Murtala Muhammed International Airport_
‘Yan media ne wainda suka samu damar zuwa suke cakude cikin mutane suna Dan baza idanuwa akan gurin fitowar baqin dasuka sauka
Wasunsu nata gyara riqon wayoyinsu,
Saninsa amatsayin AMB ALT PERM Wanda yake daukan lokaci Mai tsayi Bai zoba ga labaransa da ake bugawa lokaci lokaci akan wasu ayyukan da wasu taron da yake halarta a sauran qasashe dakuma yawanci wasu daga manyan Nan Dake yawan ziyartar qasar America matuqar suna buqatan ganinsa yasa Yan media zuwa airport din samun labarin saukarsa ayau duk da Babu tabbaci Amma dai tunda sunsamu labarin sunzo Dan tabbatarwa,.
Sanin Kota yayane yan media bazasu rasa samun labarin zuwansaba yasa Tun kafin saukarsa A Abdoul daya rigasa isowa tun satin daya gabata ya iso airport din da wuri tareda motar securities daya daga cikin securities Dake gidan gidansa na Lagos.
Sanye yake cikin navy blue _Bottega veneta_ foreign kaftan dasuka tsananin bayyanarda kyawu da haiban da Allah yayi Masa da kwarjini
Hakama manyancinsa gabaki daya a sakaye yake sbd har wannan lokacin hutu da lafiya tareda irin Rayuwar tsari da nutsuwa dayake tareda tsananin hutu da arziki da Allah yabasa suna taimakawa gurin rage manyancinsa sosai,
Wayoyinsa ne kawai a hannunsa sai wata takarda wadda Yana fitowa gabaki daya kallo yadawo kansa sbd masu daukan hotunansa dasukayo kansa securities na taresu shikuwa ko dagowa baiyiba ya kallesu direct mota suka nufa A Abdoul na gefensa bayan ya karba wayoyinsa da takardar hannunsa Yana Masa barka da sauka
Har lokacin Yan media binsa sukeyi suna daukan hotunansa tareda jeho Masa tambayoyi akan dalilin zuwansa daketa yawo na sauya wasu daga cikin manyan Ambassadors da ake zargin za’ai Wanda shine Head Amb din.
Securities ko kadan Basu Bari Yan media din sun samu isowa ko kusansa ba har yashige mota batareda yako dago kyakkyawar fuskarsa ba.
Cikin wata black BMW 7 series A Abdoul ya jasa suka bar airport din bayan A Abdoul ya kunna Masa wayoyinsa guda biyu na Nigeria
Sai alokacin ya dago ya kalli A Abdoul din tareda karban wayoyinsa Yana Nemo Numbern mahaifiyarsu Anne yasaka kiranta tareda Dora wayar Kan kunnensa.
Babban gidansa deke Victoria island suka nufa Ana parking yafito Kai tsaye ya nufi ciki Yana waya har lokacin da Anne.
Masu aikin gidan ne Mata guda biyu sai namiji daya suka ringa Dan russunawa cikin grimamawa suna cewa”
Welcome sir.
Kai tsaye yake amsa musu da hannunsa Yana Dan jinjina musu Kai duk da bai waiwayo ya kalla inda suke a tsayen ba Amma dai qaidarsa ne duk Wanda ya gaidasa Yana amsawa Koda Bai kalleka ba sbd rashin kallon mutane kamar dabiarsa ce baya iya zubawa mutum ido kamar yasan cewa idanuwan nasa na rikita mutane da kwarjininsu.
Qamshin daya fara cin Karo dashi daga babban palon na qasa yasashi Dan dago manyan fararen idanuwansa ya kalli palon take ya fahimci Mss Na’ima na garin kenan.
Kai tsaye hanyar hayewa sama ya nufa Yana sallama da Anne ya kashe wayar Yana qarasa hayewa stairs din.
Bai tsaya palonsa na musamman ba Kai tsaye Master bedroom dinsa ya nufa Wanda Yana tura kofar ya shige qamshin turarensa na _Bois Elite_ daya Gama Kama komai na dakin ya tarbesa tareda qamshin Royal Night oud Roomfresh dayake tashi shima ahankali da gyaran dakin da akai masa,
Ya nufi gaban babban mirror Dake dakin ya tsaya Yana cire maballan gaban rigarsa bayan ya aje wayoyinsa Kan wani golden table set din Dake dakin gefen babban king-size bed dinsa.
Toilet ya nufa yajima aciki kafin yafito daure da brown towel yana tsane jikinsa da wani qaramin towel din ya nufi gaban mirror ya tsaya Yana cigaba da goge jikinsa…….
Murda kofar bedroom din akai aka turo tareda shigowa gabaki dayanta cikin takun nutsuwa sai Kuma ta tsaya cak daga bakin kofar tana kallon fuskarsa ta cikin madubi shima kallo daya yayi Mata yaci gaba da abinda yake…
Jikinsa ta zubawa idanuwanta sbd daukan idanuwanta da farar lafiyayyar fatarsa keyi,
Kan qirjinsa Mai Fadi da gangaro da idanuwanta dake raunana zuwa Kan qaqqarfan qwandar hannuwansa dasuke bayyanarda lafiya da qarfinsu ga lafiyayyar fata,
Ji tayi idanuwanta sun ciko da hawaye kamar ta Dora hannu akai taita rusa ihu tana birgima aqasa akan ya taimaketa ko Wasa yabari ta ringa Yi da jikinsa Dan kuwa duk lokacinda tayi arba dashi Babu Kaya Jin take Kamar ta jawosa Tai Masa fyade Koda kuwa shi baida abinda zai Mata ita tanada abun yimasa Amma koyaushe sai Yana hanata kusantarsa sbd karta sabawa kanta da abunda zai ringa hanata sukuni takasa riqe buqatarta,
Gashi ita tayiwa kanta ta hanyar cewa zata zauna dashi ahakan har tsawon rayuwarsu bayan yayi yayi ta tafiyarta tayi aure inda za’a Bata haqqinta na aure Amma taqi,
Har sakinta yayi so biyu akan tatafi Amma ta boye sakin tace Masa bazata taba tafiyaba itama batada lafiyar zata zauna dashi ahaka bayan tasan kwadayinta akansa kullum qaruwa yakeyi duk tana ganinsa
Shiyasa yake nesanta kansa da ita kada yaringa shiga haqqinta da yawa tunda Yana iya ganin tsananin sha’awarsa a tareda ita,
Gashi shi tunda yasan baida abinda zai iyayiwa mace yasa Koda Wasa ko kiss baitaba kwatanta yiwa kowace mace ba bare harya wuce Nan duk da likitansa Yana basa tabbacin sauki zaizo Masa Amma saiyana kiyayewa Dan saukin zai iya zuwar Masa da zazzafar sha’awa Mai qarfi da hadarinda idan ya fara sex da mace zaiyi wuyar iya barinta Dan Haka yake Kan magani da tsari sbd gujewa hakan idanma lafiyar zatazo tazo Masa alokaci na iya controlling kansa.
Sakin kofar dakin tayi tareda juyawa ta koma Palo bayan taja Masa kofar tunda ba’a tsaya Masa idan Yana shiri.
Baro saman tayi ta nufi bedroom dinta Kai tsaye da sauri ta lalubo wayarta ta kunna videos din data Saba kalla Dan ragewa kanta shaawa.
Gidan tsit yake sbd sanin Maigida na gari Dan Haka kowa ya kammala aikinsa ba matsala ya Adana kansa,
Bayan sallar magrib ya sauko palon sanye cikin wata lallausan milk jallabiya daketa kyalli
Qafafunsa sanye da slippers na D&g hannunsa ko agogo Babu sai qamshinsa dake mamaye palon cikin sanyi.
Sanin lokacin saukowarsa yasa Mss Na’ima fitowa cikin wani irin ado na wata purple Embellished Emboidery super datai Mata kyau sosai sai wani qamshi Mai qarfin gaske na turarukan daban daban take bugawa ga fuskarta Tasha simple kwalliya ta nufi dining room datasan can ya nufa
Kusan atare Suka zauna Kan dining din M Sarat ta matso tafara serving nasu abincin cikin girmamawa sbd itace Mai aikinsa ta tsawon shekaru tun Bai manyantaba take Masa aiki to yanzu yazama Bata aikinma saidai bada umarni wa masu aikin saidai hidimarsa Kam har gobe itace Mai Masa.
Shiru ya ratsa gurin sunacin abinci cikin nutsuwa da kamewa yake komai nasa shiyasa komai yayi abun burgewa da koyi ne wainda suke taredashi.
Bayan Gama cin abincinsu palo yadawo ya zauna Dan bawa Mss Na’imah lokacinsa itama.
Kusa dashi sosai tazo ta zauna tareda Kai hannayenta ta Dora akan nasa Dake Kan jikinsa ta zuba Masa fararen idanuwanta tana sakin murmushin Jan ra’ayi a yangance da son Jan hankalinsa tace”
Amma dai zamu kwana biyu anan kafin ka wuce Abuja?
Dan waiwayowa yayi ya kalleta batareda ya motsaba yayi Mata kallon minti biyu kafin ya maida kallonsa kan tv cikin kamewarsa da Dan sakewar fuska tunda ita din iyalinsace a gajarce yace”
Gobe Zan wuce Abuja da yamma.
Marairaice fuska tayi tana sake shigewa jikinsa tace”
Please Turaki ka qara ko kwana biyu ne kafin zuwa abujan,
Idan muka koma gobe kana zuwa can bazakai lokacin hutawarmu ba.
Ki zauna anan idan nagamo daga Can kafin nakoma zanyi kwana biyu anan bayan tafiyata din saiki koma Abujan.
Ba Dan tasoba tace”
Ok Amma dai zanbika Abujan Kuma idan zaka dawo nasake biyoka.
Kallonta ya Dan Kuma waiwayowa yayi sbd yasan tsoronta akan zuwansa bada itaba baifi akan maganar qarin aure da Anne keson yayiba ko zai samu haihuwa.
Juyar da idanuwa tayi tana kokarin boye yanayin data shiga din Dan kuwa har cikin ranta Bata qaunar kebewar Anne da Turaki tunda tasan zancen dai daya ne na qarin auren.
Wani irin lafiyayyan murmushi ne dayafi komai kasheta yasaki Yana dauke kansa daga kallonta yabarta tana qarasa zubewa ajikinsa Dan kuwa murmushin abune dabai cikayiba Amma yanayi din sosai.
Har qarfe goman dare Yana tareda Ita yabata lokacinsa sosai kafin buqatunta suka biyo baya inda ta wawashi kudi masu matuqar yawa agurinsa Wanda dama ita sune suka riqeta a auren.
Sai daya rabu da Mss Na’ima kafin ya nufi office room dinsa na cikin gidan inda A Abdoul ke jiransa da tarin bayanansa
Yana shigowa kuwa A Abdoul din ya miqe Yana Masa barka da fitowa kafin ya zauna Kan kujerar 1 seater dake facing din A Abdoul ya miqa hannu ya karba iPad din Dake hannun Abdoul din Yana duba bayanan.
Sai dare sosai ya fito ya ta kofar Dake palon qasan ya nufi sama ya Haye
Kai tsaye ya nufi bedroom dinsa.
Washe gari qarfe Tara an kammala komai na breakfast din gidan an jere sai qarfe goma yasauko sanye cikin Ash Kaftan na babban yadin Ambassador sai hular qube
Hannunsa sanye da agogon _Chanel_
Take qamshinsa ya gauraya palon kallo daya A Abdoul da M Sarat sukai Masa Suka sauke Kai ganin Mrs dinsa a gefensa sai wani Jan girma takeyi cikin nata adon.
Breakfast yayi tareda Ms Na’imah da A Abdoul kafin ya fito zuwa Inda zai gana da baqinsa.
Qarfe biyu yagama da baqinsa yadawo gida yayi lunch tareda Ms Na’imah kafin ya haye Bai fitoba sai qarfe hudu da rabi Ya sauko Kai tsaye suka shige mota zuwa airport dukkaninsu.
A jirgi ma hankalin Na’imah gabaki daya yakasa kwanciya Dan ita harga Allah ma rashin zuwan Turakin yafi Mata kwanciyar hankali akan zuwansa
Dan zuwansa kullum cikin sakata fargaba yake,
Kishinsa take sosai sbd bazaso akaro wadda zata tayata cin wannan dukiyarba.
Umma Jamila kasa nutsuwa tayi ta ringa addabar Haj Karima Saida suka sako Kawu saidu da Kira Kan Kira ya shiryo ya taho sbd matuqar ba yana garinba Turaki yazo yatafi to fa Babu wata maganar aure bayan sukam tuni suka hau Shirin aure gadan gadan batareda lissafin komaiba ko tunani irin na masu shekaru,
Koda Kawu saidun ya iso daga nijar ya sauka a dakin Abba sosai yashiga mamaki da takaicin ganin halinda Laylah ke ciki sbd shikam kallo daya yayi Mata bayan Sa’adah takawota sun gashesa ya fahimci batada isashiyar lafiya Dan kuwa ko dagowa ta kallesa bataiba kanta a qasa ta gaidasa.
Abinci kawai yaci yayi salloli ya wuce asibiti gurin Dan uwansa yabar gidan
Yana fita kuwa saiga Alhaji Atiku da Umma Jamila sunzo gurinsa Basu tarar dashiba Dole suka koma da niyar dawowa gobe Dan subarsa yau din ya huta.
A asibiti kuwa tunda yayi ido biyu da Dan uwansa take jikinsa yayi Sanyi Dan baiyi zaton Jikin yayi Munin hakanba take qwallar tausayi Dan uwa taciko idanuwansa ya hadiye Yana jinjina Kai Yana sauraron bayanin yanda Abban yaketa fama da jikin duk tsawon lokacin Nan daga Abdullahi…
Shiru Abdullahin yayi yanason sanarda kawun wasiyar Abban na bawa AB TURAKI auren Laylah ko bayan ransa Yana shakkar Shiga zancen sbd sanin maganace Mai girman gaske tunda aure ake magana
Auren Kuma da mutum kamar Turaki,
Shi daza’a basa auren Laylah dinma da wlh Yanaso ya karba.
A asibiti Kawu ya tarewarsa Bai sake komawa gidanba ya zauna jinyar Abban Abdullahi yasamu hutu duk da kullum da daddare saiya leqo asibitin kawowa Kawun abinci duk da Babu wata wata daga gidan umma Jamila ake kawo Masa abincin safe Rana dare Kuma abincin Alfarma lafiyayye Wanda tun Kawun Bai kawo tunanin komai aransaba yafara tunanin akwai dalilin hakan Dan Haka ya zuba musu ido yaringa cin abinda Dan yasan Umma Jamila batada Tausayin bawa Dan uwan Mahmoud ko abunda bataso matuqar ba babban daliline garesuba Mai matuqar mahimmanci.
Ganin dai Kawun baida niyar dawowa gida bare suzo ayi magana dashi yasa Suka yanke shawaran haduwa dashi a asibiti Dan Haka yau da daddare Yana zaune bayan yadawo daga masallacin asibitin sallar ishai yaci tuwon semo da miyar kubewa da gandar da aka kawo Masa tareda fruits
Gamawarsa kenan Yana kokarin amsa Kiran Mai dakinsa daya shigo wayarsa saiga Alhaji Qarami tareda Alhaji Atiku da umma Jamila sai Haj Karima data iso a jiya sunshigo sanye cikin shigar Alfarma,
Miqewa yayi cikin sakewar fuska Yana cewa”
Marabanku da zuwa,
Alhaji Qarami bismillah ku qaraso daga ciki,
Alhaji Atiku barka da zuwa
Sannunku sannunku
Yanzu da Daren Nan kuke shigowa.
Haj barkanku da zuwa Bismillah ku shigo,
Hannu ya miqa musu sukai msabaha Yana sake gaidasu cikin mutuntawa duk dai ya girmesu saidai kasancewarsu manyan mutane yasa shine yafara gaidasu din Suma cikin mutuntawa fuska asake suke gaidasa tareda maida kallonsu Kan Abba cikin alhini suke tambayar jikinsa,..
Allah yakawo sauki da afuwa yasa kaffarane.
Amin Amin ya Allah,
Alhaji Atiku Naga hidima anatayi damu
Allah ya Sanya alkhairi yabada Lada
Ana kokari sosai wlh
Ngd Sosai Haj Jamila.
Bakomai Kawu saidu ai duk yiwa Kaine musamman kaida kabaro iyali kazo nesa gashima bamu samu lokaci anyi maganar datai dalilin zuwan naka.
Gyara Basu gurin zama Kawun yayi Yana zama shima kafin ya nutsu Yana kallon Alhaji Atikun yace”
Eh wlh to nazo na tararda jikin na Mahmoud ba sauki ba sauyi shine hankalina duk ya koma kansa Amma ai tunda maganar aurece ba wata damuwa duk lokacinda magabatan yaron suka tsaida ranar zuwa sai a sanar Dani naje saimu taru a tattauna din….
Kallon Alhaji Qarami sukayi sbd shi Basu fada Masa ainihin gskiyar zancenba Dan bazai taba yarda da hakan ba
Haj Karima ta karbe zancen da cewa”
Aure Kam ai magana na hannunka Dan kaine Wanda zai tunkari Wanda aka bawa auren da maganar auren kasancewar Kaine tamkar uba agareta tunda Kaine tamkar uba ga mahaifin nata Dan Haka komai a hannunka yake.
Murmushi Kawu yayi Yana jinjina Kai yace”
Hakane,
Inshallah Allah wannan aiba wani matsala bane,
Auren ne manemin Bai tashiba kokuwa?sai anemesu muyi mgn dasu….
Alhaji Qarami ne ya gyara zama Kai tsaye cikin nutsuwa yace”
Alhaji Mahmoud ne kafin Allah ya sako Masa wannan jarabawa a kwanakin baya yabar wasiyar bada auren Sa’adah ga Aminsa AB TURAKI Wanda kasani,
To ita yarinyar yanzu akwai masu neman aurenta da har mun amince anbasu saigashi Kuma Haj Karima takirani akan a dakatar da waincan din sbd yarinya mahaifinta yariga yabada ita ga Amininsa shinefa Muka dakatar da waincan sbd Afaraji ga Turakin idan ya amsa shikenan sai adaura aure abawa waincan hakuri
Idanma akasin hakan aka samu kaga dai anfita haqqin wasiya sai abawa waincan dama sukuma fitowa sai ayi dasu wannan shine taqamaimai dalilin kiranka Alan kazo Dan kuwa Babu Wanda yafi cancanta yabada aurenta Kamar Kai
Hakama Kaine kafi cancantar neman AB TURAKI da maganar sbd ba huruminmu bane mu dangin uwa.
Shiru Kawu saidu yayi Yana jinjina Kai cikin Dan mamakin zancen Yana juya zallar tazara dakuma banbancin rayuwar Dake tsakanin AB TURAKI da Sa’adah din
Saidai tunda Allah Bai haramtaba ba illa bane face qarfafa tare dakuma bawa yarinyar rayuwa Mai kyau a gaba duk da Laylah ce tafi cancanta da hakan ko Dan maraicinta dakuma shaquwar Turakin da mahaifiyarta zaifi Mata riqo na gaske sbd uwarta.
Numfashi ya sauke ahankali Yana sake jinjina Kai ya dago yace”
Babu illa Inshallah zanyi magana dashi saikuyi hanyar da zata hadani dashi din sbd Baya daukan waya sai dace.
Wannan ba matsala bane Inshallah zamu saka lokaci saimuje gabaki daya can Abuja har gidansa sai ayi maganar sbd Inshallah Ana saka ran shigowarsa gobe.
Kawu dai zancen yazo Masa wani iri Amma tunda maganar aurece zaije din bakomai bane dama shine Kamar waliyin su Sa’adah din yanzu tunda mahaifinsu ga yanda Allah yayi dashi.
Da zasu tafi kudi sosai suka bawa Kawun Amma yaqi karba yace bazai karba ba hidimar abinci kawaima da akeyi dashi ya isa.
Haj Karima da umma Jamila sai Alhaji Atiku dasukasan gskiyar lamarin zukatansu cike suke da farin ciki da qaguwa har suka Isa gidajensu
Kawu kuwa dayake mutum ne Mai maimaicin zancen bayan tafiyarsa zaunawa yayi yanata sake juya lamarin har Abdullahi yazo Nan yasake bayyanarda zancen ya Dora da cewa”
Ina shakkar son abun duniya irin na zuriar Zainab idan basune sukeson ingizani Kai zancen wasiyar da babu ba mutuncina da Turaki yake gani ya zube
Dan kuwa Ina mamakin Ta yanda Mahmoud zai bawa Amininsa daya Isa haihuwar yarsa so dubu aurenta batareda laakari da komaiba
Hakama tayaya yake tunanin Turakin zai karba auren Shi Dana mazauniba,hakama baya haihuwa…….
Shiru Abdullahi yayi Yana sauraron Kawun yanason magana Yana Hana kansa
Jin dai Kawun nata nanacin zancen yasashi bude Baki a natse yace”
Dan bada Aure kam Abba yabada aure ga Turaki Kuma yace wasiyace acikamasa ita Amma dai Kam ba Sa’adah ba……
Kawun Bai gama gane qarshen zancen Abdullahin ba yace”
To Allah yasa Turakin yasan da zancen Dan zaifi sauki da mutunci akan nine zanfara tunkararsa da zancen,
Tabbas nasan Akwai alqawarin hada zuria a tsakaninsu saidai ta ‘yaya waya sani Ashe ba yayansu zasu hadaba Matar Turakin ce zata fito ta tsatson Aminin nasa,
Wannan da Laylah ce amaimakon Sa’adah da sainace Rabon aurensa da itane yasa ya tsaya tsayin dakan auren uwarta da ubanta harma shine ya biya sadakin.
Shiru Abdullahi yayi Yana sauraron Kawun kawai sbd fahimtar ba sauraronsa zaiyiba bare ya fahimci zancensa sbd ya tsinke da zance.
******
Kwana biyu da zancen suka kwasa zuwa Abuja
Suka fara sauka gidan Haj Karima sukaci abinci suka huta tareda salloli sai dare sukai Shirin zuwa gidan Turaki,
Da Alhaji Atiku da alhajin qarami sai Haj Karima umma Jamila dai bata biyosuba sai Kawun.
Da farko ko babban gate din farko da qaton gidan ba’a Bari sun qarasa ba bare shiga ciki su Isa gate na biyu Wanda dagashi sai harabar gidan.
Daqyar Suka samu ganin A Abdoul wanda tashin farko ya sanar dasu cewar Turaki yariga yashige Yana sashen Mahaifiyarsa wadda idan Yana can bamai Kuma ganinsa Dan Yana jimawa sosai daga can Yana fitowa yake shigewa.
Neman appointment din ganinsa gobe sukai ya sanar dasu cewar goben akwai tafiya Mai mahimmanci a gabansa Wanda zaiyi tareda Mahaifiyarsa.
Sunajin hakan Alhaji Qarami yace”
Idan harda Haj Anne zaiyi tafiya Inshallah ba tantama gurin duba Mahmoud zasu tafi sbd Babu zuwan dayake batareda itaba itama ta dauka Mahmoud tamkar ‘da.
Duk da hakan Dan karsuyi tsammanin daba shiba
Kawu ya kalli A Abdoul cikin nutsuwa yace”
Kayi hkr ka kirasa a waya kokuma kakira Haj Anne a waya kace Kawu saidu ne na Mahmoud.
Shiru Abdoul yayi Yana ganin girman Kawun sbd Kiran kansa da yayi a Dan uwan Alhaji Mahmoud Wanda yariga yasan irin Aminci Mai girma dake tsakanin Alhaji Mahmoud da Turakin duk da daga baya yasan labarinsu shida Turakin
Ta wani bangaren Kuma Yana jinjina tsari da kaidar Turaki Dan Haka ya kalli Kawun cikin Yar mutuntawa yace”
Kayi hkr Kawu gskia bazaku samu ganinsaba daga yau din har goben,
Amma idan har Yan uwan Alhaji Mahmoud ne ku taimako daya dazan bada shine ku koma gida ku jirasa sbd zuwansa duba Alhaji Mahmoud kamar kaidace da baya takewa.
Shiru sukayi dukkaninsu suna kallon makeken gate din gidan Da securities ke gadi Babu alamar zasu iya barinsu Shiga Koda kuwa da sakon mutuwar Mahmoud din sukazo bare,
Dan Haka sukaiwa A Abdoul din godiya suka juya
Tsabar Babu Jin dadin rashin damar ganinsa Tun a Daren sukai booking tickets washe gari qarfe Tara na safe suka biyo jirgi Suka dawo gida.
Tunda suka dawo shi kansa Kawun yakasa nutsuwa gida yakeson komawa Amma sun hanasa
Dan Haka a matse yake Kuma takure dason komawa.
Ganin wannan bazata fishesaba yasa abdullahi ya dauko Masa wayar Mahmoud din aka saka caji yace a Nemo Masa numbern Turakin Akira masa.
Kira Kan Kira Amma Bata Shiga Dan Haka Kai tsaye yace anemo Masa numbern Haj Anne Akira masa.
Cikin sa’a kuwa tata wayar tashiga Dan haka ya karba tareda nutsuwa yana jiran ta dauka.
Harta tsinke ba’a dagaba Yana Shirin sake Kira saiga kiranta yashigo wayar Kai tsaye ya dauka cikin tattaro nutsuwa da mutuntuwa yace”
Assalamualaikum
Haj Anne muna lafiya?
Ya gida?da iyali da Turaki?
Duk kowa na lafiya?
Cikin wata irin murya Mai tarin nutsuwa da Kamala tareda zallan ilimin bokonta Dana addini dasuke bayyane ciki lafuzanta tace”
Amin w slm,
Malam saidu ya gida ya iyali?
Lafiya kalau Alhmdlh Alhmdlh,
Ya Turaki? Ance Yana qasar nazo shekaran jiya bansamu damar ganinsaba Jamian kofar gidan sukace yariga yashige Kuma washe gari tafiya zaiyi
Sai kawai muka juyo Muka dawo..
Da mamaki a sautinta tace”
Subhanallh
Lallai ansamu kuskuren rashin sanine da tabbas Turaki bazaiqi ganinkaba kuwa duk uzurin Dake gabansa.
Hakane,shiyasa ban takura akan saina gansa din ba nabari idan yasamu zuwa duba Mahmoud ne sbd maganace Mai mahimmanci yasa naso ganin nasa.
Cikin bada hankali Haj Anne tace”
Allah yasa lafiya dai?
Ko jikin Mahmoud dinne?
Akwai wata matsala ne?
Zaka iya fadamun.
Numfashi ya sauke cikin sake nutsuwa da abinda zai fada yace”
Wata babbar maganace anan da Mahmoud yabar wasiyarta wadda na takeda Dan tsauri.
Uhmm Ina jinka..
Mahmoud yabar wasiyar cewa yabada auren ‘yarsa Sa’adah ga Turaki Wanda daga hakan Allah ya tsananta yanayinsa yake cikin halin Rai da mutuwa dayake ciki ayanzu,
Babban dalilin dayasa nazo neman Turakin nayi maganar dashi shine ita Sa’adah din ta Isa aure manema Bata zuwar Mata Amma anqi Basu dama sbd wasiyar Mahmoud din,
Da nazone naji daga bakinsa idan zai karba auren kokuma abawa wasu damar aiko nasu magabatan.
Shiru Anne Tayi tana juya zancen cikin ranta,
Duk da zancen yazo wani iri sbd banbancin shekaru masu yawa dakuma yanayin rayuwar Turakin da baya son mace cikin rayuwarsa shiyasa yakeda mace daya ita dinma daqyar yayi auren bayan ta nuna bacin ranta to tayaya zai iya qara wani auren da qanqanuwar yarinya ma?
Ta wani bangaren Kuma tunanin Mahmoud din tayi tasan bazai taba barin wannan wasiya Mai nauyi hakaba Babu dalili Mai kyau
Hakama batajin akwai wata buqata ko Alfarma da Mahmoud zai nema agurinta ko Turaki su kasa cika Masa ita ko wace irice matuqar Bata Saba addini ba Dan Haka Kai tsaye tace”
Allah yabasa lafiya yasa Munada rabon shaida wannan Alkhairi daya qulla ko acikin ciwo,
Inshallah Aure Kam an karba Allah yazaba Mana abinda yafi alkhairi
Zan sanarwa da Turakin da kaina saidai shi din ba mazauni bane kamar yanda kuka sani Dan Haka idan har aure za’ayi saidai ayisa kafin yakoma cikin satin nan
Saiku shirya Inshallah idan zamuzo duba Mahmoud din zamuzo da komai sai ayi agama ba Abu bane daza’a Tara duniyaba inaga ayi al’amarin a saukake kawai abada Matar.
Godiya kawu yashiga zubawa Yana kori mata addu’a sbd dama can yasan Haj Anne macace Mai kaifi daya kamar namiji Bata Wasa kai tsaye take komai na rayuwarta shiyasa takeda matuqar girma da daraja agurin manyan mutane da dama.
Labari na isarwa su Alhaji Atiku da umma Jamila take dangi kowa yaji Wanda Sa’adah zata aura hayaniya ta kaure ko Ina ya dauka a dangi masu murna nayi masu baqin ciki nayi,
Su kam masu abun tuni aka hau fara shirye shiyen auren duk da dai auren kawai za’a daura Haj Anne tace basa buqatan hayaniyar biki
Gashi idan sukazo za’a daura auren su tafi da ita sai Yan rakiyarta su umma Jamila.
Hankalin Sa’adah yaso tashi Sosai Jin Wanda zata aura saidai hankalinta Bai qarasa mugun tashiba Saida taji umma Jamila suna maganar da Momy a daki cewan Laylah Abban yabada ba itaba sauyi sukeson Yi da ita take jikinta yayi Sanyi Takoma daki ta zauna bakin gado gefen Laylah Dake zaune tayi zuru.
Kallonta Sa’adah tayi take Idanuwanta suka ciko da hawaye ta riqo hannun Laylan Ahankali ta furta”
Bazan taba karban abinda yake naki ba nawaba har abada Laylah.,
Duk da bakida lafiya Zan tsaya tsayin dakan kin zama Matar mijinda Abba ya zaba Miki Amma ta Yaya zakije wani guri rayuwar aure a Haka bakida lafiya,
Bakida sabo,
Baki tana zuwa koinaba arayuwarki.
Washe gari ba kunya aka dauko masu gyaran Amarya takanas Dan fara gyaran Sa’adah
Ta rufe idanuwanta ta tsaya akan bazata yarda da gyaraba bare auren matuqar baza’a yarda da buqatarta tason zuwa da Laylah ba.
Umma Jamila da Haj Karima sakin Baki sukai suna kallon tsabar taurin Kan Sa’adah din,
Umma Jamila ta hauta da fada tako Ina Rai abace
Sa’adah kuwa ta kafe harda saka kuka
Haj Karima dataga suna Shirin rasa hamsin Kan biyar tace sun amince taje da ita Amma idan tayi kwana biyu zata dawo da ita gida.
Kai tsaye tace ta amince da hakan aka rufe zancen aka fara shirye shiyen biki Wanda Amaryar take matseda ganin Kawu Wanda Kiri Kiri Umma Jamila ta hanata ganinsa qarshema dauketa tayi daga gidan tamaidata gidanta aka bar Laylah da kadaici.