SIRADIN RAYUWA CHAPTER 5 BY SAFIYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA
Babban club ne na masu aji da naira wanda yake hada manyan yara daga qasashe daban daban matasa masu jini a jiki,daga can wani kebantaccen waje zaka hangeshi zaune saman teburin daya qunshi kujerun zama guda biyar,kowacce kujera akwai mutum akwai,saishi cikon na biyar din dake zaune tsakiyarsu,ba abinda yake bankawa cikinsa hayaqi,wanda duk sanda yazuqa ya fesar sai kaga wani dunqulallen farin hayaqi yatashi sama yacure guri guda kai kace an hura wutar itace ne da
jiqaqqen itace ko wutar ta mutune tana neman agajin fifita,daga saman teburin akwai saura saura da burbushin wadanda yasha masu tarin yawa,bayaga kwalbar abunsha wanda babu ko kokwanton cewa ba zallar abunsha bane da baisa buguwa ba.
“Kamal…..ka tsaida wannan hayaqin da kake bugawa cikinka kamar babur,tell us me yake faruwa,kasoma gaya mana kuma but u keep quite”.
Sauran ta hannunsa yayiwa kyakkyawar zuqa sai gata ta qare,yadorata saman table din yakashe kamar yadda yayiwa sauran,kana yafeso dukka hayaqin waje ya qarawa sama hazo sosai sannan ya muskuta ya gyara zamanshi
“Kamar ni….ni prince AA zai kora daga gidanshi?”
“What!” Suka fada kusan a tare kowa yana dubanshi,baqinciki yasake cika kamal yanajin takaicin yadda ya tozartashi cikin abokanshi dasuke sake ganin girma da qimarsa sakamakon cewa azeez din dan uwanshi ne na jini
“Amma baaabaa….ba cousin dinka bane?” Kai ya gyada
“Cousing dina ne amma yayimin haka” ya qarasa fada cikin dacin rai,daya daga cikin matasan wanda shima yaciro tashi tabar yakunnata yasoma busawa sannan yace
“Ni dama guy din fa ya tsayemin a rai,kishi nake dashi wallahi yadda kasan nasa bakin bindiha na harbeshi,kwarjininsa yayi yawa,kamar komai an bashi a rayuwa,amma….yakamata kamal kadauki mataki,dont let it to be in vain” kai yake jinjinawa,abinda yakwana biyu yana kitsama ranshi kenan yadda zai jawo abdul’azeez ruwa,ya tabbatar idan hakan tafaru zasufi samun sakewa suyi duka yadda sukeso cikin walwala tunda shima yazama dan hannu
“I know his week point,na rantse da Allah saina rama,saina dauki fansa….ba lalacewa yake gudu ba?….” Saiya saki murmushin jin dadi kana yasanya hannunsa yadaki table din dake gabanshi,dukkaninsu sun fahimci me yake nufi,don haka dariya ta gauraye wajen,daya daga ciki yasake cewa
“Maan…kace kwanan nan muma kuttun farinjininmu zai fashe if he join us,zamu sake zama big boys fa”
“Qwarai kuwa”
“Amma kunyi suya kun mance da albasa,banji kunyi magana kan hanyar da zaku jawoshin ba,aikine mai wahala idan kun manta na tuna muku,kai kamal kafi kowa sanin waye prince azeez”.
Kai ya jinjina idanunsa akan matashin
“Nafi kowa cikinku sanin wannan….nakuma tsara yadda zamu gudanar da komai,kamar yadda nasan yanayinsa zamu hilaceshi da mace,amma mace wadda tacika ta isa mace,anan matsalar take,ban gano wata mace wadda zata dace da plan din ba,takuma jure shi” shuru ne ya ratsa tsakani,kowa na nazarin maganar kamal din,don a nan gizo yake saqar
“Wow!…..na tuna….minal” daya daga ciki yafada da sauri har yana zunkudawa gaba kan kujerar da yake kai,da alama abinda yatuna din yayi mishi dadi
“Wace minal?” Kamal ya jefa masa tambayar
“Itace yarinyar da take da interest akan prince harta kasa boyewa ta bayyana mishi,amma ya tozartata cikin jama’a,na tabbata ina da yaqinin idan mukaje mata da wannan maganar komai zai tafi”
“Ya take?” Kamal yasake tambayarsa,gira ya dage masa yana sheqewa da dariya
“Minal ta hadu,idan nace maka haduwa ina nufin ta hadun din”
“Good” kamal yafada yana murmushi,yabude baki zaiyi magana wayarshi tadauki kida,yaja dan tsaki kana yacirota yana duba mai kiran,mahaifiyarsa ce,saboda haka ya daga.
“Nayi qoqarin kiran me martaba na shaida mishi abinda ke faruwa,saidai kuma yayi tafiya baya qasar kaisa,amma gobe xai dawo,dole yaji wannan maganar,tunda shi bashi da mutunci,baya ganin kowa da gashi,kana dan uwanshi har zai iya korarka daga gidan saboda yasamu daurin gindi daga mahaifiyarsa?,na shaida mata abinda ke faruwa tacemin wani wai zata bincika?,bincike na meye?”
“Rabu dasu mom,na rantse saina dauki fansa kan abinda yayimin din,karki damu na gana tsars yadda komai xai gudana”
“Kome zakayi kayi,amma karka sake kayi abinda zai nakasta shi ko illatashi”
“Baki da damuwa,sai munyi waya” yafada yana katse kiran yakoma wajen abokan nashi sukaci gaba da tsara yadda komai zai gudana.
☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️
A washegari cikin gidan nasu akayi ɗan ƙwarya ƙwaryar wuni,itadai bilkisu bata fasa zuwa makaranta ba bare wajen aikinta,don bataga wani sabon abu ba game da lamarin,hakanan batasan zaman me zatayi cikin gidan ba.
Sanda tadawo kuwa kusan babu kowa sai ‘yan kawo amarya,tadinga bin tsakar gidan da kallo yadda akayi kaca kaca da abinci,ta dinga jin ciwon hakan cikin ranta,don a qalla abincin idan aka tattara yakai abincinsu na kwana da kwanaki wanda mahaifin nasu bai iya cida su,amma saboda aure yau gashi abinci a gidansu har soro,haka ta tsallake tawuce cikin gidan.
Taji dadin yadda tasamu hannatu ta killace qannen nata duka a daki,data shigan sai tayi qoqarin sakin fuskarta,har zuwa lokacin data gama duk abinda zatayi,tasa kowannensu yasamu guri ya kwanta,ba jimawa kuwa Allah ya taimaketa dukka sukayi bacci,don haka ba’a kunnensu akayi badaqalar shigowar malam bilya da kazar amarya babu ta umma katti ba,da qyar su batulu suka shiga fadan suka sasanta yawuce abinsa dakin amaryarsa yana rawar qafa kai kace a ranar yasoma aure.
Sati guda amarya tayi tana cin amarci kai kace budurwa ce a maimakon kwanaki uku,cikin kwana bakwai din gidan babu yunwa babu qishirwa,girki ake kamar kowanne gida sau uku kuma aci a qoshi,duk da cewa ita amarya ta tsaya kai da fata kan girkinta zatayi daban,bazatayi girkin hadaka ba,hakan kuwa babu musu tasoma dora tukunyarta,wanda kullum ta Allah sai anyi tashin hankali tsakanin malam bilya da umma katti,saboda banbanci cefane da yakeyi qiri qiri,miyarta tafi takowa maiqo da zaqi.
To sannu sannu dai a haka rayuwar cikin gidan taci gaba da garawa,babu wani abu daya sauya,kullum sai qarin tsanani da nauyi dayake dake hawa a kafadar bilkisu,don bayan wasu kwanaki ya watsar dayi musu cefane ya kama na amarya ita kadai,ungulu takoma gidanta na tsamiya.
☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️
Sati guda rak kamal yayi maimartaba yayi magana da abdul’azeez tilas yace dawo gidan,hakanan ya sake tattarawa yadawo saidai bai fasa aiwatar da qudurinsa ba.
Saidai kuma duk yadda minal taso janyo abdul’azeez jikinta ta jefashi cikin sabgarsu kamar yadda kamal yabuqata abun yaci tura,haqarsu ta gaza cimma ruwa,wanda har tasoma sarewa takuma baiwa kanta amsar lallai abdul’azeez din bazai jawu ba,don ta gwada dukkan wata fikira da basira tata amma abun yaqi ci yaqi cinyewa,wanda daga qarshe tasamu kamal ta shaida masa.
“Kayi haquri kawai,don yariman yawuce dukka tunaninmu,ina ganin ka ajeshi gefe kawai ka kama wata sabgar taka” cikin fusata yadaki bencin dake gabansu
“Ba zaki gane bane,bazaki fahimta ba,idan har abdul’azeez yazama dan hannu inajin kaf makaranta ba za’a samu wadanda suka kafa tarihi cikin rayuwar bariki ba irinmu,zamuyi komai cikin wadata da qasaita ne….amma indai wannan bata samu ba,ina da wani plan din,tunda taurin kai gareshi,zan masa mai gaba daya,sai nayi tarnishing image dinshi a idanun kowa idan ma yanajin shi wani ne,sainasa kunya ta hanashi shiga cikin al’umma,atlast zanyi amfani da wannan hanyar nayi destroying duk wani tanadi da suke da batar da sunanshi da yarima a masarautarsu,kin shirya aiwatar da wannan aikin?,idan kin shirya ki fadi ko nawa ne farashin aikin ki,zan biya”.
Shuru minal tayi tazubawa kamal idanu,a mamakance take kallonshi,jiki da zuciyarta sun bata cewa lallai akwai wata a qasa,bawai a dalilin korarshi a gidan yasa zai aikata dukkan wannan abun ba,ba shakka akwai dama wani qulli duk yadda akayi tsakaninsa da yariman tun bayau ba,dan gyara zamanta tayi still tana kallonsa
“But….amma kamar kana da wani plan ne apart from dalilin da nasan ya sanyaka zaka mishi wannan abun” hannu ya daga mata alamun dakatarwa
“Wannan duka ba huruminki bane…just idan zakiyi ki fadi price” murmushi tasaka tana qarewa kamal kallo,a ajinta tana ganin kamal yayi qanqanta ya gaya mata magana haka,don haka tace dashi
“Ban amshi contract dinka don kudi ba,don basu na rasa ba,na amsa ne saboda nawa interest din,saboda haka,bani da sha’awar yin aikinka,inaga abinda zaifi kanemi wata” takai qarshe tans miqewa tsaye gamida qoqarin saba jakarta a kafada.
Kallonta yake ganin da gaske tafiyar zatayi,idan tatafin kuma baisan inda zasu samu wata kamarta ba,bugu da qari yana buqatar privacy,baisan mutane da yawa susan maganar ta yadda zaya zamana babu wani sirri kenan
“Wait minal pls…..zauna kiji wani abu daya kafin kiwuce” sai data juyo ta kalleshi sosai,kana kuma a hankali takoma gurbin data tashi tazauna,ta zuba masa dukkanin idanunta alamun tana saurarenshi.
Sai da yayi gyaran murya kadan gamida gyara zamanshi,yasake matsowa kusa da ita yadda zata jishi sosai
“Koda baki da buqatar kudi amma kina buqatar yarima ko?” Kaita gyada
“Of course..”
“Good,bari to na gaya miki abinda zai iya faruwa,wanda inada yaqinin koda ba hundred parcent bane to 99.9 parcent hakane” shuru sukayi dukkaninsu kafin yadora
“Duk wadda tasoma cikin galaba kan azeez takaishi wannan dunuyar ina mai tabbatar miki itave zataci gaba da kasancewa dashi,koda azeez zaiyi bariki,zaiyi bariki ne ta musamman ba irin ta kowa ba,kinsan dalili?”kai ta girgixa tana sake bashi dukka hankalinta
“He is arrogant kinsan da wannan,and he prides him self cewa babu wata mace data isa tayi dauke hankalinsa zuwa wannan hanyar,babu soyayya a ranshi bare a samu damar kaishi hanyar da muke kai,kinga,zai zamana yana boye sabon halinsa don kar asani a masa dariya,zai dinga qoqarin samun sirri ta hanyar yin mu’amala da mace guda,duka bayan wadan nan kuma….azeez yana da qyama da qyanqyami,so dat,kiyi tunani kigani,idan xaki iya barwa wata wannan opportunity din da kika samu….fine” yana gama gaya matan yamaida bayansa makarin kujerar yajingina yana dubanta,yana fatan maganganunsa su shigeta,ya tabbata matuqa sukayi nasarar bata azeez,babu makawa sune zasu shiga takarar neman zama sarkin kaisa,kamar yadda dokar qasar ta tanadar matuqar an samu yariman dake da damar hawa mulki da wani babban alfasha.
A hankali take jujjuya maganganunsa,wanda fiye da rabin zuciyarta tatafi kan cewa ta karba tayi koda babu ko sisi,saboda samun yarima azeez a wajenta shine babban biyan da za’ayi mata
“I can do it” ta amsa mishi,saiya saki murmushi kana yace
“Well,yayi kyau,shikenan zamuyi magana,zan gaya miki yadda komai zai kasance,rana dakuma lokaci” daga hakan sukayi sallama tadauki qaramar jakar hannunta tafice daga wajen.
☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️☀️
Sassanyar safiya ce wadda ke cike da lullumi da wani irin yanayi me dadi a qasar ta mexico,daidai lokacin da yarima ke fitowa daga bandakinsa dake manne a cikin dakin baccinsa,agogo yasoma dubawa lokacin daya fito don yaga lokacin daya rage mishi kafin shigarsu lacture,saiya dauke kanshi yana ci gaba da goge jikinsa dake cike da gargasa da qaramin towel din dake hannunshi bayan wanda ke daure a qungunshi.
Dan tsayawa yayi yana duban dakin,sai yaga kamar ba yadda yabarshi ba a sanda yashiga yashiga toilet,kamar wani abu ya canza,a nutse yasoma tattakawa yana sake qarewa dakin kallo dakyau,saidai bai sake ganin komai ba don haka yanufi gaban mudubi yadauki manshi mai taushi da qamshi yasoma shafawa yana sakin tsaki bayan yatuna cewa yau su ukune ma kawai suka kwana cikin gidan,tunda safe kuma daya shiga kitchen zaisha ruwan dumi yatarar duka sun fice,da alama kowanne cikinsu yana da lactures din safe.
Sai daya gama shafa man,ya gyara sumarshi dakyau bayan yashafe ta da mayukan gyara gashi kala kala kai kace macace,sannan ya isa gaban ma’ajiyar kayanshi yasoma duba kayan da zai sanya.
Gaba daya shigar fari yayi hatta da agogon hannunshi,yakoma gaban mudubin yayiwa kanshi ruwan turaruka masu sanyin qamshi da kwantar da rai,bedsite dinshi yajawo yadauki abinda zai dauka da wasu takardu daya gama dubawa daren jiya dake gefan madubin nashi kana yafito bayan ya murzawa dakin nashi key,don ba kasafai yake barin dakin nashi a bude ba,musamman idan yasan zaiyi nisan kiwo,mutum ne mai tsari da doka,sam bai yadda ana shiga mishi daki barkatai,shi yasa ko yana ciki to zaka samu qofarshi ya turota badai ka sameta a bude ba.
Kafin yafita daga corridor dinsa kira yashigo wayarshi,dan qaramin murmushi yafidda ganin me kiran,saif ne,amininsa dan wazirin mai martaba,waziri musa adamu,cikin yanayin dake nuna akwai sabo da shaquwa tsakaninsu yadaga wayar soma magana,daidai nan ya qaraso falon gidan.
Babu kowa cikinsa kamar yadda ya zata,sai yayi tsaye yana ci gaba da amsa wayar harya gama,motsin daya jiyo daga kitchen shi yaja hankalinsa yamaida dubanshi can,sakan talatin saiga kamal na fitowa daga kitchen din,dauke da madaidaicin plate wanda akai cups ne guda biyu da plates guda biyu wanda ke dauke da soyayyen plaintain.
Da murmushi kan fuskar kamal din ya qaraso yana cewa
“Na tsammaci kafita ai”
“Ina dai niyya,kai kadai ka rage a gidan”
“Eh,nima nagama shiryawar break kawai zanyi nafita….bismillah zo muyi break din” yafadi yana aje farantin,kallon tea da plaintain din yayi cikin mamaki,don yasan kamal din mugun lazy ne,yawanci a kitchen yake karyawa a gurguje yafice,amma yau sai gashi da kinkimo faranti,kamar zaiyi magana sai kuma yafasa,ya qarasa gaban farantin yadauki cup daya daya rage a saman farantin don kamal din yadauki dayan,yasoma kurban tea din,saiya samu hannun kujera yazauna don yasan haramcin shan abu a tsaye.
“Ohk,on my way” yaji kamal din yafada cikin hanzari ya aje cup din hannunsa,ya debi plaitain din yawatsa a bakinsa a gurguje yadubi yarima azeez
“Prince nawuce” kai ya kada mishi kawai ba tare da yace komai ba,yana qoqarin shanye sauran tea din hannunshi shima yafice.
A nutse ya isa inda ‘yar qaramar motarsa mai azabar kyau ke aje,wadda take da budadden sam,yabudeta kana yashiga yazauna
“Oh my god,whats happening?” Ya fada sanda yake da niyyar tada motar,saboda wani irin feelings da bai taba jin makamancinsa ba dake taso masa yana ratsa sassan jikinsa,har tsigar jikinsa tana tashi,uwa uba kuma uban kasala yakeji kamar wanda ya shekara yana aiki.
A qalla yakashe minti biyar yana jira ko mode dinsa zai daidaita,saidai sam babu wani sauyi tattare da yanayin da yake ciki,saima uzzura da lamarin yake,abun saiya soma bashi tsoro bayan mamaki,a kasalance yakashe motar yazare muqullin yafita daga ciki yasoma takawa zuwa cikin gidan,har wani jiri jiri yakeji,yana dafe da jikinsa yasanya muqulli ya bude gidan yashiga,da qyar ya iya kai kansa dakinsa yazube saman gado yana sake jin kowacce gaba ta jikinsa na sake mutuwa,yana kuma sake fita daga hayyacinsa,feelings din dake tare dashi yana sake ta’azzara kamar zai zauce.
Daidai lokacin kamal yafito daga maboyarsa,yaisa varender gidan wadda daga ita sai ainihin falon gidan,yatura qofar falon dako samun damar rufeta abdul’azeez bai samu ba,kamal dinne ya qarasa rufeta,kai tsaye yashige kitchen.
Tana zaune kan daya daga cikin kujeru ukun dake kitchen din,hannunta riqe da wayarta da alama charting take,cikin wata iriyar shiga wadda bata da maraba da tsirara,komai na jikinta ya bayyana,qamshinta kuma ya gauraye ilahirin kitchen din.
Tsaiwa kamal yayi yana qare mata kallo gamida hadiyar yawu da lashe baki,ji yake inama ace shine zata jewa a wannan siffar tata,alamun motsin mutum ya sanyata hanzarin dago da kanta,suka hada idanu da kamal saita zabga mishi harara,ta tsani yadda yake da shegen kallo da yadda yake yawan bibiyarta da idanunshi,ta riga data gama karantarshi tun ba yau din ba,saidai ita sam bai mata ba,hasalima baikai ajinta ba ko kusa ko alama a yadda takejin kanta a matsayin babbar yarinyar dake harka da ‘ya’yan wasu,ko wasun kansu a baya,bare a yanzun da babu wani da namiji dake burgeta ko take gani sai abdul’azeez din,yashafe tauraruwar kowanne namiji a idanunta.
Basarwa yayi yaqaraso kitchen din kamar mai rada yace
“Komai yazama ready,ki sameshi a bedroom dinsa,a yanayin da naga yake ciki bazai iya tsallakewa trap dinmu ba,i wish u all d best” yana gama fada yajuya yafice daga kitchen din,batayi jinkiri ba itama tabiyo bayanshi,saiya dakatar da ita,yadauko laptop dinsa wadda ya saitata da camerar da zai nadi komai,wadda ke maqale jikin qarfen da aka sanyawa net aka lullube gadon azeez din dashi,yakunnata ta kama,saiga hoton abdul’azeez din zaune saman gadonshi,qanqame da jikinsa,idanunshi a runtse gam,babu abinda yake fiddawa sai gumi.
Qaramar dariya yasaki mara sauti kana yace
“Uhmmm,lokacinki yafara” batace komai ba tajuya zuwa sashen daya nuna mata,saiya zaro wayarshi ya danna lambobin wayar mahaifiyarsa,bugu uku ta daga
“Mom,komai ya kammala,yanzu haka za’a fara aiki,saiki addu’an samun nasara”
“Allah ya bada sa’a son,wannan nasarar idan ta tabbata ba shakka dukkan abinda zai biyo baya mai sauqine,rushe aysha da abunda tafi tutiya dashi duk duniya shine babban aikin,Allah yabada nasara,sai naji feedback”
“Ok mom” ya fada yana kashe wayar,kana yamaida dukka hankalinsa kan laptop din yana jira yaga shigar minal dakin azeez,har wani lumshe idanu yake yana sake relaxing cikin kujerun,ko banza shima zai more da kallon yadda komai zai wakana,yakuna sakin murmushi yana hango yadda vedion da hotunan zasuyi destroying azeez da mahaifiyarsa cikin masarautar kaisa…….