RAINON Y’AN HUD’U CHAPTER 3 BY Khadijat M Abdullahi

RAINON Y’AN HUD’U CHAPTER 3 BY Khadijat M Abdullahi

Www.bankinhausanovels.com.ng 

_____________Umar ne ya shigo hannunsa niki _niki da kaya, Goggo Na washe baki ta ce” A’a Ummaru har an fara yin hidimar, Ai ban sani ba ,da mun tafi tare ” Umar na dariya ya ce” Haba Goggo, ai yanzu na manyanta ,tunda na zama Baba, Abba dai bai ce Komi ba, Momy kam dariya tayi ta ce” Goggo!!! 

    Goggo na murmushi ta kalli Hanne ta ce” Mi kike so nayi, kamar y’an Hud’u ?

    Momy na dariyar mugunta ta ce” Goggo Dama zan fada maki ne, mu zamu koma dani da Abbansu, gobe Insha Allah Sai mu dawo, tunda dare ya fara yi “

    Goggo bata yi musu ba, saboda nama da taga an siyo min “Nan dai Momy suka koma ita da Abba, aka bar Aunty Bilki…

Zama Goggo tayi tana tande baki ,ta ce” Uwar y’an Hud’u, ya jikin ?

  Banza nayi da ita, na fara cin nama, ina satar kallon Goggo, Jarirai kam Sai kuka suke tsallarawa, Umar ne ya ce” Sahibata in kingama, ki basu abincinsu ?.

    Kukan shagwa6a Na fara yi na ce” Haba Habibi, taya zan shayar da yara har guda hud’u, lallashina ya farayi, na kam tirje idona na ce” Ban San wannan ba, Goggo najin muna rigama, ga yara sun damemu da kuka, ta ce” Dan Allah Farida ki taimaki yaran nan ?

    Zun6ure baki nayi na ce”Haba Goggo ni gaskiya bazan iya ba,ga C.S in da akai min ina Jin zafinsa, ga rigimar wa’yannan yaran, a gaskiya na gaji…..

    Umar ne ya fara marairaice min ya ce” Sahibata !!! Ni ma Na ce” Sahibina 😂😂😂

Kallona yayi da Yarinya a hannunsa, ko daukaf jarirai bai iya ba, ya ce” ki taimaka min,Goggo ta ce” Haba Farida ke ki ka haufe su fa ?

  Gajiya nayi da maganar don haka, Na ce”Goggo ke ki basu susha mana ?

Zaro ido waje Goggo tayi ta ce” Rufa min asiri, taya ni zan shayar da y’ay’anki, bayan kinsan yanzu ina da shekara 60 🙆

       Aunty Bilki na jinmu ta kwashe da dariya ta ce ” Farida wallahi kuna da aiki, nan gaba …..

      Umar na tsaye , yara Sai rangwada kuka suke ,tunda suka fito duniya basu sha Abincin su ba, Likitaf dake duba ni ,tazo nan taga yara har fuskarsu tayi ja, ta ce” Sister mi ya hana ki basu Abincinsu ?

   Kallonta nayi da kyau ,sannan na ce” Kinga wancen ?

Kallon Umar tayi, sannan ta kallwni ta ce”Ee na ganshi, k’ara gyara zamana nayi na ce” tunda har yasan hanyar da yabi ya dira min ,cikin y’an Hud’u ? To yasan yadda zai shayar da yaransa 😂😂😂😂😂

     Ba likita kad’ai ba, hatta y’an jinuar dake gurin Sai da suka kwashe da dariya,😂😂😂

Goggo da tayi dariya har ta gaji, Umar ya dungura mata yarinyar ya ce” Sahibata Dan Allah na ce fa ?

   Ban kallesa ba, don haka ya fita yaje ya siyo madarar jarirai, ya kawo nan Aunty Bilki ta ce” ita abata ta had’a madarar, Goggo ta hana, ta ce “ita za abamawa, Shidai Umar bai ce Komi ba, y’ay’ansa kawai yake kallo ,don hatta fuskarsu ta fara canzawa, Goggo da tasami abinda zata had’a madarar, ai kuwa ta zauna tasha iya rabonta, sannan ta kawo sauran madarar, ni dai ina daga zaune ina kallonsu, don wallahi yadda naji wannan wahalar Babu Wanda zai min waazi na saurare shi, Goggo ta fara tallabo yarinya guda, tana Dura mata madara, Aunty Bilki ma ta dauki guda tana bata, Oga Umar ya zauna, ya fara tattare hannun riga da Na wando ya dauki sauran biyun, nan ya fara Dura masu madara ,idan ya juya damarsa ya bama guda ,Sai ya juyo haggu ya bama dayar , aikuwa dani da nurses in dake gurin ,muka kwashe da dariya,donma Allah ya rage ma Aya zaki, C.S in da akai min shi ke hanani kwasar dariyata, Umar Na kallona ya ce” Zaki yi ki gama nima ina da lokaci, Wàta ran Sai nayi dariyar da tafi ta’ki, ba dai RAINON YAN HUD’U ba ??

   Gwalo nayi masa Na ce” naji dai….

Da daddafe bayan duk mun kwanta, Jarirai suka farka, nan suka fara aikin kukansu, kuma kamar suna had’a baki,lokaci guda suke tsallarawa kuka, nan Na tashi zaune ina kunkuni, ko ba komi Y’ay’a nane,doli naji kukansu har cikin raina, Goggo na gani kwance Sai gurnanin bacci take, Na mangare Mata Kai. Figigit ta mike tana wani zare ido da lasar baki, ta ce” Farida naman ne ?

    Tsaki nayi na ce” Dan Allah Goggo ki tashi ,wa’yanna yaran sun isheni da kuka😥

    Baki Goggo ta Saki ta ce” lallai kam wagga Yarinya da ni kike zancen, dama akan wa’yannan yaran ki ka tayar dani ,dai_dai lokacin da aka mikomin kaza?

    Amma Wallahi Farida kin iya kwashe Na mutum Albarka ..!!!

    Aunty Bilki najin Dramarmu ta tashi nan ta duba fidar jariran taga wayam bakomi a ciki, ta ce” Lalala yo Farida !!! 

    Wa ga shanye madarar ?

Zumut nayi ,don ni Nama manta da wani ciwo a jikina ,na ce” Bangane ba ?

Anshanye madara, to waye yayi wannan taasar ? Goggo na wu’ki_wu’ki da ido ta ce” Ai Farida tun jiya na d’an_d’ana madarar naji dadinta ,shi ne fa yunwa ta tasarmin ,Na shanye sauran …

    Zugum_zugum muka yi ni da Aunty Bilki ,nan na dinga janyosu d’aya bayan d’aya ina shayar dasu, ko mint 10 ban iya barin suyi ba nake janyesu, haka suka gama aha ina Jin radadi da azaba, har cikin raina….

    Gashi Dama Na barsu da yunwa tunda suka fito duniya, Abu kamar had’in baki suke yi,duk Sai da na jigatu, Ai kuwa daga lokacin Na canza Na madarar yaran ,gurin ajiya…

    

    

    

    *WASHE GARI*

Ina cikin Jin dadin baccina, likta ta tayar dani, wai na tashi an sallame ni , nayi mamaki matuka, saboda ni dai a sanina Sai mutum yayi kwana ukku ake sallamarsa, Umar ne ya shigo da Yarinya a hannunsa ,ya ce” Farida taso mu tafi gida …..

    Tura baki nayi na ce” Haba Habibi nifa ban warke ba, taya za ace mu tafi gida?

    Wata nurses ce ta ce” Ke malama Dan Allah ki tafi an sallameku, taya zaku zauna da yara suna damun mutane da kuka ,A’a…..

    Tashi nayi ,jiki a sanyaye na ce” Ke Dan Uwarki, ki bar ganinki a matsayin likita ,kema macce ce kamata ,kuma y’an Hud’u Allah ya baki, Sai Naga ta karyar baki son kukan jarirai..mtsww tsaki nayi zan k’ara Wàta maganar, Umar ya janyo hannuna ya ce” Farida ki rufa min asiri, da ciwon dake jikinki zanji ,ko da rainon y’an Hud’u ?

    

    

    

*SANARWA ! SANARWA !! SANARWA !!!

Ina masu son karanta littafin (Khadijat M Abdullahi)…..

Marubuciyar ….👇🏻👇🏻👇🏻

*Rayuwar Deejart*

*Muna tare duk Runntsi*

*Mahaifiyar Abbana*

*Y’an Matan zamaninmu*

*’Kasata*

*Auren D’an Garuwa*

      Auren D’an Garuwa…yazo maku da salo kala_kala, zai nishadantar daku fadakar daku da kuma waazantuwa akan darasin rayuwa…..

Yanzuma na zo maku da wani sabo,Wanda zaisa ku nishadi da ban dariya so sai, Mai ta Ken suna *RAINON YAN HUD’U*

Y’ar’uwa ki garzayo kar ki bari a baki la
bari…

Don wallahi Babu karya idan ki ka karanta littafin *RAINON Y’AN HADU  Sai cikinki ya ‘kulle, …….

 *za ki biya kud’inki akan wannan details in…* 👇🏻👇🏻👇🏻

] DEEE: *Zaki turo 100 ta wannan account numbern 0070 457868*

*Aisha Abdullahi Mustapha

Stealing bank*

*Idan kika tura sai ki turo min shaidar biya ta wannan numbern 07064909708 da zarar na gani zanyi adding ɗinki a paid group*

 *Ga masu turo katin waya kuma hoton katin zaku ɗauka ku turo min ta wannan numbern 07064909708 Please banda VTU idan kikayi VTU kinyi asarar kuɗin ki babu ruwana hoton kati kawai zaki ɗauka ki turo min*

[ DEEE: *in kuma documents ki ke so gaba d’aya, Sai ki biya 300 ta wannan account in 0070457868 Aisha Abdullahi Mustapha Stealing bank*

Normal group =100

Vip group =200

Special group=300

________________________________

    

    

    By 

Deejart M Abdullahi….

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *