RAUDHA CHAPTER 5
Direct wani gida suka nufa me kamar kango amma da akwai Gate a gidan, suna shigar da motan suka fito da ita, su uku ne mazan yayinda ɗaya ne yaɗauke ta yasaɓa ta a kafaɗa suka nufi cikin gidan da ko ƙofofi babu sai window
+
Kamar mintuna biyar da shigan su sai gidan yasoma amsawa da wani irin kuka me ban tsoro haɗe da wani irin gurnani tamkar za’a fasa gidan, kukan sosai yake ƙaruwa sai kuma yahaɗe na mutane da yawa wanda baza ka iya gane na aljanu bane ko na mutane, zuwa can kuma sai kukan yalafa sai ga RAUDHA ta fito tana layi gashin kanta duk ya barbaje ya rufe mata fuska, duk da dare ne but bazai hana ka hango yanda idanuwan ta ke wani irin walƙiya ba tamkar yanda na mage yake yi idan tafito da dare, tafiya kawai take yi har tafice cikin gidan tadoshi cikin daji, duk da dama gidan a wajen gari yake
Sai da tayi tafiya me nisa kafin tafaɗi ƙasa yashe babu alamun numfashi a tattare da ita.
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
Washe gari har Suhaib yashirya zuwa Office yana jiran dawowar RAUDHA amma babu ita, duk da yasan bata kai wa har safiya idan tafita but yayi tunanin ko tana can ɗin ne inda tasaba zuwa, jin shiru bata dawo ba sai yatafi Office
Koda yadawo Farida ta tabbatar masa bata dawo gidan ba sai hankalin sa yayi mugun tashi, wayanta yasoma kira duk da kiran ya shiga but babu answer, sai da yayi Three missed calls kafin Rash taɗaga Kiran, tunda dama a motan Zen RAUDHA tabar jakan ta, su ma sun shiga tashin hankali musamman da suka neme ta suka rasa, daga baya kuma sai suka yi tunanin ta wuce gida ne duk da sun ji haushi sosai Zen da Maan tunda sun yi tanadin ranan sosai akanta, amma tatafi tabar su
Abinda yasoma fita a bakin Suhaib sanda Rash taɗau wayan shine “Baby Ina kika je har yanzu baki dawo gida ba kin ɗaga min hankali sosai?”.
Jin hakan sai Rash ta tabbatar akwai matsala, itama cikin tashin hankali da yanuna a muryan ta tace, “Ba RAUDHA bace ƙawarta ce, ta bar jakarta ne a wajena kuma naga kana kira”.
Suhaib dake zaune be san sanda yayi zumbur yamiƙe ba
“Whattt… Ki kace mene? Ita ina taje ne da tabar wayan a hannun ki?”.
Cikin tsoro Rash tabashi amsa da yanda aka yi su ma suka neme ta suka rasa
“Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un”. Abinda Suhaib yafaɗa kenan yana me sakin wayan a ƙasa
Lokaci ɗaya zufa ya tsatstsafo masa a saman goshi, ga wani irin jiri da yamamaye sa nan take sabida tsananin tashin hankalin da yaziyarce sa
Farida dake zaune da ciki a gaba tana tambayan sa “meke faruwa?” Be ma san tana yi ba
Sai da yayi good 5 minutes a gushewar tunani kafin yadawo dai-dai, lokacin kuwa tuni hawaye sun ciko masa idanu yakalli Farida da tamiƙe tsaye itama hankalin nata a tashe, cikin raunin murya yace
“RAUDHA .. RAUDHA..”
Abinda yake ta faɗi kenan ya kasa ma yin maganan, sai kuma kamar an tsikare sa yaɗau wayan nasa yasake kiran Numban RAUDHAN, wannan karon akashe wayan yake, ai be jira komi ba yayi waje asukwane yana sake neman layin duk da kuwa ance masa akashe ne
Farida biyo bayan sa tayi duk ta ruɗe yanda taganshi shima aruɗe, lokaci ɗaya ya fita hayyacin sa tamkar zararre, but kafin takai wajen ma tuni yaja motar sa yayi bakin Gate, dole takoma ciki tazauna jiran abinda zai biyo baya, duk da kuwa a matuƙar tashe hankalin ta yake abun ku da me ciki gashi ba lafiya tacika ba a kwanakin.
Babu inda yazarce sai police station, report yaba da akan ɓatan RAUDHA, abun ku da me shi suna ganin kuɗi nan da nan aka haɗa sa da Police zuwa school ɗin su RAUDHA, wasu kuma suka bazama neman ta
Duk wani bincike sai da aka yi but an tabbatar musu RAUDHA bata zo yau ba, daga ƙarshe aka sanƙamo su Rash zuwa station don amsa tambayoyi, koda aka tambaye su abinda suka sani sun faɗi komi basu ɓoye ba, sai dai anƙi sakin su sabida su ake zargi kasancewar su ne mutanen da RAUDHA tayi rabuwar ƙarshe dasu
Haka ƴan sanda suka dage wajen bincike, har a talabijin an saka hotunan ta ko za’a dace amma babu labarin ta har zuwa dare
Zuwa lokacin Suhaib ya gama fita hayyacin sa, kuka sosai yake yi tamkar mace, ƙiri-ƙiri yaƙi tafiya gida babu inda be yawata ba don neman ta but Allah be sa ya dace ba, sai bayan isha’i sannan yakoma gida
A yanda yadawo ne hankalin Farida yasake tashi fiye da yanda take tun safe, musamman yanda yasaka ta gaba sai rizgan kuka yake yi yana sambatu
Be san ya zai yi da rayuwan sa ba idan ba’a ga RAUDHA ba domin bazai taɓa yafe wa kansa ba, kuma yana ji ajikin sa RAUDHA itace bugun numfashin sa idan babu ita to tabbas babu shine, soyayyar da yake mata ba zai iya juran rasa ta a irin wannan yanayin ba
Sai da Farida tayi dagasken gaske wajen rarrashin sa, nasiha tayi ta masa tana nuna masa girman ƙaddara da tawakkali dashi, tabbas ɓatan RAUDHA ƙaddaran sa ne, idan kuma yajure yamiƙa al’amuran sa zuwa ga Allah to Allah me rangwame ne zai sauƙaƙa masa duk kan lamuran sa
Wannan nasihan da tayi masa ne yasanya Suhaib ya raya daren da roƙon Allah wajen bayyana masa ƙanwar sa, yana yi yana kuka cikin ficewar hayyaci, gaba ɗaya aranan be ko runtsa ba saboda tashin hankalin da yariske sa
Sosai Farida ta tausaya wa mijin ta, tabbas tasan yana cikin wani mawuyacin hali wanda samun kansa sai idan RAUDHA ce tadawo.
Washe gari da mugun zazzaɓi Suhaib yatashi har baya iya tsayuwa sabida tsananin ciwo, gashi ƙiri-ƙiri yaƙi cin abinci in banda waya da yatasa agaba yana faman kira da kuma jirayen kiran babu abinda yake yi
Daga ƙarshe ma fita yaso yi but ya gaza sai kwasan sa akayi aƙasa domin tuni ya sume
Kuka sosai Farida take yi sabida tsananin tashin hankali, duk yanda take jin ciwon ta be kai yanda take jin tashin hankalin halin da mijin ta yake ciki ba
Waje tafita takira ma’aikatan gidan su biyu da me gadi suka haɗu suka ɗauke sa zuwa mota, drever yaja aka nufi asibiti dashi
Direct emargency aka nufa dashi
Kuka kawai Farida take yi ta kasa zaune ta kasa tsaye ko jin nauyin cikin nata bata yi, wayan Yayan ta takira tafaɗa masa halin da ake ciki, ai kuwa babu jimawa yazo, shine yayi duk wani abinda ake buƙata na jigilan asibitin, daga ƙarshe ma yasaka aduba Farida saboda yanda jikin nata yatashi sai numfarfashi take yi
An bata gado akayi mata alluran barci sabida tasamu hutu don shi take buƙata a halin yanzu.
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
A can Station kuwa ba’a saki su Rash ba sai da mahaifin Zen yazo, shine yayi belin su duk da daƙyar aka bashi don shima sai da yasaki bakin aljihu.
Wajen awanni biyu kafin Farida tafarka, lokacin har mahaifiyar ta da ƙanwarta Maryam wacce akayi musu aure tare sun zo, ita Maryam ɗin ne tazo musu da abinci, don haka Mahaifiyar su wato Umma tace ma Maryam ɗin tazuba ma Farida abinci taci
Daƙyar taci sabida hankalin ta na ga Mijin ta, don Umman taƙi barin ta zuwa wajen sa ne saboda gargaɗin da Doctor yayi musu adena barin ta tana zirga-zirga da yawa Cuz tana buƙatar hutu sosai.
Sai yamma kafin Umma tasoma tafiya, daga baya itama Maryam tawuce da zummar idan ba’a sallame su ba zata aiko musu da abinci.
Lokacin da Suhaib ya farka Farida na wajen sa, tunda yatashi yagansa a asibiti yatashi hankalin sa akan sai an sallame sa, acewar sa bazai zauna anan ƙanwar sa kuma na can cikin wani hali ba be je ya neme ta ba
Daƙyar doctor yashawo kansa har ma yayarda yazauna zuwa safe, gashi dama ko kaɗan bashi da ƙwarin jiki don tun jiya rabon sa da abinci, yaƙi saka komi acikin sa sai ruwa
Yanzu ma daƙyar Farida tashawo kansa yaci abinci doctor yazo yaba sa drugs yasha, baya buƙatar raunin sa a yanzu yafi son kuzarin sa yadawo ta yanda zai fita neman Ƙanwar sa
Kwana yayi a ranan yana waya da Police don jin me ake ciki, har yanzu dai babu labarin ta.
RAUDHA bata farka ba har washe gari
+
Wajen ƙarfe 07:00am. Wani magidanci yazo wuce wa yahange ta, da farko ya ji tsoro sai dai kuma yayi shahada wajen ƙarisawa wajen ta, hannu yakai yana taɓa ta sai dai ko kaɗan babu alamun numfashi a tattare da ita, sai da yasake kai hannun sa setting hancin ta nan ma be ji komi ba, sai yariƙe tsintsiyan hannun ta anan ne yatabbatar tana da sauran rai, ajiye fatanyan sa yayi yaɗago ta yasaɓa a kafaɗa sannan yayi hanyan gida
Kasancewar safiya ne mutane duk suna gida basu kai ga fitowa ba, don haka har yakai gida be haɗu da kowa ba duk da babu nisa sosai da rugan da suke
Yana shiga yasoma ƙwala wa matar sa kira
Da gudu Lantana tafito tana aza ɗankwalin ta kanta at the same time tana amsa mishi da faɗin “Malam lafiya..?”
Sai dai bata iya ƙarisa maganar ba ganin sa saɓe da RAUDHA a kafaɗa
“Tukunna dai ɗauko min Tabarma sai in miki bayani ko?”
Lantana ta’amsa mishi dasauri tana shigewa ɗaki taɗauko tabarman kamar yanda ya umarce ta, shimfiɗa wa tayi sannan yasauke RAUDHAN akan tabarman
“Malam wannan yarinyan daga ina, aina kasamo ta?” Lantana tayi masa tambayan lokacin da tasami waje tazauna tana kallon sa
“To nima dai ga tanan tsintan ta nayi cikin jeji, ganin tana numfashi shine nataimaka nakawo ta nan”.
“To Malam me zai saka kakawo mana ita nan bayan gidan me Gari zaka kai ta? Mu kuma me zamu yi mata?”
Ɗan sauke numfashi Malam Umaru yayi kafin yace, “to nayi tunanin hakan nima ai, sai kuma na tuna ɗazu da asuba da muka yi sallah me Gari ya sanar mana zai yi tafiya a lokacin, har yake neman addu’ar mu shiyasa nayi tunanin kawo ta nan ɗin tunda ko an kaita can babu me kula da ita”.
Lantana da idanun ta suka ƙi ɗauke wa akan RAUDHA tasake cewa, “Malam nifa wlh ina jin tsoro, yarinyan fa ko motsi bata yi yanzu mu wani taimako zamu bata? Kai da ganin yarinyan nan kasan ƴar cikin birni ce, asibiti Ya kamata a kai ta, kar mu zo Garin taimako mu afka cikin matsala, idan ka kaita can sai kayi musu bayanin tsintan ta kayi kaga sai su nemi ƴan uwanta tunda su ƴan birnin sun san yanda zasu yi su same su”.
Kallon Lantanan yayi yace, “ke kina ganin haka kawai zan kai ta asibiti baza su caje Ni kuɗi ba? Dole sai mun biya kuɗi kuma kinsan ban da komi a yanzu, sannan wannan yaron ban san ranan dawowar sa ba da sai yataimaka mana, amma Ni abinda naga ya dace ki je gidan Jummai me magani tazo taduba ta sai aga abunda hali zai yi, kinga idan muka samu tafarfaɗo sai tafaɗa mana inda take mu maida ita, kinsan be kamata mu bar ta bamu taimaka mata ba domin tana buƙatar taimakon, Allah yaga zuciyar mu zai bamu nasara, ko sada ta muka yi da ƴan uwan ta zamu samu lada”.
Ajiyan zuciya Lantana taja cike da sanyin jiki tace, “to shikenan Malam Allah ya bamu ikon taimakon nata, bari inje sai mu taho da Jumman”.
“Amin Amin”. Malam Umaru ya’amsa mata
Sai da tashiga ɗaki tayafo mayafi kafin tafice zuwa gidan Jummai me maganin gargajiya
Har suka dawo ita da Jummai Malam Umaru yana nan zaune a wajen, nan dai yawuce gona yabar Jummai na duba RAUDHA akan bazai daɗe ba zai dawo, in yaso idan yadawo sai yaji meke faruwa.
Buga tagumi Lantana tayi tana kallon Jummai da tazuba kayan magungunan ta tana ta faman duba RAUDHA
Bayan wasu lokuta taɗago tana kallon Lantanan kafin tace, “Iy to matsalan yarinyan nan babba ne domin dai gaskiya yafi ƙarfi na, na kasa gano komi a tattare da ita, amma kuma albishir ɗin da zan iya muku shine zata farka a ɗan ƙanƙanin lokaci, wannan turaren kin ganshi ko?”
Jummai taƙare maganan da ɗago mata turare a ɗan kwalba, sannan ta haɗa mata da wasu saiwan icce taci gaba da faɗin
“Zaki samu garwashin wuta ki murmusa wannan iccen akai, sannan sai ki ɗiga turaren nan a wutan da zaran iccen ya gama ruruwa, zaki kawo garwashin kusa da kanta ki riƙa turare ta a ƙalla sau uku a rana, zata iya farkawa zuwa gobe ko kuma nan da kwana biyu, yanzu zaki fara daga yau ne, sau uku zaki yi mata a yau ɗin kina ji?”.
Gyaɗa kanta Lantana tayi dasauri, sannan tamiƙa hannu ta’amsa tana faɗin, “to iya abinda za’a yi kenan?”
“Eh iya abinda za’a yi mata kenan, idan kuma kwana biyu ya shuɗe bata farka ba sai ki taso ki faɗa min Ni kuma Nasan me zan yi”.
“To mun gode Allah yasaka da alheri, Allah dai yataimake mu ta tashi ɗin”. Cewar Lantana cikin jimami
“Zan wuce idan Mijin naki ya dawo sai ki faɗa masa”.
Lantana tace, “to shikenan Jummai idan yazo ɗin zan kawo miki kuɗin har gida”.
Miƙewa Jummai tayi bayan ta harhaɗa kayan ta, suka sake yin sallama sannan tafice a gidan.
Kamar yanda Jummai ɗin tace mata tayi, hakan kuwa tayi wa RAUDHA
Babu jimawa Malam Umaru yadawo Lantana tafaɗa masa yanda suka yi, kuɗi ya ba ta sadaka kamar yanda ake bata idan har ba faɗan yawan kuɗin tayi ba, Lantana ta’amsa tanufi gidan Jummai me magani takai mata kuɗin ta dawo
Tana dawowa Malam Umaru yace, “Ya kamata ki gyara mata ɗakin Basiru amayar da ita can don be kamata abarta anan ba”.
“To Malam bari inyi”.
Ɗakin Basirun Lantana tashiga da tsintsiya a hannun ta, cikin ƙanƙanin lokaci tashare ta kakkaɓe katifar ɗakin tasauya da wani zanin gadon, sannan tafito ta sanar wa Malam ta gama
Shi ya ɗauki RAUDHA zuwa ɗakin yashigar da ita
Ita kuma Lantana sai tanufi ɗakin ta taɗauko Zani talulluɓe wa RAUDHA jikin ta kasancewar ba wani kayan kirki ne da ita ba, gaba ɗaya santala-santalan ƙafafuwan ta a waje suke, ga gashin kanta shima a buɗe ya wargaje, sai da takama mata gashin taƙulle mata ta yanda bazai dame ta ba sannan tafito daga ɗakin
Anan Malam Umaru yayi mata sallama cewar ya fita zuwa majalisa, tayi masa adawo lafiya sannan tanufi bakin murhu tasoma kaye-kayen ɗaura girkin dare.
Da dare suna zaune a tsakar gida suna cin abinci, Malam Umaru yakalle Lantana bayan ya kai loman tuwon bakin sa, sai da ya haɗiye sannan yace, “Kin kuwa yiwa yarinyan nan turaren?”
“Eh nayi mata Malam, saura ɗaya ne yanzu idan mun kammala sai inyi mata”.
Gyaɗa kansa yayi be sake cewa komi ba, sai da yagama cin abincin yasha ruwa tare da sakin gyatsa yafurta “alhmadulillah Allah mun gode maka, Allah kakawo mana na kullum”.
Lantana ta’amsa masa da “ameen Ameen Malam”.
“Yanzu haka zamu zuba ido mu bar Basiru yana tafiya gantali sai yayi kwana da kwanaki kafin mu saka sa a idanun mu?”
Tsame hannun ta daga kwanon tuwon Lantana tayi, fuskarta akwai damuwa sosai izuwa yanzu, sai dai kuma ya zasu yi dole sai haƙuri, Kallon sa tayi cike da sanyin murya tace, “to ya zamuyi Malam? Abinda Basiru yazaɓar wa kansa kenan, sai mu bi sa da addu’a Allah shi zai shiryar mana dashi”.
“Hakane to Allah yashirye sa, amma abun na matuƙar damu na, ace ɗa ɗaya ya gagare mu?”.
“Amin, wata rana zai shiryu insha Allahu, rayuwan ne yanzu sai ahankali, domin ba kaɗan ba Abokan banza suna taka muhimmiyar rawa wajen gurɓacewar Yara, Allah yasa mu dace”.
Malam Umaru ya’amsa da “Ameen”. Sannan yaƙara da faɗin, “ya kamata kije kiyi mata siracen nan dare na yi”.
“To Malam”. Lantana tace hakan tana miƙewa bayan ta harhaɗa kwanonin tuwon da suka ci
Kichen takai sannan ta wanke hannun ta tanufi cikin ɗakin ta don ɗauko turaren
Shi kuwa Malam Umaru gyara zaman sa yayi bayan ya gama wanke hannun sa da baki da butan dake ajiye a gaban sa, rediyon sa yajawo yakunna yana karawa a kunne bayan ya jingina da bango ta yanda zai ji daɗi.
Sai da tagama yin mata siracen sannan tarufo ƙofan tadawo wajen Malam tazauna suna ɗan taɓa hira jefi-jefi yana kuma sauraron rediyon sa, ahaka har dare ya tsala kafin su je su kwanta.
Washe gari RAUDHA bata farka ba har dare, wuni Lantana take yi a ɗakin tazauna tasaka ta gaba tana ta kallo, ko kaɗan bata rabo da mamaki aranta, komi zuwan mata arai yake yi game da RAUDHAN, duk da kuwa ɗari bisa ɗari ta yarda da mutum ce ita, amma kuma wani lokacin sai tayi tunanin ko dai ba ƴar nan bace? to daga ina take me yakawo ta nan da har Mijin ta zai tsince ta? Abubuwa dai kala-kala.
The following day bayan Malam Umaru ya tafi aikin gonan shi itama Lantana tashirya don tafiya bikin ƴar ƙanwar baban ta da ake yi a cikin anguwan, rufe ɗakin da RAUDHA take kwance tayi tasaka igiya ta ɗaure sannan tafice agidan bayan ta jawo ƙyauren gidan
Babu me shigo musu gida don haka bata ji ɗar ɗin barin RAUDHA ɗin ita kaɗai ba, duk da bata da tabbacin zata iya farkawa ko kuwa baza ta farka ba.
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
“Kai Baaba sanƙamo min wayar ka in saka layina ciki don nawan nan ba kanta ƙalau ba, kuma ina tunanin zuwa anjima Master zai kira ni”.
Miƙo masa wayan yayi yana cewa, “to yanzu da ƙarfe nawa zan zo ɗaukar ka?”
Wulla idanun sa Basiru yayi cike da duniyan ci yace, “zuwa dare kazo ka sanƙame Ni sai mu fantsama”.
“Ok ba damuwa”.
Wayan yamiƙa masa yana buɗe motan yafito yana faman gyara wandon sa, sai da yayi dogon hamma yagama miƙar sa kafin yabugo ƙofan motan yarufe, sannan yasaƙalo da kansa cikin motan yana kallon Ƙwaro yace, “Kai Baaba ka biya ku taho tare da Garzali don yau akwai fa zaman meating, kar kace kuma ban faɗa maka ba”.
“Baka da damuwa ai Oga, zan biya mu taho tare”.
Janye kansa Basiru yayi kafin yajuya yanufi gidan su bayan ya ɗaga masa yatsu biyu yana masa umarnin tafiya.
Da fito yashiga gidan yana jan ƙafafu tamkar me koyan tafiya, nan kuwa duk cikin iskancin sa ne, wur-wurga idanu yasoma yi cikin gidan still yana ci gaba da fiton sa, shi dama ba wai damuwar sa bane da ganin iyayen nasa don haka ya hura hanci yanufi ɗakin sa, ganin an ɗaure ɗakin da igiya sai yaja tsaki yana faɗin, “kai wlh Lantana wata iriyan baƙauyiya ce, har yanzu taƙi tafaso gari ta waye, don wulaƙanci da igiya ne zata ɗaure min ɗaki duk da tasan akwai eya ne a ɗakin, wa billahil lazi nashiga naga anyi min wuff da kaya sai na nuna mata asalin kalo na agidan nan”.
Da ƙarfi ya buga ƙofan ɗakin da ƙafan sa yaburma ciki
Ganin mutum kwance a akan katifar sa yayi saurin ja da baya yana ƙara ware idanun sa, sai yanzu ya tabbatar da eh mutum ce a kwance cikin ɗakin sa
“Kutt.. mar uba..” yafaɗa da ƙarfi idanun sa akan RAUDHA
Dasauri yamatsa jikin katifan don yasake tabbatar da zargin sa yasaka hannu ya yaye zanin da aka rufe mata jiki, nan santala-santalan fararen dogayen ƙafafun ta suka bayyana, baki sake yatsaya yana kallon ta batare da ya nuna tsorata ba da ganin ta ɗin, sai kuma yakece da dariya yana faɗin
“Wlh tsuntsu daga sama gashashshe kuttt..”
Yariƙe bakin sa dake buɗe still idanun sa na yawo jikin ta
“Kaii Old man ya iya zaɓi alƙur’an, hhhh wlh na yarda suna son in dawo gida in kintsu tunda suka ajiye min zuƙeƙiyar budurwa haka, yo to aina suka samo ta ne?” Yaƙariƙe maganar nasa yana ɗaga kai alamun tunani🤔
“Kai anya Old man baya satan yaran Mutane? Daga nace yayi min aure da ƴar birni sai yaje ya sanƙamo ma mutane ƴar su? Yasin wannan babu me yarda yabashi ita, wannan ai ko a yawon duniya na ban taɓa haɗuwa da kyakykyawar yarinya kamar ta ba, anya ma?..”
Sai kuma yayi shiru yana duƙawa gaban ta yasoma shafa ta, jin wani irin taushi da skin ɗin ta ke dashi ai tuni ya soma lanɗe baki
“Na rantse da Allah ko aljana ce yarinyan nan sai na kusance ta, wayyo daɗi”.
Dasauri ya miƙe ya soma cire kayan sa cikin zumuɗi da tsananin sha’awan da yataso masa sakamakon taɓa ta da yayi, har wani rawa-rawa jikin sa ke yi.😅Subhanallah.. me kake yi haka Basiru?” Cewar Lantana da tashigo cikin ɗakin tahangi Basiru na ƙoƙarin zuge zip ɗin wandon sa
+
Cak yatsaya yana juyowa yakalle ta a kaikaice, sai kuma yakwashe da dariya yana nuna ta da yatsa yace “Kinji ki Lantana da wani zance, yo me zan yi kuwa in ba eya ne ba kin gane ai?” Yaƙarike maganar yana ɗage mata gira
Lantana da tagane abinda yake nufi tace “shin Basiru kanka ɗaya kuwa? agidan iyayen ka ko kunyan mu baka ji shine kazo zaka hayayyaƙe wa yarinya haka kawai baka san komi akanta ba”.
“To Lantana Ina ce matar da kuka yi min ne tunda nace muku kuyo min aure?”
Girgiza kanta tayi tace “A’a wannan yarinyan mahaifin ka yatsinto ta acikin jeji, ina mu ina aura maka wannan yarinyan?”
Tsaki yaja yace “to wlh ko ma ƴar uban wacece ta zama nawa, wlh ita zaku aura min don tayi min, ki ware kawai ki bar Ni nashaƙata da ita..”
Be rufe baki ba ƙaran da RAUDHA tasaki yakaraɗe ilahirin gidan baki ɗaya, idanun ta a rufe suke har a time ɗin batare da ta buɗe su ba
Dasauri Basiru yazuƙuna agaban ta yariƙo hannun ta yana cewa “ke ke ke buɗe idon ki mana, mafarki kike yi ne? Halan Ni kika gani ƴar kyakykyawa?”
Ahankali RAUDHAN tabuɗe idanun ta tana tsai dasu kan Basiru dake gaban ta riƙe da hannun ta yana washe mata baki, lumshe idanunta tayi tasake buɗe wa akansa, kamar an tsikare ta kuma tayi zumbur tatashi zaune tana wurwurga idanu cikin ɗakin cike da tsananin tsoro
Bata kai ga tantance inda take ba Basiru yajawo ta jikin sa yana faɗin “sannu kyakykyawa kin tashi daga barcin ko?”
Sai kuma yakalli Lantana dake tsaye tana kallon ikon Allah bata sake cewa komi ba
“Da Allah ki fita kin tsaya min akai, ko so kike yi kiga abinda zan mata?”
“Basiru”. Takira sunan sa cike da rawan baki, domin hankalin ta a yanzu ya tashi sosai musamman da taga Basirun dagaske yake yi don tasan halin sa
RAUDHA dake faman ƙwace jikin ta da yatattakura ya ƙwaƙume ta ƙam yana son kai hannu jikin ta, wani irin ihu taƙwalla tana ture sa, ihu kawai take yi babu ji babu gani tana faman kai masa duka, tsoro ne fal aranta sabida ganin ta a inda bata taɓa tsintan kanta ba
“Ke wlh zan ci uwar ki idan baki tsaya ba, uwar me zan miki? Ina ce zan cire miki rigan ne kisha iska naga kina zufa”.
Ganin ya ɗaga mata riga zai cire mata tariƙe da ƙarfi tana kwantsama ihu me matuƙar firgitar wa
Ita kanta Lantana roƙon sa take yi yasakar musu ƴa amma be ma san tana yi ba
Babu zato babu tsammani sai ga Basiru yayi sama an buga sa da bango, sai gashi can gefe yashe yana ƙwalla ƙaran azaba dafe da ƙeyan sa, wani irin ashar yasaki yana kallon Lantana dake tsaye itama tana kallon sa cike da tsananin mamaki, ko kaɗan bata ga sanda yaje wajen ba sai ganin sa da tayi
RAUDHA tuni ta sume babu ko numfashi a tattare da ita
Cikin azaban zafin da yaziyarce sa yace, “kuttt.. sabida wannan shegiyar yarinyan ce zaki jefo Ni nan Lantana?”
Waro idanu Lantana tayi tace, “da wani ƙarfin zan iya jefa ka nan Basiru? Wlh Ni ban ma san sanda kazo wajen ba sai ganin ka da nayi”.
Shiru yayi yana maida idanun sa kan RAUDHA, mamaki ne fal aransa don shima yasan Lantana bata da ƙarfin da zata iya mishi irin wannan jifan, ko mahaifin sa da yake da ƙarfi bazai iya masa wannan ba bare ita
“To wanene ya jefo Ni nan ɗin?” Yafaɗa afili
Kiran da Malam Umaru yake kwaɗa wa Lantana yasaka tafita dasauri tana amsa wa
A bakin ƙofa suka yi kicibir
“Yauwa Malam gwara da Allah yakawo ka, wlh Basiru ne zai yi wa ƴar mutane ta’asa, mun shiga uku Malam idan asirin mu ya tonu”. Sai tafashe da kuka
Cikin tashin hankali Malam Umaru yatambaye ta “ina Basirun?”
“Yana ciki”.
Wuce ta yayi ya shiga ɗakin tana take masa baya
Basirun na nan a inda yake, sai muzurai yake yi jin muryan Baban sa
Kallo ɗaya Malam Umaru yayi masa yanufi wajen RAUDHA, dasauri yasaka hannu yaɗauke ta yafito da ita zuwa ɗakin su, ajiye ta yayi ya saka Lantana ta ɗibo masa ruwa, amsa yayi bayan ta kawo ya shafa mata a fuska, bata farfaɗo ba sai da ya sake shafa mata wajen sau uku kafin taja numfashi tabuɗe idanun ta da suka shige ciki sukai matuƙar ja, abun zai baka mamaki idan ka kalli idanun RAUDHA
Su kansu Malam da Lantana sai da suka tsorata ganin yanda idanun nata suka sauya kala, har wani kore-kore suke yi sabida tsaban ja
Hankalin su be tashi ba sai da tasaka musu kuka me ban tausayi, wani irin kuka take yi tamkar ta haukace, gaba ɗaya ta firgice musu da kukan nata sun rasa yanda zasu yi da ita, gashi taƙi yin magana duk da kuwa tana son yin maganan, sai dai da zaran ta buɗe baki sai ta kasa sarrafa abinda zata ce illa kuka kaɗai da take iya yi
Daƙyar Malam Umaru ya dage da yin mata addu’a har kukan nata ya lafa, sai kuma ta firgice musu akan dole sai sun kai ta gida
Malam Umaru yace, “baiwar Allah ki nutsu ki kwantar da hankalin ki sai ki faɗa mana inda kike mu maida ke kinji?”
Gyaɗa masa kai tayi tana jan majina, cikin dashashshiyar muryan ta da yaƙara shigewa sosai don daƙyar ake iya jin me take cewa, tafaɗa masa inda take a Asokoro
Dayake Malam Umaru yana shiga birni sosai, kuma yana jin sunan anguwan duk da be taɓa zuwa ba, but idan ya tambaya ai za’a iya kai sa tunda ba ɓoyayyen wuri bane, don haka yasaka RAUDHA tatashi ya kai ta
Abin mamaki ta kasa tafiya domin ƙafar ta ɗaya ya markwaɗe tamkar na kuturwa sai zafi yake mata, kuka tasaka tana komawa tazauna
Cike da tausayi Lantana tace, “Malam yarinyan nan fa baza ta iya tafiya ba, kar dai wani abun ne yasame ta? aje a ɗauko me gyara ya duba ta”.
RAUDHA dake kuka tasake ɓarke musu da kuka “wai sai dai su kai ta gidan su”.
Abun har mamaki yake basu, yarinya sai kace ba mutum ba, ta ishe su da kuka sai kace sun sato ta, su kansu sun san ba ƙaramar taɓararriya bace ita ɗin, tunda gashi duk ta hana su kwanciyar hankali
Sai da Malam Umaru yasake rarrashin ta akan tazauna zai je yasamo me mota sai su tafi, hakan kuwa yafaru be jima ba yadawo da me keke napep, shi ya ɗauke ta ya kai ta har waje cikin keke napep ɗin tunda baza ta iya tafiya ba, sannan suka tafi.
🌐🌐🌐
Sanda suka isa ƙofar gidan Suhaib, wani daɗi ne sosai ya kama RAUDHA, sai dai rashin tafiyar ta ya saka dole sai da tajira Malam Umaru ya sake ɗaukar ta, dayake RAUDHA bata da nauyin jiki ko kaɗan kasancewar ta ba me yawan cin abinci ba, that’s why Malam Umaru idan ya ɗauke ta tamkar ya ɗauko ƴar baby
Itace me buga Gate ɗin gidan, sai dai shiru ba’a zo an buɗe ba
Hakan yasa Malam Umaru yaduƙa yaɗauko dutse yayi amfani dashi wajen buga Gate ɗin
Babu jimawa kuwa me gadin yafito a fusace don ganin me buga musu ƙofa haka, tozali da RAUDHA da yayi a hannun Malam Umaru sai yayi saurin wangale musu ƙaramin Door ɗin da yafito ta ciki yana ma RAUDHA sannu, duk da kuwa mamaki ne fal aransa da al’ajabin ganin ta hannun wannan dattijon
Me gadin biyo su yayi yana nuna wa Malam Umaru inda zai bi, sai kace an saka sa
RAUDHA na jin sa don haka bata yi magana ba ma.
Suhaib na zaune shi kaɗai a parlour’n lokacin da suka shigo, dasauri ya ɗago kansa idanun sa da suka gama faɗa wa suka sauka kan RAUDHA
Kafin ma yayi magana ta kwaɗa masa kira
Ai tuni yayi zumbur ɗin tashi ya nufo su da mahaukacin sauri, jikin sa na rawa yasaka hannu ya amshe ta yana kiran sunan ta
Ita kuwa kuka ta saka masa tana ƙamƙame sa sosai.
Hayaniyan su ne yafito da Farida, ganin RAUDHA ba ƙaramin saka ta farin ciki yayi ba, ai tuni itama ta nufo su tana nuna murnan ta
Tsawon mintuna goma Suhaib na rungume da RAUDHA a jikin sa yaƙi sauke ta, faɗan tsantsan farin cikin ma da yake ciki ɓata lokaci ne, domin har da hawayen sa sabida tsaban murna.
Malam Umaru dai na gefe ya saki baki yana kallon abun mamaki
Sai Farida ne ma da takula dashi tayi masa maganar ya shigo ya zauna
Sai da yazauna kafin shima Suhaib yataho RAUDHA na jikin sa ya zauna
Ganin RAUDHAN ta ƙi dena kuka sai ya soma rarrashin ta, yana share mata hawaye da hannayen sa
“Kinga yi shiru my dear, ai gashi kin dawo ko? Babu abinda zai sake raba mu insha Allahu, yi shiru ki nutsu ki faɗa min waɗanda suke da hannu wajen ɗauke ki, nayi miki alƙawari sai na ɗau babban mataki akan su”.
Sake sakin kuka RAUDHA tayi tana ƙwaƙume shi tamkar zata koma Cikin sa
Idanun Suhaib jazur ya ɗago kansa yana kallon Malam Umaru ya ce, “Malam menene haɗin ka da ƙanwata? Ya akayi tazo hannun ka?”.
Malam Umaru duk jikin sa ya yi sanyi, daƙyar ya iya cewa, “wlh nima yallaɓai tsintan ta nayi a wani jeji, shine na taimake ta”.
Daga nan ya soma faɗa musu komai tiryan-tiryan
Sosai hankalin Suhaib ya sake tashi da jin ƙanwar sa a jeji aka tsince ta, kuma cikin mawuyacin hali, Allah kaɗai yasa da rabon zata sake rayuwa har su gana, da tuni Dabbobin daji sun cinye masa ƙanwa
Ɗago kanta yayi yana kallon ta cike da tsantsan tausayawa, kana ya kalli ƙafan nata, ai kuwa sai da hawaye suka cika masa idanu sabida ganin ƙafan a nanƙwaye, saurin saka hannu yayi ya taɓa
Sai ta callara ƙara sabida azaban da ya ziyarce ta
Nan da nan Suhaib ya sake ruɗe wa, miƙe wa yayi dasauri ya saɓa ta a kafaɗa yana kallon Farida ya ce, “Wifey sallami bawan Allan nan, zan kai ta asibiti aduba mata lafiyan ƙafan ta”.
Be jira cewar ta ba yajuya yafice dasauri, a back seat ya kwantar da ita yashiga mazaunin drever, da wani irin Speed yaja motan yanufi gate yana danna Horn da ƙarfi
Tuni me gadi ya buɗe masa ya fice.Suna zuwa asibiti aka amshe ta sabida ya saki kuɗi, Doctors sun yi iya yin su don ganin ƙafar RAUDHA ya dawo dai-dai, duk da duk wani bincike da suka yi basu gano matsalan ba, kuma shi ƙafan ba targaɗe ba; ba karaya ba ba komi ba, lokacin da zasu jajja mata ƙafan sai da suka yi mata alluran barci, shiyasa har suka gama duk abun da zasu yi bata san ma suna yi ba
+
Doctor ɗin da ya jagoranci duba ta, yayi wa Suhaib bayani basu gano komi ba, amma dai sun saka mata magani da yardan Allah ƙafan zai dawo dai-dai, a hasashen da suka yi.
Wajen ƙarfe 03:20pm. Drever yakawo Farida, har da abinci ta taho musu dashi, kuma bata tafi ba sai da ta ga farkawan RAUDHAN
Suhaib ne yayi ruwa yayi tsaki akan shi zai kwana, duk da Faridan tace masa “ya bari zata kwana da ita”. But yaƙi, dole tatafi ta bar shi.
Washe gari alhmadulillah ƙafan nata ya dawo dai-dai, sai dai ba duka ba, kuma tana jin zafi sosai idan ta taka
Anan Suhaib ya tambaye ta abinda ya faru a ranan, domin shi so yake yi ya hukunta waɗanda sukai sanadin shigar ta haka
Sai dai ta kasa tuna komi, abinda zata iya tuna wa kawai zuwan ta club da fitowar ta haraban wajen, sai kuma farkawan da tayi ta ganta gidan Malam Umaru
Da damuwa Suhaib ya kalle ta yace, “Dear ki dai sake tunani ko zaki tuna wani abun?”
Ɓata fuska RAUDHA dake shan ferfesun zabo tayi, tana zaune saman gadon mara sa lafiya tayi ɗai-ɗai abun ta, tana shirin magana ne wayan Suhaib ɗin tayi ƙara
Ciro ta daga aljihu yayi yana kallon screan ɗin wayan da mamaki, domin dai ba kowa ya kira sa ba illa drevern gidan sa
Ɗauka yayi yakara a kunne yana tambayan sa “Lafiya?” Batare da ya jira cewar sa ba, bare kuma su gaisa
Drever’n faɗa masa yayi gasu a asibiti ya kawo Farida babu lafiya
Tashin hankali ne yasake riskan Suhaib, nan da nan ya tashi ya fice batare da ya bi takan RAUDHA dake masa magana ba
Sai ta kwaɓe fuska tana turo baki, ajiye Plate ɗin tayi akan drowan kusa da gadon, ta ziro ƙafafuwan ta da babu takalmi ta sauko, ahankali take taka ƙafan ta tana cije leɓe, da haka ta ƙarisa bakin ƙofa tafice
Ahanya ta haɗu da Suhaib suna tsaye shi da drever sun yi cirko-cirko
Yana ganin ta yataho da sauri yana tambayan ta “meyasa ta fito?”
Kamar zata yi kuka tace masa, “ba kai ne kafito ka bar Ni ba, kuma ina maka magana ka tafi ka bar Ni”.
Riƙe kansa yayi yace, “Oh I’m sorry Baby hankali na ne ya tashi, Wifey aka kawo ba ta da lafiya, yanzu mu je ki koma kar wani abun ya same ki”.
Girgiza masa kai tayi tace, “a’a, Ni gida zan je, a sallame Ni ni dai”.
“To Baby me zaki je kiyi agida bayan duk gamu anan? Kuma kin ga ai Doctor be sallame ki ba”. Yayi maganar yana riƙo kafaɗun ta ganin kamar ta gaji tana shirin faɗuwa
Cikin yamutsa fuska tace, “yaya Ina son in je in Yi wanka ne, Please ka saka a sallame Ni, bana son zama nan”.
Be musa mata ba, yace mata su koma ɗakin, sai yaje ya nemo likitan ya basu sallaman
Shi ya taimaka mata suka koma, sannan ya zaunar da ita ya fito
Ita RAUDHA ta ƙosa taje tayi wanka ne, shiyasaka ta matsa masa sai an sallame ta, gaba ɗaya bata jin daɗin jikin ta sabida tun ranan da tabar gida rabon ta da wanka, ita da take yin wanka sama da sau uku; huɗu a rana, amma gashi kwana uku rabon ta da tayi, ita kanta ƙyanƙyamin jikin ta take yi, musamman ma idan ta tuna gidan da tatashi ta tsinci kanta, da ɗaukan da Malam Umaru yayi mata, sai dai babu yanda zata yi tunda ahalin lalura take a lokacin.
Drever ya kai ta gida, tana zuwa wanka tayi tasaka ƴar shimi tahaye gado sai barci, ko tunanin ma ta koma asibiti taga halin da Farida take ciki bata yi ba.
Can kuwa a asibitin har wajen awanni huɗu babu haihuwar Farida, duk ta galabaita
Lokacin tuni Umman ta da Ƙanwar ta Maryam sun zo, har babban Yayan su da matar sa duk sun zo, gaba ɗaya sun yi jigun-jigun a reception ɗin suna jiran Likitoci
Sai Suhaib ne da Babban Yayan su suke zirga-zirga wajen samo abin da ake nema
Gab da magriba ta haifo ɗan ta na Miji kyakykyawa irin Suhaib sak, kowa yayi murna sosai, barin ma da aka ce musu babu abunda ke damun Farida, sai dai yaron ne tamkar bashi da lafiya don yaƙi yin kuka
Likitoci sun yi duk binciken da zasu yi akai, sannan suka sanar da Suhaib ɗin abinda ke damun yaron
Be da wani ƙoshin lafiya, irin cutan nan da yake mayar da mutum tamkar soko, yayi ta zulalan miyau, kansa yaƙi tsayuwa waje ɗaya, haka yaron yanzu yake yi, sai dai kasancewar sa jariri baza ka ga alamun zub da miyau ɗin nasa ba, sai idan ya girma
Suhaib ya shiga damuwa sosai, amma likitan ya kwantar masa da hankali, zasu ɗaura sa akan magani idan an dace komi zai wuce, da haka Suhaib ya fito Office ɗin likitan da ƙwarin gwiwa, tunda yaji akwai maganin ciwon yaron nasa, wataran kenan yana iya warke wa.
Koda yashiga ɗakin da aka kwantar da Farida duk ƴan uwan ta ne aciki, tana zaune itama tana shan tea da aka haɗa mata, yaron na kwance gefen ta baza ka ce akwai wani abinda ke damun sa ba
Ɗaukan yaron yayi yana kallon sa cike da farin ciki, ya jima yana riƙe da yaron a hannun sa kafin ya ajiye sa, yayi musu sallama akan zai je ya dawo yafice.
Gida ya wuce kai tsaye, koda yashiga parlour’n be tarar da RAUDHA ba, don haka ɗakin ta yawuce yashiga
Tana kwance har yanzu tana barci
Numfashi yasauke ya ƙarisa bakin gadon, ɗaga kanta yayi yacire pilon yazauna sannan ya ɗaura kanta saman cinyan sa, kallon ta kawai yake yi cike da tausayi, Allah ya gani yana ƙaunar ƙanwar tasa fiye da komi na duniya, soyayyar da yake mata baki ma bazai iya faɗan sa ba
Shafa gashin kanta yake yi idanun sa akanta, sai dai tunani yalula me zurfi, sai da yaji kiran sallan isha’i kafin yatashi ya gyara mata kwanciyar ta yafice
Ɗakin sa ya wuce yashiga Toilet, wanka yasoma yi, don rabon sa da wanka shima ɗin tun washe garin ɓatan RAUDHA, sai da ya ɗauro alwala kafin yafito, shirin sa yayi cikin sauri ya ɗau keey ɗin mota ya fice, sai da yatsaya a masallacin layin nasu yayi Sallah tukun ya wuce asibiti.
A lokacin su Umma duk sun tafi gida, sai Maryam da aka bari wajen ta
Shima ɗin koda ya isa ba wai zama yayi sosai ba, zuwa ƙarfe goma yayi musu sallama yadawo gida tunda Maryam ɗin zata kwana da ita.
Koda yadawo ya tarar da RAUDHA zaune a Parlour, tana ganin shi tanufe sa tarungume shi tana masa shagwaɓa, shi kuma sai biye mata yake yi
Koda taji Farida ta haihu bata wani nuna murnan ta ba, ba wai don bata yi farin ciki ba
Shima kuma be damu ba, sai yaja hannun ta suka tafi kan dainning suka soma cin abinci, ita kaɗan taci tunda tarigada taci kafin yazo, daga nan Parlour suka koma, ita kwanciya tayi shi kuma aiki yasoma yi cikin Lapton ɗin sa, kasancewar kwana biyu be je Office ba shiyasaka yake ragewa kar su taru mishi
Sai wajen 12:30am. Ya tashi, lokacin tuni RAUDHA tayi barci, sai ɗaukan ta yayi yamaida ita ɗakin ta, yarufe ta da bargo tare da ƙara mata A.C yafice.
Kamar shuɗewar awa ɗaya RAUDHA tasoma mummunan mafarki irin na ranan nan, gaba ɗaya ta haɗa gumi da zufa sai makyarkyata take yi, kuma har alokacin bata farka ba
Ƙaton maciji ne yake bin ta acikin baƙin dajin me tsananin duhu da sunkuru, kuka take tayi tana gudu tana waigen bayan ta, duk da kuwa bata ma ganin komi acikin dajin sai macijin nan me kamar wuta jikin sa
Sai da ya cafko ta yana ƙoƙarin haɗiye ta tafarka da ihu me tsananin ƙara, babu inda jikin ta baya rawa, ga kanta da yake faman sara mata kamar zai rabu gida biyu sabida dariyan da ya cika ɗakin, lokaci ɗaya numfashin ta yarabu da gangan jikin ta takoma yaraf kan gadon
Kamar wancan lokacin ihun ta babu wanda yaji agidan, har garin Allah ya waye
Zuwa tara Suhaib ya gama shirin sa zai koma Hospital ɗin, ya saka kuku ya haɗa masa Breakfast Wanda zai kai musu can
Ɗakin RAUDHA yashiga, sai dai ganin ta har yanzu tana barci be tashe ta ba yafice.
Sai ƙarfe 12:40pm. Kafin RAUDHA ta tashi, babu abinda ta tuna na game da mafarkin ta, sai dai yanda gaba ɗaya jikin ta ke mata ciwo ga tsananin zazzaɓi da yarufe ta, yunwa da ishin ruwa duk ya addabe ta, ita kanta mamakin yanda take jin wani irin bahagon yunwa take yi, ga bakin ta gaba ɗaya ya ƙafe daƙyar take iya samun miyau ɗin da take haɗiya
Rarrafa wa tayi tamiƙe tasauko daga kan gadon, sai dai kuma ƙafan ta ya riƙe sosai daƙyar take iya taka wa, zafi sosai yake mata ba kamar yanda ta kwanta jiya dashi ba, lumshe idanun ta tayi sai ga hawaye sun soma sulmiyo mata, hannu ta saka tashare kafin ta ɗingiza ahankali tanufi gaban Fridge, domin ji take yi tamkar zata mutu idan ba tayi gaggawar shan ruwan ba, ga jikin ta dake mata ciwo ko ina, kamar an hau jikin ta an kwana sukuwa a kanta haka take ji
Buɗe Fridge ɗin tayi taciro goran ruwa, tunda ta kafa a baki bata dakata ba sai da tayi rabin ruwan, kana ta zube nan ƙasa da rawan jiki, nan da nan zazzaɓin ya sake rufe ta, ta kwanta tana kuka sai juye-juye take yi.
Allah ne yakawo mata Ester, ta shigo gyara mata ɗakin, ai kuwa nan hankalin ta yatashi ta nufe ta tana kiran sunan ta, sai dai gani tayi tamkar ba ta numfashi, nan da nan ta sake rikice wa tatashi da gudu ta fice.
Suna zuwa asibiti aka amshe ta sabida ya saki kuɗi, Doctors sun yi iya yin su don ganin ƙafar RAUDHA ya dawo dai-dai, duk da duk wani bincike da suka yi basu gano matsalan ba, kuma shi ƙafan ba targaɗe ba; ba karaya ba ba komi ba, lokacin da zasu jajja mata ƙafan sai da suka yi mata alluran barci, shiyasa har suka gama duk abun da zasu yi bata san ma suna yi ba
+
Doctor ɗin da ya jagoranci duba ta, yayi wa Suhaib bayani basu gano komi ba, amma dai sun saka mata magani da yardan Allah ƙafan zai dawo dai-dai, a hasashen da suka yi.
Wajen ƙarfe 03:20pm. Drever yakawo Farida, har da abinci ta taho musu dashi, kuma bata tafi ba sai da ta ga farkawan RAUDHAN
Suhaib ne yayi ruwa yayi tsaki akan shi zai kwana, duk da Faridan tace masa “ya bari zata kwana da ita”. But yaƙi, dole tatafi ta bar shi.
Washe gari alhmadulillah ƙafan nata ya dawo dai-dai, sai dai ba duka ba, kuma tana jin zafi sosai idan ta taka
Anan Suhaib ya tambaye ta abinda ya faru a ranan, domin shi so yake yi ya hukunta waɗanda sukai sanadin shigar ta haka
Sai dai ta kasa tuna komi, abinda zata iya tuna wa kawai zuwan ta club da fitowar ta haraban wajen, sai kuma farkawan da tayi ta ganta gidan Malam Umaru
Da damuwa Suhaib ya kalle ta yace, “Dear ki dai sake tunani ko zaki tuna wani abun?”
Ɓata fuska RAUDHA dake shan ferfesun zabo tayi, tana zaune saman gadon mara sa lafiya tayi ɗai-ɗai abun ta, tana shirin magana ne wayan Suhaib ɗin tayi ƙara
Ciro ta daga aljihu yayi yana kallon screan ɗin wayan da mamaki, domin dai ba kowa ya kira sa ba illa drevern gidan sa
Ɗauka yayi yakara a kunne yana tambayan sa “Lafiya?” Batare da ya jira cewar sa ba, bare kuma su gaisa
Drever’n faɗa masa yayi gasu a asibiti ya kawo Farida babu lafiya
Tashin hankali ne yasake riskan Suhaib, nan da nan ya tashi ya fice batare da ya bi takan RAUDHA dake masa magana ba
Sai ta kwaɓe fuska tana turo baki, ajiye Plate ɗin tayi akan drowan kusa da gadon, ta ziro ƙafafuwan ta da babu takalmi ta sauko, ahankali take taka ƙafan ta tana cije leɓe, da haka ta ƙarisa bakin ƙofa tafice
Ahanya ta haɗu da Suhaib suna tsaye shi da drever sun yi cirko-cirko
Yana ganin ta yataho da sauri yana tambayan ta “meyasa ta fito?”
Kamar zata yi kuka tace masa, “ba kai ne kafito ka bar Ni ba, kuma ina maka magana ka tafi ka bar Ni”.
Riƙe kansa yayi yace, “Oh I’m sorry Baby hankali na ne ya tashi, Wifey aka kawo ba ta da lafiya, yanzu mu je ki koma kar wani abun ya same ki”.
Girgiza masa kai tayi tace, “a’a, Ni gida zan je, a sallame Ni ni dai”.
“To Baby me zaki je kiyi agida bayan duk gamu anan? Kuma kin ga ai Doctor be sallame ki ba”. Yayi maganar yana riƙo kafaɗun ta ganin kamar ta gaji tana shirin faɗuwa
Cikin yamutsa fuska tace, “yaya Ina son in je in Yi wanka ne, Please ka saka a sallame Ni, bana son zama nan”.
Be musa mata ba, yace mata su koma ɗakin, sai yaje ya nemo likitan ya basu sallaman
Shi ya taimaka mata suka koma, sannan ya zaunar da ita ya fito
Ita RAUDHA ta ƙosa taje tayi wanka ne, shiyasaka ta matsa masa sai an sallame ta, gaba ɗaya bata jin daɗin jikin ta sabida tun ranan da tabar gida rabon ta da wanka, ita da take yin wanka sama da sau uku; huɗu a rana, amma gashi kwana uku rabon ta da tayi, ita kanta ƙyanƙyamin jikin ta take yi, musamman ma idan ta tuna gidan da tatashi ta tsinci kanta, da ɗaukan da Malam Umaru yayi mata, sai dai babu yanda zata yi tunda ahalin lalura take a lokacin.
Drever ya kai ta gida, tana zuwa wanka tayi tasaka ƴar shimi tahaye gado sai barci, ko tunanin ma ta koma asibiti taga halin da Farida take ciki bata yi ba.
Can kuwa a asibitin har wajen awanni huɗu babu haihuwar Farida, duk ta galabaita
Lokacin tuni Umman ta da Ƙanwar ta Maryam sun zo, har babban Yayan su da matar sa duk sun zo, gaba ɗaya sun yi jigun-jigun a reception ɗin suna jiran Likitoci
Sai Suhaib ne da Babban Yayan su suke zirga-zirga wajen samo abin da ake nema
Gab da magriba ta haifo ɗan ta na Miji kyakykyawa irin Suhaib sak, kowa yayi murna sosai, barin ma da aka ce musu babu abunda ke damun Farida, sai dai yaron ne tamkar bashi da lafiya don yaƙi yin kuka
Likitoci sun yi duk binciken da zasu yi akai, sannan suka sanar da Suhaib ɗin abinda ke damun yaron
Be da wani ƙoshin lafiya, irin cutan nan da yake mayar da mutum tamkar soko, yayi ta zulalan miyau, kansa yaƙi tsayuwa waje ɗaya, haka yaron yanzu yake yi, sai dai kasancewar sa jariri baza ka ga alamun zub da miyau ɗin nasa ba, sai idan ya girma
Suhaib ya shiga damuwa sosai, amma likitan ya kwantar masa da hankali, zasu ɗaura sa akan magani idan an dace komi zai wuce, da haka Suhaib ya fito Office ɗin likitan da ƙwarin gwiwa, tunda yaji akwai maganin ciwon yaron nasa, wataran kenan yana iya warke wa.
Koda yashiga ɗakin da aka kwantar da Farida duk ƴan uwan ta ne aciki, tana zaune itama tana shan tea da aka haɗa mata, yaron na kwance gefen ta baza ka ce akwai wani abinda ke damun sa ba
Ɗaukan yaron yayi yana kallon sa cike da farin ciki, ya jima yana riƙe da yaron a hannun sa kafin ya ajiye sa, yayi musu sallama akan zai je ya dawo yafice.
Gida ya wuce kai tsaye, koda yashiga parlour’n be tarar da RAUDHA ba, don haka ɗakin ta yawuce yashiga
Tana kwance har yanzu tana barci
Numfashi yasauke ya ƙarisa bakin gadon, ɗaga kanta yayi yacire pilon yazauna sannan ya ɗaura kanta saman cinyan sa, kallon ta kawai yake yi cike da tausayi, Allah ya gani yana ƙaunar ƙanwar tasa fiye da komi na duniya, soyayyar da yake mata baki ma bazai iya faɗan sa ba
Shafa gashin kanta yake yi idanun sa akanta, sai dai tunani yalula me zurfi, sai da yaji kiran sallan isha’i kafin yatashi ya gyara mata kwanciyar ta yafice
Ɗakin sa ya wuce yashiga Toilet, wanka yasoma yi, don rabon sa da wanka shima ɗin tun washe garin ɓatan RAUDHA, sai da ya ɗauro alwala kafin yafito, shirin sa yayi cikin sauri ya ɗau keey ɗin mota ya fice, sai da yatsaya a masallacin layin nasu yayi Sallah tukun ya wuce asibiti.
A lokacin su Umma duk sun tafi gida, sai Maryam da aka bari wajen ta
Shima ɗin koda ya isa ba wai zama yayi sosai ba, zuwa ƙarfe goma yayi musu sallama yadawo gida tunda Maryam ɗin zata kwana da ita.
Koda yadawo ya tarar da RAUDHA zaune a Parlour, tana ganin shi tanufe sa tarungume shi tana masa shagwaɓa, shi kuma sai biye mata yake yi
Koda taji Farida ta haihu bata wani nuna murnan ta ba, ba wai don bata yi farin ciki ba
Shima kuma be damu ba, sai yaja hannun ta suka tafi kan dainning suka soma cin abinci, ita kaɗan taci tunda tarigada taci kafin yazo, daga nan Parlour suka koma, ita kwanciya tayi shi kuma aiki yasoma yi cikin Lapton ɗin sa, kasancewar kwana biyu be je Office ba shiyasaka yake ragewa kar su taru mishi
Sai wajen 12:30am. Ya tashi, lokacin tuni RAUDHA tayi barci, sai ɗaukan ta yayi yamaida ita ɗakin ta, yarufe ta da bargo tare da ƙara mata A.C yafice.
Kamar shuɗewar awa ɗaya RAUDHA tasoma mummunan mafarki irin na ranan nan, gaba ɗaya ta haɗa gumi da zufa sai makyarkyata take yi, kuma har alokacin bata farka ba
Ƙaton maciji ne yake bin ta acikin baƙin dajin me tsananin duhu da sunkuru, kuka take tayi tana gudu tana waigen bayan ta, duk da kuwa bata ma ganin komi acikin dajin sai macijin nan me kamar wuta jikin sa
Sai da ya cafko ta yana ƙoƙarin haɗiye ta tafarka da ihu me tsananin ƙara, babu inda jikin ta baya rawa, ga kanta da yake faman sara mata kamar zai rabu gida biyu sabida dariyan da ya cika ɗakin, lokaci ɗaya numfashin ta yarabu da gangan jikin ta takoma yaraf kan gadon
Kamar wancan lokacin ihun ta babu wanda yaji agidan, har garin Allah ya waye
Zuwa tara Suhaib ya gama shirin sa zai koma Hospital ɗin, ya saka kuku ya haɗa masa Breakfast Wanda zai kai musu can
Ɗakin RAUDHA yashiga, sai dai ganin ta har yanzu tana barci be tashe ta ba yafice.
Sai ƙarfe 12:40pm. Kafin RAUDHA ta tashi, babu abinda ta tuna na game da mafarkin ta, sai dai yanda gaba ɗaya jikin ta ke mata ciwo ga tsananin zazzaɓi da yarufe ta, yunwa da ishin ruwa duk ya addabe ta, ita kanta mamakin yanda take jin wani irin bahagon yunwa take yi, ga bakin ta gaba ɗaya ya ƙafe daƙyar take iya samun miyau ɗin da take haɗiya
Rarrafa wa tayi tamiƙe tasauko daga kan gadon, sai dai kuma ƙafan ta ya riƙe sosai daƙyar take iya taka wa, zafi sosai yake mata ba kamar yanda ta kwanta jiya dashi ba, lumshe idanun ta tayi sai ga hawaye sun soma sulmiyo mata, hannu ta saka tashare kafin ta ɗingiza ahankali tanufi gaban Fridge, domin ji take yi tamkar zata mutu idan ba tayi gaggawar shan ruwan ba, ga jikin ta dake mata ciwo ko ina, kamar an hau jikin ta an kwana sukuwa a kanta haka take ji
Buɗe Fridge ɗin tayi taciro goran ruwa, tunda ta kafa a baki bata dakata ba sai da tayi rabin ruwan, kana ta zube nan ƙasa da rawan jiki, nan da nan zazzaɓin ya sake rufe ta, ta kwanta tana kuka sai juye-juye take yi.
Allah ne yakawo mata Ester, ta shigo gyara mata ɗakin, ai kuwa nan hankalin ta yatashi ta nufe ta tana kiran sunan ta, sai dai gani tayi tamkar ba ta numfashi, nan da nan ta sake rikice wa tatashi da gudu ta fice.
Suna zuwa asibiti aka amshe ta sabida ya saki kuɗi, Doctors sun yi iya yin su don ganin ƙafar RAUDHA ya dawo dai-dai, duk da duk wani bincike da suka yi basu gano matsalan ba, kuma shi ƙafan ba targaɗe ba; ba karaya ba ba komi ba, lokacin da zasu jajja mata ƙafan sai da suka yi mata alluran barci, shiyasa har suka gama duk abun da zasu yi bata san ma suna yi ba
+
Doctor ɗin da ya jagoranci duba ta, yayi wa Suhaib bayani basu gano komi ba, amma dai sun saka mata magani da yardan Allah ƙafan zai dawo dai-dai, a hasashen da suka yi.
Wajen ƙarfe 03:20pm. Drever yakawo Farida, har da abinci ta taho musu dashi, kuma bata tafi ba sai da ta ga farkawan RAUDHAN
Suhaib ne yayi ruwa yayi tsaki akan shi zai kwana, duk da Faridan tace masa “ya bari zata kwana da ita”. But yaƙi, dole tatafi ta bar shi.
Washe gari alhmadulillah ƙafan nata ya dawo dai-dai, sai dai ba duka ba, kuma tana jin zafi sosai idan ta taka
Anan Suhaib ya tambaye ta abinda ya faru a ranan, domin shi so yake yi ya hukunta waɗanda sukai sanadin shigar ta haka
Sai dai ta kasa tuna komi, abinda zata iya tuna wa kawai zuwan ta club da fitowar ta haraban wajen, sai kuma farkawan da tayi ta ganta gidan Malam Umaru
Da damuwa Suhaib ya kalle ta yace, “Dear ki dai sake tunani ko zaki tuna wani abun?”
Ɓata fuska RAUDHA dake shan ferfesun zabo tayi, tana zaune saman gadon mara sa lafiya tayi ɗai-ɗai abun ta, tana shirin magana ne wayan Suhaib ɗin tayi ƙara
Ciro ta daga aljihu yayi yana kallon screan ɗin wayan da mamaki, domin dai ba kowa ya kira sa ba illa drevern gidan sa
Ɗauka yayi yakara a kunne yana tambayan sa “Lafiya?” Batare da ya jira cewar sa ba, bare kuma su gaisa
Drever’n faɗa masa yayi gasu a asibiti ya kawo Farida babu lafiya
Tashin hankali ne yasake riskan Suhaib, nan da nan ya tashi ya fice batare da ya bi takan RAUDHA dake masa magana ba
Sai ta kwaɓe fuska tana turo baki, ajiye Plate ɗin tayi akan drowan kusa da gadon, ta ziro ƙafafuwan ta da babu takalmi ta sauko, ahankali take taka ƙafan ta tana cije leɓe, da haka ta ƙarisa bakin ƙofa tafice
Ahanya ta haɗu da Suhaib suna tsaye shi da drever sun yi cirko-cirko
Yana ganin ta yataho da sauri yana tambayan ta “meyasa ta fito?”
Kamar zata yi kuka tace masa, “ba kai ne kafito ka bar Ni ba, kuma ina maka magana ka tafi ka bar Ni”.
Riƙe kansa yayi yace, “Oh I’m sorry Baby hankali na ne ya tashi, Wifey aka kawo ba ta da lafiya, yanzu mu je ki koma kar wani abun ya same ki”.
Girgiza masa kai tayi tace, “a’a, Ni gida zan je, a sallame Ni ni dai”.
“To Baby me zaki je kiyi agida bayan duk gamu anan? Kuma kin ga ai Doctor be sallame ki ba”. Yayi maganar yana riƙo kafaɗun ta ganin kamar ta gaji tana shirin faɗuwa
Cikin yamutsa fuska tace, “yaya Ina son in je in Yi wanka ne, Please ka saka a sallame Ni, bana son zama nan”.
Be musa mata ba, yace mata su koma ɗakin, sai yaje ya nemo likitan ya basu sallaman
Shi ya taimaka mata suka koma, sannan ya zaunar da ita ya fito
Ita RAUDHA ta ƙosa taje tayi wanka ne, shiyasaka ta matsa masa sai an sallame ta, gaba ɗaya bata jin daɗin jikin ta sabida tun ranan da tabar gida rabon ta da wanka, ita da take yin wanka sama da sau uku; huɗu a rana, amma gashi kwana uku rabon ta da tayi, ita kanta ƙyanƙyamin jikin ta take yi, musamman ma idan ta tuna gidan da tatashi ta tsinci kanta, da ɗaukan da Malam Umaru yayi mata, sai dai babu yanda zata yi tunda ahalin lalura take a lokacin.
Drever ya kai ta gida, tana zuwa wanka tayi tasaka ƴar shimi tahaye gado sai barci, ko tunanin ma ta koma asibiti taga halin da Farida take ciki bata yi ba.
Can kuwa a asibitin har wajen awanni huɗu babu haihuwar Farida, duk ta galabaita
Lokacin tuni Umman ta da Ƙanwar ta Maryam sun zo, har babban Yayan su da matar sa duk sun zo, gaba ɗaya sun yi jigun-jigun a reception ɗin suna jiran Likitoci
Sai Suhaib ne da Babban Yayan su suke zirga-zirga wajen samo abin da ake nema
Gab da magriba ta haifo ɗan ta na Miji kyakykyawa irin Suhaib sak, kowa yayi murna sosai, barin ma da aka ce musu babu abunda ke damun Farida, sai dai yaron ne tamkar bashi da lafiya don yaƙi yin kuka
Likitoci sun yi duk binciken da zasu yi akai, sannan suka sanar da Suhaib ɗin abinda ke damun yaron
Be da wani ƙoshin lafiya, irin cutan nan da yake mayar da mutum tamkar soko, yayi ta zulalan miyau, kansa yaƙi tsayuwa waje ɗaya, haka yaron yanzu yake yi, sai dai kasancewar sa jariri baza ka ga alamun zub da miyau ɗin nasa ba, sai idan ya girma
Suhaib ya shiga damuwa sosai, amma likitan ya kwantar masa da hankali, zasu ɗaura sa akan magani idan an dace komi zai wuce, da haka Suhaib ya fito Office ɗin likitan da ƙwarin gwiwa, tunda yaji akwai maganin ciwon yaron nasa, wataran kenan yana iya warke wa.
Koda yashiga ɗakin da aka kwantar da Farida duk ƴan uwan ta ne aciki, tana zaune itama tana shan tea da aka haɗa mata, yaron na kwance gefen ta baza ka ce akwai wani abinda ke damun sa ba
Ɗaukan yaron yayi yana kallon sa cike da farin ciki, ya jima yana riƙe da yaron a hannun sa kafin ya ajiye sa, yayi musu sallama akan zai je ya dawo yafice.
Gida ya wuce kai tsaye, koda yashiga parlour’n be tarar da RAUDHA ba, don haka ɗakin ta yawuce yashiga
Tana kwance har yanzu tana barci
Numfashi yasauke ya ƙarisa bakin gadon, ɗaga kanta yayi yacire pilon yazauna sannan ya ɗaura kanta saman cinyan sa, kallon ta kawai yake yi cike da tausayi, Allah ya gani yana ƙaunar ƙanwar tasa fiye da komi na duniya, soyayyar da yake mata baki ma bazai iya faɗan sa ba
Shafa gashin kanta yake yi idanun sa akanta, sai dai tunani yalula me zurfi, sai da yaji kiran sallan isha’i kafin yatashi ya gyara mata kwanciyar ta yafice
Ɗakin sa ya wuce yashiga Toilet, wanka yasoma yi, don rabon sa da wanka shima ɗin tun washe garin ɓatan RAUDHA, sai da ya ɗauro alwala kafin yafito, shirin sa yayi cikin sauri ya ɗau keey ɗin mota ya fice, sai da yatsaya a masallacin layin nasu yayi Sallah tukun ya wuce asibiti.
A lokacin su Umma duk sun tafi gida, sai Maryam da aka bari wajen ta
Shima ɗin koda ya isa ba wai zama yayi sosai ba, zuwa ƙarfe goma yayi musu sallama yadawo gida tunda Maryam ɗin zata kwana da ita.
Koda yadawo ya tarar da RAUDHA zaune a Parlour, tana ganin shi tanufe sa tarungume shi tana masa shagwaɓa, shi kuma sai biye mata yake yi
Koda taji Farida ta haihu bata wani nuna murnan ta ba, ba wai don bata yi farin ciki ba
Shima kuma be damu ba, sai yaja hannun ta suka tafi kan dainning suka soma cin abinci, ita kaɗan taci tunda tarigada taci kafin yazo, daga nan Parlour suka koma, ita kwanciya tayi shi kuma aiki yasoma yi cikin Lapton ɗin sa, kasancewar kwana biyu be je Office ba shiyasaka yake ragewa kar su taru mishi
Sai wajen 12:30am. Ya tashi, lokacin tuni RAUDHA tayi barci, sai ɗaukan ta yayi yamaida ita ɗakin ta, yarufe ta da bargo tare da ƙara mata A.C yafice.
Kamar shuɗewar awa ɗaya RAUDHA tasoma mummunan mafarki irin na ranan nan, gaba ɗaya ta haɗa gumi da zufa sai makyarkyata take yi, kuma har alokacin bata farka ba
Ƙaton maciji ne yake bin ta acikin baƙin dajin me tsananin duhu da sunkuru, kuka take tayi tana gudu tana waigen bayan ta, duk da kuwa bata ma ganin komi acikin dajin sai macijin nan me kamar wuta jikin sa
Sai da ya cafko ta yana ƙoƙarin haɗiye ta tafarka da ihu me tsananin ƙara, babu inda jikin ta baya rawa, ga kanta da yake faman sara mata kamar zai rabu gida biyu sabida dariyan da ya cika ɗakin, lokaci ɗaya numfashin ta yarabu da gangan jikin ta takoma yaraf kan gadon
Kamar wancan lokacin ihun ta babu wanda yaji agidan, har garin Allah ya waye
Zuwa tara Suhaib ya gama shirin sa zai koma Hospital ɗin, ya saka kuku ya haɗa masa Breakfast Wanda zai kai musu can
Ɗakin RAUDHA yashiga, sai dai ganin ta har yanzu tana barci be tashe ta ba yafice.
Sai ƙarfe 12:40pm. Kafin RAUDHA ta tashi, babu abinda ta tuna na game da mafarkin ta, sai dai yanda gaba ɗaya jikin ta ke mata ciwo ga tsananin zazzaɓi da yarufe ta, yunwa da ishin ruwa duk ya addabe ta, ita kanta mamakin yanda take jin wani irin bahagon yunwa take yi, ga bakin ta gaba ɗaya ya ƙafe daƙyar take iya samun miyau ɗin da take haɗiya
Rarrafa wa tayi tamiƙe tasauko daga kan gadon, sai dai kuma ƙafan ta ya riƙe sosai daƙyar take iya taka wa, zafi sosai yake mata ba kamar yanda ta kwanta jiya dashi ba, lumshe idanun ta tayi sai ga hawaye sun soma sulmiyo mata, hannu ta saka tashare kafin ta ɗingiza ahankali tanufi gaban Fridge, domin ji take yi tamkar zata mutu idan ba tayi gaggawar shan ruwan ba, ga jikin ta dake mata ciwo ko ina, kamar an hau jikin ta an kwana sukuwa a kanta haka take ji
Buɗe Fridge ɗin tayi taciro goran ruwa, tunda ta kafa a baki bata dakata ba sai da tayi rabin ruwan, kana ta zube nan ƙasa da rawan jiki, nan da nan zazzaɓin ya sake rufe ta, ta kwanta tana kuka sai juye-juye take yi.
Allah ne yakawo mata Ester, ta shigo gyara mata ɗakin, ai kuwa nan hankalin ta yatashi ta nufe ta tana kiran sunan ta, sai dai gani tayi tamkar ba ta numfashi, nan da nan ta sake rikice wa tatashi da gudu ta fice.Wajen da aka ajiye Telephone a parlour, nan Ester ta ƙarisa tasaka number ta kira Suhaib
+
Lokacin yana Hospital ne, don haka koda ta sanar masa sai hankalin sa ya ɗugunzuma ya tashi, tare da Doctor suka taho don bazai iya jiran har yaje ya kawo ta asibiti ba, lokacin tuni ta galabaita kenan.
Suna zuwa kai tsaye ɗakin RAUDHA suka nufa
Ester na tare da ita, har ta shafa mata ruwa a fuska tunda a tunanin ta ta suma ne, sai dai bata sani ba tsaban ciwo ne yasaka ta dena numfashi, idanun ta a rufe sai hawayen dake gangarowa ta gefen idanun ta, gaba ɗaya jikin ta ya saki sai wani irin ciwon da baza ta iya misalta shi ba take ji.
Kanta Suhaib yayi yana kiran sunan ta, gaba ɗaya ya kiɗime ya rasa ma me zai yi
Daƙyar Doctor ɗin ya kwantar masa hankali, yace masa “ya ɗauke ta ya ɗaura saman gado sai ya duba ta”.
Kamar yanda yace masa ahakan yayi
Ita tuni Ester ta fice a ɗakin ma
Duba ta doctor ɗin ya soma yi, Suhaib na zaune gefen gadon ya gaza motsa wa, zufa duk ya jiƙa masa jiki sabida tashin hankali, duk da kuwa akwai A.c da fan a ɗakin
Sai da Doctor ɗin ya gama duk abinda zai iya yi, kafin ya kalli Suhaib yayi mishi bayani akan “zazzaɓi ne kaɗai ajikin ta”. Sannan yace masa “a bata abinci taci sai a nemo maganin da za’a bata”.
Rubuta magungunan yayi ya miƙa wa Suhaib
Amsa yayi yana kallon Doctorn kamar zai yi kuka yace, “Doctor yanzu babu abinda ka gano sai zazzaɓi? Ni fa hankali na ya tashi, anya babu wani abinda ya same ta? Ba ka ganin yanda take yi ne?”
Murmushi Doctor yayi yana dafa kafaɗan Suhaib ɗin yace, “kwantar da hankalin ka Man, Ni abinda na gani kenan, ba na tunanin akwai abinda ke damun ƙanwar ka, Just zazzaɓin ne yayi mata kamu sosai that’s why tashiga wani hali irin haka, but insha Allahu komi zai zama normal idan aka bata maganin nan, in kuma be sauka ba to sai a dangana ga asibitin”.
Gyaɗa kansa Suhaib yayi cike da gamsuwa, kana yamiƙe tare da yi wa Doctor ɗin godiya
Tare suka fita cikin ɗakin, ɗaya daga cikin ma”aikatan gidan ya aika ya siyo masa maganin a Chamis, sannan ya koma ciki, shi da kansa ya haɗo mata Lunch ɗin da Kuku ya gama akan faffaɗan tiray, ya nufi saman dashi
Yana shiga ɗakin yanufi wajen ta, sai da ya’ajiye tiray ɗin a saman drowan gadon kafin ya zauna, yasaka hannu yaɗago ta yana faɗin “Baby tashi kici abinci kisha magani”.
Langaɓe kanta tayi tana son komawa, nan da nan hawaye suka cika idanun ta, cikin dashashshiyar muryan ta da baya fita sosai tace, “Yaya Sanyi”.
Suhaib duk ya ruɗe ya rasa yanda zai yi da ita, don tuni ta soma masa kuka, aza ta yayi ajikin sa yasoma rarrashin ta cike da tausayin ta, sai da yaga ta nutsu ta dena kukan sannan yamiƙe yashiga Toilet ya ɗauko mata Brush, shi ya taimaka mata ta wanke bakin ta yaje yazubar da ruwan a Toilet, sannan yadawo yamaida ita jikin sa, a haka yayi ta bata abincin tana ci, sai da ta ture hannun sa kafin yabar ta, sannan ya bata drugs ɗin ta tasha, be barta ta kwanta ba duk da kuwa tana ta mishi ƙorafi da shagwaɓan da tasaba yi, sai da ya tabbatar abincin ya narke ajikin ta kafin ya kwantar da ita yana faɗin
“Baby ko in haɗa miki ruwa kiyi wanka ne, zaki fi jindaɗin jikin ki ko?”
Girgiza masa kai tayi tana lumshe idanuwan ta, ita kaɗai tasan abinda take ji ajikin ta, tunda take bata taɓa jin irin wannan ciwon dake yawo can cikin jinin jikin ta ba, takamaime ma bata san ina ne ke mata ciwon ba, ko ina na jikin ta zafi take ji da radaɗi, ga kanta dake uban sara mata kamar zai rabe gida biyu, wasu zafafan hawaye ne suka soma sintiri a face ɗin ta, don ba ta da ƙarfin da zata iya yin kuka ma
Suhaib bawan Allah ya rasa inda zai saka kansa sabida tsantsan tausayin ƙanwar na sa, ya kai ya kawo haka yayi ta yi, sai daga baya ne dabara yafaɗo masa, ya ɗau bargo har guda biyu ya lulluɓe ta ganin yanda take rawan sanyi, heatern ɗakin ya ƙure mata ta yanda ko ina zai ɗau ɗumi, sannan ya dawo kusa da ita ya zauna yana shafa mata gashin kai, hannun sa ɗaya na cikin nata biyu ya ƙanƙame su, ahaka yayi ta lallaɓa ta har sai da yaga tayi barci tukun yasamu nutsuwar zuciya, numfashi ya sauke me ƙarfi kafin ya yatashi yafito tare da jawo mata ƙofa
Ester ya kira yace, “takula da ita zai je yadawo” sannan yafice agidan.
Barcin awa biyu tayi ta farka
Ester na gefen ta, ita ta taimaka mata da taga tana ƙoƙarin tashi
Ƙafafuwan ta kaɗai ta zuro ƙasa tana riƙe da kanta, bata tashi ba sai da tayi kamar mintuna biyar kafin taɗago kanta tana kallon Ester dake gaban ta a tsaye, ahankali cikin dishewar murya tace, “zan yi wanka”.
Ester bata ji me tace ba, sai da tamatso sosai kusa da ita tasake tambayan ta, sake maimaita mata tayi sannan ne taji ta, hannu tasaka tariƙo ta; ta taimaka mata zuwa Toilet ɗin sannan tafito.
Mintuna 20 ta ɗauka aciki kafin tafito ɗaure da towel ajikin ta, gashin kanta da suka manne ajikin ta sai zirarar da ruwa suke yi, ahankali take takawa har zuwa gaban dressing mirror tazauna
Dasauri Ester taƙariso wajen ta tana faɗin “let me help you Ma’am”.
Handrayer ta ɗauka bayan ta soka socket ɗin, tasoma busar mata da gashin kanta, bayan ta gama tasoma shafa mata Lotion a kyakykyawar white skin ɗin ta
RAUDHA bata hana ta ba, har sanda tagama shafe mata hannu da ƙafafu kafin tatsaida ita, miƙe wa tayi tanufi gaban Sip ɗin kayan ta
Ester na biye da ita, ita tabuɗe mata Sip ɗin
Ita kuma RAUDHA tanuna mata kayan da zata ciro mata
Akan gado tazube mata kayan sannan tafice.
Matsa wa gaban gadon RAUDHA tayi ta ɗauki kayan tasoma saka wa, riga da wando ne na sanyi masu tsananin taushi da kauri, kalan ruwan ƙasa, da Zip agaban rigan, Sannan ƙafan wandon da na hannayen Robber ne da ya kamata sosai, hula tasaka na kayan me tuntu a tsakiyan, gashin ta gaba ɗaya ta tusa acikin hulan tarufe har kunnen ta, sai da tasaka Socks kafin takwanta tana rufe jikinta da bargo, ba barci take ji ba but ta rufe idanun ta tayi luf akan gadon, har yanzu da sauran zazzaɓi ajikin ta, ga kuma sanyi da take ji can cikin ƙashin ta wanda gaba ɗaya ya hana ta jin daɗin rayuwan ta.
Ester CE tashigo tayi mata maganar “ko akawo mata abinci ne?”
Sai ta girgiza mata kai alamun “a’a”
Hakan yasa tafice tajawo mata ƙofan.
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
Sai gab da magriba aka sallamo su Farida, sai dai likitocin sun haɗa su da magungunan da zasu riƙa ba ma jaririn, sannan zasu riƙa kawo shi ana duba sa sau biyu a sati, har aga abun da hali zai yi kafin yasoma girma.
Maryam da wata Dattijuwar mata me suna Inna Haule, ƙanwa CE wajen mahaifin Farida, tare suka dawo gidan, tunda ita INNA Haule ita ce zata zauna da Faridan har tayi arba’in, ita kuma Maryam zuwa bayan isha’i Mijinta zai zo ya ɗauke ta.
Har a time ɗin RAUDHA na nan a kwance, duk tana jin ɗan hayaniyan su daga ɗakin ta, amma bata tashi ba bare tafito
Suhaib ne yashigo ɗakin, idanun sa akan ƙanwar nasa yaƙarisa wajen gadon yana zama, a tunanin sa barci take yi, don haka sai yaɗaura hannun sa saman goshin ta don yaji jikin nata
Buɗe idanuwan ta tayi tana kallon sa, ahankali tafurta “Ya..ya”.
“Baby kin tashi?”
“Uhmm”. Tace dashi tana ƙoƙarin tashi zaune
Dasauri yasaka hannayen sa ya taimaka mata tatashi zaune, jingina tayi da jikin sa taɗaura kanta saman kafaɗan sa, hannayen ta saƙale a ƙugun sa tasake lumshe idanun ta
Yayinda shi kuma yake shafa mata gashin kanta, yana jin yanda zafin jikin ta ke shiga jikin sa, hakan yasa zuciyan sa sake jin tausayin ta fiye da ko yaushe
“Baby”.
“Umm..”
“Ko mu koma Hospital ɗin ne?”
Girgiza masa kai tayi tana ƙara lafewa ajikin sa
Numfashi kawai yaja yana ranƙwafo da fuskar sa, ya sumbaci gashin kanta kafin ya zame jikin sa yana faɗa mata yana zuwa
Fita yayi, babu jimawa yadawo tare da tiren abinci, shi da kansa yaciyar da ita, sannan ya faɗa mata “Farida ta dawo, ko zasu je taga Baby?”
Gyaɗa masa kai tayi alamun zata je
Shi da kansa ya ɗaga ta, hannun sa na riƙe da nata ta jingina da jikin sa suka fito.
Ɗakin Faridan suka shiga, Suhaib ne kaɗai yayi sallama
Maryam dake zaune riƙe da Babyn ta’amsa mishi idanun ta akan RAUDHA
Zama akan stool ɗin mirror yayi, yayinda RAUDHA ke manne dashi taƙi ta sake shi
Cikin fara’a Maryam tace, “Ƙanwata ya jikin naki?”
Ɗan kallon ta RAUDHA tayi tana son tabbatar wa da itan take yi, ganin tana kallon ta sai ta’amsa mata a hankali
“To Allah ya sawaƙe, Allah kuma ya kiyaye gaba”.
Wannan karon Suhaib ya amsa mata yana tambayan ta “ina INNA Haule?”
Maryam ta sanar masa ta fita zuwa kichen ɗaura ruwan wankan me gejo, kafin ta ƙara da faɗin “to Nima dai yanzu zan tafi tunda Baban Aliyu ya zo, gashi har yanzu Aunty Farida bata tashi ba, idan ta tashi Yaya sai ka sanar mata Ni na tafi”.
Zuwa tayi ta miƙa masa jaririn, kafin ta ɗau jakan ta suka sake sallama tafice
Kichen ta nufa tayi wa INNA Haule itama sallama, sannan ta tafi.