SIRADIN RAYUWA CHAPTER 7 BY SAFIYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA
Baƙiƙƙirin ranta yakekamar yadda fuskarta take a murtuke kai kace saqaon mutuwa aka aiko mata dashi,idanunta na kafe waje daya ranta yana suya,babu wata sauran daraja itakam data rage mata,hotunanta sune abun dauka da turawa wani da namiji?,hawaye taji masu dumi sun taho daidai lokacin dame hoton yagama saisaita komai yafara daukan hotunan.
Ji tayi zuciyarta ba zata iya dauka ba,saboda haka tamiqe ana tsaka da dakn hotunan tawuce zuwa dakin da shine masaukinta,sai data tabbatar data kulle qofa sannan ta sanya kanta jikin qofar tasaki kuka mai ciwo.
Ta jima a haka tana kukanta,wanda ba kowa take kokawa ba wannan karon sai kanta da rayuwarta,sai data gaji don kanta kana taja jikinta zuwa cikin dakin tana fidda kayan jikinta wadanda take jinsu tamkar qaya.
**************
Batasan murmushi take ba a sanda take kallon hotunan har rakai qarshensu,lallai lubabatu ta cancanci a qara mata wani abu kan tagomashin da akayi mata,don ta iya zabe,zabe kuwa na haqiqa,tasan cewa azeez bazai taba kushe wannan yarinyar ba,zata dace da ra’ayinsa qwarai.
Sauka tayi ta kunna data dinta da kanta,kana tashiga email dinta ta tura mishi dukka hotunan,sannan takashe datar tasoma laluben wayarsa.
Daidai lokacin da yake sanye da dogon wando da rigarsa mai dogon hannu irin ta sport,qafarsa sanye da rufaffen takalmi wanda zaiyi dai dai da jogging din da yakeyi cikin hasken rana a wanda baiyi zafi da yawa ba,hakanan a layin unguwannin nasu dayafi kama da titi saboda kwalta dake shimfide akan kowanne layi.
P_cap ce a kansa,kansa saye da headphone wanda idan bakasan me yake yi ba,zaka zaci waqa ko kade kade yake ji,kamar yadda yawancin samarin yanzu suka maida wannan dabi’arsu,a maimakon wannan yanajin tafsir ne na daya daga cikin malamanmu.
Baisan da tahowarta hakanan baisan ta iso kusa dashi ba sai datayi wave din hannunta a gaban fuskarsa kana ya lura,a nutse ya waiwaya yana dubanta bai fasa tattakinsa ba,itama shi take duba fuskarta qunshe da murmushi har haqoranta suna bayyana,sanye da kayan motsa jiki irin na mata a jikinta,tana ta qoqarin daidaita kafada dashi don kar yawuceta
“Hey!” Tasake fada duk da bata da tabbacin xai jita saboda abinda ke kunnenshi,ya ganta sarai yakuma gane me tace,amma sai yadauke kai kamar bai gani ba ko babu wani mutum a wajen,gamida dan qara hanzari wajen sassarfar da yakeyi,take kuma ya zarce mata,yana kuma kaiwa qarshen layin saiya karya kwana ta yadda yasan zai bace mata.
Tsaki yaja bayan yadanyi nisa,yanajin haushin yadda bata da zuciya,hakanan yanajin haushin yadda take shige masa hanci da qudundune da yawa,farar fata ce wadda duk da baisan yaren ta ba amma yanayinta ya nuna masa tabbas baturiya ce wadda baisan daga wacce qasa tafito ba.
Qarar wayarsa ta dakatar dashi,yatsaya yana qoqarin ciro wayar daga aljihunsa hadi da neman daya daga cikin kujerun da akan ajiyesu haka siddan qasan bishiyoyin dake jere a layin haka siddan saboda hutawar masu wucewa,yadan lumshe idanu yana sauke ajiyar zuciya ganin ammi ce,yazauna sosai yana daga kiran ya kara akunneshi,bayan gaisuwa da suka saba kamar kullum tashaida masa tatura masa saqo na hoton yarinyar,yaduba idan batayi masa ba ayi gaggawar canza masa. Da to kawai ya amsa mata,yana shirin aje wayar takira sunanshi
“Kome kake,koda bata maka ba ba za’a daga abun nan nan da kwana goma ba,already nayi magana da mr james,an gama shirya wannan gidan dana shaida maka,acan nakeso kazauna,ka sameshi ka amshi keys din gidan a hannunsa,kaduba kaga idan akwai abinda baiyi maka ba kobai dace da tsarinka ba,karka manta….bana buqatar kowa yasan dalilinka na barin wannan gidan,hakanan banason kowa yasan inda zaka koma din,dole rayuwarka ta zama cikin privateness,ina fatan ka fahimta?” Kai ya gyada,sai kuma yatuna ba’a gabanta yake ba,dole yabude baki yayi magana don haka yace
“Naji ammi,godiya nake”
“Ohk” ta amsa a taqaice tana datse layin.
Aje wayar yayi a gefansa,kana ya finciki water bottle dinshi yabude yahau daddakar ruwan,sai dayasha sosai kana ya bame murfin yana sauke qaqqarfar ajiya zuciya,koda yaushe yana kwana ya tashi da mamakin tsarin amminsa,why me yasa ba zata bari yayi aurenshi da safwa ba kamar yadda aka tsara,dama aure yana hana karatu?,dama ana gindayawa namiji lokacin da zaiyi aure ne?,daidai ne hakan ka hana danka ko ‘yarka aure harsai zuwa wani lokaci da suka cika maka qudurinka?,dole a haka zai bita har takai ga gacin tsarinta,amma bayajin zai iya hada jiki ko shinfida da kowacce mace bayan safwa har qarshen rayuwarsa.
Yana gama wannan tunanin ya dauki wayarta tasa da bottle dinsa yaci gaba da tafiya don ya isa gida ba tare da yayi koda sha’awar yabuda hotunan yarinyar ba bare ya ganta,don baya sha’awar yaga ko wacece,don yasan ko wacece itan ba zata taba kama qafar safwa ba,daga inda yake yana iya hangen gida,don haka yaci gaba da takawa a hakali tunani iri iri yana bijiro masa.
Yana taka qafarsa a qofar gidan wani kiran yasake shigo masa,daya duba yaga safwa ce,kamar tasan ita yake tunani,sai fuskarsa tadan washe,wanda yawanci idan kaga irin hakan saman fuskarsa to yana nuna maka murmushi yayi a sannan,bai jinkiri ba ya amsa kiran kana ya maqaleta a kafadarshi yana saka key don bude qofar gidan.
“Kamar kinsan tunaninki nake?” Ya fada cikin sassanyar muryarsa,safwa dake kwance saman gado idanunta a rufe batasan sanda tabudesu tarwai ba,fuskarta cike da murmushi,bakinta yakasa rufuwa har sai datace
“What?,are u kidding me?” Murmushi yasaka mai sauti
“Ina miki qarya?”
“No my prince,it was just amazing” ta amsa masa tana zama sosai saman gadon,farinciki yana lullubeta
“Ohkey,let me repeat my self,tunaninki nake sanda kika kirani” farincikinta ya kasa boyuwa harsai data saki qaramar qara,tana bala’inson azeez ya nuna mata ko yaya ita din wani bangarene na musamman a rayuwarshi,hakan ba qaramin faranta mata rai yake ba
“Yau duka wannan kalamin naka shine babbar kyautar dana samu wadda babu wani abu da zai iya siyanta,thank you for making my day sweetheart” murmushi yasakeyi yana shiga falon sosai.
A falo yacire takalmanshi yana ci gaba da amsa wayar sannan yawuce kitchen don yasamu abu mai zafi ya qarawa cikinsa,ya hada coffe mai yawa har a sannan yana amsa kiran safwan kana yasake dawowa falo.
Sak ya tsaya yana dubanshi fuskarsa cike da mamaki sanda yaganshi yafito daga corridor din da babu wani daki sai nashi dakin,kamal ne,shima azeez din yake kallo
“Ina zuwa baby” azeez ya fada yana zame wayar daga kunneshi yana ci gaba da duban kamal dake tsaye.
Ko a karon banza nauyi idanun azeez din kewa mutum bare a wannan karon da akwai qamshin rashin gaskiya tattare dashi,don haka yasoma kame kame da kanshi
“Oh…ashe sai yanzu kake shigowa,no wonder naje inata knocking amma naji shuru”
“Really?,ina cewa munyi sallama dakai harka amshi aron mota ko?”
“Yeah,na dawo ne saina bawa su jabir suna da lacture sun kusa makara kuma shida mustapha” shuru yadan ratsa,abdul’azeez najin kamar ba gaskiyar ya fada masa ba,amma saiya share kawai,yazauna yaja coffe dinsa yasoma sha,yayin da kamal yayi gaba da sauri yana jin kamar wanda aka sunceshi daga wani tarko.
******* ******** ******
“Har yanzu na kasa gano meye abinda suke shiryawa,na kasa karantar da gano meye ne taketa jaddadawa yaron ya kiyaye,batason kowa yasani,taqi yarda ko bada fuskar da za’a shiga jikinta,amintattunta dukka sun kasa siyuwa,wai garin yaya aisha keson zamar mana gagara gwari?” Ta qarashe tambayar tana duban saudatu qanwa ga maimartaba abdallah sarkin kaisa,hakanan mahaifiya ga kamal.
Nannauyar ajiyar zuciya tasauke
“Aisha wata irin macace ta daban mai wayo basira dakuma fikra,babban matakin nasararta shine rashin saurin yarda da sakin jiki wa mutane,amma koma meye wannan karon bazamuyi sanya ba,zamu durfafeta ita da dukkan shirinta tuquru,sai munga abinda ya turewa buzu nadinsa….yanzu haka na tura kamal dakinsa bincike koda zamu samu wata makama na abinda ke wakana,kiranshi kawai nake jira,shi yasa na hanashi yin nesa dashi,dakuma hanashi rabuwa dashi,zamansu tare dole zaici gaba dayi mana amfani,hakanan dukkan wani shirinmu xai dinga saurin samun nasara fiye da ace suna nesa da juna” kai fulani adama ke kadawa cike da qaguwa,yayin da saudatun ke kallonta can qasan ranta itama tana shirya nata qudurin daban wanda fulani adaman batasan da zamansa ba.
Kiran kamal ne yashigo wayar mahaifiyarsa,dukkansu kiran yaja hankulansu,ta daga kana ta sanya handsfree,muryar kamal tafito tangaran
“Mom….babu abinda na iya samu ko ganin cikin dakinsa,ba wata shaida ko alama da zata bamu hasken komai fa” dukkaninsu gabansu ya fadi,ransu yabaci,cikin hasala hajiya saudatu tace
“Kamal…ka duba kuwa dakyau?” Hannu ya yarfar
“Haba mom,ke bakisan masifar da naso fadawa ba ne saboda yadda na tsaya bincikawa ko ina,saura kadan yakamani fa,daya kamanin kinsan me zai iya faruwa?,baida sauqi gayen nan fa ko kadan”
“Shikenan,zan nemeka” ta fada tana yanke kiran gamida maida hankalinta ga fulani adama da hankalinta yayi masifar tashi,ji take kamar ta kurma ihu,kenan saidai su sake sabon lale?,dukka hope din da suke dashi ya rushe?,ita a jikinta tana jin tabbas akwai abinda yake faruwa,abinda idan ya bayyana zai sama musu hanya mafi sauqi da zasu tarwatsa yarima azeez da mahaifiyarsa dama ‘yan uwansa,su rusa dukka wata martaba tashi datake idanun al’ummar qasar kaisa.
“Sun binne kuma sun boye komai,amma inaga…muci gaba da namu shirin,babu abinda zai dakatar damu” saudat ta fada tanason qara musu qwarin gwiwa.
********* ***** *******
Cikin kwanaki qalilan dukkan wani shiri ya kammala,fulani tagama shirya komai,takuma sanar a can mali kan daurin auren azeez din,saidai ko a can dinma sanarwar ta bulla ne a iyakacin mutanen da tasan ba zata samu matsala ba,hakanan labarin bazai taba zuwa kunnen maimartaba ko wani da bataso ba.
Fannin gidan malam bilya daya zama alhaji bilya saboda umra da yaje ta sati biyu a tsukin da ake masa ginin gidan kuwa gini ya kammala,ginin da ko a mafarki bai tana zaton zai mallaki gida kamarsa ba,kowa yasan ginin daa dana yanzu ba daya bane,don duk sanda aka tashi rushe tsahon gini za’a maida na zamani akan samu ashe babban fili ne,to shima kusan hakanne,gidane babba ba’a gane hakan ba sai da aka rushe aka mayar na zamani,babban falo da dakuna harda bene na maigida alhj bilyaminu.
Umma katti tadauki ciki da falo haka mama ladi,sai yaran suma aka ware musu babban daki mai hade da bandaki da aka zuba dukkan furniture da suturar sawa dai dai da kowa.
Kafin kace meye tuni alhj bilya ya shaidawa danginsa abun arziqin daya sameshi dakuma bikin diyarsa,nan da nan saiga dangi sun fara zuwa,wasu suga gida susa albarka su tafi,wasu kuma su zauna zaman jiran biki,ko a jikinsa sai dadi da hakanma yamasa,don bashi da matsalar abinci,duk kuma wanda yazo sai yace masa sirikinsa wanda zai auri bilkisune ya masa wannan hidimar,kamar yadda yake cikin sharadinsu ko sau daya bai ambaci sunan angon ba.
******* ****** *******
Duk da motar baqaqen glass ne da ita hakan bai hanata ganin irin sauyin da gidan yasamu ba muraran,ci gaba tayi da duban gidan har sanda motar tasu ta cusa kai ciki,kana aka zagaya sashen da take zaune aka bude mata,ta zuro qafafunta dake sanye da half cover takalmi da yafi kama dana sarauta.
Bata lura dasu ba saiji tayi gaba daya an taho da gudu an qanqameta,ta daga kai tana dubansu,amina ce hauwa’u sai umaima,yayin da hannatu take qarasowa cikin hanzari da sassarfa
“Yaaya…kin dawo?” Suke jero mata tambayar kusan a tare,sai taji idanunta sun soma tara qwalla kamar yadda yazame mata jiki,ta tsugunna ta rungumesu gaba daya cikin jikinta,inama ace tadawo cikinsu xasu zauna ne din din din kamar yadda suke a baya,abinda basu sani ba shine kwanaki biuu kacal xata qara tare dasu tasake musu nisan dayafi wanda tayi musu a yanzu
Sun jima a haka ba tare data iya ce musu komai ba,sannan daga bisani tace da hannatu
“Kaini ciki” da murnarta tayi gaba suna biye da ita,kowa yana qoqarin bata labarin irin sauyin da suka soma samu,kunnuwanta kawai ta iya basu tana saurarensu,ba shakka ko makaho yasan cewa sun sami canji,tun daga muhalli dama yanayin sutturar dake jikinsu,saidai ko sau daya zuciyarta taqi maraba da wannan sauyin wanda yake kamar fansa ne na mutuncinta,ko madadine na darajarta wadda nan bada jimawa ba za’a watsata.
Umma katti tasoma arba da ita a babban falon gidan,tayi darashe darashe saman luntsuma luntsuman kujeru tasanya tv a gaba tana kallo,gefe kuma mutum ukune cikin dangin abbanta wanda suke zaman jiran biki,bikin da takejin za’ayi bikine na saidata ko miqata a mazaunin baiwa.
Bakin umma katti har kunne tamiqe cikin bada wani irin girma da karramawa tana mata sannu da zuwa,hakama sauran wadanda ta taras,nan aka shiga ana akasa ina aka aje da ita,abun har mamaki yadinga bata da daure mata kai,bata jima a falon ba tawuce tabi qannenta zuwa daki,don tanason taji yadda suka rayu sati biyun da basu tare.
Shuru tayi tana jin wani sashe na zuciyarta nayin sanyi bayan ta gama sauraren dukka labaransu,babu takura,sun rayu cikin kulawa ci sha da sutura mai kyau,hakanan babu wanda yake tsangwamarsu tsakanin umma katti da mama ladi,hasalima mama ladin na jansu a jiki sosai,tana cewa sune ‘ya’yanta yanzu tunda bata da ɗa cikin gidan.
“Ya Allah,ka sake sanya tausayin wadan nan bayi naka cikin zukatansu,kasa suyi musu riqo nagartacce fiye da yadda sukayi niyyar yi” tasamu kanta dayin wannan addu’ar cikin zuciyarta.
Tunda tazo ta fuskanci ta zama ta musamman cikin gidan,kowa kaf kaf yakeyi da ita,kwananta biyu ana uku suka tashi gagarumin yinin biki cikin gidan,wanda kaf dinsa babu dangin mahaifiyarta ko qwalli daya,basu san ma wainar da ake toyawa ba,daga dangin uba maqota sai dangin kishiyoyin uwa,wanda sukayi farin fitar dango suka cika gidan don kada aci arziqi suma babu su,zuciyarta tacika fal da mamaki dakuma tunani,wasuma mutanen sam ta manta dasu cikin babin rayuwarsu saboda halin qaqa nikayin talauci da suke fama dashi,amma ayanzu kowa ya dungumo yace shidin nasu ne,kuma lallai lallai dashi za’ayi.
Duk wannan abun da akeyi su kadai suke kidansu suyi rawarsu,don ita wadda ake kira da amaryar batasanma anayi ba,tana daki liqe da ‘yan qannenta tana morewa sauran awannin da suka rage musu tare,hatta da dakin da aka ware mata cikin gidan cike fal da sutturu na alfarma wanda zatayi fitar yinin biki dasu nata kalla na bare ta bude tashiga,hatta da barorin da suka taho tare ta sanyasu sun koma gida,don bata da buqatarsu,batason ma ganin wani abu daya danganci masarautar dazai dinga tuna mata da al’amarin dake gabanta na tsahon kwanakin.
Su dinma hakan baidamesu ba,tunda dai sun samu dukka abinda sukeso,abinci da abubuwan sha na kwali dana roba gasunan birjik sai wanda ka zaba.
Darensu na qarshe tare tajima dasu tana musu karatun rayuwa wanda ba lallaine su fahimta ba,koda zasi fahimta dimma to hannatu itada umaima ne kawai zasu gane me take nufi,saiko hauwa ba’a batun su amina dama da basu ma gama sanin kansu ba bare su fahimci maganganu irin wannan.
Sun jima sosai a hakan,wanda daga bisani har bacci yadaukesu itan tana zaune tana tufka da warwara.
***** ***** ***** ******
Cikin qasar da take mallakin mahaifi ga fulani aisha aka daura wannan sirritaccen aure,tayi matuqar mamakin ganin yayunta maza har qasar ta mali bayan mahaifinta.
Duk da cewa yarima azeez din yana qasar a sanda aka daura auren amma koda gilmawarsa bata gani ba da sunan mijin da zata aura ba,hasalima da zaka ritsata kan waye mijin nata?,koda za’a jera mata maza cikinsu hardashi bazata iya tantanceshi ba,hatta da fulani aishan bata samu ganinta ba bare mai gaba dayan,wanda hakan yasake tabbatar mata lallai ta durfafi wani bigire na rayuwa na daban,saidai batasan ya tafiyar zata kaya mata ba….A hankali ta daga rinannun idanuwanta da suka jima da sauya kala tun daren jiya har zuwa wannan lokaci da awanni kadanne suka wuce da daura aurenta tana duban wanda ke shigowa katafaren dakin da aka ajeta,aka kuma wadata da dukkan wani nau’in abubuwa na more rayuwa.
Macace mai cikar haiba gamida kamala,a shekaru ba zata haura shekara arba’in da takwas ba,tana da dan jiki kadan,ba zaka kirata da mai qiba ba,tana da tsaho saidai ba wani can ba,wanda bisa dukkan alamu ma qibar murjewar jikinta ne ya sake boye tsahonta,kallo daya ta fahimci itama tana daha cikin hadiman gidan sarautar kaisa,duk da cewa bata taba ganinta ba sai yau.
Karon farko kuma a ganin farko data yi mata,taji tadanyi mata kwarjini,hakanan bataji irin abinda ta saba ji dangane da sauran matan da suke hidima da ita ba wadanda suka fito daga gidan
“Assalamu alaikum” tayi sallama matar hannunta riqe da kaya,wanda hakan yasaukar wa da bilkisu wata iriyar nutsuwa data jima rabon data ji irinta,ta motsa labbanta,karon farko tunda tazo qasar mali ta amsa mata itama cikin nutsuwa
“Wa’alaikumussalam warahmatullah” yadda yanayinta yake nuna nutsatstsiyar macace ita haka ya qaraso wajenta a nutse,ta ajjiye kayan kusa da bilkisu,sannan tazauna daga wata kujera da take fuskantarta
“Bilkisu ko?” Ta tambayi bilkisu tana dubanta,sai data daga kai ta kalleta,ason ranta ba zata amsa mata ba,don bata tsammanin akwai wanda baisan sunanta ba cikin gurguxunsu,amma sai taji tayi qimar da ba zata iya shareta ba,don a qalla ta haifeta,don haka ta gyada mata kai,itama kai ta girgiza
“Ma sha Allah,bilkisu…kowanne bawa tun yana cikin mahaifiyarsa da watanni hudu ake rubuta masa dukkanin qaddararsa,Allah S W T yakan umarci mala’ika yaje ya busa masa rai,kana ya rubuta masa dukkan qaddararsa har makomarsa bayan ya mutu,ita rayuwarmu mallakin mahaliccinmu ne,kowanne bawa da kika gani bakya rasa wani abu daya zuwa biyu cikin rayuwarsa da bayasonshi,amma kasancewarsa cikin littafin qaddararsa hakanan yake karbansa hannu bibbiyu yakuma godewa mahaliccinsa kan hakan,harma wataran kiga yana rayuwa kamar babu wannan damuwar a tattare dashi,kamar mu dai…..” Ta furta tana nuna kanta
“Allah daya haliccemu a matsayin bayinsa dukka daya muke a wajensa,amma daya tashi…..ya qaddara cikin bayinsa akwai bayin bayinsa,mu saiya sanya salsala da zuri’armu cikin tsatson bauta iyaye da kakanni,bakuma wai don baya sonmu ba,aah yana qaunarmu kamar kowanne mutum,don ya hanemu sabawa ko guduwa daga wajen iyayen gidajenmu,aikata hakan haramunne akan dukkan wani bawa abun mallaka wa uban gidansa”
“Subhanallah” bilkisu ta fada cikin ranta,kana ta daga kai tana kallon matat,macace cikakkiya kamar kallon data mata dazu,mai cikar haiba da kamala,amma tatashi a sahun bayi?,bayi da takanji ana maganarsu cikin littafin hadisi kona fiqhu,yau ga burbushinsu a wannan zamanin?.
Kamar tasan me bilkisun ke kitsawa saitayi murmushi
“Baki godewa Allah dabai sanyaki a sahun bayi kamarmu ba?,duk da muma babu abinda aka tauyemu dashi,saidai har abada bawa bawa ne,harsai sanda yasami ‘yanci,koda yasamu ‘yanci ma cikin tarihin rayuwarsa sunan ya taba BAUTAR abun halitta bazai taba gogewa ba” saita sake matsowa kusa da bilkisu sannan tace
“Sunana hafsa,amma kusan dukkan masarautar kaisa suna kirana da sodangi,nidin jakadiya ce ta yarima azeez,saidai ‘yantacciya ce kamar yadda aka ‘yanta iyaye da kakanni na,kamar yadda kowanne yarima da ake saka ran zamantowarshi sarki yake da jakadiya wadda kusan ita zatayi rainonsa har yagirma,bayan yazama sarki kuma zai riqeta ne a makwafin uwa,na gaji jakadanci daga wajen kakata,ita tayiwa sarki mu’az jakadanci,mahaifiyata kuma Allah ya jiqanta ita tayiwa sarki abdallah mahaifin azeez,ni kuma a yanzu ni nake masa…..an umarceni dana tafi tare daku zuwa mexico,nazauna daku har zuwa lokacin da aka dibawa zamanku ya qare,bilkisu…..nasan an shiga haqqinki an kuma shiga hurumin rayuwarki,hukuncine da fulani aysha ta yanke a lokacin da bana kusa da ita,duk da cewa ta quduri niyyar yin hakan ban isa na hanata ba,amma a qalla inada yaqinin bisa shawarata wasu abubuwan za’a samu sauyi da sauqi,duk da cewa ba hurumina bane,ina mata tsoron ranar da komai zai bayyana a fili…..” Ta fada tana kada kai sannan tadora
“kiyi haquri ki amshi jarrabawarki,ki kusanta kanki da ubangiji,komai zaizo miki da sauqi….sai kuma alfarma daya da nake nema ki taimakeni kiyimin” hakanan taji maganganun jakadiya sodangi yana shigarta,ta iya kalamai masu cike da hikima taushi da kwantar da zuciya,hakanan sai ta dinga ganin girma martabarta cikin idonta sosai
“An doramin dukkanin nauyi da alhakin kula daku,an jaddadamin ns tabbata komai yana tafiya yadda ya kamata har zuwa qarshen lamarin,ki taimakeni kibi duk umarnin da aka bani nabaki don girman Allah na roqeki” ta fada tana hade hannayenta waje daya,nauyin roqon datake mata takeyi,don haka da sauri ba tare data shirya ba tace
“In sha Allahu mama”
“A’ah,taimakeni ki kirani da sunan da kowa yake kirana,saboda ke a yanzu matsayinki sama yake da nawa,kusan dai dai yake da akiraki matar magajin sarki koda ta wucin gadice kuwa” kai ta kada
“Bazan iya ba,zanyita kiranki da maman indai ba zunubi na aikata ba” murmushi kawai tayi tajawo kayan data shigo dasu ta miqa mata tana cewa
“Ina fatan zaki saki jiki dani,ki daukeni kamar wata taki” karon farko murmushin da batasan ya akayi yazo ba ya subuce mata,duk da cewa iyakacinsa saman labbanta
“Ki sanya wadan nan kayan zamu wuce mexico yanzun nan,kafin nan mahaifinki zai soma magana dake,idan kin gama ina falo saiki sameni in miki jagora,idan kuma kina da buqatar wani taimakon yayin shiryawar taki ki shaidamin nashigo na taimaka” daga haka tamiqe tafice,bilkisu tabita da kallo kafin tadawo da kallonta kan kayan,haka kawai taji cikin kaso dari tasake da matar kaso goma,wanda ita kanta batasan dalili ba.
Durqushe take gaban mahaifin nata kamar yadda kowacce amarya kan tsaya gaban mahaifinta don amsar nasihar ban kwana,cikin wata iriyar shadda da aka yiwa dinkin babbar riga ta alfarma yake,yacika kujerar yanata baza rigarsa,jinsa yake kansa daya da shugaban qasa,gyaran murya yayi sa’an nan yasoma magana
“Amm….dafarko maigado babu abinda zance dake saidai nace Allah ubangiji yayi miki albarka,yadda kika min biyayya kema Allah yasa ki dace haka,Allah yajiqan maimunatu,yasa ta huta,wanda ba shakka naso ace tana raye taga wannan lokaci” ya fada yana share qwalla wadda ko digon danshi babu a idanun nashi bare kuka
“Abinda nakeso dake bilkisu kiyi biyayya,ban yafe miki ba idan kika saba kan dukkan abinda aka umarceki dashi,kibi duk umarnin da kowaye cikinsu zai baki,Allah yayi miki albarka,ya qaddaea saduwarmu”. Wannan kusan itace sallama ta qarshe data dimga tunawa tsakaninta da mahaifinta sanda take zaune cikin jirgi tana qoqarin maida qwallarta,a maimakon tsoro da zullumi dakan cika dukkan wanda yasoma shiga jirgi karon farko yake tsintar kansa a ciki a’ah,maganganun mahaifinta ne kadai ke bitar kansu cikin kwanyarta.
Su uku rak ne taga sun shiga cikin jirgin wanda suke tafiyarsu daya,daga ita sai mama sodangi,sai wata matashiya wadda a qalla zasuyi sa’annin juna da ita wanda taji mama sodangi tana kira da rakiya.
Tafiyar awanni suka sauka a qasar mexico,mexico city,tuni motar da zata daukesu ta iso,da alama ma tun kafin isowar jirgin nasu take dakonsu.
Motace maikyau ta alfarma,aka zuba kayansu sa’annan suka fice daga babban filin sauka da tashin jiragen sama na garin.
Duk da yadda zuciyarta take a cunkushe amma hakan bai hana idanunta wulqawa bisa titina da kyawawan gine ginen da suka qawata garin ba,shuru ne ya biyo baya cikin motar,sai mama sodangi da drivern da yake baqar fata wanda da alamu ma dan qasa nijeria ne suke taba hira jifa jifa,da alamu ba yaune karon farko da suka san juna ba.
Shudewar wasu mintunan na daban suka isa unguwar,wadda tsarinta dakyanta ya fita daban,bata sake gasgata hakan ba saida suka sanya kai cikin gidan,tana biye da mama sodangi wadda take kamar ‘yar jagora a wajensu,yadda take saka kai cikin gidan ya isa ya shaida maka ba baquwa bace cikin gidan,ta sanshi sosai.
Sai data soma sada bilkisu da wani daki daya sanya bilkisun tsaiwa cak cikin ‘yar fargaba tana dubanshi,komai na dakin fari ne da gold,an tsara dakin ne dai dai da ra’ayin tsari da colours din da azeez yakeso,kusan wannan shine favourite colour na bilkisun,ba wani tarkace bane a dakin amma komai na cikinsa mai aji da kyau ne,yana da fadi sosai,akwai cupboard dressing mirrow sai wani lafiyayyen dunqulallen gado da aka lullubeshi da wani ni’imtaccen farin net,akwai bedside lockers hagu da dama na gadon,wanda akan kowacce akwai fitila akai,sai wata corner daga can hannun hagu na dakin da aka dan mata ado aka aje litattafai na karatu na turanci,da fitila wadda take shige data gefan gadon,saidai tafi ta gefan gadon girma da dan haske,gaba kadan da wajen sofa ce qwaya daya iyama fara qal da ratsin gold,daga gaban gadon lallausan carfet ne madaidaici da wani dan qaramin table mahadin gadon,qasan dakin ba tiles bane hakanan ba carfet bane,wani shimfidadden abune mai kyau da ita kanta batasan sunanshi ba,labulaye ne masu kyau tsari dakuma kauri zagaye da dakin,farare ne da akayi musu adon wata rumfa daga saman kowanne golding colour haka madauran labulen suma duka kalarsu kenan,dakin bai cika haske sosai ba,saidai bashi da duhu kuma,amma luf luf yake,wanda akwai yiwuwar idan yamma tayi lis babu hasken qwan lantarki to babu shakka zai iya yin duhun.
Qaqqarfar ajiyar zuciya tasauke tana ambaton sunan Allah,kana ya dosana mazaunanta a gefan gadon,tunanin gida yana bijiro mata,tana shanshano irin nisan tazara data yiwa gida,bama gida kawai ba qasarta ta haihuwa gaba daya,wanda tunda take wannan shine karo na farko data taba barin qasarta zuwa wata qasar.
Tana nan zaune bayan awa guda aka mata knocking,rakiya ce,ta nemi izinin shigowa ta bata,cikin girmamawa ta neme izinin gyara mata kayan sawarta da sake karkade mata dakin,duk da bawani qura yayi ba bare datti,bata hanata ba ta bata dama,tana nan zaune a inda take tana kallonta lokaci lokaci,harta gama kana tashiha bandakin na wasu mintuna tafito,da alama sake wankeshi tayi.