MISBAH CHAPTER 7 BY SA’ADATU WAZIRI

MISBAH CHAPTER 7 BY SA’ADATU WAZIRI

Www.bankinhausanovels.com.ng 

Tunda sassafe farida ta bugawa deeni waya,daga jin muryarsa tasan ba lafia ba ,hankalinta yai mummunan tashi,kawai sai ta fashe mishi da kuka ,muryarta na rawa tace .

    “”Deeni ya zamuyi ? Dama abinda nake tsoro kenn kullum ,kasan babanka ba zai yarda ba ,haka abbana ba mai canja masa ra’ayi,bazai taba bari na in zauna injiraka ba ,hada ni aure zaiyi da koma waye “”

” cikin muryar rauni da matujar tashin hanklai yace 

   “”Saurareni farida, baki da wani miji sai in Nsha Allah,Allah ne ya hadamu ba mai rabamu . Inma baba yaki nizanje in sami yayana babana,Bappah na zaj daura mana aure ,ba dai abbanki zai aura min ke ba ?

 Abbanki zai aura min ke ,in har nabturo waliyyi na zai daura mana aure . Anjima kadan ,zan fita,zan wuce gombe ,zan je in sami bappah na ,kafin in wuce inason ganinki,ki fito kofar gida mu hadu”

 Nan ra amsa masa da toh,ta ajiye wayar .

 Bai bata lokaci ba yayi wanka ya kimtsa,ko breakfast bai tsaya yi ba ,ya cewa mama shi ya fita. Ko kallon mahaifinsa baiyi ba balle ya gaishe shi.

Tsawa ya daka masa tare da kiran sunansa.

  Cak deenin ya tsaya ,sai dai ko juyowa bai yi ba balle ya yi niyyar zuwa inda yake.

    Alhaji yace ,ban haifi dan da gari zai yawaye yana kallona ya wuce bai gaisheni ba,baka isa ba .” 

Jin hakan yasa deeni ya juyo ya kalleshi fuska ba walwala ya ce .

      ” Ina kwana ? Da fatan ka wayi gari lafia “”?

 Bai saurari amsar mahaifin nasa ba yasakai ya fita ,mahaifin nashi ya bishi da kallo. Baiyi mamakin hakan ba,sabida yasan halin deeni ,sai dai fa duk abinda zaiyi yi dan baazaiyi aure yanzu ba da  bai san ciwon kansa ba ,yayi haukansa ya gama .

   

“”Ina kaunarka dana ,,shiyasa nake son yiwa rayuwarka gata kafin in kai ga maka aure,,sai na maidaka mutum sosai,,mace kowa zaka sani kowacce iri kakeso a rayuwa ” 

          Mahaifiyar deeni ce ta shigo tare da matsowa inda yake , ta tsake masa tunanin da fadin “

     Alhaji bazaka sake duva maganata ba kuwa ? 

       Ka auna irin soyayyar da rayan nan suke yiwa juna , karfa ka illata rayuwarsu sabida wani dalili naka na daban . Sannan yarinuar nan ya kakeso tayi ? Dukkna tsawon rayuwarta bata da wani wanda take saurara in ba deeni ba ,kanaso ace deeni ya yaudareta ya rabata dawasu mazan kuma shi be aure ta ba ? 

     Ya dago udo ya kalleta yace ,

 In bazaki gaji da maganar nan ba ,to nima bazan gaji da fada miki a’a ba ,sabida bazan biye miki inbata rayuwar dana ba . Inshi bashi da hankali yakamata ace ke kina dashi .

   ” Alhaji a duba yarinyar nan,ita kuma meye laifinta a ciki don taso danmu,jininmu ,sai mu hukuntata akanshi ? So kake mahaifinta ya hadata da duk wanda ya samu ? Farida kamar diyarmu ce,bazamuso ta shiga gidan wani can da bata san halinsa ba ..””

      ” wannan ne damuwarki ?

   ,” duka”” ta amsa  masa .

” Saboda deeni yanason yarinyar nan fiye da tunaninka ,haka ba jima da saka burin farida tazama surikata ,uwar jikoki na . Na tabbatar da zanyi alfahati da ita ,duk inda akeson mace ta gari ,yarinyar nan ta kai “”

   “”.  To shikenn naji ,karki damu indai wannan ne damuwarki “”

     Ta kalleshi cukin murna sa doki tace ,,kana nufin ka amince ?   

    ” ki saurara ,ki sa ido kiga hukuncin da zanyj ,,ba zan bata rayuwar kowa ba “

 Yana gama fadi ya mike ya nufi dining table ,ta bishi da kallo tana nazarin kalamansa.

     Kawarai hakan ya mata dadi ,saboda akwai alamun nasara . Da murna ta mike ta bishi tana murmushi ba tare da takara ce mishi komai ba ,sai kokarin masa hidima . 

      Denni na fita kai tsaye ya wuce gidansu farida ,a kofar gida suka hadu dukkansu hankalinsu a tashe ,,farida idanunta jawur tana ta zabgar kuka tamkar wadda akace iyayenta syn rasu. Hakan ya mummunan daga hankalin deeni ,soyayyarta ya dinga ji yana ratsa shi,yaji tankar ya jawota jikinsa ya rumgumeta ,sai dai bashi da ikon yin hakan ,don hakan sai yayi abinda yasan zai iya ya hau lallashinta tare da bata karfin gwiwa cewa ba gudu ba ja da baya yana tare da ita ,alkawarin da ya mata na aure ba fashi ,yana tare da ita.

 Ta kalleshi idanu jawur sun kimbura ,ta ce 

     “”Deeni ina zan saka raina in na rasa ka ?

  ” ya zanyi rayuwar da batare da Deeni ba ?yaya zan soma rayuwa da wanj namiji a rayuwa matsayin miji ba Deeni ba ??

 Nan yayi saurin rufe mata baki ,idanunsa suka kada,ya dinga jin wani irin zafi da radadi a zuciyarsa.

   ” karki kara furta haka farida ,karki sake ambatun rayuwa da wani namiji a rayuwarki. Kinajin zan iya numfashi in ganki kina rayuwa da wani ? Farida duk runtsi,duk wuya ,duk dadi ,munabtare da junan mu. Ni ne mijinki abokin rayuwarki,in Allah ya yarda zan mutu in na budi ido naga kin auri wani namiji “””

 Hawayene ya gangaro mishi na tausayin kansu duka .

Deeni ,farida ,ku ne da sassafe haka? Lafia kike ta kuka inata magana tun dazu baku.ma san ina gurin ba ?
 A tare suka mai da kallonsu kansa,shamsu ne yayan deeni. Tuni deeni ya fada jikinsa yana kuka.
     ” ya shamsu kaji abin da Abba ya mun ko? Wai bazan auri farida ba ,ya shamsu kasan irin son da nakewa farida,ta yaya zan iya rayuwa babu ita ? 
 Itama faridan tayashi tayi tana kukan tace .
 ” ya shamsu ka taimakemu ,bazan iya auren wani namiji ba sai deeni,ya shamsu zan mutu inba deeni ,”
   Kawai ta durkushe har kasa ta rushe musu da wani irin kuka deeni na tayata . Gaba daya suka zamewa shamsu hoto,ya bude baki yana kallonsu,yana mamaki duk da yasan irin soyayyar datake tsakaninsu ganin su cikin wannan tashin hankalin ya bashi mamaki tare da tausaya musu.
   ” yi hakuri farida ” ya fada cikin muryar lallashi.
      “” ba mai rabaki da deeni insha Allah ,zan taimaka muku , dake da deeni duk kanne na ne ,share hawayenki,mike muyi magaana.” 
      Haya ya dunga sharewa deeni hawayenshi ,yana lallashinsu duka har suka dab fara samun nutsuwa ,anan ya tambayi deeni ya bashi labarin yadda sukayi da mahaifinsu,farida ma ta fada mishi yadda tayi da nata mahaifin ,ta kare zancen da kuka tana cewa “
    Ya shamsu in deeni bai fito ba wlh Abba auramun duk wanda yakeso zaiyi,ni kuma ya shamsu deeni nake so ” ta fashe da kuka .
        ” ya isa farida,naji “
   Ya fada cikin muryar lallashi da tausayawa , a ransa yace ,”soyayya me zafi ta kama zuciyar yan  yara.”
     Ya tausaya musu kwarai,musamman a wannan shekarun irin na su da dukkansu ba mai tunani dai dai,,haka nan duk yadda zaa musu bazasu taba fahimta ba ,sabida sun haifi soyayyarsu tun suna yara
suka tashi da ita ,sukayi ta rainonta ,don haka ravasu da juna ba karamin tashin hankali bane a gare su. Don haka ya kudiri aniyar taimaka musu,sabida a halin yanzu bazasu taba fahimta ba ,abu daya zasu fahimta a aura musu juna,kafin haka ya faru kuwa sai iyayensu sun canja ra’ayinsu ,ko dai baba ya hakura yayiwa deeni aure yanzu,ko kuwa Abban farida ya hakura tabar farida har deeni ya gama karatunshi. Sai dai fa wannan abin yafi komai wahala,don kuwa in duk duniya da abinda ke cikinta zasu taru basu isa su canjawa iyayensu ra’ayi ba.
        A nan ya shamsudden suka yanke shawara da deeni da farida. Cewa zasuje can Gombe su sami Bappan su suyi mishi bayani ,haka zai nemi wani yayanta ya rakashi katsina itama su sami wani yayan mahaifinta wanda in abbanta yaki amincewa shi sai ya daura mata aure da deeni,shima deeni se kanin mahaifinshi ya masa waliyyi, in yaso wurin zama gida da komai zai dauki nauyinsu akansa. 
Nan take murna ta cika zuciyar deeni da farida,har ma suka haskowa juna murmushi,suna yiwa shamsuddenen godiya .
   Kwarai yaji dadin ganinsu cikun farin ciki ,saboda shi dai daga deeni har farida kannen sa ne . 
    Bayan sun sami butsuwar ne ya tambayeta ko Abbanra ya tashi ? Don dana baba ne ya aikeshi ya  ce ya fada masa yau da yamma inbaya komai yana so su hadu,akwai maganar da zasuyi .
   Nab deeni da farida suka kalli juna jikinsu yayi sanyi,deeni ya ce ” maganar rabamu zasuyi ko ?
 Shamsu yace kwantar da hankalinka ,in ma magnar zasuyi ai mun samo mafita ko ? Kasan ko baba beji maganar bappa ba amma dai bappah zai saurare mu ,kuma ya daura maka aure ko ? 
    Farida ma tace ,Abban mu dai najin maganar Bappan mu,amma fa zai yi wuya ya canja masa ra’ayi , sai dai nima zai iya daura min aure “
    Shamsu yace to kun gani ,karku damu,kuyi murmushi”
    Nan suka masa murmushi duka,shima ya musu sannan ya shige ciki ya barsu a gurin a tsaye.
         Deeni ya kalli farida yace, ” Nsha Allah sai na mallake ki masoyiyata ,matsayin matata ta sunnah”. 
Allah ya tabbatar mana deeni,tafada tana kallon sa.
         Yace , farida in yaya shamsu ya fito zamu wuce,inaso ki tuna ki sani ,duk wuya duk rintsi muna tare,farida ke tawa ce kimun alkawari.”” 
       “” ni taka ce har abada ,ni amanarka ce””
    “”Farida nima naki ne har abada “”
   ” Mu tafi ” muryar shamsu sukaji ya fito. 
     Nan ya dinga zolayar farida yana cewa.
 ” mata zankadediyar zan masa a Gombe ,sai ku zama ku biyu ;” 
     Ai kuwa bai ankara ba ya ga tasa masa kuka ,ba shiri ya hau lallashi har ya samu tayi shuru. Yana jinjina soyayyar da suke yiwa juna . Nan ya shige ciki ya fadawa baba sakonsa ,sannan ya ciro motar sa suka kama hanyar Gombe ,farida na tsaye tana kallon su har suka bace .

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *