MY BESTIE’S HUSBAND CHAPTER 3 BY REALFAUZAHTASIU
Www.bankinhausanovels.com.ng
Wani matsiyacin kallo tabisa dashi ya matseta sosai ya cafki hannunta yajata qasa bayan ya kwarawa wutar ruwan dispenser suka sauka qasa tana turjewa tana kaimasa duka baiko saurareta ba ya cillata daki yabita gadon ta zame jikinta na rawa tana wani irin kuka ya qarayin murmushi ya shammaceta ya janyota qasa ta fado rikicaa yabita ya dannan dukansa takeyi tana yaqushinsa shegen qarfine dashi takasa tureshi saima qara luguiguiceta da yakeyi duk ihun da takeyi Masa bai qyaleta ba Saida ya wahalar da ita sosai sannan ya janye tana kuka me tafasa zuciya yayi murmushi tare da shafa gemunsa yace “Qawarki ce ta motsani Kuma ta tsorata shiyasa na hucce akanki ni ai naga hankalinki ma wlh banzaci iyanan kishin naki ya tsayaba aurene dai anriga an daura suna daya kuke amsawa idan Kinga dama ma ki qone gdan babu abinda zaa fasa jahila kawai” ficewa yayi daga bangaren ya shiga daya bangaren kasacewar shima a gyare yake ya haura saman yayi wanka ya dawo yayi kwanciyarsa tunanin Rafi’ah ya dameshi ta dauko wayarsa ya bude hotunan da sukayi dazu kamar masoyan gaske yayi murmushi ya danna numberta ya kirata lkcn Aunty Murja tana dakin tana bata lbrn tujarar da Hajiya Sahura da Ni’imah sukazo sukayi musu abin ya wucce tunaninta shiyasa kukanma ta kasayi Ja’afar ya cucesu ya raba musu zumunci shi ko tsoron Allah ma bayaji kawai burinsa yake cikawa baruwansa da damuwar wani.
+
Kiranne yasasu duban wayar gabadaya ganan an rubuta My Bestie’s husb yasata jan tsaki dubanta Aunty Murja tayi tace “ki daina wannan abun da kikeyi zai iya rabaki da Ubangijinki Allah babu ruwansa da mijin aminiyarki tunda ya qaddara ya zamo mijinki to dole kiyi takatsantsan sosa masa ran da zakiyi ke Kuma Allah saiya sosa naki kinsan kuwa radadin dake cikin ace Allah ya sosa ranka Rafi’ah?” Girgiza Kai tayi Aunty Murja tajata jikinta ta shafa bayanta tace “duk wani farin cikin duniya zai iya hanaki ya hanaki kwanciyar hankali saboda wannan abinda kike rainawa Rafi’ah ki taushi zuciyarki Ja’afar Wakil bazai taba janyewa qudurinsa ba tun kafin kukawo yanzun ma ya kafe balle yanzu da kike amsa sunan matarsa idan kika cika matsawa wahala zakisha”
Kawar da kanta tayi tace “nifa banasonsa ne Aunty banajinsa a ko saman halshena bare zuciyata don Allah ki qyaleni” daquwa tayi Mata tace “kin dade baki tsaneshi ba yanda ya nace Saida kika zama matarsa zai nace saikin soshi har kinyi kishinsa namiji irin mijinki shigarai gareshi wlh namiji me naci tsayawa araine dashi garama kibi a sannu kada kizo kema ki rifta harma ki fishi ruftawa” sake tsuke fuska tayi daidai lkcn da wayar Ni’imah ta shigo gabanta ya fadi ta kalli Aunty Murja itama kallonta tayi tace “daga Mana kiji abinda zatace”
A tsorace ta daga tare dayin sallama bata amsa sallamar ba sai wata uwar ashar data lailayo mata girjin Rafi’ah yabada wani dam ta miqe jikinta na rawa kuka ya balle mata tace “wlh Bestie bantaba son mijinki ba na fada masa yaqi amincewa abinda kikeji nafiki ji ke kishine yake damunki da tunanin naci amanarki nikuwa qiyayyace Ni’imah na tsani mijinki banasonsa wlh bantaba mafarkin kasancewar wannan gwamutsin ba bantaba mafarkin zuwan wannan cukurkudadiyar ranar ba….”
Ashar ta qara danna Mata sai Kuma ta fashe da kuka sukayi Shiru kowacce na kuka abubuwa da yawa na dawo musu can Ni’imah ta zabura tace “wai kece kishiyata matar mijina mijin da kinfi kowa sanin irin son da nakeyi masa Rafi’ah kin yaudareni kun cutar dani keda Ja’afar wlh ko zan mutu saina hanaku jin dadin wannan auren cin amanar gakinan gashi ku zauna nagani muddin Ina raye sai kunyi nadama sai kunsan kunci amanata zaku ganine dagake harshi dagayau zamu fara wasan abun da nakeso ki fara cirewa a ranki shine aminci da zumunci daga wannan ranar na yankeshi har abada kisa aranki zan iya kasheki da hannuna duk inda kika ganni kiyi qoqarin barin gurin donni maqiyiyarki ce ta gaske akan mijina ko kece Sahura uwar data haifeni wlh sai naga bayanki….”
STORY CONTINUES BELOW
Tana gama wannan mgnr ta kashe wayar Rafi’ah ta zube a qasa ta dora hannu akanta ta fashe da kuka tana cewa shikenan abinda nake gudu ya faru Aunty Ni’imah bazata taba fahimtata ba Allah ka fitar dani kasan banida laifi fin qarfina akayi….” Wayarce ta qara daukar ruri Aunty Murja ta dauka ta miqa Mata tace “ki rungumi mijinki aikin gama ya riga ya gama” karba tayi ta kara a kunnenta yayi ajiyar zuciya yace “9 misscall sallah kikeyi ne?” Shassheqar kukanta yaji yaja numfashi yace “it’s ok na gane wato kuka kikeyi ko ayyah sorry fah Kinga da muna tare da na tsotse hawayen na lashe komai Amma Babu komai lkcne banason takurawa Abba ne nifa ban buqatar komai ke kadaice nakeso da zai banike gobe da nafi kowa murna so nake duniya ta shaida da wuri ba laifina bane laifin rabone idan sukaganki da turtsetsen ciki zasu fahimci hakan”
Gabadaya haushi yake bata qara kwantar dakai yayi yace “kinsan me?” Batace masa komai ba yace “wlh inason komanki kedin dama domin Ni akayiki Rafi’ah zan nuna miki asalin so zakiyi alfahari ki godewa Allah da zabin da yayi miki” miqewa Aunty Murja tayi ta fice da hikima da dabara Ja’afar akai baiwar kalami idan yaga dama haka ya rinqa kwantar Mata da hankali duk da bata mgn Amma yasan kalamansa suna shigarta ga yanda taketa ajiyar zuciya.
Numfashi taja yace “Inasonki fiye da rayuwata My Bestie ki kasance cikin aminci 1:30am ki kwanta ki huta akwai ranar rashin baccin batazoba tukunna” kashe wayar yayi taja fasali tana jujjuya tata wayar a hannunta maganganunsa sunata yawo a kwanyarta lumshe idonta tayi tare da dauke qwallar idonta da kalamansa dana matarsa sune suka hadu suka saukar Mata da ciwon Kai ta miqe ta dauro alwala tayi sallar nafila raka’a hudu tayi addu’a me tsayi tana roqon Allah alkhairin wannan aure tace “Allah Kai kace mu roqeka zaka amsa mana tabbas baiwarka ta kasance me kawo duk wani damuwarta gareka Allah na nemi zabin miji a gurinka ka zabamin mijin aminiyata Allah Kai kace Aljannar wadanda sukayi soyayya dominka ma dabance tabbas naso Ni’imah dominka nayi Mata duk wani Abu dominka, Allah Kaine masanin sirrin fili dana boye Kaine kadai kasan dalilin zabamin mijinta a matsayin mijina Ina roqonka ka haskamin alkhairin abin Allah ka ragemin qinsa a zuciyata idan kabarni naci gaba da qinsa bazanyi masa biyayya ba idan banyi Masa biyayya ba bazan hadu dakai cikin aminci ba”
Ta Jima tana hawaye tana fadawa Allah buqatunta tana cikin addu’ar ya kirata bata dagaba daya sake kiranta ta daga jin muryarta wasai yasashi jin dadi yace “kinyimin addu’a?” Shiru tayi yaja fasali yace “ina buqatar addu’arki matata ki roqamin Allah yabani ikon adalci tsakaninku kinji matata?” Jinjina Kai tayi tace “saida safe” wani dadi ya lullubeshi suka aje wayar ta cire rigar da tayi sallah da ita tasa na bacci ta haye gadon tare da addu’ar ta kwanta.
Washegari tunda ta tashi bata sauko qasan ba kuma bata bude wayarta ba har azahar tana sama dake litinin cema azumi takeyi sai a lkcn ta bude wayarta text din Ja’afar kusan biyar bata duba ba kiransa ya shigo kamar karta daga tadai danni zuciyarta ta daga suka gaisa ya tambayeta lfyrta ta amsa yace “ina jiranki a waje” kashe wayarsa yayi tabi wayar da kallo tafi 20 minutes a zaune ya sake kiranta yace “sauri fah nakeyi kina batamin lkc”
A hassale tace “to ka tafi uzurinka mana ko na nemeka ne?” Ransa ne ya baci Ja’afar akwai baqar zuciya yace “ok” kawai ya kashe wayarsa ya juya motarsa ya fice zuciyarsa na tafasa unguwa zashi Amma wannan abinda tayi masa yasashi juyawa ya nufi Fam house nasu tun daga shigowarsa Hajiya fatsum take kallonsa yayi parking ya fito a fusace ya shiga bangaren nata domin tun safe tace tanason ganinsa bai samu fitowa ba sai yanzu yana shiga ta daukesa da mari ya tsaya cak tare da dago kansa a kasalce ya zuba Mata ido yana cije lebansa.
Shaqarsa tayi tace “nice na mareka magaji ko zaka ramane dan iska maci Amana kaikam kayi asara meye laifin yarinyar nan Ni’imah daga aurenku ko wata uku baku cikaba zakayi Mata kishiya kishiyarma aminiyarta wannan debabbiyar yarinyar yar gdan Haj Amina sangartacciya lalatacciya aini bansan lalacewarta takai haka ba wlh da ko zaka mutu bazaka aureta ba…”
Ji yayi daga bayansu an cafe da cewa “wlh Barebari fadawa kowa Shahararriyar yar iskace ta gaban kwatance duk ATBU babu Wanda bansanta ba ke qarewa ma fah Prettyn Lecturori akece mata duk wani lecture daya kwana ya tashi a ATBU yasanta ansha kamata da lectures……” Rintse idonsa yayi cikin qaraji yace “qaryane Dijah wlh qaryane Rafi’ah ba haka takeba Kuma ku tambayi Ni’imah tafi kowa sanin halinta…..” Duka Haj Fatsum takaiwa bakinsa tace “Ni’iman ubanka da uban waye ya fadi wannan din tun jiya ta kirani ta fadamin na tashi jakada yaje yayomin bincike akai aka tabbatarmin saboda haka tun kafin ka gurbata zuri’arka ka sawwaqe Mata kowa ya Kama gabansa
STORY CONTINUES BELOW
Komawa yayi ya zauna jikinsa yana rawa sai huci yakeyi tsawa Hajiya fatsum ta daka masa tace “Mgn fah nake maka Magaji” iska ya furzar ya miqe yace “bazan iyaba” yana fadin haka ya fice da sauri suka bisa da kallo yana fita mota ya shiga ya nufi gdansa inda Salma da Dijah suka kalli mahaifiyarsu sukace “kinji fah Hajiya ai dama Hajiya Sahura ta fada sun tsafaceshi a kishi irin nasa wlh da qalau yàke da sai yayi abinda kikace kigafa yanda yake dakama mana tsawa dan tsoron nakima ya daina an cire mishi wlh idan kika sake rabaki zatayi dashi gabadaya kamar yanda ta rabashi da matarsa”
Dunqule hannu Hajiya Fatsum tayi ta daki tafin dayan hannunta tace “aa Basu isaba wlh Kaltume ma da take tsafi ta qyaleni ballesu dole ma su barmin dana ba mace na haifawa ba kaina na haifawa” mayafi ta figa tace “ku biyoni” miqewa sukayi suka bita mota suka shiga driver yajasu suka fice Kai tsaye sukayiwa gdan Alh Nuhu tsinke lkcn Rafi’ah ta sauko tana kwance a parlourn saboda azumin baqar wahala yake bata Ammi tana gefenta tanayi Mata tsifar baqin dogon gashinta saiji sukayi an shigo ana dure duren ashariya da sauri Rafi’ah ta wuntsulo cikinsu babu Wanda ta sani har garama Dijah suna yanayi da Ja’afar saidai ita baqace a sanyaye ta dubesu tace “haba bayin Allah yada shigowa babu sallama kamar ba musulmi ba…..”
Dauketa Hajiya Fatsum tayi da mari tace “kaji sabuwar mara kunya Koda yake kyayi ai nasamu lbrnki dana uwarki me daure miki gindin iskanci da bin maza an fake da karatun likitanci ana karuwanci ruwan jiki ya qare an sihircemin dana an liqa masa to bamaso bamason irin tsiya irin jaraba wannan kyaun dan macijin shine yake dada rudarsa to wlh bazamu kwashi jarfaba”
Rafi’ah sai jikinta ya dauki rawa ta rinqa ja da baya suka rinqa tujararsu da zage zage babu Wanda ya tankansu sun jima sunayi itadai sai tsumar jiki takeyi data zuci Wai karuwa an fake da karatun likitanci ana karuwanci wannan kalma ta girgizata tunda take bayan Ja’afar babu namijin daya taba riqe ko hannunta Amma gashi uwarsa tana kiranta karuwa, Ammi ma kalmomin sunyi Mata ciwo Amma bazata biye musu ba tasan duk sharrin Sahura ne miqewa tayi ta Kama hannun Rafi’ah tajata suka haye sama suka barsu a tsaye sai lkcn Aunty Raziqa ta miqe tace “ashe yan iskan da yawa kema kin haifi dan iska domin kuwa babu yanda zaayi idan shi nutsattse ne yayi sha’awar auren karuwa…” Aunty Murja ce ta katseta da cewa “wai dama wannan itace uwar Ja’afar din kayy Amma albasa batayi halin ruwa ba dan bai tsotsa a nonon uwaba karuwa kuwa saidai ki gani a dakinki” Suma ficewa sukayi daga parlourn suka barsu tsaye kamar dashe sun jima suna rarraba idanu sosai suka Raina kansu ashe Suma iyayen Rafi’ah ba faqirai bane sunma fi na Ni’imah Koda yake ita dama Haj Fatsum tasani baqin cikine ya hanata tunawa wani gwauron numfashi ta sauke tayi qwafa ta fice tana cewa “kunyi da yar halak indai nice na haifi Magaji wlh bazai zauna da wannan makirar mara kunyar yarinyar ba matarsa yar arziqi daya tilo ta isheshi…”
Tunda su Ammi suka shiga ciki take aikin rarrashin Rafi’ah ta sake botsarewa tanata kuka tana cewa wlh bazata zauna da Ja’afar ba ita bazata iya masifa ba kowansa masifaffe shima masifaffe ita bazata iya masifa ba bata sababa, duk yanda ammi take tunanin shawo kanta taqi shawuwa saima qara botsarewa da takeyi tana maimata “Wai nice karuwa Ammi wlh bazan iyaba ni bazan iya masifa ba”
Shikuwa gogan gdansa ya shiga yana shiga yaci karo da Ni’imah duk ta fashe komai na parlourn hatta show glass dinta bata bariba baiko saurareta ba ya haura saman ya bude wani daki dake kulle ya debo takardunsa ya fito har yaje bakin qofa ya tsaya yace “sannu da aiki Allah ya qara lfy” Bai jira cewarta ba ya zaro raffers na 100k ya ajiye Mata yayi gaba abinsa ya fice ya tare adaidaita ya fada masa inda zashi airport ya nufa ya hau jirgi sai birnin tarayyah gabadaya Bauchi tayi masa zafi.
Haka kwanaki suketa turawa a bangare ukun duka babu kwanciyar hankali hauka sosai Ni’imah takeyi duk wani Abu me amfani na gdanta ta lalatashi Yusrah ce tazo gdan taga yanda ta mayar dashi take ta fadawa Hajiya Sahura aikuwa tayo tattaki tazo ita da Hajiya Fatsum nan suka hauta da fada suna nuna Mata illar haukanta Hajiya Fatsum tace “ina mijin naku kwana bakwai banganshi ba?” Hawaye ta share tace “nima kwana bakwai bansashi a idona ba nikadai naketa haukana” murmushi Sahura tayi tace “ya hadaki da hawan ruwa ya tsallake ya tafi yabarki garama ki canza salon kishi wannan haukan bazaisa ki samu abinda kikeso ba”
Hajiya Fatsum taja numfashi tace “ni bantaba ganin jaraba irinta Magaji ba ita kanta Rafi’an ba son auren takeyi ba jiya Muhseen yakemin bayani ni saitama bani tausayi tun ranar da mukaje mukaci mutuncinta da iyayenta tanacan ana bala’i da ita akan ita saiya saketa bazata zauna dashi ba gashi Yama kashe wayoyinsa gabadaya duk neman duniya an kasa samunsa balle asan inda yake” hararar Hajiya Fatsum Ni’imah tayi tace “qarya takeyi munafukace wlh tanasonsa ni nasanta fiye da yanda uwarta tasanta inda batajin sonsa aranta da bai isama ya rabeta ba ranar fa da aka daura aurensu fah da ya dawo yayimin hawan qawara bayan ya gama cemin yayi itace ta tada masa da sha’awa wlh idanda batasonsa ko ystsanta bazai riqeba tujararriyace ta masifa akan abinda takeqi”
Numfashi Hajiya Fatsum ta sauke tace “malam me hawainiya yace dole sai ta shigo gdannan abinda nakeso dake ki sanyawa zuciyarki salama ki barmu dasu wlh daga ita harshi tunda suka taboni saina tashi hankalinsu suda zaman lfy saidai idan anayi a lahira suyi ta shigo din Fatsum cefa” kuka Ni’imah tasa tace “kuma fah itama kwanciya zaiyi da ita kwanciyar aure ko?” Tsaki Hajiya Fatsum tayi tace “to meye don ya kwanta da ita ke kin cika shashanci dukkanku ya isheku indai Magaji ne” numfashi Hajiya Sahura tayi tace “nidai zan koma gurin na gangare ayi yanda bazai kwanta da itaba don nima banason ya hada shimfida da ita irin Haj Amina jarabane idan namiji ya dandanasu baya iya rabuwa dasu kinsansu da tsafin tsiya ke yakamata ki fadamin haka tunda kece kike bani lbrn matar babanku buzuwa” haka suka rinqa saqawa da warwarewa basubar gdan ba sai dare sukace Mata gobe ta fito da wuri zasuje gurin Mal na gangare zasu gabatar da ita sai Rafi’ah ta zama yar kallo Haj Sahura tayi Mata alqawarin gobe zatasa Dad ya canza Mata komai na parlourn ta, sunanan suna saqa da mugun zare Hajiya Innah da Karimah da Hafsatu yayan Hajiya Kaltume da sauran dangin ango sukakai kayan lefen Rafi’ah tare da sanya lkcn biki sati biyu abinda akayi zaayi wata guda Ja’afar ya murza kambu yace shi yagaji da ajiyar Mata a gidan wasu abashi abarsa kawai haka Mai martaba da Dad suka taushi Abba ya yarda a hakan Dad ne yace shi ya daukewa Abba komai da uba yakeyi shi zaiyiwa Rafi’ah nan fah gidan Alh Nuhu ya hargitse aka shiga shirye shirye babu Kama hannun yaro ana bikin auta sha lele dinner kuwa Saida aka shirya hudu tun saura kwana biyar bikin ya dawo wani salo harda Prince Day wasu abubuwa da yawa baiyi a aurensa na farko ba hatta rawar jikin da yakeyi baiyi a bikinsa na farko ba duk abinda akace yana barin jiki zai zaro ya bayar kowa yasan cewa wannan aure na musamman ne a gurinsa Amma fah baisan halin da amaryar take ciki ba tun ranar da yaje tace bata buqatarsa ko waya Bai qara kiranta ba balle yaje itama kuwa ta watsar dashi dama baa gabanta yakeba.
Sai dare yaje gidan ya tarar da hakimar tasa a zaune a parlour sai karkada qafa takeyi bai kulata ba ya haye sama yayi wanka.
Saida ya huta sannan ya sauko sanye da kayan bacci ya zauna yana danna wayarsa Rafi’ah ya Kira har tayi Ring ta katse bata dagaba ya sake Kira saboda sosai yake azabtar da kansa da rashin jin nata ta daga tayi sallama ya dube Ni’imah yace “ranki ya dade saraki sai Allah wai bakisan kin sosa raina ba ko?” Banza tayi dashi yayi murmushi yace “shiyasa kullum kike qara mamaye zuciyata kin iyabada hqr sorry My luv wow! Sunan ya hau nikam na gama sa’ar Mata a duniya, am nace ba me kike shiryawa game da shagalin bikin nan ne kinsan fah wannan bikin na musamman ne banason a samu matsala”
Mamaki ya hana Rafi’ah mgn taji yayi dariya yace “kinada basira ok karki damu zanyi qoqarin naga na daidaita komai….” Qit ta kashe wayarta ita tsoroma yabata saikace zararre shi kadai sai zance yake yana bawa kansa amsa, kissing din wayar yayi ya kalli Ni’imah ya tashi ya matsa kusada ita yace “uwargida sarautar Mata ke me kike shiryawa ne?” Dannan zuciyarta takeyi saboda hudubar da Haj Sahura da Haj Fatsum sukayi Mata amma qarshe yakaita zuciyarta tafasa takeyi murmushi yayi yace “mgnr tarihin amarya kece zaki gabatar dashi ranar dinner saboda ke kikasan komai game da ita….” Zabura tayi ta miqe shima ya miqe ya daga Mata hannu yace “baki Isa kice aa ba dolene ramawa kura aniyyarta a gdannan dole kema kiyi Mata abinda tayi Miki bazata rasa wannan gatan ba wlh Kuma banason son zuciya gaskiya nakeso na rantse da Allah kikace aa yau saikin koma gdanku Kuma kikayi son rai wajen gabatarwa sai na tsinke igiyoyin aurena akanki”…………
_Hmmm uhmm tab Allah ya qarawa Bestie’s hqr wannan tantirin miji naku ya shirya🤔_
Hayewa sama yayi yana yan waqoqinsa tabisa da idanunta daya kawo ruwa wai itace zata gabatar da tarihin amarya Kuma har yana iqirarin idan taqi zai qara sakinta zubewa tayi a gurin zuciyarta na hantsilowa tace “allah wannan wannan irin dan iskan mutunne” ta jima tana kuka kafin ta tashi gwiwa a salube ta shiga dakinta Hajiya Sahura ta Kira take fada Mata abinda yake faruwa ta danna Mata ashar tace “ke me kikace masa?” Shiru tayi tana tsiyayar hawaye tace “idan nace zanyi mgn Mom sakina zaiyi nikuma wlh bazan tashi a banza wata tazo taci bulus ba”
Shiru Hajiya tayi daga bisa taja ajiyar zuciya tace “Hakane Kinga bari na Kira uwarshi naji ko zata iya wani Abu” ajiye wayar tayi ta zauna tayi sukuti saida wajen awa daya ta wucce ta kirata tace “ki kwantar da hankalinki kije kiyi idan kin tashi ki zagesu tsaf dagashi har ita wannan shawarar uwarsa ce Kinga ko banza kin bata musu taro….” Katse Mom tayi da cewa “mom bakisan Ja’afar ba itama Barebari batasanshi ba wlh duk abinda ya furta baya masa wahalar aiwatarwa saura fa igiya biyu auren idan na kuskura nayi abinda kukace nasan biyun zai tsinke a bainan nasi”
+
Tsaki Mom tayi tace “to kiyi abinda ya dace nikam wannan tujararren mijin naki ya fara kaini qarshe wallahi idan na waiwayeshi saiya Raina kansa ace aure ko wata uku baayi ba tashin hankali ya cikashi daga wannan sai wannan kayy wannan Ja’afar din jarfa ne gsky Hajiya Fatsum ta haifo mugun iri irin tsiya irin jaraba” haka suka hadu sukayita zaginsa bata ankara da yana tsaye akanta ba Saida suka gama tana juyowa taganshi harde da hannu a qirji.
Saida taji qirjinta kamar zai tsage tsabar tashin hankali ya shafa gashin bakinsa ya juya ya ficeTsaki taja sosai yaji tsakin amma dake miskili ne bai juyaba ya bude dakinsa ya shiga ya kwanta yanata juyi babu mataimaki takaici ya cikashi ya sake gyara kwanciya kawai yaja pillow ya rungume.
Amarya Rafi’ah kuwa tananan kullum cikin quncin zuciya take ta kasa karbar auren Ja’afar a qasan ranta kowa dai daya shafeta a salube yake hidimar bikin saboda damuwar da tayiwa amaryar tasu yawa duk wata kwalliya da akewa amare taqi yarda ayi Mata hatta lalle da wankin Kai qememe taqi duk wani daya Isa ya fada Mata taji ya fada tayi kunnen uwar shegu shikuwa Abba dama da aka fada masa cewa yayi a qyaleta kukanma kansa yakeyi babu meyi Mata maganin damuwarta sai Allan daya jarabceta, ranar ranar alhamis akayi kamu juma’ah takanas Hajiya Innah ta turo me kwalliya akan ayiwa amarya nanma tayi tsalle ta dire itafa bazaayi Mata ba dole haka aka qyaleta da yamma likis aka turo wasu arnan motoci domin daukarta wai Prince’s day tana kuka tana komai Aunty Murja da Aunty Raziqa suka fito da ita cikin alqabbar da Saida akasha dambe sannan ta yarda ta saka suka sanyata cikin daya daga cikin motocin.
A cikin gidan Sarautar aka ware wani bangare aka kashe masa manyan nairori aka tsara gurin dinner tunda suka shigo sautin sarewi da algaitu ya cika Mata kunne suna busawa da bugun zuciyarta daqyar ta samu ta fara kamo addu’o’i tanayi wasu matane su hudu suka nufo matar da take suka bude suka fito da ita suka kamata anata yi musu ruwan kudade da turare itakam sai ruwan hawaye takeyi da shassheqa.
Wani bangare suka nufa da ita suka shiga Basu tsaya ba Saida sukakai qarshe suka qwanqwasa wani daki aka bude musu suka shiga Saida sukayi Mata guri a gefen gadon sannan suka russuna suka kwashi gaisuwa suka fice matsowa yayi gabanta ya jima yanajin sautin kukanta tanata shassheqa yanajin diran gunjin kukan nata har tsakiyar ruhinsa ya tsugunna a gabanta ya sanya hannu ya dage hular alqyabbar.
Babu kwalliya a fuskarta ga hawaye ya bata fuskar Amma bai hana asalin kyaunta fitowa ba, yaja ajiyar zuciya yana qara sauke injin idonsa akanta idanunta a lumshe suke sosai kukanta yake tabashi ya miqe ya zagaya dakin ya dawo fuskarsa a daure ya sanya hannu ya miqar da ita ya fara qoqarin zare Mata alqabbar ta riqe da sauri ya furzar da iska me zafi ya bude baki yace “ance rabonki da wanka tun shekaran jiya tunda bazaki iyaba ni zanyi Miki yanzu saboda banson qazanta”
Batasan sanda ta bude idanunta akansa ba yaci gaba da qoqarin cire mata rigar ta sake qanqame jikinta tana kuka tace “don….don Allah ja’…..” Rufe Mata baki yayi ya dago kanta yace “ki roqeni wani abun Banda wannan tunda Ammi da Abba Basu Isa su saki kiyi ba ni na isa nayi miki”
Baijira cewarta ba ya faketa ya dagata cak tana kuka tana shure² yaqi sauketa Saida ya dangana da ita bathroom din dama ya shirya terming dinsa kawai ya tsomata cikin ruwan alqyabbar kawaiYa cire Mata nanfa suka Dora kokawa kowa naji da taurin kai takaici ne yasa baisan sanda ya keta riqar sabuwar atamfar sharratone din ba ta rintse idonta da qarfi jikinta na rawa ganin ta saki Masa tanata ajiyar zuciya yasashi kunce zanin ya zare Mata komai na jikinta pant da bra kawai yabar Mata ya fara wanketa tayi tayi ya qyaleta tayi yaqi.
Aikuwa ta Raina kanta ta dirzu miqewa yayi ya bare sabon towel ya miqa Mata fuskarsa kamar Bai taba dariya ba yace “ki tashi jiranmu akeyi ki fito banson sakarcin nan naki” yana fadin haka ya fice daga bathroom din yama fice daga bangaren gabadaya qarasa wankan tayi jikinta har yanzu rawa yakeyi tana jera masa Allah ya Isa dama Wanda ya fada mass batayi wanka ba, towel din ta dauro ta fito ta ishe wannan matar da taje yimata kwalliya taqi da wata me kamala a zaune a dakin tsoro ya cikata amma sai taga wannan kamilar ta matso ta kamo hannunta tace “na zaci can zaa kaiminke Ashe Baban Innah ya murda kambu to hakanma yayi Salamatu kiyi ki shiryata goma na dare zaa fara walimar naga yanzu har takwas kinsan Magaji ba hqr ya cika ba” zaunar da ita tayi Salamatu ta miqa Mata Mai ta fara shafawa har yanzu ta kasa tsayar da ruwan idonta bayan ta gama salamatu ta fara aikinta ana kwalliyar hawaye na gogewa daqyar Hajiya Innah ta rarrasheta tayi shiru akayi kwalliyar tabata wani arnen leshi tace tasa ta sanyashi yayi masifar yimata kyau kasancewarsa maroon daurin dankwalinta ma an dauki kusan 30 minutes sannan aka gama Hajiya Innah ta bata sabuwar alqabba milk da akayiwa ado da Marron tasa Mata takalmin alqabbar shima milk ne sai awarwaro na gold masu tsadar gaske dayan hannun Kuma agogo sai zobba da dankunne da sarqa habawa wannan rana ta musamman ce duk da bata cikin nutsuwar zuciya data kalli kanta a madubi Saida tayi hamdala tare da ajiyar zuciya.
Bude qofar sukaji anyi jakadiya ce tazo ta fadi gaban Fulani Innah tace “Allah ya qara Miki lfy Mai martaba Magaji ne yace ayi muku mgn taro fah yayi taro ku kadai ake jira” dago Rafi’ah tayi tace “mun gama yanzu zamu fito” turaruka ta fesa Mata ta Kama hannunta suka fito kicibis sukayi dashi a qofar shigowa bangaren ya kalli Rafi’ah ya kawar dakai yace da fulani Innah “sannu mun wahalar daku” murmushi tayi tace “nadai fada maka idan kun tashi yanda zakuyi” kallon Rafi’ah yayi yayi murmushi yace “natsani wannan kukan wlh ki daina babu abinda zai hana saima tunzurani da kikeyi”
Tsakaninsu da gurin zamansu babu nisa ya janyota jikinsa ya shaqi qamshin turarenta ya sauke ajiyar zuciya suka fara takawa a haka tanata qoqarin janyewa yaqi bata dama takan wani farin carpet sukabi wasu dogarai na takensu gaba da baya sunata kirari da ihu tuni sautin dake tashi a gurin ya canza akasa na gidan sarautar saida suka zauna sannan mutane suka rinqa tasowa suna zuwa suna kwasar gaisuwa suna zuba mawa amarya da ango kari Ni’imah na gda batasan wainar da ake toyawa ba.
Saida lkc yaja sosai ta samu labari aikuwa kishi da baqin ciki ya tunzurata ta dauko mota ta fito tana rayawa a ranta wato ita bata isaba shiyasa baiyi Prince’s day a aurenta ba sai wannan auren cin amanar ya tarawa mutane, anacan anata shagali biki yayi biki taro yayi taro ango sai washe baki yake yana satar kallom Rafi’ah da tayi kicin² da fuska taketa jan zuciya shi hakanma nishadi yake bashi, batare da sunyi tsammani ba kawai saiji sukayi an wankesu da ruwan Sanyi qarara abinda yaja suka miqe gaba daya MC baisan me akeba yanata zuba babatu saiji yayi ance “ku dakata yaku taron tsinannanu Wanda kuka taru saboda auren tsinanne da tsinanniya to ku sani dukkanku kunyi kadan kuci mutunci na harni zaaci Amana a cuceni……..
Tasowa dogarai sukayi da sauri sukayi Mata cahhh suna fadin “Saita kalami yar talakawa….” Saurin daga musu hannu yayi ya miqe ya taka cikin cikar Izzarsa ya Isa gabanta tanata huci tana cije lebe, dafa hannu yayi tsammaninta marinta zaiyi sai taji ya sauke hannunta a kafadarsa ya janyota jikinsa ta fara qoqarin fincikewa yasa dukkan qarfinsa ya mannata da qirjinsa ya karbi abin mgnr yayi gyaran murya cikin sauti me nuna asalin izzar sarauta yace “da farko inayiwa baqinmu barka da zuwa tare da baku hqr a bisa abinda wannan zautacciyar tayi muku akasi aka samu baasan ta fito ba tadan hadu da matsalar brain ne idan abin ya motsa tana fuzga so do Allah kowa yayi calm down komai zai wucce am Sarkin gda da Sarkin qofa ku mayar da ita bangarenta a qara Mata tsaro don gaba kadan duka zata fara”
Yana fadin haka ya dago sakar Mata murmushi ya daga Mata yatsa ya barta tsaye sororo kafin ta ankara taji an cafeta sama an fice da ita daga gurin aka cillata a wani killataccen bangare a gdan shikuma ya koma gurin amaryarsa yana zama ta miqe ta fice daga gurin a guje ya sa aka bita itama aka riqe masa ita ya taso ya iso gareta yasa hannu ya kamota ya fice da ita daga cikin taron bangaren da aka fara kaita nan ya nufa da ita ya cillata saman kujera ya fara bala’i yana cewa “kema mahaukaciyar ce irinta da zaki biyeta ku watsarmin da mutunci a bainan nasi?
+
Miqewa tayi tana huci tace “akanme zakace mata mahaukaciya bayan kafita hauka da kana tunanin zaka samu wannan damar ka gama shimfida son zuciyarka a banza ne kana tunanin ko ita ta qyaleka duniya zata qyaleka ne? Ja’afar Ka cutar damu Allah ya isa wlh bazamu yafe maka ba Kaine Ummul aba’isin kowacee masifa ta rayuwarmu da dadi da wuya mun jurewa juna har kawo lkcn daka riskemu Ashe Kaine qaddararmu Kaine bala’in da zai fado rayuwarmu ya rusa mu kacina son kanka da son zuciya Wanda na tabbata duk Wanda yabi son zuciya qarshensa nada……”
Wata fusga da yayi Mata ta hanata qarasa kalaminta ya cillata gadon yabita ta zulle a guje ta nufi bathroom yabita ya sake wartota ya hadata da bango yace “qarya kikeyi Rafi’ah bazan taba nadama ba a rayuwata giya nasha ko caca nayi kokuwa zina na nemeki da ita da zakice zanyi nadama? Oh God” ya fada tare da bude qofar a fusace ya fice daga dakin ta koma ta zauna tana wani irin kuka me ciwo tana tambayar kanta me hakan yake nufi kenan ya kawota bangare babu kowa ya ajiyeta babu kowa nata.
Tana wannan tunanin taji an bude qofar an shigo ta dago da sauri ganin qanwar Ammi Bushira da Aunty Murja da Aunty raziqa yasata miqewa da sauri qarasawa sukayi gabanta Aunty Bushira ta Kama hannunta ta zaunar da ita tace “bazaki daina kukannan ba ko gashinan kinjawa kanki Ja’afar ya rantse bazakibar gdannan ba kinzo kenan….” Dagowa tayi da razane tace “ban gane ba?” Aunty Raziqa ce ta harareta tace “wannan haukan da kukeyi Kuna gwara kan mijinku babu abinda zaija muku sai raini da wulaqanta ita idan kishi yasata ta haukace ke mene hujjarki na haukacewa to wlh Abba yace ki kiyayi fushinsa sarai zaku raba hanya indai akan aure ne kowa ma yasan mijinku bai kyautaba to Amma shima ya zaiyi da zanen qaddararsa tun kafin a haifeshi sukayi alqawari da Ubangiji na duk wani Abu dazai faru dashi tun daga ranar da ya fara shaqar iskar duniya har zuwa Rana ta qarshe a rayuwarsa haka kema haka Ni’imah to akanme zaku haukatashi ku mayar dashi ball a tsakaninku ita ta bugashi nan ke ki bugashi can ko kin dauka saboda ya aureki don yana mijin aminiyarki babu alqalami tsakaninku to wlh ki dawo hayyacinki nasan iyayenmu basu barmu da jahilci ba saidai kana sane ka take sani sakarya kawai da takeson wasa da damarta”
Durqushewa tayi a gurin sosai kalaman Aunty Raziqa suka ratsata Aunty Murja ta dora da nata itama me ratsa bargo kafin Aunty Bushira ta cafe da cewa “gashi Allah ya baki mijin da yake sonki duniya ta shaida hakan Amma kinason yin sakacin sane masa kibi a sannu duk abinda hqr Bai bada ba to tashin hankali ma baya badashi dole yace yau a gdansa zaki kwana Ammi da Abba basuda damar sake ganinki wannan dalilin yasa zamu ari bakinsu muci musu danyar albasa Rafi’ah gdan yawa kika shigo Kuma gdan sarauta akwai qalubale a gabanki musamman daya kasance surukarki bata maraba da zuwanki dama yan uwan mijinki da suke daki daya dayan dakin Kuma su bama asan inda suka dosa ba Fulani Innah ce kawau take maraba dake sai mijinki to aikine ja a gabanki ki nutsu ki gane masoyi da maqiyi ki Kama masoyanki shima maqiyin karki canza Masa kallo karbeshi ki riritashi idan ya zaqe kai qararsa gurin Allah zaiyi Miki maganinsa abokiyar zamanki ma yanzu cikin sahun maqiyanki take yanzu haka mun barota tana alwashin saita kasheki saboda haka itama iya zama da ita zauna da ita da kyakkyawar zuciya zakiga ribar hakan anan duniya da gidan qarshe”
STORY CONTINUES BELOW
Sosai nasihar ta rinqa shigarta hadi da tsoro wannan miyagun kalmomi na Ni’imah akanta sunfi komai gigita duniyarta sun jima sosai Saida Fulani Innah ta shigo ita da Karimah sannan suka fita tana kuka tana rirriqesu sukadai samu suka tsere Haj Karimah ya ce ga hajiya Kaltume Amma batayo halinta ba tanada sanyi da sauqin hali hakan tasa sukafi dasawa da Ja’afar komai daya shafeshi baya boye Mata tana gaba gaba a cikin kowanne lamari nasa yanzun ma shine ya tasosu takanas yace su shiryata su tafi da ita gdanta bikin ma an gamashi ayi dinner gobe.
Suma nasihar suka rinqa yi Mata hade da rarrashi shikenan dai da gaske ta tabbata matarsa duk wani tsuminta da dabararta ya qare batada wani katabus kowa kalmarsa daya ta cire mgnr aminci ya riga ya rusata itama Ni’imah tayi watsi dashi ta rungume mijinta su zauna lfy, shiri sukayi Mata sosai na amaren gaske Basu gama mataba sai goma da rabi suka kamo hannunta suka fito tuni mota tayi ready kawai shiga sukayi sukadau hanyar martaba Estate suna zuwa sukayi parking suka fito da ita tanata gunjin kukanta Ammi da Abba suna fado Mata shikenan ta rabu dasu ta dawo cikin wata rudaddiyar rayuwa mara tsarin bawa zuciya farin ciki shikenan qurunqus ta tabbata kishiyar aminiyarta aminiyar da take ganin duk abinda duniya zatace bazata iya rabuwa da itaba sai gashi cikin sauqi kaidin namiji ya farraqasu har tana neman rayuwarta wani sabon kuka ya sake qwace Mata lkcn da aka haura da ita saman aka bude wani daki aka shigar da ita tare da yimata matsugunni saman wani tattausan kilishi basuyi Mata sallama ba saboda sunsan sallamar qarin tashin hankalinta zasuyi suna fitowa motar su Ni’imah na shigowa ita da wata yar yayar hajiya Sahura da tun dacan ma batason alaqar Ni’imah da Rafi’ah sunayin parking sukuma suna fita shima motarsa tana shigowa Samiha ce taja Ni’imah suka shiga ciki tana ciccijewa tana cewa “yanzu fah gurinta zai tafi ko yanzu da ita zai kwana….”
Rufe Mata baki tayi tace “ke kincika zafafawa abinda bazaije ko inaba kwana nawane amaryar maye a gabanki fah Mom tayi waya da boka na gangare yace zaiyi iyakar yinss yaga wani abu bai shiga tsakaninsu ba kuma kinsan zaiyi” ajiyar zuciya ta sauke daidai lkcn daya shigo tabisa da kallo fuskarsa babu alamun fara’a ya ajiye Mata leda ya haura sama ya jima sosai sannan ya fito ya sake wucceta har yaje bakin qofa yace “good night” wani malolo taji ya taso Mata amma data tuna tsiyar da suka kitsa sai tayi murmushi kawai ta miqe ta haura saman.
Kwanciya tayi tana saqawa da warwara inda shikuma yana fita ya bude motarsa ya dauki kayan daya siyowa amarya ya nufi bangaren gabansa har faduwa yakeyi tujarar Ni’imah bata tsoratashi kamar ta Rafi’ah itan akwai mugun kwarjini budewa yayi da addu’a ya shigà ya tsaya yana qarewa parlourn kallo yayi wani kyau an qara qawatashi sosai yaja numfashi ya haura saman kamar bangaren Ni’imah shima daki biyune a saman sai parlour qasa Kuma daki daya da kitchen da dinning area dakina biyu ya bude ya shiga ya hangeta zaune ta hade Kai da gwiwa tanata shassheqar kuka ya jima akanta yana qare Mata kallo kafin ya ajiye kayan hannunsa ya sanya hannun nasa cikin faduwar gaba ya dago fuskarta gabadaya kwalliyar dake fuskarta ta dame da hawaye yaja ajiyar zuciya yace.
“Kiyiwa Allah ki daina kukannan haka hukuncin Allah ya riga ya tabbata Rafi’ah wai ya kukeso nayine nikam?” Jan zuciya tayi ya sake gyara zamansa ya qara tallafo kanta yana me share Mata hawayen da hannunsa yace “a qa’ida tashi zakiyi muje muyi sallah mu godewa Allah duk da nasan baki murna ni inayi Amma shi aure ko bakaso rahamane da yakamata ka godewa Allah idan ya nuna maka ranar”
Da dabara yajata ta miqe sukayo alwala yajasu sukayi sallah raka’a hudu ya miqa hannu zai Kama kanta ta janye Murmushi yayi ya sake matsarta ya Kama kan nata da qarfi ya farayi Mata addu’a ya jima yanayi kafin ya gyara zamansa ya janyota jikinsa qamshinta da dumin jikinta yana ratsa nashi yanajin wata nutsuwa me gudana tana shigarsa wata qaqqarfar ajiyar zuciya ta sauke ya dago fuskarta da sauri yana mamakin dalilin tata ajiyar zuciyar cikin sanyin muryar da bata taba sanin ya mallaka ba yace “nayi Miki tanadin farin ciki dimun da’iman dawa’un My Luv don Allah ki bani hadin Kai kada ki biyewa mutane masuja da hukuncin Ubangiji inasonki zanyi hqr da komai naki kema kiyi hqr da mijinki kinji?”
Lumshe idonta tayi tanajin zagawar hannunsa a bayanta ya sauke ajiyar zuciya ya janyeta yace tashi kije kitchen ki daukomin flat na baki abinci” sunkuyar da kanta tayi yayi murmushin gefen baki yace “af sorry fah Ashe yau aikin nawane karki damu zanyi Miki komai idan kinaso har bacci ma ni zansaki kedin special ce” yana wannan mgnr ya dawo bayan ya kulle bangaren gabadaya yazo ya juye abinda yazo dashi daqyar da takurawa ya matsa mata taci hanta Tasha lemo yace “kije kiyi wanka kiyi brush inajin bacci sosai yau kunbani ciwon kai?” Batayi Masa gardama ba saboda tuna abinda ya faru dazu ta shiga bathroom din tayi brush tayi wanka ta dauro towel ta zuro alqabbarta lkcn data fito a tsaye ta tarar dashi da wata matsiyaciyar rigar bacci a hannunsa yana juyawa.
Matsawa yayi ya ajiyeta ya sanya hannu ya cirenta alqabbar ya ajiye ya Kama towel din zai cire ta riqe da sauri yaja numfashi ya miqa Mata rigar ya nuna Mata mayukan da ya fito dasu da turaruka yace “ki tabbatar kin gama kafin nazo duk abinda bakiyi ba na fito to saidai a hadu gaba bana jira idan zan kwanta” bai tsumayi amss ba ya shige bathroom din ta dauki rigar ta juyata tayi Mata kyau Amma duk rashin kunyarta bazata sata ta kwanta a daki gata gashi ba mayukan ta shafa ta fesa turarukan ta Koma kawai ta zauna ya fito ya dubeta cike da takaici gata dai kamar wayayya Amma bulkuma ce.
Baice Mata qala ba ya shiga shiryawa bayan ya gama yakai hannu ya kashe hasken ya kunna qaramin haske ya matso gabanta batare da tajishi ba ita bacci ma takeyi a zaune kawai saiji tayi yayi sama da ita ta fara zillewa tare da bude baki zatayi Masa kuka yayi saurin dora bakinsa a natan ya rufeta ruf a gadon tare da zame towel din yaja musu bargo kuka ta rinqayi masa tana gunji tanayi masa magiya……….
Daqyar da dabara saboda bayason wahalar da ita ya samu ya cimma burinsa ya saki wata ajiyar zuciya tare da dakatawa duk da dama bai yarda da mgnr su Barebari ba Amma zuciyarsa ta danyi dar saboda yasan abokin damo guza tabbas idan ta kasance aminiyar Ni’imah to komai zata iya faruwa amma sai gashi ya sameta asalin Varging duk da itama Ni’imah ya sameta da budurcinta Amma baikai qualityn na Rafi’ah ba duk masifarsa bai iya shigarta gabadaya a wannan dare ba kamar yanda ya shigi Ni’imah a daren farko.
Wani tausayinta ne ya kamashi jin yanda take kuka tana jujjuya kai tana Kiran iyayenta, ji yayi bazai iya cigababa sarai ya fahimci ba qaramar wahala zasusha ba daga ita harshi gata itanma Masha Allah akwai dauriya amma wannan abun yafi gaban dauriya saidai dabara, janye jikinsa ya farayi a hankali ya koma ya kwanta a gefenta yanajin sinadirun qaunarta yana qara zagaye duk wani bangare na jikinsa a hankali ya janyota jikinsa lkcn da wasu hawaye suka zubo masa ya rungumeta tare da hura Mata iskar bakinsa a kunnenta da haka bacci yayi ram da ita.
+
Ya dade yana kallonta ita komanta me kyaune yana godewa Allah da yayisa cikin mutane masu saa yasan aurenshi da ita ba qarfinsa ko isarsa bace kawai lucky ne da yake dashi a rayuwarsa da wannan bacci ya daukeshi shima, Kiran farko ta farka tajita tsam a jikinsa ta rinqa motsawa har ya tashi bai bude idonsa ba sai sakarta da yayi ta zura qafafunta qasa ta taka saiji tayi wani zugi ya ratsa qasanta ta cije ta miqa hannu ta dauko kayanta ta daura zanin a qirjinta ta rinqabin bango ta samu ta shiga bathroom din tayi wanka ta tsaftace jikinta tanajin zafi idan takai hannunta gurin hakadai ta gama ta dauro alwala ta fito.
Wardrobe ta bude wani sanyin dadi ya shigeta ganin kayanta a jere a ciki ta zaro doguwar riga da hijjab tasa ta shimfida sallaya ta tayar da sallah raka’atainul fajri tayi ta zauna tana istigfari ta yarda cewa istigfari shine mabudin dukkan wani alkhairi na duniya saboda shine abunda yake goge maka duk wani zunubinka ya kusantaka da Allah salin alin.
Ta Jima tana roqon Allah sanyi zuciya da ikon yiwa mijinta biyayya kamar yanda kowa yake horonta domin ta haqiqance aikin gama ya riga ya gama bata fatan shiga haqqinsa ko zata cutu tanason tayi Masa biyayya kamar yanda Allah ya hukunta bai isheta hujja ba a ranar qiyama tace da Allah saboda batasonsa ko don ya kasance mijin aminiyarta ne yasa taqi bin dokokin sa taqi yin biyayyar aure ba.
Miqewa yayi cike da nishadi ya samu kalar matar da yake mafarkin mallaka shekara da shekaru batada ganda wajen bautar Ubangiji tabbas Allah yanasonta shiyasa ya sanya duk wani mumini yake sonta, shima tsaftace jikinsa yayi yazo yayi salatul Fajri sannan yajasu sukayi asuba bayan sun idar kowannensu yayi azkar ya miqa Mata hannu noqewa tayi yayi murmushi yace “mafi alkhairin gaisuwa itace musabaha tare da sallama My Bestie ki saba ni gaisuwata kenan”
Yana fadin haka ya miqe ya cire doguwar rigarsa ya rage dagashi sai boxes ya matso ya dagota ya cire Mata hijjab din ya fara qoqarin cire Mata rigar ta riqe hannunsa tare da dago manyan fararen idanunta ta zubasu a kansa cikin saar lillahi suka fada cikin nasa yaji wani tartsatsin wutar qauna da feels gami da kwarjini sun kashe Masa jiki yayi kamar ya saketa ya fasa yace “akwai zafi kada ki takurawa kanki ki jure zaki dace inason kasancewa da iyalina a kowacce asuba hakan yanasa na yini cikin farin ciki don Allah kada ki batamin yinina a hankali zanbiki kedin special ce Rafi’ah”
Sosai gabanta ya tsananta faduwa tsoro ya dirar Mata tana tuno irin wahalar data dandana daren jiya idan yace zai qara yimata haka tana tunanin mutuwa zatayi…. Bai bata damar gama tunanin ba ya dauketa ya azata a gadon ya kashe musu glove din yayi musu cover da duvet babu abinda ke tashi a dakin sai shassheqar kukanta da nishinsa yanata zuba Mata sannu duk wata gaba ta jikinta Babu inda bai galabaita ba kafin ta samu yayi release ya kwanta luf a jikinta itakam tuni takai China a sume ya rinqa kwarara Mata ruwan albarka yana yabawa da baiwar da ilahi yayi Mata Saida ya saitu sannan ya fahimci halin da take ciki ya zare jikinsa a hankali daga nata ya dauko ruwa me sanyi ya rinqa shafa Mata.
Yanajin tayi ajiyar zuciya shima yayi bata bude idonta ba sai kukanta da taci gaba dayi ya shafa fuskarta yace “Sorry please zaki saba kinji matata Allah yayi miki dawwamammiyar albarka kin jiyar dani dadi yau ke ta dabance komanki dabanne” tashi yayi ya nufi bathroom ya hadanta ruwa yazo zai dauketa taqi dole yana kallonta ta zura hijjab dinta ta nufi bandakin tana dafa bango tana cije lebe yana kallonta cike da tausayi tana zuwa ta gasa jikinta tana kuka saboda azaba tayi wanka ta fito ta zauna saman drees stool ta dauki doguwar rigarta ta haye gadon daya cire bad sheet din ya shimfida wani ta kwanta tana jin dacin abubuwa da yawa a ranta da haka bacci ya dauketa batasan sanda ya dawo ba shima yayi wanka ya kwanta ya janyota baccin ya daukesu tare basu suka farka ba sai 11 saboda sunji jiki daga ita harshi inda uwargida Ni’imah takecan ta hadiyi baqin ciki da tashin hankali da asubar Mom ta kirata cikin dimuwa tace.
STORY CONTINUES BELOW
“Ya akayi baki binne layar da boka Na gangare ya bayar aka kawo miki ba yanzu gashinan kin rusa Mana aikinmu komai da baaso ya faru ya faru tsakaninsu” cikin gigita tace “bam…. Bangane ba naga a gabanki na binneta” dafe kai Mom tayi tace “to ya haka yanzu boka ya kirani yake fadamin yanzu aljanin daya tura ya dawo masa a galabaice ya kasa isa ga Ja’afar din duk sanda yayi yunqurin tabashi sai yaji kamar ana yayyafa masa ruwan tafasau ita Kuma Rafi’ah itama lkcn da ta tashi da asuba tayi sallah tayi addu’a shiyasa ya kasa kaiwa gareta Kinga zamufi samun sauqin tabata akanshi shidai kinsani batun yau muke barnar kudi akansa mun kasa samun galaba ba kawai aikinmu ya karkata kanta ita daya shi mu qyaleshi boka na gangare yace tabbas idan muka cika matsawa akan Ja’afar to kwabarmu zatayi ruwa domin kuwa yanada dafa’i irin nasu na gdan sarauta da baya bari su tabu”
Tuni Ni’imah ta fita daga nutsuwarta ta Kama kuka kamar wata zautacciya tana cewa “ai Kuna sane kuka bari komai ya faru tunda kunada ikon hanawa kun hanani daukar mataki a hannuna sannan Kuma kunqi dauka wlh bazan iya zama inuwa daya da Rafi’ah ba duk muna amsa sunan Matan mutum daya ba dole sai ta fita tabarmin gidana….” Katseta Mom tayi da cewa “abinda boka ya kasayi shine ke zakice zakiyi ta yaya? To bari kiji kada ma ki fara kinji dai da kunnenki abinda bokayennan uku sukace idan kika matsa kece zaki tafi kibar mata gidan ke Kuma shegiyace ke da zaki bari kishi yasa kiyi asarar zamanki matar sarki me jiran gado to tun wuri ma ki nutsu da ace zaki iyama da kin daina wannan haukan kinbi komai a sannu kin shiga jikinsu ta yanda zakifi yimusu illah”
Cikin shassheqa tace “bazan iyaba Mom ni bazan iyaba kawai ayi duk wacce zaayi na tsani Rafi’ah wlh ganinta ma zai iya sawa na kashe kaina yanzu fah banida wata taqama da zanyi Mata tasanni tasan sirrina dama da mijin zanyi Mata balli to shima tasanshi tasan komai dana sani game dashi nikam Mom bazan iya hqr da wannan baqin cikin ba….” Takaicine yasa Hajiya Sahura kashe wayarta ta rasa wacce irin ya Allah yabata da batajin shawara ana nuna Mata annabi tana rintse ido koda suke taqama da asiri wani abin sai an hada da kirsa gashi Ni’iman taqi ganewa sai shirme takeyi
Tananan zaune tanata aikin kuka ya shigo da sallamarsa mamaki ne ya kamashi ganin da gaske kuka takeyi ya zauna kusa da ita ya dora hannunsa a bayanta yace “barka da safiya uwar gida” dagowa tayi idanunta na zubar da hawaye tace “da gaske ka kwanta da Rafi’ah Ja’afar don Allah gaske ne?” Sakin baki yayi da tsananin mamakin yanda akayi ta sani, Kama hannunsa tayi tace “ka fadamin Ja’afar ka kwanta da ita kayi Mata duk abinda kakeyi min?”
Murmushi yayi ya kamo fuskarta yace “Eh hakane harma fiye da abinda nakeyi Miki nayi Mata meye damuwarki matatace inada ikon nayi komai da ita kamar yanda zanyi da ke koma fiye da haka”
Miqewa yayi ya zaro kudi ya bata yace “zanje asibiti na dawo bamata da lfy don daqyar ma nasamu taci abinci” harara tabisa dashi har ya fice taja dogon tsaki tace “shashasha Allah ya kasheta ma kowa ya huta” yana fita ta dauki mayafinta itama ta sauko qasa dakin da samiha ta kwana tace “fito mu tafi zanje na samu Uwarsa na fada Mata gara taji ta sani bazan dauki wannan wulaqancin ba harni Wai zai duba ya fadawa wai yar iskar matarsa batada lfy?”
Murmushi Samiha tayi tace “kinada matsala To yanzu idan kinkai Mata qararsa me zatayi Masa?” Tsawa ta daka Mata tace “idan zaki kizo mutafi kawai” miqewa tayi suka fita a mota lkcn Rafi’ah tadan tashi tana leqowa qasan ta window tana kallonsu suka shiga mota suka fita ta lallaba ta sauko qasa ta dan gyarashi ta shiga kitchen gashinan komai kamar banza an zuba matashi badon tanajin dadin jikinta ba saidon sabo ta fara girkinta tanajin nishadi duk gdan ya cika da qamshi, ji tayi an riqeta ta baya ana sunsunar wuyanta tadan tsorata amma jin qamshinsa yasata sauke ajiyar zuciya ya juyota suka kalli juna yayi Mata murmushi tare da kissing goshinta yace “me kike girka mana?” Sunkuyar da kanta tayi tace “barka da dawowa” wani farin ciki ne ya cikashi ya sake matseta yana shafa bayanta yace “yawwa my bried ya gda” bata bashi amsa ba sai qoqarin janyewa da takeyi yayi ajiyar zuciya yace “kamata yayi ace nazo na tarar dake a kwance kina hutawa ba a kitchen ba” sake sunne kanta tayi a qirjinsa yaja numfashi yace “hakanma yayi matata bari na tayaki tunda na dawo amma dai baki manta ba yau akwai dinner da dare…”
Girgiza masa Kai tayi tace “aa” Dagota yayi yace “aa me?” Qasa ta qarayi da kanta tace “bazan iya zuwa ba” zamewa tayi daga jikinsa ta nufi inda take gyaran nama yabi tafiyarta da kallo yayi murmushi yace “saboda kada a gane alif ya dauri fataha shine zaki batamin burget dina nagadai a hankali ma nabaki kika karba” kunyace ta lullubeta taqi ce masa komai tanajin kamar ta nutse cikin qasa yayi murmushi yace.
“Kada ki damu dama yanzu daga gurin Abba nake nace masa bakida lfy so babu me zuwa daga bangarena har bangarenki hutawa zamuyi sosai mu gama girkin mu fita mu zaga gari ko?” Harararsa tayi yayi dariya me sauti yace “inason harararnan masifar kyau takeyi miki” ganin da gaske ya zage yana tayata aikin yasata dagowa tace “ni don Allah katafi ka kwanta kabarni nayi aikina” dago idanunsa yayi yayi Mata kallon daya sata saurin shiga taitayinta, kafin tayi mgn sukaji an turo qofar parlourn an shigo ta kalleshi shima ya kalleta gabansa yabada wani rass jin sautin Mahaifiyarsa tanata kutuntume kutuntumen ashar wani abu yaji ya caki maqoshinsa yayi saurin riqota tana Shirin fita sama Hajiyan tahau shikuma yayi saurin rufe qofar kitchen din yasa Mata key ya dora Mata hannu a baki yace “rabudasu kada kice komai muci gaba da aikinmu” itadai duk jikinta rawa yakeyi ya lura da tsoronta shiyasa ya sake shigar da ita jikinsa ya murde gas din ya dora harshensa saman fatar kunnenta yana lasa a hankali ji sukayi Sun sauko Hajiyan tana cewa “qyaleni da sallamamme ya dauketa sun fice daga gdan yo budurwar arziqi ce zatasan namiji jiya har tasamu qafar yawo wlh saiya Raina kansa sakarai kawai” hawaye ne ya zubo a idanun Rafi’ah shikam Ja’afar bai daina abinma da yakeyi ba yayi biris kamar bayajinsu yana murza qirjinta dakeyi Mata wani azabar zafi a hannunsa yana tsotsar kunnenta da salon rikita lafiyyar mace janyewa yayi jin parlon yayi tsit alamun sun fita ya bude qofar yaje ya dannawa ta parlourn key ya dawo sukaci gaba girkinsu tun tanajin ciwon tijarar da Hajiya Fatsum tazo yimata har tama manta yana manne da ita suka gama girkin ta sulale ta haye saman tayi wanka ta shirya cikin atamfa doguwar riga tayi kwalliyarta simple ta sake saukowa ta zauna a parlourn tana kallo shima saukowa yayi ya iso gabanta ya dagota suka nufi dinning din shi ya rinqa ciyar da ita bayan sun gama ya miqe ya haura saman ya sauko Mata mayafinta da wayarta ya miqa Mata ta yafa ya kamota suka fice ya bude Mata motar ta shiga daidai lkcn Hajiya suka fito ita da Hajiya Sahura suka tsaya sakatoto suna kallon ikon Allah Saida ta shiga ya kulle sannan ya qarasa ga su Hajiyan ya rusuna suka gaisa tace “dama Kuna ciki mukazo kukaqi budewa?” Shafa kansa yayi yace “eh wlh muna dakin qasa dake batada lfy so Ina qoqarin sanyata tai baccine lkcn shiyasa yanzun ma zamu zaga garine” bai jira cewarta ba ya miqe yace “to Hajiya agaida gda mun gode da ziyara zan kawo miki ita har gida yanzun tana buqatar hutune hayaniya damunta zatayi”……….
Kallon kallo Hajiya Barebari da Hajiya Sahura suka shigayi Jinjina Kai Hajiya Sahura tayi tace “eh kayi danna gada ashe rashin mutuncin ba iya kan yata ya tsayaba itama uwar ba qima ke gareta ba mace tafita mutunci a gurinka” shidai ko juyowa baiyi ba ya shige motarsa ya fice a sukwane suna tafe yanata sauke murmushi itakam wayarta kawai take dannawa bataji tsayawarsa ba saida ya fizge wayar ta dago tare da sauke numfashi ya zuba Mata ido ta sauke nata yaja fasali yace.
“Saboda kin rainani kinmai dani drivernki ina tuqi kina chat ko?” “shiru tayi ta fara murza yatsunta batare data tsammata ba taji ya dakanta tsawa yace “ni abokin wasanki ne ne RAPI’AH da kika rainani inayi Miki mgn kinyimin Shiru bafa nason wannan banzan halin naki waike miskila ni zaki nunawa miskilanci” kawai saita Kama hawaye saboda sosai tsawar ta firgitata jikinsa ne yayi sanyi ya kamo hannunta yace “kuma bazaki bani hqr ba?” A dan tsorace tace “kak….kayi hqr bazan qara ba….” Hade bakinsu yayi ya jima yana tsotsarta kafin ya saketa yana sauke numfashi yace “kiyi taking care ba kowanne raini nake dauka ba”
+
Jinjina Kai tayi yayi murmushi tare da yago tisue ya fara goge Mata hawayen yace “Calm down please bazan qara ba kinji” dagansa Kai tayi ya bude motar ya fita tabisa da kallo har yayi nisa ya dawo ya leqo yace “kada ki fito yanzun zan dawo” sake dagansa Kai tayi ya nufi cikin gurin ya bata 15 minutes ya fito niqi niqi da kaya leda biyu akasa masa a but ya shigo suka tafi sosai suka zagaya gari Basu koma gdanba sai tara tun tana noqewa salonsa da nacinsa Saida yasa ta ware duk da ba mgn takeyi ba Amma takanyi dariya ko murmushi, suna komawa sukayi sallah sannan ya sake fita ya dauki kayan daya siyo ya shiga bangaren Ni’imah da sallamarsa tana zaune tana shan madara amma bai samu arziqin ta amsa ba takaici ya kamashi shi ya rasa irinta da batasan zuru ba,
Zama yayi ya zuba Mata ido ta dago tace “lfy da kallo Mal” murmushi yayi yace “kawai haukanki nake tunawa tabbas da zakiyi wasan kwaikwayo idan aka baki acting din hauka zaki iya am nace ba zan kira Rafi’ah tazo inason mgn daku” jefar da cup din tayi tace “ina zaka kirata din tab lalla….”
Dora Hannunsa yayi a bakinsa yace “shut up dallah malama shawara nace Ina nema a gurinki ne da zakiyimin haukan naki na gado yar mara tarbiyya kifa nutsu kafin na fara dakaki a gidannan wlh bazaku kasheni ba duk wacce ta kawomin hauka ubanta zanci saboda ina aurenku bashi yake nuna na zama dan iska ba jaka kawai wacce batasan zuru ba ko an fada Miki abinda kikayi min jiya kinci bilis ne to ki sani kanki kika cuta sakarya kawai Kuma wlh kika motsa anan sai kinbi gyaduma me dingishi”
Yana fadin haka ya dauki waya kira Rafi’ah ta daga da muryar bacci yace “kizo Ina bangaren Ni’imah Kuma kema kada ki batamin lkc” qit ya kashe wayarsa ta zubawa sensor din ido a ranta tace “wannan wanne irin mutum ne mara dadin zama?” Miqewa tayi ta dauki hijjab dinta tasa ta fito.
Ta nufi sashin Ni’imah ta bude ta shiga tare da sallamarta ya amsa tare da dagowa ya dubeta ita Kuma idonta nakan Ni’imah data tura dankwali gaba tare da yatsina fuska zama tayi a qasa gefensa zaman saman ba dadinsa takeji ba tace “Ina yini Best….” Daga Mata hannu tayi cikin wulaganci tace “dalla malama iya bakinki a gidan uwarki na zama Bestie dinki munafuka annamimiya maci amana…..”
Qasa tayi da kanta cikin sanyin jiki bazata iya cewa komai ba duk abinda Ni’imah zata fada akanta ta cancanta murmushi yayi yayi gyaran murya yace “ba abinda na taraku kuyimin ba kenan am ke Ni’imah dole abaki girmanki a matsayinki na uwargida Rafi’ah ki bata girmanta a matsayinta na wacce ta rigaki shigowa gidana ke Kuma kija mutuncinki banason wadannan qananun maganganun da cecekuce abinda ya faru ya riga ya faru babu wanda ya Isa sauya qaddararsa banason tashin hankali a gidana duk wacce ta nemi dagamin hankali wlh kotare aka haifemu cin mutuncinta bazaimin wuya ba, bazance ku zauna lfy ba idan kunso ku zauna idan kunso karku zauna duk ruwanku ne ku zai dama ba JM ba yauwa sai Abu na qarshe wajibi ne duk ranar da dayarku takeda kwana to wajibin wacce batada girkine taje bangaren me girki ayi dinner da ita bance break ba saboda zai zama takura amma dinner wajib ce idan kunne yaji mutunci ya tsira Allah yasa kun gane”
Numfashi yaja yaci gaba da cewa sannan kwanaki naso yin tafiya Allah bai nufaba saboda tasowar mgnr bikin nan unexpected to yanzu nan da 1 week zan tafi Mexico zan tafi da Rafi’ah idan na dawo zance Indonesia saina tafi dake Ni’imah….” Kallon Rafi’ah yayi ya dubi Ni’imah yace “me mgn tayi inajin bacci” Shiru ce ta ratsa ya dubi Ni’imah yace “kefa nake sauraro” ajiyar zuciya tayi ta harari rafi’ah da gefen ido tace “bazan iya mgn a gaban wannan la’ananniyar matar ba idan mgnr akeso ayi dani aiba sai ankirata anci mutuncina gabanta ba”
Kallon Rafi’ah yayi har yanzu kanta a qasa yake yace “ok duk wacce bazata iya mgn a gaban daya ba to ta hadiye abarta koni da ita bazan saurara ba nasan akwai sirri tsakaninmu da kowacce amma wannan ba abinda zan tattauna daku da daidai bane qin yin mgnrku yana nufin kun amince da duk abinda nace” miqewa yayi ya nufi qofa yace “idan kin gama kukan saiki taso ki fito kibani abinci yunwa nakeji”
Miqewa tayi tabi bayansa Ni’imah ta daga murya tace “Snacher kawai andaiyi asara” tsayawa tayi kamar zatayi mgn sai Kuma ta fasa ta fice ta isheshi a bakin qofar ya matsa ta shige ya kulle qofar ta nufi saman yayi saurin riqota yace “yunwa nace Miki inaji” langwabar dakai tayi tace “masa Amma kuma naga ga abincin nan” tana fadin haka ta sake juyawa zata tafi ya sake kamota ya hadata da jikinsa yace “kina min ganin damarki kizo ki bani abinci” dole ganin ya dage yasata shiga kitchen ta hado masa abincin da suka siyo ta haura saman takai masa yana zaune yana danne dannensa da system ta ajiye masa ta miqe zata fita ya cafko ta ta fado jikinsa baice Mata komai ba yaci gaba da aikinsa Saida ya gama ya janyo abincin ya gyara Mata zamanta ya fara bata tana zuzzuqewa harta hqr ta rinqa karba ganin babu fuska suna gamawa ya shiga bathroom ya hada ruwa yazo ya sake dagota ya fara rage mata kayanta so takeyi tayi gardama da yake wargima guri yake samu hakanan ta qyaleshi yajata har bathroom din sukayi wankan tare suka fito ya rinqa janta da Hira suka kwanta, yana hilatarta da hikima da komai ya hade bakinsa da nata duk ta tsorace ta fara yimasa kuka shiko yayi biris da ita yana shafa fuskarta yana hura Mata iska a kunnenta tare da wasa da dukiyar qirjinta ta riqe Hannunsa tana jan zuciya tace “don Allah ka rabu dani zafi nakeji…” Bakinsa ya dora bisa nipples dinta ta rintse ido tanajinsa ya rinqa sarrafata cikin salo da qwarewa tanajinsa yana wasa da cute dinta sanda taji yayi mata rumfa yana karanto addu’ar saduwa da iyali ta dauke numfashinta ta gama sallama kanta wahala ce takeshanta bata wasa ba gashi duk wata kalma da zata fada masa ta fada baijitaba dole tayi shiru ta qyaleshi ya moreta kamar babu anjima lkcn daya samu nutsuwa ya dagata ya janyota jikinsa yanayi Mata sannu tana kukanta tace “bakajin tausayin mutum kai kawai kanka ka sani ni dama zaka kasheni dana huta banaso ni banason abinnan Ja’afar ni don Allah ka tafi da Matarka kabarni kada ka tafi dani makarantata exam zamu fara…..”
Dora Hannunsa yayi a bakinta yana janyo numfashi yace “meyesa tun lkcn dana yanke hukuncin meyesa bakiyi mgn ba hakan zaayi dole ba shawara ba” …….