SAUDALA CHAPTER A
Wata dariya ce ta kusa kufcewa saudala , amma sai ta danne ta cigaba da cewa
” karki sake ki fito tsakar gida yanzu, ki bari sai da safe in ba haka ba anan zaki kame har sai wani daren ,
Iya da take kwance cikin kashi kai kawai ta daga jikin ta na rawa,
Tace “in kika fadawa wani wannan abinda ya faru shikenan sunan ki gawa ,
Cikin rawar baki iya tace ” kwarankwasi bazan fada ba ,
Saudala cikin tsawa tace ” rife idon ki
Tsawar da tayi yasa iya kuma sakin wani kashin😂 , cikin sauri ta rife idon ,
Mikewa saudala tayi ta wata tafiya kamar aljanar gaske tana bude hannu kamar tattabara ,
Tana zuwa daki ta dinga dariya kamar mahaukaciya ,
Tace ” zaki gane kuran ki iya , badai ni kika zaga ba ,
In sane nace karta fito sai da safe yadda zan kuma cin dariya 😂😂
Tashi tayi ta wanke fuskar ta ta cire kayan jikin ta ta kwanta,
Tunda saudala ta fita iya take kuka tana fadin
” shikenan karshe na yazo aljanu sun fara bibiyata , kai dole gobe nabar gidan nan dan bazan iya zama wannan aljanar ta kashe ni ba ,
Haka iya ta kwana bata rintsa ba , tana ji ana kiran sallah amma babu damar fita tunda aljana tace sai da safe ,
Karfe shida na safe saudala nata tsakar gida a zaune umman ta kuma ta fara hura huta dan daura abinci,
Iya ce ta fito kashi yana bin kafar ta duk ta bata wajan ,
Ai saudala tana ganin ta ta mike, amma sai tayi kamar bata ganta ba , kawai sai tayi wajan umman ta
Iya da bata kula da kowa ba cikin sanda take tafiya duk dan kar saudala ta ganta da kashi🤣🤣
Sai da ta bari iya ta fito sosai yadda babu damar komawa sannan tace
” kai umma warin kashi fa nake ji ,
Umma tace ” nima haka saude warin ya isheni ,
Sai kam saudala ta juyo ,
Tace ” lah yanzu iya kashi kikayi a kwance sai kace wata saniya ,
Ta fada tana kyalkyalewa da dariya😂😂😂
Iya ta kulu sosai tace ” baban ki ne saniya ba ni ba , banxa me kan daddawa,
Saudala tace ” kika kuma zagi na ,
Cikin masifa iya tace ” an zage kin ko zaki rama ne ,
Saudala tace ” ke dai kiji da kashin kwance ki,
STORY CONTINUES BELOW

Ta fada tana barin wajan ,
Umma tace ” sannu iya hala matsarki yayi ko ?
Iya tace ” ban sani , ni yau ma zan bar muku gidan bazan iya zama aljanu su kashe ni ba ,
Umma tace ” aljanu kuma iya ,
Sai yanzu ta tuna kashedin aljana akan kar ta fadawa kowa ,
Kawai sai iya ta fashe da kuka tana fadin
” na tuba ki yafe ni wallahi ban san na fada ba , dan Allah karki kashe ni ,
Umma dai kawai kallan ta takeyi ,
Yara ne suka fara shigowa suna fadin
” lah wallahi saudala da gaske take kunga me kashin kwancen nan suka fada suna nuna iya , 😂
Saudala ce ta shigo tace ” to muyi mata waka mana ,
Sai suka fara fadin
_tsohuwa me kashin kwance_
_ita ko kunya ma bata ji_
Saudala tana yi suna amsa mata ,
Baba ne ya jiyo hayaniya ya fito ,
Yara ya gani suna yiwa tsohuwar sa waka ,
Cikin sauri ya kori yaran , ya kulle kofar gidan,
Wajan iya ya nufa da take a durkushe tana kuka ,
Yace ” iya lafiya meya faru ?
Kafin iya ta bada amsa saudala tace
” kashin kwance tayi , kuma me wari tsiya ,
Baba yace ” ke na tambaya karna kuma jin bakin ki ,
Cikin kuka iya tace ” alkur’an bazan zauna a gidan nan ba , yau zan koma abuja wajan yayan ka , aljanu ne a gidan nan ,
Kafin baba yace wani Abu saudala tace
” tab ai duk inda kikaje sai sun biyo ki gwara za kiyi zaman ki a kauyen nan , tana gama fadar hakan ta fice daga gidan,
Iya ta kara fashewa da kuka ,
Umma ce tace ” yi hakuri iya tashi muje kiyi wanka,
Umma ta taimaka mata tayi wanka ta shirya ,sannan tayi sallah ta zauna ta zuba uban tagumi,
Saudala kam tana fita ta hadu a kawayen ta dije da talatu suka nufi gonar mlm habu,
Suna zuwa suka ga mangwaro ya fito yayi kyau ,
Bishiyar saudala ta hau in ta tsinko sai ta cillowa kawayen ta ,
A haka har suka debo me yawan gaske,
Dirowa saudala tayi dai dai lkcn mlm habu yazo wajan ,
Saudala a ranta tace ” daman kai nake jira kazo, ba dai rannan ka cemin shegiya ba ,
Zaka gane kuran ka mlm habu.🤣🤣🤣
Kome saudala zata yiwa mlm habu?🤔🤔
😂😂
Wacece saudala?🤷♀
🥰Sai mun hadu a next page🤝😘
Comment & share
Neat lady ✍🏻
🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
🇳🇬®
*_ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION📚✍🏽_*
STORY CONTINUES BELOW

[❄Dance above the surface of the world. Let your thoughts lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
Story & written
By
NEAT LADY ✍🏻
Dedicated to *MISS XERKS*😘😘
Bismillahir rahmanir rahim
4&6
Kusa da malam habu ta karasa tana zuwa tace
” Na tsinki mangwaro a cikin gonar nan me ka isa kayi ,ta fada tana murguda baki
Malam Habu ransa ya baci , yace
“Kiyi min sata sannan kizo gabana kina fada min,
Tace “An fada din kayi duk abinda zakayi ,
Ta fada tana kwasa a guje
shima ya rifa mata baya
Amfanin gonar ta dinga takewa tana wucewa ,
Ran malam habu ya kuma baci ,
Gudu take yana binta wani kofar gida tazo me malalen siminti sai sheki yake ,
robar da tasoke a kasan rigar ta ta dauko ta dinga zubawa a wajan , tana gamawa ta mayar da robar ,
Da gudu malam habu yazo wajan ai yana takawa ji kake timmmmmmm ya fadi kasa ,
Me saudala zatayi in ba dariya ba ta rike ciki tana dariya kamar mahaukaciya
Malam habu da kafarsa take masa zugi cikin bakin ciki yake kallan ta ,
Yace ” yanzu saude kuka kika zuba min dan na fadi ?
Cikin dariya tace ” Gobe ma ka kuma zagina , asha jinya lafiya,
Tajuya tayi tafiyar ta,
Mutane ne suka taimakawa mlm habu aka kai shi gida
Tafiya take tana dariya ta hango wasu mata yan birni da alama bakine a garin ,
Wajan su ta nufa tana zuwa tace
“Ku kuma daga ina ?
Daya daga cikin su
tace ” what is you’re name ?
Kutumelesy ni matar nan zata zaga da turanci ta zata ban iya ba,
Saudala tace ” da zaki zage ni da turanci an fada miki nima ban iya bane ,
banza junuary February kawai in kin isa ki rama aljana kawai ,
Tafiya take tana tunani lallai ta fadawa yan matan nan magana tunda suka kasa amsawa har ta shiga gida tana tunani,
Tana shiga tayi tozali da iya a zaune tayi tagumi ,
Kyalkyalewa tayi da dariya harda kwanciya ,
Cikin dariya tace ” wa aka samu ya wanke miki kashin , gsky kin iya kashi me wari kamar na saniya
Iya me kashin kwance sannu da kashi.
Umma ce ta daka mata tsawa tace
” ke saude iyan kikewa wannan dariyar dan baki da mutunci eyee ,
Umma nifa ba iya nakewa dariya ba kashin tane yake bani dariya , duk kauyen nan babu Wanda ya kaita yin kashi me wari , da ace zaayi gasar waddan da suka iya kashi to da iyace zata zo ta daya
Cikin b’acin rai baba yace
“Ko kiyi min shiru ko nazo na bige bakin ki ,
Iya tace ” Ku k’yaleta yau din nan zana bar gidan dan bazan iya zama aljanu suna tsorata ni ba,
STORY CONTINUES BELOW

Kafin wani yayi magana saudala tace
” hmmm iya kenan ai duk inda kikaje sai sun biyoki , balle ma duk sunji abinda kike cewa ai shikenan iya har abujan zasu biyo ki,
Iya ta fashe da kuka sosai don ta harda da abinda saudala ta fada ,
Saudala kam abin nema ya samu dariya take kamar me ,
Saida ta gaji dan kanta sannan ta mike ta shiga daki a ranta tana gwada muguntar da zata yiwa iya yau.
WACCE SAUDALA?
Saudala ‘yace wajan malam Ahmadu,
Fulani ne irin kyawawan nan ,suna zaune a garin Adamawa dake Nigeria,
Saudala tun tana karama bata jin magana akwai ta da tsokana , ta gagari yan rugar su gabadaya domin duk girman ka ka shiga harkar ta to sai ta rama , ita kadai Allah ya bawa malam Ahmadu da hafsatu wato umma,
Yarinya ce kyakykyawa sosai fara tas komai Allah ya bata dai² ita ,
Malam Ahmadu daya ne daga cikin masu kudin kauyen Dan Allah ya bashi nasibin noma ,
Iya itace mahaifiyar malam Ahmadu su biyu ta haifa a duniya daga yayan sa wato alhaji umar sai shi ,
Alhaji umar me kudi ne sosai yana zaune a garin abuja, babu yadda baiba malam Ahmadu ya dawo abuja amma yaki yace yafi son zaman kauye, iya ma tace tafi son zaman kauyen saidai suje abuja da ziyara ko su suzo,
Alhaji umar yana da mata guda daya wato halima wacce ake cewa mama, yana da ‘ya’ya gudu biyu namiji da mace daya,
Wannan kenan
Cigaban labari
_Kuyi manage da wannan kaina ke min ciwo_🤦🏼♀🤦🏼♀🤦🏼♀🤦🏼♀
Comment & share
Neat lady ✍🏻
https://www.Facebook.com/Romantic-Writers-Association-415799935882006/
💥 *ROMANTIC WRITERS ASS…*💥
*We are the star’s keep shining always*💥
🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌲🌲🌲
🌴🌴
🌳
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
Story & written
By
NEAT LADY
✍🏻✍🏻
Bismillahir rahmanir rahim
1&2
An tsahi daga islamiyya da misalin biyar da rabi na yamma ,
Wata Yarinya ce da ba zata wuce shekara goma sha uku ba ,
Tafiya take tana tsale tsale ita da kawayen ta su biyu ,
Wasu samarine irin wizayen nan an zazzago wando kasa ana ganin na ciki ,
Saudala ce ta hango su ai da gudu suka tafi wajan ita da kawayen ta ,
Suna zuwa ta sha gaban su kallan take tana kyalkyala musu dariya tana nuna su da hannu ,
Tace ” yanzu haka kuke yawo kuna sabulowa wando , daman daga ganin ku kunyi kama da yan isaka , ai gwara Ku cire wando gabadaya,
Daya daga cikin samarin yace
” ke mu zaki yiwa rashin kunya , zan kifa miki Mari wallahi,
Tace ” mare ni din , kai daman ana ganinka an San kashi kake ji wasani ma ko a wando kayi ,
Ta kyalkyale da dariya tana yi masa gwalo 😜
tace ” me kashin wando , me fitsarin kwance,
Sauyarin yaga mutane suna yi masa dariya , abin ya kara bashi haushi, ai sai ya bita da gudu
Tana ganin haka sai ta diba da gudu , kawayeta suka mara mata baya,
Gudu take yana binta wata hanya ta shiga ta bile wani wajan ,
Gida ta shiga da gudu tana zuwa tayi daki ta kulle kofa ,
Wata tsohuwa tana rike da buta a hannu da alama bandaki zata shiga taga ta shigo a guje ,
Tsohuwar tace ” ke yar nan lafi……….
Bata karasa ba kawayen saudala suka shigo suna neman wajan buya,
Ku lafiyar ku kuwa ?
Hada baki sukayi suka ce iya kura
Ai tana jin haka itama ta saki butar fitsari na bin kafar ta ta shige daki ta kulle kofa ,
Saudala da taga shiru har yanzu baa shigo gidan sai ta fito daga dakin tana haki ,
Kawayen ta suma suka fito daga wajan buyar su suna zare ido ,
Tsohuwa ta bude kofar kadan tana fadin ” ke saude ina kurar an kamata ?
Saudala ta kyalkyale da dariya tace
” Kai iya kin cika tsoro , ba wata kura mu kadai ne
Fitowa tayi tana masifa
“Amma yaran nan anyi yan jakar uba , daman ba kura bace ta tsinke ,
Saudala tace ” lah iya fitsari kikayi a wando,
Cikin borin kunya tace ” ban sani ba, shegiya da kanta kamar albasa ,
Saulada tace “iya ni kike zagi ?
” eh na zage ki ko zaki rama
Murmushi saudala tanata kada kai ,
Kawayen ta suka tafi gida ita kuma tayi allawa dan lkcn sallar magariba ya kusa,
Da dare suna zaune a tsakar gida ana cin abinci,
Saulada tace “baba
Yace na’am
Tace ” kace duk Wanda ya zagi wani kansa ya zaga ko?
Yace ” kwarai kuwa , indai mutum ya zage ka karka rama dan kansa ya zaga
Tace ” kaga dazu da iya ta zage ni kenan kanta ta zaga ko?
Baba yayi shiru ya kasa magana, ya kalli iya da take kallan sa , ya juyo ya kalli saudala ita ta zuba mai ido,
Kawai sai yace ” saude tashi kije ki kwanta dare yayi ,
Tace ” baba baka bani amsata ba,
Yace ” zan fada miki sai gobe da safe ,
Tashi tayi ta shiga daki ,
Baba ya kalli iya yace ” haba iya ya zaki dinga zagin Yarinya karama,
Cikin masifa iya tace ” na zage ta din , ahmadu ka fita idona na rife ,
Ta mike ta shiga dakicigaba
Ummu ma tayi shiru , Dan tana magana iya cewa zatayi baa sonta a gidan ,
Da misalin karfe 12 na dare saudala ta tashi daga bacci,
Bakar doguwar riga ta saka , ta shafe fuskar ta da farar hoda , tayi zanen baki akai ,
Cikin sanda ta shiga dakin iya da take kwasar bacci,
Kafar iya ta jijjiga ,
Iya tana bude ido ta ganta a zaune akusa da ita ,
Cikin kakkausar murya saudala tace
“Kina yin ihu zan shanye miki jini ,
Iya tayi shiru jikin ta na rawa sai ga fitsari hade da tusa me wari.😂😂
🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_📚✍🏻
[❄Dance above the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
*STORY & WRITTEN*
*BY*
NEAT LADY✍🏻
_Last page din nayi mistake zan saka page 5&6 nasa 4&6 , dafatan kun gane_.
*Dedicated to humairah (innahoro)*😘😘
*Kiyi yadda kike so dashi my horo*😜
+
*Bismillahir rahmanir rahim.*
7&8
*CIGABAN LABARI.*
Iya ce zaune ta rafka uban tagumi tana tunanin aljana.
Saudala ta fito daga d’aki ta zauna kusa da Iya tace.
“Iya da zakaji shawara ta kar kije Abujan nan , dan yasin na tsani zuwa birnin nan yawan cinsu duk ‘yan iska ne , kuma duk inda kika je sai aljanar ta biyo ki , gwara ma kiyi zaman ki anan”
Iya tayi shiru tana sauraran Saudala har ta kai aya sannan Iya tace,
“Babu abinda zaisa na zauna a garin nan karkari na zuwa gobe “
Tana gama fad’ar hakan ta tashi ta shiga d’aki.
Saudala kam murna ce ta kamata aranta take cewa ahh to ai da sauƙi tinda zama ki kai goben.
Bayan sallar magariba Saudala da ‘kawayenta suka nufi dandali.
Tunda suka isa sukaga samari da ‘yan mata ana zance, wani saurayi da take jin haushinsa ta gani yana kwasar love abinsa.
Murmushi Saudala tayi dan har ta shirya muguntar da zatayi musu.
Gefe suka koma wajan da babu haske sosai , Saudala ta had’a musu plan d’in da zasuyi.
wani kare Saudala ta tsokano ai kam ya biyosu da gudu,
Dije da Talatu suna ganin haka suka nufi cikin dandalin Suna ihun “kura jama’a”
mutane na juyowa suka ga Saudala tana gudu abu yana binta a baya sai kowa yayi ta kansa.
Cikin gudu wani saurayi ya fad’a cikin kwata wandon sa ya cire amma bai tsaya gyara wando ba ya cigaba da gudu abinsa.😂
Me saida kifi kam tuni kifinsa ya zube cikin kwata 🤣.
haba me Saudala zatayi in ba dariya ba , ta dinga dariya kamar mahaukaciya sabowar kamu harda riƙe ciki.
Ihu ta fara tana cewa,
“Hoooooooooo ba kura bace kare ne kuma nina tsokano shi kuyi yadda zakuyi dani”
ta fad’a tana kwasa a guje ,
Aikam suka rufa mata baya tana gudu suna binta har ta ‘karasa gida.
Da gudu ta shige gida tana faman hakki.
Tunda Baba yaganta yasan tayi halin nata ns tsokana barima daya jiyo hayaniyar mutane a waje.
Ko kallanta baiyi ba ya tashi ya fita wajen,
Dayake kowa na ganin mutuncinsa a unguwa sai suka hakura suka koma.
A tsakar gida ya tadda su Baaba ya kalli Saudala yace,
” Wai yaushe zakiyi hankali ne Saude? Ace ke kullum cikin tsokanar mutane kike , yaushe zakiyi hankali ne ?”
Iya ta kar’be zancen da fad’in,
STORY CONTINUES BELOW

“yo aishi yasa mutane ke fad’ar Yarinya kamar aljana, ita kenan kullum a cikin kawo ‘kararta ake”
Cikin bacin rai Saudala tace,
“Nice me kama da aljana Iya ?”
Iya tace, ” eh mana ko zaki dake nine ?”
Saudala tace, ” ba duka ba zagi amma hmm……”
Ta fad’a tana shigewa d’aki tana ƙwafa.
Iya kuwa sai bala’i take.
Dare mahutar bawa inji hausawa, kowa yana ta bacci a cikin gidan amma banda Saudala.
Shiri take cikin ba’kar riga wacce tsahonta da fad’inta yayi mata yawa.
Kamar yadda tayi waccan kwalliyar haka tayi wannan cikin sand’a ta fito daga d’akinta ta shiga na Iya.
Iya kam dama da ‘kyar bacci ya d’auketa sbd tsoron aljanar jiya, cikin bacci taji ana yi mata tafiyar tsutsa a kafa.
Firgigit ta tashi zaune tana zare ido.
Saudala kam ta wani zaro harshe tana zare ido.
Cikin wata irin murya ta fara cewa,
” Wato dana ce karki fad’awa kowa nazo wajanki jiya shine kika fad’a ko , to bara kiji bazan ta’ba ha’kuri ba ko kin bani ha’kuri yau babu abinda zai hana na shanye miki jini”,
“shine ke harda su yadda cewa zaki koma Abuja ko? to bara kiji ko kin koma can saina biyo ki”
Hannu tasa ta ri’ke hannun iya da karfi .
Iya kam banda kuka babu abinda take.
Cikin kukan tace,
“Dan Allah Baaba aljana kiyi haƙuri alkur’an bazan ‘kara fad’awa wani ba , dan Allah karki shanye min jini Dan Allah”
Saudala ta ‘kyal’kyale da wata irin dariya sannan tace,
“Oho miki dai indai kika ‘kara fad’awa wani babu abinda zaisa naki shanye miki jini”
Cikin kuka Iya tace ” bazanma fad’a ba kiyi hakuri Baaba aljana”
Cikin tsawa Saudala tace,
“rife idon ki”
da sauri kuwa Iya rife idonta,
Fit Saudala ta fice tana dariya.
Iya kam yadda taga dare haka taga rana, banda kuka babu abinda takeyi.
Washe gari ma haka Iya ta fito jikinta duk kashi.
aikam Saudala tana ganinta ta tafara cewa,
” Haba iya yanzu ke kullum sai kinyi kashin kwance , ni wallahi abin nan naki ya fara isata ki ta cika mana gida da wari”
Iya kam banda zubar hawaye babu abinda takeyi , band’aki ta shiga tabar Saudala tana masifa.
Ficewa Saudala tayi daga gidan tana dariya ,
Tana fita ta nufi shagon Iliya me kayan awo.
Tana zuwa ta gaishe shi tace,
” iliya dan Allah ka bani aya naci”
Cikin fara’a iliya yace ” koke fa Saude da haka kikeyi ai da ba wanda zaiyi kuka dake , bara na debo miki ayar kici”
Murmushi tayi tace, ” to Baba iliya”
Ai yana shiga ciki ta d’au ruwan butar da yake ajiye ta zuba mai a cikin fulawa , sannan ta d’ibi ‘kasa ta zuba cikin gari masara.
Yana fitowa ya ganta tanayi masa dariya.
Yace, ” lafiya ?”
Tace , ” ka fara bud’a fulawar ka da garin masarar ka sannan kayi magana , tana gama fad’ar hakan ta kwasa da gudu”
STORY CONTINUES BELOW

Tana cikin gudu taga wani abinda take so , cikin sauri ta shiga cikin dajin ta d’ebo a leda ta soke a jikin zanin ta.
Tana cikin tafiya ta gano saurayin jiya na dandali yauma shida budurwarsa da alama zance suke.
A ranta tace, ” wato bai daddara da abinda nayi masa jiya ba shine yauma ya kuma dawowa zance , zaka ci ubanka yau”
Murmushi tayi cikin sand’a tabi ta bayansu ta bud’e abinda ta d’ebo a cikin daji a hankali ta zazzage masa a baya.
Juyowa yayi ya ganta a tsaye tana jirgiza jiki,
Kafin kace me tuni sauyarin ya fara susa yana ihu.
Saudala tace, ” gobe ma ka ‘kara gaya min magana”
ta fad’a tana juyawa a guje.
Saurayin kam banda birgima babu abinda yake yana ihu ,
Budurwarsa kuwa cikin gari tayi tana neman taimako.
Lkcn data samo mutane suna zuwa suka ga yayi tsirara yana Susa ,😂
Mutane ne suka taimaka suka dauke shi daga wajan aka shiga dashi wani gida.
Saudala kam koda ta koma gida Iya ta tarar tana sharar kwalla.
Saudala ta kalle ta tace,
” Iya wai kashin kwance dad’ine dashi ne naga kullum sai kinyi ?”
Iya tayi mata banza.
Saudala ta cigaba da fad’in,
“Koni Yarinya ba zanyi kashin kwance ba balle ke tsohuwa, to a dinga miki nafkin mana dan gaskiya zaki lalata mana gida da wari 😂”
Umma tace, ” tashi ki bamu waje Saude”
Tashi tayi ta shiga d’aki bata wani jima ba sai gata ta fito da leda da kuma tsumma.
Baba ta mi’kawa shi kuna yace da ita, ” ke meye wannan?”
Tace , ” nafkin ne da za’a dinga sawa iya dan gaskiya kashin kwancen ta yayi yawa 🤭”
Baba ne ya daka mata tsawa cikin sauri tabar wajan.
Da’kyar aka rarrashi Iya tayi shiru , haka dai suka yanke shawarar zata tafi Abuja washe gari.
*GARIN ABUJA.*
Comment & Share
Neat lady ✍🏻
🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
🇳🇬®
*_ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION📚✍🏽_*
[❄Dance above the surface of the world. Let your thoughts lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
Story & written
By
NEAT LADY ✍🏻
Dedicated to *MISS XERKS*😘😘
Bismillahir rahmanir rahim
4&6
Kusa da malam habu ta karasa tana zuwa tace
” Na tsinki mangwaro a cikin gonar nan me ka isa kayi ,ta fada tana murguda baki
Malam Habu ransa ya baci , yace
“Kiyi min sata sannan kizo gabana kina fada min,
Tace “An fada din kayi duk abinda zakayi ,
Ta fada tana kwasa a guje
shima ya rifa mata baya
Amfanin gonar ta dinga takewa tana wucewa ,
Ran malam habu ya kuma baci ,
STORY CONTINUES BELOW

Gudu take yana binta wani kofar gida tazo me malalen siminti sai sheki yake ,
robar da tasoke a kasan rigar ta ta dauko ta dinga zubawa a wajan , tana gamawa ta mayar da robar ,
Da gudu malam habu yazo wajan ai yana takawa ji kake timmmmmmm ya fadi kasa ,
Me saudala zatayi in ba dariya ba ta rike ciki tana dariya kamar mahaukaciya
Malam habu da kafarsa take masa zugi cikin bakin ciki yake kallan ta ,
Yace ” yanzu saude kuka kika zuba min dan na fadi ?
Cikin dariya tace ” Gobe ma ka kuma zagina , asha jinya lafiya,
Tajuya tayi tafiyar ta,
Mutane ne suka taimakawa mlm habu aka kai shi gida
Tafiya take tana dariya ta hango wasu mata yan birni da alama bakine a garin ,
Wajan su ta nufa tana zuwa tace
“Ku kuma daga ina ?
Daya daga cikin su
tace ” what is you’re name ?
Kutumelesy ni matar nan zata zaga da turanci ta zata ban iya ba,
Saudala tace ” da zaki zage ni da turanci an fada miki nima ban iya bane ,
banza junuary February kawai in kin isa ki rama aljana kawai ,
Tafiya take tana tunani lallai ta fadawa yan matan nan magana tunda suka kasa amsawa har ta shiga gida tana tunani,
Tana shiga tayi tozali da iya a zaune tayi tagumi ,
Kyalkyalewa tayi da dariya harda kwanciya ,
Cikin dariya tace ” wa aka samu ya wanke miki kashin , gsky kin iya kashi me wari kamar na saniya
Iya me kashin kwance sannu da kashi.
Umma ce ta daka mata tsawa tace
” ke saude iyan kikewa wannan dariyar dan baki da mutunci eyee ,
Umma nifa ba iya nakewa dariya ba kashin tane yake bani dariya , duk kauyen nan babu Wanda ya kaita yin kashi me wari , da ace zaayi gasar waddan da suka iya kashi to da iyace zata zo ta daya
Cikin b’acin rai baba yace
“Ko kiyi min shiru ko nazo na bige bakin ki ,
Iya tace ” Ku k’yaleta yau din nan zana bar gidan dan bazan iya zama aljanu suna tsorata ni ba,
Kafin wani yayi magana saudala tace
” hmmm iya kenan ai duk inda kikaje sai sun biyoki , balle ma duk sunji abinda kike cewa ai shikenan iya har abujan zasu biyo ki,
Iya ta fashe da kuka sosai don ta harda da abinda saudala ta fada ,
Saudala kam abin nema ya samu dariya take kamar me ,
Saida ta gaji dan kanta sannan ta mike ta shiga daki a ranta tana gwada muguntar da zata yiwa iya yau.
WACCE SAUDALA?
Saudala ‘yace wajan malam Ahmadu,
Fulani ne irin kyawawan nan ,suna zaune a garin Adamawa dake Nigeria,
Saudala tun tana karama bata jin magana akwai ta da tsokana , ta gagari yan rugar su gabadaya domin duk girman ka ka shiga harkar ta to sai ta rama , ita kadai Allah ya bawa malam Ahmadu da hafsatu wato umma,
Yarinya ce kyakykyawa sosai fara tas komai Allah ya bata dai² ita ,
Malam Ahmadu daya ne daga cikin masu kudin kauyen Dan Allah ya bashi nasibin noma ,
STORY CONTINUES BELOW

Iya itace mahaifiyar malam Ahmadu su biyu ta haifa a duniya daga yayan sa wato alhaji umar sai shi ,
Alhaji umar me kudi ne sosai yana zaune a garin abuja, babu yadda baiba malam Ahmadu ya dawo abuja amma yaki yace yafi son zaman kauye, iya ma tace tafi son zaman kauyen saidai suje abuja da ziyara ko su suzo,
Alhaji umar yana da mata guda daya wato halima wacce ake cewa mama, yana da ‘ya’ya gudu biyu namiji da mace daya,
Wannan kenan
Cigaban labari
_Kuyi manage da wannan kaina ke min ciwo_🤦🏼♀🤦🏼♀🤦🏼♀🤦🏼♀
Comment & share
Neat lady ✍🏻
🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_📚✍🏻
[❄Dance above the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏻
*Bismillahir rahmanir rahim*
9 &10
Zaune suke akan dining suna cin abinci,
Parlour ne na alfarma kana ganin parlourn kasan an zuba dukiya .
Wata buduwace tace
“Abba wai yaushe zamuje Adamawa ne?, Wallahi nayi missing kakus da uncle?.”
Wanda aka kira da Abba ne ya d’ago kamar su d’aya da baban Saudala yayi murmushi yace.
“Abinda yake raina kenan Fadila nima ina son naje mu gaisa dasu iya wallahi.
Ya k’are maganar yana murmushi.
Mama ce tace.
“Ai kam ya kamata muje mun dad’e bamuje ba.
Abba yace. “Da tunanin da nake mu bari sai Abdurrahman ya dawo sai muje gaba d’aya tunda ya kusa dawowa”.
Cikin shagwab’a Fadila tace.
“Ni dai muje gobe in yaso in yaya Abdul ya dawo sai mu kuma komawa please Abba”.
Mama tace.
“Hakan yayi dai _dai”.
Abba ne yace.
” To Allah ya kaimu goben sai muje ko k’wana biyu ne, sai mu dawo”.
Fadila ta dinga murna zata je k’auye tun a lokacin ta fara had’a kayanta.
******************
Iliya da yaga b’arnar da Saudala tayi masa hakan yasa ya d’auko k’afa yazo wajan Baba ya sanar dashi komai.
Hak’uri Baba ya dinga bashi sannan ya d’auko buhun masara ya bashi.
Iliya kam murna ba’a magana ya dinga godiya yana tunanin gwara da Saudala tayi masa b’arna.
Bayan Baba ya shiga gida Saudala ya dinga yiwa fad’a, Saudala kam tayi shiru kamar ba ita ba amma a ranta cewa take zaka gane kuran ka Iliya
Yau dai Saudala ta bar iya ta huta bata tsorata taba saboda bata son ta tafi.
Washe gari Saudala ta shirya cikin kayan su na Fulani farare sunyi mata kyau, fita tayi daga gidan kan bishiyar k’ofar gidansu ta hau ta zauna tana kallan masu wucewa.
STORY CONTINUES BELOW

Mota Saudala ta gani me kyau ta tsaya a kofar gidan nasu.
Tana ganin mutanen da suka fito tayi tsaki tace.
“Wad’annan ‘yan birnin sunzo zasu fara zagin mu da turanci , ko da yake ai nima na iya turancin,suna zagina zan rama eheee.
Bayan bakin sun shiga gidan Saudala ta gano iliya me shago zai wuce , cikin sauri ta diro daga kan bishiyar ta tsaya a gabansa tace.
” To iliya wato shine kazo ka fad’awa Baba wai na bata maka kaya ko , to bara kaji tunda ka fad’a sai nayi maka abinda yafi wannan”.
Tana gama fad’ar hakan tayi shigewar ta cikin gida.
Tana shiga taga bak’in a zaune ana ta hira da dariyam
Abba ne yayi magana yace.
” Saudatu zo mana mu gaisa”.
Yayi maganar lokacin yana nuna mata tazo kusa dashi ta zauna.
Zuwa tayi ta gaishe su.
Fadila ce tace.
” Haba my sis baki ganni bane ko bakiyi missing d’ina ba?.
Da murmushi a fuskar Fadila take mata magana.
Bakin Saudala a bud’e tana kallonta sannan😲 tace
“Iyan kinga ta zagen da turanci, daban Allah yasa naji me kika ce ba da shikenan kin zagi iya ko”.
Ai iya tana jin haka cikin masifa tace.
“Yanzu yar nan ni kika zaga iyee ,
Haba me Fadila zatayi inba dariya ba 😂 ta dinga dariya hadda kwanciya.
Iya kuluwa Iya ta kulu cikin fada tace.
“Au dariya kike min to bada ni kike ba da iyayen ki kike gasu nan a zaune.
Lokacin da Iya take nuna su Baba.
Cikin dariya Fadila tace
“Nifa ba zagin ki nayi ba , ce mata nayi batayi kewata bane”.
Iya ce tace.
“Amma Saude anyi banza ashe abinda tace kenan kikace ta zageni .
Saudala tace .
“Iya nice banzar ?”.
Ta k’arasa maganar tana gyad’a kanta.
Iya ce tace.
“Eh kece d’in ko zaki rama ne?”.
K’wafa Saudala tayi ta juyar da kai”.
mikewa iya tayi ta shiga ban d’aki.
Ai Saudala na ganin iya ta shiga ban d’aki ta mike tayi wajan ban d’akin kamar ruwa zata debo.
Hira suka cigaba dayi suna dariya ,
Ihun Saudala suka jiyo daga bakin ban d’akin, ai da gudu suka karasa.
Cikin sauri Abba ya tambaye ta lafiya , cikin kuka tace.
“K’adangare na gani ya shiga ban d’akin kuma Iya tsoran sa take.
Iya dake ban d’aki taji an ambaci k’adangare sai ta fasa ihu a cikin ban d’akin tana tsalle.
Da gudu ta fito daga ban d’akin ko tsarki taba yiba tana tuntube ta shiga shiga d’aki ta kulle k’ofa.
Saudala ta rik’e ciki tana dariya sosai😂😂
Cikin dariyar tace.
” Baba iya fa ko tsarki batayi ba naga hannun ta duk kashi.🤣🤣
Ta sake kyalkyalewa da dariya.
Ta tsagaita dariyar tace.
” Baba ku k’ira iya ta fito tayi tsarki k’arya nake babu wani k’adangare , itace ta cemin banza ni kuma na rama yanzu.
STORY CONTINUES BELOW

Duk dariyar da Fadila take ‘buyewa sai da ta fito.
Baba ne ya daka musu tsawa yace
“Saude wai meyasa kika raina iya ne ?
Tace ” yasin Baba ba rainata nayi ba kawai ina rama abinda tayi min ne.
Abba yayi murmushi dan shima Saudala ta bashi dariya kawai dannewa yayi.
Baba yayi tsaki ya nufi d’akin da iya ta shiga .
_*Kuyi hakuri da wannan ina busy ne*🤦🏻♀_
Ina yinku masoyana😘🥰
Comment & Share
Neat lady✍🏻✍🏻
🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_
📚✍🏼
[❄Dance above the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Bismillahir rahmanir rahim*
11&12
D’akin Baba ya shiga ya ganta a lab’e a bayan k’ofa, hannun ta ya rik’o suka fito , iya kam fad’i take.
“An fito da k’adangare?”.
Baba yace. ” Iya babu wani k’adangare a band’akin nan , k’arya Saude tayi miki babu wani k’adangare da ya shiga ciki.
Juyowa iya tayi ta kalli Saudala sannan ta juyar da Kai , tafiya take kamar zata shiga d’aki kawai kaga ta d’auko tab’arya ta nufu Saudala da gudu.
Ai Saudala tana ganin ta ta k’wasa a guje tayi waje tana faman dariya .
Fadila kam kwanciya tayi a wajan tana k’yalk’yala dariya.
Fadila tace ” Shiyasa nake so nazo garin nan dan nasan zanci dariya , gaskiya dramar iya da Saudat na birgeni wallahi”.
Hararar ta iya tayi tace.
“Au Fadila ina yabanki sallah sai ki kasa alwala, kema wannan yaron me k’atan kai ya koya miki ko?”.
Fadila ta tsayar da dariyar tace.
” Yi hak’uri iya ni bada ke nakewa dariya ba Saude ce ta bani dariya, kuma in munyi waya da yaya Abdul zan fad’a masa kince masa me k’atan kai kinga sai ya fasa auran naki .”
Tsaki iya tace.
“Yo ki fad’a mana tsoronsa nake ji , ni daman na fasa auran nasa haba mutum sai miskilancin tsiya , ta fad’a ta shigewa ban d’aki”.
Bayan iya ta fito suka zauna suna ta hira.
Wani yarone yayi sallama ya shigo gidan yana kuka.
Iya tace.
“D’an nan lafiya ?”.
Cikin kuka yaron yace.
“Ina cikin tafiya na d’auko markad’en awara kawai sai Saude ta tankad’ani na fad’i, markad’en ya zube , koma ban kar na dibi na saman ta d’ebo k’asa ta zuba akai , dana tambaye ta menayi mata sai tace wai na fad’awa babana iliya ta zubar din, kuma wallahi dukana babana zaiyi .”
Kafin suyi magana Saudala ta shigo tana fad’in.
” Au k’ara ta ka kawo dan baka da kunya , na b’arar d’in kaje ka fad’awa Iliya yazo ya kuma maula a wajan Babana”.
STORY CONTINUES BELOW

Tana gama fad’ar hakan ta nufi da’ki abinta .
Abba ne ya bawa yaron hak’uri sannan ya d’auko kud’i ya bashi , yaron ya tafi gida .
Iya ce tace.
“An kawo kara ta farko kenan saura guda tara”.
Mama tace.
“Au sau goma ake kawo karar ta iya ?”.
Umma tace.
“Ko sama da goman ba”.
Fadila tace .
“Tab amma Saudat akwai tsokana”.
Fitowa Saudala tayi da’ki ta nemi waje ta zauna.
Abba ne yace.
” Ya ta zo mana”.
Kusa dashi Saudala ta zauna.
Abba yace.
“Meyasa kike tsokanar mutane uhumm?”.
Saudala tace.
” Ni fa ba tsokanar su nake ba sune suke shiga harkata”.
Abba yace.
” To ki daina fad’a kinji”.
Saudala tace.
“Tab ai ina daina fad’a zasu raina ni”.
Abba yace .
“To naji amma kinsan fad’a babu kyau ko?”.
Saudala tace.
” Abba zagi ma babu kyau ko?”.
Yace. ” Tabbas zagi babu kyau , duk wanda ya zage ki karki rama kansa ya zaga”.
Saudala tace. ” Kaga d’azu da iya ta zage ni kanta ta zaga shiyasa ma ban rama ba”.
Cikin sauri Abba ya kauda da zancen yace .
“Aji nawa kike a makaranta?”.
Tace .” Ajina uku a islamiyya”.
Abba yace ” boko fa?”.
Tace. “Ba Baba ne yace na daina zuwa ba”.
Abba ya kalli Baba yace.
“Meyasa ta daina zuwa ?”.
Baba yace. ” Tunda ta shiga makarantar kullum sai ankawo karar ta , yau ace ta fasawa wani kai, gobe ace ta zubawa malami karara , kullum da abinda zatayi suka gaji suka Kore ta”.
Abba ya kalle ta yace.
” Meyasa?”.
Tace. ” Kwarankwasi su suke tsokanata”.
Abba ne yace. ” Ki na son zuwa makarantar boko?”.
Cikin sauri tace. “Eh wallahi Abba inaso kodan na iya turanci ma”.
Murmushi Abba yayi yace.
” Insha Allah zan saka ki a makaranta kinji”.
Cikin farin ciki tace. “To Abba an gode”.
Umma ce tace. ” Waini ina Abdurrahman ne ?”.
Fadila tace. ” Kinsan aikin soja sai a slow yana can garin Ibadan suna wani taron sojoji”.
Bud’e baki Saudala tayi tace.
“Tab kice mugune dan duk wani soja mugune shiyasa suke bani haushi”.
Dariya sukayi gaba d’ayansu.
Iya ce tace. “Nikam yanzu me k’atan kai yayi shekaru 30 kuwa ?”.
Abba ne yace. “Tab Iya naki wasane to har ya k’ara d’aya akai, Fadila kuma yanzu take 19”.
Iya tace.”Amma shine har yanzu bakuyi musu aure ba ?”.
Baba yace. ” A’a ai shi Abdul yana dawowa zamuje nema masa aure dan ya sanar dani a waya ya samu wacce yake so”.
Iya tace .” Yanzu naji magana ai gwara yayi auren ya huta da tuzuranci”.
Dariya sukaji Saudala ta nayi , suka kalle da alamar tambaya,
Tace. ” wallahi ina tausayawa matar sojan nan dan nasan zata sha mugunta a wajen shi”.
Dariya tabasu gaba d’ayansu suka dara .
Da daddare Abba da Baba suka fita waje dan akwai maganar da zasuyi akan karatun Saudala.
[8/16, 15:43] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_📚✍🏼
[❄Dance above the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
+
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Dedicated to ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*😘😘
_Happy sallah💃🏻💃🏻 da fatan anyi sallah lafiya , Allah ya maimaita mana._😍😍😍😍😍
*Bismillahir rahmanir rahim*
15&16
Tafiya suke cikin tuk’in nutsuwa , tun Saudala na kalle_kalle har tayi bacci.
***
B’angaren Baba kuwa tunda ya koma gida yaga gidan yayi masa fad’i, don har cikin xuciyar sa bai so tafiyar taba amma ganin karatu ya kaita yasa ya hak’ura .
Umma ma kanta ganin gidan take wani iri , amma saboda kawaici da kunya na Fulani sai tayi shiru bata furta ba .
****
Shigar su garin Abuja Saudala ta farka, shiru tayi kamar babu ita a cikin motar.
Da yake magrib ta gabato hakan yasa suka tadda check point a kan haryar da zata kai su bila road.
Tsayawa sukayi har aka zo kansu .
Sojan ne ya nemi a bud’e masa boot d’in motar.
Da yake sojan sun saba da Abba,
Bayan ya gama dubawa yazo suka gaisa da Abba ya lek’o baya don su gaisa da mama.
Ai yana lek’o wa Saudala ta k’yalk’yale da dariya, tana nuna sojan da yatsa, tac igaba da dariya.😂😂
Abba ne yayi mata magana yace.
” ke Saudat dariyar me kike yi?”.
Kafin ta ta bashi amsa ta kuma kallan sojan da ya zuba mata ido cikin b’acin rai, yace mata
“What are u laughing?,
Are u in sense?”.
Yana nunata da yatsa
Turancin sa ya k’ara bata dariya , don ko ba’a fad’a ba tasan zaginta yayi(A fad’ar ta fa.😂)
Abba ne cikin b’acin rai ya daka mata tsawa yace.
“Wai baraki daina wannan dariyar ba”?.
Cikin dariya tace.
” Abba ganin idon sa nayi ja kamar wani dodo , yasin wannan kana ganin sa kasan yana shan giya ga wani k’aton tumbi kamar me ciki wata tara amma dai buhun shinkafa a kwana uku kake cinyewa ko? ta kara shekewa da dariya”.🤣
Banda huci 😡babu abinda sojan yake dan yana jin hausa kad’an.
Abba ne ya dinga bashi hakuri da k’yar ya hak’ura ya koma wajan aikin sa, suka ja motar suka yi gaba.
Tunda suka isa k’ofar gate d’in gidan Saudala ta fara baza ido tana kallo gidan.
Mai gadi ne ya bud’e musu suka shiga.
Kowa ya fito daga mota banda Saudala da take faman hawaye.
Fadila ta kalle ta tace.
“Saudat ki fito mu shiga gida mana.
STORY CONTINUES BELOW

Cikin kuka tace.
“Na fasa iya turanci dan Allah ku mai dani wajan Baba dan Allah”.
Wani saban kuka ta kuma fashewa dashi
Abba ne ya zagayo ya rik’e mata hannu, tamnbayarta ya fara yi yace mata.
“Meya faru Saudat ?,wani Abu aka yi miki?”.
Cikin kuka tace.
” Gani nayi kun kawo ni gidan yankan kai”.
Me Fadila zatayi in ba dariya ba,ta dinga k’yalk’yalawa hadda su rik’e ciki.
Abba ne yayi murmushi sannan yayi mata tamyace mata
“Saudat Babanki na Adamawa zai iya siyar dake?”.
Cikin kuka ta girgiza masa kai, alamar a’a.
Yace mata. ” Saboda me?”.
Amsa ta bashi. Saboda shine Baba na”.
Sake tambayarta yayi yace mata. ” Ni kuma menene a wajan ki ?”.
Tace. “Abba na”.
Ce mata yayi.
“Amma kike cewa zan yanke miki kai , nima fa Baban kine ko kin manta ne?”.
Ta girgiza masa kai
Yace mata.
” To ki k’wantar da hankalin ki babu abinda zai same ki kinji ko”.
Ta d’aga kai alamun eh
Abba ya rik’o hannun ta suka shiga parlourn.
*Banyi niyar yin typing yau ba gaskiya, amma yadda kuka dinga bina ta prvt kuna yi min magiya hakan yasa nayi muku wannan.*💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻😍
*Sai dai kuyi manage dashi babu yawa*🤦🏻♀
Comment & Share
Neat Lady✍🏼
[8/16, 15:43] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_📚✍🏼
[❄Dance above the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Dedicated to my fan’s*💃🏻💃🏻💃🏻
*Especially:*
*Pretty Aseesher*😻
*Mmn Khaleed*🥰
*Mmn Haneef*😘
*Mmn Adnan*😍
*Inna horo*🥴
*Wasila*💙
*Rasida*💖
*Zee*💖
*Mmn Zahra*🥰
*Wannan page din na kune kuyi yadda kuke so dashi.*💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻❤❤❤❤❤
*Bismillahir rahmanir rahim*
17&18
Tunda suka shiga parlourn Saudala take kallon sa.
Mama ce tace.
“Saudat mu shiga na kaiki d’akin naki kike so ko zaki zauna tare da Fadila?”.
Cikin sanyi murya tace.
“Zan zauna da Fadilan”.
Mama ce .
“Fadila rik’e ta ku tafi d’akin, tayi wanka ta shirya.
STORY CONTINUES BELOW

Hannun ta Fadila ta rik’e suka tafi d’akin.
Iya ma d’akin da take sauka idan tazo ta nufa ta shiga wanka.
Tunda suka shiga d’akin Saudala ta nemi waje ta zauna tayi tagumi.
Fadila ce ta rik’o hannun ta tace.
” Sis tashi muje kiyi wanka”.
B’ata rai Saudala tayi tace.
“Ke zaki yi min wankan ko me?”.
Murmushi Fadila tayi tace.
“A’a zan nuna miki yadda kayan band’akin yake ne”.
Mik’ewa Saudala tayi ta shiga toilet d’in, Fadila ce ta bita ta nuna mata komai sannan ta fito .
Koda ta fito daga wanka Fadila ta fita daga d’akin, shiryawa tayi sannan ta rama sallolin da ake binta.
Bayan sun ci abinci kowa yaje ya kwanta .
Tunda Saudala ta k’wanta take juyi gaba d’aya kewar iyayen ta take , ji take ina ma bata zo ba a haka har bacci ya d’auke ta .
Tunda sukayi sallar asuba Saudala ta kasa komawa, wanka ta shiga tayi,shiryawa tayi cikin blue d’in kayan su na Fulani, parlour ta fito taga Mama a cikin kitchen tana had’a break fast.
Shiga kitchen d’in tayi tace.
” Mama ina kwana”.
Juyowa Mama tayi fuskar ta d’auke da murmushi tace.
“Lafiya lau, Saudat har kin tashi?”.
Saudala tace.
” Na kasa komawa baccin shiyasa na fito na taya ki aiki”.
Mama tace. “A’a bakomai ki huta ba sai kin taya ni ba kinji”.
Saudala tace. “A’a Mama zan taya ki nima ina so na iya dafa irin abincin ku”.
Murmushi Mama tayi sannan tace.
” To shikenan d’auko dankalin can na nuna miki yadda zaki yanka “.
Bayan sun gama had’a break fast suka jera akan dining.
Komawa Saudala tayi cikin kitchen d’in ta gyara inda aka b’ata dan Saudala ba dai tsafta ba,bayan ta gama ta fito ta koma d’akin su .
Abba ne ya sauko daga sama shida Mama, zama sukayi akan dining.
Fadila da Saudala suka fito suka zauna suma , cikin girmamawa Saudala tace.
“Abba ina kwana “.
Da murmushi a fuskarsa sannan yace.
“lafiya lau yar gidan Abba da Baba kin tashi lafiya?.
Tace. “Lafiya lau “.
Yace. ” Masha Allah “.
Saudala tace.
” Wai ni ina iya ne ?.
Abba yace ” yanzu zaki gan……..
Kafin ya rufe baki sai gata ta shigo tana b’allar goro.
Akan kujera ta zauna dan ita bata hawa dining.
Abba ne ya tashi yaje ya durk’usa har k’asa yace.
“Iya barka da asuba “.
Iya ta washe baki tace.
“An tashi lafiya dai ko?.”
Yace.
“Lafiya lau , d’azu na shiga kina bacci”.
Tace “eh yau na dad’e ban farka ba”.
Mama tace. ” Iya an tashi lafiya? “.
Iya tace. ” Lafiya lau halimatu “.
STORY CONTINUES BELOW

Saudala tace .” Iya ina kwana “.
Juyowa tayi ta harari Saudala sannan tace
” lafiya ” ta fad’a tabe baki tayi.
Murmushi Saudala tayi ta girgiza kai kawai.
Fadila tace. ” Morning kakus”.
Ciki masifa tace ” ke kika san inda zaki sami motar bani zaki tambaya ba.
Cikin dariya Fadila tace.
“Nifa ba mota nace miki ba cewa nayi ina kwana”.
Tsaki iya tayi tace.
“Saude mik’o min nawa shayin”.
Murmushi mugunta Saudala tayi sannan tace.
“To Iya”.
Had’a mata shayin tayi sannan ta mik’e ta kai mata.
Tunda Iya takai kofin bakin ta Saudala take murmushi.
Ai iya na zubawa a bakin ta ta saki wata kara.
Cikin sauri Abba yazo kusa ita yana fad’in
” lafiya Iya”?.
mata Shayin bakin ta ta dawo dashi tana fifita baki.
Fuska d’auke da murmushi Saudala tace .
“Abba ni na zuba mata gishiri a maimakon sugar ,sannan ban bari shayin ya huce ba na kawo mata “.
Ta cigaba da fad’in
“Abinda yasa nayi mata haka dana gaishe ta kafin ta amsa min sai da ta harare ni ramuwar hararar da tayi min kenan”.
Tana gama fad’in haka ta juya ta bar wajan .
Cikin masifa Iya tace.
“Bani kika yiwa ba iyayen ki kika yiwa ummaru da Ahmadu ,
Ko kallan ta Saudala bayi ba tayi shigewar ta da’ki,
Wani shayen Abba ya had’o mata da k’yar aka samu tasha tana gama sha ta koma da’kin ta.
Da rana ma Saudala tare suka dafa lunch ita da Fadila,
Suna zaune ana cin abinci banda harara babu abinda iya takewa Saudala,
Saudala kam sarai ta ganta amma ta basar kamar bata ganta ba.
Abba ne ya d’auko waya ya kira Baba.
Bayan sun gaisa dasu iya Abba ya bawa Saudala wayar.
Cikin sauri ta karb’a suka gaisa da Baba cikin harshen fullanci.
Bayan sun gama wayar kiran Abdulrahman ya shigo.
D’auka Abba yayi bayan sun gaisa aka bawa Mama suka gaisa ,
Fadila ma ta karbi wayar cikin shagwaba tace.
“Bro yaushe zaka dawo?, kasan fa nayi missing dinka”.
Daga daya b’angaren yace
“Sorry my sister insha Allah zan dawo very soon kinji”.
Tace. ” Zuwa nan da yaushe zaka dawo? “.
Yace. ” Insha Allah cikin week d’in nan zaku ganni”.
Cikin farin ciki tace
“Allah ya kaimu”
Yace “Ameen”
Saudala ta mik’awa wayar tace.
“Ku gaisa da Yaya Abdul”.
Hannu tasa ta karb’a ta kara wayar a kunne tace
“Ina huni”
Gabansa ne ya fadi jin wata murya me dadi yana gaida shi ,
STORY CONTINUES BELOW

Shiru yayi Saudala ta kara fad’in
“Ina huni”
Jin anyi shiru sai ajiyar xuciya da aka yi ,abin ya bata haushi tayi tsaki ta mikawa Fadila wayar,
Fadila tace
“Bye bro”
Ta fad’a tana kashe wayar.
Saudala kam a ran ta fad’i take.
“Wato wannan mutumin dan wulakanci ina gaishe shima yaki amsawa , to ya kori gaba”.
Tashi tayi ta nufi daki.
Bangaren Abdul kuwa………
Comment & Share
Neat Lady✍🏼
[8/16, 15:43] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_
📚✍🏼
[❄Dance above the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Dedicated to all my fan’s*😍😍
*bismillahir rahmanir rahim*
13&14
Abba ya kalli Baba yace
“Ahmad wace shawara ka yanke game da karatun Saudat?”
Baba yace ” gaskiya ban yanke komai ba , dan duk makarantun kauyen nan babu makarantar da basu san wacece Saude ba .”
Abba yace ” to kana nufin haka za’a ba’rta babu karatu ? Kuma gashi Yarinyar tana son yin karatun.”
Ajiyar xuciya Baba yayi sannan yace
” Ni kaina inason tayi karatun, amma halin Saude yafi karfin shekarunta .”
Abba yace ” to inda wata shawara in zaka yarda .”
Baba yace ” me zai hana na yarda , inaji.”
Abba yace ” me zai hana na dauke ta mu tafi da ita can Abuja tayi karatun?”
Baba yayi shiru dan gaskiya yana kaunar diyar sa , amma babu yadda zaiyi neman ilimi zata tafi.
Ganin yayi shiru sai Abba yace
“In kaga hakan da takura a kya’leta kawai, sai a nemo wata anan.”
Murmushi Baba yayi yace
“Kana damar yankewa Saude hukunci , dan matsayin mahaifin kake a wajan ta , na amince ku tafi can din .”
Abba yace ” Ai ba ita kadai ba har kai wannan karan tare zamu tafi , gwara mu koma can gabadaya family dinmu.”
Murmushi Baba yayi yace
“Hamma umar ka takura sai na koma Abuja , ni kuma na fisan zaman nan .”
Abba ya mike yana fadin
“Nidai na fad’a maka” , ya fad’a yana shigewariyar sa , amma babu yadda zaiyi neman ilimi zata tafi.
Ganin yayi shiru sai Abba yace
“In kaga hakan da takura a kya’leta kawai, sai a nemo wata anan.”
Murmushi Baba yayi yace
“Kana damar yankewa Saude hukunci , dan matsayin mahaifin kake a wajan ta , na amince ku tafi can d’in .”
STORY CONTINUES BELOW

Abba yace ” Ai ba ita kad’ai ba har kai wannan karan tare zamu tafi , gwara mu koma can gaba d’aya family d’inmu.”
Murmushi Baba yayi yace
“Hamma umar ka takura sai na koma Abuja , ni kuma na fisan zaman nan .”
Abba ya mike yana fad’in
“Nidai na fad’a maka” , ya fad’a yana shigewa cikin gidan.
Baba da yake jin k’aunar dan uwansa na ratsa shi , kawai sai yayi murmushi ya biyo bayan sa .
Suna shiga suka tadda Saude tasa iya a gaba tana fama shek:a mata dariya,
Ai Saudala tana ganin su Baba tace
“Baba iya tunanin dan tsohon mijinta takeyi da ya mutu ya barta .”
Ai tana fad’ar hakan iya sai hawaye ,
Ai kam Saudala an samu abinda ake so , tace
“Allah sarki iya hadda hawayen Soyayya,” ta fada tana shek’a dariya.
Abba yace ” yanzu Saudat baban namu shine tsoho ?”
Saudala tayi murmushi tana kallan iya.
Abba yace ” Daman akwai maganar da nake son muyi gabadayan mu.”
Iya tace ” Muna jinka “
Abba yace ” Game da karatun Saudat mun yanke shawara zamu tafi da ita Abuja tayi karatun a can, ba ita kadai ba har shi Ahmad d’in nake son mu koma ina so gaba d’aya family d:inmu ya koma can .”
Cikin jin dadi Mama tace
“Hakan yayi kyau Wallahi, gabad’aya a koma yafi sauki kuma zumunci zai da’da kulluwa.”
Iya ta washe baki tace
“Kai Allah yayi muku albarka, ai hakan yafi kowa yana ganin kowa , kai amma naji dad’in wannan maganar.”
Baba yace ” tunda kun takura na koma can zan koma amma bazan tafi tare daku ba , zan biyo ki daga baya kunga akwai sauran aiki a gabana.”
Murmushi Abba yayi yace
” mun yarda, damun burina na ganmu tare a waje daya .”
Kukan Saudala sukaji ,
Mama ta tmbye ta meya faru?
Cikin kuka tace
“Yanzu muna komawa Abuja na daina ganin su Talatu da Dije , na daina hawa bishiya ,
Ta kuma fashewa da kuka , ta cigaba da fad’in
“Kuma yan’ birnin ance yakewa mutum kai suke , ni kuma bana son a yanke min kai.”
Tace ” ni kawai ba zani ba”
Ai kam Saudala an samu abinda ake so , tace
“Allah sarki iya hadda hawayen Soyayya,” ta fad’a tana shek’a dariya.
Abba yace ” yanzu Saudat baban namu shine tsoho ?”
Saudala tayi murmushi tana kallan iya.
Abba yace ” Daman akwai maganar da nake son muyi gaba d’ayan mu.”
Iya tace ” Muna jinka “
Abba yace ” Game da karatun Saudat mun yanke shawara zamu tafi da ita Abuja tayi karatun a can, ba ita kadai ba har shi Ahmad d:in nake son mu koma ina so gaba d’aya family d’inmu ya koma can .”
Cikin jin dad’i Mama tace
“Hakan yayi kyau Wallahi, gaba d’aya a koma yafi sauk’i kuma zumunci zai da’da k’ulluwa.”
STORY CONTINUES BELOW

Iya ta washe baki tace
“Kai Allah yayi muku albarka, ai hakan yafi kowa yana ganin kowa , kai amma naji dad’in wannan maganar.”
Baba yace ” tunda kun takura na koma can zan koma amma bazan tafi tare daku ba , zan biyo ki daga baya kunga akwai sauran aiki a gabana.”
Murmushi Abba yayi yace
” mun yarda, damun burina na ganmu tare a waje d’aya .”
Kukan Saudala sukaji ,
Mama ta tambaye ta meya faru?
Cikin kuka tace
“Yanzu muna komawa Abuja na daina ganin su Talatu da Dije , na daina hawa bishiya ,
Ta kuma fashewa da kuka , ta cigaba da fad’in
“Kuma yan’ birnin ance yankewa mutum kai suke , ni kuma bana son a yanke min kai.”
Tace ” ni kawai ba zani ba.”
Abba yace ” ni kaina a yanke yake Saudat? “
Tace “A’a
Yace ” to ba wasu masu yankewa mutum kai a can , ko kin fasa iya turancin ne ?”
Cikin sauri ta girgiza kai alamar A’a
Yace ” to ki kwantar da hankalin ki ki zama me ko’kari a makaranta ni kuma zan baki kyauta me kyau kinji “.
Ta gyad’a kai
Yace ” ko kefa”
Iya ta tab’e baki tace
” Allah yasa dai ki iya karatun.”
Banza Saudala tayi mata ko kallan ta batayi ba.
Tashi kowa yayi yaje ya kwanta , Saudala da Fadila suka kwanta d’aki d’aya , ganin Fadila a d’akin ya hana Saudala zuwa d’akin iya .
Washe gari Saudala da Fadila bayan sunyi wanka sun karya suka nufi cikin gari .
Suna cikin tafiya Saudala ta gano aminanta suka tafi suna hira , hannun ta rike da abinda ake harbo tattabara.(ban san sunan sa bane )
Har sun gota wani waje sai Saudala ta dawo baya ,
Wata budurwa ce da ita da Saurayin ta sun juya baya suna hira , zanin jikin budurwa ya matse ta wato ta tamke shi kenan, gashi sai wani da’da turo bayan ta take.
Abin harbin tattabara Saudala ta d’auko ta saka dutse ta saita dai-dai setin d’uwawun ta harba ,
Budurwa tana tsaye taji abu me zafin gaske , ai kam ta k’walla k’ara ta fashe da kuka.
Cikin fusata Saurayin ya juyo yaga wacce tayiwa sahibar sa haka , ai yana juyowa suka had’a ido da Saudala .
Cikin sauri ta zame yabar wajan , dan be manta lokacin da ta zuba mai karara ba .
Fadila ta kalleta tace
” meyasa kikayi hakan?”
Saudala tace ” maganinta nayi ba kiga yadda ta matse zanin taba , kuma tana wani k’ara turowa, kinga ai gobe bazata kuma ba.”
Da k’yar buduwar nan ta shiga gida dan Saudala ta fasa Mata baya .
Haka suka cigaba da zaga gari har suka dawo gida .
Washe gari aka fara shirye- shiryen tafiya, tun safe su Talatu suka zo yin ban kwana da aminiyar su,
Suka fito daga gidan suka tsaya a bakin mota , iya tuni an shiga mota Saudala kam tana tsaye,
STORY CONTINUES BELOW

Baba ya kalli Saudala yace
” Kiyi karatu da kyau kinji Saude , kar kiyi wasa , sannan ki daina tsokana kinji.”
Kai kawai ta d’aga mai .
Sukayi sallama da Umma nan itama tayi mata nasiya sannan suka shiga mota .
Abba ya kalli Baba yace
” Zuwa wane lokacin zamu sa ran ganin ka?”
Yace ” ina gama abinda yake gabana zamu tawo insha Allah. “
Abba yace ” Allah ya kaimu”.
Ya amsa da Ameen.
Mutanen gari kuwa sai murna suke Saudala ta tafi,
Basu San Saudala duk ta gane masu murna ta girgiza kai kawai.
Motar su Saudala ta tashi suka fara tafiya Saudala ta leko ta taga tace ,
“Dije ki fad’awa idi me kifi wallahi na dawo sai ya raina kansa “.
Suna d’aga mata hannu har suka daina ganin motar.
*TSOKACI*
_wannan rana da muke ciki yau rana ce babba ,domin wannan rana Allah ne da kansa yake saukowa yana raba rahamar sa, yan uwa kada muyi sakaci da wannan dama muyi amfani da ita kila wata shekarar bama cikin duniyar, mu yawai ta ambaton Allah da istigifari da karatun Alkur’ani , bamu san inda zamu dace ba kila wani a wannan ranar Allah yayi masa gafara_,
_kar mu zagi wani , kar muyi munafuncin wani_,
_Allah kasa muna daga cikin wadanda akayiwa kyautar Aljanna a wannan rana Ameen_🙏🏻
*Daga yau gaskiya baza ku kuma jina ba sai bayan sallah in Allah ya kaimu*😃😃😃😃😃
*A dai ci nama a hnkl kar aje garin neman jira a rasa ido*🤣😂😂😂😂 *a cika mana bandaki da🚽*😜😜
Comment & Share
Neat Lady✍🏼
[8/17, 12:20] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_📚✍🏼
[❄Dance above the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Dedicated to my family*😘😘🥰🥰
*Bismillahir rahmanir rahim*
19&20
B’angaren Abdul kuwa tunani yake a ransa ko wace kuma wannan, a fili yace .
“K’ila garin gajibe -gajiben Mama taje ta dauko wannan”.
Tsaki yayi ya dauko waya ya k’ira sahibar Hadiza suka sha love abin sa.
****
Saudala kam ta kasa manta wulakanci da Abdul yayi mata .
Kwa’fa tayi tace.
” Zan rama wulakanci da kayi min ne , ba dai naji ance cikin satin nan zai dawo ba hmmm,”
Da da’ddare bayan an gama cin abinci ana zaune a parlour ana hira .
Abba ne ya kalli Saudala da tayi shiru kamar ba ita ba , yace .
STORY CONTINUES BELOW

“Saudat”
Tace “Na’am”
Yace ” ki shirya gobe da safe zan kai ki makarantar da zaki dinga zuwa, in yaso sai ku dinga tafiya islamiyya da Fadila. “
Cikin farin ciki wanda ta kasa buyewa tace.
“Toh Abba Allah ya kaimu .”
Ya amsa da Ameen.
Murmushi kawai Saudala take yi har beauty point dinta ya loba.
Fadila tace “sister an zama yar makaranta.” Ta fada tana murmushi.
Mama tace ” to Saudat a dage da karatu dai “.
Tabe baki iya tayi tace
” ba girin-girin ba tayi mai “.
Abba yace ” Haba iya ya zaki ce haka , fatan alkairi ya kamata kiyi mata .”
Tabe baki iya tayi ta dauke kai .
Saudala tace ” kinga wan’nan tsohuwar babu ruwan ki dani , in ba haka ba ko hmmm.”
Iya tace ” ki karasa mgnr ki mana.”
Banza Saudala tayi mata kamar bata ji ba .
Mikewa Abba yayi yace .
“To iya sai da safe , zan shiga na kwanta “.
Iya tace ” Allah ya tashe mu lafiya , ni kam ba yanzu ba sai na gama kallan wannan wasan .”
Mikewa Mama tayi tabi bayan mijin ta .
Tabe baki iya tayi tace .
“Daman nasan ba wata kwanciya da zaiyi , matar sa tabi bayan sa yace wani zai kwanta.” 🤭
Mikewa Fadila tayi ta shiga d’aki dan maganar iya ta bata kunya .
Saudala kam sam bata fahimci me take nufi ba .
Bayan kowa ya tashi daga parlourn ya rage daga Saudala sai iya wacce ta fara gyan’gyadi .
Zuwa mintina biyar tuni iya bacci ya dauke ta , ai Saudala na ganin haka tayi murmushi ta mike ta kashe TV sannan ta kashe filar parlourn, parlourn yayi duhu sosai har baka ganin gaban ka .
Da lalibe ta isa kujerar da iya take bacci ,zama tayi a kusa da ita sannan ta kafar iya girgiza har iya ta bude ido.
Iya na bude ido taga waje duhu , daman iya badai tsoron duhu ba .
Ido Saudala ta zare ta kurawa iya ido. 😳
Iya data rude bata ganin komai sai hasken idon Saudala tunda a kusa da ita take .
Ganin ido a kusa ita yasa ta kara budewa jikin ta har rawa yake .
Baki Saudala ta washe 😁 hakoran ta suka fito.
Ai iya na ganin hakora a waje kawai sai ta fara hawaye, dan gani take kamar cinye ta za’ayi.😂
Sai da Saudala taga iya ta gama tsorata dan yadda take kuka kamar karamar Yarinya, haka yasa Saudala ta mike tana tafiya da baya har ta bar parlourn.
Iya ganin ta daina ganin ido da hakora sai ta fashe da kuka .
Gashi tana so taje ta kwanta amma zata iya tashi ba , hakan yasa ta kwanta akan kugerar da take kai gaban ta na faduwa .
Bata san lkcn da bacci ya dauke ba.
Da asuba Abba ya sauki zai tafi masallaci yaga iya a kwance akan kujera.
Zuwa yayi ya tashe ta a firgice iya ta mike zaune tana zare ido .
Abba yace “anan kika yi bacci kenan iya .
STORY CONTINUES BELOW

Iya dai har lkcn tsoron parlourn takeyi , kallan Abba tayi tace .
” kai ni dakina , ta fada cikin rawar murya .
Abba ganin a firgice take sai ya rike hannu ta ya kaita daki sannan ya nufi masallaci.
Da nufin da safe zai tmbye ta da safe .
washe gari da huri Saudala tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga ta atampa.
Fitowa tayi ta shiga kitchen tana taya Mama aiki.
Bayan sun gama hada break fast suka jera a dining , zama Saudala tayi tana jiran fitowar Abba.
Abba yana saukowa daga sama ya yangi Saudala a zaune da alama jiran sa take .
Zama yayi akan dining yace .
” Saudat har an shirya ne ?”
Juyowa tayi fuskar ta dauke da murmushi tace .
“Eh Abba na shirya kai kadai nake jira.”
Yace “Saudat sarkin zumudi , to zo kici abinci sannan mu tafi .”
Murmushi Mama tayi tace .
“Ai tana son karatun ne shiyasa, Saudat shiga ciki ki k’ira Fadila.”
Shiga tayi ta sami Fadila ta shirya da alama makaranta zata tafi .
Saudala tace ” yauwa daman Mama ce tace na k’ira ki “.
Fadila tace ” daman yanzu zan fito ,nima ina da lecture k’arfe tara .”
Tare suka fito suka zauna .
Mama tace ” na lek’a iya amma har yanzu bata tashi ba.”
Abba yace “naga yau ma a parlourn nan ta kwana sai da asuba na tashe ta na kaita d’aki , tabbas akwai abinda yake damun ta dan naga a tsorace take, zan tambaye ta in ma dawo daga aiki.”
Mama tace ” Allah yasa dai lafiya. “
Abba yace ” Ameen “.
Fadila tace “kai iya ta ciki rigima wallahi”.
Saudala dai babu abinda tace abincin ta kawai take ci.
Mik’ewa Abba yayi yace.
” To Saudat tashi mu tafi .”
Mik’ewa Saudala tayi tana murmushi .
Fita suka yi suka hau mota suka nufi makaranta.
Suna zuwa suka nufi office din principal din makarantar , da sallama Abba ya bude office din suka shiga .
Principal yana ganin Abba ya mike yana fadin ,
“Alhaji umar yau kaine a office dina , sannu da zuwa ga waje ka zauna.
Musabaha sukayi sannan Abba ya zauna yace .
” Musa ga ya’ta na kawo ta ina so a sata a jss 2 , duk da kwata -kwata bata huce primary two ba ta daina zuwa makarantar , amma zan dauko lesson teacher yana koya mata a gida.”
Principal Musa yace.
“To za’a kaita jss2 din , amma in naga bata karatu zan sanar da kai sai a dawo da ita baya .”
Murmushi Abba yayi yace.
” yauwa nagode, kuma dan Allah kasa ido akanta in har bata karatu ka fad’a min.”
Yace ” insha Allah .”
Abba yace ” yaushe zata fara zuwa ?”
Principal yace “zan baka uniform yanzu in yaso zuwa jibi sai ta fara zuwa.”
Abba yace ” to shikenan nagode”.
Principal yace “ka wuce haka a waje na.
Ita dai Saudala tunda suka shigo ta zubawa principal ido gaba d’aya ta kasa d’auke ido daga kansa .
Abba yace” Saudat baki gaida malamin mana”.
Ai Abba yana fad’ar haka Saudala ta kya’lkya’le da dariya tana nuna principal da yatsa…
Principal ganin tana yi masa dariya sai ransa ya b’aci amma sai ya danne bai nuna ba.
Cikin tsawa Abba yace .
“Ke Saudat! dariyar me kike yi ?”.
Cikin dariya tace.
“Abba shi kuma wan’nan haka hancin sa yake kamar socket d’in da Fadila take jona charji , yasin da muka shigo na zata socket din ne , daman akwai hanci kamar faranti a duniyar nan.”
Ta kuma fashewa da dariya kamar mahaukaciya.
Tsawa Abba yayi mata sannan aka samu tayi shiru.
Shikam principal banda yak’e ba abinda yake .
Abba yace ” ke fita ki jira ni a bakin office d’in nan .”
Mik’ewa tayi ta fita.
Abba ya dinga bawa principal hak’uri .
Principal yace ” babu komai ai yarinta ce. “
Abba yayi masa godiya ya karb’i uniform d’in ya fita.
Saudala tana tsaye ya fito , ya kalle ta yace ” muje”.
A bakin mota yayiwa driver waya yazo ya maida Saudala gida .
Kafin driver yazo Abba ya kalli Saudala yace .
“Kar kiga nayi miki shiru akan abinda kika yi ki zata bazan miki magana ba , ina sane sai mun koma gida.”
Da yake drivern yana kusa nan da nan sai ga gashi ya iso, ta shiga suka tafi , Abba kuma ya tafi office.
Tunda Saudala ta koma take bawa Mama labarin malami mai hancin socket , banda dariya babu abinda Mama take yi .
Mama tace ” daman Saudat akwai mutum mai hancin socket?”
Saudala tace “ai kam yau na gani Mama, ta fad’a cikin mamaki.
Wayar Mama ce tayi k’ara tana dubawa taga sunan Abdul.
D’auka tayi bayan sun gaisa yake cewa.
” Mama ku sa ran ganina jibi eh warhaka .”
Cikin farin ciki Mama tace
“Allah ya dawo da ku lafiya.”
Yace “Ameen”. Sannan ya kashe wayar.
Mama ta kalli Saudala tace .
” jibi Yayan ku zai dawo .”
Saudala tace “Allah ya kaimu”.
Amma a ranta cewa tayi .
” Ranar rama wulakanci na ya kusa kenan.”
Mik’ewa tayi dan taje tayi tunanin abinda zata yiwa wannan sojan dan ta rama wulakancin da yayi mata.
Mama tace ” ina kuma zaki ?.”
Saudala tace ” fitsari nake ji.”
Tana gama fad’ar hakan ta shige d’aki.
D’aki Saudala ta shiga direct wajan kayan ta ta nufa , tana zuwa ta bud’e ta fara birkita kayan ta har ta gano abinda take nema.
Wannan abin harbo tat’tabarar ta dauko tayi murmushi tace.
“Da wannan zan rama abinda kayi min soja, wannan shine maganin me wulakanci irin ka” .
Mayar da abin tayi sannan ta mik’e ta fito parlour.
Tana fitowa ta gano iya a bakin k’ofar parlourn ta kasa shigowa .
Nufar wajan ta Saudala tayi tace.
“Iya lafiya yau ban ganki ba?”.
A hankali iya ta karaso cikin parlourn ta zauna tana zare ido.
Saudala tace ” Iya me kike tsoro ne haka”?.
Saudala tayi-tayi iya ta fad’a mata abinda yake damunta amma tak’i .
Daman Saudala bata son ta fad’awa kowa abinda ya faru , shiyasa ta kya’leta ta tashi ta bar wajan.
Bayan sallar la’asar Fadila ta dawo , Mama ta sanar da ita game da dawowar Abdul .
Murna wajan Fadila ba’a magana , Allah-Allah take jibi tayi taga yayan ta.
Saudala kam tab’e baki tayi, sannan ta cigaba da abinda take .
Da daddare ana zaune a parlour Abba ya kalli Saudala yace .
“Saudat”.
Tace “Na’am”.
Yace ” abinda kikayi d’azu kin kyauta kenan, ya zamuje wajan mutum neman alfarma amma ki kalle shi kice wai da kika ga hancin sa kin zata socket ne “.
Fadila dake cin abinci taji ance mai hancin socket sai kuwa ta kwashe da dariya hadda rik’e ciki.
Abba ya cigaba da fad’in
” Ki nitsu ki shiga hankalin ki , in ba haka ba zan fasa saki a makarantar kinji “?.
Kai Saudala ta daga tace .
” To”.
Abba yace ” Fadila da safe kuje tare ku kai d’inkin uniform d’in ta .”
Fadila tace. ” To Abba Allah ya kaimu.”
Saudala da Fadila suka mik’e suka yi musu sai da safe suka shiga d’aki.
Abba ya kalli Iya yace.
“Iya d’azu wai meke damun ki ne”?.
Iya tayi shiru kamar bata jiba .
Juyin duniya amma Iya tak’i fad’ar abinda ya faru , Abba ya gaji ya rabu da ita.
Iya kam tsoro take kar aljanar kauye ce ta biyo ta ta shanye mata jini.
STORY CONTINUES BELOW

Washe gari su Fadila suka Kai d’inki suka dawo .
Saudala tana murna gobe tayi ta fara zuwa makaranta, Fadila na murnar dawowar yayan ta .
Saudala tare suke komai na gidan , ko abinci za’a dafa to da ita a kitchen din .
Kwana ukun da tayi a gidan har ta dan koyi wani abun.
Washe gari tun karfe shida Fadila da Saudala suka tashi daga bacci.
Saudala ta shiga wanka , ita kuma Fadila ta nufi kitchen ana ta tarar da Mama tana abincin tarbar Abdul.
Abba kansa yace yau babu zuwa office saboda d’an lele zai dawo.
Saudala ta shirya cikin farar riga da farin hijjabi iya wuya sai pink din siket iya gwiwa, sai farar safa da takallimi .
Uniform din ya karbe ta sosai sunyi mata kyau jakar da Abba ya siyo Mata ta dauka ta fito parlour.
Fadila na ganin ta tace .
” Masha Allah sis uniform din yayi miki kyau sosai .
Murmushi kawai Saudala tayi .
Abba ya sauko yana fad’in.
“A’a Saudat har an shirya?”.
Saudala tace “Eh Abba na shirya”.
Yace ” Ga driver da zai dinga kaiki can ya karaso , d’azu nayi magana da lesson teacher d’inki yace zai dinga zuwa ranar alhamis da juma’a da yamma, sannan ranar asabar zaki fara zuwa islamiyya munyi mgn da headmaster makarantar yace za’a kai ki aji 3 har uniform dinki ya bani anjima za’a kai dinki. “
Abba ya cigaba da fad’in.
“Saudat ki tsaya kiyi karatu , duk abinda baki gane ba ki tambaya malamin kinji ko.”
Saudala tace ” insha Allah zanyi Abba. “
Abba yace ” Allah ya amince .”
Fitowa Saudala tayi ta shiga mota suka dau hanyar makaranta.
Suna barin layin motar da aka kawo Abdul tana shigowa layin.
Saudala kam da suka isa makaranta office din principal suka nufa ita da driven .
Principal ya dinga hararar Saudala , tana lura dashi amma taki d’agowa dan tasan tana dagowa dariya zatayi.
ID card din makarantar ya bata ta rataya shi a wuya sannan ya kira wani malami Yace ya kaita aji.
Tunda Saudala ta shiga ajin take kare masa kallo , gaba daya yan ajin basu fi su ashirin ba , kuma ko wanne sit mutum biyu ne .
Wani sit Saudala ta gani mace daya ce a zaune hakan yasa ta je ta zauna a kusa da ita .
Bayan ta zauna Yarinyar dake zaune ta mik’a wa Saudala hannu tace .
“Sunan khadija ke fa”?
Saudala tayi murmushi tace .
” Sunana Saudat. “
Saudala tace Saudat ne saboda haka Fadila tace ta dinga fada.
Khadija tace ” ko zamu iya zama kawaye ?”.
Murmushi Saudala tace.
“Babu damuwa “.
Malami ne ya shigo hakan yasa suka yi shiru.
Saudala na ganin malamin ta fara k’unshi dariya.
Malamin ya lura da ita yace .
” ke me kikewa dariya ?”
Cikin dariyar data fara fitowa tace ……………..
STORY CONTINUES BELOW

*Aradu na gaji*😩😩😩😩😩
*A kawo min fanta 🍾🍹 da ice cream 🍦ko nayi kuka*.😫😫😫😫😫
Comment & Share
Neat lady✍🏼
[9/3, 20:22] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_📚✍🏼
[❄Dance the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
_*DON’T 4GET VOTE, COMMENT AND ALSO FOLLOW US ON WATTPAD*_
*@ABORIGINALWRITER’SASSO.*
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Dedicated to Kululu fan’s group, Saudala fan’s group 1&2*
_*Kuyi hakuri zaku dinga jina shiru weekend sabida wani dalili🤦🏻♀🤦🏻♀, amma insha Allah zan dinga yi muku long page.*_
*Bismillahir rahmanir rahim*
23&24
Saudala ta kalli malamin tace.
“Yasin tasono na gani a hancin ka , anya kuwa yau kayi wanka? ta fada tana toshe hanci😷.
Ai kam yan’ aji suka kwashe da dariya .
Cikin borin kunya yace .
” ba shi bane gashin hanci ne”.
Saudala ta kalli shi tace.
“Gsky na shaki wannan k’aryar”.
Malamin da yaga Sa udala tana niyar tozarta shi a gaban dalibai kawai sai ya basar ya bar wajan .
Har ya bar wajen ya nufi wajan board (allo).
Da yake Hausa teacher ne hakan sa suka dinga yin Hausa a ajin.
Abdul kuwa motar sa na shiga gidan yaga su Fadila a tsaye suna ta murmushi.
Cikin sauri daya daga cikin sojajon ya bude mai kofa .
Cikin kasaita ya fito daga motar cikin kayan sojoji fuskar sa dauke da murmushi.
Abdul fari ne sosai yana da dogon hanci irin na Fulani ga ido dai-dai shi , gashin kansa kuwa a kwance kina ganin sa kinga bafulatani sosai.
Abdul dogo ne bashi da kiba sai dai yana da dan fadi daga sama amma ba sosai ba , sam Abdul bai kama da soja ba in dai ba sani kayi ba baza kace soja bane .
Da murmushi ya nufi inda su Mama suke a tsaye.
Da gudu Fadila taje ta rungume shi Rana dariya , cikin farin cikin ganin k’anwar sa ya daga ta sama yana juyawa suna dariya gabadaya.
Abba ne yace ” to in kun gama kazo mu gaisa ko.”
Sauke ta yayi ya nufi wajan Abba.
Har kasa ya durkusa ya gaida Abba.
Murmushi Abba yayi yace ” to mu shiga ciki mai gaisa .”
Rike hannun Fadila yayi suka shiga parlourn.
Bayan sun gaisa da Abba da Mama ya kalli iya wacce ta dauke Kai kamar bata ganshi ba.
Abdul yace ” lallai wannan tsohuwar ko magana ma babu kenan.”
STORY CONTINUES BELOW

Kallan sa iya tayi tace.
“To sannu mai k’atan kai.”
Hade rai Abdul yayi yace.
“Wai iya baki San sunana bane zaki dinga cemin me k’atan kai.”
Iya tace ” ni kam nasan sunan ka, nifa na rai neka .”
Abdul yace ” to meyasa ba’kya fadar sunana?, ya tambaye ta cikin tsokana.”
Tace “to mara kunya sunan mijin nawa zan fada, an fada maka kowa irin iyayen kane iyayen zamani eyeeee?.”
(sorry na manta ban fada muku ba Abdul yaci sunan mahaifin Abba da Baba , ma’ana mijin iya kenan.
abinda yasa ba’a boye sunan ba sbd shiya marigayi mijin iya shine yace in har sunan sa akasa to baya butakar a boye a dinga fada kawai , shiyasa ake cemai Abdul.)
Murmushi Abdul yayi yace .
” Haba to meye dan kin fada , ai ba wan’can Abdulrahman din kike nufi ba ni kike nufi. “
Matsar hawaye iya ta fara dan ya tuno mata da habibin ta.😂
Da sauri tabar parlourn tana goge hawaye.
Dariya Fadila take tana fadin.
“Iya an tuno da tsohuwar Soyayya, naso Saudat ta nan akayi wannan dramar .”
Baki Mama ta rike tace .
“Tab ai da Saudat na nan da Iya ta shiga uku.”
Abba yace ” ai Saudat sai dai a barta .”
Abdul ne yace ” wace kuma Saudat?.
Fadila tace ” yanzu bro Saudat din ka manta , Saudat din uncle na Adamawa fa .”
Cikin mamaki yake kallan Fadila yace .
“Na tuna ta, kinsan rabon dana ganta tun tana shekara shida lkcn da naje yiwa uncle sallama zamu tafi wani course a Lagos , kice yanzu ta girma sosai.”
Mama tace ” Ashe in ka ganta baza ka gane taba , dan tana makaranta ne da yanzu tana nan.”
Murmushi yayi yace ” in ta dawo na ganta.”
Nan Fadila ya bashi labarin ai ta dawo nan da zama .
Abdul yaji dadin lbrn sosai dan shi yana son yaga yara suna zuwa makaranta.
Mikewa yayi yace.
“Abba bara naje nayi wanka na dan huta .”
Abba yace ” zuwa anjima sai ka sakko muci abinci. “
Yace ” to Abba”, ya fada yana fita daga parlorn.
Saudat kam ta maida hankalinta sosai wajan karatu .
Bayan mlmin Hausa ya fita malamin mathematics ya shigo ya fara nasa karatun.
Da yake mathematics ne ba turanci ake sosai ba Saudala ta fahimce shi sosai .
Tunda malamin English ya shigo Saudala ido ya fara raina fata , dan malamin bature ne ko hausa baya ji .
Idan malamin ya fadi abu da turanci sai ta tambayi kawar ta khadija ta fassara mata da Hausa.
A haka har tadan fahinci wani abun .
Da misalin karfe biyu aka tashe su,
suka fito ita da khadija daga ajin suna tafiya suna hirar karatun da akayi musu.
Principal ne yazo wucewa suna hada ido da Saudala ta kya’lkyal’le da dariya tana nuna mai hanci da hannun ta.😂
Sarai yasan dashi take amma ganin dalibai da yawa yasa ya basar kamar bai kula ba.
STORY CONTINUES BELOW

Yayan khadija ne yazo daukar ta tare suka karasa da Saudala, khadija tace .
“Yaya kaga k’awata , ta fada tana nuna Saudala.”
Murmushi yayi yace .
“Ya kike “?
Kallan up and down Saudala take masa sa sannan tace .
” lafiya lau , amma dan Allah yayan khadija na tambaye ka”.
Yace “ina jinki”.
Tace ” yau kayi wanka kuwa hala?naga kayan duk sunyi dau’da.😂
Kallan kansa yayi dan yasan gaskiya ta fada , cikin kunya yace .
“Nayi mana kawai na fito zan tawo ne sai na fadi shiyasa.”🤭
Saudala tace “kawai sai ka fadi kamar mara hankali kawai ka fadi gaskiya ba’kayi ba .”🤣
Cikin jin haushi Khadija tace .
“Haba Saudat yayana nefa.”
Saudala tace ” to dan yayan kine bazan fadi gaskiya ba .”
Yayan Khadija da yaga Saudala na neman kunya tashi sai yaja hannun k’anwar sa suka shiga mota .
Tsaki Saudala tayi tace.
“G’ardin banza kawai ko wanka ba yayi.”😅 (ko ina ruwan ta oho😂)
Drivern ne ya gano Saudala yazo yayi mata magana suka shiga mota suka tafi.
Isar su gidan Saudala taga sojoji a ko ina sai huci suke .
Rike baki Saudala tayi tace.
” Su kuma wadan nan musu kama da dodonin fa.”😆
Koda ta shiga parlour babu kowa a ciki da alama kowa yana d’aki kenan.
D’akin su ta shiga ta ajjiye jakar ta , kaya ta cire ta shiga wanka.
Bayan ta fito ta shirya sannan tayi sallah , parlour ta fito dan cin abinci.
Har taga cin abinci babu wanda ya fito .
Tashi tayi ta shiga d’akin Mama da sallama.
Amsawa Mama tayi tace .
“A’a yan makaranta har an dawo ?.”
Saudala tace ” eh Mama tun dazu har naci abinci ma, Mama ina Fadila?.”
Mama tace ” kin san yayan ku ya dawo tana can dakin sa , kema kije ku gaisa .”
Saudala tace ” to Mama. “
Juyawa tayi ta fito daga d’akin direct d’akin su ta koma ta dauko jakar ta ta fara karatu.
A ranta tace ” na rasa wanda zan je mu gaisa sai wan’can me wulakancin.”
Tayi tsaki ta cigaba da karatun ta.
B’angaren Abdul kuwa hira suke tayi shida Fadila.
Fadila ta mike tace .
“Yaya Abdul bara na koma nasan yanzu sister Saudat ta dawo .”
Abdul yace ” gaskiya kina ji da wannan Saudat din.”
Murmushi Fadila tayi tace .
“Sosai kuwa “.
Yace ” ok sai na shigo anjima.”
Tace ” to , a gaida aunty Hadixa.”
Murmushi yayi yace .
“Zata ji”.Ta juya ta fita .
Yau kam Fadila tasha lbrn makaranta a wajan Saudala.
Da dad’dare bayan an gama cin abinci kowa yana zaune a parlourn banda Abdul da yake d’akin sa sabida yayi ba’ki.
STORY CONTINUES BELOW

Mikewa Saudala tayi ta koma d’aki .
Parlorn ya rage daga Abba sai Mama sai Fadila, iya ma tana d’aki har tayi bacci.
Fadila tana kwance ta daura kanta akan cinyar Mama.
Abdul ne ya shigo parlorn yana fadin.
” ke sai kinje kin karya Maman, oya tashi .”
Cikin shagwab’a tace .
“Mama kin gan shi ko.”
Mama tace ” rabu dashi kinji.”
Rike baki Abdul yayi yana fadin.
“Nidin Mama.”?
Mama tace ” eh”.
Abba yace ” rabu da ita kaji babana zo ka kwanta kaima.”
Zuwa Yayi ya kwantar da kansa a kafadar Abba .
Dai-Dai lkcn Saudala ta fito daga d’aki.
Ganin kato kwance a jikin Abba sai Saudala tace.
“Tab jama’a kuzo kuga katon gardi a parlourn nan , shi ko kunya baya ji kalle shi kamar wani buhun siminti.😂😂😂
Cikin kunar rai Abdul ya dago yaga me cemai gar’di.
Jama’a wai Abdul ne gar’di 😂😅😂😂
Ku taya ni ganin abinda Abdul zai yiwa Saude.🤣
Comment & Share
Neat Lady✍🏼
[9/3, 20:24] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_📚✍🏼
[❄Dance the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
_*DON’T 4GET VOTE, COMMENT AND ALSO US ON WATTPAD*_
*@ABORIGINALWRITER’SASSO.*
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Dedicated to Mummy Khaleed & Aeeshert pretty*😘😘😘😘
*Comment din ku na sani nishadi yana kara min kwarin gwiwa, page din kune kuyi yadda kuke so dashi*.
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*Bismillahir rahmanir rahim*
27&28
Cikin b’acin rai Abdul ya Mike ya nufi hanyar parlorn.
Daya daga cikin yaran sa ne ya gano Abdul yana tawowa jikin sa duk ruwa kamar wanda ruwan sama yayi wa duka.
Cikin sauri ya nufe shi yace .
“Oga lafiya na ganka haka”?
Ko kula shi Abdul bai yi ba ya shiga cikin parlorn.
Mama da Iya suna zaune a parlorn suka ga ya shigo a fusace ga ruwa na diga a jikin sa .
Mama tace. “Lafiya Abdul na ganka haka?”
Kafin ya bada amsa Saudala ta riga shi da fad’in.
“Kai wannan mai hancin karas d’in yau kuma wasan ruwa aka yi”.😂
Ta fad’a tana rik’e baki.
Sai kuwa Iya ta karb’e da fad’in .
” Amma kaji kunya da girman ka kake wasan ruwa, 🤣 yadda ka jika jikin ka mtwssssss Allah ya s’auwake[ Jama’a wai Abdul ne me wasan ruwa😂]”.
STORY CONTINUES BELOW

Ta k’are maganar tana dariya
Abdul kam ya sara me zai ce , lailai wannan shi ake cewa ga mari ga tsinka jaka.
Kallan Saudala yayi da take shek’a masa dariya .
Cikin b’acin rai Abdul ya nuna Saudala Yace.
“Ni zaki zubawa ruwa sannan ki zo kina raina min hankali,ki shiga hankalin ki , ni ba sa’an ki bane wallahi dan na k’arya ki ba wani abu bane a waje na , zaki San ni kika yiwa haka .”
Fuuuuuuu ya juya ya fice daga parlorn.
Saudala kam gaba d’aya tsoro ya kamata,gaban ta sai fad’uwa yake.
Mama ce tace mata
“Saudat mai yasa kika zubawa Abdul ruwa uhumm?”.
Saudala tace .
“Mama shine fa ya mare ni”.
Mama tace
” Au ramawa kika yi Kenan “?
Saudala ta d’aga kai alamar eh.
” Mama tace ” Haba Saudat Abdul fa yayan ki ne yanzu idan Baba yaji abinda kike yi zai ji dadi “?
Saudala tace ” A’a “
Mama tace ” to ki daina kinji , in anjima kije d’akin sa ki bashi hakuri.”
Saudala tace ” To”.
Iya tace
” Au yanzu Yarinyar nan ke kika yi masa wannan wankan san’nan kika ce wai wasan ruwa yayi , kai amma ke yar jakar uba ce .”
Mama tace
” ke ma dai Iya da wani zance kike , yanzu Abdul da girman sa sai yayi wasan ruwa ?”
Iya ce tace.
” Yo wa yasa ni.”
Saudala kam d’akin su ta shiga tana fadin.
“Hmmm indai sai na bashi hakuri zai hakura sai dai to nima sai dai ya bani hak’uri in ba haka ba sai dai mu cigaba daga inda suka tsaya.”
Abdul kuwa zagaye yake a cikin d’akin ya rasa tunanin me zaiyi.
Zama yayi akan kujera yace .
” Zan koyawa Yarinyar nan hankali zata San ba irin mu ake rainawa ba .”
Da dad’adare suna zaune amma banda Abdul .
Saudala da kanta ta bawa Abba labarin abinda ya faru san’nan ta dora da cewa.
“In yana so na daina fada da shi to ya bani hakuri.”
Ta fada cike da yarinta .
Murmushi Abba yayi yace .
“Naji ramawa kika yi amma ai shi yayan kine ko kin manta ?”
Tace ” A’a “.
Yace ” to ki daina hakan babu kyau , gobe in kin dawo daga makaranta kije ki bashi hakuri. “
Tace ” To”.
Washe gari ta kama Friday Saudala da huri aka dawo daga makaranta.
Bayan lesson teacher dinta yazo sungama karatu ta koma parlour .
Tana zaune tana tunanin taje ta bashi hakuri ko kar taje .
A fili tace ” Ai Abba ne yace naje gwara inje kar Allah ya kona ni a wuta.”
Mikewa tayi ta nufi d’akin Abdul .
Tofa ga Saudala zata shiga d’akin Abdul😂
STORY CONTINUES BELOW

*Yasin dazu nayi typing nayi wajan 2read more kawai sai WhatsApp dina ya goge*😕😕😩😩😩 *Da har nayi xuciya na fasa typing din sai kuma nayi wannan din*😣🥺
*Kuyi hakuri dashi babu yawa*😁😁
Comment & share
Neat Lady✍🏼
[9/3, 20:24] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
®🇳🇬
_*ABORIGINAL WRITERS ASSOCIATION*_📚✍🏼
[❄Dance the surface of the, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
_*DON’T 4GET VOTE, COMMENT AND ALSO US ON WATTPAD*_
*@ABORIGINALWRITER’SASSO.*
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Dedicated to ABORIGINAL WRITERS ASS…*😍😍😍💃🏻💃🏻
_*Mmn Adnan ina taya ki murnar fara sabon book dinki me suna RAYUWAR RUMAISA Allah yasa mu an famana da sakon da yake cikin sa.*_
*_Mum aysar kema ina taya ki murnar fara sabon book dinki mai suna KISAN GILLA Allah yasa kin fara a sa’a._*
*Bismillahir rahmanir rahim*
25&26
Cikin b’acin rai Abdul yake kallan Saudala da ta r’ike kugu tana girgiza.
Abdul yace ” ke ni kike kira da G’ardi k’aton banza ?”.
Cikin rashin tsoro Saudala tace .
“Ai sunan da ya dace da kai kenan, namamajo kawai.”
Cikin zafin nama ya da’uke ta da mari yace.
“Ni zaki yiwa rashin kunya , ni sa’an kine , wacece ke?”
Cikin mamaki Saudala take kallan sa , wai yau ita aka mara .
Cikin f’ada Mama tace .
“Kai Abdul meye haka ya zaka mari yarinya haka kawai eyeeee.”
Cikin b’acin rai Abdul yace .
“Mama ba’kya ganin rashin kunya take min, ni zata cewa namamajo , wai dan Allah ina kuka samo wannan mara kunyar ?”
Abba ne ya katse shi da fadin.
“K’anwar taka kake cewa wace ita , Saudat cefa .”
Abdul ya kurawa Saudala ido ne sai yanzu ya gane ta .
Abdul yace “wai Abba kana nufi wan’nan yar wajan uncle ce ?.”
Mama tace ” itace mana ka dau hannu kawai ka mari Yarinya.”
Abdul ya kalli Saudala da take hawaye yace .
“Rashin kunya kike ji dashi ko , to zan saita miki zama a gidan nan .”
Cikin masifa Saudala tace .
“Sai dai mu saitawa juna zama Wallahi.”
Cikin b’acin rai ya mika hannu zai kamota , cikin sauri ta gudu .
Sai da taje k’ofar d’aki san’nan ta juyo tace.
“Kuma yasin sai kayi nadamar mari na , mai hancin karas kawai .😂
Ganin ya nufo ta tayi saurin shiga d’aki ta kullo k’ofa.
Abba ne yace ” Abdul zo ka zauna. “
STORY CONTINUES BELOW

Dawowa yayi ya zauna , Abba yace .
“Abdul Saudat k’anwar kace yadda ka dauki Fadila a matsayin kanwa haka nake so ka dauki Saudat, sai kayi hakuri Saudat bata da dama kuma gsky ban ji dadin marin da kayiwa Saudat a gabana yanzu gashi zaka jawowa kan’ka raini a wajan ta, daman baka kula Saudat ba ya ka cika balle har ka daga hannu ka mare ta, ita ma Saudat din zanyi mata magana, ka kiyaye gaba bana so ka kara mai’maita abinda tayi yanzu.”
Mikewa Abba yayi yana fadin.
“Ni na shiga ciki sai da safe .”
Fadila tace “Allah ya tashe mu lafiya .”
Mama tace ” Abdul kasan sai Saudat ta rama abin kayi mata , ko da ike baka san halinta bane , mu kwana lafiya , ta fada tana Mikewa ta sau sama.”
Parlorn ya rage daga Abdul sai Fadila.
Fadila ta kalli Abdul tace .
“Yaya Abdul kayi hakuri haka halin Saudat yake bata jin magana, kuma na tabbata sai ta rama abinda kayi mata yanzu.”
Dago ido Abdul yayi ya kalli Fadila dan shi a rayuwar sa baya san raini ko k’adan .
Yace ” aikam zan saita mata zama a gidan nan dan baza juri rashin kunya ba. “
Fadila tace ” baka ji wai me tace maka ba sai dai ku saitawa juna. “
Yace ” wai shekarun ta nawa ?”
Fadila tace ” sha biyu zuwa sha uku naji umman ta ta fada. “
Yace ” shine zata ce zata saita min zama dan ta raina ni , amma zan cire mata aljanun da suke kan’ta .”
Fadila tace ” ka dai yi a hankali bro dan itama bata da dama.”
Cikin fusata yace ” me ta isa tayi min zata rama marin ne kome?”
Fadila tace ” ko kadan bazata rama mari ba amma sai ta samu hanyar da zata fanshe .”
Mikewa Abdul yayi yace .
“To mu zuba ni da ita .”
Yana gama fadar hakan ya fice daga parlorn.
{Nima dai nace mu zuba mu gani Abdul😂 Dan ni team din Abdul ce💪🏻}1
Abin dariya ya bawa Fadila a ranta tace .
“Yanzu Saudat ta samu sabon abokin fada .”
Shirga d’aki Fadila ta tar da Saudala a zaune tana kada kafa.
K’arasa wa tayi ta zauna kusa da Saudala tace .
“Saudat kina zaune kenan na zata ma kinyi bacci.”
Kallan ta Saudala tayi sannan tace .
“Ta yaya zanyi bacci bayan abinda wannan mai hanci karas din yayi min .”
Fadila tace ” yaya Abdul din ne mai hancin karas”?
Saudala tace “shi din”.
Fadila tace “yanzu ki kwanta kinga gobe kina da makaranta kar kije ki makara.”
Banza Saudala tayi mata kamar bata ji ba .
Murmushi Saudala tayi tace .
“Na samo yasin .”
Fadila tace ” me kika samo “?
Saudala tace ” babu komai “.
Mikewa Saudala tayi taje kwanta abin ta .
Abdul kuwa ma’makin rashin kunyar Yarinya yake .
Kwafa yayi yace ” zan gyara miki zama Yarinya. “
Da haka bacci ya dauke shi.
Washe gari Saudala ko Abba bata gani ba kudin break ma Mama ce ta bata ta tafi makaranta.
STORY CONTINUES BELOW

Masha Allah Saudala tana fahimtar abinda ake koya musu , matsalar ta kawai turanci amma idan tanu gobe za’a fara yi mata lesson sai hankalin kwanta.
Yau kam da k’yar khadija ta kula Saudala sabida tana jin haushin ta jiya tacewa yayan ta baya wanka.
Da taimako khadija Saudala take gane wani abin na turanci.
Bayan an tashi Saudala ta dawo gida tayi wanka tayi sallah ko abinci bata ci ba bacci ya dauke ta.
Bayan sallar i’sha kowa yana parlorn a zaune .
Saudala tana zaune tana na game a wayar Fadila dagowar da zata yi suka hada ido da Abdul , tsaki tayi ta girgiza mai kai alamun zamu hadu.
Abba yayiwa Saudala fada akan rashin kunyar da tayiwa Abdul .
Abinda ya kuma tun zura Saudala kenan .
Washe gari bayan ta dawo daga makaranta bayan sallar la’asar lesson teacher dinta yazo suka fara karatu.
Alhamdulilah Saudala tana fahimtar abinda ake koya mata .
Bayan sun tashi har tayi hanyar parlour ta dawo baya , Abdul ta gani a bayan gidan yana zaune yana waya.
murmushi mugunta Saudala tayi cikin sauri ta shiga parlour Allah yasa bb kowa .
Sama ta hau taje wajan wata window wacce a saitin ta Abdul yake a zaune .
Ruwa ta debo cikin bokiti taje dai-dai tagar ta shara mai ruwa.🤣
Abdul yana zaune yaji saukar ruwa a jikin nan da nan ya gigice yana share na fuskar sa .
Dariyar ta ya juyo daga sama yana juyawa suka hada ido .
Hannu ta dago mai alamun hiii.😂
Tace ” ko kana bukatar wani wankan ne mai hancin karas.🤭
Ta fada tana kyal’kyale’wa da dariya.😂
Cikin b’acin rai Abdul ya Mike………..
Ina team din Saudala?😂🤣
Comment & Share
Neat Lady✍🏼
[9/3, 20:25] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
🇳🇬®
*_ABORIGINAL WRITER’S ASSOCIATION(YAN ASALI)._*📚✍🏼
[❄Dance above the surface of the world, let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
_*DON’T 4GET TO VOTE, COMMENT & ALSO FOLLOW US ON WATTPAD @*_
_*Aboriginal WrtersAsso.*_
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Bismillahir rahmanir rahim*
31&32
D’aki Saudala ta shiga ta bude kayan ta ta dauko abu ta boye a cikin riga ta fito.
Fitowa Harabar gidan tayi tana ‘karewa motocin gidan kallo.
Murmushi tayi ganin duk motocin basa nan sai ta Abdul kawai da yasa aka wanke masa.
Gefe ta koma inda babu wanda zai ganta .
Gwafa din da ta buye a rigar ta ta dauko had’e da kibiya gudu uku.
STORY CONTINUES BELOW

Kibiyar tasa a jikin gwafar ta saita tayar motar ta harba.
Taya daya ta sace .
Kuma dauko wata kibiyar tayi ta d’an matsa kad’an ta kuma sai ta wata tayar ta harba.
Tashi ta zata koma daya gefen dan ta sace sauran ta ganshi ya fito cikin sauri.
Tsayawa tayi tana kallan sa tana k’unshe dariya.
Abdul kuwa yana ‘karasowa motar ya bude ya shiga .
Kunna motar yayi amma kuma ta’ki tafiya.
Fitowa yayi cikin rudewa yake kallan tayoyi har gudu biyu a sace .
Dafe Kai yayi cike da ta’kaici .
Ya juya yaga ba motar Mama yaga babu ta Abba babu wacce ake kai Saudala makaranta.
Kuma kallan tayar yayi sai a san’nan ya lura da kibiyoyin da suke a jikin motar.
Cike da mamaki ya ciro kibiyar yana kallah.
A ransa yace “me kawo kibiya a jikin taya? Kenan da gan’gan akayi kenan , amma wazai yi masa haka?”
Juyowar da zaiyi yaga Saudala a zaune a ‘kasa tana dariya hadda bir’gima.😂
Suna had’a ido Saudala ta mike tana rawa cikin wak’a take fad’in ,
“Ahayye na rama abinda akai min, kai ma dole ka makara yau , koma dai menene na rama.”
Gwalo tayi mai ta kuma kyal’kya’lewa da dariya .
Abdul ran sa in ya kai trillion ya b’aci , cikin sas’sarfa ya nufe ta yana huci.😡
Ai Saudala na ganin haka ta Mike a guje ta shiga parlour.
Mamana zaune a parlour ita kadai tana kallo taga shigowar Saudala a guje ta shiga d’aki ta kulle k’ofar.
Mama tace ” ke Saudat lafiyar ki ku……….., bata karasa ba taga Abdul ya shigo a fusace .
Bai tsaya kula Mama ba yayi hanyar d’akin su Saudala.
Mama ta rike baki tana kallan sa cike da mamakin me kuma ya had’a su.
Dukan k’ofar yake kamar zai bal’lata , wayar sa ce ta fara ringing yana dubawa ya dafe kai cikin sauri yayi picking yana fadin ,
“Gani nan zuwa “.
Kashe wayar yayi ya juya ya fita.
Abdul yana fita yaga drivern da yake kai Saudala ya dawo , kar’bar motar yayi ya fita a guje.
Saudala na jin fitar sa ta bude k’ofar tana dariya tana fadin.
“Kadan ma ka gani mai hancin karas.”😏
Abdul bai dawo ba sai bayan sallar i’sha , ko parlourn bai shiga ya wuce part dinsa dan yau ransa a b’ace yake.
Sai kusan karfe Tara san’nan ya fito ya shiga parlourn.
Kowa yana zaune banda Abba da Saudala da take assignment a d’aki.
Tunda ya shigo fuskar sa a had’e take , dining ya nufa ya fara bud’e-bud’e.
Mama tace “ai Abdul sai dai Fadila ta dafa maka abinci dan dazu nayi b’aki abincin ya kare .”
Abdul yace “ga wani ai anan.”
Mama tace ” uhum na Saudat ne itama bata ciba.”
Murmushi yayi yace ” Mama Saudat din ta dafa wani yunwa nake ji .”
Ya fada yana kai loma .
Saudala kam tana cikin yin assignment taji cikin ta na kiran yunwa , mikewa tayi ta fito daga d’akin.
STORY CONTINUES BELOW

Tana fitowa tayi wajan dining, bata kula ma dashi akan dining din ba sai da taji k’arar plate san’nan ta kalle shi.
Wata dariya ce ta kufce mata ai kam ta shiga kya’kya’tawa.😂
Sanin halinta yasa babu wanda yayi mata magana .
Iya kuluwa Abdul ya kulu , wato ta mayar dashi ma mahaukaci kenan.
Sai da ta gaji dan kanta san’nan tayi shiru tace ,
“Mama ina abinci na?”
Mama tace “kin gama dariyar to abincin ki gashi nan Abdul yana ci sai dai ki dafa noodles in zaki iya.”
Tace “Daman bana son cin wan’nan abincin tunda naga yaro ba ‘kashi a ciki ya da gar’gaje a ci……….
Bata karasa ba Abdul ya Mike da sauri ya isa wajan sin din wajan dining din yana zubar da abincin bakin sa.
Ai Saudala tana ganin haka ta fara dariya kamar sabuwar kamu.
Cikin sauri Fadila ta iso wajan ta rike shi tana fadin,
” Sannu bro”.
Mama tace ” Saudat yaushe kika ga yaro ba ‘kashi a ciki ?”
Cikin dariya Tace ” yasin Mama k’arya nake babu abinda na gani , tunda nima ban ci abincin ba shima bazai ci ba.”😂
Tana gama fadar hakan tayi d’aki a guje.
Da kallo suka bita suna mamaki wayo da tsokanar Saudat.
Abdul kuwa kamar ya daura hannu aka yayi ihu haka yake ji.🙆🏻♂
D’aki ya koma ransa a b’ace ya shiga zagaye d’akin.
Fridge ya bude ya dauko ruwa mai sanyi ya sha yana ajiyar xuciya.
Zama yayi akan kujera yana tunanin abinda zai yiwa Yarinyar nan.
Haka ya ‘bata lkc a zaune ya rasa abinda zai yiwa Saudala dan ya huce fushin sa.
A fili yace ” in ba zane Yarinyar nan nayi ba bazata shiga hankalin ta ba.”
Tashi yayi ya nufi d’akin su Saudala.
Yanzu babu kowa a parlourn kowa ya tashi,
Da k’arfi ya bu’de d’akin, a zaune yaga Saudala tana ya dariya ita kadai, dan Fadila taje d’akin Mama dauko littafin ta.
Tana ganin sa tayi tsit kamar ba ita ba.
K’araso inda take yayi , kunnen ta guda daya ya kama ya mur’da shi da k’arfi.
Ihu Saudala tayi tana hawaye.
Kafin tayi wani abu ya dauke ta da mari , ta bude b’aki zata kuma ihu yace ,
“Kina k’ara yi min ihu sai na Zane ki da waya.”
Dif ta mayar da kukan tana ajiyar xuciya.
Zama yayi san’nan ya kalle ta yace,
“Wato ke baza ki nutsu ba ko, ke ga mara kunya , to bara kiji indai haka zakiyi to ni kuma bazan gashi da zane ki ba.”
Cikin kuka tace ” Allah yaya Abdul ya daina .”
Cikin tsawa yace “shut up ur dirty mouth, ni zaki rainawa hankali, to bara kiji daga yau mun sa k’afar wando daya dake tunda b’aki da mutunci.”
Zaro ido tayi tace ” yasin ni ba yar’ iska bace da zansa wando d’aya dakai .”🤣
Taso bashi dariya amma sai ya basar dan in ya sake yayi dariya shikenan zata kuma raina shi.
H’ade rai yayi yace ,
STORY CONTINUES BELOW

“Ni dai na f’ada miki in kunne yaji jiki ya tsira .”
Ya Mike ya fita daga d’akin.
Tunda ya fita Saudala take kuka , ga zafin da kunnen ta yake mata , gashi yace zasu saka k’afar wando d’aya.
Tace ” wlh sai na rama nima yadda kasa jikina yana zafi yasin kai ma sai kaji a jikin ka , banza mugu dan iska.”😂
Wane plan zata kuma h’adawa Abdul kuma🤔🤣
Comment & Share
Neat Lady✍🏼
[9/3, 20:26] Sady Beb: 🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
🌴🌴🌴🌴
🌳🌳
🎄
😜 SAUDALA 🥴
❣❣❣❣❣❣❣
🇳🇬®
*_ABORIGINAL WRITER’S ASSOCIATION(‘YAN ASALI)_*📚✍🏼
[❄Dance above the surface of the world,let your thought lift you into creativity that is not hampered by opinion.]
_*DON’T 4GET VOTE,COMMENT AND ALSO US ON WATTPAD*_
*@ABORIGINALWRITER’SASSO.*
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*NEAT LADY*✍🏼
*Bismillahir rahmanir rahim*
29&30
Da sallama Saudala ta shiga parlourn.
Yana zaune a kan kujera ya d’aura laptop akan center table yana dan’nnawa , da alama aiki yake .
Da’kyar ya amsa sallamar ko dagowa bai yi ba ya cigaba da aikin sa.
D’aya daga cikin kujerun Saudala ta zauna .
Cikin sanyin murya tace .
“D’aman Abba ne yace nazo na baka hakuri .”
Tana gama f’adar hakan ta Mike zata fita .
“Ke”!
Abdul ya f’ada cikin tsawa lkcn da take k’oka’rin b’ude k’ofar.
Juyowa tayi tana kallan sa.
Yace “Dawo ki zauna .”
Ganin yadda ya h’ade rai yasa Saudala ta koma ta zauna a inda ta tashi.
Tsawa ya daka mata yace .
“S’akko k’asa ki zauna ko na b’alla ki.”!
Ba k’aramar tsora ta Saudala tayi ba dan bata son tsawa.
Cikin sauri ta zamo daga kan kujerar ta zauna akan carpet.
Abdul yace ” Haka ake bada hakuri a g’arin ku”?
Saudala tayi shiru bata amsa ba.
Abdul yace “ba magana nake miki ba .”
Kai ta g’irgiza alamun A’a.
Ganin tana neman ta mai d’ashi mahaukaci kawai sai ya zare belt ya nan’nada a hannun sa.
Yace ” naga alama in ba d’ukan ki nayi ba zaki yi magana ba .”
Cikin kuka Saudala tace .
“A’a”.
Yace ” sabida kin raina Abban ne kome?”
Saudala tace ” A’a”.
Yace “to mene ne?”
Shiru tayi bata amsa ba .
STORY CONTINUES BELOW

Mikewa yayi k’amar zai d’ake ta .
Cikin rawar murya Saudala tace .
“Da…..Allah….ka…yi …….ha….k..u..ri.”
Yace ” bazan hakura ba tunda ke dai b’aki da kunya.”
Tace ” nafa baka hakuri dan Allah yaya Abdul ka hakura.”
Komawa yayi ya zauna Yace.
“Me yasa kika r’aina ni.?”
Tace “na dai’na.”
Murmushi yayi yace “na fahince ki akwai tsoro san’nan akwai rashin kunya.”
Laptop dinsa ya cigaba da dan’nawa , ita kuma ta h’ada kai da guiwa tana fadan kuka.
Kallan ta yayi san’nan yace .
“Tashi ki ban waje .”
Ai kafin ya rife b’aki tuni ta Mike taje b’akin k’ofa.
Sai da ta r’ike handle din k’ofar tace .
“An yi maka rashin kunyar kuma duk abinda kayi min yanzu yasin sai na rama , mugu kawai .”😂
Tana gama f’adar hakan ta fice a guje .
Shikam Abdul mamakin ta yake an’ya kuwa bata da al’janu.
Da gudu Saudala ta shiga d’akin su tana mai da numfashi.
Fadila ta kalle ta tace .
” Lafiya naga kin shigo da gudu?”
Juyawa Saudala tayi dan ita bata masan tana d’akin ba.
Saudala tace ” babu komai. “
Fadila tace ” to Allah ya kyau’ta.”
Washe gari ranar asabar da wuri Saudala ta tashi tayi wanka ta nufi kitchen dan ta taya Mama aiki.
Da yake ba makaranta haka Saudala ta dinga game a waya kafin lkcn islamiyya yayi.
Fadila ce ta fito tace “Mama nikam yau ina yaya Abdul ya shiga “?
Mama tace “ai da sas’safe ya tafi Adamawa”.
Saudala tana jin ance Adamawa sai kawai ta fara kuka .😣
Mama ta kalle ta tace .
” Saudat me ya faru?”
Cikin kuka tace ” ina son ganin Baba da Umma na da’de ban gan’shi ba .”
Fadila ta dafa ta tace .
“Ki daina kuka sis nan da wasu kwa’naki Baba zasu dawo nan , kiyi hakuri ki daina kuka.”
Share hawayen ta tayi bata ce komai ba.
*****
Abdul kuwa tunda ya isa Adamawa ya ‘karasa gidan Baba .
Baba yana zaune a tsakar gida yana cin abinci Umma tana d’aki .
Sallama Abdul yayi ya shiga gidan .
Baba yana ganin sa ya mike yana fa’din.
“Abdul kai ne sannu da zuwa .”
Zama Abdul yayi yana murmushi.
Sosai Baba yayi farin cikin ganin d’an nasa .
Bayan sun gaisa da Umma Abdul ya huta yaci abinci suka fita shi da Baba.
Wayon gonakin Baba dana Abba suka yi.
Shi kansa Abdul yaji d’adin zuwan sa g’arin .
Bayan sun koma gida Baba yace.
STORY CONTINUES BELOW

“Ina ko Saude nasan tana nan tana tsokanar da ta saba .”
Dariya Abdul yayi yace.
“Ai yanzu ba Saudat din da bace ai in ka ganta baza kace ita bace .”
Cikin jin da’di Baba yace .
“Alhamdulilah haka ake so ai.”
Shikam Abdul ya f’adi haka ne sabida hankalin Baba ya kwanta.
Baba yace “Abdul wan’can sati naje Kano nayi binkice akan Yarinyar da kake neman aure , a yadda aka bani bayani ha’ki’ka iyayen ta masu mutunci ne kowa yana yaban mahaifinta sosae, ina so a cikin wan’nan wata zanje mu gana da iyayen ta akan maganar biki, nan da yaushe kake so asa ranar?”
Sun’kuyar da kai Abdul yayi yana sauraren sa.
Baba yace “kayi shiru baka ce komai ba .”
Cikin kunya Abdul yace .
“Baba duk lkcn da yayi muku yayi min nima.”
Baba yace to shike’nan zan muyi waya da hamma umar din naji ta b’akin sa.”
Abdul yace “to Baba”.
Haka suka wuni suna shan hira.
Washe gari Abdul ya baro Adamawa cike da tsara ba.
***
Da magariba Abdul ya shiga garin Abuja .
Ya isa gida ya nufi parlorn Mama .
Gaisa wa kawai suka yi Dasu ya juya ya koma part din sa dan a gajiye yake.
Da safe ta kama Monday Saudala an yi shirin makaranta amma har lkc ya kusa kurewa driver bai zo ba.
Gashi Abba da wuri ya fita balle ya sauke ta .
Abdul Mama tayiwa waya tace yazo ya kai Saudat makaranta.
Bayan Mama ta gaya masa ta koma d’akin ta .
Shi kuwa Abdul yana sane ya ‘ki fitowa da wuri har sai da Saudala ta makara.
Ko da suka shiga motar ko kallan ta baiyi ba itama kuma bata ce kala ba.
Suna zuwa ya sauke ta ya juya.
Saudala tana shiga taga ana d’ukan makara ga Saudala ta tsoron d’uka, tana ihu aka yi mata wan’nan d’ukan.
Ai kam ta dau alkawari sai ta rama abinda yayi mata.
Haka ta dawo gida ranar ko karatun bata gane ba .
Bayan kwana biyu da yam’ma Saudala tana zaune a parlour Abdul ya shiga cikin sauri.
Mama tace ” Abdul saurin me kake yi ne haka?”
Yace ” Mama waya aka yo min yanzu ana neman mu shine zanje na shirya na tafi.”
Yana gama f’adar hakan ya fita.
Mama tace ” Allah ya bada sa’a.”
Saudala najin haka tayi murmushi tace .
“Yadda ka sani nayi letting a makaranta kai ma yau sai kayi letting.”
Mikewa tayi ta nufi d’aki.
Me kuma zata yiwa Abdul🤔😂