RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 3 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 3 BY HALIMA K/MASHI

 

 

 

don ta samar da sotsan tsamara gauraye. Ashe ita tana

aikin banza ne, gara ma da ta sani tun da wuri.

Ta dago jajayen idanunta ta kalle shi, yana da

Kimar da ba za ta iya maida mishi magana ba, don haka

ta sake sunkuyar da kanta.

Alhaji yace

“Duk abin bai kai a yi wannan

tone-tone ba, kada in Kara jin an yi zancen saki, ko

asiri www.Dailynovels.com.ng

Ya dubi Hajiya Amina, yace

“In kin ci gaba

da dagewa a kan wannan maganar zan ta sa ki har

gaban Hajiya Azumin, sannan mu je gurin malam su bani hujja’

Ya nuna ta da yatsa,

“Kin san zan iya Alhaji Musa ya ce,

“Wannan shine gaskiyar

magana

Mama ta ce, «Ni wallahi duk wannan abu ba a

son raina suka faru ba. Ban so aka tono wadannan zantukan ba, tunda ban san komai a kai ba. Mun dai z0

duba mara latiya

Alhaji yaja tsaki, “Ga shi mun rasa jam’in

magariba a kan zantukan nan marasa tushe, bare makama

Ya kalli Hajiya,

‘”Ke ce babbar mai laifi a cikin

wanna al’amarin”

Ya kalli Salma «Tashi yarinya kin ji daga

wanna durkuson

Salma ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta yunkura

da niyyar tashi. Kafafunta sun yi tsami, ba za su iya daukarta ba, don haka ta koma ragwat! Ta zauna.

Alhaji Musa ya ce,

‘”Sannu, Kafafun naki duk

sun yi tsami ko?”

Ya sa hannu a cikin aljihunsa ya ciro kudi ya

kirga naira dubu goma sha biyar ya mika wa Shatima, ya ce,

“Ga shi ka sai mata waya ko karama ce, don ita ma ake saka mata katin ko da iyayenta sa gaisa

Ta dubi Alhaji Musa ta ce,

“Baba na gode”.Muryarta tana rawa.

Yace

“Babu komai “yata”

Yaci gaba,

‘da Kowacce ta koma gurinta ta zauna lafiya da mijinta da

“yar uwarta, zuciya daya

Amna ta kalli Hajiya,

“Babu maganar asiri-asiri ko?”

• Alhaji ya amshe,

“Babu wata magana da ta

shafi asiri, duk sharri ne’ www.Dailynovels.com.ng

Ta ce,To, ku gaida gida”.

Ta nufi sashenta cikin jinjina abin da ya faru.

Aliya ta mike tana fadin, “Ga shi ko abincin ma

ba ku ci ba. To ku gaida gida”

Salma ta bi Aliya da kallo, ba ta shakka ita ce ta hada komai. Ta soma tuno wasu abubuwa da ta yi mata masu kama da ingiza mai kantu ruwa.

Salma ta yunkura ta mike da kyar ta dubi su

AlhajiBaba ku gaida gida”

Ta kalli su Hajiya,

– “Sai anjimanku, Allah ya

tsare hanya Su Alhaji suka ce,

“To sai anjima, ki yi hakuri

kin ji ko?”Hajiya ta tabe baki tare da raka Salmar da harara.

Nan Alhaji ya yi ma su Hajiya fada sosai,

sannan suka ce,

“Ku shirya bari mu yo sallah mu zo

mu wuce”

Salma ranar da zazza6i ta kwana, haka kuma ba

ta jin cewa za ta je a yau. Lokacin da Shatima ya shiga

gurinta da safe tana nade a zanin gado a can tsakiyar

gadonta. Ya kira sunanta,

“Salma”.

Da kyar ta daga idanunta jajir ta ce, “Na’am.”

Ya ce, “Ya ya dai, ba ki da lafiya ne?”

Ta maida idanu ta rufe, zuwa yanzu ba ta son taji ko ta ga Shatima. Ta ce,

*”Dan zazzabi ne’

Ya hau gadon ya saka bayan hannunshi a

sassan wuyanta. “Kai! Haka jikin naki ya yi zafi? Tashi

in kai ki asibiti www.Dailynovels.com.ng

Ta yunkura tare da fadin, “Ka barshi kawai, zai

bari anjima kadan

Ya ce, “To in turo Aliya ta duba ki?”

Ta ce,

“Ka barta anjima kadan zan warware”

Ya ce,

“Yaushe ki ka soma gardama da ni?”

Salma ta yi shiru,

Ya kama hannunta,

“‘Sakko in kai ki asibiti”

Jallabiya ta saka

suka tafi.A bakin

makarantarsu suka tsaya, ya rubuta *yar takarda ya ba

wa mai gadi ya ce ya kai ofishin shugaban makaranta.

An ba ta allura da magunguna, ya dawo da ita

gida. Ya shiga gurin Aliya. Da ma ta ga fitarsu, ya ce,

don Allah ta lura da ita ba ta da lafiya.

Aliya tace, “To”Yana fita ta zauna cikin fargaba, kar dai ita ma

wannan cikin gare ta? Na ba ni ni Aliya, nice kenan

zan zama karshe?”

Ta mike da sauri tare da fadin, “Bari na je

dakin Salmar na gani”

Ta same ta kwance kan kujera. Salma tana

gaminta a ranta ta ce, “Allah ka yi min tsari da duk

sharrin da matar nan ta zo min da shi

Aliya ta je gabanta ta tsaya tare da rike kugu,

“Ashe ba kya jin dadi?”

Salma ta ce,

“Uhum”.

Aliya ta ce,

“*Ko ke ma cikin ne?”

Salma ta ce, “Oho! Ni ma ban sani ba”

Ta sake matsawa kusa da ita,

“Wane irin gwaje-

gwaje aka yi miki?”www.Dailynovels.com.ng

Salma ta yi mata banza. Tsaki ta ja ta fita tana

mitar, yana fadin ba ya sonta amma ga shi nan da

cikinsa a jikinta.

Salma ta shiga kunci da bakin ciki sakamakon

kalaman Shatima. Duk da wautarta da Kuruciya ta san

Shatima ya ba da ita badawa ta karshe, ya kunyatata

gami da tozartata. Ta yanke ma kanta dakatar da son

Shatima, sannan za ta ja baya da shi. Za ta ci gaba da

kallonshi a matsayin Yaya kurum

***

Kwanci tashi asarar mai rai inji masu iya

magana. Amna da Nafisa ciki na ta girma. Domin

Amna tana da shidda, Nafisa tana da wata biyar.

Shatima ya samu Amna da batun zuwa awon

ciki, ta ce masa ita sai sun dawo daga umara. Ya dube

ta cikin al’ajabi,

“Za ku je ummara yaushe?”

Tace

“Jibi insha Allahu za mu tafi da su

Momy

Yace, “Ikon Allah, shine ban isa ki fada min

ba bare ki nemi izinina?”www.Dailynovels.com.ng

Ta ce,

“Jiya Mom ke fada min ni ma’

Shatima ya yi shiru cikin bacin rai. Ya sauke

ajiyar zuciya, abu daya zai sa ba zan hana ki ba, amma

gaskiya a guji shigar min hakki”

Ta dube shi.

“Ban gane ba? Kana nufin da sai

ka hana?”Yace

“Kwarai kuwa

Ta yi *yar dariya irin ta rainin wayo, ta ce,

“Kai

kana da son rigima”

Ya kauda zancen don ba ya son su fara sa’insa,

don haka sai ya ce, “Ke nan ba ki nan za a yi bikin su

Hannatu, yaran Yayan Alhaji marigayi na Kaduna?”

Ta dan yatsina baki,

“Ko ina nan ka san bai

zama lallai inje ba don bana son hayaniyar mutane

Shiru ya yi yana kallonta, don tuni ya lura ba ta

son duk wani al’amari da ya shafi danginsa, domin ko

kwanan baya da Hajiya Kaka ta yi rashin lafiya babu

yanda bai yi ba a kan su je a duba ta ba, amma ta ki,

kuma sauran duk sun je. Amma bari ya yi mata uzuri ta haihu.

Bikin “ya’ya biyu za a yi, babban dan Kaka

wanda ya rasu, bikin a Zaria za a yi shi. Haka kuma

bikin zai kama ana saura sati daya azumi. Da Amna ta

HMMM LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe www.Dailynovels.com.ng

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *