RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 23 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 23 BY HALIMA K/MASHI

 

 

Ta ce, Zan tura abina ne daga wayar Aisha

ka aje min. bai san dalilin da ya kasa hana taba, illa dai ya ce.

“Kar ki yi min wasa da wayà. Tun kafin ta

nemo Aishar ta soma daukar sabbin hotuna da wayar ta Shatima ta sake zuwa ta Dauki Jafar suka yi wasu. Aliya ta sha mamaki ganin wayar Shatima a hannun

Salma, ta tura

duk hotunan da ta yi a

wayoyin jama’a sannan ta je ta kai masa. Lokacin saura su ‘uku a cikin dakin da suka ci abinci. Ta mika mishi tare da godiya, sannan tace Yaya ni ma fa

zan je kai Anty Badi’ atu”.

Ya ce,Ina?”

Ta yi shiru don jin yanda ya amsa da karfi.

Munnir yace

“‘Katsina mana

Shatima ya hade rai,

*Koma ciki malama

babu inda za ki je

Za ta yi magana ya ce,

“Bana son jin komai”

Salma jiki babu Karfi ta fita ta koma cikin

gida. Dakin Hajiya Kaka ta shige ta takure a bakin

~ gado. Hajiya Kaka da take zaune kan sallaya suna

hira da wasu

*yan uwansu ta kalli gadon tare da

tambayar wane ne nan ya yi rijib a gado?

Salma cikin damuwa tace

“Nice

Hajiya Kaka tace

“Salamatu ce?’

Salma ta ce. “Ni ce Kaka’

Ta ce.A’a na ga kin saka kaya kin fita

yanzu?”

Salma cikin shagwaba ta ce,

*Yaya Shatima

ne wai ba zan je raka Anty Badiatu ba, kuma Kaka yadace a ce shi yana babba ya mu hudu matansa ace babu wanda ya je rakiyar Kanwarsa gidan miji?” Kaka tace

*Zance yake yi, dole kuwa a samu

mai zuwa a cikinku. Ina Shatima, a kira min shi”Salma ta ce,

“Sal dai in sa a kira shi kar ya ce

Karansa na kawo

Hajiya Kaka ta ce,

*Kira min Saude ta sa a yi

min magana da shi”

Salma ta fita cikin murna ta bar Hajiya Kaka

tana fadawa wadanda suke zaune tare, kirki da hangen nesa irin na Salma.

Tace

“Yarinyar nan ga ta karama amma

lissafi gare ta irin na manya, ga ta da kokarin kyauta ga girmama mutane

Saude ta shigo tana fadin,

“Ga ni kaka, ina

shiryawa ne za mu kawo amare ki musu fada a kai su

gurin iyayensu a zo a tafi, don Badi’ atu tuni Alhaji

ke waya su zo tafiya da nisa”

Kaka ta ce,

“To ku kokarta ko a tafi. Yanzu, ban da shirme irin naShatima a ce ko

daya cikin matansa babu mai

zuwa?” Anty Saude ta ce Ai ba zai yiwu ba, tunda ita babbar cikinta ya girma ita karamar mu je tare ko

kuma Maman Jafar tunda Nafisa babu hali ita

wanna ga tsohon ciki’ Kaka ta ce,

“Kira min shi an ce yana dakin

•bakina Salma tana jiyo muryar Shatima yana gaisawa da mutane a falo ta shige bandakin Hajiya Kaka. Tana jin lokacin da yace

“Kaka ga ni, an ce

kina nemana ruwa a jallo Ta ce.

“Zauna dan nan ka fada min in ji ko

gaske ne. wai babu wanda zai je a cikin matanka Yace

‘Me za su je kuma su yi kaka?”

Tace Ka ji zancen banza, kai ne fa babba a

cikin gidanku, matanka hudu amma babu wadda zata raka kanwarta, ai ko dai da ka ji haushi. Babu wadda fa ta je jere cikinsu’

Shatima ya ce,

“To wa za shi cikinsu, Nafisa suma cikin hidima suke, Aliya ta yi nauyi, ita ko

Amna ba son shiga jama”a take yi ba’

Salma ta bude Kofar bandakin ta fito daidai

lokacin da Kaka ke fadin, “To ai ga Salamatu”

Ya kalli Salma,

“Kin zone kin kawo karata?”

*Yan dakin suka sa baki da cewa,

*Gaskiya matanka ya dace su wakilceka a wanna tafiya’ Jin baki ya yi yawa ya ce,

“To shi kenan

Kaka su je duk wadda za ta

Ya dubi Salma, “Ki same ni a dakin baqi

Kaka ta ce,

“Kada in ji ka yi mata fada, ba

Kara ta kawo ba”Ya ce,

“Kar ki damu Kaka kudin shan ruwa a

hanya zan ba ta Salma ta kalle shi don ta, ya sakar mata harara. A tsorace tabi bayansh, motarshi ya shiga ita ma ta bude ta shiga. Ya rufe ta da fada, ta

sunkuyar da kai yana fadin,

“Ke shegen yawo ki kasa a ranki shi ya sa har ki ka kai Karata, ina ta lura da

rawar kanki da ki ka kama yanzu. Jiya ina kallonki

Salma ta yi saurin dubanshi tare da fadin,

“Mene?’Ya ce,

“Mayafi ma aje shi ki ka yi ki ka kama

yawo haka jiki duk a matse, kina manta cewa kina da aure ma ko?”

Salma ta sauke ajiyar zuciya ta godw ma Allah

da ya sa iya rashin mayafin ya gani. Ta girgiza kai tare da fadin,

“Bana mantawa Allah kuwa

Ya ce,

“Kuma tunda kin matsa sai kin je ki je

din, amma ki

sani duk wani motsinki zan sani,

sannan kuma ko naira ba zan ba ki ba

Ta saki fara’a,

“Babu abin da zan yi ma, babu

komai in bà ka da kudi

Yace, “Ina da shi, ba zan bada babe

Salma ta ce,

“Yaya in har kana ga zuwana din

ba ka so Allah a barshi. Da ma dai rashin dacewar aCe mu ba mu je bane kana kai babba shi ya sa har na

yi magana Yace

“In kin zauna ma me za ki yi min? ki

je kawai abinki”Ta ce,

“To na gode, bari inje in shirya”

Har ta fita, yace

“Amsa Dubu biyu ya ba ta, ta sa hannu biyu ta karba,

ta ce, “Na gode

A Katsina gidan amarya ya yi kyau, duk da

cewa kowa da barinsa. Ita da kishiyarta amma gida daya suke, irin tarbar da suka samu daga dangin

mijin su ne suka saka ran cewa ta karbu gurinsu.

kishiyar ce dai sai dai a ce Allah ya kade fitina,

domin kanta tsaye washegari bayan an yi budar uwargidan don a hada su, tace

“Kar ku ce min

amana, don ba a bada amanar kishiya

Anty Saude ta ce,

“To, mu dai fatanmu a

zauna lafiya, zama na amana”

Ta ce,Idan ta so haka za a zauna

Duk suka sha mamaki, don haka da suka

dawo dakin Badi’atu suka yi ta mata nasiha, tare da

jaddada mata hakuri. Da za su taho Badi’atu ta sha

kuka, haka ma Salma.

A Zaria kuwa bayan tafiyar

‘yan kai amarya

Katsina, Shatima ya samu su Aliya ya ce su shirya su

koma don gobe zai wuce Abuja. Amna dama a takure

take, nan suka koma gidan Hajiyan Shatima don shiryawa. Aliya kuma ta ce, bari ta je gidansu su

gaisa tunda ba taje ba. Har ta ce da zai barta zuwa gobe. Yace

a’ a, su gama komai zuwa bayan

magariba. Ya dauki mota ya nufi gidan su Nafisa

lokacin motocin daukar amare sun fita da suke nan an kuma kwashi jama’ a. Har,zai juya don ya san kila

HmMm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *