RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 14

RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 14

 

 

Nafisa ta tashi zaune, ta ce Hamida ta saka

mata pillow zata jingina. Ta ce “Hamida yanzun

Karfe nawa?” Ta ce,

“Tara na dare.

Nafisa ta CE

“Tabdi! Kin san wai me nike son ci?”

Hamida ta yatsina baki ta ce, “A’a

Ta ce

“Zogala! Ji wata fitina, ni da bai dame ni ba

Hamida ta ce

“Ni yanzun ina za a samu wani

zogala?” Nafisa ta ce,

“Kira min Ya Shatima.”

Yana dakin Aliya daidai lokacin da wayar tayi

ringing, ya zo daidai da lokacin da Salma tayi

sallama a dakin na Aliya, hannunta dauke da

littafin ta wanda za”a koya mata,

Aliya ta amsa, sannan Shatima ya kalleta bayan

ya dauki wayar yana duba suman. Zumbur! Ya

mike tare da daga wayar ya ce, “Nafisa!”

Hamida ta ce,

“Ni ce, ta ce kazo* Ya ce,

“To

gani nan zuwa.Ya kalli Salma

“Ya aka yi?”

Tace,

“Yaya dama assignment ne za a nuna mini.”

Ya kalli Aliya,

“Duba mata don Allah, bari in je

gurin Nafisa in ji

Aliya tayi

‘yar dariyar yake tace WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

“Sai ka

dawo, don Allah ka ce ina yi mata sannu.

Yana fita Aliya ta kalli Salma kallon sama da

kasa irin kallon wulakanci da raini, ta ce “Aka yi sati da Lahadi duk ba ki tuna da assignment ba sai

yanzun da ki ka ganshi a nan dakin? To bari in ja

miki kunne, duk ranar da yake dakina na haramta

miki zuwa.

Salma ta ce, “Anty don Allah kiyi hakuri, ina ta

tunanin yanda zan ma Yaya magana ne,

” Aliya ta

fizgi takardar tana dubawa. Salma ta cE

” Anty

bari ki ga yanda aka ce….

Aliya ta katseta da cewa,

“Da Allah ni yi min

shiru, ke ce za ki nuna min, tun kafin a haifi uwar

me alli Balbela take da farinta.”

Salma ta ce,

“Me ki ka ce?” Aliya ta ce,

“Tun

kina^yar mitsitsiyarki ni ke zuwa boko, kuma

muke rubuta maths.

Salma ta ce, “Yi hakuri.”

.” Don ta lura Aliyar

tayi maganar cikin fushi ne. bata koya mata ba, sai

dai ta rubuta ta bata tare da cewa gashi nan ni bani

da lokacin yi miki wani nune-nune.

Salma taje daki tana dubawa cikin kokwanto,

tana tunanin gaskiya da kyar in haka ne, amma

zata je da shi Makaranta ta nuna ma Salma

Dankasa

Shatima ya shigo,

“Ina Salman?” Ta ce,

“Nayi

mata ta wuce, yarinyar nan Allah Yasa dai tayi

karatu, naga dan abin da ta kasa ganewa,

ga takardarta duk ziro

Ya ce,

“To don Allah ki ke taimaka mata, sai a

hankali.

Aliya ta ce,

“Har Lesson na ce zan ke yi

mata.” Ya ce, “To ai ko na gode. Yanzu ina zan

samu zogala?” Ta ce, “Wake so?” Yace”Nafisa.Ce. WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Tace

“Gashi dare ya yi. Amma ka tambayi

Maigadi, in za’a samu danye sai a

dafa mata

yanzun ayi mata kwado.

Ya ce,

“Haka ne.

Maigadi ya ce, “Can makotan suna da shi

Sai gashi an samu, nan da nan Aliya ta zage ta

dafa, ta cE

“Sai kuma in da za a samu kuli-kuli

Nan ma Maigadin aka sake tuntuba. Shi ya bazu

cikin unguwa sai kusan sha daya saura ya dawo.

Kura-Kura aka samo. Aliya dai aka zage aka

daka, ta kwadanta mata. Nan ya

dauka ya kai

mata. Tasa a gaba kuwa tayi ta ci, cikin ikon Allah

kuma sai gashi bata yi amai ba,

Salma tana zuwa Makaranta, ta nuna ma Salma

Dankasa, Salma ta ce

“Wa ya yi miki?”

Tace

*Matar Yayana

Salma ta ce,

“To ba daidai bane.

Ta dauko littafinta ta nuna mata.

*Kin ga nIfa.

* Salma mamaki ya cikata, amma ta share tace

‘”Bari ta sake kwalewa sai tayi kafin Malaminsu ya

ISO.

Amna cikin bacci taji karar wayar Shatima. Ta

kalle shi yana ta bacci, da alamu yau ya gaji sosai,

don sun je Abuja ne sai ma goma ya shigo gidan.

Ta kai hannu ta shafa fuskarshi,

“Honey ana WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

kiran wayarka tun dazu.” Ya bude ido da kyar, taCe

“Ka gaji ko?” Ya ce,

“Na gaji sosai.”

Yana

daukar wayar daidai lokacin kiran ya tsinke.

Yana dubawa yaga sau tara ana kira. “Nafisa!”

ya furta da karfi tare da mikewa tamkar bai taba

bacci ba. Amna ta dube shi, “Wai ina za ka?” Yace,

“Nafisa, ina zaton jikin ne.”

Amna ta sakko itama bata yi mishi magana ba,

illa dai taje ta murda makullin kofa ta cire key din

tare da fadin, “Ba za ka fita ba. Na gaji da irin

wannan abun, don ciki bai fi ciki ba.

Saboda salo bata tashi kiranka sai ranar da ka

ke dakina? Sau biyu tana yi min haka, ba zan bari

tayi na uku ba, tunda naga abin nata yana neman

ya zarme.

Shatima ya ce, “Haba Honey, kin san fa cikinta

ba irin naki ba ne.

Ta ce, cikin mamaki,

“Au!

Dama akwai wani ciki na musamman ne wanda

kayi mata shi ni baka yi min ba?” Ya ce “Ba haka

nake nufi ba, nata cikin me yawan laulayi ne. Don Shatima ya kira. Hamida ta ce,

“Tun dazun

yake kira.” Aliya ta ce “Bar shi kar ki daga har sai

ya fito, in yana dakin wannan ‘yar gwal din ba ya

iya fitowa, yanzu dubi jikin baiwar Allahn nan

amma ya wofintar da ita. WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Hamida ta ce

“Allah nima abin ya bani haushi,

na kira shi ya fi sau ishirin amma bai ko daga ba

Da ya daga ya ce min yana zuwa shine fa shiru

Aliya ta ce,

“Sai ga shi ya kira ni wai inzo

Hamida ta cE

“Ai mun gode, Allah ya saka da

alkairi. Ai har Mamanmu na fada mata irin

taimakon da ki ke mana.

Aliya ta ce,

“Ai yi wa kai ne.

.” Sai da aka kira

sallar Asubahi sannan ta koma dakinta.

Shi ko Shatima zama ya yi a kan durowar gefen

gado, yana ta kiran layin Aliya, ita kuma ta baro ta

can dakinta domin da ta Nafisa ya yi ta kira yana

tambayar Hamida ko Aliya tazo? Tana fada masa

cewa bata z0 ba.

Bayan yayì sallah ya ce “To yanzun sai ki bude

ni in dubo ta ko?”

Ta Ce

‘”Ai ba yanzun ka ke zuwa ba.

Ya cE

“To yanzun kuma zamu iya

samun matsala tunda gari ya waye

Ta ce,

“Mu

samu mana, dama nasan ba zaka kula dani ba kaje ka rabo ni da gidanmu ina can cikin tattali

kaje ka dauko ni.” WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Ya ce, “Kin raina kulawar da nake ba ki? To ki

fada min abin da ki ke son in ke miki don ki

tabbatar da ina kula da ke

” Ya fada ranshi a bace.

Ta ce

“Ga shi ka kwana zaune kana dakina

zuciyarka na gurin wata.”

Ta ce, “Yiwa kai ne dai,

kuma bana fata kema wata rana in haka ta faru za

ki ji dadì in ta hana ni fitowa in wofintar da ke?”

Ta ce”Ni dai ba zan bude ba, dama ka shiga

wanka in ba haka ba zaka yi lattin zuwa office.”

Ganin da gaske ba za ta bude ba, ya bi shawarar ta

ya shiga wanka. Kan ya fito ta bude sai ya fita

zuwa dakinsa ya hau shiri.

Bai ko kalli karin da Ladi Mai aiki ta hada

mishi ba, ya nufi fita. Kofar a damke take, ya

waigo ta fito tana tsaye a falon. Ta ce,

“Ga abin

karinka.

” Ya girgiza kai, “Bana jin yunwa.

Ta ce,

‘”Ai ko ba za ka dakin wata ka karya ba.

Ta soma hada mishi shayi, Har gurin Kofar ta

Zota bashi. Ya amsa tare da fadin “In da ace za ki

ke hada min ko shayin ne a duk ranar da nike

dakin ki da na yi tasa miki albarka WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Ya kai

Karshen maganar tare da kurbar shayin

Da sauri ya watso shi domin suga ya ji har

cikin kwakwalwar kanshi. Ya mika mata shayin

“Ga abin ki, bude ni.” Ta kalli agogo, duk abinka

sai shida ta cika,

Ya ce,

“Amna har yanzun ina mamakin ki

sosai, ashe kin iya mugunta har haka?”

‘ Ta ce,

Na daina bari ana raina min wayo.”

Ya jingina da

bango,

“Shidar dai saura minti hudu.

Ta ce,Inma minti daya ne sai ya cika.”

Ya samu Nafisa a yan da take, ya kira Likita

ya ce zai kawo ta asibiti don fa jikinta ya yi laushi

Likitan yace

“Ko ka kawo ta babu abin da zamu

¡ya mata da ya wuce wannan ruwan. Amma zan

fita zuwa asibiti, ka fito bakin titi in same ka sai

muje in ga.jikin.

Haka kuwa Shatima ya fita ya yi jiran kusan

minti biyar kafin Likitan ya iso. Shi kanshi Likitan

ya tausaya ma Nafisa, ya ba da wata allura ta

tsaida amai, ya ce ayi mata a gani. Amma ciki irin

wannan Kila sai ta kai wata biyar zata samu dan

Salma tana ta jiran Shatima har takwas ta gota

Ta fito taje dakin Aliya nemanshi. Aliya ta ce an fada miki nan yake?”

Salma ta ce,

“Ni wallahi

yanzun bana tuna in da yake.”

Ta ce, WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

“Yana dakin Amna.

” Har zata wuce sai

taga sun fito da Likita. Ta rusuna ta gaida su,

sannan ta ce.

“Yaya mun yi latti.

Ya kalli agogon

hannunsa. “Haka ne, ya ba ki tafi ba? Nafisa ce ba

lafiya ban san lokaci ya tafi haka ba.

Ta ce,

“Anty ba lafiya, bari in dubata.

Sun

gaisa da Hamida, sannan tayi wa Nafisar sannu.

Ranar latti taje Makaranta, sai da ya roka aka bude

mata don har sun ce ta koma.

**

Wata ranar Litinin misalin Rarfe biyu da minti

bakwai. Salma ta sauka daga kan Mashin a bakin

Gate din gidansu. Ta ba mai mashin kudin sai taga

bakuwar mota zata shiga gidan.

Maigadi yazo yana tambayar Direban gurin wa

suka z0? Salma ta kalli Direban, kamar ta taba

ganinshi a wani guri. Sun yi kama da Shatima

kadan.

Taji lokacin daga bayan motar an ce,

“Uwar

Maigidan ce

Gaban Salma ya fadi, domin ko a

ina taji muryar Hajiyar Shatima ba za ta manta ba.

HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE

WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *