RAYUWAR ASMAU CHAPTER 4
Washe gari kamar yadda ta tashi tin asuba ta tashi.+
Sallah tayi ta zauna tai karatun al kur’ani sannan ta janyo littafin ta ta kara dubawa ta jima tana duba littafin sannan ta mike ta sauka kasa. Mami ta dan kamawa abubuwa ssannan ta koma sama.
Wanka tayi ta shirya cikin wata maroon kalar doguwar riga mai dogon hannu.
Golding din takalmi da jaka ta dauka sai bakin hijab da ta saka iya kar sa kirji.
Ba karamin kyau tayi ba fuskar ta tayi fes a ciki.
Idonun ta sun kara gaske da girma girar nan tata a kwance luf luf. Leben ta sai kyallin man lebe yake.
Dakin Dady ta shiga suka karya sannan tai musu sallama ta fito ta tafi dakin Ya Buhari.
Yana zaune a gaban system ta same shi. Karasawa tayi ta ce,
“To su Yaya me ake aka tashi da sasafen nan.””
Bai kula ta ba. Dan durkusawa tayi ta gaishe shi. amsawa yayi yana dagowa ya kalle ta.
Baki ya tabe ya ce
“Baki kyau ba.”
Murmushi tayi ta ce,
“Kyan kaga nayi.”
“Ahakan?”
Kai ta gyada masa.
“Uhmm dauki abonki afirij.”
Ya fada yana nuno mata firij din.
Gun firij din tayi ta bude. Ice cteam ta gani a ciki dayawa. biyu ta dauka ta ce,
“Yaya in na dawo na dauki sauran.”
Kallon ta yayi ya ce.
“A dawo lafiya.”
Sannan ta fita. Dakin Mami taje tai mata sallama sannan ta sauka kasa.
Baba yana ganin ta ya taso yayi wajen motar ya fito da ita.
Sai da suka gaisa sannan ta bude gidan baya ta shiga.
Kiran Yaa Aslam ne ya shigo dauka tayi,
Bayan sun gaisa yake cewa “amman dai tana ckul ko?”
“Aah Yaya yanzu dai zan tafk.””
“Amman dai kinsan kin makara a yadda kika fadan kina da test ko?”
“Ah haba dai!”
“Eh man tara saura minti goma. Minti goma zai kai ki ckul ne.”
“Insha Allahu!”
“To Allah bada sa’a sai kin dawo ki turon pics din ki ina jira.”
Ta katse wayar selfie ta dauka ta tura masa sai anan taga ashe dai da gaske Yaa Aslam yake ta makara ta tabbata nan da minti goma da kyar zasu karasa.
Addu’a take Allah yasa kar ya shiga har sai ta shiga.
A hankali Baba ya dinga jan su har suka karasa makaranta.
Lokacin tara da minti goma. Da sauri ta fita daga motar.
Hango shi tayi yana nufar ajin cikin takun kasaita yake tafiya.
Yana sanye da golding kala shadda ya saka brow kalar takalmi da hannun sa rike da waya ya kara a kunne daga gani amsawa yake.
Ba kara min kyau yayi ba. Fatar sa ta kara kyau da sheki. Gashin kansa ya kwata luf luf dashi.
STORY CONTINUES BELOW

Ganin ya karasa ajin ma. yasa ta tsaya daga inda take hangen sa.
Waje ta samu ta zauna daga gefen ajin ta kifa kanta akan jakar ta ta fashe da kuka.
Ta dade tana kukan dan har karfe goma bata dago ba tana ta shesheka.
Karfe goma dot ya fito daga ajin rike, da takardu a hannun sa. Yana karasowa inda take akai kiran wayar sa.
Daukar wayar yayi, ya kara a kunnen sa yana kallon Asma’u da ta kifa kai.
A wajen ya tsaya ya amasa waya, tana jin yadda yake maganar a hankali amman ta kasa dagowa.
“Yanzu zan karasa office din kin karaso ne?”
Ya tambaya.
“Ok!”
Kawai ya ce ya kashe wayar.
Sai da ya kara kallon ta sannan ya bar wajen. yana barin wajen zainab ta karaso tana dago kanta.
“Kuka!”
zainab ta fada tana share mata hawaye.
“Ba dole nai kuka ba. Wannan course din kar ya jawon Matsala fa”
Ta fada tana kara fasa wani kukan.
“Haka ne, amma kinsan Sir Sabir yana da sauki kai da kin shigo zai iya barin ki.”
“Haba Zainab sau nawa nake makara yake kyale ni so kike a fara kawo wani zargin bayan kinsan baya bari a shigar masa aji duk wanda ya makara daya ga ya shiga juyawa yake.”
“Kinga bar wannan zancen kije gun sa, kawai ki baahi hakuri kiji me zai ce,
ya kara bada wani Assignment din ma in bai miki ba kinga kina da assignment balantana ma insha Allahu zai miki.”
“Uhmm fa Zainab kar naje yaki min. Ni dai wallahi na hakura”
“Dallah can tashi muje!”
ta kamo hannun ta suka nufi office din sa.
A bakin office din ta bar ta. Yauma kamar rannan ta dade tsaye a kofar amman ta kasa kwankwasa kofar
Cikin sanda ta dan kwankwasa. Izinin shiga ya bada. wata faduwar gaba ce ta sameta.
A hankali ta daura hannun ta akan kofa, ta murda ta budo. Nan ma ta dau minti biyu kafin ta tura ta shiga.
Tana shiga taji wani sanyi me ddi hade da kamshin turare na dukan ta.
Tsayawa tayi a gun kafin tayi sallama. wata yarinya dake gefen sa, tana bude masa fulas din abincin data kawo ta zuba mata ido.
Yarinyar zata yi shekara goma sha shida zuwa sha bakwai Kyakyawa ce suna kama da Sabir kamar kanwar sa.
‘Yar yayar sa ce tazo musu hutu shine Mamah ta aiko ta, ta kawo masa abinci dan tasan halin sa da kyar zai ci wani abu gashi ya fito bai karya ba.
Kallon Sabir yarinyar tayi ta daga masa kai.
Ya ce,
“Uhmm Maryam zo ki tafi nagode kar Mamah ta tafi ta barki.”
Maryam ta ce,
“Kai Uncle wallahi Mamah ta ce, in tabbatar da kaci tukkunna “
murmushi yayi wanda ya kara fitar da kyawun sa ya ce,
“Da yake, ni yaro ne ko. Ko ni yaro ne, ina uncle din ki zaki ce sai naci abinci ne, maza zo ki tafi kice naci kinji.”
Ya fada yana daukar dankalin da aka soya a cikin kwai da attaruhu da albasa yana ci.
Gefen kuma kunun gyada ne da yaji madara.
Jakar ta ta dauka ta ce,
“Allah Uncle haka zan ce baka ci ba.”
Tayi gefen Asma’u dake tsaye tana jin su.
“Sannu!”
Ta fada tana mika mata hannu.
Dagowa Asma’u tayi ta kalli yarinyar kamar su daya da Sabir.
Dan murmushi Asma’u tayi ta mika mata hannu ita ma suka gaisa.
Murmushi Maryam tayi ta ce,
“Sunana Maryam Suleiman ni ‘yar yayar Uncle Sabir ce.”
Kallon ta Asma’u tayi da idon ta da suka canja kala ta dan yi murmushi ta ce,
“Ni kuma Asma’u Suleiman!”
Maryam ta ce,
“Lah suna Baban mu daya amman wallahi Asma’u kin burge ni kawai naji ina sonki.”
Murmushi Asma’u tayi ta ce
“Nagode sosai.”
Sabir dake zaune yana cin dankali yana kallon su ya ce,
“To Maryam kije kar Mamah ta tafi ta barki dai Allah ke kadai zaki zauna a gida har magariba.”
Sakin hannun Asma’u tayi ta ce,
“Na tafi sai nazo gun ki wata rana.”
Murmushi Asma’u tayi ta daga hannu tana mata bye bye har ta fita.
Kai ta juyo ga sabir da ya zuba musu ido sai fitar da murmushi yake
Tana juyowa ya mai da kan sa ga abinda ke gaban sa.
Asma’u ta ce,
“Sir dan Allah ka taimaka min!”
“Dame fa?”
Ya fada yana cin dankalin sa cikin kwanciyyar hankali.
“Sir Test wallahi makara na yi shiyasa “
Bai dago ya kalle ta ba ya ce,
” *Husnah* wai ke kullun sai kin makara!”
Da sauri ta dago kanta jin sunan da ya ambata.
Ido suka hada wannan yasa tai saurin dauke kan ta.
“Ji idon ki me ya same shi? Kuka ko?”
Kai ta girgiza.
“To mene?”
“Ba komai.”
” *Husnah* baki ban amsa ba. Me yasa kike makara?”
Shiru ta karayi.
“Tin yaushe kike tashi?”
Ya tambaye ta.
Asma’u ta ce,
“Asuba!”
Kai ya jinjina ya ce,
“Me kike yi har kike makara?”
“Ba komai!”
“Ba komai amman kuma kike makara?”
Kai ta gyada.
“Ki fadan abinda kike in kika tashi tin asuba.”
Kasa tayi da kai ta ce,
“Mami nake dan tayawa aiki sai nai shirya. Kuma in nace bazan karya ba sai Dady ya zaunar dani sai naci. daga nan sai naje na tashi Yaya Buhari na gaishe shi na taho makaranta.”
Murmushi yayi jin yadda take maganar cikin shagwaba. ya ce,
“Ku nawa ne a gidan ku?”
“Daga Dady sai Mami, sai Yaya Buhari sai ni!”
Ta fada tana wasa da hannun ta.
“Kina da kanwa ko kani?”
Kai ta girgiza ta ce
“A’ah!”
Ya ce,
“No wonder ashe shiyasa kike shagwaba ko dan kece autah ko?”
Fuska ta dan bata tayi shiru. Ya ce,
“Eh mana. In ba haka ba menene na kuka dan baki shiga class ba.”
Shiru tayi ya ce,
“Dauko takarda.”
Tai saurin ajiye jakar ta tana daukar wata takarda.
Kujera ya nuna mata ya ce,
“Zauna!”
Ta zauna. question din ya karanto mata ta rubuta.
Abincin sa ya cigaba da ci cikin kwanciyyar hankali. Sai da ya gama ya koma cikin office din inda aka zuba masa wasu hadadun kujeru da kayan kallo.
TV ya kunna ya rage volume