SILAR GIDAN AIKI CHAPTER 26
Biki nata matsowa, mahaifin Mansur yasa an gina musu gida kusa da nasu, Flat ne me 3 bedrooms gidan ya hadu matuk’a se wanda yagani+ Tunda bikin ya matso Mansur kullun yana makale da nazeefa a waya ba abunda ke rabasu se bacci shima cikin baccin to mafarkin junansu sukeyi Bangaren Mubeen kuwa, Tinaninshine ya rabu biyu yanason Ameerah amma wata zuciyar tana ka hakura da ita kawai ka nema wata, mubeen ne zaune a wajen ginin makarantar da akemai yaji bazai Iya hakuraba, shi duk abunda zai faru zaije ya sanar da ita yana sonta idan ma wani ya rigashine ya sani dan kar yai 2 zero, Daukar motarshi yayi ya tafi kofar gidan su Ameerah ya tsaya, wani yaro ya Kira yacemai please ya shiga ya ce Ana kiran Ameerah yaron yace tom Shiga yayi yaron yai sallama yace wai ance Ameerah tazo, Nazeefa suna zaune da Ameerah suna hiran yanda bikin Zai kasance “Ameerah tace Ni kuwa? Yace Ameerah akace, Amira bata yardaba dai tace ya mutumin yake? Yaron yace Farine dogo Dukansu basu kawo Mubeen bane, Nazeefa da rawan jiki ta dauka gyale tace Bari na rigaki ganinshi idan yamun shikkenan ko kawata nasan zai miki kema Ameerah binta da ido tayi tana dariya tace kawata bakida dama wlhi ganinan fitowa nima, AI bata jirataba ta dauka gyale ta fita Kanshi na kasa dan kasa dagowa yayi sui 4 eyes, Sallama yai mata kamar haka, Salamu Alaikum gimbiyar Mata! nasan zaki mamakin ganina anan Kiyi hakuri yaji anmai shuru D’ago kan da zaiyi sukai 4eyes da Nazeefa Tace Bro dama Kaine? Dan tsuke fuska yayi aranshi yana da yasan zai sameta da baizoba, Nazeefa kuwa kallonshi takeyi abubuwan da suka faru a da take ganinshi a idanta, Da sauri tabar wajen Zata shiga cikin gidan kenan sukaci Karo da Ameerah, Har Ameera na tsokanarta tace kinga guy din yayi kuwa? Wani kirkiro murmushi tayi tace inkinfita zakiganshi Nazeefa shugowa dakin Su Ameerah tayi, Waje ta samu ta zauna tafara tinanin yakamata tabar kishin nan, Mubeen bazai taba zama nataba, Kuma da take ganin shi mai laifine ai dukansune da laifi, tunda har itama zatai aure to why not tabar shi shima ya aura kawarta inhar tana sonshi Kuma da ace matar natuba tana rasa miji tabbas itama kuwa baza’a auretaba so tacire komai a mind dinta, Kawai ta fuskanci gaba, Allah ha yafe mana gaba daya Ameen Dakko wayarta tayi takira Mansur suka Fara hirar soyayya taji sanyi aranta, har yana tsokanarta saura kwana nawama? Tace kafini sani sukai dariya dukansu *** Ameerah kuwa tunda ta fita taga mubeen gabanta ya Fara fadi, Kasa tsayawa dakyau tayi, Sallama yai mata ta amsa muryanta na rawa Murmushi yayi yace like you’re not comfortable ko? Girgiza kai tayi alamun a’a Magana suka suma ya sanar da ita manufar zuwanshi ne, shi da gaske yake aurenta yake so yayi, Aran Ameerah taji dadi sosai dama ba wani soyayya take soba indai miji ya fito da gaske ze aure ta shikkenan, Amma tadan yi shuru agabanshi kamar tana nazarin Wani Abu Malama Ameerah yace Ya akaine ko dai akwai takurane? Cemai tayi a’a kaga yanzu bazan yanke hukunci ba dole senayi magana da magaba ta na, yace hakane zuwa yaushe zanji amsarki? Tace kamar Sati daya Yai murmushi yace Allah yasa muji alheri tace Ameen sannan ta shige gida Shi kuma driving ya Fara yahau kan titi yana tinanin AI dakyar zata amince saboda yaga Nazeefa a gidan and he is sure ta fadama mata abunda ya taba shiga tsakaninsu Yar karamar tsaki yaja yace tabbas ka zama na kirki ma babban abune saboda yau da gobe duk abunda ka aikata seya fito, Allah ka yafemun yace Sannan ya Fara istigfari har ya Isa gida be dena ba Ameerah jikinta a sanyaye ta shugo dakin ta tadda Nazeefa na waya Fizge wayar tayi ta kashe tace mayyar love bakya gajiya? Nazeefa tace laaa dama Ana gajiya da abun da kakesone? Ameerah tace a’a Nazeefa tace kingani Ameera tace Amaryanmu kinsan menene? Nazeefa tace a’a Ameerah tai shuru ta kasa fadan ma Nazeefa maganar Wani murmushi Nazeefa tayi tace kinwani yi shuru ni nasan komeye, Ba auranki yakeso yai ba? Maganar taba Ameerah mamaki sosai gashi ba dama ta karyatata, Tace Kamar kinsani cikin wani irin murya Tace Ni bazan Iya auranshiba saboda ke nasan you still love him shima haka so Ni bazan Kara fita bama gaskiya Nazeefa ce ta dafa kafadarta tace wayace miki haka? Kinga sonshi idonane? Ko kingani a idonshi? Kawai kinsan Mu yan uwane dole akwai so dinnan amma wallahi ki aureshi bakomai indai kina sonshi. Kallonta tayi cike da mamaki, Bata taba tinanin hakan ba, rungumeta tayi dan farin ciki, Nazeefa tace bakomai kawata kin wuce haka Allah ya tabbatar da alheri Tace Ameeen Tunda Nazeefa ta dawo gida hankalinta na gun Mansur jitai tana bukatar ganinsa, Dan haka ta kirashi tace yazo, Yace kamar kin shiga raina nima I really want to see you, murmushi tayi tace tom Seka zo I love you darling muaahhh Tashi tai a dakinta ta shiga room din mahaifinta tace baba na kara dawowa+ Yana kwance yanajin radio Ta shugo yace Yar baba ya akaine, Tace kan maganar gidansu Ameerah plz Murmushi yayi yace AI tun jiya akasai musu gidan anadan Kara fentine sai yasa nasan zuwa gobe zasu gama se muje gaba daya mugani, gidan nanan kafin a karasa gidan su inda suke Rungumeshi tayi tace you’re a darling dad, kasani farin ciki sosai, Yace bakomai Yar baba Daki ta shiga ta kwanta a gado iskan fanka na shigarta tanajin dadin yanayin, Wani murmushi tayi Tace nagodewa Allah da yasa iyayena suka amsa maganata Dan Allah nayi kuma inason Mubeen ya gane Na wuce shi a komai, Dan nasan tabbas Shima yanada niyyar gyara musu Ko chanza musu gida Kwance take tana kallon silin, Tinanin Mansur ya fado Mata, smiling tayi sannan ta fara tina rayuwarta na da, Alhamdulillah tace Tabbas ba Wanda ya dace dani sai Kai MANSUR tana cikin tinaninshine Phone dinta ya Fara ringing, dubawa tayi taga LOML murmushi tayi tai picking Hello Sweet Heart ganinan a kofar gidanku, OK My love tace ganinan fitowa yace alright Tashi tayi ta chanza rigar da tasa, tasa wata atamfa, Tai daurin chakwar (tuge kaga tsiya) sedan gyalenta a kafada tai bala’in kyau, Flat shoe ta dakko ta fesa turara ta shiga tace wa ummanta da babanta Zata Dan fita sukace OK Tunda ta fito Mansur ya kafeta da ido kamar yaune ya fara ganinta, Jiyai ta karamai kwarjini kodan besaba ganinta da atamfa bane, ga dinkin ya amsh jikinta ko Ina na jikinta ya fidda shape kamar ka saceta ka boye Tabarakallah Masha Allah yace a mind dinshi Tana matsowa bude mata kofar motar yayi ta shugo ta zauna irin a giccen nan ta gefe tana facing dinshi Kamshin turaranta ya dake hancinshi, Lumshe ido ya farayi yace Sannu da zuwa gimbiya, Na taso ki ko cikin Rana? Soma magana tayi Murya kasa kasa tace ko kadan habibi nah, Ina fatan kananan lafiya Bin lebenta yai da ido gashi yasha lipstick, yace inanan lafiya sumul balle dana ganki se naji kamar ankaramun power (Karfi) murmushi tai ta kasa ma magana Yace Baby dama nazone mui maganar Bikin wani event da wanne kikeso ayi? Kara gyara zama tayi tace kasan dai bawani frnds gareniba, Kamu se bridal shower kawai zanyi, Yace Alright bakomai Amma kamar nawa zai isheki da komai da komai tace eh senayi calculating Zan maka text yace ok Suna cikin hakane Abdallah ya kirashi yace yana Ina? Yace wlhi ganinan gidansu Nazeefa Abdallah yace Kaimun congrats dazu munje asibiti Madan nada Ciki Wani ihuuu Mansur yayi yace Masha Allah, Nayi muku murna, Allah ya inganta yace Ameen Matar Abdallah ce ta fisge wayar tace Ango ai Ina fushi dakai ko amarya baka taba kawomun itaba to bazanzo bikinba nama fadama Afuwan yace Mata inshaa Allah yau Zan kawota, tace banaso seda na roka Itama Nazeefa ce ta amshe wayar tace Yar uwa kiyi hakuri gamunan zuwa tace to Allah ya kawoku Matar Abdallah ta bashi wayarshi, itama Nazeefa ta ba mansur wayarshi, Mansur yacewa Abdallah matan nan fa da gaske suke, Dukansu sukai dariya sannan suka kashe wayar Are you ready mutafi yace? Tace nop bare na shiga na sanar dasu Umma yace hakane Shiga tai ta samesu suna zaune tace Dan Allah Abba zamuje gidan matar abokinshine shine nace bari na tambayoku Umma tace to bakomai kardai a dade kuma a kula sosai tace Inshaa Allah, Baba ma yace saita dawo. Daki ta shiga ta chanza gyale tasa babba sannan ta dako jakarta da wayarta ta fito Kyau yaga ta karamai sosai, bude kofar motar tayi ta shiga, Mansur sake baki yayi yace A’ah wata kwalliyar aka sake Dan ingani, Tace laa kawai gyale na chanza fa, Yace gskiya kinyi kyau sweet Heart, Matso muyi hoto, Matsowa tai ya dakko IPHONE X dinshi sunata Snapping pics sun bala’in yin kyau, sannan ya dauketa itama ita kadai WhatsApp ya shiga Yasa a status maza da abokan arkinshi se comments sukeyi wai sun bala’in yin kyaiu gasu perfect match sedai yai murmushi Driving yafarayi ahankali sunajin sautin wakar Umar m Sharif har suka Isa gidan Suna isa Abdallah ya fito yai musu barka Da zuwa sannan yai musu iso har falon, sunyi kyau sosai, Abdallah kasa hakura yayi yace Kai Masha Allah kungankune wallahi kamar anyi, Mansur yace kamar anyi mene? Abdallah yace auren mana, Nazeefa rufe fuskarta tayi Dan kunya Mansur kuwa yai murmushi suka shiga dakin Mansur yace Ina madam, fitowa tayi tace ai ba ruwana dakai amaryace tawa, Mansur yace Duk kuyi ku gama, Maman unborn Itama rufe fuksa tai Dan kunya tace Amaryanmu tashi Mu shiga ciki abunmu, room din matar Abdallah suka Shiga Sannan taje ta kawo masu Abdallah couscous da miyan kaji, Se ruwa da 5alive ta jiye masu sannan ta shiga da nasu ciki Nazeefa na gani tace laa dama yunwa nakeji, Matar Mansur tace yauwa haka nakeso Ashe ke Yar garice da wasune sai suce wani yunwa Nazeefa tace baruwana nidai bana wasa da abinci tace yauwa kawata, taci ta koshi sosai sannan suka Fara hita, tora kofa sukai abunsu Abdallah yace Kaga matan nan fa karsu hada mana Kai, Mansur yace kaima kasan sedai kar a kuma amma mata se Allah ai sukaci dacin abincinsu suna hira Matar Abdallah ne tace saura befi kwana 6 bako? Nazeefa tace eh Wallahi sannan tace wani shiri kikeyi? Nazeefa tace se ahankali dama gobe nakeso naje gidan kawata intasan wani gidan gyaran jikine ta Kaini Matar Abdallah tace kinzo gidan so karki damu Yanzu dai bani number wayarki zuwa gobe Inkinshirya Zan kiraki sannan kuma ta bata wani sirri tace idan kinkoma gida ki jika kanunfari kinasha Da Zuma idan ma kinada madara ki Kara akai kisha Tace Kai nagode Sosai Basu gama magana ba sukaji Abdallah na kwankwasa kofar sukai shuru Yace Angama gulmar Matarsa tace bamu gamaba Dan dai ka buga mana kofane yai Dariya Yace Amarya kizo angonki na jiranki Fitowa tai suka hada ido da mansur ya kashe mata ido sannan ya daga mata gira yace I love you ahankali, tana kallon labensa tagane me yace Smiling tayi taji kunyarta ya karo Rakosu sukai har haraban gidan seda sukaga sunshiga motar sunfita sannan suka dawo cikin daki Matar Abdallah tace Ina ya samo wannan kyakkyawar yarinya haka? Yace it’s a long story semun zauna tace Masha Allah Mansur suna tafe suna hirar soyayyarsu gwanin sha’awa Har kofar gida yazo ya sauketa, Bude kofar tayi bayan sunyi sallama Zata fita kenan ya janyo mata gyale, tsayawa chak tayi, sannan ta waigo, Yace Love wallahi kamar karki tafi, Smiling tayi tace Dear saura kwana nawane? Murmushi yayi yace Kwana 6 Ko yana magana yana lashe baki yana kare Mata kallo daga sama har kasa hade da wani kashe mata ido, tuni ta gane inda ya dosa tace Love, Allah ya shiryaka, Murmushi yayi yace AI Indai akan sonkine I think I’m in the right way, tace uhmm tai tafiyarta gida+ Jiyai kamar ya bita amma ba hali, seda ya bari ta shiga gidan da kusan 5 mins sannan ya tada motarshi yai gida Koda yaje gida Daki ya shiga yai wanka yasa jallabiya na shan iska yai alwala yai sallah yai karatun qur’ani sannan yaita addu’a Nazeefa kuwa tunda ta shiga Gida itama Room din iyayenta ta shiga ta samesu sunata kiran wayar yan uwa da abokan arziki Wanda aka Zauna tare, suna Sanar da su bikin Nazeefa satin nan mai zuwa. Nazeefa Sannunku da gida tai musu sukace yauwa har kindawo? Tace eh, Sukace madallah Dakinta ta shige itama tadan watsa ruwa tasa Riga bame nauyi ba, tahau gado tai kwanciyarta, Lalubo wayarta tayi cikin jaka taga, Tetxs kusan guda 10, fara karantawa tayi tai murmushi aranta tace M.T sarkin soyayya itama fara aikamai tayi, Shima yana gani yaji dadi sosai aranshi Wunir ranar dai ba wani baccin kirki sukai ba dan sun kusan raba dare suna chats na soyayya Washe Gari Misalin karfe 10:00 na safe baban Nazeefa yace ta kirawo kawarta shin suna gidane? Nan Take Nazeefa ta kira Amerah ta tambayeta tace yes suna gida, Nazeefa tace OK, Sanar da iyayanta tayi sannan suka Tafi gaba dayansu, Gidansu da akasaima su Ameerah suka Fara zuwa, Nazeefa tace Masha Allah kai gidan ya yi ba laifi, 4 bedrooms ne se falo guda biyu ga kitchen da dakunan maza har biyu kowanne da bayinshi ga Dan madaidaicin tsakar gida harda shukan gwanda da gwaiba lol, Nazeefa tace Allah ya Kara daukaka baba Yace Ameen kema Allah yaiwa rayuwarki Albarka, rike hannunshi tayi tace Ameen baba na, Umma hafsatu ma tace Masha Allah Fitowa sukai suka wuce gidansu Ameerah, Nazeefa ce ta Fara shiga ta sanar dasu da iyayanta suke, Allah yasa baban Ameeran nanan fitowa yai, yai musu bismillah su shugo, Bayan sun shugu sun gaisa nan Baban Nazeefa ya sanar dashi abunda sukazo dashi Baban Ameerah yace banfahimce kaba gida nawaye? Wani gida kuma? Baban Nazeefa yace Gida muka baku halak malak, Nan gidan gaba daya ya kaure da murna Dan dadi abunda basu taba tsammanniba, lalle mutanan nan sun cika yan halak, Ameerah kuwa kasa magana tayi Dan dadi, kallon Nazeefa kawai takeyi, tabbas Wasu kawayen yan amanane wasu kam Kullun burinsu suganka cikin wahala, Rungumo Nazeefa tayi tana kuka tana mata godiya tace kidena wallahi, Mu godewa Allah ne kawai tace hakane Baban Nazeefa yace to Alhamdulillah sai ku tashi gaba daya muje gidan ku gani sannan yaba mahaifin Ameerah takardun gida, Dukansu suka tashi suka tafi, sukaga gidan Masha Allah, Wayyo Dadi, Yara se tsalle suke sundawo sabon gida, Ga bishiyan gwaiba da gwanda ga tiles se kyalle yake, Tsalle suke tayi suna yeeehhh muma muna zama yan gayu, Nazeefa na tsaye ta tino da rayuwarta nada irin wahalan da tasha Aranta tace nima hardani na zama yan gayu lol, Maman Ameerah tai musu Godiya sosai, tace inshaa Allah yau sai kwanan sabon gida, Yara suka Kara tsalle, *** Mansur ne ya Kira Nazeefa akan cewar yauma yanason ganinta, tacemai please yayi hakuri, Ga abun dake faruwa Su Ameerah sun koma sabon gidansu so da ita ake komai bazasu sama daman haduwa ba, Yace please ya saukar da murya kamar me shirin yin kuka yace inane gidan nazo kinsan yau bazan Iya bacci inbangankiba? Tamai kwatance yace OK kinachan dai ko? Tace eh yace at anytime Zan Iya zuwa tace OK I love you yace, I love you too STORY CONTINUES BELOW Matar Abdallah ma kiranta tayi tace ya maganar gyaran jikin zakizo yaune? Tace Nop munshiga kasuwa sai zuwa gobe inshaa Allah tace to bakomai Allah yakaimu **** Yara nata murna, Nan Baban su Ameerah yaje ya samo mota aka fara fitar da wasu kayan, Wasu kayan kam Sedai barinsu a gidan akai Dan sun tsufa, Dasu Nazeefa akai komai, sannan mahaifin Nazeefan yaje aka siyo masu abincin shinkaga buhu 4 masara ma 4 catton na taliya 10, galan manja da mngyada bibbiyu kai kayan abincin da duk ake bukata haka ya siyo musu, Ranar yasha addua sosai Dan har masallaci seda akaimai addua Iyayan Ameerah sunji dadin da basu taba jiba, sukaiwa makota bankwana suka koma sabon gidan, suka kulle gidan saboda Ameerah nada yayyi maza 2 in zasui aure saisu gyara gidan kawai Alhamdulillah Ameerah itama tace what a blessed day! Suna zaune Da Ameerah, Nazeefa wayarta yai ringing tana dubawa tace please Amirah zo muje angon ne! Tashi sukai su biyu suka fita, Mansur har gigicewa yayi da yaga Amirah basa kama sosai amma tafiyarsu da komai daya, Ikon Allah yace Har suka karaso, Amirah ce ta Fara gaisheshi ya amsa yanda take magana kamar Nazeefa, tacemai ya jiki yace Alhamdulillah na warke Nazeefa tace itace kawata Amirah da nake baka Labari, ita kadaice kawata, Kara kallonta yayi yace Ayyah muna haduwa ai amma bantaba Mata kallo irin nayau ba har Dan kamafa kukeyi, Nazeefa tace haka ake cewa, kasan kawance Inna gaskiyane Hakane Dama yace tabbas kuwa Yanzu dai ya kike? Kawarmu kema kina Lafiya? Amirah tace lafiya lau Mansur beson komai game da gidan ba yace ya sabon gida? Allah yasa albarka Tace Ameen, ka karawa Nazeefa godiya wallahi iyayanta suka sai mana Kurawa nazeefa ido yayi abun na bashi mamaki, yana mamakin irin Zuciyar nazeefa Nason tamako, halin Nazeefa dana iyayanta suna burgeshi, waennan tabbas yan Aljanna neh, Kallonta yakeyi amma ya sunduma cikin tinani seda Nazeefa tasa mai hannu a fuskar irin tana waving dinnan sannan ya dawo daga tinanin da yake Yace Kai Amarya ai ko fadamun kyayi, Tace afuwan Angona yace ni Sena Shiga na gaisheshu inbahaka bazan hakuraba Ameerah taji dadi sosai aranta tace muje to, Nazeefa tace kunya nakeji, Amirah tace kunyar Mara kunya ba, Mansur yace help me tell her kawarmu Tare suka shiga gidan, Ameerah tace wanda Nazeefa zata aurane sukace Masha Allah, Allah Sanya alheri…. Sannan suka fito, Amerah kuma ta zauna a gida cos tasan akwai hiran da zasui na masoya Koda suka fito Mota ya bude masu suka Shiga, Ya kunna A.C yana kallon yanda AC ke shigarta aranshi yace Amarya kenan, ni kuma nace zakai ma yi bayani ne Lol, hira sukai Sosai, irin kallon da yake mata taji she’s not comfortable at all, cos kame kame ta Fara kamar Mara gaskiya tace please kallon ya isa haka Dan Allah, yace say wetin? Ahani kallon Abu na, Rufe ido tayi tace please Naaaaaaaa! Yace OK still bedane kallontaba Karkata wayarta tayi taima Ameerah flashing sai gashi ta fito, Dena kallon Nazeefan yayi sannan ya sauke glass din, Ameeah tace gani! Tace yeah dama maganar Event din da za’ine kamar nawa zai Isa Mansur aranshi yace Nazeefa ce kenan ta kirata, cos kwata kwata yanzu basui maganar event ba, Ameerah tace ehh kinsan ba wasu kawaye ne da muba kamune se bridal shower kuma I think 200K ma yayi yawa, Mansur yace 200K yayi yawa fa Kikace, Nan Ameerah ta tino fa Ashe mansur gidan kudi ne! Tace eh, yace A a ga 500K dai ya basu a cikin leda yace idanma basu isaba kuimun waya, tace OK Nazeefa tace to zamu tafi yace OK, Saura kwana nawane? Ya na magana yana kallon boobs dinta Tace 5 ne fa, Da alama za’ai fama dakai ko? Dariya yayi seda yaga sun shiga gidan sannan ya wuce Koda suka shiga gidan hirar yanda bikin zai kasance sukai, Nazeefa tace kawata nifa gabana fadi yakeyi wallhi, Ameeerah tai kasa kasa da murya tace bari na Fara miki waqa tun yanzu…ke kikace kinaso da bakice kinaso ba da ba’abaki shiba…Nazeefa daukar filow tayi ta jefeta dashi tace kema zaki sani ay Nazeefa tace ki rike kudin nan gobe zamu hadu semui magana tace OK.. Misalin karfe 6 na yamma Nazeefa tace zata tafi gida, Ameerah sun fito kenan Zata rakata suka ci Karo da Dr Bashir Abokin Mubeen kallonsu yayi, Ameerah ta wani gallamai harara, Nazeefa kuwa Tsaki tayi tace Banza kawai Dr Bashir kuwa kasa magana yayi aranshi yana wannan gidansu waye badai Nazeefa ba cos yasan tafi karfin gidan nan Labewa a wani wajen yayi har ta rakata ta sama napep, Yaga Still ta dawo ta shiga gidan Dr Bashir yace Alhamdulillah tazo ma gidan sauqi cos kusa damu take, ai soyayya sabuwa zanzo maki dashi…….hmmmmm Muje ZUWA