RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 12 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 12 BY HALIMA K/MASHI

 

 

 

Shatima ya saki Amna cikin sauri, ranshi ya

mugun baci ya ce,

“Gaskiya wannan karon ba zan

amince da abin da ki ka zo da shi ba, shi ya sa ki kaqi in kai ki kowane asibiti?”

Ta ce, “Wai me ya sa ka ke son mu yi rigima

ne? Duk abin da iyayena suke yi saboda lafiyata ina tsammanin jin dacinka ne, da kuma hutar da kai a kan

was abubuwan?”Shatima ya ce,

“A bar ni mana in yi daidai

Karfina. Ni fa sai ina ganin kamar ana nuna ban isa ba,

ko kuma na kasa Ta ce,

“Ok, in lokacin ya zo sai ka fada wa Dad

din ba zan je ba”.

• Ta juya ta fita cikin fushi.

Ya yi shiru a cikin dakin, wata zuciyar ta ce

masa, kada ka bi da fushi, ka bi komai a sannu. Ya fito shi ma, ba ta falon kai tsaye dakinta ya nufa ya same ta

kwance a kan gado. Ya zauna ya dafa ta,

“Kin yi fushi kenan?”

Ba tare da ta dago ba ta ce,

“Ta ya ya ba zan yi

fushi ba, kowane lokaci sai ka dinga nuna bacin ranka

in an ba ni kulawa. Har ka sa na soma tunani, na saka shakka a cikin son da ka ce kana min

Ya tashi ya dago ta zaune, sannan ya rungumeta,

“Ki yi hakuri matata. Tsananin sonki ne ya sa bana son ki yi nisa da ni”

Ta sa hannuwanta ta ta dago fuskarshi,

“In haka ne ba sai mu tafi tare ba?”

Ya kalli cikin idonta,

“Akina fa?”

Ta ce, “Shine kadai matsala”Yace

“Ina son mu je asibiti a duba ki, don a

tabbatar min cikin lafiya

Ta ce, “Yana lafiya fa, ko a saudi da muka je

sun auna ni sosai”

Ya ce, “To ,,,,,,,,,fa?”

Ta ce,Cikin watan da za mu shiga ne, biyar ga

wata”Ya ce,Yaushe ne tafiyar?”

Ta ce, “A na kan shirin tafiya kenan, zai yiwu

ma cikin satin nan don na ce ma su Dad bana son in fara labour kafin a kai ni”

Ya ce, “Aiki ki ke so a yi miki?”

“‘Ni na fi son aiki in samu baby ba tare da na

wahala ba Shatima ya ce,

“To Allah sauke ki lafiya Ta ce,

“Amin Ya ce,

“To ya za a yi da kayan gadon can na

waje?”Ta ce,

“Ni na san ya za a yi da shine? In akwai

gurin da za ka ajiye ta ka ajiye kawai”

Ya ce,

“In ba dakin Salma zan kai ba, ba ni da

gurin da zan aje”

Ta ce,

“Ni fa ba abin da zan yi da shi”

Salma tana juye shinkafa a kula don ranar mai

da yaji take son ci, sai ta ga maigadi da Shatima suna

shigo da kayan gado. Ba ta ce komai ba, suka shiga da

su dayan dakin suka jujjingine har da sif. Ta yi musu

sannu, Baba maigadi ne kawai ya amsa. Yana fita

Shatima ya kalle ta, “Kayan Amna ne kada ki Bannata musu”

Salma ba ta iya amsa masa ba, domin dai ta san

duk cikinsu babu wacce za ta yarda a kai mata ajiyar

kayan kishiya. Wata zuciyar ta ce Ki ka sani ko don

ba ki da kaya a dakin ne, da kina da shi ba zai zo ya

cire naki ya sa ba

Sai ta amince da hakan, kuma ta ji ta sauke

haushin da ta ji. Wannan shine ya sa kullum Salma take da kyakkyawar zuciya, don tana da kyautata wa

kowa zato.

Duk da Shatima ya yi iya kokarinshi don kada

Amna ta fita wata Kasa da sunan haihuwa sai dai hakan

ya ci tura don ya yi kokarin kai ta asibiti dan ya hada

baki da likitan ya kara a kan lokacin da ake tsammanin

haihuwarta. Sun je an samu nasarar yin hoton, kuma an

Kara kamar yanda aka sa. Nufinshi kafin su yi shirin tafiya ta haihu.

Amma sai dabarar tashi ta tada musu da

hankali, har ma ta sa suka soma haramar tafiyar. Amna ce ta yi mugun daga hankalinta tunda ta ga takardar

hoton, kusan wata daya da kwanaki ya Karu a kan

dukkan hotunanta na baya. Cikin damuwa ta kira mahaitinta ta sanar da shi, ya ce lallai ta shirya su tafi a

cikin satin nan maimakon na sama.

Dole Shatima ya sa ido suka aiko aka dauke ta

suka tafi. Abin da bai sani ba ma iyayenta suna shake

da shi, domin nasu ganin ya kamata ya dauki uzuri gurin aikinshi su tafi tare. Amna ce ta ke nuna musu

cewa, aikin babu damar hakan. Ya shiga mugun tashin

hankali da damuwa. Aliya ce ta rungume shi tana

lallashi tare da ba shi magana. Hakan ya sa shi son

kasancewa tare da ita a ‘yan kwanakin nan.

Sati uku da tafiyar su Amna aka ciro santalelen

yaro mai kyau kama da ubansa, mahaifin Amna da

kanshi ya kira Shatima yana masa albishir da samun

karuwar. Murna sosai Shatima ya yi tare da kiran nasa

mahaifan ya sanar musu. Nan da nan labarin haihuwar

ya watsu a dangi. Hajiya aka shiga shirya kayan barka.

Shatima yana kwance a kan katifarsa ranar

dakin Salma yake. Kwanaki uku kenan da haihuwar,

amma maijegon ta ki daga layinsa. Ya san tana fushi

ne tunda suka tafi sau daya ya kira ta, shi ma Aliya ta

matsa masa. Ya tura mata sako yana mai rokon

alfarmarta cewa ta daga, sannan ya sake kira. Ta dauki

wayar ta yi shiru duk da tana jin sallamar da yake dokawa.

Ya ce, “Ki yi hakuri Honey, ko mene ne tunda

mun zama iyaye bai kamata muna fushi ba. Zafin rabuwa da ke har kuka na yi, shi ya sa bana kiranki”Cikin shesshekar kuka ta ce, “Ka nuna min

matsayina, kuma na gani. Sai dai kullum in tayi

Momy karyar mun yi waya kana gaida su, don kawai

kada mutuncinka ya zube amma ba ka gani”

Nan Ya yi lallashinta, da kyar ta sauko sun yi waya sosai, kuma za su dawo cikin satin da za a shiga.Dun Ya ce, “Suna fa?”

Ta ce, “Sai satin sama”

Ya ce,A nan za a yi mishi huduba?”

Ta ce, “Dad zai masa dama ya ce mu yi

maganar sunan da za a sa mishi da kai”

Don ya sake faranta mata, ya ce, “Na ba ki zabi zumata

Ta ce,Kamanninka da yaron ya sa na darsa

sunanka a zuciyata, in ni zan zaba ina son a sa mishi

Muhammad Ja’atar”Ya ce,

“Yanda ki ke so haka za a yi, amma na

sa za a yi taron rada suna a gidanmu can Zaria, bikin

mata sai kun dawo”

Ta ce Haka ya yi”

Ya Ce.

“To a turo min hoton yaron nawa in

ganshi”Ta yi dariya,

“Ka ci sa’a da na ce sai randa

• muka dawo ka ganshi”.

Ya ce, “Da ma ni mai sa’a ne tun daga lokacin

da na mallaki zuciyarki

Ta sake sakin dariyar jin dadi sannan ta ce,

“Zan turo maka yanzu ta whatsapp”

Ya kalli yaron cike da so tsantsa da kauna, fari

ne tas cikin kayan jarirai masu kalar sararin samaniya.

Tabbas yaron yana kama da shi sosai. Ya mike ya

dauki jallabiyarsa ya zura.

Salma tana zaune tana assignment ta dago ta

dube shi, shi ma ya kalle ta tamkar zai yi magana

amma sai ya fasa. Ta maida kai ta ci gaba da rubutunta

domin inda sabo ta saba da yanda Shatima ya rikide

yanzun. Ta kula kwanakin nan yana cikin farin ciki da walwala.

Dakin Aliya ya shiga ya nuna mata hoton

kyakkyawan yaronsu. Ta yi farin ciki tare da fadin,

“Yaron nan kama yake da kai sak!”

HMmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *