya na sauke tare da fadin zan gwada in gani to.
  Har na kwanta kuma na juyo nace mata maryam idan ya bani motar fa ai na kashe kaina a gurin iyayyena wallahi.
  Kyautan mota wasa ne khadija ai ba baki zaiyi ba kai tsaye anan kin ga zamu san abin yi kuma nace to shike nan tunda haka kika ce tare da juya mata baya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
            SEENABU
Wanan magana ya tsaya min a rai sai dai gaskiya ban aminta da maganar maryam ba don ba zan iya bude baki na in roki namiji koda kwandala ba balle har mota.
  Ina zan kai mota idan ya bani a gida ince dasu ina nasamo mota kana wa yaban motan akan wani dalili zai min kyautar mota haka inma har zai bani din.
  Gaskiya maganar ta bai karbu ba a wuri na sam zandai gwada mata nima ba kyale bace zan mata abinda sai tarena kanta da kanta anan na aje maganan azuciyata.
  Sai dai ban fada ma maryam abinda na yanke a zuciyana ba nabar abin a raina don ita maryam ba abinda ya damay ta wanan nake ganin a gurin su ba komai bane hakan sai abin alfahari.
   Washe gari na mike kamar komai ba faru dani ba ajiya ganin yadda na sake yasa maryam dauka ko na dauki shawaranta ne.
   Ban damu da fita ba don yanzu karatuna shine a gabana ranan mun dawo maryam ke tambaya na wai har yanzu taji shiru mana ko ban buga ma AA waya bane akan batun motar.
 Banza nayi da ita kamar badani take magana ba sai da ta sake tambayana nace mata don Allah maryam ki bar wanan zancen .
   Don bashine a gabana ba yanzu abinda nazo yi nake fuskanta ban son abinda zai raba min hankali ko kadan.
   Amma dai khadija kin kwabsa wallahi don kawai kin tambayi AA abu shine kike ganin rage ajine a gurin ki wanan ai ba komai bane wallahi.
  Yan mata nawa samari ke sayawa mota kuma a zauna lafiya so maye bai sakawa a yi wanan ai kara ma kanki daraja ne ba wani abuba.
   Wani kallo nayi mata nace rokon shine karin daraja ga mace rokon ma irin na rashin hankali haka wai ma idan har ya bani motar ina kike son in kai mota yanzu.
  May yasa kike magana kamar wata bagidajiya ne khadija samu yafi iyawa aida samu din ai yadda zakiyi dashi ba abu bane mai wahala.
   To bazan roka din ba period sai kuma may a take ta bata ranta a wuri banza nayi da ita na mike ina dauko kayana da zan goge itama batayi min magana ba.
    Yana zaune a falon shi kiran Fati ya shigo mai a waya bayan sun gaisa dashi dan shiru ne ya biyo baya sai can ta kau da nata miskilancin tace naga dubu dari biyar ga account dina dazun.
   Shima cikin magana kamar yana gune dayin maganan ya bata amsa da cewa eh kudin da kika bukatane nace a tura maki har wanda zaki wanin abin.
  Angode tace mashi zata kashe wayan yace ke baki taba kiran mutum sai idan wani lalurar kudi ko wani abin ya taso maki zaki kira.
   Bazaki kira kiji halin da mutum yake ciki ba anan tace yanzun kiran nawa inyi godiya ya zama laifi ne kuma ?
  Tsuki yaja tare da kashe wayan ya lumshe idon shi yana jin takaicin wanan baki halin na fati a kulun ita bata taba wayewa tana nan a yadda ya san ta a baya.
  Karan takalma daji ne yasa shi bude idanuwan shi ya sauke a gare ta ba laifi idan zata fita tana kwalliya na kure a daka.
  Sai dai a gidane baka taba samun ta a cikin shiri yadda ya kamata gashi shi mutum ne mai son yaga mace ko yaushe a cikin kwalliya hakan nayi mashi dadi sosai.
   Karasowa tayi gare shi tana fadin zan fita don kasan yau saura yan kwanaki kadan bukin namu zan leka inga may ake shiryawa a gidan kareemay din.
   Yanzu wa kike fadawa da zaki fita kin nemi izzinina kan zaki fita din  kallon shi tayi tana dariya tace wata sabuwa ke nan ?
   Yanzu fitan ma da zanyi nan cikin gari sai na nemi izinin ka ko may bafa gari zan bari ba wanan wani magana kake nema kuma ?
   No ba sai kin nemi izzini ba tunda haka kika daukar wa kanki amma ki sani komai daren dadewa watarana wace zata nemi izzini na a gidan nan tana tafe.
   Da sauri ta gimtse fuskan tace bako a gidan nan ba idan ma mafalki kake ka falka ba wata shegiyar mace da zata sake shiga rayuwan ka kuma muddin ina raye kai koma ban raye na fada maka haka.
   Kina zancen ki dai yanzu don kin ga ban tashi ba cikin daure fuska tace don Allah mu bar wanan zancen zan fita lafiya kana son bata min rai na.
 Ta juya ta fita ba tare da tayi mai sallama ba don ranta ya gama baci sosai dashi a lokacin nan ta fita ta barshi zaune a falon .
  Zaman falon yaji ya ishe shi daga inda yake zaune yake jin kukan yar shi na zuwa mashi haka yasa ya mike yabi inda kukan nata yake zuwa.
  A dakin Yanyala ne kukan ke fitowa ya tsaya daga kofa yana kwakwasawa ba a karba ba yasa kai dakin ya samu yarinyar ta tashi daga barci tana zaune tana kuka ita kadai a dakin.
  Dauko ta yayi zuwa sama yayi mata wanka ya bata abinci har ya shirya ta ya fito gidan ba wanda ya nemay ta cikin gari ya fita da ita yawo.
   Gidan Yusuf ya nufa ya samu zai fito sai suka fita tare da yusuf din Yusuf ne ya kalle shi yace ina mukayi yanzu ga yarinya ka dauko kuma ?
  Yace dashi kaini gun khadija please batare da ya kalle shi ba murmushi Yusuf din yayi yace yau ranka a bace yake halan ?
   May kagani kace haka yace naji kace in kai gun khadija abinda na dade banji ba a gare ka shiyasa nasan an bata maka rai ke nan.
  Ya furzo iska daga bakin shi tare da kara rungumay yarinyar a jikin shi yace ban san irin rayuwan Nafisa ba Yusuf yau da yake ranan hutu ga kowa daya kamata in zauna gida in huta da iyalina.
  Sai gashi ta kirkiro fita wanin unguwar da baida dalilin komai wai kawar kawarta ne zata buki shine suka fita gin shirye shiryen bukin.
   Aka bar wanan yarinyar tana kuka ita kadai a dakin da sauri Yusuf yace subbahanallahi ina masu kula da yarinyar suka tafi kuma ?
   Yaja tsaki yace itama ta iya fita tabarta don may zasu tsaya kula mata da ya suma sun tafi nasu mana.
  Kai Allah ya sauwaka da halin bariki wallahi ba don nasan ka tun farko ba Abdulsamad da sai ince auren bariki kukayi da nafisa.
   Yanzun dai ni kaga ina jin kunyan Khadija wallahi na dade ban kirata ba kuma ban nemay ta ba tasan kuma muna garin .
  Ranan yakai three weeks mun hadu da ita da Nafisa a shago nakaita taiwa Bannan sayayya sai gasu ita da maryam har dan rikincin kayan shafa yaso hada su a gurin.
  Kasan halin nafisa da rashin hakkuri nan dai suka rikece ya bashi labarin komai da ya faru a wurin a tsakanin mu.
  Dariya Yusuf yayi sosai yace dakyau khadija baki daukan ta kwana ko kadan AA yace shine matsala ta da ita wallahi.
    A bakin hostels din mu suka tsaya aikawa sukayi a kirani bayan an tabbatar masu da ina ciki wata Annah ce tazo ta fada min ina da baki a waje.
  Ban tsaya wani gyara ba nasa kai na fita ganin kowaye yake nemana din tun daga nesa na hangoshi yana ma yarinyar wasa a mota.
   Har na iso inda suke fuska daure bai dago kai ba hannkalin shi naga yarinyar muryana yaji ina gaida Yusuf.
   Ya dago ya dan kalle ni bance dashi komai ba lafiya dai na gan ku a wanan lokacin na tambayi Yusuf din cikin daure fuskana.
   Haba kaunata kin daure fuska haka kamar ba gobe ai kya gaida dayan yayan naki ko tunda kin gan mu tare dashi nace ai ba wuri na yazo ba.
   Ka taba ganin mai arziki mijin hamshakiya yazo wurin diyar matsiyata wace bata kai matsayin a tsaya da ita ba ?
  Haba khadija ina wanan maganan ya fito haka kuma nace gashi nan ai ka tambaye shi idan nakai matsayin yazo inda nake sai ya fada ma .
    Murmushi AA din yayi yace da zaki shigo daga ciki zaifi don wanan zafin ranan zai iya maki illa anan har lokacin bai daina wasa da yarinyar ba.
  Ido na waro waje nace mota ai sai ku da matan ku yar matsiyata da bata gaji shiga mota ba ina zan taba motar ku in sha maku talauci a ciki.
  Motan ku na gama shigar ta tun ranan na dogara ga yadda Allah yayi mu ni da mahaifa bamu kai kan mu inda Allah bai kai mu ba.
   Ido ya runtse yana jin maganan da nake fadi har cikin ranshi Yusuf yace dakata kauna na nasan abinda yasa kike wanan maganan yanzu ma shi yace muzo mu duba ki don tun ranan bai samu lokacin zuwa nan ba.
   Ga kuma yar ki nan ya kawo maki ita ki ganta mun san Nafisa bata kyauta a yadda kukayi din nan ina ganin shine dalilin ramshin zuwan shi gurin ki don yasan dama a jirace kike dashi gashi kuma ashe har yanzu baki huce ba ke ?
   Akan may zanyi fushi da abinda ta fada ai gaskiya ta fada ba karya ba ni yar tallakace bamu da ko keke a gidan mu ita kuma da ya mayar yar masu arziki ba rawa taiwa Allah ba ya bata shi.
   Sai dai ta sani daren baiyi ko balle gari ya waye tajira taga zuwan daren tukun kafin ta wullakanta mutum.
   Yarinyar ne tasa rikici don haka hankalin mu ya koma gare ta yana dan jijiganta ta kallon inda nake tsaye a side din Yusuf tana mika hannun ta.
  Yusuf yace kin ga Banan tana ba mamanta hakkuri on behave of her father murmushi nayi ina kallon yarinyar nace fine girl wanan bai shafe ki ba ko ?
  Daga inda nake na mika hannu sai yarinyar ta zillo zuwa gurina banyi gigin karban ta a wurin shi ba sai cewa nayi ku kaita gida mana.
   Taga kuna kama da uwar ta ne take dauka ko ita ne nace Allah dai ya tsare min kama da wanan matar yarinyar bata bar kukan ba haka yasa naji har cikin raina na mika hannu ya miko min ita in dauke ta.
   Da sauri ko tazo wurina karban yarinyar nayi ina dan jijiga ta a hankali tare da shafa mata bayan ta sai tai shiru tana ajiyan zuciya a jikina.
  Ikon Allah banan kin san ta ne Yusuf ke fadan haka yana dariya AA yace daga inda yake zaune dauka ta ko maman ta ne don ta ganta fara.
  Farin mu ba daya da ita na na fadi a tsiwace shi dai murmushi yayi kawai bai yi dogon magana ba sai Yusuf ne yace dani wai yanzu na fahinci gori  motar nan ya bata maki rai sosai fa.
  Wallahi ko daya raina bai baci ba don nasan rashin ilimi ne yasa ta fadi haka ba wai tasan ni ko wacece bane don ita halinta ne wanan.
    Khadija kina son mota da sauri na dago kai ina kallon shi kamar bashi yayi maganan ba sai kuma na mayar da hankali na gurin yarinyar dake kokarin yayemin gyale dana yafa a kaina.
  Yusuf yace ana tambayan ki wai kina son mota ne kai na girgiza nace ina yar tallaka dani ina zanje da mota ita mota ya dama a yanzu har take fankama da hakan.
    Kiran sallah azahar aka fara yi Yusuf yace tau ashe har lokaci ya jane haka ban an kara ba zamu tafi da fatan kanwana ta huce ko ?
  Murmushi nayi don ban son jan zance ina son fara aiwatar da shiri na akan buzuwa yanzu ina kokarin mika yarinyar gare su tare da fadin .
  Sai ko yarinyar ta make a jikina taki zuwa karshe da na matsa da mikata sai tasa muna kuka tana lafewa a jikina.
    Yusuf ya juya ya kalle shi tare da fadin yaya ke nan za ayi yace mutafi kawai anjima zan dawo in dauke ta in mai da ita gida.
   Bazatai kuka na na tambaya da sauri yace ba gashi kin gani da idon ki ba taki zuwa wurin mu ku shiga da ita don ba gida zan tafi ba dama.
  Haka suka ja motar su suka tafi yarinyar kuma bata damu da tafiyan su ba din muka shiga ciki da ita maryam bata nan sai da ta dawo ta samu ina bata indomie dana dafa mata tana ci.
  Tambaya na tayi ina na samo yarinya haka diyar AA ne na bata amsa kai tsaye ido waje take kallona da mamaki a ina kika samota kuma ?
  Shiya kawo ta na bata amsa in bata wanan in bata wancan har barci ya dauki yarinyar .
  Ina da wasu set din ribon a jiye kana na a hankali na kama kan ta ina mata kitso tana barci .
  Har na gama bata tashi ba na daura mata ribon din a kowani tukuwa yarinyar ba tashi don yadda nake kama mata kan a hankali.
   
Wayan shi ne Nafisa ta kira a gigice wai basu ga Banan ba a gida yace kamar ya ba a ganta ba may kike nufi.
  Nan ta rikece mashi tana koro mashi bayanin yadda yanyala ta kirata daga gidan buki tana fada mata basu ga yar su ba wai.
  Yace maganan banza ke nan duk inda suka kai min yarinya na su fito min da ita kafin in dawo gida ko rayuka ku su baci ya kashe wayan cikin hasala.
   Ranan dai nafisa ta kirashi a waya yafi a kirga bai dauka ba kuma bai koma gidan ba kamar yadda suke jiran shi ya dawo duk ta fita hayacin ta yar ta ta bata a gidan.
   Yanzu baiji kunyan idon ki ba khadija ya dauko yar shi ya kawo maki yar matar da tayi maki zagin wulakanci  a saman hanya.
   Wallahi da nice ba zan ko kalli inda yarinyar nan take ba balle ya bar min ita da sunan lalashi duk wanan abin fa sallon  ba da hakkuri ne irin na maza.
  Shi a dole matar shi ta saba maki ya wani dauko yarta ya kawo maki nan don ya nuna maki ya isa da gidan shi ko may ?
   Dariya nayi nace ke ma kin san in dai wanan mutumin ne ba zai taba bani hakkuri ba bakina da nashi ba kuma kawo min yarinyar yayi ba nan .
  Sun zo da itane tagani ta lakemin taki yarda su tafi da ita shine yabar ta har anjima zai zo wai ya dauke ta yace .
  Tace bakin ji ba may ye na kawo maki ya kina makaranta kina fama da karatun ki ni dai nasan akwai wani abu a bayan wanan abin.
  Tashin da yarinyar tayi ne tana kuka hankali na ya tashi na rarashe ta tea na hada mata tare da bata cup cake sai tayi shiru taci gaba da wasan ta.
   Sai bayan magariba ya dawo daukan yarinyar ya bugo layina yana fadin gashi ya dawo in fito da yarinyar ya mayar da ita gida.
  Tun daga nesa ya kura muna ido yana kallon mu cikin mamaki yadda yarinyar batai min kiuya ba har muka iso gurin tana ganin shi ta washe baki tana dariya.
  Sai dai yana tara hannu tazo ta make tare da lafewa saman kafaduna ban san lokacin da murmushi ya subce min ba yace Banan yau fushi kike damu ne a gidan haka ?
  Nace kasan yaro kamar kyanwa yake yana son a kyautata mashi ko da yaushe indai zai samu jiki gurin mutum .
   Wanan ne kuma bata samu a gurin mu daga ni har uwar ba mazauna gida bane dukkan mu nace kuna daukan alhakin ta gashi babu ruwan ta wallahi.
  Dan shafan ta da nakeyi daga tsaye yasa ta koma barci nace kaga tayi barci yanzu lalaba ka maida ita wurin uwar ta tun kan ta tashi tasa rikici.
  Banji yace komai ba haka yasa na dago ido ina kallon shi sai naga yana wani lumshe ido yana kallon mu.
  Da sauri na kawar da kai daga kallon shi kamar bangan shi ba muryan shi naji yana fadin .
   Kun dace da Banan kamar kece uwar ta kenan goyo zai maki kyau sosai fa nace don Allah kakai yarinyar nan gida tun bata tashi tasa rikici ba.
   Yace af koran mu kike yi don na fadi gaskiya gaskiya kuma da kama da ita kamar kece mahaifiyar ta fa.
  Nace kaidai ka sani da jan magana a bayan idon uwar ta zaka iya fadin komai yanzu .
  Tsoron idon uwarta nake ashe nace ai naga zahiri ne ranan don Allah ka karbe don hannuna ya fara tsami da daukan ta.
   Miko jikin shi yayi don ya dauki yarinyar numfashin mu ne ya hade a guri daya nayi saurin ja da baya jikina yana rawa rigumay ta yayi a jikin shi yana fadin Thanks for today Banan da baban ta sun gode.
   Yana kallon kan yarinyar da ya sha kitso fuskanta ya fito shar da goshin ta saboda kitson da akai mata din yace wayayi mata wanan kitso haka nace gun wa ka kawo ta.
  Matsala na dake kenan tambaya a cikin tambaya halin ku na yan Africa leda na miko mai ciki da kayan ciye ciye nace a rika mata wanan idan ta tashi yai min godiya muka rabu yana cikin farin ciki da ya kasa boye wa.
   Sai da ya wuce a zuciyana nace ko yaya akayi yazo da wanan yarinyar nan yanzu kuma may zai koma ya fada mata kai halin maza sai su wallahi maganan maryam ne ya dawo min a raina.
   
Ya na isa gida suna waje bakin get cirko cirko dasu sai da ya gama seta kan sa ya fito da yarinyar a kafadan shi.
     Gaba daya suka nufo inda yake nafisa ta mika hannu zata karbi yarinyar ya gwauce ya wuce ta ba tare da yayi mata magana ba.
  Sai da ya kwantar da yarinyar dake barci a saman gado ya juyo zai wuce ta tace ashe kaine kafita da yarinyar nan baka fada muna ba.
  Ke ki fita min a ido banson maganan banza har kina da bakin tambaya na haka da kikasa kafa kikabar ta agidan tana kuka iidan wani abu ya samay ta fa.
  Wallahi kasan su Yanyala na barwa ita amma sai suka bugo min waya suna fada min wai basu ganta ba.
  Yace bari kiji akan yarinyar nan zan iya bata muku rai baki daya a gidan nan duk sanda kuka bari haka ya kara faruwa.
   Kitson dake kan yarinyar dake barci saman gado take kallo muryan ta ne take tambayan shi a wurin mace kakai ta ke nan wani kallo yayi mata sai lokacin ya tuna da zata iya tambayan shi haka.
  Kallon yarinyar yayi da take a kwance shar kamar zaiyi magana sai kuma yaja kafar shi ya wuce zuwa dakin shi.
  Zuciyar shi a cunkushe yana jin bacin rai wanka yayi ya fito ya shirya gado ya koma ya kwanta da niyar taba aiki a laptop din shi .
  Amma sai yasamu kan shi da jin kasala nan ya fara tunane abinda na fada masu yau tunane ya zurfafa dayi sosai har zuwa daukan yarinyar daje yi da yamman nan.
   Ido ya lumshe yana tuna irin yanayin dayaji lokacin da muke hada jiki wurin amsan yarinyar yace a fili khadija khadija yana girgiza kai a hankali.
   Bude idon shine yaga Nafisa tsaye tana mashi kallon tuhuma dakyat ta iya daga kafa zuwa wurin da yake kwance tace yaya naga yanayin ka gaba daya ya sauya ne ?
  Samad ina kakai min yarinya yau wuni guda ace batai kuka ba nifa wanan abin ya daure min kai.
   Gun wa kakai ta baka fada min ba yace muna gidan Yusuf da ita muna aiki shiyasa kika ga ban damu da kiran da kike min ba din tunda nasan yarinyar na wuri na.
   Wani irin ajiyan zuciya ta sauke tare da zama a bakin gadon tana fadin sai yanzu hankalina ya kwanta wallahi.
   Gobe da safe zan bar gidan nan zamu je gyara ma amarya gida juyowa yayi yana kallon ta tare da tambayan ta wai a wakike cikin wanan bukin ne don naga kin mayar dashi kamar bukin gidan ku .
  Ga buki can za a yi a kaduna amma banji kina shirin zuwa ba sai wanan bukin da baki da wani dalili dashi kike maganan shi haka.
  Tace bukin wa za ayi a kaduna din idan ma na sani bazan tafi ba wanan kai ya shafa don ni bai shafe ni ba yace haka kika ce tace kwarai kuwa.
 Gyara kwanciyan shi yayi ya bata baya tace don kawai za ai bukin kannen Fati zan kwashi kafana in je don ban san ciwon kaina ba ko may ?
  Mutanen da basu sona basu kauna na basuki su bude ido suji ance na mutu ba a yau din nan kake son in kusance su.
 Ban son Fati ban kaunan ta da duk wani nata don su, , , enough Nafisa ya ishe ki ya isa haka baki zuwa ya isa wanan kalamin ba da Fati kikeyi ba dani kike yi don nima zurian gidan ne ko kin manta ne da hakan ?
  A kusan tsatso daya muka fito da Fatin da kike aibantawa haka da yan uwan ta may Fati ta tare maki a duniyan nan da baki kaunar ta haka saboda wani bakin kishi naki can mara dalili.
Matan nan tun shigowan ki gidan nan kika dauki tsanar duniya kika dagwara mata katse shi tayi da fadin muka dai dagwara mata don bani kadai takewa abinda takeyi ba.
 Yace matsalan ki daban nawa daban ko may Fati tayi min nimijin tane kuma uban diyan ta zan zauna da ita a ko wani irin hali.
  Samad ni kake fada ma kai mijin Fati ne kuma uban diyan ta kake ni kake fadawa haka a gaba  yace an fada maki kiyi abinda zakiyi.
  Wani shuumi murmushi ta sauke tace dama maza haka kuke don kana takama da wanan dandanin da taima shine har kake ganin ta a mace take yanzu.
  Kutawa tayi tafita daga dakin rai a bace ita samad zai kawo wa wani maganan wata matar shi can wai fati wai may yasa shirin ta akoda yaushe yake lalacewa ne idan tayi.
  Tasan dai tanayi amma kuma maimakon yayi aiki yadda take so sai komai yazo ya lalace daga baya taki jinin fati da diyan ta a duniyan nan amma mace kamar kaska duk wanan abinda takeyi sai fatin ta dawo a rayuwan samad din.
   Tana ganin taje gida tayi aiki akan kowa nashi amma kuma yanzu ta lura asiri bai cika kama samad din ba idan tayi ko tayi bai wani dadewa yana tasiri a jikin shi sai abin ya kare.
  Kudi dai bata da matsalan shi ko nawane ta bukata tana samu a gurin samad din yanzu abinda tafi zargi shine mahaifiyar shi take lalata mata aikin ta don haka wanan karon da hajiya mama zata kara don na samad din mai sauki ne.
  Don ko yanzu a tafin hannun ta yake don dai sai abinda tace dashi a gidan bai musa mata inba wani lokaci da yakan dan turza mata ba wai shi a dole ga namiji.
   Tasha alwashin wanan karon sai taga bayan duk wani mai mata aiki ta bayan fage akan samad din zata raba shi da kowa nasa taga yarda uwan nashi zatayi.
  Da haka barci ya dauke ta tana rungumay da yar diyar ta mumunan mafalkin da tayine ya falkan da ita sai gumi take hadawa a dakin duk da sanyin ac dake dakin alokacin.
  Wacece wanan macen da tayi mafalki da ita samad din ta ya rike ma hannu yara na binsu a baya kodai don ta kwanta da zancen Fati ne a ranta tayi wana mafalkin haka.
  Mace tare da samad din ta kaita kada tana fadin wanan ba gaskiya bane koma may ne gobe zata je wurin malamin ta a duba mata agani.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
            SEENABU
Ganin zamu dan huta har kwanaki yasa na yanke shawaran zuwa kaduna wurin Ya Amina in masu hutun dan break din da muka samu a can.
   Bayan mun fito daga lectures ne na shigo na fara shirin tafiya kaduna maryam ma da tasa rai a gidan su zamu yi dan break din sai ganin ina shiri takeyi ta tambaye ni nake cewa kaduna zan tafi in duba ya Amina kin san hutun nan ban samu zuwa can ba.
  Ranta ya baci amma na bata hakkuri akan wani lokaci ai zan tafi nayi Sa,a ina zuwa na samu mota ta cika saura mutum biyu.
   Bamu dade ba motar ta bar tashan motar na da gudu sosai sai dai muna wuce maraba mun dan ba kauyen dage gaba baya kadan motar tamu ta tsaya.
   Drivern yayi tsaki yana fitowa daga motar ya fita ya bude gaban motan ya dan taba ya dawo ya tayar taki tashi bude motar yayi yace mu fita daga waje mu sha iska zai duba motar.
  Abu wasa wasa muna wurin har hudu na yamma motar bata gyaru ba raina duk ya baci nayi tunane kala kala a wurin tsaye.
  Wasu motoci ne guda uku tafe a jere da gudu suka wulga a gaban mu, ina jin mutanen dake cikin motar suna fadin kai jama,a akwai dai motoci a duniyan nan hadadu wallahi duba motocin nan kamar su suka kera kan su don Allah.
  Kuran motan da suke magana akai nabi da kallo sai naga motan suna dawowa baya a hankali zuwa inda muke kawar da ido na nayi daga kallon su na mayar da hankali na ga waya.
  Muna charting da maryam ina fada mata abinda ya faru damu a hanyar jin muryan masu hiran nayi suna fadin wai Allah yaba wasu duniya duba mutanen cikin motar nan don Allah.
  Daidai nan na dago ido na in ga abinda suke magana akai Yusuf ne yake kokarin fitowa daga motar tare da AA a daidai inda sukai parking yana kallon mu.
  Yi nayi kamar ban gansu ba na dukar da kaina a kasa ina ba maryam amsa ya karaso yana gaida mutane tare da sallama suka amsa mai a mutunce suma don yadda yazo masu din.
  Bayan ya gaisa dasu ne yake tambayan driver motar ce ta samu matsala yace wallahi Alhaji lafiya kalau kuma na fito da ita halin karfe ne kawai.
  Wurina ya mayar da hankalinshi yana fadin khadija ina zaki haka a wanan lokacin bamu sani ba kuma ?
  Ko kaina ban daga na kalle shi ba nace KD a takaice wata mata da muke mota daya ta dan manyanta matar dama akwai zuba don bakin ta bai huta ba tunda muka tsaya din.
  Sai cewa tayi malam hala matar ka ce matar oga nane gashi can a cikin mota zaune tace haba.
  Tun shigowan mu nasan yarinyar nan diyar manya ne ko kuma matar wani babba dama ina mamakin abinda ya shigo da ita motar hanya yanayin ta kawai ya nuna min haka.
   Dago kai nayi ina kallon matar da mamaki karara a fuskana zan yi magana tace in kina ma Allah kiyi hakkuri kibi mijin ki yarinyar nan kila shiya sa motar tamu tsayawa haka nata tashi ba kin ko san girman tashi (yaji)ga diya mace wurin Allah.
   Aiko jin haka sauran mutanen suka sa muna baki a lokaci daya ga abin dariya abin kuma haushi har da drivern suna ta bani hakkuri.
   Drivern da kan shi ya dauko jakkata wanda dan karamin traveling bag ne na saka kaya na a ciki dama, driver ya dauka yakai wurin motar tasu.
  Hannu Yusuf yasa a aljihun shi yaciro kudi yaba duk mutanen dake wurin dubu bibiyu wai su shiga wani mota su tafi.
  Godiya sosai sukai mashi suna kara min nasiha akan hakkurin aure anan kan dariya saida ya subce min a fuska na.
  Bude min baya yayi wai in shi ga naja na tsaya a wuri daya bakin motar tare da fadin kada ka manta na fada ma bazan sake shiga motar ku ba again.
  Haba khadija ai ko don idon mutane nan da nayi wa karya ki daure ki shiga ji yadda matan nan ke hada ki da Allah tana  fada maki yaji fa baida kyau ga mace .
  Wa nayiwa yaji din ai gara su san gaskiya tinda ban san inda zan kara haduwa dasu ba yanzu idan mun rabu don haka please sauke min kaya na in tare wani motar in tafi.
   Don gidan mu a motar haya muka saba tafiya tunda bamu da motar yace please kanwa na kada mu tsaya jayayya anan kiyi hakkuri don girman Allah mu tafi yamma keyi yanzu hanyan kuma babu kyau kin sani.
 Girman Allah da ya ambata ne yasa na shiga motar ba tare da nayi wani magana ba kuma sanyi da kamshin motar ne suka daki fuska na a lokaci daya.
   Kira, a ke tashi a cikin motar a hankali muna shiga sauran motocin suma suka tashi muka kama hanyar kaduna ga yamma yayi.
  Sai da muka danyi nisa da tafiya yace kin daiji abinda manyan mata suka fada maki fushi baida kyau khadija don ko wanan tafiyan ya ishe ki ki gane mu da alheri muke bin ki khadija.
  Sai yanzu AA yayi magana da cewa ke kina haukane ko rashin sanin ciwon kai ne yakai ki bin motar haya cikin wa yan nan mutane haka masu yawa.
   Idan wani abu yaje ya samay ki a cikin jejin nan fa kina son ki salwantar da rayuwan ki ne a banza ko may ?
  Tunda ya fara magana ban dago kai na kalle shi ba kaina yana a wayata sai da naji ya fadi hakane na dago kaina nace a tsiwace .
  In salwantar da kaina kamar yaya don kawai nabi motar haya zan salwantar da rayuwana yace a zurke yana kallona.
                May yakai ki shiga motar haya a wanan hanyar ?
   Nace ai kasan ubana tallakane ko banda motar da zan shiga inwa  mutane tsiwa asan ina dashi, don banda motar  ya wuce ta haya a yanzu don kowa yasan ubana ban kwadayin karaya ko abin wani a rayuwa.
  Wani kallo ya watso min daga inda yake zaune ya kada kai ya koma ya zauna yana maida numfashi.
   Yusuf ne yace kaunata kin san kowa ke din mai tsada ce a yanzu don Allah kibar wanan gangancin da rayuwan ki murmushi nayi nace ganganci kai nama rasa may zance dasu alokacin.
   Gudu suke shararawa da mu sai can ya juyo kamar mai maganar lalama yana fuskantana yace kina jina daga yau duk inda zaki ki buga ma Yusuf waya a turo maki mota bana son shiga irin wa yan nan motocin please I hope you understand me ?
  Malam bafa don na shiga motar ku bane yanzu zaisa ka dinga bani commad son ranka ina dai nike da rayuwana bawani ba.
  Ya ce haka kika ce nace kwarai kuwa don may zan ka so takura min kamar wani wanda ya ajeni can a gidan shi.
  Ya juyo ya kara fuskantana yace haka kike so kiga an adanaki a gida ko sanan zaki bi maganan da ake fada maki na kula da kan ki ?
  Nace haka din ne ai shiya na fada haka kawai ba matar aure nake ba zaka wani kafa min doka kamar wace ke karkashin wani.
   Yusuf yace kai kanwa ta ba kayau ne haka yasa kikaji ana maki magana kada ki dauki zancen da zafi mana.
  Yace barta ai ka santa da bakin tsiya wanan bakin naki ya kai karshen  tsiwan sa daga yau zaki kula kisan abin fadawa mutum.
  Wai ma may zaki je kaduna a wanan lokacin haka kuna karatu ko kin fara wasa da karatun ki ne yanzu ?
  Nace kai wanan ya dama ni gurin yar uwata zanje in dubata karatu kuma nike da abina ba wani ba.
  Murmushi yayi yace yarinyar nan ina tausayawa ranan da bakin nan naki zai dinke ya koma shiru wallahi kaina na kawar wanan karon ban biye mashi ba ya koma ya jingina da kujara ya dafe kan shi da hannun shi daya.
  Sai Yusuf ne ke dan jana da hira jefi jefi ban bashi amsa sosai sunyi sayayya a hanya sai ba a wani dade ba sai gamu mun shigo garin kadauna garin gwauna.
  Lokacin duhun yamma ya fara a yi sosai nace ku sauke ni in karasa a motar haya wani irin kallo ya watso min daga inda yake zaune yace saboda kin saba shiga motar hanya baki mai dashi komai ba ko ?
  Koda muka shigo layin mu har an fara kira a wasu wurare na magariba daidai get din gidan Ya Amina Yusuf ya tsaya da motan da muke ciki na fito tare da fadin yayana na gode sai da safe.
   Ki gaida sister idan kin shiga kice muna mata yaya jikin kafin mu shigo gaida ita zataji kawai nace dasu na dauki jakata na nufi ciki.
  Sai dai may daga get din har ciki a rufe na gansu waya na ciro ina kiran ta har ya katse ba a dauka ba nan dai na sake kira karo na biyu yana gab da katsewa ne aka daga wayan nace.
  Ya Amina kina ina nazo gida ban samay ku ba gida a rufe khadija ce nace eh don ba muryan ta naji ba a wayan.
  Tace mommy ce Amina tana gidan mu sallah take yi nace ok ina wuni mommy tace lafiya kalau yaya hanya nace Alhamdullahi mommy.
  Na kashe wayan don ban son dogon magana da ita nasan dai tunda mommy tasan nazo kamar Ya Amina taji ne na zo din.
   Na dan jima a tsaye sai can na hangota da saurin ta tana fadin ke tafiya haka babu sanarwa ashe kina hanya ne ?
   Don Allah bude min gida ni fitsari ya damay ni tun a mota nake jin shi wallahi tace kika ki magana a tsaya maki kiyi  haka fa na jawo matsala ga mata.
  Tsuki nayi lokacin da ta bude gidan na fada da sallama a bakina ban tsaya ba na aje jakka kawai na fada ban daki da sauri.
 Har da alwala na dauro kafin in fito na zo falo na tayar da sallah don bata cikin falon a lokacin ban daga gurin ba sai da na gabatar da ishai.
   Wayana ake kira na dauka maryam ne take tambaya na yaya hanya kuma mun isa kd din nace mun iso yanzu tace an gyara motar ne nace ina fa ke dai bari maryam.
   Muna wurin ana gyara motar ba sai ga dan fitinar ga ba mai shegen izzan tsiya tace wa nace wa kika sani ni wallahi da nasan yau zai shigo kaduna ne da ban zo ba wallahi.
   Wai kina nufin su AA wallahi maryam su muna tsaye a jejin nan da na fada maki sai kawai ganin su nayi daga sama kamar a mafalki a gurin.
   Fitowa yaya Amina daga dakine yasa nace ma maryam ta bari idan na huta zan kirata muyi magana,  muryan Ya Amina ne naji tana tambayana mota ce ta baku wahala a hanya.
  Nace bari ya Amina banji dadin wanan tafiya ba yau don dai kawai na kwallafa son ganin ku ne nayi shi dana koma wallahi.
  Gashi ko abinci ban tsaya nayi ba na ranane na rage wa yara don mun shiga gidan su mommy kin san ana buki a gidan nace buki kuma ina suka samu buki ?
   Tace a, a kin san ai da gidan su da gidan su Fati matar Abdulsamad kamar Family daya ne kannen ita fati din ke aure ai.
  A raina nace no warder ashe shi yasa mutanen nan nan suka zo garin ashe buki suke yi gaskiya naga an shake mota da kaya haka ?
  May zakici yanzu in dafa maki ko in shiga aurin mommy in karbo maki abinci don ni naci ko acan tun dazu.
  Nace barshi ko tea ne zan sha idan na watsa ma jikina ruwa zan kwanta muna wurin zaune muna hira sai mukaji sallama.
  Binta ce da zainab da wasu kawayen su biyu da ban san su ba suna dauke da basket din abinci a hannun su.
  Da ihu Binta ta karaso inda nake ta rungumay ni tana fadin wallahi khadija Adamu nafi kowa farin cikin zuwan nan naki ko kema dama kin san da zancen bukin ne wai ?
  Nace cikin fara,a wallahi bansan da zancen wani buki ba zuwa nayi duban ya Amina na kawai don nayi kewan ta da yarana.
  Aiko wallahi kinzo a sa,a don akwai casu wallahi nace ke har yanzu baki daina maganan wani casu ba can  tace ba dole ba mutumiyar fa za aiwa engament jibi .
  Da sauri nace wa kenan kuma ta nuna min zainab tana fadin gatanan a gaban ki kuwa wallahi wayo take son muna nidake.
   Kallo na mayar ga zainab din dake zaune tana faman taba wayan ta nace wai da gaske ne ko sherin Binta ne kawai dayar yarinyar tace da gaske ne wallahi.
  Dan ihu nayi nace amma zainab kin bani mamaki ashe da Allah bai kawo ni ba da saidai inji labari.
   Tace a wani yanayi ba haka bane khadija nima ban dauka a yanzu za, ayi abin ba na dauka ko da sauran time ne shiyasa ban fada ma kowa zancen ba.
  Ta fada cikin izza da yanga sai yau nake ganin mugun kamar su da yayan nata komai nasu iri dayana sosai sunfi dauka kamanni da mahaifinsu fiye da kowa a gidan.
  Nayi murna kwarai sai can na kallo ta nace wai waye wanan lucky guy din da ya iya sace zuciyar wanan yar kwalisan yarinyar haka a lokaci daya.
   Binta ne ta bani amsa da fadin ina guy fin nan abokin yayan mu da always Suna tare da yayan mu Abdulsamad mijin buzuwa din nan wanda ake ce Yusuf.
   Shine ya sace zuciyar wanan mai zurfin cikin tsiyan da kike gani nima da muke daki daya da ita ban taba sanin wanan labarin ba sai da abin yanuna ya fashe naji.
  Kin san matar shi ta rasune a wurin haihuwa shakara biyar da ya wuce shine bai yi wani aure har yanzu ashe rabon zainab ta shiga gidan shi ne ya kashe matar .
  Harara zainab din ta aika mata na ki kama kan ki dinan nace amma zainab kinyi dace da mutumin kirki dan arziki daya san mutuncin mutane.
  Binta tace kin san shi khadija da kike fadin haka wallahi kin canka daidai kuwa don har yau ban taba jin wani hali nashi na assha ba da aka fadi.
  Na dafa zainab din ina fadin yar uwa ina tayaki murna da wanan babban kamu da Allah yayi maki muma Allah ya kaimu ga danshin ki.
  Zainab tana murmushi tace baki dai so bane khadija da tuni wani yayi wuf dake wanan zubin naki sai kace wata halfcas dake wani namiji zai ganki ya kau da ido gurine kawai maza basu samu ba.
   Kiba da dama yanzu ki gani in bakiga layi a kofan gidan nan ba har ba iyaka na maza a kofan gidan nace ba zasu samu ba yanzu zainab baki ba dai in nan gaba na kammal karatuna na fara aiki ko shi sai kila.
   Ya Amina da tunda muka fara magana baita magana ba sai yanzu tace yarinya in tunanen ki ke nan ki canza don baba a jirace yake dake wallahi.
  Nace Ya Amina baba ai yafi kowa sanin matsalana karatune burina inga na zama babban lauya wata rana Binta tace wai da mun sha dauri wallahi.
 Nace kamar ko kin sani don da na gida zan fara sharia na kada ma kiji wai binta ki rike dakayau a ranki.
   Zainab tace kinga mun kama zuba kamar ba gobe ga abincin nan mommy tace mu kawo maki a gurin ta ma muke jin zuwan naki yanzu.
   Daga inda Ya Amina take zaune tace wai mommy dai bata gajiya yanzun fa muke maganan abincin nan kamar ta sani sai gashi ta aiko muna dashi.
  Mommy ai tafi danan wallahi inji dayar yarinyar ta fada kowa yace wallahi halin mommy ai yayi ne sosai.
  Basu jima ba sukai muna sallama akan gobe zamu hadu sai mu kara tatauna abinda za a yi nace dana san da wanan zance ai da tare muka zo da maryam.
  Binta tace Allah sarki ban tambaye ki maryam din ba nace tana can na barta tace gobe ita ma gida zata tunda na wuce na barta.
  Har bakin get na rako su suka tafi na dawo ciki a inda na bar ya Amina zaune a nan na samay ta nace wai ina yaran suka tafi ne tace suna can gidan kakannin su zasu kwana masu biyu.
  Ban san zaki zo ba aida ban kai su can ba don in samu yadda nake so ne yasa nakai su can inji dadin shiga mutane babu takura.
   Wanka na shiga na fito na saka wani dogon riga a jikina na shan iska mai dan karamin hannun yadin rigar baida kauri sosai falo na dawo na samu ya Amina tana kallo.
   Zama nayi ina jawo kulan abincin da mommy ta aiko min dashi nayi mamakin ganin abincin haka kamar na wata hamshakiya.
 Ban san lokacin da nace wai mommy irin wanan hadin haka wallahi ni har kunyar matar nake ji Allah kuwa.
  Dariya Ya Amina tayi min tace ko har kun fara sarakutane da ita ban sani ba nace wa zata bani cikin diyan ta haka dai kawai nake jin nauyin ta yanzu.
   Wai ni ina Abdulsamad ne ina zancen ku ya kwana dashi ne tun lokacin ban kara jin labarin ba ko da yake yanzu kin fi zama minna ai.
   Tsuki nayi ina zama kasa nace ina ruwa na da wanan miskilin mutum da bai san darajan mutane ba halin su au daya da matar shi shiyasa nasu yazo daya da ita.
  A,a wallahi baki ko fahince shi ba khadija Abdulsamad mutum ne wallahi mai mutunci da sanin ya kamata  ke dai kice Allah ya hada shi da yar banza mata ne mara mutunci kwanaki fa har gari nan tazo taci ma iyayyen shi da matar shi mutunci.
  Don Allah ya Amina abinci zan ci kada ki fada min maganan haushin nan ai ita bata da laifi shine mai lefin don ni wallahi da nice Fati da tasha takaici a wurina.
  Don wallahi tsab zan zauna da ita don tun yanzu na karanci iya shegen ta balle fati da suka zauna tare tasan halin ta da komai nata may zata gwada mata.
  Ke dan Allah can kin san aure ne da kike wanan haukan haka auren fa akace maki khadija ba wani abu ba ita mace dama ta gaji ganin haka walau mai kyau walau akasin hakan.
  Abincina naci gaba daci ban taka mata ba ganin nayi shiru itama taja bakin ta tayi shiru tunda ta fahinci ban son zancen .
   Ina gamawa tace min a dakin ta zan kwana tunda ita kadai ne a gidan kuma ba a gyara dakin nawa ba don bata san ina tafe ba.
 Nace aiko dakin baiyi wani datti ba dan fes na ganshi har da ban dakin tace duk sati ina shiga ina gyarawa don gudun irin haka duk da haka ki bari sai gobe idan an gyara ki kwana a ciki.
  Bayan nagama don naci abincin sosai na kwashe kayan zuwa kitchen daki na koma nayi shirin kwanciya wayana kawai na dauka da hijabin da zanyi sallah da safe na fito xuwa dakin ya Aminan.
  Na samu ta shiga wanka haka yasa na kwanta abina don dakin ba bako na bane wayana kunna na bude data sakone ya dinga shigo min daga ciki biyu kawai na duba na farko sokon mamud ne yana tambayana karatu.
  Sai kuma karshe da yake ce min ya matsu in gama muyi aure in haifa mai yara masu kama dani yana yawo dasu a mota a gari.
  Tsuki naja ina fadin baka da hankali mamud nice zan shiga ma ta uku gida don na rako matan duniya komay ?
    Sai sakon maryam tana fadin hostel din ba dadi dana tafi don haka gobe gida zata tunda safe duk da tasan yayan ta basu gari da mijin ta.
  Zatai zamane na kadaici koda taje amma yafi mata zama a hostel bani amsa na bata nace niko kinga nazo na samu ana buki anan har da engement din zainab da Yusuf alama murna ta nuno min tace yaushe ne bukin nace mata sturday idan Allah ya kai mu.
   Gobe zaki ganni tace kai maryam da gaske tace insha Allah ko naje gida Anty basu kasan suna waje da mijin ta ai gara inzo inda kike muyi hutun tare.
 Mukai sallama ina murna har ya Amina ta fito ta samay ni hakana nake fada mata gobe maryam zata zo tace ashe ina da bakuwa gobe a gidan kin ga sai kin min list din abinda take ci a sayo maku kada tazo nan ta takura.
  Dariya nayi nace da kin hutar da kanki don maryam suna masu kudi ne kawai amma bata da matsalan komai wallahi komai da kika san muna ci tana son shi.
  Allah ya kawo ta lafiya nace amin daga haka had barci ya dauke ni nayi mafalkin ga mutane sun taru ina kuka haka yasa na kasa barci har safe nakai a hakan.
   Haka na tashi da safe a cikin damuwa ina tsoron in fadi wani abu mumuna ya faru dani da gari ya karasa wayewa nace da anty zan fita bakin titi in ba da sadaka.
  Bata tsaya tambaya na ba na fita zuwa titin in da nayi saa na hadu da wata mata mabukayi tana neman abinda zataci da yaran ta na bata dubu biyu tana min addua na juyo zuwa gida.
  Ban yi nisa ba ina karyo kwanan unguwar mu tun daga nesa na gane A A tafe a cikin kayan motsa jiki yana judging shi da su mutum biyu a bayan shi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *