- SOYAYYAH
- CHAPTER 2
- Hannun ta Ummy ta rik‘e suka nufi da k’in ta tayi mata bath, ta shirya ta cikin sky blue with touches of red atamfa sannan ta d’auko small white hijab ta saka mata.
- Dama ta sata ta d’auro alwala dan haka saida tayi sallah sannan suka dawo falour.
- Abinci ta zuba mata Ya Haidar dake zaune ya karb’a ya zaunar da ita a side d’in shi ya shiga feeding ta, dan yasan ba son cin abinci takeyi sosai ba.
- Tana gamawa Kuwaysah ta shigo tace ” Ukhteey ki fito Ya Suwayd yace 5:00 pm dai_dai muje ya koya mana assignment “.
- ” What? What the hell do you think you are saying Ukhteey, am not going you guys know how wicked he is amma ku rasa gun wa zaku kaimu assignment sai shi ” Safwah ta fad’a in I know am already die tone. Ta fashe da kuka tana ita bazata je ba, ganin zata b’ata musu lokaci suka tafi dan ko 1 minute suka k’ara akan time d’in daya fad’a you are in trouble.
- Dakyar Ummy ta rarrasheta itama ta d’auko books d’inta ta tafl, lokacin dataje a bakin k‘ofa ta tsaya dan ta kasa shiga.
- Dakyar ta samu tayi gathering courage ta shiga da sallama, kusa da Kadsah tajeta nemi guri ta zauna. Cikin daka tsawa yace ” gidan ubanwa kika tsaya? ”
- Ba ita ba harsu Samha saida suka tsorata da tsawar, Lubnah ce tayi k’arfin halin cewa ” Ya Suwayd abinci take ci lokacin da muka tawo “. Maido da kallon sa yayi kanta yace ” Who asked you? Ko ita bata da baki? The next time kika sake yimin shish shigi saina fasa miki baki good for nothing kawai ” Am sorry ya Suwayd ” Safwah ta fad’a da rawar murya tana b’uya a bayan Kuwaysah. Dirty look ya watsa mata sannan ya shiga koya musu, saida suka gama sannan yace kowa ya flto da lesson book d‘insa, d’aukowa sukayi ya bawa kowa example yayi solving.
- Dan mugunta mai makon ya basu same question saiya basu different, wayar sa ya d’auka k’irar iPhone 7+ yayi facing direction d’in Safwah. 15 minutes later, kowacce ta duk‘ufa sai solving take, Safwah ce ta taso tazo gaban sa ta mik’a masa book d’inta. Are you sure you did it right? “ ya jefo mata tambayar fuska a d’aure.
- Nodding kanta tayi alamar Eh, saukar Marin dataji ne yasa ta remembering ba’a yi masa talk da body language, ” yes am sure ” ta fad’a tana tears dan sosai marin ya shige ta, gurin daya mare ta kuwa tuni yatsun sa suka fito rud’u_rud’u kasancewarta fara.Duba littafin yayi ya cilla mata a fuska, cikin d’aga murya yace ” What kind of nonsense is this? Is this how I teach you huh? ” shiru tayi jikin ta sai rawa yake hawaye kuwa kamar an bud’e lalataccen tap, ita dai tasan yarda ya koya musu tayi sai dai in he is up to something. ” Answer me is this how l teach you? ” ya sake tambayar ta harshly. Da sauri tace ” No please sorry Ya Suwayd, don’t beat me I will correct it “. ” Oh no wonder, kina sane kikai min wannan haukan kenan? Good you must answer me “.
- Hango Kuwaysah yayi sai kuka take, ai kuwa ya dawo kanta ” Ubanki nayi miki kike min kuka? ” Shiru tayi not ready to talk, hakan kuwa ba k’aramin hasala shi ya sakeyi ba, “ yau zanga k’arshen iskancin ki, koma can side d’in ” yayi mata pointing kusa da Safwah. Kallon Lubna yayi da take shirin yin kuka yace ” Wallahi karki yarda Kimin kuka if not saina Iahira ya fiki jin dad’i “, tuni ta had’iye kukan ta, ita dama ba komai yasa take shirin yin kukan ba sai ganin Safwah ma tayi solving yace ba dai_dai ba, to sufa Suda they are not fans of mathematics, ai kawai su shirya wa kabarin su. Uwarki kike kallo a fuskata? ” ya watsowa Samha tambayar a tsawace, kawar da kanta tayi dan ita sam yanzu bawani tsoron shi take ba tunda ba shekaru da yawa ya bata ba, kamar yarda ya bawa su Safwah ba. Banza dak’ik’iya tun kina k’aramar ki kin iya kallon cikin idon namiji k0? Zaki gane kuran ki lunatic kawai ” Samha daurewa kawai take dan da halin tane rashin kunya da saita nunawa ya Suwayd ba tsoron shi take ji ba, dan sosai kalaman sa suka tab’a mata zuciya.
- ” Time up duk wadda ta k’ara koda one word sai ranta ya b’aci, ku bani books d’in ” ya fad’a with burning face.
- Jiki na rawa suka mimmik‘a masa, dubawa ya shiga yi ya d‘ago yana binsu da kallan takaici. ” lnnah lillahi wa’innah ilaihir raji’un ” yayi exclaiming da k’arfl, suko ko wacce banda zare ido babu abinda take.
- ” Ashe mahaukata na tara a gaba na bansani ba, tab wallahi zaku gane kuren ku, ashe asarar school fees kawai ake amma ace common solving maths kun kasa ” a fusace ya shige bedroo d’in su ya d’auko wani belt mai kyau da tsada na company’n Gucci. Takan Samha ya fara sai da yayi mata lilis sannan ya jefa mata book d’inta, cikin daka tsawa yace ” kuma kafin na k’irga uku kibar d‘akin nan “, aiko rufe baki bata bari yayi ba ta kwasa ana kare.
- Then back to Lubnah itama ta daku ba k’arya d’an da dafa bango tabar d’akin.
- Maido da kallon sa yayi kan Kadsah dake ta faman zare idanu yace ” tashi ki tafi ki bani guri, kin wani tsare ni da ido kamar mayya “, jiki na rawa ta kwashi books d’inta ta gudu. Allah sarki Safwah da Kuwaysah kallo d’aya zakai musu su baka tausayi, amma dan rashin tausayi irin na Suwayd ya zane musu jiki and again ya sasu kneel down. Ko ajikin sa yaja system d’in shi ya shiga danne_danne, Safwah jiri takeji yana neman kada ta dan zazzab’i harya rufe ta, ahankali tace ” Ya Suwayd please we are sorry “. ” +15 minutes ” shine amsar da ya bata batare da ya d’ago ba.
- Ahankali taga duhu ya gifta mata kawai ta sulale a gurin , ihu Kuwaysah ta kwalla tana kiran sunan Safwah,jin bata bata amsa ba ya sata takai hannu ta tab’a ta, sai dai me sam bata numfashi.
- lhun ne ya jawo hankalin Suwayd, cikin daka tsawa yace ” dallah can Mahaukaciya rufemin baki, tashi ki fita kafin na karya ki, idiot bastard kawai “. Jiki a sanyaye ta mik’e ta fita tana kuka mai ban tausayi, tana fita ya nufi dispenser da sauri ya d’ebo ruwa yazo ya yayya fa mata.
- Doguwar ajiyar zuciya tayi sannan ta rukun kume shi ” Ya Suwayd please don’t beat me, am very sorry I will never do it again “. Tausayin tane yayi bala’in kama shi jin yadda jikin ta ya d’au zafi kuma sai rawa yake amma ya dake yace ” dallah malama cika ni, banza Aljana kawai ” sannan ya murd’a kunnen ta cike da mugunta yace ” next time idan na baki solving maths kimin hauka, zakiga abinda zan miki, kuma kafin na k’irga uku ki fice min a d’aki “. Allah sarki Safwah she knows his last statement is impossible to her, haka ta samu da rarrafe ta taf‘l tana saka hannun ta a waje yana gama k’irgan sa. ‘
- ” Come back idan kika sake ko taku d’aya kika k’ara sai ranki ya b’aci “, dajanjiki ta dawo tana kuka tana bashi hak’uri amma mugun sai da ya sake dukan ta sannan ya barta ta fita. A hanyar shiga Babban falour ta fad’i dan bata da sauran k‘arfln da zai k’arasa da ita, tana kwance helpless hannun ta dafe da kanta saiga ya Omar da Uthman nan sun dawo daga work.
- Sam basu kula da ita ba saida suka zo k’ofar shiga suka ganta, da sauri Ya Omar yayi kanta ” Safwah are you alright? What’s wrong with you? ” A yadda take ko sanin wanda ke kanta batayi, da Sauri Ya Uthman ya ciro wayar sa k’irar phantom 8 ya kira family doctor d’in su. dan yadda yaga jikin ta na shiveting kad’ai ya tabbatar masa da zazzab’i a jikin ta.
- D’aukar ta ya Omar yayi suka nifi part d’in Ummy, cikin yanayin damuwa Ummy ta nufo su tace ” mai ya same ta? ”
- ” Wallahi Ummy muma bamu sani ba, mun dawo muka ganta helpless a bakin k’ofar Babban falour ” said Uthman with concern. ‘ Wani abu ne ya tokare Ummy a mak’o shi amma ta daure tace ” shinnfid’e ta Omar kuje kuyi sallah ana kira ‘.
- Ajiye ta yayi kamar yadda Ummy ta umarce shi sannan suka fice, kusa da Safwah Ummy ta zauna ta rungumeta ajikin ta, wasu hawayen bak’in ciki suka shiga zubo mata tana takaicin tsanar da Suwayd yayi wa tilon ‘yarta.” Babu komai Safwah na komai yayi farko zaiyi k’arshe ” tayi Maganar a zuciyarta sannan ta share hawayen ta. ‘6:00 pm‘
- Safwan ne ya shigo d’auke da jakar sa a baya, kasancewar sai six yake dawowa, falour’n Ummy ya k’araso ya nemi guri ya zauna, yafi 5 minutes a zaunejin shim har lokacin bata fito ba yasa shi mik’ewa ya nufi part d’in Granny. ” Assalamu Alaikum. twiny where are you? Am back ” jin shiru ba’a amsa ba ya nufi bedroom d’in Granny.
- Ganin ta yayi ta fito daga toilet yace ‘ Granny sannu da gida “.
- ” Yauwa Twiny’n Safwah ka dawo kenan? ”
- ” Yeah na dawo but where is my Twiny? ‘
- Murmushi tayi tace sun tafi assignment dear “. ” Gurin wa? ” ya tambaya da sauri heart d’in sa na beating so fast. ” I don‘t know ” ta bashi answer a tak’aice.
- Fice wa yayi ya koma part d’in Ummy’n su, ya koyi sa’a tana zaune akan two seater sofa tana karanta Hisnul Muslim, kusa da ita yazo ya zauna yana ta b’ata rai.
- Ita kuwa bata kula shi ba harsaida ta gama addu’o’inta ta shafa sannan ta maida kallon ta kansa tace ” My Soldier what happened? Why are you frauning your face? ” ” I don’t see my Twiny Ummy, rabona da ita since morning and now almost 11 hours ban sata a idona ba, ya za’ayi bazan damu ba, and naje duba ta Granny tace sunje assignment “.
- Smile Ummy tayi tace ” yanzu duk rashin ganin Safwah’n ne yasa kake b’ata rai haka? ” Gyad’a mata kai kawai yayi sannan yace ” wait Ummy waye yake koya mata assignment d‘in? ” “ Nikam ka cika ni da surutu tashi ka tafi mosque lokacin sallah yayi ” batare da yace komai ba ya mik’e yayi waje rai a b’ace.
- Ahankali Safwah ta bud’e baki tace ” Ummy please save me Ya Suwayd will kill me, Ummy please tell him I am sorry I will never do it again “, tausayin tane ya k’ara kama Ummy cikin zubda kwalla tace ” kiyi hak’uri Baby Ya Suwayd will never kill you “.
- ” Ummy help me hold my head cirewa zaiyi, Ummy sanyi nakeji ki rufe ni ” ta fad’a da rawar murya idanun ta a rufe suna zubda hawaye. Hijab d’inta ta cire ta rufa mata sannan ta wuce ta d’auro alwala tazo ta tada sallah, bayan ta idar ta dad’e tana kwararo addu’a sannan ta mik’e ta zauna kusa da Safwah. Bata dad’e da zama ba Ya Omar suka shigo tare da Doctor, da sauri Safwan ya k’araso yana kallon Ummy, dai_dai lokacin kuma Safwah ta bud’i baki tace ” Ummy ina Twiny d‘ina? Ki kirawo min shi, I really miss him inaso in ganshi Ummy “, da sauri Safwan ya rik’o hannun ta yace ” am here Twiny, waya tab’a min ke? Sarkin mugun ta k0? Kiyi shiru inna zama soldier he will be the first person that I will shot “. ” Shut up Safwan kada na sakejin wannan maganar a bakin ka, kaji ko? ” Nodding kansa yayi, sannan Doctor ya k’araso ya sawa Safwah drip then ya rubuta mata medicines d’in da za’a siyo.
- Bayan sallar isha kowa ya hallara a dinning amma banda ‘yan matan gidan, Daddy ne (Abban Sayyid) Yace ” ina ‘ya’ya na ne? ”
- Mummy (Maman Sayyid) ce tace “ suna can suna jinya dan da alama sun tabo yayan nasu Mammy (Maman Suwayd) ce tace ” ai wallahi Suwayd ka kiyaye ni, takurawar da kake yiwa yaran nan tayi yawa, tun suna tsoron ka har sai sunzo sun daina, kaga dai yadda Haidar da Sayyid ke wasa da su amma kai in sun ganka kamar sunga mala’ika, more especially ma Safwah dan sunan ka ma inta ji jikinta har rawa yake
- Mik’ewa yayi rai a b’ace zai bar dinning d’in dan arayuwar shi ya tsani fad’a, Abuu (Abban Safwah) ya kalle shi yace ” yi hak’uri babana koma ka zauna, idan bakayi musu ba wa zakayi wa, ba k’annen ka bane
- Komawa yayi ya zauna Ummy tayi sewing shi, cike da nishad’i da k’aunar juna suke cin abincin, family’n dai abin sha’awa dan ‘yan matan ne kawai babu hatta Granny ma tana gun. Bayan sun gama kowa ya nufi part d’in sa, Allah sarki Ummy daren ranar bata runtsa ba tanajinyar ‘yan biyun ta, tana matuk’arjin dad’in yadda Safwan da Safwah ke bala’in k’aunarjunan su, dan indai d’aya ya kwanta to Insha Allah d’ayan ma saiya kwanta.
- The following day, Suwayd ne ya shigo part d’in Ummy sanye da uniform d’in sa. orange long sleeve shirt with black neck tie, sai black trouser, da Rolex d’aure a tsintsiyar hannun sa sai belt mai kyau da tsad’a na company‘n Lv sumar nan tashi tasha gyara, tsayawa fad’an kyan da yayi zan rage muku wani abu, he is just spackling as how light does. …
- K’arasowa yayi ya gaida Ummy dake zaune akan e seater tana kallon twins d’in ta, tun da ya shigo yake kallon Safwah a zuciyar sa kuwa cewa yake ” Ya sahibatul wajha jamila (ya ma’abociyar fuska mai kyau), wa sautur rai (da daddad’ar murya), anti jamilatun ( ke me kyau ce) ana uhibbuki hubban shadidan (ni ina ina sonki so mai tsana ni) ana asifya Habibty (kiyi hak‘uri ya masoyi yata) “.
- Maganar Ummy ce ta dawo dashi daga zancen zucin da yake, still idon sa nakan Safwah da tunda taji muryar sa ta runtse ido tana jin wata muguwar tsanar sa.
- Mik’ewa Ummy tayi ta nufi fridge ta d’auko masa fura da nono, dan al‘adar sa da ita yake breakfast, yana cikin sha Haidarya shigo, bayan sun gaisa da Ummy yace da Suwayd ya tashi su tafi kar suyi late, mik’ewa sukayi suka yiwa Ummy Sallama suka tafl.
- AT SCHOOL
- Final year student shine sunan dake rubuce a saman class d’in, koda na shiga teacher nagani yana musu mathematics, gaba d’aya sun bashi attention more especially su Suwayd da suke zaune a front seat.
- Bayan teacher‘n ya gama ya fita, wata ‘yar kyakkyawar budurwa da bazata wuce 14 years ba ta taso, hannun ta d’auke da sky blue coloured heart shape cake. “
- Seat nasu Suwayd ta k’araso, ta tsaya a gaban Suwayd daya duk’ufa kan duba maths d’in sa.
- ” Suwayd ” ta kira sunan shi da wata iriyar murya, banza yayi da ita kamar baiji ba.
- ” Suwayd ” ta sake maimaitawa da rawar murya, d‘agowa kawai yayi yana kallon ta batare da yace komai ba.
- ” Suwayd I know you hate me, but at least please accept my gift ” ta fad’a tana mik’a masa cake d’in dake hannun ta.
- ” So you really want me to accept a gift from you? Zee why don‘t you hear word? For how long have I been warning you to stay out of my business? But since you have no heart give me “, hannu na rawa ta mik’a masa. Sai dai me yana karb’a ya yab’a mata a fuska sannan ya fizi hanky a hannun ta ya goge cream d’in daya b’ata masa hannu, cike da rashin mu‘unci yace “ I know you must be happy now Suwayd yayi using handkerchief d’inki, now seki bar gurin nan before I did something stupid “. Ya cilla mata handkerchief d’in a fusace, da sauri kuwa ta rik’e.
- Haba gaba d’aya class ya d’au ihu wasu na fad’in Suwayd ya burge su wasu kuma na fad’in bai kyauta ba, da sauri Haidarya mik’e ya rik’e hannun ta suka fice daga class d‘in. Bai tsaya ko ina da ita ba sai school garden, kallo d‘aya zakayi masa ka hango tsantsar b’acin rai ” haba Zee for Goodness sake menene amfanin haka, for how long have I been warning you to stay out from Suwayd’s life, meyasa bakyajin magana? Zee you have no heart at all, yanzu ai kinji dad‘i he embrace you in public, now sai kiyi giving up and move on “ Haidarya fad‘a zuciyar sa na wani irin tafasa dan Suwayd ya bala‘in k‘ona masa rai. Sai alokacin wani irin kuka ya kwacewa Zee,ji take inama Allah ya d’auki rayuwarta ta huta, sam zuciyar ta batai mata adalci ba da ta fad‘a tarkon Suwayd, meyasa ta kasa cire shi aranta, meyasa a kullum jin soyayyar shi sabuwa take a zuciyar ta, wani kukan ta k‘ara dashi.
- Haidar kuwa wani bala’in tausayin tane ya dirar masa, handkerchiefya ciro a pocket nasa sannan ahankali ya kai hannun sa kan fuskarta yana wiping mata cream d’in da yayi staining mata face d’inta.
- Sannan ya shiga fad’a mata sweet words, dakyar ya samu ta lafa da kukan sannan yaja hannun ta suka k’arasa kan kujerun dake garden d’in suka zauna, dukda ranshi a b’ace yake amma ya danne ya shiga bata funny stories masu sa dariya, murmushi kawai take amma kallo d’aya zakai mata kasan na yak’e ne, dan ita kad’ai tasan mai takeji deep down inside her heart, ganin kamar ta d’an saki ranta yace ta koma class dan yasan by now akwai teacher a class …………