RAYUWAR ASMAU CHAPTER 15 KARSHE

 RAYUWAR ASMAU CHAPTER 15 KARSHE

Da dare da wuri ta mishi girki kafin ya dawo, ta shige d’aki tana gama sallolinta tayi shirin kwanciya, doguwar riga ta saka iyakar gwiwa pink, mai santsi dabin jiki, tayi kyau sosai, mukulli ta saka ta rufe d’akinta ta haye gado tayi addu’a ta kwanta.

Aslam kuwa tinda ya fita da yamma yaje gidan Momy. Tambayar da Asma’u tayi ya amsa da tana lafiya.

Daga nan Asibiti ya biya, sai da akai magariba ya taho gida.

Yana driving ne amma zuciyar sa na can tunanin halin da Asma’u take ciki.

Bai son damuwar ta bai son bacin ranta. Dole ya san yadda zai  dawo mata da farin cikin ta.

Sanda ya isa gidan kamar yanda ya zata, tayi barci ko motsinta bai jiyo ba, d’akinshi ya shiga ya watsa ruwa yayi shirin kwanciya sannan ya fito ya zauna yaci abincin data girka mishi, hankalinshi duk naa wurinta harya gama.

A hankali ya murd’a Kofar d’akinta, jinta yayi a rufe, kamar yadda ya zata. komawa dakinshi yayi ya dauko makullanshi yazo ya bude a hankali ya tura kofar ya shiga.

K’arasawa yayi inda take, kasa d’auke idonshi yayi a kanta, a fili yake furta,

“Alhmdlh, Allah nagode maka da ka mallaka min Asma’u. Ya Allah ka nunamin ranar da Asma’u  zata gane irin son da nake mata,” tsugunawa yayi saitin fuskarta yana tunanin yanzu da suna zaman lafiya ne zai kwanta da ita ne a kirjinshi yanajin lallausar fatar ta, shi kadai yasan yanayin da yakeji idan yana tare da Asma’u. Abinda ya dade yana fatan ya faru kenan.

Hannunshi yakai ya shafi fuskarta, ya d’aura hannunshi saman lebanta, bakin sa ya kai kan nata ya dan sumbace ta.

Mikewa yayi ya rufe kofar ya koma dakin sa.

Alwala ya kuma yi. Dan Kusan kwanan zaune yayi yana fad’ama Allah damuwarshi.

Washe da wuri ta gama masa duk abinda zai bukata sannan ta koma daki.

Sai da ta tabbata ya fita sannan ta fito ta gyara gidan

Daki ta koma tai wanka tai ado sosai a jikin ta da fuskar ta.

Bata san dalili ba yau dai ta tashi da farin ciki da son yin kwalliya.

Ta zauna ta karya. Kitchen ta shiga ta fara hada hadar abincin rana.

Fried rice tayi wacce ta wadata da hanta, tayi farfesun naman kaji, tayi cislow.

Cake ta kwaba tai baking sannan ta yi meat pie.

A daining ta jere su tayiwa wajen ado mai kyau.

Kitchen ta koma ta hada lemon kwakwa da madara ta saka dabinoi ta sa a firij.

Wanka ta kara tai Kwalliya sosai kamar amarya. ta saka wani papper less mai kyau da tsada wanda duk jikin sa stones ne da suka kara masa kyau sai daukar ido yake..

Red and black kala. Sosai tai kwalliya ta feshe jikin ta da turare mai kamshi sosai.

Dan kunne da sarka ta saka jajjaye, Babban falo ta koma ta zauna tana kallo.

Wajen karfe uku ta jiyo sallamar sa, amsawa tayi ba tare da ta dago ta kalle shi ba.

Shi kuwa tin da ya shigo ya zuba mata ido, dan yaga tai masa kyau.

Karasawa inda take ya zauna a gefen ta. Dagowa tayi ta zura masa manya manyan  idon ta masu dimauta shi, kallon sa ta tsaya yi, sosai yayi kyau.

Yana sanye cikin Sky blue din shadda yai kyau da shi.

STORY CONTINUES BELOW

Fatar sa ta dada yin fresh, ya dada haske kyaun sa ya kara fitowa jikin sa ya murje. Ya dawo cikaken balaraben sa

Iska ya hura mata, wannan yasa tai saurin dawo wa cikin hayyacin ta.

Kai ya daga mata alamar ‘Menene?’

Kai ta dauke daga kallon sa. Hannun ta ya kamo wanda tai masa ado da jan lalle.

Saitin bakin sa yayi da hannun ya sumbata. Zai yi magana kenan yaji ana knocking.

“Waye?”

Ya tambaya.

Mai gadi ne ya ce,

“Nine! Bakuwa kayi.”

“Cene ta shigo.”

Ya fada yana kallon Asma’u.

Mikewa yayi ya ce, bari na shiga na watsa ruwa.

Yana shiga tana shigowa ba kowa bace face Pretty.

Asma’u da bata san ta ba ta amsa mata sallamar da tayi tana mikewa.

Wajen zama ta nuna mata sannan itama ta zauna.

Gaisawa sukai, Pretty ta ce,

“Baki sanni ba. Ko Aslam yana nan?”

Kai Asma’u ta daga ta ce,

“Eh amman yanzu ya shiga wanka.”

Ta mike ta kawo mata lemo da snack. Lemon kadai ta dan sha ta zauna jiran sa.

Sai kallon Asma’u take a ranta ta ce,

“Ashe haka Asma’un take ahh lallai doke Aslam yaso ta. Duk da yarinya ce amman tana da sura mai kyau. Allah sarki na cutar dake.’

Duk wannan maganar a zuciya take yin ta.

Sai da tai minti ashirin Asma’u taga Aslam bai shigo ba ta mike ta shiga ciki.

Yana gaban mudubi Daure da towel a kugun sa, yana ta kalkale jikin sa, Asma’u ta shiga.

Ganin sa a haka yasa tai saurin juya baya.

Kallon ta yayi yai murmushi, magana ta fara yi cikin rawar murya,

“Kayi bakuwa ana jiran ka.”

Ta fada, tafiya ta fara yai saurin kamo hannun ta ya juyo da ita.

Kin juyowa tayi, shi ya juyo da ita da hannun sa.

Ido tai saurin runtsewa. Murmushi yayyi ya jata kan gado.

Zaunar da ita yayi ya saka kayansa. Sai da ya gama ya ce,

“To matsoraciyya na gama bude idon.”

A hankali ta fara bude idon ganin ya saka kayan yasa ta bude su.

Mikewa tayi ta ce,

“Yaya tana jiran ka fa.”

“Na sani.”

Hanya tayi zata fita ya ce,

“Zo ki gyara ni man.”

Ya fada yana mika mata turare.

Amsa tayi ta fefesa masa. Ta ajiye. tafiya ta fara ya ce,

“Oh!”

Juyowa tayi, ya ce,

“Comb my hair man!”

Amsar comb din tayi ta taje masa kai. Tana direwa tayi waje.

Bayan ta yabi, suka fita. Hannun ta ya kama, suka jera har zuwa falo.

Da yake Pretty ta juya ma hanyar da suke fitowa baya bai gane ita bace

Zagayawa yayi ya zauna ba tare da ya kalli bakuwar ta shi ba.

Asma’u kuma tayi hanyar sashen sa. Saboda taga yai bakuwa.

Dagowa yayi ya ce,

“Sann…..”

Bai karasa fadin abinda zai fada ba yai saurin mikewa.

“Me kika zo min a gida?”

Ya fada cikin tsawa. Wanda ya janyo hankalin Asma’u.

Juyowa tayi ta tsaya kallon sa. Lokaci daya ya canja.

STORY CONTINUES BELOW

Fuskar sa tai jajir,  da Hannu ya nuna mata kofa alamar tazo ta fice.

Zubewa tayi a kasa tana rokar sa ya tsaya ya saurare ta amman ya kafe akan sai ta fita.

Asma’u ce ta koma dakin ta kama hannun sa ta ce,

“Haba Yaa Aslam ka tsaya man.”

Hannun sa ya kwace ya ce,

“Bazan tsaya naji ba. ta fice min da gani.”

Kallon sa Asma’u tayi taga ransa a bace yake sosai.

Hannun Pretty ta kama zaunar da ita.

Wajen Aslam ta karasa shima ta zaunar da shi.

Kansa ta shafa masa har ya samu ya sauke ajiyar zuciya.

Kallon sa tayi, ta ce,

“Kiyi hakuri duk da bansan me ya faru a tsakanin ku ba amman ka saurare ta”

Ta fada tana mikewa. Hannun ta ya kamo, ya zaunar.

Kallon sa tayi ya gyada mata kai alamar ta zauna.

Zaman tayi, ya ce,

“Na baki minti biyu ki fadi abinda ya kawo ki, ki bar min gida na.”

“Hakuri na zo na baka!”

Ta fada cikim sanyin murya.

“Indai hakuri ne ki tashi ki tafi bana bukata kara ganin kki a rayuwa ta. Rayuwar da nai dake a baya ma ban san nayi ba.”

“Nasan da haka Aslam amman ka yafe min, nazo na bawa Asma’u hakuri ne.”

Kallon ta Asma’u tayi cikin rashin sani ta ce

“Ni kuma? Ni da ban sanki ba.”

“Eh baki san ni ba, amman ni nasan dan har na cutar dake.”

Kwalar idon ta ta goge ta ce

“Dan Allah ki yafe min.”

Kallon Aslam, Asma’u tayi.

Shima kallon ta yayi ya kama hannun ta. Kallon Pretty yayi fuskar sa a hade ya ce,

“Malama kiyi mana bayani da zamu gane, da me kika cutar min da kanwata kuma matata.”

“Aslam tinda na fara son ka kake fada min kana da mata Asma’u ni kuma a duniya na tsani Asma’un nan ganin irin son da kake mata. Duk inda naje ayiwa Asma’u abu sai ace bazai kamata ba dan ba a zaune take ba. Ina shiga damuwa na  son ka ga shi kai baka san ma ina yi ba. Wannan yasa naje har nijar na samu bokan da yai min aiki har ka auren ka bar Asma’u.”

Hannun sa Asma’u ta saki, tana mai zaro ido.

Hannun ta ya kara kamawa, Pretty ta ce,

“Na maka asiri ka manta da ita da komai nata, sai da naje kano kwanakin baya ake fadan irin halin da Asma’u ta shiga a sanadin rashi ka. Nayi dana sani nayi nadamar raba ku. Dan Allah ku yafe min. Dan naga darasi ga masu bin bokayr yanzu wai ni ke dauke da cutar HIV”

Ta fada tana kuka. Asma’u ma kukan take dan ita da wane ido ma zata kalli Yaa Aslam.

Aslam ne ya jata jikin sa yana lallashin ta.

Amman kuka take kamar me. Ganin ya kasa lallashin ta ya sanya ya kalli pretty ya ce,

“To kinji dadi kinzo kin ta dan hankalin mata. Tashi ki bamu waje.”

“Kayi hakuri banyi haka da zumar bata mata ba. Nayi ne dan na wanke ka. Dan nasan ko yaya ne zata rike ka da abinda kai mata.”

“Bana son jin komai tashi ki fita.” Ya fada yana nuna mata kofa.

Hannun sa Asma’u ta saukar ta girgiza masa kai.

Kallon Pretty tayi ta ce,

“Ba komai na yafe miki haka Allah ya kaddara wa rayuwar mu sai dai kece sila amman Allah ya riga ya tsara. Na yafe miki. Ki nemi yafiyar ubangiji ki.”

Sosai Pretty tai mamaki haka ma Aslam duk da yasan halin Asma’u ita komai a gun ta mai sauki ne inda zaka nemi yafiyar ta in ka bata mata.

Jikinsa ya jata yana rumgume ta sam, Da kyar Pretty, ta ce,

“Nagode Asma’u nagode.”

Aslam ta kalla, ta ce,

“Kai ma ka yafe min.”

Kai kadai ya gyada mata. Mikewa tayi jiki a sanyaye, ta fita.

Aslam kuwa tinda ta fita ya kara matse Asma’un sa a jikin sa yyana jin wani tausayin ta.

Daman yasan dole rashin sa ya sa ta a wani hali. Shima ya shiga halin mawuyaci Allah ne dai yayi da sauran sa.

“Baby nah!”

Ya kira sunan ta

Kasa amsawa tayi sai, ‘Uhmm’ da ta fada.

Dankwalin kan ta ya zame, yana shafa gashin kanta.

Magana ya fara a hankali ya ce,

“Baby na yanzu kin yadda ban rabu dake dan son rai na ba. Dan Allah kiyafe min. Wallahi ni mai son ki ne, ina kaunar ki Husnah”

Magana Asma’u ta fara a hankali, ta ce,

“ka yafemin don Allah ka yafe mu, muyi rayuwarmu cikin farin ciki, wayyo naa shiga uku na cutar da masoyinah, a rashin sani, duk bacin ran bari na da kayi ne, ka koyamin rayuwa dakai, lokaci daya ka guje ni, a lokacin nayi zaton mutuwa zanyi idan har baka tare dani, nasha wahala Yaa Aslam don Allah ka yafe mun ka gafararka mijina.”

Sambatu kawai take ita kadai, tana kuka, kwantar da kanta ya karayi saman kirjin sa, tana shessheƙar kuka, ji tayi yaa kara matseta a kirjinshi, yaa daura hannu saman kanta.

“Baki min komai ba Asma’u duk a rashin sani ne. Na yafe miki Asma’u bazan taba kin yafe miki ba. Ke da abinda kika min da wanda zaki min a gaba duk na yafe miki Asma’u. Ina kaunar ki Asma’u nasan bazan taba iya hada son ki da wata ba. Nai miki alkawarin daga ke ba kari ni naki ne ke kadai. Kamar yadda kike tawa ni kadai. Ina kaunar ki Husnah”

Kuka kawai Asma’u take. Dago da fuskar ta yayi yana lashe hawayen fuskar da harshen sa.

Sai da ya tabbatar da ta daina kukan sannan ya dago ta sukai daining a cinyar sa ya daura ta ya dinga bata abinci a baki.

Sai da ta koshi sannan, ya fara ci yana ci yana santi.

Suna gamawa suka koma falo.  Rungume juna suka karayi, cikin wani irin yanayi na so da kaunar juna.

**** ****

**************

Da dare nan Asma’u aka kalkale jiki aka sha gyara akai wanka cikin ruwan turare masu dadi da rikita duk wanda ya shaka.

Dan ko da Aslam ya ganta kasa gigicewa yayi. saida sukayi sallah raka’a biyu na godiya ga ubangiji, sun dade Aslam na kwararo musu Addu’o’i, na zaman lafiya da zuri’a dayyiba, sannan suka shafa ya tashi ya barta har lokacin tana addu’ah.

Sai data gama ne yace

“wannan irin dadewa haka? Me aka rokar mana ne?”

Murmushi tayi ta ce,

“Ina roka Allah, ya kare mu da sharin mai sharri ya raba mu da duk wani rashin fahimta dazai shiga tsakaninmu, kaine mutum na farko, kuma kai kadai na fara so a zuciyata, ina fatan zamowa matarka har a aljanna. Sannan uwar ya’ya.”

Yace

“Ameen Allah yasa, farin cikinah, idan har Aljanna a tafin kafata take, na rigada na daga miki, ina Sonki sosai Husnah na!”

Hannunta yaja yahadata da jikinsa yafara kissing din bakinta, wuyanta da goshinta nan yafara rudata da soyayyarsa tareda janta zuwa gado acikin dabara ya rabata da kayan jikinta nan yafara shakar kamshin dake fita ajikinta, wasannin daya saba yi mata yafara amma na yau yasha bamban dana kullum nan Asma’u tafara fita hayyacinta saboda wahalar yadda yake murza nafulanin ta.

Duk kukan da Asma’u take yi bai sashi kyaleta ba dan idon sa ya rufe, sosai yake kokarim shigar ta.

Asma’u ta jigata sosai ga azabar datake ji ajikinta, dakyar Aslam yadan kyaleta ta huta in banda hawaye babu abinda take yi, tana dan hutawa Aslam  yafara shafarta tareda kokarin maimaita abinda yayi domin ba karamin rudashi Asma’u tayi ba.

Nan kuma tafara kokarin hanashi amma takasa dan jikin ta yayi sanyi, sai da yajishi zamzam sannan ya iya hakura amma dakyar ya iya barinta, dakyar tayi masa magana da dasasshiyar muryarta, bani ruwa nasha cikin sauri Aslam yadauko mata babbar robar ruwa yabata tana karba tafara sha bata ajiyeba sai data shanye ruwan ciki tas.

Ajiyar zuciya ta sauke. Ta lumshe ido, bacci wahala ya dauke ta. 

Zuba mata ido Aslam yayi yana kallonta hakika Asma’u ita ce sashe na rayuwarsa,

‘Allah sarki yau namiki rashin tausayi Asma’u,’

Ya fada acikin zuciyarsa, magana yacigaba da yi, a ransa,

“Lallak Asma’u ta daban ce, komai nata daban ne, haka ma ni’imar ta da ban ce, dan yasam ba kowa ke da irin ta matarsa. Yadda yaji ta ya kara dada masa ganin darajar ta da kimar ta. Ta wuce duk inda yake tunani.

Amman yasan yai mata ba dai dai ba, tana budurwa yayi sau biyu a lokaci daya. Duk da shi likita ne,

To ya zaiyi ya kasa controlling kan sa ne, kallon ta yayi ya ce,

“Allah sarki Husnah ki yi hakuri.”

Juyi tayi, tana mai kara saukar da wata ajiyar zuciyar dan ta sha kuka.

Tashi yayi yashiga toilet yayi wanka yai alwala. yafito yasa kayan baccin sa.

Sallah yai tayi ta godiya da Allah ya jima yana sallah kafin ya hau kan gadon yaja ta jikin sa.

Wani bacci mai dadi wanda ya dade yana mafarkin irin sa ya dauke ta.

Sai da Asuba sannan ya  tashi yayi sallah amma bai tashi Asma’u  ba. yazauna zaman jiran Asma’u ta farka, gefenta ya kalla duk wurin yagama baci kai

‘Asma’u  yau kinsha wuya’

STORY CONTINUES BELOW

yafada yana shafa gashin dake kwance a hannunta ahankali tabude idanuwanta wadanda sukayi ja kamar jini.

Jin jikinta a mace kanta tadauke bata kalli Aslam ba tai Yunkurin saukowa daga kan gadon tayi  amma ta kasa.

Aslam yai sauri ya karasa gun ta yana fadin

“Sannu kin tashi.”

Hararar sa tayi tafara saukowa ahankali amman sai ta kwala wata irin kara.

Toilet ya kai ta ya hada mata ruwa dai dai wanda zata iya shiga.

Yana saka ta, ta kwala kara ta kamkame shi tana zubar da hawaye.

Duk yadda taso ya cire ta a ruwan ki yayi, sai da ya ji ya huce sannan ya kara hada mata wani ruwan. Nan ma kuka tayi masa. Sai da yai mata ruwa uku duk tana kuka sannan ya barta.

Ko a haka ya tabbata yayi aika aika kenan.

Wankan tsarki ya taimaka mata tayi yai mata wanka sannan ya fito da ita ya shirya ta.

Doguwar riga da hijab ya saka mata. A zaune tayi sallah.

Kan gado ya dauke ta ya mayar. Baccine ya daukesu wanda yake cikeda nishadi da annashuwa sai wurin 11 sannan Asma’u farka.

Aslam baya dakin kasa sauka tayi daga kan gadon.

Idon ta ta runtse, sai ga hawaye. Dakin aka bude, daga kai tayi tana kallon sa.

Da sauri ya karasa wajen ta yana ce mata sannu.

Daukar ta yayi ya kai ta bandaki.

Ruwan wanka ya hada mata. Shi yai mata wanka ya fito ya nado ta cikin towel.

Kwantar da ita yayi, ya  zare towel din jikin ta, da sauri ta kamkame jikin ta tana masa kuka.

Jawo ta jikin sa yayi ya ce,

“Husnah ba abinda zan miki, duba ki nake son yi.”

Kuka ta saka masa. Ba yadda zai yi haka ya kira Dr Yasmeen dan tazo ta duba ta.

Kwalliya yai mata ya saka mata kaya falo ya dauke ta  ya kai ta.

Kirchen ya shiga ya dauko basket. A kasa ya jere musu kayan abincin.

Janyo ta jikin ta yayi ya hada mata tea.

Doya da kwai ce, sai farfesun kayan ciki da kunun gyada.

Kallon sa tayi ta ce,

“A ina ka samo abinci?”

“Momy na fadawa baki da lafiya ta aiko mana dashi”

Da sauri ta dago ta marairaice fuska ta ce,

“Kece me yake damuna?”

Murmushi yayi ya ce,

“Abinda ya faru man.!”

“Wayoo Allah na, na shiga uku, Kai Yaa Aslam yanzu haka kacewa Momy”

sai ta sa kuka.

Lallashin ta ya fara yi, ya dauko ta ya zaunar akan kujera.

Wayar sa ce tayi kara, dauka yayi, ya ce,

“Ki shigo sai ki shigo kofar dake hannun dama.”

Yana rufe baki sai ga sallamar ta nan. Amsawa yayi.

Asma’u dake jikin sa idon ta arufe ta bude idon ta.

Murmushi ta sakarwwa Dr Yasmeen.

Zama Dr Yasmeen tayi, suka gaisa da Aslam.

Asma’u ta kalla suka gaisa. Aslam ta kalla ta ce,

“Me yake damun ta ne?”

“Duba ta nake so kiyi, taki bari na na duba ta.”

Ya fada yana mikewa.

Fita yayi ya barsu a dakin. Bedroom suka sshiga.

Duba tayi ta girgiza kai. A ranta tan cewa,

“Dr Aslam sai kace ba likita ba.”

Kallon Asma’u tayi ta ce,

“ina zuwa?”

Ta fita. Aslam na ganinta ya mike ya ce,

“Lafiya?”

“Eh taji ciwo ne zan dauko abu a gida.”

“A’ah ga first aid box nan.”

STORY CONTINUES BELOW

“No traditional ones za ai amfani dashi.”

“Ok”

Kawai ya ce ta fice.

Daki ya shiga ya tadda Asma’u kwance. Sannu yai mata. Murmushi tayi masa.

Tausaya ya dinga mata. Dr Yasmeen bata dade ba ta dawo.

Sai da ta sanar masa sannan ta dawo dakin.

Bandaki ta shiga ta hada mata ruwa sannan ta taimaka mata ya shiga cikin ruwan.

Sai da ta gasa ta sosai sannan ta hada mata wani ruwan maganin.

Sai da ta kara gasa ajikin ta sannan ta dawo daki tana wata irin tafiya.

Zama tayi akan gado, sai da tai mata dinki. Abin tausayi Asma’u dai hawaye take. sallama Dr Yasmeen tai masa, tana fada masa magani da allurar da zai mata.

Dakin sa ya shiga, ya dauko First aid box magungunan da zaiyi amfani dasu ya diba ya tafi dakin ta,

Dakin ta ya shiga, tana ganinsa ta sunkuyar da kanta,

“Sannu Baby na ga magani nakawo miki kinji,”

Fuska ta bata ya ce

“please kiyi hakuru ki sha kinji.”

karba tayi na dan taso ba tadauki ruwa tasha maganin, ya ce,

“To sauranki allura.”

Ai kuwa nan tace bata san zance ba, maganin ma dan tana jin jiki ne.

Kuka ta saka masa, rumgume ta yayi cikin dabara ya zame zanin jikin ta ya tsira mata.

kuka ta saka masa bakin ta yai saurin rufe wa da nashi wata iri sumba yai mata.

Sai da ya tabbatar tai shiru sannan ya kyale ta.

Ranar dai yinin jinya yayi, komai shi yake mata.

Abinci kuwa daga na safe har rana da dare Momy ce ta kawo musu.

Washe gari da rana suna zaune a falo Asma’u kwance tai dai dai da ita kan Aslam, suka jiyo knocking.

Mikewa yayi ya buda kofar Momy ya gani. Nan da nan ya bata hanya, yana amsa jakar ta.

Asma’u na jin muryar ta ta mike, a hankali ta karasa wajen ta ta rumgume ta.

Zama sukai, Aslam ne ya kawo mata lemo da snack duk dan kar Momy ta gane tafiyar Asma’u.

Momy bata dade ba ta tashi ta ce tafiya zatai. Hijab har kasa Asma’u ta saka ta rakata bakin mota.

Amman duk da haka sai da Momy ta gane tafiyar ta ba dai dai ba.

“Ciwo kika ji a kafa ne?”

Momy ta tambaya.

“Eh dan bigewa nai dazu.”

“Ayyah sannu kina kula, zan aiko miki da musu aiki ma.”

“Kai Momy nagode amman ni zan iya ai ba wani aiki.”

“Kin tabbata?”

Kai ta gyada ta ce,

“To duk da haka dai zan kawo miki ko daya ce ta taimak miki da wani abun.”

“To Momy.”

“Sai ku ajiye ta a boys quaters ko?”

Kai ta daga. Sallama sukai ta tafi tana mai musu addu’ar zaman lafiya.

Duk yadda Aslam yake jin bukatar ta hakura yayi dan yasan yai mata aikin rannan sosai

Sai da ta watsa ke sanna ya fara nuna mata bukatar sa.

Sosai Asma’u ta tsorata amman kuma ba yadda zatai hakkin sa ne.

Tin yamma yake rawar jiki da lallabata.

Da dare bayan sun ci abinci, da kansa ya dauke ta sukai bangaren sa.

Tare sukai wanka duk da Idon Asma’u a rufe yake dan ita wata irin kunyar Yaa Aslam take.

Tana mamaki in yana mata wani abu. Takan ce daman haka Yaa Aslam yake.

Ya iya soyayya mai tsawa a zuciyar wanda akai wa.

A wannan ba karamin wahala Asma’u taji ba, dan ji tayi kamar daren su na farko.

Duk jikin ta ciwo, washe gari da asuba tare sukai wanka ya tafi massalaci tai sallah a gida.

Bacci suka koma sai sha daya ta tashi ta janye jikinta ahankali tayi kissing din kumatunsa tatashi ta shiga.

A hankali take tafiya tana dingusa toilet ta shiga tayi wanka tafito ta shirya ta tsara kwalliyarta cikin wata yar doguwar riga mai hannun shimi ja bata da nauyi ta bi shape din jikinta. Ta feshe jikin ta da turaruka masu kamshi.

Kitchen ta tafi ta hada musu break, ta jere su, tadawo dakin inda Aslam yake lokacin ya bude idonsa, hannu ya mika mata cikeda kunya ta karaso tashiga jikinsa. Dan in ta tina yadda suka kasance a jiya wata kunya take ji ita kadai.

Kiss yafara bata tako ina yana shakar kamshin jikinta wanda yayi mutukar rudashi, gashin kanta yafara shafawa, ahankali tace

“kaje kayi wanka kaji,”

“uhm uhm nidai kece zaki yimin.”

yafada cikeda shagwaba dariya Asma’u tayi tasake kamkame shi.

Sai da ya gama jagwalgwala ta sannan suka shiga wanka suka cudi junansu sannan suka fito suka shirya, sabuwar kwalliya Asma’u  tayi cikin material kore mai kyau wanda yayi mata kyau tayi kwalliya sosai tasha turare shi kuma Aslam kananan kaya yasa thee quarter da bakar riga, hannunta yakama suka fito falo.

Dining suka nufa, ya zaunar da ita asaman cinyarshi, abinci ya zuba musu soyayyiyar doya da kwai da farfesun kaji da kunun shinkafa ga wainar da kayan tea, abaki yafara bata har ta koshi. Sannan ta fara bashi a baki wani lokacin idan ta bashi sai yaki sakin hannun nata ko ya dan cijeta da haka tagama bashi.

Daukarta yayi yakaita cikin falo ya ajiye ta akan carpet ya kwantar da ita ajikinsa hannunsa yasa acikin rigarta yafara laluben na shanunta ganin rigar jikinta zata rage masa jin dadi yasashi janye zip din rigar hannunsa Asma’u ta rike, ta ce,

“Yaa Aslam kabari mana dan Allah “

Dariya yayi ya cire rigar ya dora bakinsa akan dukiyar fulaninta yafara wasa dasu da harshensa haka ta kyaleshi har yagama sha’aninsa sannan ya rabuda ita, wunin ranar nan Aslam bai iya koda leka kofar gida ba. Jin sa yake kamar yau ne ranar amarcin su.washe gari tunda wuri ta tashi tafara gyara gidanta, da falo tafara ta gyarashi fes sannan ta gyara part din ta da nashi.

Ta shiga kitchen ta gyara, dama daga ita sai yar karamar rigarta mai kamada shimi milk colour shara shara da dan karamin gajeren wandonta iya cinya.

Dankali ta dauki ta fara ferayewa, caraf taji hannun mutum akan kirjinta tana jiyowa atsorace taga Aslam ne,  tsaye yana yi mata dariya daga shi sai gajeren wando fari da farar best ta maza, ajiyar zuciya ta sauke,  duka takai masa ya goce, ta ce,

“shine zakazo ka tsorata ni ina aikina?”

“Am sorry my Baby love, nima aikin nazo na tayaki to kuma sai naga bamu gaisaba.”

Murmushi ta dan yi, ta durkusa ta ce,

“Ina kwana?”

Kallon ta yayyi ya ce,

“Ba irin wannan ba.”

Ya fada yana jan ta jikin sa.

juyawa tayi taci gaba da aikinta.

“Ni dai ka bari na gama aiki na tukkuna.”

Hannun sa ya daura akan dukiyar fulanin ta, juyowa tayi ta ce,

“Haba Honey love,”

“Ni ki barni na gaisa da su.”

Hararar sa tayi ta juyawa, ta ce,

“Kai dai Allah yashirye ka dai sam bakajin kunyata,”

Murmushi Aslam yayi ya ce,

“Ina jin kunyarki mana.”

“A hakan?”

Ta fada tana yin aikin ta.

Kara jinsa tayi a jikin ta. Ta ce,

“To yau baka jin yunea ne?”

Murmuahi yayi ya kashe mata ido ya ce,

“Indai zan same ki ai ba wata yunwa da zanji.”

Juyawa tayi ta tana murmushi.

Shiru tayi ta kyaleshi saboda tasan idan ta biye masa bazai barta tayi aikin ba.

Fita Aslam yayi zuwa harabar gidan har an share an bawa shuka ruwa.

Ciki ya koma ya nufi  kitchen din ya sameta lokacin tana soya kwai har takusa kammala hada breakfast din duk gidan ya gauraye da kamshi abayanta Aslam ya tsaya ji yake kamar ya rungumeta amma kuma tana aiki, ci gaba da tayata aikin yayi har tagama bayan tagama ta debo kayan ta jera akan dining taja hannunsa ta ce,

“zo muje muyi wanka.”

Jan hannun Aslam, tayi zuwa dakinta inda ta shiga toilet ta hada musu ruwan wanka suka shiga sukayi cikin so da kaunar juna. suna fitowa ta shiryashi cikin Ash din trouser da bakar t-shirt ta fesa masa turaren ita kuma ta shirya cikin wani leshi pink and ash colour ta gyara fuskarta tasha kwalliya tasa jan janbaki tayi jagira tafesa jikinta da turare takafa daurin dan kwali sannan taja.

Aslam da ya zuba mata ido ya kasa ko da motsi dan kyaun da tai masa. Juyowa tayi ta sakar masa murmushi.

Hannun sa ta kama jikin sa ya ja ta ya rumgumo. fuskar su ya hada da ta shi, light kiss ya manna mata a wuyan ta.

Murmushi ta saki ta ce,

“Allah love na biye maka baza ka bar mu muci abinci ba.”

Murmushi yayi ya kama hannun ta suka nufi falo. suka hau kan dining table ta zuzzuba musu abincin tahaye kan cinyarsa tafara cin abincin tana fadin muci, Kai ya makale, ya ce,

“A’ah ni ki bani.”

Murmushi tayi ta fara bashi a baki suna ci yana zuba mata shagwaba.

Suna gamawa ta ce,

“Yaa Aslam yanzu ka dada ci, karage cin abinci kaga nauyinka yayi yawa gashi sai kiba kakeyi,”

STORY CONTINUES BELOW

Murmushi yayi ya ce,

“waya fada miki abincine yake sani kiba?”

Kallon sa tai da mamaki ta ce,

“To meye yake saka?”

Daukarta yayi cak ya nufi dakinsa da ita yana fadin muje na nuna miki abinda ke sani kibar, akan gadonsa ya direta ya shige jikinta Yana ya mutsa ta.

Ya ce,

“kece kike sani yin kiba sugar love,”

Murmushi tayi ta ce,

“Oh ashe ni kake tsotsewa kai kana kiba ni ina ramewa ko,”

dariya yayi ya kama bakinta ya tsotsa. Ya ce,

“Kina son kiba ne?”

Kai ta gyada ta ce,

“Wai na dan dada kaganni fa.”

Murmushi yayi ya ce,

“Menene baki da shi Hussy, komai na jikin dai dai da shekarun su, basu yi kadan ba. Bama nan.”

Ya fada yana shafa kirjin ta.

“Da nan.”

Ya shafo kugun ta. Wani yar taji. Murmushi yayi ya ce,

“Kuma kinsan me?”

Kai ta girgiza, Ya ce,

“Sweet din ki ma daban yake, kullun kara dadi kike,”

Ido ta rufeda tafin hannun ta. dariya yayi ya janye hannun ya ce,

“kinsan wani abinda yake bani mamakin?”

Kai ta girgiza, ya ce,

“A duk lokacin da na kusance ki jin ki nake, kamar a lokacin na fara sanin ki diya mace, kina daya daga cikin matan da suke daban wanda da an gama kusantar ku, wajen ke rufewa ya koma yadda yake,”

Fuska ta rufe tana murmushi. Hannun ta ya janye, ya ce,  “Husnah ke yar baiwa ce, samun kamar ki sai an tona, da na rasa ki da bansan yadda zanyi ba. Ke farin cikin raina. Ina son ki, ina kaunar ki, ki yafen duk abinda nai miki.”

Ya fada yana shafar dukiyar fulaninta rungume shi tayi tafara kissing dinsa, tasa harshe tafara lasar kowanne sashe na jikinsa shidai Aslam duk tagama ruda shi, kunya ta ajiye agefe tashiga nuna masa soyayya. yafara kokarin cire rigarta, nan ya shiga romancing dinta.

Sai da suka shayar da junan su da soyayyar su sannan sukai wanka.

Wasu kayan Asma’u ta dauko masa shadda fara kar da farin takalmi da hula tabashi. Da yake ya ce, zai je gun Momy.

Da kanta ta shirya shi,  ta fesa turare yayi kissing din bakinta yafita, har bakin gate ta rakashi sannan ta koma gida.

kitchen ta shiga ta dora girki ta shirya jallop rice with salad tayi farfesun danyen kifi ta zuzzuba acikin flasks tajera akan dining.

Ta shiga wanka tafito tayi sallah ta shirya cikin wata riga da skirt na english wears, rigar kalarta pink mai hannun shimi da babban botir guda daya agaban rigar daga kirji sannan ta matse ta sosai ta bayyana surar jikinta skirt din kuma iya gwiwa ne, black kala. ya kama mata hips dinta sun fito.

Ribon ta sakawa kanta kawai, ta zubo da gashin gadon bayan ta. tafesa turarruka da humra kala kala tayi kwalliya a fuskarta sannan ta fito falo.

Zama tayi ta kunna TV. Can ta mike ta shiga daki. tana fitowa Aslam yana shigowa dagudu taje tafada jikinsa ta rungume shi tafara kissing din bakinsa, fuskarsa, goshinsa da kumatunsa, hannunsa takama zo muje karage kayan nan kazo kaci abinci, kayan jikinsa ta cire masa ta dauko masa, three quater da ramar riga.

Shi dai kalon ta kawai yake, sosai tai masa kyau ta kuma ruda shi.

Abinci ta zuba musu yana fara ci, yafara yi mata santi yana bata labarin mai Momy.

Sun gamawa ya  yadauketa zuwa dakinsa agadonsa ya direta yakai hannu yacire botir din dake gaban rigar tata nan yafara wasa da albarkatun kirjinta. Sai da komai ya lafa sanan Aslam yashiga wanka yafito lokacin bacci ya dauke Asma’u.

STORY CONTINUES BELOW

Zama yayi yana kallon ta yana sa mata albarka.

Kiran Sallar La’asar da aka kira shi ya sa ya fara shafa kan Asma’u.

Ido ta bude, ta kalle shi. Murmushi ya sakar mata ya ce,

“Baby na ta shi ki wanka an kira sallah.”

Mikewa tayi a hankali ta shiga bayi. Kaya ya saka ya fita massalaci.

Haka zaman Aslam da Asma’u ya kasance cikin nunawa juna soyayya da kauna da tattalin juna har watanni suka shude kwanaki suka tafi, yau watan su biyar da aure.

Tana kiran Mami haka Yaa Buhariin ya shigo Abuja yana zuwa ya ganta.

Asibitin ta yana hannun Ya Buhari da Sir Sabir. Suna kula mata dashi.

yau tunda wuri Asma’u ta tashi bayan tagama koduwa a hannun Yaa Aslam.

Kitchen ta shiga tafara kiciniyar hada musu breakfast yayinda shi kuma Aslam yana can yana gyara musu bedrooms dinsu sai da yagama sannan ya fito.

Asma’u tunda tafara fasa kwai taji zuciyarta tafara tashi haka tadaure tafasa tahada ta kada tafara soyawa. Ta soya daya biyu ana uku nan taji zuciyarta tana tashi cikinta yahau juyawa dasauri tadauke kaskon ta nufi dakinta da gudu ta shiga toilet tafara sheka amai kamar zata amayar da kayan cikinta.

lokacin da Aslam yashiga ya tarar bata gama ba. Karasawa yayi ya soya. Yana gamawa  yabita dakinta a toilet yajiyota tanata aikin sheka amai dasauri yabita cikin toilet din ya riketa har ta gama aman ta kuskure bakinta, a kafadarsa ya daukota ya kaita kan gado ya kwantar da ita, bargo taja ta lulluba saboda sanyi taji tana ji kamar me.

Sosai Aslam ya fara yi mata sannu dasauri ya fita yaje ya dauko first aid box dinsa yazo inda take ya zuko allura asirinji ya yaye bargon data rufa tana ganin allurar tafara kuka nan ta hau magiya.

Dariya Aslam yafara ya ce,

“kinjiki matsoraciya to ranar da zaki haihu yaya zamuyi?”

Hawaye tafara taki yarda lallashin duniyar nan yayi taki yarda matseta yayi ajikinsa wata kara ta callara da sauri ya hada bakinsa da nata ya kankameta yajanye rigar jikinta ya soka mata allurar nan tafara fusge fusge amma bai barta ba sai da yayi mata allurar, kwanciya tayi tafara nishi daga nan kuma bacci yayi awon gaba da ita.

rigarta Aslam yadaga yafara shafa cikinta da rabon dai Asma’u zaki haifa min yara ya fada yana kissing din cibiyarta. Goilet ya shiga ya gyara sannan ya dawo ya zuba mata ido.

Ta jima tana bacci kafin ta tashi tana tashi Aslam ya matso

“me zakici maman baby?”

Fuska ta yamutsa ta ce,

“Maman me?”

“Maman Baby na ce.”

Murmushi tayi ta ce,

“Ni din?”

Kai ya daga yai murmushi ya ce,

“Baby love insha Allahu kin kusa ajiye min Baby. Zan yi farin ciki in har Allah ya azurtani da d’a daga gareki.”

Kallon sa take da mamaki ta ce,

“Sweet love kenan.”

Ta fada tana mikewa. Toilet ta shiga. Wanka tayi ta fito.

Zama tayi tana shafa mai. Gefen ta ya koma ya zauna. Ya ce,

“Sannu Baby love.”

Murmushi tayi ta ce,

“Ni fa bana jin komai. Zuciya naji tana tashi kawai.”

Ta mike ta dauki wani dogon wando tied ta saka, sai yar karamar riga da ta saka. Ta bade jikin ta da kamshi.

“Muje kaci abinci.”

Ta fada tana kama hannun sa.

Fita sukai. A falo ta zauna ta hada tea, shima ta hada masa.

Dankali ta zuba musu da kwai, ta zuba musu farfesun kifi.

Hannu ya sa ya fara ci, tea ta sha kawaai kallon ta yayi ya ce,

“Zo nan.”

Mikewa tayi ta hau kan cinyar sa, dankalin ya dauko ya bata abaki.

Amsa tayi ta ci, kwai ya gutsuro ya bata.

Tana sawa a baki, taji cikin ta ya hautsi na.

Mikewa tayi ya janyo ta jikin sa, kafin tai magana ta fara kelaya amai.

Sai da ta wanke shi tas sannan ya lafa mata.

Daukar ta yayi ya nufi daki bandaki ya shiga da ita yai mata wanka. Shima yayi sannan ya fito Ya canja mata kaya.

Rawar sanyi ta fara kamar dazu, da bargo ya lullube ta.

Kallon ta yayi ya ce,

“To me kike so kici? Kinga baki ci komai ba.”

“Wainar shinkafa.”

Ta fada tana kara shigewa bargo.

Mikewa yayi ya zauna yana jijjiga ra. Ya jima dan sai da bacci ya dauke ta sannan ya tashi.

Ya mata kiss a goshi ya fita.

Wani restaurant ya nufa yana zuwa ya samu. siya yayi ya taho gida.

Yana shiga ya nufi bedroom inda ya baro ta. Tana cikin bargo har lokacin Amman ta tashi. ajiyewa yayi ya nufi kitchen.

Plate ya dauko, da lemon kwali na Mango.

Yana zuwa ya zuba mata, dauko ta yayi ya ajiye akan sofar dake dakin..

Lemon ta kalla ta ce,

“Na orange nake so “

STORY CONTINUES BELOW

Mikewa yayi da sauri ya nufi kitchen ya dauko ya koma.

Sosai taci wainar dan sauran ma a firij ta saka.

Tun daga lokacin lafiya ta yiwa Asma’u wuya ga uban amai da takeyi komai taci sai ta amayar.

Lemo Kadai take iya sha shima a rana guda daya take yini tana sha.

Momy kam ba karamin tausayawa Asma’u take ba dan ta rame.

Da ta ce Asma’u ta koma gidan ta har kuka Aslam yai mata dole ta barta.

Amman kullum tana hanya zuwa duba ta.

Da Aslam yai wa Momy korafi akan aman da take yi.

Momy cewa, tayi,

“Ai wannan Aman na lokaci ne, lokaci daya zata daina sai a hankali.”

Mami ma da taji Asma’u na da ciki tayi murna.

Haka Zainab da takanas tazo duba ta, tana ganin Dadyn ta ta farai masa wasa.

Sosai tai murna da zuwan Zainab komai ta dauko Zainab da Dadyn ta, ganin su ma sai yasa ta warke.

Dadyn ta kuwa kullim yana gun ta yaro ya dada wayo dan har an yaye shi ma.

Kwana biyu sukai ta koma. Asma’u na cewa ta bar mata Dady.

Zainab ta ce,

“Kiji da na cikin ki ma.”

A lokacin ita kuma Nusaiba ta haifi dan ta Namiji aka saka masa sunan Dadyn Sabir Marzuk suke kuran sa da Fauwaz.

Itama Zainab tana da yaron ciki a lokacin.

Maimuna ma ta haifi yar ta mace aka saka mata ssuna Asma’u. Suke kiran ta little Husnah.

Asma’u ce kwance acikin kujera a falo shi kuma Aslam yana kitchen yana soya mata wainar fulawa, falon ya kawo mata ta tashi tafara ci sai data cinye tafara sheka amai shi kanshi Aslam sai data wankeshi da amai, rigar jikinta ya cire mata yafara gogge mata jikinta.

Ido ya zuba mata, kirjin ta ya kara cika, haka nan hip din ta sun bude. daukarta yayi yakaita toilet yayi mata wanka shima yayi yadaukota yakawota daki.

Magani ya bata ta sha sai bacci. Yana tausayawa Asma’u dan tana sha wahala sosai.

Ido ya zuba mata, ya ga ta rame sosai. A ransa ya ce,

“Wannan Babyn yana wahalar min da Honey bae ta.”

Jikin ta ya shiga ya kwanta. Baccin ne shima ya dauke shi.

Sai da cikin Asma’u ya girma sannan ta samu sauki.

Tin daga lokacin kuma sai kwadayi ya bude.

Komai tasa a kawo mata. Momy kuwa yau ita ce kai mata kaza gobe kaza duk abinda tasan zata ji dadin sa.

********

Cikin Husnah ya girma haihuwa ko yau ko gobe.

Komai Aslam ne,  ke yimata hatta wanka da wanki shine yake yi mata.

Yau tin rana take jin ciwon ciki amman bata fadawa Aslam ba.

Har dare suka kwanta.  cikin dare ta tashi da ciwo.  Nan Aslam ya tashi ya duba yaga haihuwa ce.

Kasacewa tin da cikin ta ya shiga wata tara ya debo kayan da zasu bukata ko da irin haka ta faru haihuwar dare kenan.

cikin kankanin lokaci ta haifi jariranta tagwaye guda biyu duk maza nanfa Aslam yafara murna.

Shi ya gyara ta, yai mata wanka ya shirya yaran sa.

Gari yana wayewa ya fara shelar fadin haihuwar Asma’u

Ai kuwa yan uwa da abokan arziki suka yita xuwa ganin jariran.

Da Momy ta zo, take cewa Asma’u gida zata tafi ayau sai tayi 40 zata dawo, nan kuma Aslam  yace bai san zancen ba babu inda Asma’u zataje

Fada Momy ta rufe shi dashi ta shiga hadawa Asma’u kayanta.

STORY CONTINUES BELOW

Tana mitar yarinya aure shekara daya da wata hudu bata je gida ba sannan ta haihu ma baza ka bar ta taje ta huta ba.

Asma’u kanta bata son tafiya tabarshi amma, tana son taje gida a kula da ita.

Duk da tasan shima zai kula da ita amman kuma zata kara hutu bare ma yara biyu ai sai da taimako.

Momy da kanta ta kai Asma’u har Kano nan Mami ta  shiga murnar ganinta.

Aslam kuwa tunda ta tafi bai kirata ba dan fushi yake wai meyasa zata tafi bada izininsa ba, ko kanon ma yaki zuwa.

Sai dai duk abinda ake bukata ya turawa Momy shi dan Momy ta ce, sai anyi suna zata koma.

Ana gobe suna sai ga Aslam, da kaya niki niki. Dan set din alkwati ya ciko musu kowa da kayan sa.

tinda yaje ya dauki yaran ya kasa ajiye su.

Sosai yake jin kaunar yaran a cikin ransa yana mai godewa Allah da ya azurta shi da yara har biyu duk maza. Anan yai musu huduba da Suleiman, Sunan Dadyn Asma’u sai Muhammad sunan Dadyn sa.

Ranar suna anyi shagali sosai inda yara suka ci suna Suleiman da Muhammad.

Anyi shagali dan duk kawayen su Asma’u sun zo na makaranta.

Maryam ma taje a lokacin tana da yaron ciki. Anyi bikin ta da Naufal lokacin Asma’u ba lafiya wannan ya hana Asma’u zuwa sai sako da ta aika mata.

Sosai Asma’u tai murna da zuwan ta. Haka Nusaiba ta zo ita ma da kayan barka da Danta Fauwaz ya girma dan watan sa hudu.

Ana gama shagalin suna Aslam da Momy suka fara shirin tafiya.

Aslam kuwa ya san. Zai yi missing din Asma’u ace sai tayi arba’in.

Tana daki a kwance taci ado sai fitar da kamshin take, su yan biyu suna wajen Momy.

Dakin taji an turo, daga kai tayi ta kalle shi. Murmushi ta aika masa ya karaso cikin dakin.

 

kusa da ita ya zauna ya tsura mata ido tana sanye da jar atamfa mai ratsin baki ajiki tayi dan kwaliyya jikin ta ya murje, kirjinta ya cika sosai.

Janyo ta yayi jikin sa, can kuma ya daga ta, ahankali yadaga rigarta ya kwantar da kansa acikinta,

Wasa ta fara da gashin kansa. Ya ce,

“Husnah kice zaki bini dan Allah.”

Murmushi tayi a ranta ta ce,

“Da yake gani uwar marasa kunya ba.”

Mikewa yayi ya ce,

“Baki ce komai ba.”

Ta ce,

“To me zance? In nace zan bika ai nayi rashin kubya ko?”

Kai ya girgiza ya ce,

“ba wani rashin kunya.”

“Hmm!”

ta fada tana wasa da yatsun hannun sa.

“Wallahi zan shiga wani hali in bakya tare da ni. Ki taimaka kizo mu tafi kinji love.”

Dariya ta dan yi ganin da gaske dai Yaa Aslam yake.

“Au dariya kike?”

baki ta danne da hannu ta girgiza kai.

“Shikenan Allah aure zan kara.”

nan take taji gaban ta ya fadi.

Dagowa tayi ta kalle shi sai kuma ta dauke idon ta.

Mikewa yayi ya fice ya barta cikin fargaba da tsoro.

Washe gari da safe sai a falo ma tajiyo shi, mutumin da adakin ta suke karyawa.

Yana zaune yaran sa akan cinyar sa yana ta daukar su hoto.

Zama tayi a gefen sa ta dan rage murya ta ce,

“Ina kwana?”

Bai kalle ta ba duk da kamshin da take yana fizgar sa, amman ya maze ya cigaba da abinda yake.

Ayman ta dauka, wato usaini mai sunan Dadyn Aslam.

Sannan ta dauki, Aayan mai suna Dadyn ta.

Tana amsar su ya mike yayi dakin sa.

Shayar dasu tayi sannan ta mike ta shiga dakin Mami.

Suna zaune Mami da Momy. Sai da ta gaisar da su sannan ta mika musu Baby.

Momy ce ta mike ta ce,

“Bari na kira Aslam yazo mu tafi.”

Ta fice can sai gasu sun shigo, Aslam ya canja shiga zuwa wata Ash kalar shadda.

Yayi kyau, kamar ka dauke shi. Sai tashin kamshi yake.

Akwatin ya dauka ya sauka sannan ya dawo Mami ce ta mike tabi bayan sa.

Momy ta kalli Asma’u ta ce,

“Asma’u zamu tafi munyi magana da Mamin ki mun yanke zaki wata uku saboda yaran su kara kwari kin haihuwar fari ce kina bukatar kulawa. Naso ki zauna a guna amman naga tinda kikai aure baki zo kinga Mamin ki ba. Amman wata haihuwar ni zan kula dake. Da kai na zan zo na dauke ki in lokacin yayi. Duk abinda kike bukata kina sanar dani “

Ta karasa maganar tana shafa kanta. Tace,

“Ki zauna mun tafi Allah kara lafiya.”

Momy ta fita. Asma’u kuwa hawaye taji yana zubo mata Ta ce,

“shikenan sai yai auren da yace zai yi.”

Mikewa tayi takarasa window tana kallon su, suna shiga mota.

Aranta tace,

“Lallai Yaa Aslam ko ya min sallama.”

Waya ta dauka ta tura masa da text din Allah ya kaisu lafiya.

Ta koma ta kwanta akan gadon Mamin ta.Tin daga ranar Aslam bai kara kiran ta ba dan yai fushi sosai duk da yana son yaji ta sai dauriya da yake sai dai ko ya bugi cikin Momy ko in suna waya yana musu labe.

Sosai Asma’u ta damu, amman kuma tana cikin jin dadi da kula da hutu.

Mami bata barin ta da kadaicin da zata zzauna tinani.

Ba abinda take a gida daga wanka sai bacci. Ko yaran sai zasu sha mama ake kawo mata su.

Gyara kuwa da wanka sosai Mami ke mata dan jkin ta har ya saba gashi Mami ta ce wata ukun nan sai an mata wanka dan haihuwar fari ce kuma ya’ya biyu dole a gyara ta in ba haka ba faba zata ji jiki.

Sai anan ta gane manufar da akace sun ka je gida. Dan ta godewa Momy da tace lallai lallai sai ta zo kano,

Tana shan gyara banda cima da Mami ta canja mata.

Sosai ake kula da ita. Kuma akai akai Zainab da Nusaiba da Maimuna suna zuwa duba ta.

Sai dai tausayin Aslam da take ji dan ta san waye Aslma bama akan bukatar sa. Baya iya jure rashin ta gashi wai sai tai wata uku abin da kamar mamaki tasan yanzu yana can yanda takura.

Abinda yafi tsaya mata ma arai kar yaje yai auren da yace zai yi da ya zatai zatai sharing din sa da wata in ta a har kuka tkeyi.

Aslam kuwa yana can yana ta lisafin arba’in.

Ranar da sukai Arba’in a ranar ya dauki waya ya kira ta dan a lokacin ya huce.

Tana dagawa, ya farai mata sururai na irin murna da yake zata dawo.

Shiru tayi a ranta ta ce,

“Bayan ance sai nayi wata uku “

“Ba kyaji nane?”

Y fada.

“Uhmm ina ji.”

“Amman kikai shiru. Kiyi hakuri ban daina kiran ki dan komai ba sai dan gudun kar na shiga wani hali in na kira ki. Wallahi da kyar nake iya bacci ina missing naki Husnah.”

Ajiyar zuciya ta sauke. Ta ce,

“Sai hakuri, tinda kaga su Momy sunce sai nayi wata uku zan dawo. Ka kara hakuri nima ina kewar ka.”

Ido Aslam ya zaro, ya ce,

“Wata uku.”

Kai ta gyada. Wayar ya kashe a ransa ya ce,

“Wallahi bazan iya ba matata zan dauko.”

Baiwa Momy maganar ba ma ya fara shirin tafiya kano.

Yau ya dira a Kano. Gida yayi kai tsaye.

Mami bata nan taje unguwa gida ya rage daga Asma’u dake dakin ta tana bacci ita da yaran ta. sai mai kula da yaran a kasa.

Yana zuwa suka gaisa ya tambayi Mami aka ce bata nan.

Sama ya hau dakin Asma’u ya shiga. Tana kwance, tana bacci tana sanye farin less dinkin riga da siket

STORY CONTINUES BELOW

Ba kwalliya a fuskar ta amman tayi kyau dakin da ita sai tashin kamshi take.

Zama yayi a gefen ta ya zuba mata ido. Kan sa ya daura akan kirjin ta.

Cikin bacci taji kamar kamshin turaren Aslam.

Ido ta bude ta ci karo da fuskar sa. Ido ta mutsuka ta mike zaune.

Zama ya gyara, Aslam ne, dai, yasha shadda brown colour da hula sai zuba kamshi yake.

hannunsa takama ta ce,

“yaushe kazo?”

Ya ce,

“Nazo kinata bacci.”

Murmushi tayi. Jikin ta ya shige, ya rumgume ta.

Motsin su Aayan da Ayma ne ya sa ya juya.

Suna cikin gadon su, mikewa yayi ya dauki, Aayan ya ajiye a cinyar ta sannan ya dauko Ayman.

Mama take bawa Aayan tana gamawa ta mika masa shi ta amshi Ayman shima tana bashi.

Yaran ya zubawa ido yana kalla tamkar yayi kaki ya ajiye saboda tsananin kamarsa dasu yaran an saka musu kaya iri daya pink din riga da blue wando sai farar rigar sanyi a sama.

Yan yatsun hannun Aslam ta murza, kallon ta yayi ya kasa dauke ido. Ta ce,

“yadai?”

Tafada tana kallonsa. Murmushi yayi yai wa Aaayan addu’a sannan ya ajiyr shi. Ayman ya amsa shima yai masa addu’a ya kwantar a gefen dan uwan sa.

Kallon ta ya tsaya ta ce,

“Ya dai?”

Bai bata amsa ba sai kan sa da ya sunkuyar a cibyar ta. ya tura kanshi cikin rigarta ya fara lasar cibiyarta.

Murmushi tayi tashafo sumar gashin kansa tace

“Honey Love ya hanya?”

Shiru bai bata amsa ba domin duk ta gama tafiya da hankalinsa, ita kanta yatafi da imaninta saboda kamshin turarensa kadai yakashe mata jiki.

Dagowa yayi ya ce,

“Nazo na tafi da kune.”

Ido ta zaro ta ce,

“Haba dai.”

“Oh bakya son ki koma?”

Kai ta girgiza. 

kiss yabata akan lips dinta

“yawwa baby gobe zamu tafi to.”

Murmushi tayi ta ce,

“Allah kaimu.”

Sati yayi sannan ya koma da kewar su. Haka ending month ma ya koma a lokacin watan su biyu da sati biyu.

Tunda Aslam  ya tafi ya fara shirin karbar Asma’u  gaba daya gidan ya sake mata komai sabo tun daga kan furnitures har fentin gidan komai yadawo sabo kamar gidan amarya.

itama Asma’u  acan sosai Mami ke gyara ta.

Taje gidan Uncle Habu da Kanwar Dady Momy Binta da Uncle iliyasu. duk sunji dadi sukai mata alheri.

Sannan taje grin su Mami wajen yan uwan su Mami. Kwananta bakwai ta dawo.

Sannan ta zaga kawayen ta. Suma da suke yawan kai mata ziyara. Har gidan Maman zainab da Mamayn Sir Sabir taje.

A daren ranar kuma sai ga Sir Sabir da Nusaiba da Baby Fauwaz.  Sun gaisa ya daumi yara yana tai musu addu’a. Da zasu tafi ya ajiye musu dubu dari ya ce a sai wa yara riguna.

Tai masa godiya har wajen kota ta rakasu sannan suka tafi.

Ranar Alhamis sai ga Momy nan. Nan tasan lokacin lafiyar ta ne yaxo.

Zainab ta fadawa Zainab tazo ta dauke ta   kai ta aka gyara ta.

Akai mata lalle, da gyaran gashi tafito ral kamar amarya. Ranar a gidan Zainab ta kwqna. Zanab ce dafa wannan takai mata haka nan Yaa Huhari duk ya debe yaran ranar yaran gun su suka kwana. Dan Yaa Buhari akwai son Yara.

Washe gari ta daqo gida Zainab ce duk ta hada musu kayan su. Momy ma da taga yaran taga sun yi saurin girma ta kalli Mami ta ce,

“Amina me kike bawa yaran nan naga duk sun kara girma da kyau bama ‘ya ta.”

Murmushi Mami tayi ta ce,

“Nima ina mamaiin girman yaran nan sai kace ba yan biyu ba.”

Momy ta ce,

“Daga nonon Maman ta sune.”

Ranar kusan kwana sukai ana hira da su Mami dan Asma’u sai bar musu yaran tayi ta tafi ta kwanta.

In da washe suka dau hanya. Suna zuwa Momy gidan ta ta kai ta.

Gidan da ta ga ya canja, kamar sabon gida.

Tayi mamakin irin aikin da akai a gidan dan za ta ce har gidan yafi lokacin da ta tate kyau da tsari duk yadda wancan tsarin yayi kyau.

Tare da Mama mai taya ta raino suka tafi. Lokacin da suka je Aslam baya nan. Dan haka ta hau gyaran gidan Ta debe su Yaman ta kai ma Mama dan ta rike mata su. duk da ba wani datti yayi ba komai tsab yake.

Haka ta kara gyara shi ta turare shi da turaren wuta mai dadi da kamshi. Tini gidan ya kara kau da fitar da iska mai dadi.

kitchen ta dora Coconut rice sai miyar da tayi ta zuba kji. tayi da farfesun hanta, Bayan ta gama ta diba ta kaiwa Mama. ta dauko yaran tai musu wanka ta shirya su ta sa sukai bacci.

itama tai wanka ta shirga cikin body hug ja da bakin wando  takama gashin kanta da jan ribom, sai da ta turare gidan da kanta da daddadan kamshi tukunna tazauna a falo tana jiran zuwan Aslam.

Har akai isha’i bai shigo ba. Tana kwance tana kallo yana shiga ya hangota zaune cikin kujera das da ita tamkar budurwa.

Tsayawa yayi yana kallonta tana juyowa suka hada ido ya tsuke cikin Ash suit, tasowa tayi tazo ta shiga jikinsa tana magana a hankali

“sannu da zuwa  Honey love,”

kasa magana yayi ya cafki bakinta yafara tsotsa tuni itama tafara mayar masa da martani, ganin tsaiwar zata gagaresu yasata kama hannunsa zuwa bedroom dinsa suna shiga yajata kan bed, ya kwantar da ita ya fara sinsinar ta rike shi tayi tace,

“ka zo kaci abinci,”

“bazan iya ba.”

yafada acikin kunnenta

“To tsaya na taimaka maka da cire kayan.”

A hankali ta fara cire masa.

Jan ta yayi ka gado, kayanta yafara cirewa dasauri dasauri nan yashiga nuna mata zallar so, sai dai ita Asma’u ji tayi kamar ranar farkonsu dan dakyar ya iya shiga ga wani radadi da takeji, shi kam Aslam washar dashi dan ji yayi Husnahn Sa tadawo sabuwa fil.

Soyayyar da ya nuna mata ta tsaya mata a rai dan baza ta taba mantawa da wannan irin soyayyar ba. Sosai ya nuna mata irinnyadda yai kewar ta da yadda ya ke jin ta a ran sa.

Bayan komai ya gama wanzuwa ne Aslam ya jata jikin sa yana zuba mata mata albarka sun jima a haka yana shafa gashin kanta. Sannan ya ji tana saukar da numfashin ta a hankali

Dubawa yayi yaga har tayi bacci. tashi yayi  yashiga wanka yana cikeda annashuwa yana fitowa yanufi dakinta acan yaga twins dinsa sunata bacci

Dakin da take ya koma. Har lokacin tana bacci. Kanta ya shafa a hankali yana hura mata iska a cikin kunnen ta. Ido ta bude, ta tashi daga baccin, kallon Aslam tayi da idonta jajur duk jikinta ciwo yake yi mata gashi ji take ko tafiya bazata iya yi ba.

Fuska ta shagwabe, ta ce,

“zanyi wanka.”

tafada tana turo baki.

Murmushi yayi ya mike ya shiga bandaki ya hada mata ruwa

Daki ya koma ya dauke ta ya kaita bandaki. Shi yai mata wanka dakyar ta iya taka kafarta tadawo daki  tana dawowa tawuce dakinta ta kintsa tasa wata doguwar riga iya kar ta cinya. batayi wata kwalliya ba tadawo dakinsa. Yana zaune, ta ce,
“zo muje kaci abinci danni yunwa nakeji sosai,”

Tashi yayi daga shi sai gajeren wando sukaje falo dakyar take tafiya suna zuwa ya kwaso musu abincin ya kawo kan carpet ya ajiye yafara zuzzuba musu nan tafara ci.

kallonta Aslam yayi, ya ce,
“sannu baby, Allah miki albarka.”

Batayi masa magana ba har sai data koshi. Kallon ta ya sake ya ce,
“Sannu!”

Hararar sa tayi ta ce,
“Eh ai ka min sannun, wallahi Yaa Aslam baka bina ahankali koda yaushe da karfi kake yi min,”

Ta fada tana turo baki. Dan tsotsar bakin yayi, sannan ya ce,
“kiyi hakuri ba laifaina bane,”

Mikewa tayi ta shiga dakin ta. Duba su Aayan tayi taga suna bacci.

Falo ta dawo ta  hau kan kujera tamike kafa. Biyo ta yayi yana mata tausa.

Ido ta lumshe, ya ce,
“Ba tin yau ba na fada miki a irin jinsin matan da kike. Ku kalilan ne, wannan yasa kike jin jiki a duk lokacin da nai kwana biyu ban kusance ki. bare yanxu wata uku fa. Ai dole. Ni kam naji dadi na. Na samu yar baiwa, wace ko da yaushe take a budurwar sabuwa.”

Ido ta bude tana kai masa duka. Hannun ta ya kama, ya fara kissing na ta. Nan da nan jikin ta yai sanyi.

***************

Tsakanin Aslam da Asma’u zamane suke yinsa na kaunar juna da soyayya, yaransu sun girma sunyi wayo yanzu watansu 9 amma idan ka gansu zaka zaci sun shekara daya dan suna gudun ko ina.

Sosai suke Samu kulawa daga wajen iyayen su da Kakkanin su.

Dan in suka ga Momy ko Mami har wani shagwaba suke musu dan sun san abinda suke so shi za ai musu.

Zaman lafiya mai hade da soyayya da kaunar juna shi yake wanzuwa tsakanin Aslam da Asma’u.

Su Yan biyu na da shekara hudu Asma’u ta sake samun ciki.

STORY CONTINUES BELOW

A lokacin har an saka su a makaranta. Yara kyawawa da su abin sha’awa.

Wannan cikin alhamdulilah ba wani laulayi sai kwadayi.
Daga ta ce, kaza take so sai ta ce kaza.

Aslam kuwa yau shine dafa wancan soya wancan dan in ita tayi bata iya ciki.

Duk da haka tana kokari wajen kula da gidan da mai gidan ta.

Wannan karan ma yan biyu ta haifa duk mata. Akasa wa hassana Fatima, suke kiran ta Nabihah sai usaina Amina ake kiran ta da Nabinah.

********——–*********
*BAYAN SHEKARA 12*
Sanye take cikin wani tamfatsatsen leshi mai kyau baki da ja. sai kamshi take zubawa, falo ta fito babu kowa, ta tagar baya ta leka.

Hangon su tayi, Aslam na zaune rike da jarida. yana sanye da three quarter da yar karamar rigar shan iska. Sai  Aayan da Ayman suna buga ball. Sun saka kayan ball a jikin su. Da ka kalle su zaka ga kamar su daya da Aslam ba abinda suka baro shi. Kamar ya’yan labara bawa ko da yake baban su jinin larabawar ne.

Gefe kuma Nabibah da Nabinah ne, sai Autar su, Husnah wacce shekarar ta hudu, suke kiran ta  da Nawal.

Sun zaune suna duba littafi. Suna sanye da farin dogon wando da pink riga.

Kansu an musu parking da pink ribon. Kafar su ma pink cover shoe ne.

Can Aslam ya mike yai Cikin gida. yana shigowa ya hangota tsaye tana kallon yaransu ta window, bayanta yaje ya rungumeta akoda yaushe son Asma’u yake ji yana shigarsa sosai gata dai haihuwarta uku yaranta biyar amma har yau bata gundurarsa.

Juyowa tayi ta rumgume shi ita ma. kissing nasa ta fara ko ta ina. Ganin tsaiwar baza ta dauke su ba yasa ya dauketa cak a kafadarsa yayi cikin dakinsa da ita.

A Kan gado Ya kwantar da ita yafara yi mata wasanni masu rikitarwa.

Sosai suka shayar da juna su zumar soyayya tsadadda   sannan sukayi wanka suka fito, kwalliya suka sake tasaka yellowar atamfa shi kuma yasa blue kalar shadda.

Mayafi ya dauko mata suka fice daga gidan. Hanyar cikin gari taga sun nufa.

Kallon sa tayi tace,
“sai ina?”

Murmushi yayi ya ce
“Rufe idon ki!”

Idon ta ta rufe. Parking yayi ya fito ya bude mata site din da take.

Hannun ta ya kama ya ja ta. Dai da suka tsaya samnam ya ce,
“Open ur eyr my queen.”

Ido ta bude, wani katon asibiti ta gani a gaban ta.

Kai ta daga, ta ga an rubuta *ASMAAAF CLINIC*
Ido ta bude ta ce,
“Means?”

Murmushi yayi ya ce,
” *ASMAAAF* Means, Asma’u, Suleiman, Muhammad Aslam, Amina, Asma’u, Fatima.”

Rumgume shi tayi, ta ce,
“Yayi kyau!”

Murmushi yayi ya ce,
“Naki ne!”

Kallon sa tayi da mamaki ya ce,
“Kin wuce haka a guna Asma’u. Kece farin ciki na rayuwa ta cikar buri na. Banda abinda zan saka miki da shi sai dai ina miki addu’a Allah ya biya miki bukatun ki na alheri Allah ya hada mu a gidan Aljanna dani dake da yan uwan mu musulmai baki daya.”

Rumgume shi ta yi sai kuma kuka, ba wanda ta tino sai da Dady da ya ke ce mata Ko baya raye ya bar mata farin ciki. Farin cikin ta kuma sune Aslam da Yaa Buhari da Mamin ta.

Lallai yau ta dada yadda Yaa Aslam da Yaa Buhari da Mamin ta sune farin cikin ta. Tana kara godiya ga Allah da ya mallaka mata Uwa kamar Mami.
Ya bata Yaya kamar Yaa Buhari mai burin ganin farin cikin ta. da kyautata mata kullum burin sa ganin ta bata da damuwa tana cikin farin ciki da walwala
STORY CONTINUES BELOW

Sannan ya bata Miji Yaya kamar Yaa Aslam wanda samun kamar sa sai an tona. Kullim.cikin kaunar ta da nuna kata kyautar ta yake. Bai da buri sai.na yaga ya kyautata mata. To.ita kuwa mai zatayi in ba addu’a gare au ba. Tare da Dadyn ta da Mami da Yayun nata.

Daga nan gida suka yi. Suna komawa ta shiga kitchen. Ita ce girka wancan dafa wancan.

Dan karamar walima ta hada musu a gidan aka ci aka sha akai hoto. Sannan ssuka zauna kamar yadda sukai akai hira anan kuma. A zauna ai karatun al kur’ani wanda duk dare kan a kwanta da asuba in an tashi sai anyi izifi daya gaba dayan su. daga nan  za ai ta bada labari bama Husnah da kullum sai ta basu labarin Dadyn ta.

Wanda suke ji daman yanan ja suma ya nuna musu tashi kalar soyayyar. Duk akn su sun san Dady kuma kullum akai sallah sai an masa addu’a Allah jikan sa.Nawal kuwa da ba wayo takan ce
“Ummu ki ka’ ni gun Dadyn ki.”

Sai dai Asma’u tai murmushi ta ce,
“Zamu je gun sa amman sai munyi aiki na gari a rayuwar mu. Dan Dady mutum kirki ne.”

Abibda Dady ya roka ta cika masa dan yaran sun tashi da son sa da masa addu’a in kaji ana labarin Dadyn Asma’u sai kazata yana da rai wani abun.

Sun jima sannan kowa ya je ya kwanta.
Sai da tai wanka sannan ta fito daure da towel Aslam ne yashigo dakin.

Tsayawa yai abakin kofa ya harde hannu a kirji.
Kallon ta yake yadda kugun ta yake juyawa. murmushi tayi ya karasa wajen ta.
Turare take shafawa ya karasa,
kugunta ya rike yace
“shekaru goma sha uku kenan amman har yanzu kina nan a yadda kike, ko ma nace kinfi da dadi.”

Ya karasa maganr yana rada mata wani abu.
Juyowa tayi ta daura hannun ta asaman kafadar sa, ta ce,
“Kai ma haka!”

Bakin su ya hada, ya fara bara wani irin zazzafan kiss.
Sai da yayi iya yin sa sannan ya dago ya ce,
“Kece Farin cikina Husnah”

Ido ta lumshe, tayi lamo a jikin sa.

Ya ce,
“Yau xamu samowa Nawal kani ko kanwa, tinda naga kamar tsarawa kike duk sai sunyu four to five years ko.”

Duka ta kai masa tana shigewa jikin sa.  Nan ya shiga ga nuna mata zallar so.

*ALHAMDULILAH

*Dukkan godiya sun tabbata ga Allah da ya bani ikon rubuta wannan littafin lafiya. Ina kara godiya ga Allah.*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *