RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 13

RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 13

 

 

ya nafi dakim Nafisa sai ya tuna yau a gurin Salma

yake. Ya juya ya nufi dakinta.

Tana kan Darduma a can kuryar dakinta, tunda

tayi sallah ta kasa tashi, ga faduwar gaba don

lokaci-lokaci sai ta dafa Kirji. Matuka ta tsorata da

fushin Shatima, har yana fadin zai mata duka!

Tana jiyo sallamar Shi tsoro da fargaba suka

hanata amsawa. Ya aje• hularshi a kan kujera ya

nufi kicin. Ya dauko goran ruwa guda daya, ya zauna.

Duk da babu sanyi da ya daga sai da ya sha fin

rabi, sannan ya aje goran. Yayi ajiyar zuciya. Ya

dauki wayarsa ya kira Nafisa, tana dagawa ya ce ta kawo masa jakarsa nan dakin Salma.

Babu-gardama Nafisa ta dauko ta nufo dakin

Salma. Da alamu wannan bacin ran na Shatima ya

saka matan nashi, shiga taitayinsu, musamman

Salma.

Tayi sallama a Rofar dakin ya daga murya ya

Ce Shigo mana, kin coge kamar wadda za a cinye

ta.” Ta shiga ta mika mishi tare da fadin “An www.dailynovels.com.ng dawo

lafiya?” Ba tare da ya kalleta ba ya ce, “Lafiya?”

Ta wurga, ido tana kallon falon Salma, cikin

mamaki duk da take ji a family ana cewa su Salma

matsiyata Ne bata yi tsammanin tsiyar har ta kai

haka ba.

Ta taba baki tare da fadin “Uhum!” Ya dago

daga kokarin da ya ke na ciro Laptop a Jaka ya ce,

“Ya ya?” Ta girgiza Kai tare da sake kallon dakin

ta ce, “Babu komai,

‘ Ya ce, “To kina iya tafiya.

Ya fahimci dakin take ma wanna yatsinan.

Salma da ke ciki tana jin su. Lokacin tana ta

shawara a kan ta fito ko kar ta fito? Jin fitar Nafisa

sai ta yi ta maza ta fito.

Cikin tafiya tamkar Wahainiya ta nufi kicin. Ta

dauko Tiren da ta jera kuloli guda biyu, daya farar

shinkafa daya miya. Sai dan karamin kwanon silba

da ta zuba naman yau farfesun shi tayi.

Ta bude dan kwandon da ta yanka ganyen latas

da kokumba, shima ta dora.

Ta.zo ta dire tiren, kan ya zube ma saboda

yanda jikinta ke Bari ta sauke daga tiren ta jere, ta

koma ta dauko cokali da plate, da goran ruwa da

kofi.

Ta dago da niyyar tambayarshi ta zuba.

mishi, sai suka hada ido. Cikin sauri ta sadda kanta har da dauke numfashinta. Domin ta zaci zai

antaya mata mari ne.

Jin shiru ta sake dagowa. Muryarta na rawa ta

Ce.

“Yaya in zuba maka?”

-Na koshi.

* Ya fada a

daKile. Da gudu ta mike kuma a rikice zata yi

daki, tamkar ya kwashe da dariya sai ya dake ya

ce.Ke” Kamar zata saki fitsari ta tsaya cak

amma ta kasa waiwayowa.

Ya ce,

“Zo nan ki kwashe kayanki, ko nine zan

kwashe miki?”

•Ganin rawar jikin tata zubar da abincin a Rofar

kicin, da rasa me zata yi sai ta fashe da kuka. Yana

kallonta yayi murmush: ya dauke kai Ta kwashe www.dailynovels.com.ng

ta kai kicin, tazo ta haye gado ta kudundune.

Lokacin ne Shatima ya samu dama har ya yi

dariya sosai. Sai kuma ya ji zuciyarsa tayi masa

sauki. Ya yarda da batun Likitoci, da suka ce

dariya tana rage damuwa.

Yana bude aiki zai fara, sai •yaga sakwanni a

Emel din sa. Tun karfe uku sakon ya shigo cikin

akwatinsa, suna da meeting a Abuja karfe tara na

safe.

Yayi hamdala da yaga sakon yanzu, da sai da

safen zai gani.

Dole Zai yi bukin din jirgin safe na karfe

takwas.

Salma bata yi bacci sosai ba, tana jin Shatima

ya shigo har da gyara mata kwanciya. Tana jin shi

yayi alwala ya tada nafila.

Da asubahi ta tashi tayi sallah, ta fito zuwa

kicin. Kan sallaya

taganshi yana

karatun

Alkur’ani, irin dan Karamin nan.

Taje ta dafa ruwan zafi, sannan ta soma suyar

dankali kafin shida ta hada komai. Ta fito ta samu

ya fito wanka yana cikin dakinta yana saka kaya.

Tsam! Ya tsuke cikin suit bulu me duhu, rigar

ciki bulu me haske. Tayi saurin dauke kanta

lokacin da taga zai waiwayo. Ya iso gurinta, tayi

saurin tsugunnawa tana fadin, “Ina kwana?”

Ta dauke numfashinta jin bai amsa ba, kuma

bata yi zato ba sai taji an kama kafadunta an mikar

da ita. Idanunta a lumshe hawaye suna kwaranya.

Cikin taushin murya ya ce, www.dailynovels.com.ng

“Salma!” Ta bude

idanunta a hankali, sunyi jajir. Ya ce, ‘

“Wai kukan

me ki ke yi haka?”

Cikin rawar murya ta ce,

“Ban

san ranka zai baci ba, jiya wallahi da ba zan ce zan

bi ka ba.

Ba zaton shi ta sulale Kasa kan gwiwarta.

“Ka

yafe ni don Allah.” Ya zauna a kan kujera. “Tashi

ba kiyi min laifi ba, jiya ne raina yana bace ba

laifinki ba ne.

* Ya dauki hankicin shi da ke gefe

Ya share mata hawaye.

Ya ce,

“Tashi ki kawo min abin karin.

” Ta ce,

“Na kawo.

” Ta juya don hada mishi shayi. Yana

kallonta tun da ya hada shayi a gabanta, shi kenan

kullum haka take hada mishi babu kuskure

Suga da yake irin ta kwali yake amfani da ita ta san adadin da yake so. Ta

mika mishi, sannan ta sa cokali me yatsu ta ciro

mishi yankan Biredi guda,uku, tasa a cikin plate,

sannan ta aje mishi kwai da dankali.

Ya ce,

“Sannu da Rokari, kina Koari sosai

Ta dube shi “Na gode.

” Cikin jin dadi ta nufi kicin

don kammala kayan da ta yi aiki da su. Yana goge

baki da ‘yar takardar share baki. Ya ce, “Zan tafi

Abuja.

Ta dan ware ido cikin mamaki ta ce,

*Kuma

yaushe za ka dawo?”www.dailynovels.com.ng

Yace

“Yau insha Allah

Ya nuna mata dubu daya a kan kujera, “Ga kudin

namanki nan.

” Ta ce,

“To Allah Ya dawo da kai

lafiya.” Ya shafa kumatunta “Na gode.

Ya fita ta koma kicin ta ci gaba da aikinta. Ya

sallami sauran ya fita. Maigadi ya ce,

“Alhaji yau

motar babu lafiya ne?” Ya ce, “A’a zan hau Jirgi

ne zuwa Abuja, yanzu zan dauki motar haya ne.

YADDA ZAN FAHIMCI MUJINA

Na daya, na fahimci baya cin danyan kifi, na

biyu ba ya son a shiga huruminsa in yana cikin

fushi, na uku yana son komai a gaskiya.

Tayi murmushi da ta karanta, a fili ta ce,

*Insha

Allah sai na gama fahimtar halayensa.

* Ta tashi ta

maida littafin. Ta dauki kudin nama ta fita zuwa

grin Maigadi, sai aka kwankwasa Kofa

Yaje ya bude, cikin mamaki sai ta hango Yaya

Hadiza, cikin mura taje ta rungumeta. Ta dauki

Amira don murna. Yaya Hadiza ta ce, “Duk cikin

murnar za ki dauki wannan Katuwar yarinyar”?”

Da gudu ta dawo ta ba Maigadi sako ta Koma.

Hadiza ta ce “Kin gan mu sai yau ko?” Salma taCe Wallahi kullum ina ta kewar Inna, ya ba kuzo da ita ba?”

Tace

“Sai ta fita takaba sannan zata zo Suna ta hira, Hadiza tace

“Kin yi fari kin Kara dan

Tsawo, amma ba kiba. www.dailynovels.com.ng

Salma ta Ce,

kuma sai ina ganin kamar nayi Kiba.” Ta ce, ‘

“Kin

dai yi kyau, Kila Kibar sai nan gaba.

Ranar ta yini har yamma suna hira. Ta

ba Salma shawarar yanda zata dinga adana kudi

maimakon cin kilon nama kullum. Ta ce, “Na dari

uku ya ishe ki, sauran sai ki ke adanawa. Sai ki ga

kin tara kudin da za a gyara miki daki, duk abin da

babu a sai miki kafin Allah ya ba ki ciki ki haihu

mutane su zo.”

Salma tace

“Sai dai in tambaye shi in ya

yarda, don bana son in yi masa rashin gaskiya, na

kula ba ya son haka.

Hadiza tace Ke amma sakarai ce ko? Ance

miki maza suna son a rage musu kudin cefane

ne?”‘ Salma tayi shiru a ranta tace

*Don shawara

na dauka, amma sai ya yarda, kawai wataran ya

ganni da kudi ya ce ina na samo…?°

Hadiza ta katse mata tunani da cewa,

“Ke fa

har yanzu sakara ce ko?” Salma ta ce,

“Naji Yaya

Hadiza, zan adana.

“To ina ki ke zuwa

kitso?”

sai dai in dan kama da kaina in yi kalaba

Ta ce Ai da yake ma gashin naki ba shi da

zuciya, ko an yi banza da shi sai yayi ta hauka

Salma ta ce Shi ko Yaya ma da na ce ina son “

kitso sai ya ce ya fi son gashin a haka, sai dai in ina son a gyara min in mishi magana

Hadiza  www.dailynovels.com.ng

“To shi kenan, kin ko fara zuwa

Makaranta?” Salma ta ce,

“Nasan ya na sane shi

yasa bana mishi zancan

Da za ta tafi, Salma ta ce “Gashi bani da kudi

sai dari biyun Yaya da ya ce in aje masa, bari dai

in debo miki biskit su Amira sa ke zuwa

Makaranta da shi.

Hadiza tace

“‘In kuma yazo yaga an diba fa?”

Salma ta ce, “Nawa ne ya sai min har da alawa, shi

baya cin irin su.

” Hadiza tayi dariya tar da fadin

“Yar gata

Ta saka hijabi da nufin raka Hadiza har bakin

titi. Hadiza ta ce “A’a babu ruwana, kin taba yin

rakiya ne?” Salma ta ce,

“Ban taba fita ko wajen

Gate ba, Allah ina son in fita

Suna cikin jayayya sai ga wata bakar mota.

Shatima ya fito wani abokin aikinsa ya kawo shi.

Ya fadada fara’arsa.

“Sannu da zuwa,

” Ta ce,

“Yauwa Alhaji. www.dailynovels.com.ng

Suka

gaisa. Ya ce

“Ba dai za ki tafi ba?”

Tace

“Wallahi zan tafi ne tun safe nazo.

” Ya ciro kudi a

aljihun wandonshi ya mika mata.

“Ga shi ki hau mota.

” Ta ce,

“Da ka bar shi.”

Yace

“A’a ki amsa, ni na ba ki.” Ta amsa tare da

godiya. Salma ta kalle shi, “Yaya zan dan rakata

titi.”

Ba tare da ya kalleta ba ya ce,

“A’a, ki koma

daga nan.

Ta tsaya cak! Ta mika ma Hadiza ledar

hannunta. Ta ce, “Ki ce ina gaida Inna, ki bata dari

biyar cikin kudin da ya ba ki.

.” Hadiza ta ce, “Ko

ba ki ce ba zan bata. www.dailynovels.com.ng

Ta koma daki ta same shi a cikin dakin bacci,

yana rataye suit din shi a jikin madubinta. Ya ce,

“Wato za ki fita ba izini ko?” Ta ce,

“Ban zaci

zaka yi fada ba. Yace

“To ko waye ya zo ban amince kiyi

rakiya gaba da Gate ba.

Ta ce,

“To Yaya, insha

Allahu.

” Nan ma ta dauko littafin rubutunta, shima

ta rubuta, har ya kalleta ya fito bandaki.

“Me ki ke yi da littafin?”

Ta ce, “Ina yin ‘yan

rubuce-rubucena ne yace

“Yana da kyau haka.

To me ki ka ba Hadiza din?”

•Ta kalle shi “Ai bani

da ko sisi, sai kudin ka dari biyun ka da ka ce in

aje maka.

Yace

“Kuma a dakin ba ki da abin bata?” Ta

girgiza kai tareda dan tabe baki,

“Me gare ni Yaya, na dai ba; Yaranta biskit dina, tunda shi ai

ka ce nawa ne ko?”,

Ya cc, “Eh.” Tace

“Ka ji abin da Ya Hadiza tace?” Ya tattaro hankalinga garè ta  da tambayar.

“Me ta ce?”www.dailynovels.com.ng

Ta ce, “Wai in Rage siyan nama da

yawa sai in tara kudin, wai in sai kamar ,na dari uku nace sai na tambayeka in ka yarda

Yace to sauran kudin ayi me dasu? Wai in adana sai a siya min abinda bani dashi

Yace to ai ta baki shawara ne ni bani da matsala da haka in kina ra,ayin rage cin nama  kina iya yin hakan tace na gode yaya•Yayi murmushi,

“Sarkin

godiya. Gobe za a kawo form na Makarantar, ki.

Ba ta san lokacin da ta buga tsalle ba har ta kai

inda ya ke ta kuma rungume shi, tana fadin

“Na

gode Yaya.

Yayi dariya,

“Ki samu nutsuwa in

fada miki.”

Ta durkusa a gabanshi,

“To Yaya na nutsu.”

Ya ce Makarantar a nan Unguwar take kusa da

titi, sannan maza ne da mata, in kin shiga ki kama

kanki bana son kiyi abota da wadanda ba za ki

karu ba, ki sa kai kiyi abin da ya kai ki.”

Salma ta ce Insha Allahu zan kiyaye.” Ya ce

“Ban ce musu ke matar aure ba ce, kin ga ke za ki

HMMM LABARIFA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE

www.dailynovels.com.ng

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *