TAMBARIN TALAKA COMPLETE

TAMBARIN TALAKA 💅

+
                   1to5
https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/
Alhmdlh godiya ya tabbata ga Allah wanda ya sake bani daman rubuta wannan labarin bayan na kammala “SAINA AURESHI” Allah ka bani ikon gama wannan littafin lafiya dan alfarman annabi Muhammad (S A W) 
PLZ BANDA YAWAN KORAFI BANCE KAR AMUN GYARA BA, BUT IN ZA’AYI GYARAN AYI TA HANYAR DAYA DACE PLZ👏
Gida ne ginin kasa wani wajan ya rufta, an rufe da buhu, saman kwanan ya tsofe duk yayi tsatsa, kana ganin gidan kasan lallai talauci yana cikin gidan dumu2, dan haka na shiga gidan in dauko muku bayani dakyau, daki uku ne a cikin Gidan, ciki da falo guda biyu,sai wani karamin daki, dakunan duk ba wasu girma garesu ba, jin gunjin kuka a karamin dakin yasa na le’ka, wata yarinya da bazata wuce shekara goma sha bakwai ba, naga Tana kuka tare da shesheka, fara ce amma saboda wahala farin nata ya boye, Tana kukan ne rike da cikinta domin yunwa take ji, kaman zata mutu,wata mata ta leko dakin ta Saki baki tare da fadin au kuka kikeyi sai kace wanda aka bigeki, jar uba, shiga dakin tayi ta cakumi wuyan yarinyar Tana fadin bari inci ubanki sai kiyi kukan da hujja, matsiyaciya, dukanta takeyi tako ina, yarinyar na fadin dan Allah inna tani kiyi hakuri,amma Tani ko a jikinta domin hakurin da take bata kaman ma Kara zugata takeyi, saida ta mata lilis ta tabbatar data daku sannan ta barta Tana fadin yar iskan yarinya kinzo kina kuka a daki, maza ki fito kije ki siyomin garin tuwo, kuma wlh idan kika dade sai jikinki ya kuma gaya miki, dakyar ta tashi jiki babu kwari ta amshi kudin sannan ta fita, bata wani dadeba ta dawo, tani ta watsa mata harara tare da fadin maza kije ki hadamin huta kafin yan sa ido suce bana baki abinci, ta amsa da toh, ta nufi murhun, wata mata ta fito daka dayan dakin Tana fadin wlh tani kiji tsoran Allah, yarinya bata miki komai ba kullum ki kamata ki jibga, anya tani kina tuna mutuwa kuw……  Dallah dakata munafuka ke har kin isa ki dinga shiga sabga ta wlh ahir dinki, ni nafi karfinki wlh, kuma karki manta a karkashina kike domin nan gida nane, matar tace gidanki ko gidan marayu? Nan Suka dunga gayama juna magana ita dai indo tuwo ta daura amma ji take kaman a tsakiyan kanta suke wannan ihun,….. Wacece Indo?
WACECE INDO
Mlm aminu shine mahaifin indo, mazaunin taraba ne a karaman hukuman karan lamido, fulani ne na taraba, yana da mata daya maryam, mlm aminu talaka ne bashi da kudi, domin nanin takalmi yakeyi, gidansu gidan kasa ne,duk da talaucin shi, gidanshi Alhmdlh suna ci koda babu dadi ciki zai dauka, domin mlm Aminu yace TAMBARIN TALAKA CIKINSA, koda ba’a sami tuwo ba za’asha fura ko gari,cikin farin ciki, Mlm Aminu suna zaune da kanin shi a gidansa mai suna musa, yana da mata tani, tana da yara biyu mata, bintalo tayi aure sai abu, Sa’ar indo, tani azabbar Mace ce domin sai abunda tace ma musa yakeyi, ita kuma maryam Tana da hakuri sosai sai yasa mijinta ke sonta, yaran mlm Aminu biyu, yusuf wanda saida ya shekara biyar kafin aka haifi aysha indo, wanda suke kira da indo, aysha tun Tana jaririya take dakyau gata fara sol, Tana da shekara 7 a duniya mahifinsu ya rasu, tun daka lokacin rayuwa ya canza musu, musa ya kanaye gidan duk da bashi da Gado domin Yusuf ya musu katanga, wannan abun yasa Mlm musa tsanan maryam da yaranta musamman ma Yusuf, maryam tun rasuwan mijinta take ta fama da ciwo sosai, wata rana Tana zaune da yusuf da indo a daki bata jin dadin jikinta, ta kalli yusuf wanda ya kusa gama secondary, tace yusufa dan Allah koda bayan raina inaso ka kula Min da indo karka bari tayi maraici domin bata da kowa sai kai, Yusuf jikinshi yayi sanyi yama kasa magana yana sauraranta idonshi ya kada yana zubar da hawaye, itama indo duk da batayi wani wayau ba ganin halinda suke ciki yasa itama ta nutsu Tana hawaye, maryam taci gaba da fadin yusufa duk rintsi ka kulan min da ita karka bari tayi zaman kadaici ka zame mata uwa da uba, domin bata da kowa sai kai, ni nasan ciwan nan bazai barni ba, naso inyi tsawan rayuwa dan in kasance daku, amma bana jin hakan zata faru, Tana zuwa nan ta fara hawaye taci gaba da fadin sannan inaso kabar indo tayi karatu dan Allah domin tayi alfahari da kanta wata rana,rayuwan Mace kalilan ne, Tana fadin haka ta kamo hannun yusuf dana indo ta rike tana murmushi, lokaci daya bakinta yayi motsi Tace ga garinku nan, Allah ya mata rasuwa, Yusuf da indo sunsha kuka sosai har tani ta tausaya masu, haka rayuwa ta kasance musu tun daka lokacin rikonsu ya dawo hannun kanin babansu mlm musa da Matar shi tani, mlm musa ya kane naye gidan ya zama nasa, dan haka ya kullama Yusuf shairi kan cewa yana neman kanwarsa, mai gari ya kori Yusuf daka garin kan cewa duk sanda ya sake zuwa sai an kashe shi, wannan ne sanadin barin Yusuf garin mlm musa da tani Suka kanai naye gida Suka sa yar haya mai suna jamila, tana tausaya ma indo sosai sai dai babu yanda ta iya, tani taci gaba da musguna ma indo bata zuwa islamiya balle boko sai daukar ma tani tallan kayan sana’a yau tani tayi wannan gobe tayi wancan kuma idan Indo bata saida ba sunanta sorry, domin ranan sai taci duka sosai, kuma ta hanata abinci, mlm musa idan ya dawo shima ya kara mata wannan shine rayuwan Indo….. 
STORY CONTINUES BELOW
Taku Maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅
                      NA
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA
                        5to10 
https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/
Indo ta kammala tuwan ta kwashe sannan ta daura miyan kuka, bata jima ba, ta kammala miyar koriya shar dan ban tunanin ansa manja a ciki, dakin tani ta nufa da sallama, kaman dai kullum tani bata amsa ba dan haka tace inna na gama, tani tace toh dan uwarki a bakin kofar zaki tsaya ba zaki shigo ki Kawo min ba? Cikin sauri ta bude bakin labulan daya canza kala daka fari zuwa milk colour, ta Shiga jiki a sanyaye bayan ta ajiye ta dan tsaya ko zata bata nata, tani tace uban Me kike jira kuma mayya mai bakin hali, Ai yau tunda kika ja wancan bakar matar tamin tujara wlh baza kici wannan abincin ba , ta sakar mata rankwashi mai zafi tare da fadin fitar min a daki kar ki tasar min y’a, simi2 ta fice hannunta nakanta Tana hawaye dan taji zafin rankwashin sosai, dakinta ta shiga ta kwanta akan tabarman ta, kuka takeyi Tana fadin yusufa dan Allah kazo ka tafi Dani tun kafin inna tani ta kashe ni, duk da inda Tana yarinya lokacin da mamanta ta rasu ta rike wasu abu, musamman burin mahaifiyarsu na indo tayi boko, amma gashi babu islama balle boko, duk da itama indon tana so amma babu dama dan tani fur tace talla zata dinga mata domin kan indo bana boko bane, na daukan kayan tallah ne, haka indo ta kwana da yunwa duk da baccin da tayi rabi da rabi ne domin yunwa ga yunwan dare bashi da hankali amma duk nacinta haka tabar indo, 
1
Washe Gari tunda asuba indo ta fara share tsakar gidan wanda babu suminti sai ‘Kasa, duk da garin bai gama haske ba, domin tani tace indai ta fito batai shara ba sai taci ubanta sai yasa takeyi daka ta idar da sallah, bayan ta gama sharan ta dauki bokiti domin dibo ruwa a rijiya, gidan da take dibo ruwan basu tashi ba dan yar kofar kyauran nasu a rufe yake dan haka ta nufi rafi domin ta dibo rafin akwai nisa sosai kuma yawanci maza Suka fi zuwa, domin yan iskan garin anan suke taruwa in Suka ga mace har fyade suke mata, haka indo ta nufi rafin dan tasan indai ta koma tani taga babu ruwa toh kashinta ya bushe , Allah ya taimaketa bata ga kowa ba harta gama diba, sannan ta fara hada kayan wanke2 a lokacin tani ta fito Tana hamma kaman za taci mutum, gefen murhu ta kalla sannan ta kalli indo tare da fadin amma ke ko matsiyaciya yanzu murhun ma baki hada ba, dan iskanci, indo tace kiyi hakuri inna So nake idan na gama wanke2 in hada, tani tace au yanzu har sai kin gama wanke2 bayan Kin san abu bata da juriyan yunwa, wlh kafin in fito daka bayi ki hada murhun nan, indo da sauri ta nufi murhun Tana hadawa bata dadeba wutan ya kama danma itacen busashene, tani ta fito daka bayi ganin wutan naci tace maza ki daura ruwan kunu tunda kullum ke sai an fada miki, Daura tukunya tayi,tare da hada kayan wanke2 Tana cikin yi abu ta fito Tana fadin tani an gama kunun? Tani tace ina fah wannan mai idon kaman na mayu ta tsaya bata lokaci kuma tasan sarai bakya jure yunwa, Abu tace wlh tani laifinki ne aida kinci ubanta nidai yanzu yunwa nakeji gaskiya, tani ta tashi ta nufi indo wai dan uwarki ba zaki duba ruwan koya tafasa ba, Indo jiki na rawa ta tashi dan kar tasha duka ga yunwa Tana ji, bude tukunyan tayi ruwan yana alaman tafasa, ta kalli tani tace inna yanzu zaiy….kafin ta karasa taji saukan mari ke wace irin yar iska ce, kunu tun dazu kin kasa gamawa, bayan kin san sarai abu bata da hakurin yunwa shegiya mai bakin hali, dakikiya komai sai anyi ta nanata miki, bakya daukan komai, indo data rike fuska dan zafi ta nufi tukunyar dan taga alaman ya tafasa, daukan ruwan tayi ta juye a kunun tare da rufewa, tani ta dauki kunun tayi daki dashi ,indo taci gaba da wanke wankenta, duk wannan abunda akeyi jamila na daki Tana ji amma babu yanda ta iya, bayan indo ta gama aikinta ta nufi dakin tani tare da fadin inna na gama, mlm musa yayi tsaki tare da fadin wannan yarinya ko mayya naso ace itama ta mutu tabi iyayenta matsiyaciya ita dai kanta na kasa dan bata san yana ciki Bama, tace ina wuni abba, yace ni ba abbanki bane ki kirani da musa na, mara mutunci kawai, tani ta tura mata kunu dan kadan a kofi tare da fadin gashi mayya dan nasan danshi kikeyi, indo ta amsa tare da fita daka dakin tunda ta kafe kanta a kofin saida ta shanye kunun sannan ta ajiye, jinta take kaman bata sha komai ba, domin kunun dan kadan ne, Tana zaune a dakinta  tani ta bude dan kyauren Tana fadin au ba zaki zo ki fere rogon ba, indo tashi tayi tani ta kai mata rankwashi akai, tare da fadin mayya kawai, indo fere rogon take tayi, sannan ta daka, bayan ta daka ta dauko karamin abun nikansu na dutse, haka ta dinga nikawa yana laushi sannan ta kwashe tasa wani, bayanta da hannunta babu abunda yake sai ciwo kaman zata mutu dan azaba domin bayanta yayi mugun rikewa, ga rogon da yawa, bayan ta kammala tani ta fito ta hada tare da mummulawa harta gama sannan ta kirga tace ma indo ta soya, bayan ta gama suya tani tace na dubu biyu da dari hudu da ishirin ne wlh ki tabbata kin dawo mun da kudina dai2 sannan karki dawo min gidan nan in baki siyar ba, indo ta amsa da toh sannan ta dauki buta dan ta wanke Jikinta tani tayi saurin cewa ajiye min buta uban me za kiyi dashi? Indo tace zan wanke jiki nane, tani ta tabe baki tare da fadin dama kinzo kin wuce dan banga amfanin wanke jikin ki ba, haka ta ajiye butan ta fita, hanyar tasha ta nufa domin tasan anan zata fi saurin yin ciniki wata mota ce ta danno da gudu indo garin saurin ta matsa wainar rogo ta kife a kasa…….
1
STORY CONTINUES BELOW
Taku maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅
                      NA
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA
                        10to15
https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/
DEDICATED DIS PAGE TO  AYSHER HUYMERAH LIKYMO❤
Indo kuka ta Saki Tana kallo ganin babu komai a roban domin duka ya zube a kasa, gashi mai motan bai tsaya ba, yara ne Suka fara wawa suna diba, indo ta tashi Tana kuka Tana kora yaran idan tabi wannan ya gudu wani ya dawo haka Suka maidata kaman mahaukaciya, ganin yaran Sun kwashe duk da kuwa akwai kasa a kai yasa indo zama a gefen titi Tana kuka kaman wacce akace mamanta ta mutu, duk wanda yaga yanda take kuka saiya tausawa mata, sai dai kuma duk masu tausaya mata babu wanda zai iya biyan kudin domin kowa nata kanshi, duk wanda yaji abunda ya faru sai dai yace mata Allah ya kyauta ko kuma yace yara basa duba hanya sai suyi ta sako kai bakin titi, indo saboda tashin hankali yasa ko yunwa bata ji duk da kuwa ta diba lokaci mai tsawo a wajan Tana kuka, domin bata ma tunanin Zuwa gida, dan tasan yau in taje gida kwananta ya kare domin tani kasheta za tayi, indo ta tsine ma mai motan nan yakai sau dubu tare da fadin ko waye wannan ya cuceta
Tani keta faman surfa ashar Tana fadin wlh yau saina ci uban wannan yarinyar yanzu har an kira magrib bata dawoba, kai wannan ko yar iska, kullum sai ta Sani surutu yau zanyi maganinta wlh saina nuna mata ni tani bani da imani wlh, abu tace yoo tani bakece kike Raga mata ba, sai yasa ta raina ki ba, inda kina dukanta kullum kaman sau goma a rana aida tabar miki iskanci, Tani tace kin san gidan akwai yan tsurku masu jira ayi suyi ta yayata ka, kaman ka kashe mutum ko an Kama ka da kato, abu tace tani yasin mu kori wannan jamilan munafuka ce, rannan fah da kika fita har daba indo abinci tayi ina daki ina ji, Tana cewa tayi sauri taci Kafin ki dawo, tani tace bura uba yaushe akai hakan shine baki fada min ba, abu tace rannan mana, tani ta tashi fuuu tayi kofar jamila ta fara fadin fito bakar munafuka, jamila dake daki duk Tana jin abunda suke fada,ta fito Tana fadin karki balla min kofa wlh tani ki fita a idona, tani tace jar uba, ni kike fadama haka toh wlh yau sai kin kwashe kayanki kin bar min gida, bakar munafuka, jamila tayi dariya tace saiki dawo min da kudin hayan dana baki, nan tani tayi shuru domin ta rasge kudi, ganin tani tayi shuru yasa jamila fadin wlh tani kiji tsoran Allah yarinyar nan marainiya ce, bakya jin tsoran hakkinta ya kamaki duk kin kanai naye dukiyar su keda Mi……  Dallah yimin shuru ina ruwanki wlh jamila ki fita daka idona wlh ni da kaina ina tsoran kaina wlh karki hasala ni wlh idan baki fita daka idona ba saina maidaki abun tausayi, jamila tayi murmushin takaici tare da fadin wlh tani ina guje miki hakkin yarinyar nan ya kamaki amma tunda kince haka kije kiyi tayi kema Ai kin haifa, tani tace toh mai bakin baki babu abunda zan gani Dani da yarana sai alkhairi, nan tani taita zagin jamila ganin haka yasa jamila ta koma daki tare da fadin kudinsu na karewa zasu bar gidan dama mijinta tun tuni yake cewa su tashi amma tace ita tafi son zaman nan, yaso ta bishi cikin taraba inda yake aiki tace a’a, amma wannan karan zata bishi ko kuma su canza Gida.
Wani makeken gida ne, naga motoci nata shiga, nima dai nace bari inje inga mai akeyi a ciki, motoci sunkai talatin a cikin gidan daka ganin alama taro akeyi a cikin gidan, dan haka nima na kusa kai, wani katon falo na gani fadan tsaruwan falon bata lokaci ne, jin magana nayi kasa2 dan haka na nufi inda nake jiyo maganan, subhanallah wani hadaddan Guy na gani kaman balaraban kasar dubai, wannan daka ganin shi ya hada jini da larabawa, daka gani meeting sukeyi, sun dauki wajan 30mnt sannan mutanan Suka fara fita, wannan Guy din na gani ya tashi ya haura sama wani naga ya bishi yana fadin majeed yaushe zamu je wajan mum ta kirani yakai sau goma, Majeed ya tsaya tare da kallon shi yana fadin kai, abdul wlh kana takura min tun dazu kake min mita ka bari in huta mana, yana fadin haka ya nufi wani daki, bedroom ne dakin babba ne komai na dakin brown ne yayi kyau sosai, rage kayan jikinshi ya fara yi, sannan ya shiga toilet, yayi wajan 30mnt sannan ya fito yana goge gashin kanshi da towel, saida ya gyara gashin nashi sannan yasa wata jallabiya ya kwanta, wayanshi yaga yana haske, tsaki yayi tare da daukan wayan lokaci daya yayi murmushi ganin sunan Mum ne a jikin screen din wayan, dauka yayi tare da fadin Mum cikin shagwaba yake magana, tace son kai nake ta jira, yace Mum am so tired wlh sai yanzu muka gama meeting, ga surutun abdul, Mum tace kai son Abdul dinne yake da surutu, yace eh Mum dazu fah muna hanyar zuwa nan wata yarinya tazo zata shiga mu kuma mun zo wucewa shine ta zubar da kayan kanta, shine wai mu tsaya a biyata, dan na hana driver shine yake ta surutu, Mum tace son ai gaskiya abdul yake fada maka, kaida na sanka da tausayi aiko bakai bane sila ya kamata ka tsaya ku bata kudin asaran da tayi ,  ganin Mum din kaman itama tana supporting Abdul yasa yace Mum bari in huta anjima zan shigo, murmushi kawai tayi tare da fadin sai kazo……… ku biyo ni domin jin waye majeed
STORY CONTINUES BELOW
Taku maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅
                      NA
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA
                        15to20
https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/
Abdul-majeed d’ane ga governor din Taraba state, mai ci yanzu wanda yake neman kujeran Sanata a halin yanzu, govn Muhammad mutum ne mai tausayi dajin qan na kasa dashi, govn muhd iyayenshi masu kudi ne gaba da baya, ya taso cikin kudi a kasar Egypt yayi karatun sa, inda a nan ya hadu da fatima suka fara soyayya fatima balarabiyar kasar Egypt ce, soyayya suke sosai lokacin da iyayenta Suka sani hankalinsu ya tashi sosai domin basu taba Kawo yarsu zata fada soyayya da wanda badan kasar suba, dakyar iyayenta Suka yarda akayi bikin ganin gudan yar tasu ta nace, haka akai biki na gani da fada, aka kawo fatima Nigeria taraba state,shekaransu biyu da aure Suka haifi abdul Majeed tun yana karami yake dakyau domin sak mahaifiyarshi zaka rantse mahaifinshi ma balarabe ne idan ka ganshi, ga gashi irin na larabawa da yake dashi gwanin ban Sha’awa, tun daka kanshi haiyuwa ya tsayama fatima, duk da abun yana damunta amma mijinta ko a jikinshi ,govn muhd bayan ya gama karatu ya fada siyasa dan abunda ya karanta ma kenan political science, tun daka Chiarman ya fara yaci zabe, yazo dan majalisan taraiya, ganin irin aikin da yake ma Al’umma yasa Suka ce ya fito takaran govn da farko yaki yarda amma ganin magiyan mutane yasa ya yarda cikin ikon Allah kuma ya haye, govn Muhd ya Kawo ci gaba sosai, wanda a yanzu yana neman takaran sanata, A Majeed tun yana yaro iyayenshi suka sangartashi domin shi daya garesu a London yayi karatu kuma a nan ya hadu da yar president mai suna zainab suka Fara soyayya, bayan sun gama karatu Suka dawo suka ci gaba da soyayansu a nan A Majeed yana da taimako da tausayi ga kyauta, bai dade da dawowa ba ya samu appointment daka CVN Central Bank of Nigeria, aka bashi mukamin mataimakin GM tun daka lokacin ya koma abuja da zama, yana yawan zuwa taraba sosai shekaranshi biyu akan mikamin akai bikinsu shida zainab bikin da aka kashe naira kaman babu gobe, Zainab mace ce mai nuna isa da gadara harta masu mata aiki tsoran yi mata laifi suke gata Tana da kishi sosai duk da bawai wani kula da mijin nata take ba, yau Tana can kasar gobe tana wancan kasar duk da abun yana damun A Majeed amma haka yake hakuri domin yana sonta sosai, zainab Tana da Kyau sosai Tana da diri mai kyau uwa uba ga kudi ga babanta president sai yasa take yin abunda take So, ga miji ta samu na nunama tsara domin A majeed namiji ne wanda duk wata Mace za tayi burin samu ga kyau ga kudi ga miskilanci idan kaga yana magana da dariya To shida iyayenshi ne ko abun kaunar shi zainab, amma bai cika magana ba, sai dai akwai kyauta da tausayi,zainab duk wani abu ta samu sai yasa take taka wanda taso, A Majeed yaso su zauna a taraba shida Zainab amma taki gidan daya gina a taraba in yazo a nan yake sauka harta meeting ma in yana Dashi a nan yake yi wani zubin abdul abokin a Majeed ne yaron abokin mahaifinshi ne abdul tare suke aiki a cbn abdul yana jure halin miskilancin A Majeed amma shi bashi da aure wannan kenan. 
MUN DAWO KAN LABARI
A Majeed sai wajan 4 ya tashi, toilet ya nufa yayi alwala sallah yayi, sannan ya koma toilet yayi wanka, ya fito yana shiryawa cikin wata riga da wando masu kyan gaske, ya dauki lokaci yana gyara gashin shi, tare dasa Turare kala2, kamshi kawai ke tashi tako ina, kai tsaye ya fito falo abdul ya gani yana cin abinci a takeaway, A Majeed, ya tabe baki tare da fadin yanzu takeaway kake ci ba zaka bari muje gidan Mum ba, Abdul yace sai inyi ta jiranka yunwa ya kashe ni koh? A Majeed ya tabe baki tare da fadin inka ga dama ka fito muje, Abdul tashi yayi yabi bayanshi, A Majeed a baya ya zauna driver yaja motar Suka fita abdul kuma cikin motarshi ya shiga shima ya bisu a baya, kai tsaye wani dangareren gida naga Sun shiga ga sodoji da police makil a wajan gidan, harta cikin gidan ma security ne makil, bayan driver ya faka A Majeed ya fito shima abdul ya bude tashi motar ya fito nan security Suka Fara gaida A Majeed amma ko kallo basu isheshi ba danshi haushin gaisuwan ma yake ji, sai abdul ne ke amsawa, falon gidan yayi Bala’in tsaruwa sosai,wata mata wacce ba zata wuce shekara  45, amma kyan jikinta zaka dauka ba tafi shekara 30 ba, kana kallonta kasan balarabiya ce, Tana zaune akan makeken kujeran falon Tana shan fruit ganin gudan jinin nata yasa ta tashi da sauri tayi hugging dinshi tare da kamo hannunshi ta zaunar Dashi akan kujera kaman wani yaro karami, shi kuma sai kara shagwabe mata yake, abdul dai dariya yakeyi dan inda sabo ya saba da ganin irin son da Mum ke nuna ma dan nata, shi kuma yaita shagwaba kaman dan jariri, Mum tace son ya abuja cikin hausa tayi maganan amma zaka dauka da larabci takeyi, yace Mum lfya, yunwa nake ji, Mum tace tashi muje dinning sai a sannan ta lura da abdul dake ta dariya Mum tace Abdul Ashe tare kuke ban lura ba, ya aiki?  Nan ya amsa da lafiya tare da gaida Mum din sannan Suka nufi dinning Mum ce tayi saving dinsu duka, A Majeed cin abincin yake kaman za’a dauke mai,mum kallonshi take tana tausaya mai domin ita dai matarshi bata da lokacin dafa abinci, sai masu aiki wani tym din kuma yaci takeaway indai abinci zaici cikin natsuwa toh yazo taraba ne, bayan Sun kammala Abdul ya mike tare da fadin mum zan koma abuja yanzu, Mum tace Abdul dare zai maka fa, yace wlh Mum ina da aiki sosai gobe,  baby Boy ne yasa muka zo taraba wai anan za ayi meeting, A Majeed ya tamke fuska tare da fadin wlh abdul Ka rainani da yawa, kasan ni boss dinka ne wlh idan ka kara cemin Baby boy saina turaka maiduguri course, dariya abdul yayi sosai tare da fadin Mum bari in tafi, mum tace toh ina zuwa danna wani abu tayi kaman remote saiga wata tafito cikin riga da skirt baki kanta babu dan kwali, mum tace Kawo min bucket na dambun nama daya da cake, tace ok your excellence, ba tayi minti uku ba ta Kawo ita da wata, Mum tace Abdul gashi sai kayi taci Allah ya kiyaye hanya, ya amsa da ameen sannan ya Kalli A Majeed daya wani tamke fuska yace A majeed na wuce yace safe journey, sannan ya fita ,nan Mum da dan nata Suka zauna suna ta fira cikin So da kauna. 
STORY CONTINUES BELOW
Indo dai Tana wajan da take Tana kuka, Abdul dake tafiya yaga kaman yarinyar dazu ce,da kayanta ya zube, kaman zai wuce dan bai tabbatar ba, har yayi gaba ya dawo baya, bayan yayi parking ya  fito sai yanzu ya gane itace domin roban yana makale a hannunta, yace baiwar Allah lafiya kuwa, bata bashi amsa ba sai kuka da takeyi kanta na mata ciwo, yace ko kurma ce ke, nawa ne kayan naki, cikin sauri ta dago Tana fada mishi, tausayi yaji ta bashi kudin koh 3k bai kai ba, mota ya koma ya dauko 5k ya bata amsa tayi da sauri ko duba yawan kudin ba tayi ba, ta fara  fadin ngd tare da rugawa da gudu dan taje gida yana kiranta amma ina tayi nisa……. 
Taku maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅
                     NA
                     
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA
🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝
Vote me on wattpat @maryam-obam
WWW.maryamobamnovels.blogpot.com
                      20to25
DEDICATED DIS PAGE TO…
UMMY ONTOP ❤
INA YINKI SOSAI🤝ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MIKI HAR GADON BACCINKI👏
Abdul kai ya girgiza tare da daga kafada ya nufi motarshi ya wuce, tuki yake yana tunanin tsawon lokacin da yarinyar ta kwashe a wajan, domin ya tabbata bata je gida ba, a hankali ya furta Allah ya kyauta 
Kai tsaye gida ta shiga, tani na zaune akan tabarma ita da abu, suna surfa mata zagi kan taki dawowa sai gata ta shigo, Tani tashi tayi fuska daure ta nufota tare da mika mata hannu alaman ta bata kudinta, indo cikin sauri ta mika mata sababbin dubu daya2 da Abdul ya bata, indo amsa tayi tana kirgawa washe baki tayi tare da fadin, wajan wa kika je ya miki juye?  Indo tace Inna dana fita ne wainar rogon ya zube shine wani mutum ya tambayeni na nawa ne, shine yaban kudin, tani tace sai kuma akayi me, indo tace sai nazo gida, tani tace oh yau naga makira dan ubanki ba zaki fadamim abunda kukayi ba, indo ta fara kuka Tana fadin wlh inna babu abunda mukayi, Abu dake zaune a gefe ta tashi tana yatsina fuska tace Tani kinga baki duketa ba amma tana miki kuka wlh ta rainaki, nan Tani ta harzuka ta fara dukan indo saida ta mata lilis sannan ta barta, indo dai dakyar taja jiki tayi daki, ga kanta na ciwo domin kukan da tasha, ga zafin duka, ga yunwa abubuwa sun hadu sun mata yawa, lokaci daya zazzabi mai zafi ya rufeta ta fara rawan sanyi.
Tani bayan sun shiga daki ita da yarta Abu, Tani ta kalli abu tace kinga wannan sabbin kudin wlh ajiye su zanyi domin bazan kashe suba, saida bikin ki, Abu ta washe baki tare da fadin Tani wai yaushe zanyi aure ne, kinga fa dan jummai kullum sai yace yana son ya turo kinki bari yazo, Tani ta daure fuska tare da fadin haba Abuwa, mai za kiyi da dan jummai bayan kin san bashi da sana’a Ai gwara ki auri mai kudi ko yaran mai gari, Abu tace hakane kuma fa Tani, jiya naji ana fadin dan mai gari, ma ya dawo daka wani kasa a jirgi ake Zuwa wai ya gama karatu, Tani tace To kinga yanzu abunda zaki dinga yi kullum ki dinga wanka kina kwalliya ki dinga yawan wucewa ta wajan gidan mai gari hala ya ganki yace yana so, koya kika ce? Abu tace kai Tani kina da wayau ni yarinyar mai gari ma kawata ce wlh saudat kinga sai in dinga zuwa wajanta, Tani tace yauwa yar autata, yanda kike da kyan nan Ai sai mai kudi, Abu ta washe hakora cikin jin dadi, suna cikin firan malam musa ya dawo abu ta koma falo dan yin bacci.
Indo na kwance taji an kira asuba, gashi zazzabin da takeji kaman ana kara rurashi ne, ko tashi ta kasa balle tayi sallah, ganin lokaci zai kure yasa ta tashi dakyar ta nufi waje tayi alwala, hakoranta sai kadawa suke domin sanyi, bayan tayi sallah, ta dan kwanta bacci ya dauketa, har wajan karfe bakwai da wani abu, Tani ta fito taga batai shara ba gashi babu ruwa sosai, dakin indo ta nufa ta buga kofar da karfi ta bude, shiga tayi taga indo a kwance tana bacci, Dagewa tayi iya karfinta ta d’aka mata duka, indo a razane ta tashi tare dayin wata kara, ganin Tani a tsaye a kanta yasa ta fara kokarin tashi amma ta kasa, Tani tace dan uwarki ni kike so inje inyi aikin ko wa? Indo tace kiyi hakuri inna wlh bani da lafi…..  Tas ta wanketa da mari ubanki da rashin lafiyan, in baki da lafiya wannan keta shafa,bani ba dan haka maza ki fito wlh kizo ki fara hada wuta, ki daura ruwan kunu Kafin kije dibo ruwa, yar iskan yarinya kawai kin san sarai Abu bata da jimirin yunwa amma dan iya shege shine zaki zauna kina bacci har yanzu wai baki da lafiya ai wlh indai kina cikin gidannan dole kiyi aikin ki wlh koda kuwa ciwo zai kashe ki, indai kinga na kyaleki to gawarki ce dan nasan daka ranan kin gama amfani, ba zaki tashi ba sai na karyaki makira, dakyar indo ta tashi tana kuka ta fita, murhu ta hada tare da daura ruwan kunu, sannan ta fara shara, jamila ta fito tace tabar sharan za tayi, Tani ta leko tace wlh baki isaba, jamila wlh kina shigar min hacci da yawa, ita dai indo ci gaba tayi da sharanta duk da kuwa Tana jin jiki, jamila kai ta girgiza tare da komawa daki Tana tausaya ma indo, bayan ta gama sharan ne ta fita dibo ruwa, Allah yasa yanzu gari ya waye sosai kowa ya bude gida, makotansu ta shiga ta dinga dibowa, har saida ta gama, ruwan kunun nata tafasa amma Tani taki hadawa wai dole sai Indo ta hada, haka Indo ta dama kunun kaman kullum tani ta dauke bayan ta dama, indo ta hada kayan wanke2 ta zauna tana wankewa tare da rawan sanyi, harta gama Tani ta kwala mata kira, da sauri ta nufi dakin bayan ta gaida mlm musa baiko kalleta ba balle ya amsa, tani ta bata kunu da kosai guda uku, gashi maza kici kizo ki daka rogo, indo ta amsa tare da fadin toh, sannan ta koma daki bayan tasha kunun ta danji dama2 sai dai har yanzu Akwai zazzabin a jikinta,haka ta fito ta dauko rogo ta fere sannan ta daka ta fara nikawa har yayi laushi, har dishi2 take gani, yau ita ta liliya sannan ta soya, bayan ta gama takai ma tani ta kirga, tace wlh karki dawo min dako guda daya gida, tace toh inna, Tani tace matsiyaciya sai ladabin karya kaman mutuniyar Allah, sai shegen bin maza kaman karya, indo dai shiru tayi tare da daukan roban ta fita.
STORY CONTINUES BELOW
Yan mata, Yan mata, kodai kurma ce ke, ya inata magana kinyi shuru, indo ta tsaya tare da fadin kayi hakuri wlh banji bane, na nawa zan baka? Murmushi yayi tare da fadin tunanin mai kikeyi haka? Sai a sannan indo ta dago ta kalli fuskanshi, kyakyawa ne ajin farko ga gayu duk yanda akayi wannan badan kauyensu bane, ba’ko ne, ganin tayi shuru tana kallonshi yasa yace kiyi hakuri idan tambayan ba tayi miki dadi ba, ni sunana sulaiman yaron mai gari, nan indo ta gaidashi ,murmushi yayi tare da amsawa yace amma mai yasa kike tallah bakya zuwa makaranta gaki kyakyawa, Indo shuru tayi ganin yana kallonta yasa tace zan tafi tallah kar in dade aimin fada, bai ce mata komai ba sai ido daya bita dashi ganin haka yasa tayi gaba abunta, ganin zata mishi nisa yasa yabi ta harya cimmata yace ya zaki tafi bayan ina magana dake, indo tace dan Allah kayi hakuri wlh idan na dade za’a bigeni kuma inna tace in saida duka, nanata kalman yayi duka sannan yace na nawa ne duka? Tace na dubu daya da dari shida da shabiyar ne, kai ya girgiza tare da zaro dubu biyu yace gashi,tace bani da canji yace ki rike canjin, yanzu sai kizo mu zauna acan idan yara sunzo wucewa sai mu dinga basu sadaka, mu kuma sai muyi firan mu koh, ganin yanda yake kallonta gashi yana mata kwarjini yasa tayi shuru bata ce komai ba, dakyar ta yarda Suka koma gefe, shi da kanshi in yaga yara yake zuba musu ya basu, indo har yanzu tana jin zazzabin dauriya kawai takeyi ga yunwa, kaman daka sama taji yana fadin gashi kema kici, wainan rogon ne ya zuba mata da yawa a takarda amsa tayi ta fara ci, hannu baka hannu kwarya, kallonta yake tayi yana mamaki harta gama ya amso mata ruwa a wani shago, indo tayi nak rabonta da taci abinci ta koshi harta manta sai yau, yace baki fadamin sunanki ba, tayi kasa dakai tace sunana indo, dariya yayi yace aysha koh? Tace eh yace toni zan dinga kiranki da esha hakan yayi koh? Bata san lokacin da tayi murmushi ba tare da daga mai kai sannan ta tashi tace toh ni zan tafi kar ace na dade tunda ya kare, ido ya bita Dashi sannan yace toh muje in rakaki sai inga gidanku koh?  Zare ido tayi…….. 
Taku maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅
                     NA
                     
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA
🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝
Vote me on wattpat @maryam-obam
WWW.maryamobamnovels.com
                      25to30
DEDICATED DIS PAGE TO…
MRS DAN MALIKI
UWAR GIDA SARAUTAR MATA💑 ALLAH YA KARA MUKU SON JUNA KEDA OGA 
YA TSOLE IDON MAKIYA👏
Murmushi yayi tare da fadin ko bakya son insan gidan kune? Kai ta girgiza alaman a’a, yace ok To muje, tace idan aka ganni dakai za’amin fada, yace ok ina ne gidan, tace dan Allah kar kazo wlh idan inna ta ganka sai anyi min duka, shide mamaki take bashi idan ta kira kalman duka, ganin yanda tayi kaman za tayi kuka yasa yace toh shikenan yanzu a ina zan kuma ganin ki? Tace idan na fito tallah, yace shikenan ki gaida gida, sauri ta farayi kaman zata tashi sama, wani yaro dake wasa a wajan amma yana da wayau yace kai kasan yarinyar can?yaron yace eh, nan ya tambaye shi ina ne gidansu, yaron yace muje in nuna maka, nan sulaiman yace suje, indo Kafin ta shiga gida saida tayi canji a chemist tasai Magani sannan tasha ta boye sauran canjin kar tani yau ma tace tabi wani, bayan ta shiga gida babu kowa a tsakar gidan dakin Tani ta shiga ta ganta a kwance, Tani na ganinta ta tashi tare da mika mata hannu, indo ta bata kudin, kirgawa tayi taga sun cika dai2 Tani tace amma yar nan kina da bakin hali, yau shine kika ‘ki zuwa wajan da za’ayi miki juye ki samo min sababbin kudi, ita dai indo shuru tayi bata ce komai ba, nan Tani tayi ta sababi tare da bata wani tuwan dawan daya kwana biyu, amsa tayi dan baci ma za tayi ba dan a koshe take, dakinta ta nufa ta kwanta domin ta huta, maganin da tasha yasa zazzabin ya saketa, ta fara bacci Tani ta shigo taga tuwan a gefe ita kuma tana sharan bacci, Tani tace jar far uba, bacci ma kikeyi fita tayi sai gata da buta ta fara zuba mata Ruwa a jiki da sauri Indo ta tashi cikin tsoro ganin Tani yasa ta tashi tsaye tare da fadin yakuri inna dan Allah, Tani tace dallah rufemin baki shegiya maza fita kije kimin cefane, ta mika mata naira dari gashi ki siyomin wake gwangwani daya, tarugu na goma, albasa na goma farin magi guda daya kuma idan kika dade ni dake ne, kuma wannan tuwan ubanki ne zaici,?tace inna zanci kaina ke ciwo tani ta tabe baki, tare da mika mata kudi, bayan ta amsa ta sakar mata ran kwashi mai zafin gaske fita indo tayi tana hawaye tare da rike kan, kai tsaye inda aka aiketa ta nufa ta siyo komai ta dawo gida, ko zama ba tayi ba ta hada murhu domin daura abincin dare. 
STORY CONTINUES BELOW
A Majeed ne a cikin katon office dinshi, yana danna wayanshi, Abdul ne ya shigo bayan yayi nocking, abdul yace kai A majeed yau wata rana, A Majeed yace mai kake nufi? Abdul yace naga yau ka dawo kuma gaka a Office kaida in kayi tafiya sai kayi kwana biyu baka leko ba, amma yau gaka a office, A Majeed yace kana da sa ido wlh Abdul ni mai ya Kawo ka ma, abdul yace babu komai kawai nazo wajanka ne, so nake muyi magana, A Majeed yace badai a office ba sai ka bari idan nabar office muyi maganan a gida, Abdul sanin halin abokin nashi yasa yace toh ba damuwa tare da tashi ya koma Office dinshi. 
Kaman yanda A Majeed yace ma Abdul a gida za suyi maganan hakan ko akayi domin bayan A Majeed ya fito Abdul shima binshi yayi har gidanshi, bayan dukansu sunyi parking A Majeed ya fito, baiko kalli abdul ba yayi ciki, shima abdul din binshi yayi ciki, wani dangareren falo naga abdul ya zauna, irin falon larabawa, falon yayi mugun haduwa da tsari,wata ce ta fito tasa riga gown amma ya tsaya dai2 giwa irin dai kayan da masu aikin turawa ke sawa, ta ajiye ma abdul snack da drink, Abdul ko kallon abun bai yiba, shidai jira yake A Majeed ya fito suyi magana, A Majeed bai fito ba saida ya kwashe wajan 1hr Kafin ya fito cikin bakin jallabiya ba karamin kyau yayi ba, domin ya fito sak balarabe, kallon Abdul yayi tare da fadin ina jinka, abdul yayi ajiyan zuciya tare da fadin kasan ranan da zamu taraba a wajan wani kauye akwai yarinyar da tazo tsallaka titi mu kuma munzo har tayi bar…..  Plz ya isa haka abunda kake son fada nake son ji ba labarin wata ba, Abdul yace A Majeed labarin akanta ne domin tana da halaka Dashi, A Majeed yayi tsaki tare da tashi yace idan akan yarinyar da baka santa bane baka ma san inda take ba, zakai min magana so u better change d topic, Coz bazan saurare kaba, Abdul yace A Majeed I know where she is wlh am in love with d girl, A Majeed yace what? Kana nufin kana sonta? Abdul yace haka nake nufi, A Majeed yace kai gaskiya kaban mamaki duk matan dake Nigeria wayayyu, masu class educated ka rasa wacce zaka ce kana So sai mai talla yar kauye, abdul yace A Majeed I luv her and am ready to marry d girl, yarinyar nan za tayi abunda wayayyar Mace ba zata iyayi ba, sannan waye wa da yawa yana sa kauyanci, bani da burin auren macen data waye sosai, nafi son inyi aure a karamin gida, ma’ana gidan da basu da hali, saboda duk abunda na Kawo mata she will appreciate it, amma idan yar babban gida ce tana ganin iyayenta masu kudi ne, komai za tayi ban isa in hana taba, duk munin abun sai dai inna gaji in saketa, sannan ita…..  A Majeed yace enough plz ka cikani da surutu am so tired I need to rest, abdul yace ok na tafi, bayan Abdul ya fita A Majeed bedroom dinshi ya nufa tare da kwanciya ya dauki wayanshi ya doka ma Zainab kira, har ya katse bata dauka ba, ya kuma kira shima batai picking ba, tsaki yayi tare da jefar da wayan gefe, domin tun jiya yake kiranta taki dauka ya rasa dalili.
Mlm musa da Tani suna zaune akan tabarma, Mlm musa ya kunna yar Radio dinshi yana ji, suna dan fira jefe2 shida Tani abu na gefe Tana zaune, maganan siyasa ake tayi a Radio din, mlm musa yayi tsaki tare da fadin sai suyi ta maganan sunyi titi da gada, mu ina ruwanmu dasu, mu kawai su bamu abinci, Tani tace aifa kam domin indan talaka akeyi mudai “TAMBARIN TALAKA” RUMBUN SA, yaro ne yayi sallama, bayan Tani ta amsa yace wai ana kiran esha, Tani tace waye kuma asha, kai jeka tambaya wa ake nema, yaron ya fita sai gashi ya kuma dawowa wai indo ake kira, Tani tace wanene yaron yace wani ne a mota, Tani tace kodai Abu akace ka kira? Yaron yace indo akace in kira, tani ta kalli Abu dake zaune tana kumbura fuska tace ke tashi kije hala ke ake nema, tashi abu tayi ta dauko gyalenta duk ya kode amma ita gani take kaman sabo, indo dake d’aki tana jin komai gabanta sai fadi yake domin tunda Yaron yace esha ta gane sulaiman ne, Abu ce ta shigo tana kuka, Tani ta tashi da sauri tana tambaya lafiya? Abu tace tani dan mai gari ne fah, wai kuma wajan indo yazo, harda wani cemin wai sonta yake yi, Tani ta Saki wani uban ashar tare da nufa dakin indo……MARYAM ALHASSAN DAN’IYA

+

🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝

Vote me on wattpat @maryam-obam

WWW.maryamobamnovels.com

                      30to35

DEDICATED DIS PAGE TO…

hafsat mamani
(Maman jawaheer)

Ina yinki sosai My darling sis much luv❤

Bude kofar tayi da karfi, indo ta tashi zaune dan tsoro, dakin duhu babu haske, Tani tace ina kike makira, ta kwala ma abu kira tare da fadin kawo min fitila, Abu ta Kawo Mata fitilan tare da haska fuskan indo, Tani tace dan ubanki a ina kika san yaron mai Gari? Indo tace inna ni wlh ban sanshi ba, kawai ya siya wainar rogo ne, Tani tace dan ubanki karya zaki min, indo tace wlh inn…..  Tas ta fara marinta tare da dukanta tako ina, ni zaki ma karya, yar iska, dama shine yake lalata ki, shine ya biyoki har gida, Tani dukanta takeyi tako ina, saida ta mata lilis Kafin ta barta, tace wlh idan na sake ganin yazo gidan nan nemanki saina yanka ki yar iska, ta fita fuuuu, zama tayi kusa da mlm musa Tana fadin shima d’an mai garin in banda asara ya rasa wacce zaiso sai wannan makiran yarinyar, kalli Abu yarinya kyakyawa sai dai fari kawai wacan makiran zata nuna mata, mlm musa yace ai yarinyar nan yanda kika san mayya shegia ni dama ta mutu mu huta, Tani tace hmmm yar iskan sai taurin rai inda zata mutun aida nafi kowa murna wlh, Abu tace Tani nifa gskiya ina son yaron mai gari, tani tace bayan mayyar can yace yana so, Abu tace wlh Tani bazan yarda ba nifa shi zan Aura Kin ganshi ne dan gayu, gashi sai kamshi yake yi, ga mota, ni wlh Tani kisan yanda za kiyi in aureshi, Tani tace toh naji Abu na kwantar da hankalinki kaman kin aureshi kin gama, Abu ta wangale baki tana murna, indo na daki Tana kuka gwanin tausayi lokaci daya zazzabi ya kuma rufeta, babu abunda take tunani sai dan uwanta yusuf shine kawai yake sonta ta tabbata inda yana nan da yanzu yana ta rarrashinta yana bata hakuri, yanzu ko ina ina oho, yana da rai ya mutu duk bata sani ba, kuka ta kuma Saki mai ban tausayi,ta dauki lokaci tana kuka har dare ya tsala sosai bacci da yake barawo ne yai awon gaba da ita.

Tunda asuba ta farka, duk da jikinta baya mata dadi haka ta fito ta share gida sannan ta dauki roba domin dibo Ruwa, gidan kusa da gidansu basa nan, dan haka ta nufi rafi, ta dibo ruwan tana kokarin daurawa a kanta, taji an rike mata kugu, da sauri ta waiga taga dan jummai ne saurayin Abu, tayi saurin matsawa da baya tare da sakin ruwan ya zube, dariya yayi yace haba yan mata miye abun jin tsoran nifa taimakonki zanyi, indo ta dauki bokintin da nufin ta wuce ya janyota ta fara ihu, ya fara dariya tare da fadin ihunki banza domin babu mai jinki, dan babu kowa a nan kinga gwara ki yarda kiban hadin kai, nifa taimaka miki zanyi, kuka ta fara tana rokanshi akan yayi hakuri ya barta amma ina bai masan Tana yiba, da yaga tana mai ihu yasa ya toshe mata baki da dayan hannunsa, tare da kokarin cire mata riga, tana ta kokarin tureshi amma ta kasa, riganta ya farka nan kirjinta da suke tsaye kyam Suka bayyana nan dan jummai idonshi ya kada tare da kara rudewa, kokarin kai hannu yayi yaji anyi jifa dashi ta gefe, nan aka fara dukanshi ganin dukan bana wasa bane kuma ya gane yaron mai gari ne yasa ya gudu, indo rufe jikinta tayi da dan kwalin kanta tana kuka, sulaiman ganin yanda tayi yasa ya cire Rigan shi ya bata ya koma daka shi sai singlet, mika mata yayi yace gashi kisa, da sauri ta amsa ya juya baya ta saka, yace ta tashi ya rakata gida, bata tashi ba kuma bata mishi magana ba, sai kuka da takeyi, sulaiman jin kukan yake har ranshi domin tunda ya ganta yaji yana sonta, zama yayi kusa da ita yace esha dan Allah kiyi hakuri kibar wannan kukan kizo muje in raka ki gida, kai ta girgiza alaman a’a, yace saboda me, dakyar ta iya furta za’a bigeni, yace kaman ya?  Cikin kuka tace dan Allah kayi hakuri karka kara kulani domin inna tace duk sanda na kara kulaka saita kashe ni, daukan bokitin tayi ta diba ruwan, har tayi gaba ta tsaya tace zan aiko maga da riganka nagode, Sulaiman kasa cewa komai yayi domin gaba daya abun ya daure mishi kai, wai wacece Indo? Koma dai wacece ina sonta kuma bana tunanin zan iya rabuwa da ita, tashi yayi domin ya nufi gida dama ya fito gudu ne,ya biyo ta rafi shine yaga wannan aika aikan,  koda indo ta nufi gida bata ga kowa ba, hakan ya mata dadi ta nufi daki ta cire rigan Sulaiman da yake ta kamshi mai dadi ta dauko wata kodaddar rigan atamfanta tasa, sannan ta boye nashi rigan, yanzu gari yayi haske makotansu sun bude kofa dan haka nan taje ta dibo ruwan ta cika ko ina, sannan ta hada murhu tasa ruwan kunu, kaman dai kullum, yau da wuri ta hada wainar rogo, gashi Tani ta hanata abinci haka ta fita tallah, tare da rigan Sulaiman inta ganshi ta bashi, amma har takai tasha bata ganshi ba, tana ta yawo wajan motoci tana fadin asai wainar rogo, babu laifi an dan siya, kadan ya rage, har takai yamma sauran bai Kare ba, dan haka ta nufi hanyar gida ga yunwa tana ji, muryan sulaiman taji yana fadin esha, kaman karta tsaya sai dai dole ta tsaya kodan ta bashi rigan shi, tsayawa tayi ya karaso inda take, mika mishi rigan tayi tare da fadin kayi hakuri ban wanke maka ba dan kar inna ta gani, kallonta yake yi yana murmushi, yace Ai yanzu ba nawa bane naki ne rigan, kai ta girgiza alaman a’a ni bana so, yace toh nima dai bazan amsa ba, ajiye mai tayi a qasa tayi gaba binta yayi yana fadin ta tsaya suyi magana, ganin bata da niyan tsayawa yace shikenan anjima zanzo gidan naku, cak ta tsaya tana hawaye tare da rokanshi akan karya zo, ganin tana hawaye yasa ta bashi tausayi yace toh shikenan indai bakya so inzo to kizo mu zauna a can muyi magana, bata musa mishi ba ta bishi, a dan wani dakali Suka zauna, yace esha ina son ki fadamin ke wacece, nan indo ta fad’a mishi tare da fadin dan Allah tunda kaji koni wacece dan Allah ka rabu Dani, Sulaiman idonshi ne ya kada yayi jaa, tabbas ya tausaya mata, ita indo tana ganin idan yasan ko ita wacece zai rabu da ita, amma sai taji sabanin hakan, yace esha tunda nake ban taba ganin macen da naji inaso ba sai ke, labarinki da kika bani yasa na kara sonki sosai, esha inaso kimin alkawari komai zai faru baza ki gujeni ba, har ranan da za muyi aure, tabbas an zalinceki keda dan uwanki, ni na yarda dake bazaki aikata wani abu mara kyau ba, zan tayaki neman dan uwanki har Allah yasa a dace, nidai so nike kimin alkawarin zaki yarda ki aureni sannan ba zaki taba gudu naba komai zai faru, indo shuru tayi domin tabbas karyane tace bata son sulaiman duk da shi din ba Sa’an auranta bane, kaman yasan abunda take tunani yace shi so babu ruwanshi da kudi ko mikami, dan Allah ki amince dani, rufe fuska tayi tare da fadin nima ina sonka amma bazan taba aurenka ba, cikin tashin hankali yace saboda me? Tace Inna ba zata bari inyi aure ba., sulaiman yace karki damu zan ma mahaifina magana duk yanda mukayi zan fada miki, murmushi tayi tare da fadin to ni zan tafi kar ace na dade, yace toh yanzu sai yaushe kuma ko inzo gida anjima zare ido tayi, ganin haka ya fara dariya tare da fadin wasa nake miki amma lokacin da zan fara zuwa ya kusa kinji My esha, bata ce komai ba sai murmushi kawai yace gobe in kin fito diban ruwa sai mu hadu, rufe fuska tayi ta ruga da gudu dan ta tuno abunda dan jummai ya mata……

STORY CONTINUES BELOW

Yawan comment yawan posting

Taku Maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅

                     NA

                    
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA

🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝

Vote me on wattpat @maryam-obam

WWW.maryamobamnovels.com

                      35to40

DEDICATED DIS PAGE TO…

Maryam Obam novel grp😘

Ina yinku irin sosai din nan One luv❤

Murmushi sulaiman yayi, tare da girgiza kai, yana mamakin son da yake ma yarinyar Lokaci daya, koda indo ta shiga gida, Tani da Abu suna tsakar gida akan tabarma suna cin tuwo, sallama tayi babu wanda ya amsa mata, dan haka ta nufi inda tani take tace inna gash….. Tani tace yanzu sauran da kika dawo dashi ubanki ne zai siye yar iska, indo tace inna wlh ina ta yawo dashi amma yaki karewa naga yamma tayi shine na dawo gida, Tani tace maza ki dauka ki fitar min Dashi wlh kar inga ko daya a roban nan, indo dauka tayi ta fita waje tama rasa ina zata dashi, can tace bari taje gaban layin su domin Akwai inda maza ke taruwa suna fira, nan ta nufa ta zauna a gefe da wainar rogon, harta gama zamanta ta gaji babu wanda ya siya, ganin dare nayi yanzu wajan takwas da wani abu, da sauri ta tashi domin ta tuna tana da canjin da suilaiman yabar mata, gida ta nufa tana dan sand’a Allah yasa babu kowa, dakinta ta shiga ta juye wainar rogon duka na saba’in ne, ta kirga kudin ta fito,dakin Tani ta nufa inda ta gansu ita da mlm musa suna yar fira, kanta a ‘Kasa tace inna ga kudin, amsa Tani tayi ta kirga taga sun cika dai2 dauko sauran tuwan da suka rage tace gashi, amsa tayi tare da fadin ngd, sannan ta fita, ruwa ta diba a kofi ta nufi dakinta, wainar rogon ta cinye sannan ta hada da tuwan, ranan saboda koshi cikinta kaman zai fashe, haka ta kwanta cikin jin dadi.

A Majeed ne kwance a bedroom dinshi, ya lullube da blanket, sai rawan sanyi yakeyi, ga wayanshi na ringing amma babu daman dauka, dan bazai iya tashi ba, yau kwana biyu yana daki bashi da lafiya, ga Abdul yana Kaduna daya tabbata da yazo ya duba shi, bude kofar akayi aka shigo d’akin, Mum dinshi ce cikin sauri ta karaso kusa dashi tana fadin son maiya sameka, tabashi tayi taji jikinshi zafi radau, cikin tashin hankali ta kira security din gidan tace suzo su sashi a mota, bayan an sashi a mota direct hspt Suka nufa, nan aka amsheshi aka fara duba shi, Dr yayi wajan 30mnt Kafin ya fito, ya kalli Mum wacce kana ganin A Majeed kasan danta ne, domin suna mugun kama, da turanci ya mata magana dan baya zaton ma tana jin hausa, yace suje office, bayan Sun shiga Dr ya fara mata bayani kaman haka…..  Hjy wannan yaronki ne koh? Mum tace eh yaro nane, Dr mai yake damunshi? Dr yace sperm ne ya tarun mishi a mara,yana da karfin Sha’awa sosai, shine ya haifar mishi da zazzabi, hjy inaga dai matsalan yaran ki shine ku mishi aure gskya, Mum shuru tayi amma ranta yayi mugun baci dan me wlh ba zata sabu ba, bazata bari a kashe mata gudan dan nata bat, dole ma ya kara aure, miye amfanin auren nashi matarshi kwata2 bata da lokacinshi, dr ne ya katseta da fadin anyi mishi alluran bacci nan da 1hr zai tashi, mum tayi mishi godiya sannan ta nufi dakin da dan nata yake, yana kwance yana bacci, kanshi ta fara shafawa cike da tausayi sai taga ya rame mata, kun san d’a da uwa, wayan Mum ce tayi ringing daukan Jakarta tayi ta ciro wayan, mijinta ne dauka tayi tare da fadin Habibi… Katseta yayi da fadin har kin kai? Yana dai lafiya koh?  Mum tace gamu dai a asibiti, cikin tashin hankali his excellency yace maiya faru, nan Mum ta bashi labarin komai da yanda Dr ya fada mata, his excellency shima baiji dadin abunba amma saiya boye nan yaita kwantar ma matarshi da hankali akan gobe zai dawo kasar dan baya nan sunyi tafiya da president, tace Allah ya kaimu ya dawo min dakai lfya, ya amsa da ameen sannan sukai sallama,  tana nan zaune tana ta saka irin yanda zata mishi wannan karan domin wlh ba zata sabu ba, a kashe mata yaro duk da tasha mishi maganan karin aure yana zullewa amma wannan karan bada wasa zata mishi ba.

STORY CONTINUES BELOW

Abdul ya taso daka Kaduna, kai tsaye taraba ya nufa, direct kauyensu indo, nan ya shiga yaita yawo amma baiga mai kama da ita ba, har yanzu fuskanta yake gani tana kuka, murmushi yayi tare da juya motarshi domin ya shiga jalingo ya kwana gobe ya dawo da safe nemanta, ko Allah zaisa a dace.

Yau dambu Tani tayi, domin tace a canza sana’a, duk a roba aka jera aka rufe da leda baka, indo ta dauka bayan Tani ta mata kashedin karta dawo mata dako kadan, kai tsaye tasha ta nufa nan da nan aka siye, ta juyo, tazo tsallaka titi taga mota tasha gabanta, komawa tayi da baya, tare dayin dan tsaki su masu kudi basa daraja talaka, fitowa yayi yana sakar mata murmushi tunani ta fara a ina tasan fuskan shi, lokaci daya itama ta sakar mishi murmushi domin tuno da ko waye, tabbas ya mata babban taimako tare da ceton rayuwanta, karaso wa yayi inda take, yace sorry, wlh kar ki bace min ne yasa na tawo da sauri, murmushi tayi tare da fadin ina wuni, amsawa yayi da lfya, sai kika gudu rannan ko sunanki baki fadamin ba, tace kayi hakuri, yace toh ya sunan? Tace indo, dariya yayi tare da fadin aysha koh? Tace eh, nan yaita dan janta da fira duk da ya lura tana sauri,yace inane gidan ku? Tace idan kabi can ka mike sai kayi kwana ka kara wani kwana sai ka mike…..  Dariyan da yake yi yasa tayi shuru itama tana dan murmushi, yace haba aysha ai wannan kwatancen bazan gane ba, yanzu dai kizo muje sai in kaiki kinga sai inga gidan koh? Shuru tayi can tace kayi hakuri ba’a zuwa gidan mu, abdul yace saboda me? Tace inna ta hana zata bigeni idan kazo, yace niba tadi zanzo ba, ke kanwata ce, ya fadan mata hakan ne dan ta yarda ta nuna mai, tace itafa inna bata so kowa yazo dan Allah kayi hakuri kar kasa ta bigeni, yace toh yanzu ina zan dinga ganinki? Tace a nan cikin tasha nake Kawo tallah kullum, Abdul yayi dan murmushi tare da fadin ina zuwa,mota Ya bude ya dauko wata leda, ya mika mata tare da fadin gashi, girgiza mai kai tayi tace ka barshi ngd ,yace haba aysha nifa yayanki ne, dakyar ta amsa tare dayi mishi godiya, yace ni tunda baki son sanin sunana shikenan, tace kayi hakuri inaso, yayi murmushi  yace toh yaya abdul, yace bari in barki ki tafi gobe zan koma abuja zanzo muyi sallama, tace toh sannan ta wuce, hanyar gidansu ta nufa tana jin tsoran shiga da ledan duk da bata ma san miye bane a ciki, koda ta shiga gida lambo ta farayi tana lekawa ji tayi ankira sunan tah cikin tsoro ta waiga……

Taku Maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅

                     NA

                    
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA

🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝

Vote me on wattpat @maryam-obam

WWW.maryamobamnovels.com

                      40to45

DEDICATED TO….

HABIBA SALEH❤

Jameela ta gani, ajiyan zuciya tayi,jamila tace lafiya indo kike ta rabe2, Tani bama ta gidan, Jameela da tun shigowanta sai yanzu ta lura da ledan dake hannunta mai kyau, tace indo ledan nan fah, indo mika mata tayi tare da fadin dan Allah gashi ki ajiye min, kai jamila ta girgiza tare da fadin sai kin fadamin inda kika samo shi, indo tace toh Inna jamila, muje d’akin ki kar inna ta dawo ta gani, jamila tace muje, bayan Sun shiga d’akin jamila sun zauna, jamila ta Kalli indo tare da fadin ina jinki indo, shuru indo tayi domin bata san ta inda zata fada mata ba, uwa uba kuma tana jin tsoran abunda zai biyo baya, jamila kaman ta lura da hakan, yasa ta fara fadin indo karki damu inaso ki fadamin komai domin ni innan ki ce, nan taita gayama indo magana mai dadi, kun san babba ya iya kwantar ma yaro da kai koda yaron baiyi niyan fadin abu ba, sai kuji yana fad’a, nan Indo taba jamila labarin komai harda haduwanta da sulaiman da yanda sukayi, jamila ajiyan zuciya tayi duk da shima Abdul ta fahimci yana son indo dinne, amma tunda bai fada mata ba, itama ba zata ce Komai ba, numfashi ta sauke tare da bude ledan turare ne kala2 dasu chocolate da biscuits, jamila tace kai wannan kaya haka, yanzu dai abunda za’ayi ki dauki Turare daya ki boye saiki dinga amfani Dashi, inya Kare sai kimin magana in kara miki, amma fah ki boye kar tani ta gani, daga kai tayi alaman toh, sannan jamila tace ta diba chocolate din, diba tayi tace ma jamila ta rike sauran, jamila tace a’a sunyi yawa kwara daya kawai ta dauka, ta ajiye mata sauran, jamila ta kira sunanta da indo, amsasa tayi sannan jamila tace inaso ki bani hankalinki duk da bani da iko dake amma zan baki shawara, ki fadamin tsakani da Allah kina son sulaiman, ido ta rufe tare da daga ma jamila kai, dariya jamila tayi, tare da fadin shikenan yanzu sai ki jira amsa daka Sulaiman din tunda yace zai fadama mahaifinshi, nan taita ba indo shawara akan yanda zata dinga tafiyar da rayuwa cikin sauki, sun dauki lokaci Kafin Indo ta fito dan kar Tani ta dawo ta ganta a nan.

STORY CONTINUES BELOW

Mum na zaune har A Majeed ya farka, ganin Mum kusa dashi yasa abun ya bashi mamaki dan haka ya kare ma dakin kallo, ya tabbatar yana asibiti ne, lumshe ido yayi tare da fadin Allah yasa Dr bai fadama Mum matsalata ba, jin hannun Mum yayi tana shafa gashin kanshi, bude ido yayi a hankali, murmushi ta sakar mai tare da fadin Alhmdlh, son ya jikin naka? A hankali yace Mum da sauki, yaushe kika Zo?  Tace dazu nazo na ganka cikin wannan halin, bari in kira Dr, fita tayi jim kadan sai gata ita da Dr, nan Dr ya dan duba shi,sannan ya fara dan tsokan shi, Oga ya kamata ayi aure shine maganin matsalan, ji yayi kaman yasa ihu gashi a gaban Mum duk kunya ta rufeshi, shiko Dr ko a jikinshi, nan Dr ya rubuta mai wasu Magani da za’a bashi kafin su wuce, A Majeed yasan Mum tasan komai haka ya tashi jiki babu kwari bayan an basu maganin Suka nufi gidan su mum dake abuja domin tace ba zata gidansa ba, hakan akayi, driver ya aika yace ya siyo mai jallabiya guda biyu da zai sa, Kafin ya koma gida, wanka yayi sannan Mum ta kawo mai abincin da tasa aka siyo kafin tayi girki, kadan yaci sannan ya kwanta, bacci ne ya dauke shi, ganin haka Mum ta nufi kitchen ta duba kayan ciki, abunda babu ta bayar a kawo mata su, wanda suka zo tare kuma ta basu kudi tare da cewa suba driver ya siyo musu abunda suke so, Mum ta kammali komai ta nufi dakin dan nata, ji tayi yana waya yana fadin yanzu Baby kina ganin kin kyauta yau wajan 7 days ina kiranki baki packing, ban san mai take ce mishi ba,naji yana fadin kin san ina missing dinki sosai har hakuri na ya kare yau na dawo daka hspt, gskya Baby kina cutana da yawa, shuru yayi yana sauraranta Kafin yace ok plz come back 2moro, I love you too My angel, kashe wayan yayi Mum dake tsaye gaba daya takaici ya kamata wlh bazata sabu ba, idan shi baison ciwon kanshi ba, to ita tasan zafin haiyuwarsa, dakin ta karasa ta ganshi a zaune murmushi ya sakar mata ganin fuskan Mum din a daure yasa yasha jinin jikinshi tare da fadin Allah yasa ba maganan matarshi zata mishi bah,mum zama tayi a gefen gadon dakin tace ya jikin? Yace da sauki My Mum, dan murmushi tayi tare da fadin muje kaci abinci,yace No Mum bana jin yunwa sai anjima zanci, tace toh shikenan, tashi tayi ta fita, jim kadan sai gata ta dawo da wani bowl a hannunta naman Rago ne, bashi tayi tace gashi kaci amsa yayi ba tare da musawa ba, ya fara ci, fita ta kuma yi ta dauko mishi maganin shi da drinks, duka naman ya cinye tare dashan maganin, dan fira Suka fara can mum tace A Majeed kai yanzu haka kake so kaita zama koh? Shuru yayi domin yasan za’a rina, taci gaba da fadin yau matarka tana can kasan gobe tana can, baka da iko da ita, inkai baka son kanka karka manta ni ina sonka kuma kasan bazan dauka ba, tun tuni nake maka maganan karin aure kana nokewa toh wlh kaji na rantse wannan karan sai ka kara aure, inko kaga bakai auren nan ba toh wlh bana raye, yau shekara nawa dayin aurenka har yanzu shuru babu karuwa yau mata nacan gobe tana can, shidai shuru yayi dan yasan Mum tunda ta rantse dakyar ta canza zance, zufa yana keto mai tako ina, Mum tace na baka nan da wata daya ka Kawo min wacce kake so tashi tayi ta fita daka dakin fuuuu, A Majeed innallilahi wa Inna’ilaihira jiun kawai yake fada, yanzu da wani idon zai kalli zainab yace zai kara aure, bayan ya mata alkawarin bazai mata kishiya ba, kuma sun tsara yanda zasu tafi da Al’amarin su, kai gskya bazai yihuwa ba dole yama Mum bayani yanda zata fahimce shi, duk da yasan yana da karfin Sha’awa amma hakan ba matsala bane zai fara azumi, hmm tabdi lallai kana da aiki A majeed, bari dai nayi shuru🙊 inga yanda zata kaya .

Indo ta fito da dambu ta nufi tasha kaman jiya aka siye duka, tana zaune a wani benci a cikin tashan dan bata son komawa yanzu, kaman daka sama taji magana waigawa tayi taga Abdul, ita harga Allah ta manta yace mata zaizo, cikin sauri tace ina wuni yaya Abdul, yace lafiya qalau kanwata tun dazu nake ta jiranki a waje nayi wajan awa daya, naji shuru shine nace bari in shigo koh zan ganki, tace kayi hakuri wlh na manta ne,kuma tun dazu na siyar, yace toh yanzu ni zan koma abuja, gashi baki da waya, ni kuma kullum ina son jin muryan kanwata, murmushi tayi tace hakane sai dai idan ka dawo, yace kai gskya zan dan dade coz ina da aiki sosai yanzu dai na samo mana mafita, muje waje, tashi tayi ta bishi Suka fita waje, mota ya bude ya dauko wani leda, yace gashi waya ne, akwai sim a ciki, sai kisa caji, kai ta girgiza tace ka barshi ni bana bukatan waya, yace saboda me? Tace hakanan mu bamu da wuta ma a garin mu, shuru yayi cikin mamaki,babu yanda baiyi ba akan ta amshi wayan taki, haka ya mayar tare da bata kudi yace tunda taki amsa shima dai Kin amsa tayi sai da yayi mata da gaske Kafin ta amsa, sallama ya mata tare da fadin zai zo ranan juma’a koh sati, tace toh sannan ya wuce, tsallaka titi tayi sai ga dan jummai yasha gabanta, yana fadin indo ina washe baki tunda kin hanani kanki zan turo gidanku inna aureki ai babu wanda ya isa ya hanani inyi yanda naso koh, tace waye zai aureka Allah ya kiyaye, dariya yayi tare da fadin wlh saina aureki indo ke gobe2 zan turo gidanku sai inga ta tsiya……..

STORY CONTINUES BELOW

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
         *DASHEN ALLAH……*
*(TOGETHER WE STAND NENVER DIVIDE FOR ALL)*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

                      45to50

*DEDICATED TO….*

*FAIZA DABO……Allah Ya raya Baby girl akan tafarkin addinin musulunci👏*

Indo bata kara cewa komai ba, tayi gaba abunta, binta yayi da kallo tare da lashe baki yana fadin inna aureki zan kwashi dadi, gida ta nufa tayi sallama Tani na zaune Akan tabarma duk ta cinye, tace sannu da gida inna? Bata amsa ba sai hannu data mika mata alaman ta bata kudin, mika mata tayi ta girga taga ya cika, Abu ce ta fito da tilin kayan wanki ta zubar a kasa tare da komawa ta dauko wasu, kayan da yawa sosai ta Kalli indo tace ga sunan kizo ki wanke Min ta wurga mata naira ishirin gashi ki siyo sabulu, indo babu yanda ta iya hakan ta dauka ta fita bata dade ba ta dawo, dakinta ta nufa zata shiga tani tace kee ina zaki kuma kizo ki kwashe kayan nan, indo tace inna hijjabina zan ajiye, Tan bata kuma cewa komai ba sai tsaki da taja ta shige daki, indo na shiga daki ta boye kudin da abdul ya bata cikin kayanta dake daure a leda, sannan ta fito ta fara wanki kayan da uban yawa ta dauki Lokaci sosai har wajan karfe goma saura tana waje tana wanki gashi ta gaji ga yunwa, haka ta gama wankin bayanta duk ya rike ga ruwan gidan ya kare, daukan roba tayi ta nufi gidan makotansu ta dibo kadan Kafin safiya yayi, bayan ta gama ta nufi dakin tani sallama tayi tace inna na gama tani tace toh naji mayya saiki tashi kije kisha ruwa ki kwanta domin sauran tuwan dana ajiye miki abu ta cinye,tashi tayi ta fita jiki a sanyaye dakinta ta nufa ta dauko kudin da abdul ya bata ta nufi dakin jamila tura kofar tayi a hankali dan kar ajita, jamila dake kwance ta tashi da sauri jin an bude mata kofa yar fitilan kwanta ta dauko ta haska taga indo ce, tace indo lafiya Kuwa?  Indo tace lafiya inna jamila mika mata kudin indo tayi tace gashi ki ajiye min, jamila a ina kika sami wannan kudin indo tace inna jamila wannan mutumin ne ya bani wanda yaban kayan jiya, jamila ta dan bata fuska tare da fadin indo daka yau karki kara amsan abun wani saurayi domin ki tsira da mutuncin ki, indo tace wlh Inna jamila babu yanda banyi ba amma saida yaban, nan ta bata labarin yanda sukayi, jamila tace toh Allah ya saka mishi da alkhairi, yanzu dai bari inga nawa ne, kirgawa tayi taga dubu ishirin zare ido jamila tayi tace kai wannan uban kudi haka,  yanzu mai zakiyi dasu, Indo tace inna makaranta nake son shiga wlh ina son nayi karatu in zama wata abu, jamila tace Allah sarki indo sai dai burinki kaman bamai yihuwa bane saboda Tani ba zata barki ba, indo jikinta yayi sanyi domin tasan haka dinne, jamila ta dauko mata shinkafa ta manja taji kayan miya sosai ta bata, nan indo ta fara ci sosai abincin ya mata dadi, tas ta cinye, jamila tace tunda kin gama tashi ki tafi daki kar Tani ta ganki, tace toh tare da tashi ta fita tana sambo kaman munafuka ta shiga dakinta.

Washe gari kaman kullum indo ta Gama aikinta, sai dai abu daya dake damunta rashin ganin Sulaiman kwana biyu, har taje tasha ta siyar da dambu ta dawo gida,  ko zama ba tayi ba Tani tace ta daura tuwan dare, haka ta gama Tani ta dan yafa mata kadan kaman wani karamin yaro zaici, dauka tayi taci da babu ai gwara babu dadi, Mlm musa ne ya shigo yana ta sababi ai wannan zancan banza ne, akan wani dalili, Tani tace lafiya kuwa? Yace wlh ina zaune majalisa sai gashi mai  gari ya aiko a kirani, ina zuwa wai dansa ne yaga y’ata yace yana so, wlh nasha koh Abu yake magana ashe wancan tsinannar yake nufi, Tani cikin sauri tace toh mai kace musu? Ai ce mishi nayi an mata miji, Tani tace oh yau naga iya shege amma wannan dan mai gari ko dan banza,koda yake ba’a banza ba ta kama masa kurwa, dan mayya ce ta gada wajan iyayenta…….  Sallama sukaji mlm musa ya fita tare da amsawa bai dade ba sai gashi cikin Fara’a da jin dadi, yace toh gashi dai Dan jummai ya aiko neman auren indo na kuma bashi, Tani guda ta saki tare da fadin ai dama ita saida irin su dan jummai, Abu dake daki ta fito tana fadin Tani saurayi nane fah? Tani tace ke dallah mai za kiyi da dan jummai wannan matsiyacin aike sai mai mato irin na yaron mai gari, washe baki Abu tayi tare da fadin kai Tani sai yasa nake sonki, Tani tace mlm ai sai asa bikin da wuri koh, yace duk yanda kika tsara ai yayi, indo dake bakin kofa babu abunda take sai kuka, yanzu shikenan dan jummai zata Aura, kazami gashi dan iska yasha yima mata fyade a garin amma maman shi saita fita ta shiga ta rufe bakin iyayen yara jummai akwai shegen bin bokaye bata son laifin danta gashi bata da mutunci, kaf cikin kauyensu babu wanda baya sana’a sai shi, wanda zuciyarshi ta mutu, dakyar indo ta tashi ta shiga daki tana ta sharan kuka.

STORY CONTINUES BELOW

A Majeed, dakin Mum dinshi ya nufa, ya sameta tana danna laptop, zama yayi kusa da ita tare da fadin mum plz ki fahimce ni, bani da burin tara mata Zainab ta isheni rayuwa Mum plz karki bata min tsarin da nayi, just give me another punishment….. Dakata A Majeed karin auren ne horar wa,? Lallai kayi nisa sosai kaiga Romeo and Juliet koh? Shuru yayi baice komai ba, taci gaba da fadin bazaka gane abunda nake hango maka ba sai nan gaba, Allah bai azurtani da samun yara masu yawa ba, kai daya Allah Ya bani, na dauka zaka so kayi aure danka tara yara inga jikoki na da yawa amma kaida matarka baku da ra’ayin tara yara, inma kai kana dashi matarka bata dashi karka dauka bana son matarka ne, a’a wlh ban taba kinta ba sai dai halayenta da bana so kawai, jikinshi ne yayi sanyi yanda yaji tana magana, yace Mum kiyi hakuri zamu gyara insha Allah, kai ta girgiza tace A Majeed auren ne baka son karawa amma karka manta na rantse maka babu fashi , yace shikenan Mum ni bani da zabi ki bani duk wacce ta miki yana fadin haka ya tashi ya fita fuuu ………

*Naji korafi bana typing da yawa bana posting akan lokaci zan kara yawan rubutu…….*

*Amma sai na fara ganin comment da sharhi sosai zan kara yawan rubutu*

*Taku Maryam obam😘**💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

                      50to55

*DEDICATED TO….*

*MY ANGEL FAUXY MUM SAHMA❤*

Mum ta bishi da kallo yanda ya fita kaman iska na turashi ajiyan zuciya tayi, tare da fadin zan ko zaba maka, komai za kayi aure dai babu fashi, kiran number din Abdul ta shiga yi, ringing biyu ya dauka tare da gaida ta, bayan Mum ta amsa tace Abdul ina abuja kazo ina son ganin ka, yace toh Mum nima ina hanyar shigowa abuja dinne,tace OK Allah ya kawo ka lfya tare da kashe wayan.  Shiko A Majeed Gidan ya bari gaba daya ya nufi gidanshi ranshi a bace yake sosai, dan mai yasa Mum zata wani sa ya kara aure, shi matarshi ta isheshi baya tunanin zai iya hadata da kowa sai dai kawai yace baya son halinta, kuma ai duk abunda takeyi akwai yarinta a ciki nan gaba zata gyara, yanzu taya ma zai Kalli Zainab yace mata zai kara aure, kai No bazai taba yiwuwa ba, inko Mum tayi min haka batai min adalci ba at all, dan gajeran tsaki yaja ya dauki phone dinshi ya kira Abdul, harya gama ringing bai dauka ba tsaki ya kuma ja tare da jefar da wayan.

Jummai ce zaune Tana surfa Bala’i akan danta bazai auri indo ba, yarinyar da tun tana karama yayanta ya lalata ta, shine mafa sanadiyan barinshi garin nan, dan jummai dake zaune yace haba jummai dan me zaki hanani aurenta ni wlh babu mai hanani, ya tashi ya fita yana surutai, kallon mijinta tayi tace sannu aika kyauta kaine a gaba wajan neman auren ma dan jummai wannan yar ko yayi maka kyau Allah ya bada Sa’a, bai ko kalleta ba balle ya amsa saima tashi yayi shima yabar gidan.

Tunda akasa maganan bikin indo da dan jummai, Tani ta shiga ta fita domin tace Abu saita riga indo aure koh kuma ayi rana daya, indo na daki tana kuka saiga yaro yayi sallama wai dan jummai na kiran indo, Tani tace kace Tana zuwa, Tani tayi shewa tare da wage baki tana kiran indo, fitowa tayi cikin hijab, Tani takai mata duka dan ubanki bazaki amsa ba, shegiya makira kawai, maza ki fita dan jummai na jira, bata ce komai ba ta fita, a waje ta sameshi, yana ganinta ya wage baki duk datti, yace indo In dodo, Indo ta dan jummai, har na kosa ayi bikin musha amarci ai ranan zanci dadi, indo toshe kunne tayi dan haushin maganan shi take ji, kwata2 babu tauna zance komai ya fado mishi fada yakeyi, ga warin jikinshi ma kawai ya ishe mutum, yace indo in dodo yanzu idan mukai aure tunda kin hanani ranan mai zaki min, bata kulashi ba sai hawayen dake zuba a idonta, bai damu da shurun nata ba yaci gaba da fadin a salulan garba mai gwanjo naga wani abu da turawa sukeyi, sai su hade bakinsu waje daya suna sha…..  Da gudu indo ta shige gida, Tani na zaune taga ta shige daki da gudu, tashi tayi tabi bayanta, tace ke dan uwarki miye haka?  Indo tace wlh inna dan iska ne dan Allah inna nifa bana sonshi, dariya Tani tayi tare da fadin aiko kina So ko bakya So wlh sai kin auri dan jummai shegiya gaki babbar yar iska kina bin maza a tasha suna miki juye makira, ko kin dauka ban san komai bane, shegiya har kina da bakin kiran wani dan iska munafuka mai bakin hali maza ki tashi ki fita yar iska kawai, tashi tayi tana kuka ta kuma fita ganin baya nan yasa taji dadi ta dawo gida tayi ta maka mata duka a baya tare da fadin matsiyaciya nan da sati biyu za’ayi bikin inga ta tsiya, daki ta shige tana kuka.

STORY CONTINUES BELOW

Yau mijin jamila ya dawo garin, murna wajan jamila ba’a magana domin wannan karan kafarta kafar mijinta, ranan jamila anata soye2 Tani ana ta hadiyan yawu tare da yima jamila sannu da aiki 🤣 jamila dai amsawa take amma tasan badan Allah take Mata ba, ranan dai Tani ta zauna anata jan jamila da fira harta gama girki ta zuba ma Tani, nan Tani aka amsa ana ta washe baki ta shige daki🤣 dama shi take jira, Tani da abu suna daki suna kwasar abinci saiga yaro yayi sallama wai ana kiran Abu yayar indo, Abu ta fito tace waye? Yaron yace yaron mai gari ne, da sauri Abu tace kace ina zuwa, daki ta koma ta shafa powder, Tani tana ta mata kirari tana dariya Abu tace kai Tani gskya akwai ki da fada da cikawa gashi har ya kawo kanshi, Tani tace saima kinga ya turo maganan aure, Abu fita tayi ta ganshi ya hade hannunshi biyu ya hade, murmushi take tayi kaman wata sauna, tace sannu yakake, yace lafiya ba tare da bata lokaci ba nidai sonki nakeyi kuma da aure dan haka mai kika ce? Abu tace babu komai na amince yanzu kawai ka turo, yace toh Alhmdlh zan fada a gida sai azo ayi komai cikin lokaci kadan, suna cikin fira saiga indo ta dawo daka tallah ido ta bisu Dashi ta shiga gida tana kuka, har Abu ta dawo gida tani tana ta guda sai kace an daura auren, tun daka lokacin kullum sai sulaiman yazo wajan Abu, indo tun tana jin abun na damunta harta fara cirewa a ranta domin tasan sulaiman ya mata nisa, ko sanda yace yana sonta dama tasan yafi karfinta, tasa ma ranta dan jummai dai shine wanda zata aura tunda haka Allah ya tsara mata duk da idan yazo wajanta babu firan da yake mata saina batsa wani lokacin ma har kokarin kamota yake yi, in taga hakan saita gudu, Tana shiga gida kuma Tani ta korata tace ta koma.

An yanke bikin indo da Abu nan da sati biyu,abu anata raban cingam, sai shirin biki akeyi Tani Tana ta gyara Abu, biki ya rage kwana uku aka Kawo akwatin abu guda uku, kaya ne makil anata maganan akwatin ai Abu tafi duka matan garin wannan kayan masu uban yawa kaf kauyen babu wanda aka taba kawo ma kaya irin shi, Tani anata guda da yada habaici ai yarta mai kashin arziki ce, ita dai indo tana daki Tana rusar kuka yanzu dai shikenan dan jummai ya kusa zama mijinta, wasu mata ne tsofaffi guda biyu Suka shigo da bako a hannu nan aka gaigaisa Suka Mika ma Tani bako din tare da fadin ga kayan akwatin indo inji dan jummai, Tani ta saki guda tare da budewa atamfa kala biyu sai leshi guda daya, kuma duk babu dinki, Tani ta fara fadin Abu mai kashin arziki ba irin su o o ba masu kashin tsiya sudai tsofaffi basu ce komai ba Suka fice……

*plz ku sani a addu’a mura da ciwon wuya ya sani gaba*

Taku Maryam obam 😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed, Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

                      55to60

*DDEDICATED THIS PAGE TO……*

*HAUSA NOVELS GROUP*

*INA YINKU RIN SOSAI DINAN*

*MUSAMMAN…..*

*MUMMYN SULTAN*
*MANANA NOOR*
*HASSY AMINU*
*MARYAM BALA*

Tani ta fara nunawa mutane kayan indo nan masu dariya Suka fara masu tausaya ma indo dai shuru sukayi kaman su jamila, sai shirye2 akeyi na biki amma ita indo inda zata mutu da tafi jin dadi, ji take da zata iya data kashe kanta ta huta, ankai kayan Abu gidan mai Gari gefe daya mai Gari ya ware ma Sulaiman, manyan daki ne ciki da falo da bayi safe content, ginin bulo,babu laifi Tani ta mata kaya na gani da fada domin ta kashe kudi, yan uwan tani Sun cika gidan makil sai guda kake ji a gidan da habaice2 da yan uwan tani da ita kanta tanin suke ma indo, indo na daki Tana kuka ga yunwa tana ji sosai, Tani ce ta bude kofar ta kalli indo sama da kasa tace sannu yar iko, kinzo kin kwanta kina rusa kuka sai kace kanin uwarki ne ya mutu, maza ki tashi kije kiyi wanke2 makira, tashi tayi ta dauki hijab tasa, Tani tace sai shegen rufe jiki kaman munafuka, indo ta fara hada kayan wanke2 yan uwan Tani sai hantaranta suke ita dai bata ce komai ba sai faman hada kaya takeyi harta gama ta fara wanke wa, kayan sunyi yawa sosai sai kace duka kwanukan yan unguwan ne dan yawan su, haka ta wanke su tas, ga yunwa bayan ta gama tani tace maza taje ta dibo ruwa duk da yamma tayi haka ta fita dibo ruwan, haka taita zuba ruwan suna amfani Dashi kuma da gayya sukeyi gashi tani tace sai ta cika komai, haka taita dibowa har aka kira magrib Kafin ta gama, jamila ta faki idon mutane ta shige dakin indo tace mata maza ta fita waje zata fito ta sameta, hakan ko akayi bayan indo ta fita jamila ta sameta a waje, nan jamila ta bata abinci tace taci indo amsa tayi Tana ci kaman za’a kwace Allah Sarki *TAMBARIN TALAKA* *cikin sa* bayan ta gama ci jamila tace indo kin san abdul wanda kika bani labari kwanaki koh? Tace eh yaya Abdul, jamila tace eh yazo nan neman mahaifinki ya hadu da mai gida na, ashe ya taba aiki gidan su abdul din, nan ya bukaci yasan ko ke wacece nan ya fada mishi komai, yace yazo da magana mai mahimmanci ban san dai ko miye ba, amma yace insha Allah zai taimaka miki dan haka ki kwantar da hankalinki kinji, indo tace toh inna jamila nagode, jamila tace tashi ki koma ciki kinji, tashi tayi ta shiga gida tare da tunanin yaushe rabonta da yaya Abdul din ma harta manta, tace Allah sarki yaya abdul ko baka taimakeni ba wannan karan kayi min babban taimako a rayuwa bazan taba manta alkhairin ka ba, wani hawaye mai zafi ya zubar mata a ido, tunawa da Sulaiman da tayi da irin son da yake fada mata yana mata, bata taba son wani namiji ba sai shi amma gashi ya yaudareta gashi sonshi ya kamata har gobe bata tunanin zata iya cire sonshi a ranta, amma tana rokon Allah ya cire mata.

STORY CONTINUES BELOW

Jummai ce zaune da kawarta mai suna habiba, habiba tace jummai ke yanzu bari Za kiyi dan jummai ya auri wannan yarinyar wacce tun tana karama tasan namiji? Hmm kedai bari habiba aini wlh yanda bana kaunar mutuwa ta haka bana son wannan auren amma dan jummai da babanshi Sun kafe, yanda kika san an musu baki, habiba tace zo kiji naso inji maita fada mata amma na kasa jiyowa, dariya naga sunyi tare dayin tafi.

Rana dai bata karya sai dai uwar diya taji kunya, yau za’a daura aure a kofar gidan mai gari kaman yanda mlm musa ya bukata, auren Abu aka fara daurawa kafin aka daura na indo, nan akai ta yamadidi akan auren musamman ma na indo inda aketa surutu akan auren, kowa abun ya bashi mamaki jin kudin sadakin indo har dubu dari,

Tani na zaune ana ta yada habaici,saiga wata makociyar su ta shigo da sauri Tana fadin tani Tani, Tani tace wannan uwar kira haka, tace ke labari na kawo miki kin san an daura aure kuwa? Tani tace eh yanzu yaci ace an daura, Matar tace To indo dai dan jummai yace ya fasa, Tani tace kaman ya matar tace ai yanzu bada shi aka daura ba da wani aka daura kuma naji anc…… Bata karasa ba mlm musa ya shigo cikin tashin hankali yana zufa Tani tace mlm an daura kuwa? Yace eh an daura sai dai dan jummai yace ya fasa auren nan wani yace yana so a bama danshi, ban musa Ba na amince nan ya zaro dubu dari kudin sadaki ya bada Tani tace kutumar uba mai kace……..  Hmmmm wa indo ta aura ku biyoni domin jin amsa…

*kuyi hakuri da wannan dakyar na muku wlh bana jin dadi*
                 *nagode da addu’a ina yinku sosai*

MARYAM ALHASSAN DAN’IYA

+

🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝

Vote me on wattpat @maryam-obam

WWW.maryamobamnovels.com

                      30to35

DEDICATED DIS PAGE TO…

hafsat mamani
(Maman jawaheer)

Ina yinki sosai My darling sis much luv❤

Bude kofar tayi da karfi, indo ta tashi zaune dan tsoro, dakin duhu babu haske, Tani tace ina kike makira, ta kwala ma abu kira tare da fadin kawo min fitila, Abu ta Kawo Mata fitilan tare da haska fuskan indo, Tani tace dan ubanki a ina kika san yaron mai Gari? Indo tace inna ni wlh ban sanshi ba, kawai ya siya wainar rogo ne, Tani tace dan ubanki karya zaki min, indo tace wlh inn…..  Tas ta fara marinta tare da dukanta tako ina, ni zaki ma karya, yar iska, dama shine yake lalata ki, shine ya biyoki har gida, Tani dukanta takeyi tako ina, saida ta mata lilis Kafin ta barta, tace wlh idan na sake ganin yazo gidan nan nemanki saina yanka ki yar iska, ta fita fuuuu, zama tayi kusa da mlm musa Tana fadin shima d’an mai garin in banda asara ya rasa wacce zaiso sai wannan makiran yarinyar, kalli Abu yarinya kyakyawa sai dai fari kawai wacan makiran zata nuna mata, mlm musa yace ai yarinyar nan yanda kika san mayya shegia ni dama ta mutu mu huta, Tani tace hmmm yar iskan sai taurin rai inda zata mutun aida nafi kowa murna wlh, Abu tace Tani nifa gskiya ina son yaron mai gari, tani tace bayan mayyar can yace yana so, Abu tace wlh Tani bazan yarda ba nifa shi zan Aura Kin ganshi ne dan gayu, gashi sai kamshi yake yi, ga mota, ni wlh Tani kisan yanda za kiyi in aureshi, Tani tace toh naji Abu na kwantar da hankalinki kaman kin aureshi kin gama, Abu ta wangale baki tana murna, indo na daki Tana kuka gwanin tausayi lokaci daya zazzabi ya kuma rufeta, babu abunda take tunani sai dan uwanta yusuf shine kawai yake sonta ta tabbata inda yana nan da yanzu yana ta rarrashinta yana bata hakuri, yanzu ko ina ina oho, yana da rai ya mutu duk bata sani ba, kuka ta kuma Saki mai ban tausayi,ta dauki lokaci tana kuka har dare ya tsala sosai bacci da yake barawo ne yai awon gaba da ita.

Tunda asuba ta farka, duk da jikinta baya mata dadi haka ta fito ta share gida sannan ta dauki roba domin dibo Ruwa, gidan kusa da gidansu basa nan, dan haka ta nufi rafi, ta dibo ruwan tana kokarin daurawa a kanta, taji an rike mata kugu, da sauri ta waiga taga dan jummai ne saurayin Abu, tayi saurin matsawa da baya tare da sakin ruwan ya zube, dariya yayi yace haba yan mata miye abun jin tsoran nifa taimakonki zanyi, indo ta dauki bokintin da nufin ta wuce ya janyota ta fara ihu, ya fara dariya tare da fadin ihunki banza domin babu mai jinki, dan babu kowa a nan kinga gwara ki yarda kiban hadin kai, nifa taimaka miki zanyi, kuka ta fara tana rokanshi akan yayi hakuri ya barta amma ina bai masan Tana yiba, da yaga tana mai ihu yasa ya toshe mata baki da dayan hannunsa, tare da kokarin cire mata riga, tana ta kokarin tureshi amma ta kasa, riganta ya farka nan kirjinta da suke tsaye kyam Suka bayyana nan dan jummai idonshi ya kada tare da kara rudewa, kokarin kai hannu yayi yaji anyi jifa dashi ta gefe, nan aka fara dukanshi ganin dukan bana wasa bane kuma ya gane yaron mai gari ne yasa ya gudu, indo rufe jikinta tayi da dan kwalin kanta tana kuka, sulaiman ganin yanda tayi yasa ya cire Rigan shi ya bata ya koma daka shi sai singlet, mika mata yayi yace gashi kisa, da sauri ta amsa ya juya baya ta saka, yace ta tashi ya rakata gida, bata tashi ba kuma bata mishi magana ba, sai kuka da takeyi, sulaiman jin kukan yake har ranshi domin tunda ya ganta yaji yana sonta, zama yayi kusa da ita yace esha dan Allah kiyi hakuri kibar wannan kukan kizo muje in raka ki gida, kai ta girgiza alaman a’a, yace saboda me, dakyar ta iya furta za’a bigeni, yace kaman ya?  Cikin kuka tace dan Allah kayi hakuri karka kara kulani domin inna tace duk sanda na kara kulaka saita kashe ni, daukan bokitin tayi ta diba ruwan, har tayi gaba ta tsaya tace zan aiko maga da riganka nagode, Sulaiman kasa cewa komai yayi domin gaba daya abun ya daure mishi kai, wai wacece Indo? Koma dai wacece ina sonta kuma bana tunanin zan iya rabuwa da ita, tashi yayi domin ya nufi gida dama ya fito gudu ne,ya biyo ta rafi shine yaga wannan aika aikan,  koda indo ta nufi gida bata ga kowa ba, hakan ya mata dadi ta nufi daki ta cire rigan Sulaiman da yake ta kamshi mai dadi ta dauko wata kodaddar rigan atamfanta tasa, sannan ta boye nashi rigan, yanzu gari yayi haske makotansu sun bude kofa dan haka nan taje ta dibo ruwan ta cika ko ina, sannan ta hada murhu tasa ruwan kunu, kaman dai kullum, yau da wuri ta hada wainar rogo, gashi Tani ta hanata abinci haka ta fita tallah, tare da rigan Sulaiman inta ganshi ta bashi, amma har takai tasha bata ganshi ba, tana ta yawo wajan motoci tana fadin asai wainar rogo, babu laifi an dan siya, kadan ya rage, har takai yamma sauran bai Kare ba, dan haka ta nufi hanyar gida ga yunwa tana ji, muryan sulaiman taji yana fadin esha, kaman karta tsaya sai dai dole ta tsaya kodan ta bashi rigan shi, tsayawa tayi ya karaso inda take, mika mishi rigan tayi tare da fadin kayi hakuri ban wanke maka ba dan kar inna ta gani, kallonta yake yi yana murmushi, yace Ai yanzu ba nawa bane naki ne rigan, kai ta girgiza alaman a’a ni bana so, yace toh nima dai bazan amsa ba, ajiye mai tayi a qasa tayi gaba binta yayi yana fadin ta tsaya suyi magana, ganin bata da niyan tsayawa yace shikenan anjima zanzo gidan naku, cak ta tsaya tana hawaye tare da rokanshi akan karya zo, ganin tana hawaye yasa ta bashi tausayi yace toh shikenan indai bakya so inzo to kizo mu zauna a can muyi magana, bata musa mishi ba ta bishi, a dan wani dakali Suka zauna, yace esha ina son ki fadamin ke wacece, nan indo ta fad’a mishi tare da fadin dan Allah tunda kaji koni wacece dan Allah ka rabu Dani, Sulaiman idonshi ne ya kada yayi jaa, tabbas ya tausaya mata, ita indo tana ganin idan yasan ko ita wacece zai rabu da ita, amma sai taji sabanin hakan, yace esha tunda nake ban taba ganin macen da naji inaso ba sai ke, labarinki da kika bani yasa na kara sonki sosai, esha inaso kimin alkawari komai zai faru baza ki gujeni ba, har ranan da za muyi aure, tabbas an zalinceki keda dan uwanki, ni na yarda dake bazaki aikata wani abu mara kyau ba, zan tayaki neman dan uwanki har Allah yasa a dace, nidai so nike kimin alkawarin zaki yarda ki aureni sannan ba zaki taba gudu naba komai zai faru, indo shuru tayi domin tabbas karyane tace bata son sulaiman duk da shi din ba Sa’an auranta bane, kaman yasan abunda take tunani yace shi so babu ruwanshi da kudi ko mikami, dan Allah ki amince dani, rufe fuska tayi tare da fadin nima ina sonka amma bazan taba aurenka ba, cikin tashin hankali yace saboda me? Tace Inna ba zata bari inyi aure ba., sulaiman yace karki damu zan ma mahaifina magana duk yanda mukayi zan fada miki, murmushi tayi tare da fadin to ni zan tafi kar ace na dade, yace toh yanzu sai yaushe kuma ko inzo gida anjima zare ido tayi, ganin haka ya fara dariya tare da fadin wasa nake miki amma lokacin da zan fara zuwa ya kusa kinji My esha, bata ce komai ba sai murmushi kawai yace gobe in kin fito diban ruwa sai mu hadu, rufe fuska tayi ta ruga da gudu dan ta tuno abunda dan jummai ya mata……

STORY CONTINUES BELOW

Yawan comment yawan posting

Taku Maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅

                     NA

                    
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA

🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝

Vote me on wattpat @maryam-obam

WWW.maryamobamnovels.com

                      35to40

DEDICATED DIS PAGE TO…

Maryam Obam novel grp😘

Ina yinku irin sosai din nan One luv❤

Murmushi sulaiman yayi, tare da girgiza kai, yana mamakin son da yake ma yarinyar Lokaci daya, koda indo ta shiga gida, Tani da Abu suna tsakar gida akan tabarma suna cin tuwo, sallama tayi babu wanda ya amsa mata, dan haka ta nufi inda tani take tace inna gash….. Tani tace yanzu sauran da kika dawo dashi ubanki ne zai siye yar iska, indo tace inna wlh ina ta yawo dashi amma yaki karewa naga yamma tayi shine na dawo gida, Tani tace maza ki dauka ki fitar min Dashi wlh kar inga ko daya a roban nan, indo dauka tayi ta fita waje tama rasa ina zata dashi, can tace bari taje gaban layin su domin Akwai inda maza ke taruwa suna fira, nan ta nufa ta zauna a gefe da wainar rogon, harta gama zamanta ta gaji babu wanda ya siya, ganin dare nayi yanzu wajan takwas da wani abu, da sauri ta tashi domin ta tuna tana da canjin da suilaiman yabar mata, gida ta nufa tana dan sand’a Allah yasa babu kowa, dakinta ta shiga ta juye wainar rogon duka na saba’in ne, ta kirga kudin ta fito,dakin Tani ta nufa inda ta gansu ita da mlm musa suna yar fira, kanta a ‘Kasa tace inna ga kudin, amsa Tani tayi ta kirga taga sun cika dai2 dauko sauran tuwan da suka rage tace gashi, amsa tayi tare da fadin ngd, sannan ta fita, ruwa ta diba a kofi ta nufi dakinta, wainar rogon ta cinye sannan ta hada da tuwan, ranan saboda koshi cikinta kaman zai fashe, haka ta kwanta cikin jin dadi.

A Majeed ne kwance a bedroom dinshi, ya lullube da blanket, sai rawan sanyi yakeyi, ga wayanshi na ringing amma babu daman dauka, dan bazai iya tashi ba, yau kwana biyu yana daki bashi da lafiya, ga Abdul yana Kaduna daya tabbata da yazo ya duba shi, bude kofar akayi aka shigo d’akin, Mum dinshi ce cikin sauri ta karaso kusa dashi tana fadin son maiya sameka, tabashi tayi taji jikinshi zafi radau, cikin tashin hankali ta kira security din gidan tace suzo su sashi a mota, bayan an sashi a mota direct hspt Suka nufa, nan aka amsheshi aka fara duba shi, Dr yayi wajan 30mnt Kafin ya fito, ya kalli Mum wacce kana ganin A Majeed kasan danta ne, domin suna mugun kama, da turanci ya mata magana dan baya zaton ma tana jin hausa, yace suje office, bayan Sun shiga Dr ya fara mata bayani kaman haka…..  Hjy wannan yaronki ne koh? Mum tace eh yaro nane, Dr mai yake damunshi? Dr yace sperm ne ya tarun mishi a mara,yana da karfin Sha’awa sosai, shine ya haifar mishi da zazzabi, hjy inaga dai matsalan yaran ki shine ku mishi aure gskya, Mum shuru tayi amma ranta yayi mugun baci dan me wlh ba zata sabu ba, bazata bari a kashe mata gudan dan nata bat, dole ma ya kara aure, miye amfanin auren nashi matarshi kwata2 bata da lokacinshi, dr ne ya katseta da fadin anyi mishi alluran bacci nan da 1hr zai tashi, mum tayi mishi godiya sannan ta nufi dakin da dan nata yake, yana kwance yana bacci, kanshi ta fara shafawa cike da tausayi sai taga ya rame mata, kun san d’a da uwa, wayan Mum ce tayi ringing daukan Jakarta tayi ta ciro wayan, mijinta ne dauka tayi tare da fadin Habibi… Katseta yayi da fadin har kin kai? Yana dai lafiya koh?  Mum tace gamu dai a asibiti, cikin tashin hankali his excellency yace maiya faru, nan Mum ta bashi labarin komai da yanda Dr ya fada mata, his excellency shima baiji dadin abunba amma saiya boye nan yaita kwantar ma matarshi da hankali akan gobe zai dawo kasar dan baya nan sunyi tafiya da president, tace Allah ya kaimu ya dawo min dakai lfya, ya amsa da ameen sannan sukai sallama,  tana nan zaune tana ta saka irin yanda zata mishi wannan karan domin wlh ba zata sabu ba, a kashe mata yaro duk da tasha mishi maganan karin aure yana zullewa amma wannan karan bada wasa zata mishi ba.

STORY CONTINUES BELOW

Abdul ya taso daka Kaduna, kai tsaye taraba ya nufa, direct kauyensu indo, nan ya shiga yaita yawo amma baiga mai kama da ita ba, har yanzu fuskanta yake gani tana kuka, murmushi yayi tare da juya motarshi domin ya shiga jalingo ya kwana gobe ya dawo da safe nemanta, ko Allah zaisa a dace.

Yau dambu Tani tayi, domin tace a canza sana’a, duk a roba aka jera aka rufe da leda baka, indo ta dauka bayan Tani ta mata kashedin karta dawo mata dako kadan, kai tsaye tasha ta nufa nan da nan aka siye, ta juyo, tazo tsallaka titi taga mota tasha gabanta, komawa tayi da baya, tare dayin dan tsaki su masu kudi basa daraja talaka, fitowa yayi yana sakar mata murmushi tunani ta fara a ina tasan fuskan shi, lokaci daya itama ta sakar mishi murmushi domin tuno da ko waye, tabbas ya mata babban taimako tare da ceton rayuwanta, karaso wa yayi inda take, yace sorry, wlh kar ki bace min ne yasa na tawo da sauri, murmushi tayi tare da fadin ina wuni, amsawa yayi da lfya, sai kika gudu rannan ko sunanki baki fadamin ba, tace kayi hakuri, yace toh ya sunan? Tace indo, dariya yayi tare da fadin aysha koh? Tace eh, nan yaita dan janta da fira duk da ya lura tana sauri,yace inane gidan ku? Tace idan kabi can ka mike sai kayi kwana ka kara wani kwana sai ka mike…..  Dariyan da yake yi yasa tayi shuru itama tana dan murmushi, yace haba aysha ai wannan kwatancen bazan gane ba, yanzu dai kizo muje sai in kaiki kinga sai inga gidan koh? Shuru tayi can tace kayi hakuri ba’a zuwa gidan mu, abdul yace saboda me? Tace inna ta hana zata bigeni idan kazo, yace niba tadi zanzo ba, ke kanwata ce, ya fadan mata hakan ne dan ta yarda ta nuna mai, tace itafa inna bata so kowa yazo dan Allah kayi hakuri kar kasa ta bigeni, yace toh yanzu ina zan dinga ganinki? Tace a nan cikin tasha nake Kawo tallah kullum, Abdul yayi dan murmushi tare da fadin ina zuwa,mota Ya bude ya dauko wata leda, ya mika mata tare da fadin gashi, girgiza mai kai tayi tace ka barshi ngd ,yace haba aysha nifa yayanki ne, dakyar ta amsa tare dayi mishi godiya, yace ni tunda baki son sanin sunana shikenan, tace kayi hakuri inaso, yayi murmushi  yace toh yaya abdul, yace bari in barki ki tafi gobe zan koma abuja zanzo muyi sallama, tace toh sannan ta wuce, hanyar gidansu ta nufa tana jin tsoran shiga da ledan duk da bata ma san miye bane a ciki, koda ta shiga gida lambo ta farayi tana lekawa ji tayi ankira sunan tah cikin tsoro ta waiga……

Taku Maryam obam😘💅 TAMBARIN TALAKA 💅

                     NA

                    
MARYAM ALHASSAN DAN’IYA

🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝

Vote me on wattpat @maryam-obam

WWW.maryamobamnovels.com

                      40to45

DEDICATED TO….

HABIBA SALEH❤

Jameela ta gani, ajiyan zuciya tayi,jamila tace lafiya indo kike ta rabe2, Tani bama ta gidan, Jameela da tun shigowanta sai yanzu ta lura da ledan dake hannunta mai kyau, tace indo ledan nan fah, indo mika mata tayi tare da fadin dan Allah gashi ki ajiye min, kai jamila ta girgiza tare da fadin sai kin fadamin inda kika samo shi, indo tace toh Inna jamila, muje d’akin ki kar inna ta dawo ta gani, jamila tace muje, bayan Sun shiga d’akin jamila sun zauna, jamila ta Kalli indo tare da fadin ina jinki indo, shuru indo tayi domin bata san ta inda zata fada mata ba, uwa uba kuma tana jin tsoran abunda zai biyo baya, jamila kaman ta lura da hakan, yasa ta fara fadin indo karki damu inaso ki fadamin komai domin ni innan ki ce, nan taita gayama indo magana mai dadi, kun san babba ya iya kwantar ma yaro da kai koda yaron baiyi niyan fadin abu ba, sai kuji yana fad’a, nan Indo taba jamila labarin komai harda haduwanta da sulaiman da yanda sukayi, jamila ajiyan zuciya tayi duk da shima Abdul ta fahimci yana son indo dinne, amma tunda bai fada mata ba, itama ba zata ce Komai ba, numfashi ta sauke tare da bude ledan turare ne kala2 dasu chocolate da biscuits, jamila tace kai wannan kaya haka, yanzu dai abunda za’ayi ki dauki Turare daya ki boye saiki dinga amfani Dashi, inya Kare sai kimin magana in kara miki, amma fah ki boye kar tani ta gani, daga kai tayi alaman toh, sannan jamila tace ta diba chocolate din, diba tayi tace ma jamila ta rike sauran, jamila tace a’a sunyi yawa kwara daya kawai ta dauka, ta ajiye mata sauran, jamila ta kira sunanta da indo, amsasa tayi sannan jamila tace inaso ki bani hankalinki duk da bani da iko dake amma zan baki shawara, ki fadamin tsakani da Allah kina son sulaiman, ido ta rufe tare da daga ma jamila kai, dariya jamila tayi, tare da fadin shikenan yanzu sai ki jira amsa daka Sulaiman din tunda yace zai fadama mahaifinshi, nan taita ba indo shawara akan yanda zata dinga tafiyar da rayuwa cikin sauki, sun dauki lokaci Kafin Indo ta fito dan kar Tani ta dawo ta ganta a nan.

STORY CONTINUES BELOW

Mum na zaune har A Majeed ya farka, ganin Mum kusa dashi yasa abun ya bashi mamaki dan haka ya kare ma dakin kallo, ya tabbatar yana asibiti ne, lumshe ido yayi tare da fadin Allah yasa Dr bai fadama Mum matsalata ba, jin hannun Mum yayi tana shafa gashin kanshi, bude ido yayi a hankali, murmushi ta sakar mai tare da fadin Alhmdlh, son ya jikin naka? A hankali yace Mum da sauki, yaushe kika Zo?  Tace dazu nazo na ganka cikin wannan halin, bari in kira Dr, fita tayi jim kadan sai gata ita da Dr, nan Dr ya dan duba shi,sannan ya fara dan tsokan shi, Oga ya kamata ayi aure shine maganin matsalan, ji yayi kaman yasa ihu gashi a gaban Mum duk kunya ta rufeshi, shiko Dr ko a jikinshi, nan Dr ya rubuta mai wasu Magani da za’a bashi kafin su wuce, A Majeed yasan Mum tasan komai haka ya tashi jiki babu kwari bayan an basu maganin Suka nufi gidan su mum dake abuja domin tace ba zata gidansa ba, hakan akayi, driver ya aika yace ya siyo mai jallabiya guda biyu da zai sa, Kafin ya koma gida, wanka yayi sannan Mum ta kawo mai abincin da tasa aka siyo kafin tayi girki, kadan yaci sannan ya kwanta, bacci ne ya dauke shi, ganin haka Mum ta nufi kitchen ta duba kayan ciki, abunda babu ta bayar a kawo mata su, wanda suka zo tare kuma ta basu kudi tare da cewa suba driver ya siyo musu abunda suke so, Mum ta kammali komai ta nufi dakin dan nata, ji tayi yana waya yana fadin yanzu Baby kina ganin kin kyauta yau wajan 7 days ina kiranki baki packing, ban san mai take ce mishi ba,naji yana fadin kin san ina missing dinki sosai har hakuri na ya kare yau na dawo daka hspt, gskya Baby kina cutana da yawa, shuru yayi yana sauraranta Kafin yace ok plz come back 2moro, I love you too My angel, kashe wayan yayi Mum dake tsaye gaba daya takaici ya kamata wlh bazata sabu ba, idan shi baison ciwon kanshi ba, to ita tasan zafin haiyuwarsa, dakin ta karasa ta ganshi a zaune murmushi ya sakar mata ganin fuskan Mum din a daure yasa yasha jinin jikinshi tare da fadin Allah yasa ba maganan matarshi zata mishi bah,mum zama tayi a gefen gadon dakin tace ya jikin? Yace da sauki My Mum, dan murmushi tayi tare da fadin muje kaci abinci,yace No Mum bana jin yunwa sai anjima zanci, tace toh shikenan, tashi tayi ta fita, jim kadan sai gata ta dawo da wani bowl a hannunta naman Rago ne, bashi tayi tace gashi kaci amsa yayi ba tare da musawa ba, ya fara ci, fita ta kuma yi ta dauko mishi maganin shi da drinks, duka naman ya cinye tare dashan maganin, dan fira Suka fara can mum tace A Majeed kai yanzu haka kake so kaita zama koh? Shuru yayi domin yasan za’a rina, taci gaba da fadin yau matarka tana can kasan gobe tana can, baka da iko da ita, inkai baka son kanka karka manta ni ina sonka kuma kasan bazan dauka ba, tun tuni nake maka maganan karin aure kana nokewa toh wlh kaji na rantse wannan karan sai ka kara aure, inko kaga bakai auren nan ba toh wlh bana raye, yau shekara nawa dayin aurenka har yanzu shuru babu karuwa yau mata nacan gobe tana can, shidai shuru yayi dan yasan Mum tunda ta rantse dakyar ta canza zance, zufa yana keto mai tako ina, Mum tace na baka nan da wata daya ka Kawo min wacce kake so tashi tayi ta fita daka dakin fuuuu, A Majeed innallilahi wa Inna’ilaihira jiun kawai yake fada, yanzu da wani idon zai kalli zainab yace zai kara aure, bayan ya mata alkawarin bazai mata kishiya ba, kuma sun tsara yanda zasu tafi da Al’amarin su, kai gskya bazai yihuwa ba dole yama Mum bayani yanda zata fahimce shi, duk da yasan yana da karfin Sha’awa amma hakan ba matsala bane zai fara azumi, hmm tabdi lallai kana da aiki A majeed, bari dai nayi shuru🙊 inga yanda zata kaya .

Indo ta fito da dambu ta nufi tasha kaman jiya aka siye duka, tana zaune a wani benci a cikin tashan dan bata son komawa yanzu, kaman daka sama taji magana waigawa tayi taga Abdul, ita harga Allah ta manta yace mata zaizo, cikin sauri tace ina wuni yaya Abdul, yace lafiya qalau kanwata tun dazu nake ta jiranki a waje nayi wajan awa daya, naji shuru shine nace bari in shigo koh zan ganki, tace kayi hakuri wlh na manta ne,kuma tun dazu na siyar, yace toh yanzu ni zan koma abuja, gashi baki da waya, ni kuma kullum ina son jin muryan kanwata, murmushi tayi tace hakane sai dai idan ka dawo, yace kai gskya zan dan dade coz ina da aiki sosai yanzu dai na samo mana mafita, muje waje, tashi tayi ta bishi Suka fita waje, mota ya bude ya dauko wani leda, yace gashi waya ne, akwai sim a ciki, sai kisa caji, kai ta girgiza tace ka barshi ni bana bukatan waya, yace saboda me? Tace hakanan mu bamu da wuta ma a garin mu, shuru yayi cikin mamaki,babu yanda baiyi ba akan ta amshi wayan taki, haka ya mayar tare da bata kudi yace tunda taki amsa shima dai Kin amsa tayi sai da yayi mata da gaske Kafin ta amsa, sallama ya mata tare da fadin zai zo ranan juma’a koh sati, tace toh sannan ya wuce, tsallaka titi tayi sai ga dan jummai yasha gabanta, yana fadin indo ina washe baki tunda kin hanani kanki zan turo gidanku inna aureki ai babu wanda ya isa ya hanani inyi yanda naso koh, tace waye zai aureka Allah ya kiyaye, dariya yayi tare da fadin wlh saina aureki indo ke gobe2 zan turo gidanku sai inga ta tsiya……..

STORY CONTINUES BELOW

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
         *DASHEN ALLAH……*
*(TOGETHER WE STAND NENVER DIVIDE FOR ALL)*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

                      45to50

*DEDICATED TO….*

*FAIZA DABO……Allah Ya raya Baby girl akan tafarkin addinin musulunci👏*

Indo bata kara cewa komai ba, tayi gaba abunta, binta yayi da kallo tare da lashe baki yana fadin inna aureki zan kwashi dadi, gida ta nufa tayi sallama Tani na zaune Akan tabarma duk ta cinye, tace sannu da gida inna? Bata amsa ba sai hannu data mika mata alaman ta bata kudin, mika mata tayi ta girga taga ya cika, Abu ce ta fito da tilin kayan wanki ta zubar a kasa tare da komawa ta dauko wasu, kayan da yawa sosai ta Kalli indo tace ga sunan kizo ki wanke Min ta wurga mata naira ishirin gashi ki siyo sabulu, indo babu yanda ta iya hakan ta dauka ta fita bata dade ba ta dawo, dakinta ta nufa zata shiga tani tace kee ina zaki kuma kizo ki kwashe kayan nan, indo tace inna hijjabina zan ajiye, Tan bata kuma cewa komai ba sai tsaki da taja ta shige daki, indo na shiga daki ta boye kudin da abdul ya bata cikin kayanta dake daure a leda, sannan ta fito ta fara wanki kayan da uban yawa ta dauki Lokaci sosai har wajan karfe goma saura tana waje tana wanki gashi ta gaji ga yunwa, haka ta gama wankin bayanta duk ya rike ga ruwan gidan ya kare, daukan roba tayi ta nufi gidan makotansu ta dibo kadan Kafin safiya yayi, bayan ta gama ta nufi dakin tani sallama tayi tace inna na gama tani tace toh naji mayya saiki tashi kije kisha ruwa ki kwanta domin sauran tuwan dana ajiye miki abu ta cinye,tashi tayi ta fita jiki a sanyaye dakinta ta nufa ta dauko kudin da abdul ya bata ta nufi dakin jamila tura kofar tayi a hankali dan kar ajita, jamila dake kwance ta tashi da sauri jin an bude mata kofa yar fitilan kwanta ta dauko ta haska taga indo ce, tace indo lafiya Kuwa?  Indo tace lafiya inna jamila mika mata kudin indo tayi tace gashi ki ajiye min, jamila a ina kika sami wannan kudin indo tace inna jamila wannan mutumin ne ya bani wanda yaban kayan jiya, jamila ta dan bata fuska tare da fadin indo daka yau karki kara amsan abun wani saurayi domin ki tsira da mutuncin ki, indo tace wlh Inna jamila babu yanda banyi ba amma saida yaban, nan ta bata labarin yanda sukayi, jamila tace toh Allah ya saka mishi da alkhairi, yanzu dai bari inga nawa ne, kirgawa tayi taga dubu ishirin zare ido jamila tayi tace kai wannan uban kudi haka,  yanzu mai zakiyi dasu, Indo tace inna makaranta nake son shiga wlh ina son nayi karatu in zama wata abu, jamila tace Allah sarki indo sai dai burinki kaman bamai yihuwa bane saboda Tani ba zata barki ba, indo jikinta yayi sanyi domin tasan haka dinne, jamila ta dauko mata shinkafa ta manja taji kayan miya sosai ta bata, nan indo ta fara ci sosai abincin ya mata dadi, tas ta cinye, jamila tace tunda kin gama tashi ki tafi daki kar Tani ta ganki, tace toh tare da tashi ta fita tana sambo kaman munafuka ta shiga dakinta.

Washe gari kaman kullum indo ta Gama aikinta, sai dai abu daya dake damunta rashin ganin Sulaiman kwana biyu, har taje tasha ta siyar da dambu ta dawo gida,  ko zama ba tayi ba Tani tace ta daura tuwan dare, haka ta gama Tani ta dan yafa mata kadan kaman wani karamin yaro zaici, dauka tayi taci da babu ai gwara babu dadi, Mlm musa ne ya shigo yana ta sababi ai wannan zancan banza ne, akan wani dalili, Tani tace lafiya kuwa? Yace wlh ina zaune majalisa sai gashi mai  gari ya aiko a kirani, ina zuwa wai dansa ne yaga y’ata yace yana so, wlh nasha koh Abu yake magana ashe wancan tsinannar yake nufi, Tani cikin sauri tace toh mai kace musu? Ai ce mishi nayi an mata miji, Tani tace oh yau naga iya shege amma wannan dan mai gari ko dan banza,koda yake ba’a banza ba ta kama masa kurwa, dan mayya ce ta gada wajan iyayenta…….  Sallama sukaji mlm musa ya fita tare da amsawa bai dade ba sai gashi cikin Fara’a da jin dadi, yace toh gashi dai Dan jummai ya aiko neman auren indo na kuma bashi, Tani guda ta saki tare da fadin ai dama ita saida irin su dan jummai, Abu dake daki ta fito tana fadin Tani saurayi nane fah? Tani tace ke dallah mai za kiyi da dan jummai wannan matsiyacin aike sai mai mato irin na yaron mai gari, washe baki Abu tayi tare da fadin kai Tani sai yasa nake sonki, Tani tace mlm ai sai asa bikin da wuri koh, yace duk yanda kika tsara ai yayi, indo dake bakin kofa babu abunda take sai kuka, yanzu shikenan dan jummai zata Aura, kazami gashi dan iska yasha yima mata fyade a garin amma maman shi saita fita ta shiga ta rufe bakin iyayen yara jummai akwai shegen bin bokaye bata son laifin danta gashi bata da mutunci, kaf cikin kauyensu babu wanda baya sana’a sai shi, wanda zuciyarshi ta mutu, dakyar indo ta tashi ta shiga daki tana ta sharan kuka.

STORY CONTINUES BELOW

A Majeed, dakin Mum dinshi ya nufa, ya sameta tana danna laptop, zama yayi kusa da ita tare da fadin mum plz ki fahimce ni, bani da burin tara mata Zainab ta isheni rayuwa Mum plz karki bata min tsarin da nayi, just give me another punishment….. Dakata A Majeed karin auren ne horar wa,? Lallai kayi nisa sosai kaiga Romeo and Juliet koh? Shuru yayi baice komai ba, taci gaba da fadin bazaka gane abunda nake hango maka ba sai nan gaba, Allah bai azurtani da samun yara masu yawa ba, kai daya Allah Ya bani, na dauka zaka so kayi aure danka tara yara inga jikoki na da yawa amma kaida matarka baku da ra’ayin tara yara, inma kai kana dashi matarka bata dashi karka dauka bana son matarka ne, a’a wlh ban taba kinta ba sai dai halayenta da bana so kawai, jikinshi ne yayi sanyi yanda yaji tana magana, yace Mum kiyi hakuri zamu gyara insha Allah, kai ta girgiza tace A Majeed auren ne baka son karawa amma karka manta na rantse maka babu fashi , yace shikenan Mum ni bani da zabi ki bani duk wacce ta miki yana fadin haka ya tashi ya fita fuuu ………

*Naji korafi bana typing da yawa bana posting akan lokaci zan kara yawan rubutu…….*

*Amma sai na fara ganin comment da sharhi sosai zan kara yawan rubutu*

*Taku Maryam obam😘**💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

                      50to55

*DEDICATED TO….*

*MY ANGEL FAUXY MUM SAHMA❤*

Mum ta bishi da kallo yanda ya fita kaman iska na turashi ajiyan zuciya tayi, tare da fadin zan ko zaba maka, komai za kayi aure dai babu fashi, kiran number din Abdul ta shiga yi, ringing biyu ya dauka tare da gaida ta, bayan Mum ta amsa tace Abdul ina abuja kazo ina son ganin ka, yace toh Mum nima ina hanyar shigowa abuja dinne,tace OK Allah ya kawo ka lfya tare da kashe wayan.  Shiko A Majeed Gidan ya bari gaba daya ya nufi gidanshi ranshi a bace yake sosai, dan mai yasa Mum zata wani sa ya kara aure, shi matarshi ta isheshi baya tunanin zai iya hadata da kowa sai dai kawai yace baya son halinta, kuma ai duk abunda takeyi akwai yarinta a ciki nan gaba zata gyara, yanzu taya ma zai Kalli Zainab yace mata zai kara aure, kai No bazai taba yiwuwa ba, inko Mum tayi min haka batai min adalci ba at all, dan gajeran tsaki yaja ya dauki phone dinshi ya kira Abdul, harya gama ringing bai dauka ba tsaki ya kuma ja tare da jefar da wayan.

Jummai ce zaune Tana surfa Bala’i akan danta bazai auri indo ba, yarinyar da tun tana karama yayanta ya lalata ta, shine mafa sanadiyan barinshi garin nan, dan jummai dake zaune yace haba jummai dan me zaki hanani aurenta ni wlh babu mai hanani, ya tashi ya fita yana surutai, kallon mijinta tayi tace sannu aika kyauta kaine a gaba wajan neman auren ma dan jummai wannan yar ko yayi maka kyau Allah ya bada Sa’a, bai ko kalleta ba balle ya amsa saima tashi yayi shima yabar gidan.

Tunda akasa maganan bikin indo da dan jummai, Tani ta shiga ta fita domin tace Abu saita riga indo aure koh kuma ayi rana daya, indo na daki tana kuka saiga yaro yayi sallama wai dan jummai na kiran indo, Tani tace kace Tana zuwa, Tani tayi shewa tare da wage baki tana kiran indo, fitowa tayi cikin hijab, Tani takai mata duka dan ubanki bazaki amsa ba, shegiya makira kawai, maza ki fita dan jummai na jira, bata ce komai ba ta fita, a waje ta sameshi, yana ganinta ya wage baki duk datti, yace indo In dodo, Indo ta dan jummai, har na kosa ayi bikin musha amarci ai ranan zanci dadi, indo toshe kunne tayi dan haushin maganan shi take ji, kwata2 babu tauna zance komai ya fado mishi fada yakeyi, ga warin jikinshi ma kawai ya ishe mutum, yace indo in dodo yanzu idan mukai aure tunda kin hanani ranan mai zaki min, bata kulashi ba sai hawayen dake zuba a idonta, bai damu da shurun nata ba yaci gaba da fadin a salulan garba mai gwanjo naga wani abu da turawa sukeyi, sai su hade bakinsu waje daya suna sha…..  Da gudu indo ta shige gida, Tani na zaune taga ta shige daki da gudu, tashi tayi tabi bayanta, tace ke dan uwarki miye haka?  Indo tace wlh inna dan iska ne dan Allah inna nifa bana sonshi, dariya Tani tayi tare da fadin aiko kina So ko bakya So wlh sai kin auri dan jummai shegiya gaki babbar yar iska kina bin maza a tasha suna miki juye makira, ko kin dauka ban san komai bane, shegiya har kina da bakin kiran wani dan iska munafuka mai bakin hali maza ki tashi ki fita yar iska kawai, tashi tayi tana kuka ta kuma fita ganin baya nan yasa taji dadi ta dawo gida tayi ta maka mata duka a baya tare da fadin matsiyaciya nan da sati biyu za’ayi bikin inga ta tsiya, daki ta shige tana kuka.

STORY CONTINUES BELOW

Yau mijin jamila ya dawo garin, murna wajan jamila ba’a magana domin wannan karan kafarta kafar mijinta, ranan jamila anata soye2 Tani ana ta hadiyan yawu tare da yima jamila sannu da aiki 🤣 jamila dai amsawa take amma tasan badan Allah take Mata ba, ranan dai Tani ta zauna anata jan jamila da fira harta gama girki ta zuba ma Tani, nan Tani aka amsa ana ta washe baki ta shige daki🤣 dama shi take jira, Tani da abu suna daki suna kwasar abinci saiga yaro yayi sallama wai ana kiran Abu yayar indo, Abu ta fito tace waye? Yaron yace yaron mai gari ne, da sauri Abu tace kace ina zuwa, daki ta koma ta shafa powder, Tani tana ta mata kirari tana dariya Abu tace kai Tani gskya akwai ki da fada da cikawa gashi har ya kawo kanshi, Tani tace saima kinga ya turo maganan aure, Abu fita tayi ta ganshi ya hade hannunshi biyu ya hade, murmushi take tayi kaman wata sauna, tace sannu yakake, yace lafiya ba tare da bata lokaci ba nidai sonki nakeyi kuma da aure dan haka mai kika ce? Abu tace babu komai na amince yanzu kawai ka turo, yace toh Alhmdlh zan fada a gida sai azo ayi komai cikin lokaci kadan, suna cikin fira saiga indo ta dawo daka tallah ido ta bisu Dashi ta shiga gida tana kuka, har Abu ta dawo gida tani tana ta guda sai kace an daura auren, tun daka lokacin kullum sai sulaiman yazo wajan Abu, indo tun tana jin abun na damunta harta fara cirewa a ranta domin tasan sulaiman ya mata nisa, ko sanda yace yana sonta dama tasan yafi karfinta, tasa ma ranta dan jummai dai shine wanda zata aura tunda haka Allah ya tsara mata duk da idan yazo wajanta babu firan da yake mata saina batsa wani lokacin ma har kokarin kamota yake yi, in taga hakan saita gudu, Tana shiga gida kuma Tani ta korata tace ta koma.

An yanke bikin indo da Abu nan da sati biyu,abu anata raban cingam, sai shirin biki akeyi Tani Tana ta gyara Abu, biki ya rage kwana uku aka Kawo akwatin abu guda uku, kaya ne makil anata maganan akwatin ai Abu tafi duka matan garin wannan kayan masu uban yawa kaf kauyen babu wanda aka taba kawo ma kaya irin shi, Tani anata guda da yada habaici ai yarta mai kashin arziki ce, ita dai indo tana daki Tana rusar kuka yanzu dai shikenan dan jummai ya kusa zama mijinta, wasu mata ne tsofaffi guda biyu Suka shigo da bako a hannu nan aka gaigaisa Suka Mika ma Tani bako din tare da fadin ga kayan akwatin indo inji dan jummai, Tani ta saki guda tare da budewa atamfa kala biyu sai leshi guda daya, kuma duk babu dinki, Tani ta fara fadin Abu mai kashin arziki ba irin su o o ba masu kashin tsiya sudai tsofaffi basu ce komai ba Suka fice……

*plz ku sani a addu’a mura da ciwon wuya ya sani gaba*

Taku Maryam obam 😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed, Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

                      55to60

*DDEDICATED THIS PAGE TO……*

*HAUSA NOVELS GROUP*

*INA YINKU RIN SOSAI DINAN*

*MUSAMMAN…..*

*MUMMYN SULTAN*
*MANANA NOOR*
*HASSY AMINU*
*MARYAM BALA*

Tani ta fara nunawa mutane kayan indo nan masu dariya Suka fara masu tausaya ma indo dai shuru sukayi kaman su jamila, sai shirye2 akeyi na biki amma ita indo inda zata mutu da tafi jin dadi, ji take da zata iya data kashe kanta ta huta, ankai kayan Abu gidan mai Gari gefe daya mai Gari ya ware ma Sulaiman, manyan daki ne ciki da falo da bayi safe content, ginin bulo,babu laifi Tani ta mata kaya na gani da fada domin ta kashe kudi, yan uwan tani Sun cika gidan makil sai guda kake ji a gidan da habaice2 da yan uwan tani da ita kanta tanin suke ma indo, indo na daki Tana kuka ga yunwa tana ji sosai, Tani ce ta bude kofar ta kalli indo sama da kasa tace sannu yar iko, kinzo kin kwanta kina rusa kuka sai kace kanin uwarki ne ya mutu, maza ki tashi kije kiyi wanke2 makira, tashi tayi ta dauki hijab tasa, Tani tace sai shegen rufe jiki kaman munafuka, indo ta fara hada kayan wanke2 yan uwan Tani sai hantaranta suke ita dai bata ce komai ba sai faman hada kaya takeyi harta gama ta fara wanke wa, kayan sunyi yawa sosai sai kace duka kwanukan yan unguwan ne dan yawan su, haka ta wanke su tas, ga yunwa bayan ta gama tani tace maza taje ta dibo ruwa duk da yamma tayi haka ta fita dibo ruwan, haka taita zuba ruwan suna amfani Dashi kuma da gayya sukeyi gashi tani tace sai ta cika komai, haka taita dibowa har aka kira magrib Kafin ta gama, jamila ta faki idon mutane ta shige dakin indo tace mata maza ta fita waje zata fito ta sameta, hakan ko akayi bayan indo ta fita jamila ta sameta a waje, nan jamila ta bata abinci tace taci indo amsa tayi Tana ci kaman za’a kwace Allah Sarki *TAMBARIN TALAKA* *cikin sa* bayan ta gama ci jamila tace indo kin san abdul wanda kika bani labari kwanaki koh? Tace eh yaya Abdul, jamila tace eh yazo nan neman mahaifinki ya hadu da mai gida na, ashe ya taba aiki gidan su abdul din, nan ya bukaci yasan ko ke wacece nan ya fada mishi komai, yace yazo da magana mai mahimmanci ban san dai ko miye ba, amma yace insha Allah zai taimaka miki dan haka ki kwantar da hankalinki kinji, indo tace toh inna jamila nagode, jamila tace tashi ki koma ciki kinji, tashi tayi ta shiga gida tare da tunanin yaushe rabonta da yaya Abdul din ma harta manta, tace Allah sarki yaya abdul ko baka taimakeni ba wannan karan kayi min babban taimako a rayuwa bazan taba manta alkhairin ka ba, wani hawaye mai zafi ya zubar mata a ido, tunawa da Sulaiman da tayi da irin son da yake fada mata yana mata, bata taba son wani namiji ba sai shi amma gashi ya yaudareta gashi sonshi ya kamata har gobe bata tunanin zata iya cire sonshi a ranta, amma tana rokon Allah ya cire mata.

STORY CONTINUES BELOW

Jummai ce zaune da kawarta mai suna habiba, habiba tace jummai ke yanzu bari Za kiyi dan jummai ya auri wannan yarinyar wacce tun tana karama tasan namiji? Hmm kedai bari habiba aini wlh yanda bana kaunar mutuwa ta haka bana son wannan auren amma dan jummai da babanshi Sun kafe, yanda kika san an musu baki, habiba tace zo kiji naso inji maita fada mata amma na kasa jiyowa, dariya naga sunyi tare dayin tafi.

Rana dai bata karya sai dai uwar diya taji kunya, yau za’a daura aure a kofar gidan mai gari kaman yanda mlm musa ya bukata, auren Abu aka fara daurawa kafin aka daura na indo, nan akai ta yamadidi akan auren musamman ma na indo inda aketa surutu akan auren, kowa abun ya bashi mamaki jin kudin sadakin indo har dubu dari,

Tani na zaune ana ta yada habaici,saiga wata makociyar su ta shigo da sauri Tana fadin tani Tani, Tani tace wannan uwar kira haka, tace ke labari na kawo miki kin san an daura aure kuwa? Tani tace eh yanzu yaci ace an daura, Matar tace To indo dai dan jummai yace ya fasa, Tani tace kaman ya matar tace ai yanzu bada shi aka daura ba da wani aka daura kuma naji anc…… Bata karasa ba mlm musa ya shigo cikin tashin hankali yana zufa Tani tace mlm an daura kuwa? Yace eh an daura sai dai dan jummai yace ya fasa auren nan wani yace yana so a bama danshi, ban musa Ba na amince nan ya zaro dubu dari kudin sadaki ya bada Tani tace kutumar uba mai kace……..  Hmmmm wa indo ta aura ku biyoni domin jin amsa…

*kuyi hakuri da wannan dakyar na muku wlh bana jin dadi*
                 *nagode da addu’a ina yinku sosai*

*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

+

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

                      60to65

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*MY AMINIYA KAWAR RAI DA RAI HABIBA BUSY😝*

Dubu dari fah kace sadakin indo? Yace hakane wlh ban san mai arziki bane, niko tsayawa inji daka ina yake ban yiba, Tani tace wlh baza ta sabu ba, dan ban yarda da wannan auren ba, nan jamila ta ranged’a buda tana fadin dama haka Allah yake abunsa duk wanda yace uwar wani ba zatai bacci ba, to wlh tashi ma ba zata rintsa ba, kuma dama hausawa na cewa in zaka gina ramin mugunta gina shi gajere wata kil kaine zaka fada, kin so ki bata rayuwan yarinya ki bata wanda bai dace da itaba baya sana’a sai uwarshi ta bashi yarki yake so amma kika hanashi kika So bashi indo to yanzu kinga lamarin uban giji koh, nan Tani ta hasala da yan uwanta sukai kan jamila suna ta yabama juna magana, dakyar mijin jamila ya janyeta yai daki da ita, itako Indo duk abunda ke faruwa tana ji babu abunda takeyi sai kuka, yanzu wata aura? Waye mijinta? Wani kukan ta kuma saki jin tani na fadin hala ma dan yankan kaine, inba dan shan jini ba, yaushe za’a bada sadaki har dubu dari sai kace yar Sarki, nan dai sukai ta fadin magan ganu gidan biki dai ya koma kaman gidan mutuwa domin babu wani jin dadi a cikin gidan dan Tani zuciyarta ji take kaman zata fashe, a haka dai har yan daukan Abu suka zo a mota biyu daukan amarya dangin tani suna ta guda tare da fadin mudai mun san asalin wanda yarmu ta aura badan yankan kai bane, suna cikin haka sai ga motoci Sun shigo layin da yawa a kalla za suyi ishirin na daukan indo da yan uwanta Wanda suke son zuwa, nan Abu ta fara kuka wai bata son Sulaiman ita mijin indo zata aura yafi Sulaiman kudi, tashin hankali🙆‍♀ nan akai ta toshe mata baki kar dangin sulaiman suji, amma taki yin shuru, jamila kam ta shirya indo cikin wata doguwar riga da aka aiko ma mijin jamila yace in anzo daukanta a sa mata, indo tayi kyau duk da har yanzu kuka takeyi Tana fadin ita bata san wannan auren, kar a shanye mata jini, dakyar da dadin baki jamila ta samu tayi shuru, amma fa zuciyarta cike yake da tsoro har yanzu, musamman ma da taji ana fadin motoci sun kai dari na zuwa daukanta, nan cikinta ya kara rudewa dan tsoro, amma jamila Tana ta bata baki harta gama shiryata Suka fito , nan Tani ta tare hanya tace wlh babu inda za’a da Indo, domin ita sam bata yarda da wannan auren ba, hmmm tashin hankali, waje ma Abu ta tirje akan sai ansa Sulaiman ya saketa domin ita mijin indo take so, nan wata yar uwan maman Sulaiman din ranta ya baci, tace dama badan Allah ta auri Sulaiman din ba, Abu tace eh ina ruwanki nan aka fara cacan baki da dangin amarya da ango, masu daukan indo sunji shurun yayi yawa ga hayani nan aka kira mijin jamila akan a bada amarya, shiga gidan yayi yaga Tani ta tare hanya tana fadin babu inda za’a da indo indai indo tayi aure tabar gidan nan toh gidan dan jummai ne, dan ni wannan dan iskan auren ba yarda Dashi nayi ba, mijin jamila yace haba Tani wannan wani irin magana ne yarinya dai an daura mata aure mutane sun shaida dan haka ki basu hanya a fita da ita, nan ta fara fadin toh munafiki dama kaida matarka ku kuka shirya komai toh wlh makircinku bazai taba aiki akaina ba wlh, indo dai babu abunda take sai kuka, mijin jamila ganin Tani ta hakince taki basu hanya ya fita jim kadan sai gashi da mlm musa, mijin jamila yace ka mata magana ta bada hanya a fitar da yarinya anzo daukan ta, mlm musa ya kalli tani yace ki matsa su wuce Allah yasa ma in an kaita su yanke mata kai, Tani da bakin ciki da hassada suke cinta tace wlh bazan matsa ba, ganin dagaske Tani take yasa mijin jamila fita, waje kuma rikici ake sosai har Sulaiman shima yazo wajan amma abun mamaki saiya fara rarrashin Abu, Yan uwanshi ransu ya baci dan haka suka wuce suka barshi da amaryan tashi, babu rarrashin da bai mata ba amma taki yarda ta bishi, suna cikin haka saiga motan sodoji har guda uku da gudu Abu ta shige gida sodojin Suka shiga gidan da mijin jamila a gaba, Tani taga Abu ta shigo da gudu ta fara tambaya lafiya nan Abu ta fara fadin Tani…..  Kafin ta karasa sodoji sun shigo gidan Tani Ba shiri ta matsa a hanya Tana gani su jamila da indo Suka fita, Tani baki ya mutu taga sojo mazan fama🤣 nan aka sa amarya a mota ita daya sai jamila Suka shiga wata motar nan dangin tani suma suka shige motocin domin sunce baza’a barsu a baya ba, cikin masu shiga motar harda makota dan dai suje su karas, nan mota ta tashi aka fara tafiya

1

STORY CONTINUES BELOW

Anyi tafiya mai nisa Kafin suka Isa wani makeken gida, nan aka firfito, jamila ta nufi motar da amarya take ciki, tace ta fito, wasu mata guda biyu suka musu iso, har cikin wani makeken falo, wanda zaka rantse ba’a Nigeria kake ba, Nan sukai ta kauyanci masu taya ta murna nayi masu bakin ciki nayi irin dangin Tani, amarya dai Tana waje ita da jamila basu riga sun shiga ba, wasu motoci ne Suka shigo gidan guda uku, bayan sunyi parking, abdul ya fito ata farkon na biyun Mum din A majeed ce, sai security a cikin na ukun, wajan su indo Suka nufa nan Mum din A majeed tace sannun ku, ta kamo indo tare da fadin sannu da zuwa yata, nan ta rike hannun indo sukai dayan sashin gidan tace ma indo ta shiga da kafar dama da bismillah, hakan koh tayi idon indo dai a rufe yake, har suka shiga ciki, bayan Mum ta zaunar da ita Suka gaisa da jamila nan Mum tace itace maman mijin indo, jamila ta kuma gaidata domin ita dai mamaki take yanda taga Mum na hausa, Mum tace ma indo yata bude fuskan in ganki mana, dai2 lokacin abdul ya shigo da sallama shida A Majeed, Mum tace har ka karaso Tana yi tana kallon dan nata daya tamke fuska kaman wani dodo, Mum ta kalli jamila tare da fadin ga mijin aysha nan ta nuna A Majeed daya tamke fuska, nan Suka gaisa da jamila, Mum tayi musu nasiha sosai, sannan tace ma jamila tazo suje su kwanta, jamila tace yau zasu koma babu yanda Mum batayi ba amma jamila tace yau zasu tafi, nan Mum tasa azo a maida su tare da raba ma ko wacce dubu ishirin2 nan sukai ta murna,  aka kwashe su zuwa kauyensu, Mum ta kira A Majeed taja mishi kunne sosai akan indo tare da mishi nasiha yaji tsoran Allah sannan ta wuce shima abdul wucewa yayi jiki ba kwari dan ya tabbar ma kanshi ya rasa indo har abada……….  To ga indo dai da A majeed a gida su biyu  komai zai faru oho ku biyoni dan jin ya akai indo ta auri A majeed…

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

                      65to70

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*MY DEAR F MARDIYAH LAWAN AKA PRETY MARDY…. KINA WUTA🔥 ALLAH YA BAKI IKON GAMA NOVEL DINKI LFY…. KOWA DA RANARSA*

A Majeed ya dade a waje kafin ya shiga ciki, yanda take a zaune fuskanta a rufe haka ya kuma samunta tsaki yayi tare da wucewa dakin shi abunshi ya kwanta, koda ya shiga daki toilet ya fada yayi wanka, sai da ya dauki lokaci yana gyara gashin kanshi, wayanshi yaji yana kara, tsaki yayi ya nufi wajan wayan murmushi ya sake ganin zainab ke kiranshi, dauka yayi tare da fadin Baby yanzu nake son in kira ki, tayi murmushi tare da fadin kasan komai namu muna yi lokaci daya, sai yasa nima naji ina son kiranka yanzu nan Suka sha firansu daka karshe tace mishi tana son ya dawo gobe dan tayi missing dinshi dan shuru yayi ya lura idan yazo jalingo bata So ya dade duk da bawai tana bashi kulawa bane in yana wajanta amma sai ta damu ya dawo, katse shi tayi da fadin Baby Why r You silent? Ajiyan zuciya yayi tare da fadin Baby kiyi hakuri jibi zan dawo, nan tace ita bata yarda ba dakyar dai ya samu ya shawo kanta ta amince, bayan sunyi sallama yayi dan tsaki tare da fadin ina tsoran my Baby tasan da wannan auren da Mum tamin,dan shuru yayi na lokaci Kafin yace zan nemi mafita Kafin lokaci ya kure min.

ZAMU DAWO BAYA KADAN

In mai karatu bai manta ba, kun san lokacin da A majeed yace ma Mum dinshi ta zaba mishi duk wacce ta mata, a lokacin ta kira abdul yace yana hanyar dawowa daka abuja…..  Bayan Abdul ya shigo abuja direct wajan Mum din AM ya nufa bayan tasa an cika mishi gaba da kayan ciye2 yaci ya koshi sannan ta kalleshi ta fara mai bayani yanda sukai da AM sannan ta daura da fadin tana son ya sama mata yarinya mai ladabi wacce ya yarda da ita kuma tana son yarinya daka poor family domin bata ga ranan auren yar masu kudi ba, Abdul shuru yayi yana tunani can yace ma Mum akwai wata yarinya Tana taraba a karaman hukuman karan, nan yaba mum labarin haduwansu amma bai fada mata cewan yana sonta ba, ya kuma cewa zai kara bincika akan halin yarinyar, Mum tai ta mishi godiya, tabbas Abdul bayan ya koma gida abun ya dameshi domin yana son indo, sai dai kuma ance kaso ma dan uwanka abunda kake So ma kanka, sai yasa ya soma AM indo abdul yana tausaya ma abokin nashi wanda yake kaman dan uwa a gareshi domin kwata2 Matarshi bata da hali ko kadan, sannan yana ganin AM zaifi kula da indo sosai ba kaman shi ba, Abdul kwananshi hudu ya koma taraba don son sanin wacece indo, yayi tambaya tare da kwatancen indo inda yazo har gidansu nan ya hadu da mijin jamila wanda ya taba aiki a gidan su abdul din, abdul ya fada mishi komai da komai akan abunda ya kawo shi, mijin jamila ya fada mishi abunda ake shirin yima indo tare da bashi labarinta abdul ya tausaya mata sosai tare da fadama mijin jamila zai taimaka mata insha Allah, nan sukai sallama akan zai dawo, koda abdul ya koma yaba Mum labarin indo bai boye mata komai ba kaman yanda aka fada mishi Mum harda hawaye tare da fadin zata kwatan ma indo hakkinta amma abdul ya bata hakuri akan tabar maganan Allah zai saka mata, Mum tace taji Tana son yarinyar ba zata bari a bata wanda ake shirin bata ba, bayan mijinta ya dawo ta fada mishi hukuncin data yanke da farko yaki yarda saida ta nuna mishi damuwa sosai kafin ya amince, ya tura wakili akan aje wajan mai anguwan garin a nema ma dansa auren, mai gari ganin dan governor ne bai musa ba duk da bashi bane mahaifin indo amma kauye suna mutunta masu Gari tare da daukan duk wani abu da sukace da mahimmanci ba kaman bariki ba da aka raina su ba, mai gari ya amince duk da yasan neman aure kan aure babu kyau,yace jibi ne bikin sai su zo a daura, koda Mum da Dad din AM Suka kirashi Suka fada mishi ansa bikin nashi jibi kuma za’a daura bai ce komai ba akan bikin sai rokan su da yayi akan yana son auren ayi shi kaman na sirri, nan Mum tace bai isaba akan wani dalili za ayi *AUREN SIRRI* littafin Sis bagudo Dad dinshi ne yaita bata baki akan tayi hakuri shima koda dan nashi bai fada ba hakan yake ganin za’ayi tunda basu fada ma kowa ba, gashi jibi za’a daura, amma nan gaba kowa ai zaiji, dakyar Mum ta yarda da hakan AM yaji dadin hakan domin dama baya so Zainab ta sani, yaso yayi tafiya shida Zainab din ma Mum ta hana tace kuma jibin dole yazo jalingo babu yanda ya iya dole yaje, su Mum kuma Suka koma washe gari, koda akazo daurin auren his excellency wakilci ya tura, mai Gari mutane an taru sai ga dan jummai yazo yace ya fasa, nan wakilin yace yana So a bama danshi wanda Abdul ne yasa yace hakan nan mlm musa yace ya amince domin yana tsoran indo taki aure sulaiman yace zai aureta nan gaba tunda akwak aure tsakani, amma ganin an bada dubu dari sadakin indo ya tashi yabar wajan cikin tashin hankali….  Toh kunji abunda ya faru har AM ya auri indo……  MUN DAWO KAN LABARI

STORY CONTINUES BELOW

indo na zaune a falo Tana kuka, tare da tunanin koya za tayi rayuwa a nan oho, gashi bata san waye mijin nata ba, koma dai waye ba damuwan ta bane tunda ta kubuta daka auren dan jummai, toh amma wani mai kudin ne ya aureta kaman yanda taji ana fada kuma ko da ganin tsaruwan falon tasan mahaukacin mai kudi ne mai wannan gidan, duk da a tsorace take domin har yanzu bata cire cewa dan shan jini ta aura ba, domin ganin girman gidan da falon, saboda kuka kanta ya fara mata wani irin mugun ciwan kai ga yunwa domin tun safe bata ci komai ba, haka dai ta kwanta a falon cikin tsoro har bacci yayi awon gaba da ita.

Yan kai amarya sun isa Gida cikin farin ciki dajin dadi, domin da yawansu koda dubu biyar tasu ta kansu basu taba rikewa ba, yau sai gasu da dubu ishirin nasu na kansu, lallai indo yar arziki ce, sai sa mata albarka sukeyi, ciki kuwa harda dangin Tani, gaba daya matan gidan Tani suka shiga nan suka samesu ita da Abu sunyi jugum babu mai magana, nan jamila ta fara gudu sauran matan suka cabe ana fadin indo mai kashin arziki nan suka fara ba Tani labari irin abun arzikin da aka musu da kudin da aka basu Tani dan tsabar bakin ciki kasa magana tayi sai Abu da tasa kuka wai ayi ma mijin indo asiri shima ya aureta kaman yanda akama Sulaiman ya aure ta nan mata aka fara salati………

Taku maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      70to75

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*ALL MASOYAN NOVELS DINA INA YINKU IRIN SOSAI DIN NAN😍*

Tani ta fara kokarin toshe ma Abu baki, amma ina ta fadi komai, nan mutane sukai ta Allah wadai da halin Tani,ciki harda yan uwanta, wata yar tani ce taja hannun Abu domin a kaita gidan mijinta Abu tana ta tirje2, haka aka fitar da ita, sanda Suka Isa gidan mai gari maman Sulaiman tace sam ita sai sulaiman ya saki Abu domin yanzu akazo aka fada mata asiri akama danta ya auri Abu, nan rigima ta kuma barkewa, saida mai Gari yazo ya kashe wutan tare da cewa akai Abu dakinta, nan Suka shigar da ita ciki, amma maman Sulaiman da yan uwanta Sun kudirin aniyar koran Abu tako wani hali wannan kenan.

Indo wajan asuba ta farka domin ta saba tashi lokacin abun ya zame mata jiki, Tana So taje tayi sallah ta rasa inane bayi, tashi tayi domin taga wata kofa, kitchen ne, tana shiga ta fito da gudu dan tsoro domin kayan electric din Sun bata tsoro takurewa tayi waje daya tana dan kuka kasa2, dai2 lokacin A majeed ya fito cikin jallabiya zashi masallacin kofar gidan, ganin mutum yayi a takure ta rufe fuska da alama ma kuka takeyi, dan tsaki yaja tare da fadin wai wannan abun Mum ta bani a matsayin mata, wani irin haushin indo yaji yana ji, duk da bai taba ganin fuskanta ba, domin a rufe yake, masallaci ya nufa, harya dawo daka masallacin tana nan yanda take kaman zai wuce ya tsaya tare da waigowa, magana ya fara kaman baya son yi kee, indo da sauri ta dago fuskan nan tata ta jagule da hawaye gashi fuskan ta kumbura idonta yayi jaa, wani irin takaici yake ji, yace ki tashi ki shiga can dakin tare da nuna mata da hannu, indo kaman jira take ta tashi da sauri ta nufi dakin tana tafiya kaman zata fadi, domin ita tsoran shi take ji, dan taga mutum sak bature amma yana mata hausa ga shegen kyau, lallai wannan dan shan jini ne, shikenan tata ya kare, koda ta shiga dakin rufe kofan tayi da sauri saboda tsoro, shiko A Majeed tsaki yayi tare da fadin yanzu wannan abun Mum ta zaba min duk matan dake kasar nan, ta rasa wanda zata bashi sai yar cikin shi, toh wannan mai zata iya min? Dan murmushi yayi tare da fadin never bazan iya hada jikina da wannan abun ba, dakinshi ya shige ya kwanta tare da tunanin hanyar da zaibi ya rabu da wannan karaman yarinyar da Mum ta jajibo mishi wai da sunan matarshi a haka har bacci ya dauke shi.

STORY CONTINUES BELOW

Indo tunda ta shiga dakin ta kuma tsorata domin gadon dakin kanshi abun kallo ne, ita dai tasan gado na karfe mai rumfa irin na inna Tani amma yau taga wani daban, ga dakin katoto, ga carfet a tsakiyan dakin, a kasan tiles din dakin ta zauna Tana kuka, jin sanyi yayi yawa yasa ta tashi ta hau kan kujeran dakin ta kudun dune, bacci ne ya dauketa, saida Gari yayi haske sannan ta farka ganin har rana ta fara yi batai sallah ba, yasa ta tashi da sauri ta fara dube2 kofar dakin ta bude tana lambo kaman wata munafuka har ta karasa falo, ta bude kofar waje, babu kowa sai motoci a fake masu kyan gaske, famfo ta hango da sauri ta nufi famfo din ta bude tayi alwala, ta koma ciki, tana shiga falo taganshi a zaune yana kallo, tunda take bata taba ganin tv ba a rayuwanta ihu ta saki tare da kokarin bude kofar ta fita, amma saboda tsoro ta kasa budewa, A Majeed tashi yayi ya nufi inda take tare da daka mata tsawa kee miye haka?  Bata daina ihun ba sannan bata daina kokarin bude kofar ba, tsaki yayi tare da janta yai hanyar dakinta da ita,ganin haka ta kara rudewa tana ihu tare da fadin dan Allah karka yanka ni, dan Allah kayi hakuri ka maidani gidan mu, wayyo yaya yusuf za’a kashe ni yau, zai shanye min jini…..  Cak A Majeed ya tsaya yana kallonta cike da takaici yanzu wannan abun Mum ta auro min da sunan mata kai gskya Mum ta gama dani, jin kaman ya tsaya yasa indo ta sadakar an Kawo wajan da za’a yanka ta, idonta a rufe duk take wannan ihun, ta Fara fadin shikenan yau zan mutu rayuwa na yazo karshe an Kawo ni gidan yankan kai, A Majeed shi yama rasa abunyi dan takaici sake mata hannu yayi yabar wajan dakinshi ya koma yana ta kaiwa da komowa kaman Mai yin Parade, toh a ina Mum ta samo wannan yar kauyen yarinyar ita da bata san mutane sosai a kasar nan ba, duk inda Mum ta samo ta wannan ba damuwa na bane, dole in sallameta ta koma gidansu bada dadewa ba, wayanshi ne ya fara kara dauka yayi yaga Mum ce, gaidata yayi bayan ta amsa tace ya aysha? Shuru yayi tare da tunanin wacece aysha, Mum ta katse shi da fadin Hello son ko baka ji nane, yace inaji mum, sai yanzu ya Tuna da yarinyar da Mum ta aura mishi, wato itace aysha din, yace Mum ni gaskiya Mum yanzu duk matan da suke kasar nan,educated sai a rasa wanda za’a bani sai wannan illiterate din, yar kauye, gskya Mum zan sallameta ta koma gidan su, Mum kashe wayan tayi ba tare data gama jinshi ba, kallon wayan yayi tare da jefa shi kan gadon dakin, shiryawa ya fara yi domin gskya bazai iya kara kwana da wannan yarinyar ba a gidan nan, yau zai koma Abuja.

Indo jin shuru bata ga an yanka ta ba, yasa ta dan bude ido, taga ba kowa dan haka ta shige daki da gudu tana ajiyan zuciya tare da godema Allah da ba’a yanka taba, tunanin su inna jamila ya fado mata yanzu hala ma suna can an yanka su, Allah sarki inna jamila ta kuma fashewa da kuka, turo kofar da akayi ne yasa ta tashi da sauri tana yin baya, Mum ce ta shigo dakin duk da bata santa ba taga kaman su daya da A Majeed, cikin Fara’a Mum tace aysha mai ya faru kike kuka ji fuskan ki ya kumbura koh dukanki yayi? Indo jin maganan matan yasa hankalinta ya dan fara kwanciya domin ta tabbata ita bata yanka mutane amma shi namijin nayi, dan haka ta matsa kusa da Mum tana fadin dan Allah ki fitar dani in tafi gida karya yanka ni, Mum tayi dan murmushi tare da fadin babu mai yanka ki, ki kwantar da hankalinki kinji?  Indo dai shuru tayi bawai dan ta yarda ba, Mum tace muje kici abinci, tare da rike mata hannu suka fita falo, TV din dai yana nan a kunne, nan indo ta kuma sakin ihu,mum ta riketa tare da fadin aysha lafiya kuwa?nuna ma mum TV din tayi da hannunta abun yaba Mum dariya tace haba aysha TV ne fah, bude idonki ki gani, a hankali ta bude idon tare da manne wa a jikin Mum tana gani, a BBC yake taga baturiya tana magana ta kalli Mum da take mata murmushi ta kuma kallon matan TV din taga basa kama kawai fari ne Iri daya sai dai na Mum yafi kyau kuma tafi matar TV din kyau, mum tace muje kici abinci kinji…..  Dai2 lokacin A Majeed ya fito da akwati yana ja, Ganin Mum yasa ya tsaya yana mamakin yaushe tazo, Mum ido ta zuba mishi tana kallon shi…….

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

STORY CONTINUES BELOW

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      75to80

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*MY TA GABAN GOSHIS UMMY ON TOP❣❣*

Ganin irin kallon da mum take mishi yasa ya ajiye akwatin tare da sosa kai yana fadin morning Mum Ashe kinzo? Tace inda ban zo ba tafiya za kayi kenan koh? Ta kafeshi da ido tana sauraranshi, indo tun ganin fitowanshi ta Kara makale Mum tare da rufe ido, ganin bashi da niyan magana yasa Mum taci gaba da fadin wai abdul-majeed yaushe ka koyi rashin jin magana ne? Yanzu duk abunda na fada maka kenan a banza koh? Toh bari kaji wlh idan kana son ganin bacin raina ka tsallake abunda na fada maka, jan hannun indo tayi Suka nufi dinning, ta zaunar da ita tare da zuba mata abinci, ganin yanda indo ta takure yasa mum ta kalleta tare da kiran sunanta aysha ki saurare ni da kyau, babu abunda zai faru dake ki saki jikinki nima mamanki ce kinji, sannan ki daina jin tsoro wancan mijinki ne, kinji kai ta daga alaman eh, sannan Mum tace ta fara cin abincin chips nd egg ne da Tea sai farfesun naman kaza, indo ci take sosai ganin tana ci yasa Mum tabar wajan ta koma kan kujeran falon A majeed dake tsaye yana kallonsu wani irin takaici yake ji, wai waccan yarinyar ce matarshi wanda inda ya haiyu da yanzu yana da Sa’anta, ganin Mum ta zauna yasa ya matsa kusa da ita yace Mum…..  Daga mai hannu tayi alaman ya kyaleta, yace plz Mum listen to ur son yana maganan ne kaman zaiyi kuka, bata kuma ce mishi komai ba ganin haka ya fara magana Mum plz ki fahimce ni, bawai bana son auren bane, yarinyar ce bana so duk maganan nan yana yine cikin turanci, yace mum she’s young mai zata min and batayi karatu ba, kwata2 bata da wayewan da nake bukata a wajan mace, Mum ido ta kafa mishi yanda yake bayani har yakai aya, tayi ajiyan zuciya tare da fadin ka gama? Shuru yayi bai ce komai ba, shurun nashi bai dameta ba, ta fara magana idan kai ka manta ni ban manta ba, dan haka bari in Tuna maka, na baka zabi akan ka kawo Mata, kace in zaba maka, ko ka manta da anyi haka?  Yace mum yes but amma ba irin wannan nake So ba…..  Mum cikin tsawa tace mishi ya isa haka A Majeed inma irinta kake so ko ba irinta ba wannan ya rage naka, bai kuma cewa komai ba sai daure fuska da yayi yana hararan indo yanda yaga tana cin abinci, Mum ta tashi tace indo ta biyota, daki, Indo binta tayi cikin dakin data kwana bayan Sun shiga, Mum ta zauna akan kujeran dakin tare da cema indo ta zauna itama akan kujeran, indo zama tayi a kasa, Mum tayi dan murmushi tare da fadin a kai nace ki zauna, tashi indo tayi ta zauna a kai, Mum ta dan kafe indo da ido, ta aiyana a ranta yarinyar fara ce kyakyawa sai dai farin ya boye saboda wahala, Mum tace aysha bari kiji ki saki jikinki sosai nan gidan mijinki ne, nan Mum ta fada mata yanda akayi har danta ya aureta, lallai abdul ya taimaketa a rayuwa domin shine ya rabata da auren dan jummai, wani irin waje mai mahimmanci ta ajiye abdul cikin zuciyarta, Mum ce ta katseta da fadin yanzu abunda nake so dake duk wani abu da yake damunki ki fadamin kinji kar ki boyemin komai sannan akwai kaya a wardrobe sai dai basu da yawa,anjima za’a kawo miki akwatin ki,sannan za’a hado da tela ya gwada ki, sannan zansa a kawo miki mai tayaki zama, duk wani abu da baki ganeba zata nuna miki, kai indo ta daga domin yanzu ta yarda da Mum tasan ita da A Majeed ba yan yankan kai bane, nan Mum taita kwantar ma indo da hankali sannan tayi mata sallama akan za’a kawo abincin rana bada dadewa ba, koda Mum ta fita a falo taga dan nata fuska a daure bata kulashi ba tazo zata wuce ganin haka yasa yace Mum zan koma gobe akwai Office Monday mum tace zanyi tunani akai sanna ban yarda ka tafi ba har sai kaji daka gareni, tana gama fadin haka ta fita ba tare da ta jira amsan dan nata ba, A Majeed ji yayi kaman yasa kuka dan takaici yanzu Mum ta bashi wannan yar kauyen sannan dan ya nuna damuwa akai shine take fushi dashi, wannan wani irin abune yake faruwa dashi wanda ko a mafarki bai taba tunanin za’a mishi auren dole ba, yes auren dole mana tunda shi baso yake ba, dan tsaki ya ja tare da fadin gskya zai je ya sami Dad dinshi akan yayi ma Mum magana da Wannan tunanin ya danji sanyi a ranshi.

STORY CONTINUES BELOW

Indo ta rasa inane bayi, Tana so tayi wanka ga fitsari ya dameta tun dazu, bude kofar dakin akayi wata yar dattijuwa ce, ta shigo dakin da murmushi, indo cikin dashewan murya tace mata ina wuni? Matar ta amsa da lafiya yata, ya naganki haka fuska babu kwalliya maza shiga toilet kiyi wanka kinji, indo ta fara zare ido To inane cholit kuma, kaman daka sama taji matar tace zo ki gani, nan ta bude wata kofa a cikin dakin indo baya tayi da sauri dan tsoro toilet ne, nan matar tayi dariya dan Mum ta bata labarin indo bata san komai ba Tana son ta koya mata, tace yata zo ki gani kinji? Indo girgiza kai tayi alaman a’a, ganin haka matar ta kamo hannunta tace shigo kiga yanda ake amfani Dashi, ihu indo tasa tana fadin dan Allah karki shigar dani, amma bata saurare ta ba, har saida ta shigar da ita, sannan tace ma indo ki nutsu yata babu wani abu, nan ne bayi, indo ta danyi shuru amma tana hawaye, nan ta nunama indo yanda ake amfani da komai na bayin sannan ta fita tace tayi wankan, indo sharp2 tayi domin har yanzu a tsorace take, matar tace badai har kinyi wankan ba, tace eh nayi, nan taba indo wata doguwan riga tace tasa, rigan yayi ma indo yawa kadan bayan tasa, tace suje falo Tela zai gwada ta, Tela ya gwada indo sannan matar tace sunanta Maryam indo hawaye ya fara zuba a idonta jin sunanta daya da mamanta,matar tace lafiya aysha? Indo tace naji sunanki daya da inna ta, matar tayi dan murmushi tare da fadin To saiki dinga cemin Mama koh?indo ta daga kai alaman eh cikin jin dadi,tun daka wannan lokaci indo take kiranta da mama.

Kaman yanda A Majeed yace hakan ko yayi ya sami mahaifinshi akan a rabashi da matar da Mum dinshi ta bashi, Dad dinshi ya nuna shima bai yarda ba tare daja mishi kunne akan karya fara cewa zai saketa domin bazai zubar mishi da mutunci ba, A majeed haka ya koma gida cikin takaici, washe gari da sassafe ya nufi gidan nasu domin yayi ma mum sallama akan zai wuce, lokacin Mum na kitchen domin indai his excellency na gari ita take mishi abinci da kanta, gaida Mum yayi ta amsa babu yabo babu fallasa, yace Mum zan wuce ne gobe akwai Office, Mum ta danyi shuru can tace ok amma da matarka Zaka tafi dam gabanshi ya fadi……..

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      80to85

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*DADIQA ISAH*😍

Domin baiyi zaton mum zata mishi maganan tafiya da wacce ake kira da matarshi ba, yace mum bada ita zani ba, Mum tace wannan kuma bazai taba faruwa ba dole ka tafi tare da matarka, dan shuru yayi na wani lokaci kafin yace Mum ita a nan zan barta ta dinga zama sai in dinga zuwa, Mum tace sam hakan bazai taba yihuwa ba, ganin Mum ta dage kuma taki bashi fuska yasa yace shikenan mum, amma da an barta Friday zan zo sai mu koma tare kafin nan nasa an gyara inda zata zauna, Mum shuru ta danyi tana nazari kafin tace shikenan hakan yayi, Allah ya kiyaye hanya, ya amsa da ameen, sannan Mum tace ka dai sallameta koh, dan naga kaman da shiri ka fito, yace eh Mum munyi sallama da ita, Mum taji dadi sosai har tana ce mishi ya tsaya yayi breakfast, yace No mum ina so in kai da wuri tace ok tare da bashi dambun nama da drink, fita yayi driver ya ja, suka daga abuja, A Majeed rabonshi da ganin indo tunda Mum tazo jiya kenan bai kara ganinta ba, amma yace ma Mum sunyi sallama.

STORY CONTINUES BELOW

Indo ita da Maryam wacce take kira da Mama yanzu suna zaune a falo, Mama tana koya mata yanda ake canza channel indo an rike remote ana dannawa, idan ta canza channel daya sai tayi dariya irin ta canza dinnan, Mama babu abunda take sai dariya tare da mamakin irin kauyancin indo, haka indo taita canza channel Tana dariya, Mama ganin abun bamai karewa bane, yasa tace tazo su zaga gidan taga ko ina, tashi indo tayi ta bita suna shiga ko wani lungu da sako, gidan kato ne sosai domin falo uku ne a cikin gidan akwai guda biyu a kasa sai daya a sama, daki uku a kasa, biyu a sama da falo babba, indo dai baki da ido ta bude tana kallo, Mama Tana ta mata bayani,har suka zo kitchen dake kasa, indo tace Mama ni kam tsoran nan nakeji wlh, Mama tayi dariya tare da fadin ki daina jin tsoro aysha, nan kitchen ne, indo kasa fadan kitchen tayi dan haka tace mai kenan? Mama tace wajan yin girki, indo ta zaro ido cike da mamaki, nan ne wajan yin girki tabdi, to ya banga murhu ko dutse ba ko akan me akeyi oho, mama ce ta katse mata tunani tare da fadin matso ki gani, nan indo ta matsa Mama ta kunna Gas sai ga wuta ya kawo indo da gudu tabar kitchen din tana fadin mun shiga uku,mama da sauri ta fito tana dariya tare da cewa indo tazo su koma ciki, indo taki yarda sai fadi take wutan ya mutu? Mama tana ta dariya babu yanda batai da indo ba akan su koma kitchen din amma taki yarda su koma, domin abun ya bata tsoro.

Mama tana taimaka ma indo sosai musamman wajan yin tsaftan jiki, domin a rana sau biyu take sata yin wanka, wanda ada sai tayi wata batai wanka ba, suna zaune a falo suna hira, Mama tace wai ni kam aysha kullum kanki a rufe,bude mu gani, indo ba tare da damuwa ba ta cire dankwalin kanta, nan Mama tasa salati ganin kan a dangare ga wari na tashi, tace aysha haka kanki yake, Indo dai bata ce komai ba, mama waya ta dauka ta kira Mum, bayan Mum ta dauka Sun gaisa take cema Mum ya kamata aysha taje Saloon, Mum tace ku shirya zansa driver yazo ya daukoku sai a mata a nan, Mama tace toh ranki ya dade, nan Mama tasa indo ta kara yin wanka, tare da fito mata da wani riga da skirt tace tasa, indo ta fito wanka tasa Mama ta bata powder ta shafa, babu laifi ta danyi Kyau, Mama ta bata gyale ta yafa, basu dade ba driver yazo ya daukesu akai gidan mum dasu, indo anata kalle2 har Suka shiga ciki, a makeken falon gidan suka zauna, basu dade da zama ba aka cika musu gaba da kayan motsa baki, Mum ce ta fito cikin shiga ta alfarma fuskanta dauke da Fara’a, tace sannu Maryam, maryam tayi murmushi tare da fadin yauwa ranki ya dade nan ta gaida Mum, itama indo ta gaida Mum, cikin Fara’a Mum tace aysha zo mana tare da miko mata hannu, alaman tazo inda take, tashi indo tayi ta nufi inda Mum take, nan Mum ta fara tambayanta ya kwanan bakwanci? Indo kunyan Mum takeji bata amsa ba sai murmushi, mum daukan wayanta tayi tasa a kunne tare da fadin kizo ciki, bata dade da ajiyewa ba, wata mata tazo cikin riga da skirt baki da baby hijab fari, tace yauwa hafsat ga Aysha nan ki gyara mata kai da gyaran jiki, hafsat ta amsa da ok ma, Mum ta kalli indo tare da fadin aysha tashi kuje, indo tashi tayi tabi bayan hafsat din, bayan sun fita Mum ta kalli, Maryam tace mai kika fahimta a gidan? Maryam tace ranki ya dade tunda naje gidan ban kara ganin shiba, haka kuma ban ganshi wajanta ba, mum tace ya wuce abuja, amma ai yazo sunyi sallama koh? Tace a’a bata ganshi wajanta ba sai dai in a waya ya mata, Mum shuru tayi amma Kana ganin fuskanta kasan ranta a bace yake, can tace ma Maryam inaga zaki koma ki dibo ma aysha kaya da dai abunda zata bukata sai ta zauna a nan kafin ya dawo dan tare nake so su tafi, maryam tace ranki ya dade inda zaki dauki shawara na aida an barta a nan sai a sata makaranta in yaso sai ya dinga zuwa, domin naga aysha bata san komai ba,nan taba Mum labarin abunda indo tai tayi Mum dariya tayi sosai sannan tace hakane gskya tana da bukatan tasan wani abu, bari zansa a duba mata makaranta duk da tayi girma ,maryam tace gskya hakan ya kamata nan sukai ta tattaunawa.

An wanke ma indo kai, gashinta har gadon baya kun san Fulani ba baya ba wajan gashi, gashi an Mata gyaran jiki tayi kyau fuskan ta tayi dan haske kadan, ita kanta hafsat din tayi mamakin gashin indo, nan tace ma indo suje ciki, bayan sun shiga wajan Mum, Maryam tace kai Masha Allah, mum tace kai aysha kinyi kyau sosai, Maryam tace muga gashin indo ta cire dankwalin, maryam ta saki baki domin ganin yawan gashin, Mum tace Masha Allah sai kace balarabiya wajan gashi su Maryam sukai dariya, nan Mum tace ma hafsat yanzu gyaran jikin zuwa nan da yaushe za’a daina? Hafsat tace za’a mata kaman na sati biyu, dan naga fara ce sosai idan aka mata farinta zai fito sosai, nan Mum tace ok, tun daka wannan ranan indo ta dawo zama gidan mum ga tela ya kawo mata wasu kayanta dinkin dai2 jikinta Mum tasa ana koya mata abubuwa da dama irin su girki da makeup, ranan da indo zata fara shiga kitchen anyi drama har sai da Mum tazo kafin ta shiga.

STORY CONTINUES BELOW

A Majeed tunda ya tafi sati biyu kenan bai zoba, Mum Tana zaune a falo, ita da indo tana fada mata zata fara zuwa islamiya gobe, indo taji dadi dan tana son karatu kuma ko ba komai tasan addininta, wayan mum ce tayi ringing ta dauka ganin bakuwan No kuma na waje yasa tayi mamaki ko waye kuma bana kasar su bace Egypt, dauka tayi muryan A Majeed ne yace Mum barka da warhaka, tashi tayi daka falon ta nufi Daki,tace lallai A Majeed ka kyauta kana ina yanzu?  Yace Mum ina London Zainab na raka wani meeting da za suyi, ran Mum ya baci sosai tace wlh na baka nan da jibi ka dawo gida kuma direct jalingo zaka tawo, tana fadin haka ta kashe wayan tare da takaicin abunda dan nata yayi, tana ta kiranshi No dinshi a kashe Ashe ya tafi London da matarshi, lallai saina saba ma A majeed sosai.

Indo an fara zuwa islamiya tana karatu, sannan Mum tasa wani Mlm na koya mata a Gida but islamiya da boko,  yau indo da ciwon ciki ta tashi da alama period za tayi, a daki ta wuni Mum jin shuru yasa ta nufi dakin indo din, ta ganta a kwance tana juye2, nan Mum ta karasa da sauri tana tambaya aysha lfya kuwa? Indo ciki ta nuna mata alaman yana mata ciwo, nan ta kira dr ya fara dubata, ya bata Magani tare da cema Mum period ne za tayi, Mum tayi mishi godiya tare da sallaman shi, Mum tasa aka hada ma indo Tea ta tasar da ita tana bata indo tasha sannan ta bata Magani tasha, taba indo pad tasa, Mum ita ta fadama indo yanda za tayi amfani Dashi duk da indo tana jin kunya amma Mum ko a jikinta, bayan indo tasa pad din ta kwanta bacci ya dauketa.

*Kuyi manage da wannan zuwa gobe muga dawowan A Majeed yanda zai kwashe da mum*

*plz ku dinga sharhi akai domin yana da amfani*

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      85to90

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*SAD’ASH*
*1 DIN BA 2 DIN BA😝*

Indo sai wajan 4 ta farka babu laifi ta danji dama2, Mum ta shigo dakin ta ganta a zaune tace sannu aysha, ya cikin ya daina koh? Tace eh da sauki, mum wayanta ta danna tare da sawa a kunne tace ki kawo Min paper soup din chicken da abu mara nauyi, ina sama, tana fadin haka ta kashe wayan, ba’a dade ba sai gashi an kawo chicken soup din da snack, a tray Mum tace haba ba snack zaki kawo ba mara lfya zata ci, abinci nake So, ki bata ko dankali ne, tace ok ma, ta ajiye ma indo chicken din,har matar zata fita Mum tace ta tsaya tare da kallon indo ko a Kawo miki tea ne? Indo tace eh, Mum tace ta kawo snack din sannan ta hado Tea din, ta amsa da ok ma sannan ta fita bata dade ba sai gata da Tea din, Indo taci ta koshi harda ragewa, haka Mum taita kula da indo ranan bata je islamiya ba, sai dai da lesson teacher dinta yazo ta fita duk da mum tace ta zauna tace ta warke.

Mum na zaune a falo sai ga A Majeed ya shigo, zama yayi a inda take ganin ta daure fuska babu alaman wasa yasa ya shiga tai tayinsa, gaidata yayi bata Amsa ba sannan bata kalleshi ba,yace Mum plz am so sorry nasan nayi kuskure amma dan Allah kiyi hakuri fushin ki Bala’i ne a kaina, jin haka yasa jikin Mum yayi sanyi, tace kasan da haka kake kin bin umarni na, kake yin abunda ya maka dai2? Yace Mum kimin afuwa dan Allah, kun san d’a da uwa,tace shikenan naji zan hakura amma sai kabi abunda na tsara ma,yace insha Allah my Mum tare da kara matsawa kusa da ita, tace A Majeed akan matarka aysha yarinyar alkhairi ce a gareka amma ba zaka gane ba sai nan gaba domin yanzu giyar son matarka na kanka baka gane tayi dai2 da ba dai2 ba, komai tayi a wajanka dai2 ne, nasha fada maka wlh ina son matarka har cikin raina, sai dai halayenta da bana so, yau shekaran ku nawa da aure amma har yanzu ban taba ji kace tayi batan wata ba, duk da haiyuwa na Allah ne, amma kwata2 matarka inaga bata da burin haiyuwa yanzu, bani da yawan dangi ko yara amma ina son inga jikoki na, bawai na maka auren nan dan in kuntata maka bane a’a kawai dai dan na lura Kana da bukatan hakan ne, A Majeed ya rike hannun mum dinshi yana dan murmushi yace Mum ngd amma dan Allah kiban umarni in saki yarinyar nan in yaso sai in auri wata…… Mum tace ya isa haka ta dakatar dashi, dan shuru tayi  tama rasa abun cewa Can tace A Majeed miye illan wannan yarinyar toh da baka sonta? gyara zama yayi dakyau sannan yace mum akwai abubuwa da yawa, kinga ni mutum ne Mai san Mace yar gayu kyakyawa wacce ta waye, mai ilimi sosai wannan yarinyar yar kauye ce bata da ilimi da wayewa gata karama wlh Mum abun kunya ne a gareni ace wannan yar kauyen mata tace, nayi miki alkawarin zan auri mata har uku in kina bukata amma ki barni in rabu da wannan plz mum, Mum ajiyan zuciya tayi tare da fadin shikenan naji duk matsalanka, amma ka bani lokaci kadan zan bukaci ka rabu da ita da kaina, cikin jin dadi yace thank My Mum tare da rungumeta, Mum murmushin takaici kawai takeyi wato shi Mace yar gayu wayayya yake So bayan ga daya nan a gidan shi yana shan wuyanta amma bai daddara ba, shi babu ruwan shi da tarbiya sai wayewa lallai A Majeed yayi nisa,katseta yayi da fadin Mum yunwa nake ji sosai wlh, tace ga abinci can a kan dinning, tashi yayi ya nufi dinning din, indo da tazo zata sauko falo taji suna magana jin zai nufo wajan tabar gun da gudu tana hawaye, daki ta shiga tana kuka, tabbas gaskiyan shine, ita ba ajin shi bace, taya za’a hada mai tallah da dan gwamna aure ai wannan abun ma kowa yaji yasan bamai yuhuwa bane, tabbas dan mai kudi sai yar mai kudi, yar tallah sai dan talaka dan uwanta wani hayewa ne ya zubo mata, tare da fadin dama dan jummai ta aura da yafi mata kwanciyan hankali duk da tasan auren nashi ba hutu bane domin badan Allah zai aureta ba, amma shine dai2 da ita duk da har gobe sulaiman ne a ranta amma shima tasan yafi karfinta, haka taita tunani tana kuka.

Koda A Majeed yayi ma Mum sallama akan zashi gidan shi bata hana shi ba, sai cemai tayi sai da safe, ya fita cikin jin dadi domin ya kusa rabuwa da matar da aka jajibo mai, Mum tashi tayi ta nufi dakin indo, jin karan bude kofa yasa indo ta kwanta kaman tana bacci, Mum ganinta tayi a kwance ta kura ma fuskan indo ido, bata ga munin yarinyar ba, domin kuwa indo tafi Zainab dinshi kyau nesa ba kusa ba, domin indo ita bata makeup din da matarshi takeyi inda itama za tayi da sai an dauki indo da gudu Kafin matar tashi da yake ji da ita, mum bayan ta gama tunaninta ta fita daka dakin cikin tausayin indo , jin ta fita yasa indo ta bude ido tare da ci gaba da kukanta.

Abu bayan an tafi an barta taita kuka, Yan uwan sulaiman suka shigo dakin suka ganta tana aikin kuka, kanwar sulaiman saudat wacce Sa’ar Abu dince kuma kawarta ce tace kunga shegiyar wai kuka takeyi, nan saudat taita zungurin Abu dake kuka, Abu ta tashi ta cakumi saudat da nufin ta rama nan suka tarun ma Abu suka mata lilis, sulaiman ya shigo yaga ana jibgar Abu nan yaita Bala’i akan me zasu dukar mai mata, mai gari jin hayaniya shima yazo gefen yaron nashi, nan yaga kannan sulaiman da yayyinshi mata mai gari ya tambaya mai ke faruwa nan sulaiman ya fada mishi abun da sukai ma matarshi mai gari ya musu fada sosai akan idan basu fita daka lamarin matar sulaiman ba sai yayi mugun saba musu, nan suka fita suna fadin an mallake musu dan uwa, shima mai Gari fita yayi, nan sulaiman yaita rarrashin Abu, amma ina taki yarda wai ita saiya saketa ta auri mijin indo, sulaiman dai ranan a waje ya kwana dan tashin hankali.

Washe gari Mum da indo suna dinning suna breakfast sai ga A Majeed ya shigo falon kamshin turaren shi ya cika wajen, yace morning mum gaban indo yahau bugawa tunda ta ganshi, Mum tace morning, ganin indo yasa ya tamke fuskat dan shi yasha ma ko ta koma kauyensu, yanzu wannan yar ficiciyan ake kokarin manna mishi, To inyi me da ita, duk da yaga ta dan canza akan da amma shi yasan wannan ba tsaranshi bace domin shi sai babban Mace irin zee dinshi, Mum ce ta katse shi da fadin lfya naga ka tsaya kerere? Yace Mum ni zan wuce Abuja yanzu, Mum tace ok Allah ya kiyaye hanya, ya amsa da ameen, tare da fadin yaushe Dad zai dawo tace gobe insha Allah, yace ok tare da fita, indo sai da taga ya fita ta sami nutsuwa.

A Majeed ya koma abuja, koda ya nufi gida Zainab ce zaune a falo ita da wasu mata guda biyu daka gani kawayenta ne, nan Suka gaisa da A majeed, ya zauna kusa da madam din tashi dako kallo bai isheta ba, yace swty am back, ta tabe baki tare da fadin I though ai a can zaka tare, domin naga mamanka tana kokarin raba ni dakai, bini2 kace tace tana nemanka am tired of this, bazan dauki wannan ba wlh, daya daka cikin kawayenta tace hmm ai sai yasa gwara ka auri wacce mum dinshi ta mutu mother in low ar wicked wlh dat Why ni bazan auri wacce Mum dinshi ke raye ba W……..  Tas saukan mari taji akan fuskanta A Majeed ne ya kai mata mari tare da fadin how dare u zaki dinga fadin irin wannan maganan akan Mum dina, Infact ma wa yasa bakin ki get out of My house ya nuna mata kofa, daukan jakanta tayi dayar ma ta tashi tayi waje zainab na kiransu amma suka wuce, Zainab ta kalli A Majeed tace u try ka nunawa duniya kafi son mamanka akai na dan haka yau sai kaban takarda na in yaso sai kaje ka zauna da family dinka……

TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

1

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      90to95

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*SIS AYSHA MAMAN HUDA😍*

A Majeed shuru yayi ba tare da yace mata komai ba, ganin kaman ya maidata wata Sauna tana magana baya kulata yasa ta matsa kusa dashi tana fadin A Majeed tun muna mu biyu ka sakeni, kallon ta yayi cikin fushi tare da fadin kin ci darajan abu guda biyu amma da yau saina sakeki kaman yanda kika bukata, cikin gadara tace bana son inci darajan komai ni nafi karfin kace naci darajan komai wlh sai dai ni ince kai ne ke cin daraja ta da iyayenka, domin kasan mahaifina shine No 1 a kasar nan dan haka yau ko mai kasha sai ka sakeni tas ya sauke mata mari tare da fadin bansha komai ba zan nuna miki cikin hayyacina nake, saki dai kike bukata koh? Shuru tayi hannunta nakan fuska tana mamakin marin da yayi mata gashi taga kaman zai iya sakin nata domin duk wannan abun da takeyi cika baki ne bawai so take ya saketan ba, ganin karya aikata yasa tabar falon da gudu tana kuka, shima ganin haka yasa ya fita daka gidan gaba daya domin kanshi yaji yana juya mai har ga Allah yana son Zainab sai dai a yau ya fara ganin halin nata mara kyau da Mum dinshi ke fada tana Dashi, wanda shi a da komai ta mishi baya ganin laifinta duk da kuwa tana mishi abunda yafi haka, kodan yau ta taba Mum dinshi ne yasa har yaga laifin nata, tabbas hakane domin yana son Mum dinshi fiye da yanda mai karatu yake tunani, dan tsaki yayi tare dajin haushin wannan kawar Zainab din wai mother inlow are wicked, tunda yabar gidan sai dare ya dawo a falo ya ganta taci uban kwalliya da English wear, top din da tasa gaba daya ta kameta kirjinta duk a bude abunda A Majeed yake masifar so kenan duk da ba wani girma nata suke dashi ba amma tasan yana rudashi, da sauri ta nufeshi tayi hugging dinshi tana kuka tare da fadin am So sorry my swt, kara matseta yayi tare da shafa bayanta cikin kunnan ta ya rada mata stop crying my baby, cikin kissa tace Baby yanzu baka So na ka canza min ta dan janye jikinta daka nashi,A Majeed da ya riga ya fara fadawa da sauri ya matsa kusa da ita yana fadin ba haka bane baby I…..  Da gudu ta tafi dakinta tana kuka da sauri ya bita a kwance ya ganta akan ‘katon gadon ta tana faman kuka nan hankalinshi ya tashi ya shiga rarrashi dagata yayi ya fara kissing dinta tare da shafata tako ina itama tuni ta fada ranan dai A Majeed yaji dadi domin rabonshi da wani abu ya hadasu harya manta duk da wani lokacin daki daya suke kwana, Zainab ita da kanta tasan samun namiji irin mijinta zaiyi wuya ga kyau ga kudi duk da kudin ba matsalanta bane domin tana dasu wanda bata san nawa ta mallaka ba ma,ita burinta ta sami mijinta ita daya a kullum tana tsoran yaje jalingo ko Egypt kasar mum dinshi kar yaga balarabiya yace zai aura ko Mum dinshi tace ya auri wata daka danginta, domin balarabiya ce kawai zai aura take ganin zata yi kishi da ita dan tasan suna da kyau amma babu wata yar Nigeria da zatai gigin auran mata miji ma ta zauna lfya, domin tana matukar kishin mijinta dan zata iya aikata komai a kanshi sannan bata son yana yawan sex da ita dan a ce wanta yana saurin tsufar da mace hmm tabdi jam ban taba jin haka ba sai a wajan zee🤣.

Mum tayi shawara da Maryam akan mai ya kamata tayi ma indo dan rayuwanta ya in ganta, Maryam ta bada shawaran a sata a wata makaranta na mata wanda ba suyi karatu ba mai suna NEVER GIVE UP IN LIFE,  za kayi karatun wata biyar zasu koya ma boko yanda zaki kula da kanki da tsafta da sauran su, Amma ko wanne fanni2 ne Maryam tace a sa aysha a fannin boko dana girki, Mum tayi na’am da batun kuma taji dadi sosai sannan kuma idan mutum ya gama za’a bashi certificate na primary school sannan idan an fara waec da mai bukatan ci gaba da karatu suna da center mutum yana biya yayi amma in za kayi waec sai ka zauna harna shekara daya Kana karatu in kuma primary certificate ne wata biyar, Mum tace aysha shekara daya za tayi domin zata ci gaba da karatu, mum tasa anyi ma indo komai da komai, fara zuwa kawai ya rage shima cikin satin nan zata fara zuwa,.

STORY CONTINUES BELOW

A Majeed na office yana duba wani abu cikin system sai ga Abdul ya shigo, bayan ya zauna ya kalli A Majeed tare da fadin angon aysha ya amarya da uwar gida, tamke fuska yayi tare da daina danna system din yace kasan nasha fada maka ka daina min irin haka, kawai ka fadamin abunda ya kawo ka, in kuma ba komai ya kawo ka ba ka tashi ka koma office dinka, Abdul yace Allah ya baka hakuri ango kasha kamshi A Majeed kara tamke fuska yayi tare dayin banza da abdul, ganin haka Abdul yace na samo wata yar Kaduna ina so musa rana muje ka ganta, A Majeed tabe baki yayi tare da fadin ina wannan yar kauyen da kace Kana so da? Abdul murmushi kawai yayi tare da fadin abar dai wannan zancen wancan tayi aure, kawai nidai yaushe kake da Time muje? A Majeed yace bari muga Next Week sai muje ko ran Friday, Abdul yace OK Allah ya kaimu tare da tashi dan ya koma office dinshi.

Indo an fara zuwa makaranta, tun safe inta fita bata dawowa sai 4, tana dawowa zata islamiya, in tayi sallah taci abinci lesson teacher yazo, ran lahadi ne kawai take dan samun hutu,domin babu Skul sai islamiya da lesson, kuma babu laifi tana fahimtar karatun dan tana son itama taga tayi ilimi, sai dai kullum burinta taga dan uwanta yusuf, Mum Tana kula da indo sosai ta gefen sutura kayan kamshi da sauransu, ga abinci mai gina jiki da take samu yasa jikinta yake murmurewa ga girma tana karayi, Mum ta lura tana da girman jiki amma rashin cin abu mai kyau yasa bata girma sosai amma yanzu Alhmdlh komai ya fara bayyana, gashi sunyi wani irin shakuwa da Mum duk da indo na jin kunyan Mum, suna zaune suna fira mum take fada ma indo inta gama karatun ta Egypt zata taci gaba sai ki zauna wajan ummi na, indo taji dadin hakan sosai tare da kudiran kara dagewa da karatu.

Zabe yana ta gabatowa domin his excellency wannan karan Senate yake son zuwa, anata campaign, Mum Tana Bussy kwana biyu domin akwai masu taya mijinta campaign mata da ita take basu duk wasu abu da suke bukata, indo itama takan taya Mum da bata shawara musamman da taji his excellency yace yana son a kara yawan titi ayi a layi2, indo ta sami Mum a daki tana zaune ita daya, Mum tace aysha dazu nazo ai naga kina bacci, indo tayi murmushi tare da cema Mum barka da hutawa, Mum ta amsa da yauwa, nan indo tace ma mum akan titi din da his excellency taji yana fada idan aka karayi zaisa talakawa suji dadi, indo tace Mum inaga shi talaka baya bukatan titi ta kofar gidansa indai akwai a babban hanya, shifa *TAMBARIN TALAKA* rumbun sa, indai talaka zai ci ya koshi bashi da matsala domin shine burin shi, inaga da ayi wannan titin gwara an raba musu jari koh da babu yawa, Mum da tunda indo ta fara magana take kallonta da mamaki yanda har tayi wannan tunanin mai kyau, Mum tace kai aysha gskiya kinyi tunani mai kyau, anya ma Ba political science zaki karanta ba? Indo dariya tayi kawai, Mum tace hakan za’ayi gobe zan kira meeting sannan anjima kadan zan gayama his excellency wannan shawaran, koh da Mum ta sanar ma his excellency wannan shawaran yaji dadi sosai tare da cewa gskiya kinyi tunani mai kyau, Mum tace bani nayi wannan tunanin ba aysha ce, yace wace Aysha? Tace matar A Majeed, yace yauwa suna nan lfya dai koh, dan ina tsoran wannan yaron, kwanaki yazo ya sameni akan a raba auren naki yarda, mum taba his excellency labarin abunda yayi tare da gaya mishi yarinyar tana nan gidan, ranshi ya baci sosai tare Da fadin dan mai yasa Mum bata gaya mishi ba sai yanzu, daukan wayanshi yayi ya kira A Majeed, bayan ya dauka yana gaidashi amma his excellency bai amsa ba sai ma fadin da yayi kazo jalingo gobe da safe sannan ya kashe wayan, his excellency yace ma mum tunda ya aureta dole ya zauna da ita ban yarda da zancen saki ba, gobe dole ya tafi da matarshi in yazo Mum za tayi magana ya dakatar da ita tare da fadin ban san jin komai naga In akabi ta Yaron nan saiya zubar min da mutunci tashi yayi tare da cema Mum ina da meeting sai na dawo.

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

STORY CONTINUES BELOW

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      95to100

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*ZAINAB ZEE BABY😍*

Mum shuru tayi tama rasa abunyi, harga Allah itama Tana son indo ta koma gidan mijinta sai dai tana gudun irin zaman da za tayi a abuja din, haka taita tunani kala2, tare da tausayama indo din, domin tasan tunda A Majeed ya iya bude baki yace baya sonta a gabanta tasan tabbas idan aka matsa mai akan indo din zai iya yi mata wani abun ko matarshi, Mum gaba daya ta kasa sukuni zama tayi tana jiran mijin nata ya dawo suyi magana, koda his excellency ya dawo Mum ta mishi magana akan a bar indo a nan yace hakan bazai yihu ba, bawai an aurota bane dan ta zauna dasu ba, dole gidan mijinta zata zauna, ganin tashin hankalin da matar tashi ta shiga yasa ya kamo hannunta yace kiyi hakuri babu abunda zai faru nasan abunda kike gudu, insha Allah babu abunda zai faru zanja mai kunne sosai karki damu, Mum ajiyan zuciya tayi ta danji dama2.

A Majeed duk da yau monday amma haka ya tawo jalingo tare da tunanin lfya dad yake neman shi, karfe goma da wani abu ya sauka a jalingo, gidan shi ya sauka sai da ya kimtsa domin baya tunanin ko yaje gida zaiga Dad dinshi yanzu, wajan 12 ya nufi gidan nasu koda ya isa anata kiran sallah masallacin dake kofar gidansu ya nufa mutane ancika sosai ciki harda mai girma governor, bayan an idar, his excellency yana ta gaidawa da mutane yana jin matsalan su, wanda hakan ya zame mai jiki kullum in yana kasar yana sauraren kukan mutane, tare da dan nasa Suka shiga gida, a falo suka sami Mum a zaune tana karanta news paper, A Majeed wajanta ya nufa yana fadin sannu da hutawa my mum, mum murmushi tayi tare da fadin yauwa ya hanya? Ya amsa da lafiya his excellency zama Yayi Mum ta tashi ta nufi kujeran daya zauna tare da fadin food is ready fah, yace ok tashi yayi Suka nufi dinning wasu manyan kuloli ne Sun kai goma akai kana ganin hummer din kasan masu tsada ne, abinci kala2 na gida dana waje, Mum ta zuba ma mijinta da dan nata, suna ci suna taba fira sama2 A Majeed shidai ya kosa yaji ko miye Dad ke neman shi, har Dad ya kammala ya kalli A Majeed yace ka sameni falon sama inka gama, Mum ta tashi tabi mijinta saman itama, A Majeed kasa cin abincin yayi tare da tambaya toh maiya faru wata zuciyar tace may be Akan campaign dinshi zasu tattauna dan haka yaci gaba dacin abincin shi, sannan ya haura sama, A kan kujera yaga Dad Mum na gefenshi, shima samun waje yayi ya zauna, Dad yace Abdul-majeed Ashe baka da kirki? Dam A Majeed yaji gabanshi ya fadi dad yaci gaba da fadin dama har yanzu baka hakura da maganan aurenka ba, toh wlh baka isa ba domin ba zaka maidamu mutanan banza ma, mum dinka tamin bayanin komai dan haka in zaka tafi zaka wuce da matarka sannan wlh kar inji kar in gani in naji ka mata wani abu wlh sai nayi mugun saba maka, Dad yaja mishi kunne sosai daka karshe yayi mishi nasiha, A Majeed gaba daya takaici ya isheshi koda zai koma gidansa Dad yace su tafi tare da matarsa babu yanda ya iya, nan Mum tasa indo ta fito su tafi tare dasa masu aiki su hada mata kaya, gaba daya an hadama indo kayanta, Mum tace ta tafi da kadan sauran driver zai kawo Mata abuja din Indo babu abunda take sai kuka domin bata son rabuwa da Mum ga karatun ta,sannan bata san zuwa gidan A majeed, domin harga Allah tsoranshi take ji sosai, Mum tayi mata nasiha sosai tare da fadin komai ya mata ta kirata ta fada mata, ta dauko waya taba indo tare da fadin akwai number dina a ciki, indo ta amsa tare da godiya,mum tace zata sa a bata transfer na skul dinta sai ta farayi a abuja, indo taji dadin hakan sosai, har mota Mum ta rakata A Majeed yana mota a baya fuska daure kaman ance mamanshi ko babanshi ne wani ya rasu, Mum baya ta bude ma indo itama ta shiga tare da fadin aysha komai aka miki ki kirani ki fadamin kinji tana fadin haka ta rufe musu motar, driver yaja, indo kuka take kasa2, A Majeed wani irin takaici yake ji gashi baya son yin wani abu a gaban driver direct gidanshi Suka nufa, fita yayi ya shiga ciki da sauri, itama fita tayi ta dauko akwatin ta karami taja tai ciki, dakinta na gidan ta shiga, ruf da ciki tayi akan makeken gadon dakin tana kuka, tare da tunanin wani irin rayuwa za tayi a gidan A Majeed, karan wayanta ne yasa ta dan tsagaita kukan tare da dauka taga Mum ce ,shuru tayi tare da kara goge hawayen fuskanta ta dauki wayan mum tace aysha baiyi miki komai ba koh? Tace eh Mum, mum tace toh shikenan indai ya miki wani abu ki fadamin zan dauki matakin daya dace akai, tace toh Mum sannan sukai sallama.

STORY CONTINUES BELOW

Washe gari da safe indo ta tashi tayi wanka domin ta riga ta saba kullum sai tayi wanka  da safe da kuma yamma wanda Mum ce tasa take hakan harya zaman mata jiki, wata doguwar riga tasa ta kamata ta sama, dankwali ta daura ta nufi kitchen domin yunwa take ji, dan tasan inta zauna a daki yunwa ne zai kashe ta, kitchen ta shiga wanda a yanzu ta daina jin tsoro🤣 store ta bude taga babu komai, fridge ma haka babu komai sai drinks kala2, rufewa tayi tana tunanin mai zata yi domin dai yunwa take ji, sama ta koma ta dauko gyalenta tare da bude jakarta ta dauko kudi a cikin wanda Mum take bata in zata Skul, ta fita gate ta nufa taga security din gidan tace musu dan Allah a ina zan samu shago? Daya daka cikinsu yace ta kawo mai za’a siyo mata, tace a’a zata da kanta, nan ya kwatanta mata ta fita, shagon da nisa sosai, tafiya takeyi a kafa da yake anguwan masu hannu da shuni ne sai dai kaga mota jefi2 tazo ta wuce, wani katon shago ta gani nan taje ta siya indomie guda biyar da Egg guda goma sannan ta dawo gida, a falo ta ganshi hada ido sukayi, gabanta taji ya fadi domin Allah yasa mata tsoranshi bana wasa ba, tamke fuska yayi hanyar kitchen tayi, jin maganan shi tayi yana fadin daka gidan uban wa kika fito? Tsayawa tayi cak gabanta na dukan uku2, bata bashi amsa ba haka kuma bai kara yin magana ba, amma daka ganin alama yana jiran amsan nata ne, bata ga sanda ya tashi ba kawai taga mutum a gabanta tare da amsan ledan hannunta yana dubawa yaga ko miye, jefa mata yayi tare dayin tsaki yace wa yace ki fita? Tace naje siyo abunda zanci ne, wani kallo ya mata tare da fadin daka yau idan kika kara fita siyo wani abu sai nasa an ballamin ke, idiot yana fadin haka ya shige dakinshi yana jin haushin indo gaba daya ta zaman mishi matsala idan ya tuna matarshi ce wani irin takaici yake ji, yarinyar da batafi ayi rainonta ba wai ita aka aura mai, toilet ya shiga yayi wanka domin yaji baya son zaman garin gwara ya koma Abuja kawai, ita indo tunda ya tafi ta shiga kitchen ta dafa Indomie dinta a kitchen dinma ta zauna taci ta wanke komai, lokacin da zata fito ta ganshi yana jan akwati fuska daure yace kizo mu wuce, yana maganan ne kaman baya son yi, daki ta koma ta dauko kayanta a cikin akwati tare da feshe jikinta da turare sannan ta fito, a bakin gate ta ganshi yana ba security kudi yana murmushi, a zuciyarta tace dama yana dariya sai taga ya kara kyau, ajiyan zuciya tayi tare da nufa motar driver yasa mata kaya a boot ta bude baya ta shiga motar kamshi ga a.c a kunne, harya gama sallaman su ya nufo motar ya bude ya ganta a baya tsaki yaja tare da fadin tashi ki fitar min a nan ki koma gaba, bude motar tayi zata fita komai ya Tuna kuma oho yace dawo ki zauna, rufe kofan tayi tare da zama, shima ya shiga ya zauna driver yaja,gudu mota take ta shararawa a titi A Majeed fuska a daure yake ta lallatsa wayanshi, ita ko indo duk ta gaji ga sanyin AC din ya dameta yana so ya sata bacci gashi bata son yi, indo dai bacci ya dauketa ta wajan kofa tasa kanta, A Majeed ya waiga yana kallonta tare dayin tsaki ya juyar da kanshi gefe.

Sun shiga cikin dangareren gidanshi a lokacin indo ta farka, bayan driver yayi parking A Majeed ya fito, indo tana nan zaune tana tsoran fita tasha masifa, wucewa yayi ba tare daya kalleta ba, driver ne yace hjy ki fito an kawo, bude kofar tayi ta nufi inda taga A Majeed yayi, gidan ya hadu ga masu gadi kala2 wani katon falo ta ganta a ciki A Majeed ta gani da wata mata kyakyawa ta rungumeshi, indo ta danji wani iri ganin yanda tamai domin abun ya bata kunya, dan sakin shi Zainab tayi tare da fadin keee daka ina haka? A Majeed ya waiga yaga indo ce, yace oh swty tare muke, kallonshi tayi alaman ban gane ba, kaman ya fahimci hakan yace na kawo ta ne dan ta dinga min traditional food kinga basai na dinga zuwa jalingo sosai ba, Zainab tayi dan murmushi tare da fadin hakan yayi ta kuma kallon indo dake tsaye tana mamaki tabe baki tayi domin kwata2 taji indo bata mata ba, kai anya zan zauna da wannan a matsayin yar aiki kuwa No gskya ya kamata asan abunyi ba’a gida na bah…

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

STORY CONTINUES BELOW

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      100to105

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*HAFSAT MAMANI MMN JAWAHEER😍*

A Majeed ne ya katse mata tunani da swty a bata wajan zama, Zainab tace gskiya Baby ni bana sonta kawai ta koma inda ta fito sai a sami wata, A Majeed shuru yayi Kafin yaja hannun Zainab sukai ciki, komai ya ce mata oho sai gasu sun fito indo dai tana nan a tsaye takaici ya isheta, Zainab ta tabe baki tare da fadin na yarda zaki dinga min aiki So sai dai bana son kazanta sannan bana son sata dan ku yaran talakawan nan daka an baku dama sai ku fara yima mutum sata, duk ranan dana kamaki da wani abu nawa wanda ban baki ba saina kulleki harda iyayenki, Hope kinji abunda na fada indo da hawayen da take boyewa dan kar su zubo lokaci daya Suka zubo tare da fadin naji, Zainab tace good, kiran wata tayi a cikin masu aikinta tace a kai indo dakinsu, A Majeed yana zaune bai tanka ba, indo wani irin tsananshi taji tana yi, ta tabbata baya sonta kaman yanda yake fada, shikenan dai talaka a wulakance ake kallonshi koda yaushe, mai kudi yana ganin kanshi kaman wani Sarki, jiba yanda take gayamin magana kaman zata cinyeni danya, tabbas koma miye A Majeed yaja min tunda baya son auren mai zai sa bazai sakeni ba, in sami dai2 ni in aura, wani hawayen ne ya kuma gangaro mata, a dai2 lokacin Suka karasa dakin da za’a kaita, dakin babba ne akwai katifa guda uku manya, sai TV dake manne a jikin bango da AC, matar tace ma indo ga gadon ki nan, indo tace toh tare da ajiye kayanta akan katifa din dakin, matar tace zaki fara aiki idan madam ta fadi abunda zaki dinga yi, indo tace toh sannan matar ta fita, tana fita indo ta saki kuka tare da fadin ta tabbata inda sulaiman ta aura da bazai mata haka ba duk da tasan shima yafi karfinta nesa ba kusa ba, karan wayanta taji dauka tayi taga Mum ce, ta dauka da fadin barka da Gida Mum? Mum tayi murmushi daka gefenta tace aysha kina lafiya koh,? Tace lfya Mum, Mum tace ya naji kaman kinyi kuka ko ma dai ince kina kuka? Tace ba kuka nakeyi ba mum mura ne ya kamani, Mum tayi ajiyar zuciya daka gefenta tace ya dai sai miki Magani koh? Tace eh, Mum tayi dan murmushi tare da fadin nakira inyi miki ya hanya ne tunda tafiya babu sallama, kiyi ta hakuri da abokiyar zaman ki Dashi kanshi mijin naki sannan ki dage da addu’a komai zai wuce, indo tace ngd Mum, Mum taci gaba da fadin zan mishi magana a duba miki islamiya a nan kafin ki fara zuwa skul din nayi magana dasu akan a baki transfer sunce sai nan da sati biyu, indo taji dadi sosai tunda zata ci gaba da karatu koba komai zata dinga dibe ma kanta kewa domin harga Allah bata son zama gidan nan tunda taga irin tarban data samu da kaskantar da ita din da akayi koh da yake dama ita tunda talaka ce ai a hakan za’a kalleta, Mum ce ta katseta da fadin dan Allah komai ya miki ki fadamin kinji karki boyemin komai, ke bama shi ba ko matarsa ce ta miki wani abu ki fadamin indo tace toh Mum sannan sukai sallama, indo tace Allah Sarki Mum ita bata da wulakanci irin na masu kudi koh dai dan ita ba yar kasar bace oho, kai shima haka dad din A Majeed din yana da kirki, toh a ina dansu ya koyo irin wannan halin? Domin dai iyayenshi mutanan arziki ne, ko da yake shima yana da kirki dan taga yanda yake da masu aikin shi, toh ko dai nice daya tsana bayamin kirki,tabbas hakane haka taita tunanin ta har aka Kawo Mata abinci taci tayi sallah.

Zainab tunda taga indo taji ta tsaneta ita da kanta ta rasa dalili sai dai tana ganin ko dan tana da kyau ne yasa bata sonta dan ta lura da indo tana da kyau na Bala’i sai dai kyan nata bai gama fitowa ba dan taga kaman bata wani waye sosai ba, idan yarinyar ta kile tabbas babu namijin da zai ganta bai so ya aureta ba, wannan abun yake damun zainab dan koda indo ta wuce dakin masu aiki, zainab ta dire akan sai an kori indo A Majeed ya dinga rarrashinta akan tayi hakuri Mum ce ta bashi ita akan ta dinga musu aikin girki, kuma dakyar Mum ta bashi ita dan yace yana son irin abincin ta, wata sabuwa jin yace Mum ta bada indo yasa ta kara tsanan indo din, tare da burin safiya tayi ta fara horata ta yanda ba zata sami lokacin kanta ba balle har ta daukan mata hankalin miji kaman yanda take tsoro.

STORY CONTINUES BELOW

Washe Gari tun wajan 8 A Majeed ya tafi office, Zainab tasa aka kira mata indo, bayan indo tazo ta gaida zainab, bata amsa ba sai fadin da tayi miye sunanki? Indo tace aysha, tabe baki tayi sannan ta kalli indo din tace daka yau ke zaki dinga wanke2 kina mopping din ko ina sannan ban yarda a dinga shigo min falo da sunan mopping ba in mijina yana nan ba, da sassafe zaki dinga yi Kafin ya fito, dan ni bazan iya cin abincinki ba dan baki kai wannan matsayin ba, ina fatan kin fahimta indo tace eh,. Tun daka wannan ranan indo ta fara aiki ga gidan kato haka take goge ko ina in Zainab taso yin rashin mutunci tace bai goguba, haka zata sa ta kara gogewa, ganin kaman aikin baya damun indo yasa zainab tace ita zata dinga yima masu aikin gidan abinci indo tace toh haka kullum inta tashi da asuba zata fara aiki bata samun hutu sai dare domin daka ta tashi zata daura ma masu aikin gidan abinci tayi shara da goge2 inta gama tayi wanke2 sannan abincin rana, inta gama na rana saina dare, duk da abun yana damun indo bata taba gaya ma mum ba duk kuwa da yawan tambayanta da takeyi, indo tana samu taci ta koshi kuma tana kara girma da kyau Zainab har mamaki takeyi ganin kaman indo bata damuwa da aikin da takeyi sai dai yanzu ta dan fara raga ma indo din domin ganin kaman A Majeed din ya tsani indo din.

Mum ta kira A Majeed akan maganan makaranta indo tace ana abuja akwai islamiya So zata dinga zuwa tun safe sai 6, yace OK zaisa a kaita, koda yama Zainab magana tace ita sam bata yarda ba, sai dai indo ta zaba aiki ko karatu babu yanda baiyi da Zainab ba amma taki yarda, ganin haka shima ya share maganan dan baya son gimbiyar tashi tayi wani tunani akai, yau wajan watan indo daya a abuja da sati biyu, har yanzu bata zuwa skul abun na damunta duk ta rame saboda tunani, yau Zainab zata bar kasar domin zata raka Mum dinta Canada, tunanin yanda zata bar indo a gidan take ita ta rasa dalilin da yasa bata son indo ta zauna waje daya da mijinta, kiran A Majeed tayi a waya akan zata kai indo Skul din,yaji dadin hakan sosai nan ya fada mata inda skul din yake, tare da ce mata inta je ta fada musu itace akama transfer daka jalingo hakan ko akayi bayan driver ya kaisu basu bata lokaci ba aka gama komai indo a can aka barta abun dadi ma babu wani nisa daka skul din da Gida, amma akwai dan tafiya kadan, ita Zainab tana ganin indo zata wuni bata Gida inta dawo kuma sai bacci da wannan tunanin yasa ta kai Indo skul din ,itako indo farin ciki takeyi sosai, Zainab anyi tafiya an bar kasan kuma a kalla za tayi sati biyu ko uku, indo ta dage da karatu sosai ga girki da take koya shima, islamiya ma suna karatu sosai daka ta dawo gidan in tayi wanke2 taci abinci sai bacci da safe kuma tayi shara da mopping ta wuce skul yanzu bata girki sai wanke2 da shara, yau indo ta fito tana shara wanda falon ma babu wani datti amma kullum sai an share an goge, A Majeed ne ya fito daka gani abu yake son dubawa, kallo daya yama indo ya kauda kai ita kam bata daina sharan ba dan tana sauri tayi ta gama kar tayi lati, sai dube2 yakeyi a kasa ya hango wata takarda da sauri ya nufi wajan dauka yayi ya bude cikin fushi ya karasa inda indo take da karfi ya jata tare da wanka mata mari mai dan karan zafi har sai da taga Star yace ke wace irin mahaukaciya ce kin san takardan miye wannan da zaki share? Yanzu inda ban fito ba dakin share kina aiki kaman mahaukaciya bakya duba abu, cikin kuka tace kayi hakuri a kasa na gani ban……  Enough ya katseta tare da fadin fitar min daka nan idiot, zama yayi a falon yana huci kai wai mai yasa Mum ta aura mishi wannan abun ne gskya ya kamata indau mataki akai, tashi yayi ya nufi dakin masu aiki amma babu kowa a ciki dan tsaki yaja tare da komawa falonshi yana tunanin ina taje, indo koda ta fita daka falon skul ta wuce dan dama ta gama komai falon ne kawai ya rage, tana kuka har ta nufi skul babu kowa sai ita daya dan 8 suke Zuwa yanzu kuma 7 , tana nan zaune har aka fara zuwa, tun daka wannan lokacin Indo bata kara bari sun hadu da A Majeed ba duk kuwa Dashi yana son ganinta domin ya gaji da zama da takeyi a matsayin matarshi,  satin zainab biyu ta dawo Nigeria A Majeed yana falo sai gata ta shigo cikin fushi ko kallonshi ba tayi ba ta nufi dakin indo ta janyota  har suka karaso falo, ta jefar da indo ta kalli A Majeed tace dagaske wannan jakar matarka ce?…….. Muje zuwa

STORY CONTINUES BELOW

Taku maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      105to110

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*HASSAN ATK🤝*

A Majeed da sauri ya tashi tare da fadin god forbid taya zata zama matata? Zainab tayi wani irin dariya tare da fadin ok tunda ba matarka bace yau zata bar gidan nan tunda bana ubanta bane, daga kafada yayi kalan I don’t care dinnan,ganin haka yasa zainab ta fara janta har riganta ya yage daka sama, ganin riganta ya yage yasa ta fara kokarin ta yaga mata shi duka indo babu abunda takeyi sai kuka tare da tsanan A Majeed da Zainab tabbas koda yau bata ce tabar gidannan ba toh ta barshi kenan har abada, A Majeed ganin ta yaga mata riga kirjinta duk a bude idonshi ya sauka a kai nufansu yayi tare da rike zainab din yana fadin swty what are you doing? Mai kike shirin yi haka? Ta fara kokarin kwatan jikinta daka nashi tana fadin wlh yau saina kashe ta kaima zan dawo kanka, riketa yayi da karfi yana fadin na fada miki ba matata bace, dai2 lokacin Mum ta shigo gidan tace tabbas ba matarka bace, nufa wajan indo tayi da take durkushe tana kuka, Mum ta daga ta tare da fadin muje kisa kaya, dakin da indo take nan suka nufa, Mum takaici duk ya cikata wato yar aiki suka maida aysha, lallai A Majeed ka nunama duniya bamu isa dakai ba, ita ta taya Indo hada kaya domin tace bazata kara kwana a gidan ba, Mum da indo suka fito Mum itace ke jan akwatin indo din, A Majeed da sauri ya nufeta yana son amsan akwatin mari Mum ta sakar mai tare da fadin nagode da abunda ka aikata dama tun tuni jikina ya bani akwai abunda ke faruwa duk da Aysha Tana boyemin tace komai lafiya, sai yasa nayi zuwan ba zata, Ashe abunda zan gani kenan, ta kalli Zainab da take muzurai kaman zaki najin yunwa tace bari kiji in fada miki abunda kike son ki tabbatar, aysha matar abdul-majeed ce, amma daka yau ba matarshi bace, ta Kalli A Majeed tace ka rubuta min takardan aysha kuma saki uku nake So yanzu ka ban, Zainab da sauri tabar wajan jim kadan sai gata da takarda da biro tana mikama A Majeed, bai amsa ba bai kuma yi mata magana ba, illa Mum ce data karaso wajan ta amsa takardan cikin takaici ta mika mai, amsa yayi ga mamakin Mum sai gashi ya fara rubutu, harya gama ya mika ma Mum tare da fadin Mum kiyi hakuri naso in zauna da ita amma na kasa sata a raina domin bata cikin tsarin macen da nake so….  Mum jan hannun indo tayi wacce take ta faman kuka suka fita mota Suka shiga driver yaja, gidan su na abuja suka nufa, Mum Tana shiga ta zaunar da indo ta fara mata nasiha akan tayi hakuri haka Allah ya tsara mata, sannan tana rokan indo akan taci gaba da zama da ita karta ce zata barsu, indo ta kasa magana sai kuka mum ta janyota jikinta ta rungumeta itama tana hawaye, dakyar ta samu ta rarrashi indo tayi shuru, ranan zazzabi ne ya kama indo sosai Mum ta tsorata dan haka suka nufi hspt Dr yace damuwa ne ya mata yawa tana bukatan hutu, nan ya bata Magani sannan suka dawo, washe Gari suka dawo jalingo, Mum ta fadama his excellency abunda ya faru tun a waya ranshi yayi mugun baci, koda su Mum suka dawo yace ta bashi takardan amsa yayi ya Fara karantawa kaman haka *NA SAKI AYSHA SAKI DAYA MUM KIYI HAKURI BAN TABA SON AYSHA BA, BANA SON FUSHIN ALLAH A KAINA DAN ALLAH MUM KI GAFARCI DANKI* his excellency bayan ya gama karantawa yace Allah yasa haka shine alkhairi yace Mum ta kira mishi aysha din, Mum ta tashi ta kirata bayan tazo his excellency yace aysha naji abunda ya faru da farko dai zan baki hakuri akan abunda ya faru sannan in nemi alfarmanki akan ki zauna damu har Allah ya fito miki da wani mijin, tace insha Allah sannan ban rike komai a raina ba komai ya wuce, his excellency yaji dadi sosai yana ta sa mata albarka, tare da fadin zai zamo mata uba ta dauka tana tare da iyayenta, taji dadi sosai,  bayan indo ta fita Mum tace akira A Majeed ya karasa ma indo sauran sakin, his excellency yace babu kyau saki uku duk da daya yayi mata bana ma tunanin zai dawo da ita tunda ya tsaneta kawai ki barshi .

STORY CONTINUES BELOW

A kwana a tashi babu wuya indo ta gama idda, kuma tana zuwa makaranta ta kara kyau da girma sosai komai nata ya fito domin Mum Tana tsaye a kanta wajan gyarata da bata abubuwa masu gina jiki, farin indo na asali ya fito har wani sheki takeyi dan haske, gashi babu laifi tana jin turanci yanzu dan bada wasa take karatun ba, tun Mum da Dad na fishi da dan nasu har suka hakura sai dai tun daka ranan daya rabu da indo bai kuma ganinta ba, sai dai abun yana dan damunshi dan bazai taba manta sanda yaga kirjinta a waje ba har yanzu abun na idonshi ya kasa mantawa duk da kuwa lokacin ana cikin tashin hankali, Abdul yaji abunda A Majeed yayi ya kira indo ya bata hakuri sannan yayi fushi da abokin nashi sosai.

Wasa2 dai indo an kammala karatu anyi waec ta sami 8 credit, nan Mum ta fara mata  kokarin fita zuwa Egypt Alhmdlh indo ta sami gurbin karatu a kasar masar wato Egypt inda ta sami medicine duk da indo taso ta karanci political science amma bashi aka bata ba, tare da Mum indo aka daga zuwa kasar misra, wai indo a jirgi first time in history😂 abun mamaki kuma batai kauyanci ba, kodan yanzu an waye ne oho, amma fah ta dan tsorata kawai ta dake ne irin ita Big girl din nan😁 koda suka sauka a kasar Egypt driver yazo ya daukesu nan iyayen Mum sukai ta murnan ganin yar tasu kaman zasu cinyeta dan murna, ummi tana ta jan indo jikinta domin taji tana son indo, haka shima baban ummi din da Mum ke kira da abba, nan sukaci Suka sha, ummi da turanci take ma indo magana dan bata jin larabci, kwanansu biyar suna yawo a Gari kafin Mum ta fara ma indo kuciba2 harta gama mata komai harda islamiya aka saman mata, washe gari driver din su ummi yakai indo ta fara lecture, haka idan ta fito zaizo ya dauketa in zata islamiya ma haka, indo an fara sabuwar rayuwa  watan mum daya ta dawo Nigeria, Indo karatu take sosai babu laifi tana ganewa, tayi wata kawa balarabiya mai suna fatima suna shiri sosai indo tana dan jin larabci kadan2 duk da yawanci maganan da turanci sukeyi danko a islamiya ana hada musu da turanci, suna Waya da abdul jefi2.

A Majeed gaba daya ya kasa gane Zainab domin tunda indo tabar gidan rabon da wani abu ya shiga tsakaninshi da Zainab dan tace hala ma wai ya hada jiki da indo din karya shafa mata cuta, wai sai anje anyi gwaji, ganin yana cutuwa yasa ya yarda akayi duk da yana ta rantse mata babu abunda ya faru shida indo din amma taki yarda anyi test bashi da wani cuta, ta dan sakar mai amma ba sosai ba, gashi yanzu ta karo wulakanci sai tabar kasar tayi wajan wata daya bata nan, gashi idan ya mata magana ta inda take shiga ba tanan take fita ba, wata rana tayi tafiya watan ta daya da sati daya tunda ta tafi sau biyu sukai waya shima daka ta dauka sai tace tana aiki zata kirashi idan yaji shuru saiya kirata taki dauka, daka baya ma yaji wayanta a kashe, koda ta dawo ya mata magana wai ita fah Karya takura mata ta fara business ne, ranan hakurin A Majeed ya kare yace mata nifa mijinki ne ina da hakki akanki kin maidani kaman wani hoto, nifa mutum ne ba dutse ba, ina da Sha’awa,tabe baki tayi tare da fadin to ni mai ya dameni da Sha’awan ka? Idan kaji abun ya dameka basai kasha Magani ba, ranshi ya kuma baci yace tunda haka kikace ki sani bana zina kuma ba zaki sa in fara ba ina da bukatar Mace dan haka zan kara aure, wani uban ashar ta saki tare da fadin wlh baka isa ba, karka manta wacece ni, bari in fada maka wacece Zainab yar president babana ne na daya a kasar nan banga wata wacce zan iya kishi da itaba a cikin kasar nan ko wacce iyayenka sukai gigin hadaka da ita fita tayi ta barni, danma ranan mamanka ce ta kwace ta da tayi rayuwa a prison ita da iyayenta yanda babu mai kuma yimin shishigi, ina da kudi ina da ikon da zan hanaka auren ko wace Mace dan haka ka cire wannan abun a ranka ni Zainab ni daya ce matarka a cikin duniyan nan so you have to be very careful akan abunda zaka dinga fada,tana gama fadin haka ta wuce ta barshi zama yayi yana mamaki dama haka Zainab take? Sai yau ya gano abunda Mum take nuna mai lallai yaba Zainab dama da yawa, tunawa da indo yayi nan take yaji nadaman abunda yayi mata lallai wayewa da yawa Bala’i ne, yau yaga illan wayewa wanda gashi matarshi tana nuna kaman itace keda iko Dashi, tuna kalaman abdul yayi da yake cemai yafi son ya auri yar talaka wacce ko mai ya mata zatai godiya ta amsa hannu bibbiyu baya son macen data waye sosai, nan take ya Tuna da maganan Mum da take fadin na maka gata son amma ba zaka gane ba sai nan gaba,.hmmm muje zuwa

STORY CONTINUES BELOW

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      110to115

*DEDICATED THIS PAGE TO….*

*AYSHA BAGUDO INA YINKI IRIN TOTALLY DINNAN😍*

A Majeed ya dauki lokaci mai tsawo a zaune, tare da tunanin abubuwan da suka faru a baya, Zainab kam tana shiga daki toilet ta fada tayi wanka ta fito ta shirya cikin riga da wando tayi kyau sosai, zama tayi a dakinta Kana ganinta kasan ranta a bace yake tabbas in bata tashi tsaye ba A Majeed yana son ya nuna mata wuyanshi yayi kauri, dan murmushi tayi lallai wannan karan idan da gaske yake muddin ya kara aure sai tasa yayi dana sani, domin tana son mijinta kuma ita daya zata zauna Dashi, har yau tana ganin auren indo da aka bashi a matsayin an mata wulakanci a rasa wacce za’a bashi sai yar matsiyata har yanzu bawai ta kyale indo bane inda zata ganta koh tasan inda take dasai ta koya mata babban darasi yanda babu wata Mace da zatai gigin auran mata miji nan gaba, amma koh yanzu bata baci ba tana jira taga wace mace zai Kawo a matsayin mata inma dagaske yakeyi haka itama taita tunani.

Zabe yazo anyi zabe his excellency yaci zaben senator yanzu su Mum sun dawo abuja da zama, sannan mahaifin Zainab ya kara cin mukamin shi na president domin mutumin kirki ne mai tausayin talakawa, Zainab an kara fasowa gari tare da karo wani sabon wulakanci, yau tana can gobe tana can A Majeed tun yana magana har ya daina yasa mata ido, sai dai abu daya dake damunshi yanda zaiga indo ya bata hakuri akan abunda yai mata dan akwai sanda yaje wajan mum yana bata hakuri akan ta yafe mishi tace ta yafe mai duniya da lahira, yaji dadi sosai yai shuru na wani lokaci sannan yace Mum dan Allah ina zanga aysha?mum tamke fuska tayi tare da fadin ban sani ba, kamo hannun mum yayi tare da fadin Mum plz,mum tace ni bamma gane aysha da kake nufi ba, dan shuru yayi domin yasan Mum ta gane kawai dai so take taji daka bakinshi dakyau, yace Mum matar da kika aura min, Mum tace ban san inda take ba yanzu, may be ma tayi aure jin kalman tayi aure abun ya dan taba shi domin a yanzu yana ji zai iya zama da indo ko dan faranta ma mum da kuma irin hakurin yarinyar tashi yayi ya fita jiki a sanyaye Mum ta bishi da kallo tare da fadin Ai aysha yanzu tafi karfinka kaje ka karata da matarka wacce ta waye

BAYAN SHEKARA HUDU

wata doguwar yarinya na gani a tsaye da wani akwati kusa da ita, tasa jallabiya black ta yane fuskanta da gyalen jallabiyan ga glass tasa a fuskanta kallo daya zaka mata kace balarabiya domin irin farinta da kyanta kaman nasu, doguwa ce amma ba sosai ba, ga kirjinta a cike, duk da jallabiyan da tasa bai kamata ba kana kallonta kasan tana da diri mai kyau, gani nayi anyi hugging dinta Mum ce sai yanzu na gane Ashe indo ce😱 cikin jin dadi aysha ta kara rungume Mum, Mum tace aysha barka da dawowa nan driver ya amshi kayan aysha ya tafi Dashi, Mum na rike da aysha kaman wata jaririya suka nufi mota, motoci har biyar akazo daukan aysha indo, direct gidansu Mum suka nufa dake abuja, bayan Sun karasa cikin makeken gidan su, nan sukai ciki Mum takai indo dakinta, indo taji dadi sosai domin ganin wannan ne dakinta an kayata mata shi, komai Pink, harta Cotton din da bed din, dakin yayi kyau sosai Mum fita tayi dan tabar indo ta kimtsa toilet ta fada tayi wanka, tasa wata doguwar riga mai kyan gaske, ta feshe jikinta da turare bata shafa mai ba, ta daura dankwali ta nufi falo inda abinci ke jiranta a dinning, zama tayi Mum tayi saving dinta, indo ta faracin abinci cikin natsuwa da kwarewa, Mum sai kallonta take tana mamakin irin kyan data kara da girma, har indo ta gama nan suka fara fira da Mum, suna cikin haka sai ga Abdul yazo indo ta dan bata fuska, Abdul ya gaida Mum ta amsa cikin Fara’a, sannan ya kalli indo yana murmushi tare da fadin aimin afuwa plz naso inzo in daukeki aka kirani emergency daka office, indo cikin hausanta wanda zaka tadauka tana larabci ne tace aini yaya abdul nayi fushi dakai ka barni a airport inata jira, yace sorry my sister, dan turo baki tayi irin na shagwaba wanda ita bada hakan tayi ba, dariya Suka Saki su duka harda Mum, abdul ido ya kura mata yana ta kallonta yana mamakin irin kyan data kara da girma wanda shi tun asali yana ganin kyanta, ga wani irin wayewa da tayi, gashi magana daya biyu sai tasa turanci da larabci hausan ma kaman bata wani iya sosai ba, haka sukai ta fira har abdul ya tashi yayi musu sallama indo tashi tayi tabi bayanshi domin tana son suyi magana, bayan Sun fita tace yayana wai ya maganan auren naka? Yace hmm ki bari kawai akwai dan matsala ne amma inaga komai ya kusa zuwa karshe, indo tace wani irin matsala kuma? Nan ya fara fada mata yarinyar kaman wacce take rikonta ba yarta bace so kaman bata so yarinyar tayi aure tafi son taita mata bauta, indo shuru tayi tana nazari lallai mata da yawa za suci wuta, dan tuna rayuwanta tayi a baya da yanda yanzu ta sami canji duk saboda Abdul lallai ya kamata itama ta taimaka mishi, nan dai tace bari idan ta dan kwana biyu ta huta za suyi shawara akai, motar A Majeed ne ya shigo cikin gidan, indo kallo daya tamai ta gane shi, dakanshi yake tukin, kawar da kanta tayi taci gaba dayi ma Abdul magana, A Majeed da Tun shigowanshi ya ganta gabanshi yaji ya fadi tare da fadin tsarki ya tabbata ga Allah domin bai gane indo bace dan tayi mugun canzawa, danshi a tunanin shi wata daka cikin yan uwan Mum dinshi ne, bayan yayi parking ya fito ganin yana nufo su yasa indo tayi ma Abdul sallama ta wuce, A Majeed da ido ya bita yana tunanin inda ya santa, Abdul ne ya katse mai tunani da fadin yanzu wajanka nake son zuwa, A Majeed yayi ajiyan zuciya tare da fadin ya akayi Abdul yace maganan zuwa Kaduna, A Majeed yace kai har yanzu kana nan da wannan yarinyar duk da iyayenta sunce sun mata miji, Abdul yace wlh basu mata miji ba kawai dai uwar rikonta ne keda matsala, nan suka tautauna amma gaba daya hankalin A Majeed yana ga yarinyar data shiga yanzu dan haka yace ma Abdul su shirya suje Friday sannan ya shige ciki, koda ya shiga Mum kawai ya gani a falo, bayan sun gaisa ya dan sosa kai tare da fadin Mum kinyi bakuwa ne? Mum tace wace bakuwa kuma? Dan shuru yayi can yace wacce ta Shigo yanzu kaman yar kasar ku ce dai, Mum tayi murmushi tare da fadin au kodai aysha kake nufi, cikin razana ya furta aysha tabbas itace dan yanda yake tunanin a ina ya santa sai yanzu yaga kamannin sak…..

STORY CONTINUES BELOW

Taku Maryam obam*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      110to115

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

A Majeed gaba daya ya shiga cikin rudani tare dayin daya sani, tunawa yayi da Mum ta taba gaya mishi hala ma tayi aure, hada hannunshi yayi ya buga da karfi, Mum ta kalleshi tace lfya kuwa, idonshi lokaci daya ya kada yayi ja wani irin zafi yake ji kirjinshi nayi, Mum ganin halin daya shiga yasa ta tashi da sauri ta nufo shi tana fadin maike damunka? Dakyar ya furta babu komai Mum kawai kirjina ke ciwo, tashi yayi ya fita Mum ta bishi da kallo yana fita abdul ya kira yace Abdul kana ina ne? Abdul yace ina Gida, kashe wayan yayi ya shiga motarshi ya nufi gidan abdul, bayan Mai gadi ya bude mai gate yayi parking, kai tsaye falon gidan ya shiga abdul na falo yana cin abinci cikin take away, A Majeed zama yayi akan kujera tare da lumshe ido abdul da ido ya bishi bai dai ce mishi komai ba, A Majeed yayi wajan minti biyar kafin yace abdul aysha tayi aure ne? Abdul yace wace aysha kuma? A Majeed yace matata mana, abdul yace toh kai ina ruwanka da ko tayi aure koh batayi ba, A Majeed yace plz ka bani amsan tambaya na kawai, dakyar Abdul ya fada mai cewa batai aure ba, A Majeed wani irin ajiyan zuciya yayi cikin jin dadi domin yasan komai zai zo mishi da sauki tunda batai aure ba, abdul ne ya katseshi da fadin A Majeed mai yasa amma kake son sanin hakan, dan murmushi yayi tare da fadin saboda ina son in dawo da matata mana, abdul yace amma dai wasa kakeyi koh? A Majeed yace wasa fah kace, toh inma wasa kake gani toh ka daina dauka hakan, abdul yace inda zan baka shawara kar kayi gigin furta wannan maganan domin aysha ba ajinka bace ko ka Manta ne, itafa yar aikin matarka ce, ganin abdul na son bata mai rai yasa yabar gidan cikin fushi, Abdul ya girgiza kai tare da fadin Allah ya ganar dakai abokina.

Indo suna falo suna breakfast harda dady, duk da tana jin kunyan dady amma yana janta a jiki kaman yarshi domin yana tausayama yarinyar, dady yace aysha yaushe za’a fara aiki ne? Kallon Mum tayi alaman tayi magana, Mum tace babu abunda zance gwara ki fada dariya sukasa, indo ganin Mum taki cewa wani abu, yasa tace dady koda yaushe a shirye nake, yace toh Alhmdlh na bada komai naki dama Office dinki na jiranki, indo tayi godiya, dady yayi gyaran murya tare da fadin aysha ya kamata ki shirya kije kiga Gida ki gaidasu koda kwana biyu kiyi musu, Mum tace hakane ya kamata taje taga yan uwanta nima abun yana raina, indo ji tayi kaman an soka mata wani mashi, bata kaunar zuwa garinsu abubuwan da Suka faru suka fara dawo mata, har yau sulaiman na ranta sai dai kuma tana son taji ko anji labarin yusuf, wannan tunanin yasa taji tana son zuwa, nan sukai ta dan fira, A Majeed ne ya shigo gidan idanshi nakan indo daure fuska tayi ganin ita yake kallo, Dad ya tashi tare da fadin zani majalisa yau akwai zama sai na dawo aysha ki shirya Monday sai ki fara zuwa office, A Majeed Dam yaji gabanshi ya fadi domin baya son ta fara aiki kar a mishi kwace amma yasan yanda zaiyi, bayan Sun gaisa da Dad din nashi ya wuce, zama yayi akan dinning din shima ya fara cin abinci, wayan indo ne yayi kara dauka tayi tare da fadin ina nan ina zani, dan murmushi tayi tare da fadin haba fatima ai Nigeria yafi dadi ina tare da Mum dina duk da larabci tale maganan wani kuma da turanci, A Majeed ido ya kura mata yana kallon ta yana mamaki, harta gama wayan, tashi tayi tabar wajan ido A Majeed ya bita Dashi yana mamakin irin yanda ta canza, wayan Mum ne yai kara ta dauka tare da fadin an Kawo ne?ban san mai akace mata ba tace gani nan zuwa, tashi tayi ta nufi dakinta jim kadan sai gata ta fito da Gyale ta kalli A Majeed bari inje in dawo yanzu bazan dade ba, yace ok Mum, bayan fitan Mum indo jin karan kaman an rufe Gate ta dauka A Majeed ne ya fita dan haka ta fito falon, tana sauka ta ganshi wani iri taji kaman ta juya sai taga hakan bai dace ba dan zai dauka ta damu dashi ne, mai makon ta zauna a falon saita nufi kofar fita wajan bukka taje da yake yana bayan gidan, dan kwanciya tayi akan kujera mai kaman lilo tana danna wayanta, jin kaman ana kallonta yasa ta tashi ta zauna ido suka hada kauda kanta tayi taci gaba da danna wayanta, zama yayi kusa da ita, kamshin turaren shi ya bugi hancinta, Tana so ta tashi tana gudun bashi dama domin idan yaga ta tashi haka zai dinga mata, daure fuska tayi, kiran sunanta yayi cikin wani irin murya kirjinta taji yana bugawa da karfi, aysha nasan nayi miki kuskure a…….  Tashi tayi tabar wajan da sauri, A Majeed gaba daya jikinshi yayi sanyi wani irin sonta yaji yana kara shiganshi, itako dakinta ta shiga tasa kuka tare da Tuna abunda matarshi Dashi kanshi sukai mata wani irin tsanarshi taji yana shiganta jin an bude kofan dakin yasa ta rufe ido kaman mai bacci Mum ce ta shigo dakin domin ta dawo bata ga A Majeed ba, tana so taji ko ya tafi ne, ganin Indo tana bacci yasa ta koma tare da fadin toh ina ya nufa dan taga motarshi, ko data gidansu ya fita oho, shiko A Majeed kasa tashi yayi yana tunanin yanda zai shawo kan indo ya dauki lokaci mai tsawo a wajan Kafin ya fito yaja motarshi ya tafi,gida ya koma a falo yaga zainab ita da wata kawarta ko kallansu baiyi ba ya wuce Zainab tabe baki tayi kawarta dai bata ce komai ba sai kallon yanda Zainab take wani tabe baki takeyi ita kawar tana fadin inda ita take da wannan Guy din da anga luv, kawar tashi tayi tare dayi mata sallama ta wuce, Zainab daki ta wuce inda taga A Majeed zaune yana danna laptop tace wai A Majeed mai kake nufi kwana biyu kana ta wani shan kamshi, bai kulata ba yaci gaba dayin abunda yakeyi, ganin ya maidata Sauna yasa ta kwace laptop din ta jefar tace ni nafi karfin in dinga maka magana kana kyaleni, kana mantawa da ko wacece Zainab, dan murmushi yayi tare da fadin bani da time dinki fita yazo zaiyi ta tare mai hanya tare da fadin babu inda zaka sai da yarda na, shuru ya mata ba tare daya kuma cewa komai ba, ganin kaman rigiman take so yasa ya barta ya koma ya kwanta tana ta surutai tunani yake tayi very soon zanyi maganin ki kwata2 duk ta fitan mai a rai duk yanda yake sonta….V

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      120to125

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Plz nayi mistake a page 115to120 sai nasa 110to115  ayi hakuri plz, yanzu sai a fara daka page 120to125

Zaune take a wajan bukka tana danna wayanta, daka gani tana jin dadin wajan, dan tsaki tayi tare da ajiye wayan ta kwanta akan kujeran lilo din dake wajan ido ta lumshe kaman mai bacci amma idonta biyu,ba komai take tunani ba illa halin da Abdul yake ciki, tare da tunanin ta yanda zata bi ta taimakeshi, domin Abdul yana daya daka mutanan da suka taimaketa wani irin zafi taji ranta na mata tuna irin wahalan da tasha da wanda bata fata koda makiyinta ne ya fada irinshi, kamshin turaren da taji yasa tasan A Majeed yazo wajan domin irin kamshin turaren shi taji, bata motsa ba balle ta bude ido, tayi wajan minti uku tana shakan kamshin ba tare data motsa ba, A Majeed wanda tun zuwanshi ya kafa mata ido yana kallonta yanda take kwance idonta a lumshe, wani irin yanayi yaji yana shiga mai wuyan misaltuwa, ganin idan yaci gaba da kallon nata zai iya shiga wani hali yasa yabar wajan cikin wani yana yi, tafiya yake amma kaman bayayi dan tafiya yake a hankali dan gaba daya jikinshi ya mutu, baiko shiga Gida wajan Mum ba yabar gidan, jin ta dade a haka kuma bata daina jin kamshin turaren ba, yasa ta bude ido amma bata ganshi ba, mamaki ta fara toh ina yake, kodai bashi bane yazo? Amma kuma kamshin shi naji, dan shuru tayi na wani lokaci can tayi tsaki tare da fadin koma dai shine ba damuwa na bane, jin kamshin turaren kaman yana kara mata yawa yasa tabar wajan dan bata son duk wani abu daya dan ganceshi, koda ta shiga ciki bata ganshi ba abun ya daure mata kai tare da tunanin mai yasa toh take tajin kamshin shi, tabe baki tayi alaman bai daman ba.

Mum da indo suna zaune suna fira,mum tace jibi dai za’a fara zuwa office, indo dariya tayi tare da fadin harna kosa in fara Mum na gaji da zama waje daya babu wanda na sani balle inje ziyara, Mum tace ai nima dai zaman naki Gida baya min dadi gwara ki fara aikin ko a can kya samo min siriki na, dai2 lokacin A Majeed ya shigo wanda yaji abunda Mum ta fada fuska tamke ya zauna bayan yayi sallama ciki2 mum ce kawai ta amsa amma ita indo cikin ranta ta amsa, wayanshi yake ta dannawa tunda ya gaida Mum bai kuma cewa komai ba, amma gaba daya hankalinshi na wajan Indo, Mum tace ya kamata kije kiyi shopping abubuwan da zaki bukata Dan nasan masu aiki suna bukatan kayan makeup dasu Turare sabo da shiga cikin al’umma, A Majeed Wanda tunda ya shigo baice musu komai ba sai yazu yace haba Mum miye nayin wani makeup dan mutum zai shiga Al’umma, gwara mutum ya zauna yanda Allah yayi shi bawai yaita ma fuska fenti ba sai mutum ya koma kaman aljani, yana fadin haka yai shiru tare daci gaba da danna wayanshi kaman bashi yayi wannan dogon zancen ba, Mum dan murmushi tayi tare da fadin ai kowa da irin choice dinshi naga wasu masu yin shafe2 din suke So dan sune suke ganin Sun waye, shuru yayi bai kuma cewa komai ba domin yasan Mum magana ta fada mishi, indo da tunda ya shigo falon take a takure tashi tayi tare da fadin Mum bari yau in shiga kitchen, Mum murmushi tayi cikin jin dadi tare da fadin kice yau za muyi dinner da abincin larabawa, dariya tayi wanda saida dimple dinta ya lotsa A Majeed wani irin sonta yake ji yana fisganshi ganin ta shige kitchen duk sai yaji ya takura da zaman, dan tsaki yayi wanda bai san ya fito ba, Mum ce ta daga kai ta kalleshi tare da fadin kai kuma lfya kuwa, yace lfya fuska a tamke irin na shifa asan abunyi Dashi, Mum tashi tayi tabar falon, ganin haka shima yabar gidan gaba daya cikin wani irin yanayi,tuki yakeyi yana tunanin ta hanyar da zai shawo kan Aysha wanda ya lura kaman baya gabanta dan yanda take nuna mishi kaman Dashi da babu duk daya wani iska ya furzar mai zafi tare da daukan wayanshi ya kira Abdul cikin murya irin na wanda baya san magana yace Kana ina? Abdul ya amsa da ina Kaduna dan tsaki yayi tare da kashe wayan, juya kan motarshi yayi ya koma gidan Mum domin in yana ganin indo yana shiga cikin nishadi ko ba komai ganinta na sashi cikin farin ciki da annashuwa, koda ya koma gidan bai shiga ciki ba wajan bukka ya nufa inda yaga wani littafi a wajan an rubuta the doctor, dan shuru yayi bayan ya karanta sunan tare da fadin kenan Dr ce yanzu, wani iri yaji tunawa da a asibiti zata fara aiki ranshi yaji ya baci dan yasan da mutane zata dinga hulda manya da kanana, gashi yasan babu wanda zai ganta bai loraba wani takaici ya kuma ji tunawa da yayi babu aure a kanta, kenan kowa yana da daman yi mata magana, ya dauki lokaci mai tsawo yana sakawa da kullawa jin kiran sallah magrib ne ya gane ya dade a wajan dan haka masallaci ya nufa yaje yayi alwala aka fara sallah, koda aka idar mutane sun fara fita wasu kuma suna nan zaune domin suna jira lokacin sallah isha’i yayi idan sukayi sai su koma gaba daya cikin masu jira harda A Majeed wanda yake ta faman addu’a akan Allah ya mallaka mai aysha a karo na biyu har aka kira sallah aka idar sannan ya fito ya shiga gida, a dinning yaga Mum da indo wacce take cikin wani doguwan riga Red material ne kayan saman ya kamata kasan kuma ya bude, ga dan kwalin kayan ta dan yafe kanta Dashi duk da babu makeup a fuskanta tayi kyau sosai kun san jan abu da karama mutum kyau ido ya bita dashi wanda ta dago suka hada ido da sauri ta kawar da kanta tare dajin haushin hada idon da sukayi, shigo murmushi ya sakar mata da suka hada idon zama yayi akan daya daka kujeran dinning din, Mum tace au dama baka wuce ba?yace eh har na tafi na dawo dan inyi dinner a nan, cikin ran indo tace inda tasan zaiji da batai girkin ba domin bata son duk wani abu da tayi yaci ko ya yaba wani abu nata dan haushi yake bata sosai…..  Jin muryanshi tayi yana fadin aysha plz samin abincin ba indo ba harta Mum tayi mamaki indo kaman ba zata sa ba amma ganin Mum a wajan yasa ta tashi tare da zuba mai ta tura mai gabanshi ta kalli Mum tace Mum good night, Mum tace tun yanzu aysha Allah ya tashe mu lfya, daki ta wuce bawai dan tana jin bacci ba kawai dan kar taci gaba da zama da A Majeed ne yasa tabar wajan, koda ta shiga daki tsaki tayi tare dajin haushin zuba mai abincin da tayi, shigo tana barin wajan yaji ya kasa cin abincin danshi ba abincin yake bukata ba ita kawai yake son gani, irin kallon da Mum take mishi yasa ya fara cin abincin yaji dadinshi sosai, harya gama ya tashi tare da fadin Mum bari in tafi in Dad ya dawo a gaida shi, tace OK sannan ya fita da ido Mum ta bishi tana takaicin halin dan nata yau shekara nawa da aure amma har yanzu baida da ko daya, wanda ita koda yaushe burinta bai wuce ace taga jikanta ba,amma tunda haka yake so sai yaje yaita yi.

STORY CONTINUES BELOW

Indo ce cikin atamfa tayi kyau sosai saman kayan tasa kalan rigan likitoci, dan karamin gyale ta yafa a saman kanta, falo ta fito inda taga Mum tana zaune cikin shiri Mum tace yauwa sai kizo muje in kaiki domin in raka ki zuwa Office, indo tayi dariya cikin jin dadi sannan suka fita, driver ke tuki indo da Mum suna baya har katon asibitin da zata fara aiki, bayan driver ya faka suka fito duk wanda ya gansu zai ce indo yar Mum ce ta cikinta domin irin kyan da suke Dashi, har cikin asibitin suka shiga inda Suka je wajan wanda Dad yace su nema nan ya amshesu da murmushi tare da raka su har Office din indo din, office din babba ne ciki harda dan karamin gadon duba mara lafiya ga AC da TV dake manne sai kujeran zamanta da guda biyu na zama, office din dai irin na Dr babba, indo gefen hawan jini da sugar da zuciya ta karanta, sai yasa Office dinta yake da girma, Mum bayan ta gama gani ta mata murna sannan ta wuce tare da fadin driver zaizo ya dauketa inta gama, nan aka shigo ma indo da file na marasa lafiya babu bata Lokaci tace a fara shigowa, wani tsoho ne ya fara shigowa wanda kallo daya zaka mai ka gane mai arziki ne sai dai ciwo yasa duk ya rame, nan indo ta mishi umarni daya zauna bayan ya zauna tace maike damunshi nan ya fara mata bayani, tana rubutawa harya gama ta fara mai tambayoyi yana bata amsa, wanda yake fada mata dakyar yake tafiya kafanshi ya kumbura, tace yahau gadon dake dakin ya bude kafan ta gani, bayan ya zauna ya bude kafan taga yanda ya kumbura kuma guda daya, Magani ta rubuta mai tare da fadin idan ya kare ya dawo, fita yayi wani ya shigo haka taita duba mutane a ranan ta duba mutane sun kai ishirin, sai wajan 8 ta gama Wanda driver yazo ya dauketa sukai Gida suna shiga A Majeed na shigowa, ganin kayan dake jikinta yasa ya tamke fuska da sauri ya nufeta Kafin ta shiga ciki, tare mata gaba yayi tare da fadin aysha inason magana dake, shuru tamai ba tare data kulashi ba fuskanta a daure, ga kamshin turaren shi da yake tashi, haka shima ta gefenshi jin kamshin turarenta yake yi gaba daya ya fara kashe mishi jiki, cikin wani irin murya ya kira sunanta bata amsa ba sai daka kanta da tayi alaman ya matsa mata ta wuce ido suka hada wanda saida gabanta ya fadi da sauri ta kawar da kanta gefe ta juya da baya zata bar wajan dan bazata iya tsayuwan ba, riganta ya rike ta baya wanda yasa ta tsaya cak……

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      125to130

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

*NGD DA KIRANA DA KUKAYI AKAN LAFIYA BANYI POSTING JIYA BA DA MASU YIMIN MESSAGE DUK NA GODE LAFIYA NA QALAU SAI DAI CIWAN KAI DA YASA NI GABA TUN JIYA HAR YANZU DA NA DAURE DAN INGA NA FARANTA MA MASOYA NA RAI SOSAI NAKE JINKU KAMAN YANDA KUKE KAUNAR NOVEL DINA INA MUKU ONE LUV❤*

Zuciyanta taji yana tafarfasa tare da fadin wai mai yake nufi da ita ne haka, cikin fushi ta waiga amma ganin irin kallon da yake mata yasa ta kasa yi mishi masifan da taso tamai, tsaki ta danja tare da wucewa ta gefenshi ba tare da taji abunda zai fada mata ba, wani irin iska ya furzar cikin wani yanayi mai wuyan misaltuwa,shima cikin ya shiga, koda indo ta nufi falo a nan taga Mum harda Dad suna dan fira, da sallama ta shiga duka Suka amsa, Mum tace a’a likita bokan turai, dan rusuna wa tayi ta gaida Dad da Mum, cikin Fara’a suka amsa Dad yace ya office din dai2 lokacin A Majeed ya shigo yana sallama yana magana kaman baya son yi, amsawa sukayi, zama yayi kusa da Dad din nashi wanda shima Dad din kallonshi yake tare da fadin yauwa kai dama nake nema, wai ya maganan contract dinne? Kayi signing kuwa? Yace eh nayi Dad tare da tashi yana fadin bari in dauko maka, indo tashi tayi ta shige daki, toilet ta fada tayi wanka,tare da alwala bayan ta idar da sallah isha’i tasa wata doguwar rigan bacci ta kwanta tare da lumshe ido, koda A Majeed ya dawo baiga ayshan shi ba gaba daya yaji zaman ya gundureshi amma ya kasa tashi ya tafi dan yana tunanin zata fito ganin har karfe tara da wani abu yasa ya tashi yayi ma iyayen nashi sallama, koda A Majeed yaje Gida baiga Zainab ba hakan bai wani dameshi ba dan inda sabo ya saba duk da abun yana bata mishi rai sosai, bedroom dinshi ya shiga kai tsaye toilet ya shiga wanka yayi ya fito da wani karamin towel yana goge kanshi kaman kullum zama yayi yana gyara gashin kanshi sai kamshi daya kara gauraye dakin Zainab ce ta shigo cikin night gown wanda komai na jikinta ana gani, abun ya bashi mamaki na ganinta a wannan lokacin dan baiyi zaton tana gidan ba kuma abun mamaki yau itace a dakinshi cikin wannan yanayi bai gama tsinkewa ba sai da yaji hannunta cikin jikinshi tana shafa shi tako ina, nan A Majeed ya fara mayar mata da martani dan dama kwana biyun nan dauriya kawai yake ranan yayi mamakin yanda zainab ta saki jiki dashi sosai, cikin jin dadi bacci ya daukeshi, koda ya farka bai ganta a dakin ba, dan murmushi yayi tare dajin dadi harga Allah yana son Zainab sai dai halayanta da baya so har take shirin fice Mai a rai gaba daya,  ta gefen Zainab kuwa koda ta koma daki tsaki tayi tare da fadin shegiyan mata maita bani ne yau har nake nemanshi dakai na, gidan wata kawarta taje wata mai maganin mata wacce take Kawo ma kawar tata tazo inda ta basu tace suyi testing Zainab kaman ba zata shaba dakyar ta dan lasa kadan jin dadin maganin mai kama da zuma yasa ta amsa taita sha tun a gidan ta shiga wani hali ba shiri ta dawo Gida, dan tsaki tayi tare da fadin dan ba kara kar aje a maidani tsohuwar karfi da yaji ina cin ganiyan kuruciya Na, koda Gari ya waye A Majeed dakin zainab din ya nufa amma bata ciki ranshi yaji ya baci tare da fadin ina taje da safen nan, wayanshi yaji yayi kara kaman shigowan sako, kaman bazai duba ba ya dauko wayan ya duba sakon daka Zainab dinne *na tafi China jirgin mu 8 zai daga naga kana bacci na wuce saina dawo* wani irin iska ya furzar mai cike da takaici zama yayi tare da fadin wai mai Zainab take nufi Dashi ne haka? Sai kace ba matar aure ba in za tayi tafiya bata gaya min,Dan ajiyan zuciya yayi tare da fadin zanyi maganin abun daukan daya daka key din motarshi yayi ya bar gidan direct gidan mum ya nufa jin motsin mutum a kitchen yasa ya nufi kitchen din dan yasan indai Dad na Gida Mum ke mishi abinci, ganin wacce ke kitchen din yasa shi sakan wani murmushi tare da tsayawa a kofar kitchen din yana kallon yanda take aiki cikin natsuwa, Kare mata kallo yake tayi wacce take dauke da doguwan riga ya dan kama ta saman, kasan kuma a bude yake, ta daura dan kwalin kayan gaba daya ji yake kaman yaje yayi hugging dinta amma babu dama, jin kaman ana kallonta gashi kuma tana jin kamshin turaren shi tun dazu, yasa ta waigo sukai ido biyu wani murmushi ya sakar mata, saurin kawar da kanta tayi tare da waigawa taci gaba dayin aikinta, jin kamshin turaren shi kaman a kusa da ita yasa ta dan waiga ganinshi tayi kusa da ita, har suna iya jin numfashin juna, kokarin kaucewa takeyi dan tabar kitchen din gaba daya amma ya tare hanya domin a gabanta yake, cikin muryanshi Wanda kaman baya son yin magana ya kira sunanta tare da fadin plz ki saurare ni, mai yasa kike irin wannan fushin akai na, kina nunawa kaman baki sanni ba, inaso kiyi hakuri akan duk abunda na miki a bay…… Jin kukanta yasa hankalinshi ya tashi ba tare daya karasa abunda yake son fadi ba, cikin damuwa yasa hannunshi da niyan ya share mata tayi saurin kawar da kanta gefe ganin kaman kukan nata karuwa yakeyi gashi har cikin ranshi yake jin kukan na bai san lokacin daya janyota jikinshi ba tare da lumshe idonshi, da karfi tasa ta tureshi amma ko gezau baiyi ba domin ya riketa dakyu, cin zafin da yayi a hannunshi yasa ya saketa da sauri ta fita da gudu cizonshi tayi a hannun bude wajan yayi ya gani ya tashi yayi ja ga shaidan hakorinta nan a wajan, idonshi daya kada yayi ja ya furzar da wani irin iska mai zafi, fita yayi daka gidan gaba daya kai tsaye gidanshi ya koma gaba daya ranshi a jagule.

STORY CONTINUES BELOW

Itako indo tana shiga daki ta fada gado tana ci gaba da kuka, wai mai hakan ke nufi mai yake shirin faruwa ne, lallai na yarda namiji bashi da Kunya ko kadan yau itace A Majeed har yake kokarin taba jikinta bayan wasu Lokaci da suka wuce yake nuna kyamanshi akanta a fili ba tare da tuna yanda za taji ba a ranta, wani irin tsananshi taji yana karuwan mata a rai fiye da, dah, ganin zata office yasa ta fada toilet tayi wanka idon nan nata ya dan tashi, powder kawai ta shafa tare da feshe jikinta da turare, ta fito falo cikin riga da zani na Atamfa sai rigan likita akai da wani karamin gyale ta yafe kanta dashi tayi kyau sosai, Mum bata falo dan haka ta wuce office ba tare da tayi breakfast ba, driver ya kaita ya ajiyeta, kai tsaye Office dinta ta shiga ta fara duba mutane takai wajan shabiyu tana ganin mutane sannan ta fito dan ta nemi abinci kusa da asibitin akwai wani wajan snack da coffee, ta ajiye farar rigan Dr din a office ta nufa wajan inda taga yawanci mutanen wajan laraba da turawa sunfi yawa kuma duk yawanci coffee din suke sha, zama tayi akan kujera da babu kowa, nan ta fara duba abunda takeso shawarma tasa a Kawo Mata da chapman, fara ci tayi a hankali kaman bata son ci, yazeed wanda tun shigowanta wajan ya kafeta da ido tashi yayi ya zauna wajan da take tare dayi mata sallama amsawa tayi, sannan yace kiyi hakuri na zauna ba tare da neman izininki ba,dan murmushi tayi tare da tashiwa tace babu damuwa na gama, yace ya zaki tafi daka zama na, plz ki zauna duk maganan da yake mata da turanci yake yinshi, tace sorry ina sauri dai2 lokacin mai amsan kudin yazo tazo zata bayar ya riga ya biya kallonshi tayi a karo na biyu tace nagode tana fadin haka tabar wajan binta yayi da kallo tare da fadin sai yanzu na sami matar aure domin duk irin quality din da yake nema wajan Mace ya gansu a tare da ita wacce ko sunanta bai sani bah…

Taku Maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      130to135

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Dan lumshe ido yayi tare da tashi wanda kamshin turarenta duk ya cika shi, motarshi ya shiga benz yaja yayi Gida, waye yazeed? Yazeed dane daya tilo wajan iyayenshi bawai ina nufin shi daya Suka haifa ba yana da yaya Mace wacce tana London ita da mijinta, sai shi da iyayenshi suke masifar So kasan cewanshi karami kuma namiji shine yake gabansu kullum babanshi Alhaji Ibrahim dan asalin sokoto ne, yana sana’an mai yana da gidajen mai da dama, yana da kudi sosai amma a abuja suke zaune, tun tuni suke fama da dan nasu yayi aure amma yaki yi Mum dinshi hjy Bilkisu har Yaran kawayenta take kawo mai amma yaki zaba, ganin haka yasa ta zuba mai ido, yana da burin auren Mace mai aji wacce tasan kanta, koh da yazeed yaje Gida tunanin indo yaita yi wanda abun yazo mai a bakon abu, dan murmushi yayi domin yasan bai taba ganin abu yana So ba bai samu ba, yazeed ba fari bane Ba kuma baki bane, chocolate colour kenan yana da kyau dai2 misali, koda indo ta koma Office kira ta samu daka Office din director inda za suyi meeting bayan Sun shiga nan aka fada mata ranakun da zata dinga zuwa Monday da talata, ran Monday da safe talata kuma da yamma hakan ya mata dadi ga kuma albashi mai tsoka, bayan an fito daka meeting dinne ta kira driver yazo ya dauketa bai dade ba yazo, Suka wuce Gida.

Tunda A Majeed ya shiga bedroom dinshi bai fito ba domin yanda yake jin jikinshi wani iri ga kamshin turaren indo daya dameshi yasa shi cikin wani yanayi dakyar ya tashi ya fada toilet yayi wanka amma still kamshin na nan sai juyi yakeyi tare da kallon inda ta cijeshi yana dan shafawa a hankali, yanda yake ji a zuciyanshi yafi zafin cizon sau dubu, domin babu komai sai son indo dake addabanshi, zazzabi ne ya rufeshi wanda yasa ya kasa fitowa waje koh sallah a daki yake yi dan bazai iya zuwa masallaci ba, haka ya kwana baiko leko ba, yana ciki yana fama da zazzabi sosai,

STORY CONTINUES BELOW

Indo da mum suna zaune a falon kasa, abdul ya shigo da sallama, duka Suka amsa da Fara’a, abdul ya gaida Mum cikin kulawa ta amsa da abdul har yanzu dai kana ta fama, dan murmushi yayi tare da zama, Mum taci gaba da fadin ni inaga daka hakura da yarinyar wlh ka auri wata nan gaba in Allah yasa matarka ce sai ayi, indo ce tace Mum niko nafi son ya auri yarinyar wlh saboda irin halin da take ciki, Mum tace hakane aysha taimako ne amma Abu yau wajan shekara biyar ana fama, indo ta danyi shuru can ta nisa tace niko Mum dan Allah inaso inje inga yarinyar, Mum kallonta tayi tare da fadin babu damuwa zan fadama Dad sai kusa rana, Abdul yaji dadin hakan sosai, masu aikin gidan ne suka Kawo ma Abdul Abun taba baki, ya kalli indo yace ya Office din? Indo tace Alhmdlh, wayan Mum ne yayi kara dauka tayi ban san mai ake fada mata ba naji tace gani nan zuwa, kallon abdul tayi tace wai A Majeed ne tun jiya daya shiga Gida bai fito ba, gashi matarshi bata nan shine driver dinshi ya kira, abdul yace bari inje in gani, mum tace muje tare, Bin abdul tayi akabar indo a gida wacce tunda taji hakan jikinta ya mata wani iri, daki ta koma ta kwanta tana jin wani iri.

Koda su Mum sukaje gidan a dakinshi suka sameshi ya lullube duk da AC din dakin a kashe yake amma yana ta rawan sanyi cikin tashin hankali Mum ta kira No Dr dinsu wanda yace mata gashi nan amma baya kusa zai dan kai nan da 30mnt,kwatancen gidan A majeed tamai sannan ta kashe, abdul fita yayi yabar Mum ita daya cikin tashin hankali tama rasa abunyi jin muryanshi tayi yana fadin aysha I love You come back to me I will treat you like a queen, shuru tayi tana mamaki, daukan wayanta tayi ta kara kiran Dr din yace yana hanya karta damu, Mum tace koh su Kawo shi hspt ne, yace ta bari ya kusa zuwa ba’a dade ba sai ga Dr din da abdul nan aka fara dubashi inda Dr ya mishi allura tare da bashi Magani, yace ma Mum a bashi abinci yaci, amma mai ruwa, mum da sauri ta hado mishi Tea cikin kitchen din da yayi kura dan Zainab ta Kori masu mata aiki sai dai wani lokacin ta kira azo a Mata shara duk saboda gudun kar a kara nanata abunda akayi da indo, mum rikoshi tayi tana bashi tea din jikinshi yadan fara rage zafi dan alluran da aka mai,mum ta bashi Magani yasha nan dr yama Mum sallama tace ya tsaya su tayata kama A Majeed din a sashi mota domin gidanta za’a kaishi hakan koh akayi aka kamashi suka nufi gidan mum din, sama akayi Dashi kusa da dakinta inda aka kwantar Dashi akan gadon dakin, idonshi a lumshe daka gani yana fama da ciwan sosai, Mum ruwa ta dibo tasa towel a ciki tana matsewa tana dan shafamai a jiki, lokaci daya zafin jikin ya sauka bacci ya daukeshi, Mum wani irin tausayin dan nata take ji, amma idan ta tuna abunda yayi sai taji ranta na baci, domin ya nuna mata baya son gatan da tamai, kun san d’a da uwa😢, dakin indo ta nufa wacce take zaune amma hannunta biyu akan fuskanta daka gani tunani takeyi domin har Mum ta shigo bata ji motsinta ba har saida ta kira sunanta, tayi firgit tare da tashi tana kakaro murmushi tana fadin sannu da dawowa Mum, mum amsawa tayi tare da zama akan gadon dakin ganin haka yasa indo ta zauna a kusa da ita, Mum tace aysha lafiya kuwa? Dam taji kirjinta ya buga kodai A Majeed ya fadama Mum ta cije shine, jin Mum tayi tana fadin aysha wannan irin tunani haka har in shigo baki san na shigo ba, dan Allah ki fadamin abunda ke damunki, ajiyan zuciya tayi tare da fadin babu komai Mum kawai dai ina tuna halin rayuwa ne, da yanda abubuwa sukan canza, Mum tayi dan murmushi tare da fadin hakane Allah babu yanda baya lamarin sa, sai yasa akeso bawa ya kasance mai godiya a duk halin daya sami kanshi, Allah yakan jaraba bawa ta hanyoyi da dama idan yayi hakuri ya dangana sai kiga Allah ya Kawo mai sauyi cikin sauki, indo wacce hawaye ya zubo mata a fuska tace hakane Mum sai yasa a kullum nake kara godema Allah daya hadani daku a rayuwa na, Mum janyota tayi jikinta tana fadin ki daina hawaye Allah ya fimu sanin dalilin haduwan mu duk da abunda ya hadamu ya raba mu amma Allah bai sa mun rabu ba har yau muna tare wanda zan so mu…..  Dan shuru Mum tayi ba tare data karasa abunda take son fadi ba, indo jin tayi shuru ta dago ta Kalli Mum wacce idonta yake hawaye cikin tashin hankali indo take tambayan Mum lafiya kuwa? Mum rike ma indo hannu tayi tana dan murmushi ga hawaye kuma na zuba, tace aysha Allah yasa min sonki tun kafin in ganki tun lokacin dana ji labarin ki nake burin in taimaka miki, naso ace in kasance dake har abada domin nasan in A Majeed yana tare dake har abada muna tare sai mutuwa,dan shuru Mum tayi Kafin tace nasan nan bada dadewa za kiyi aure ki tafi gidan wani May be ma ya hanaki zumunci Dani, wani hawaye ya zubo ma indo mai zafi tare da fadin Mum har abada ke mahaifiya tace duk Mai sona dole ya soki,mum rungume indo tayi tare da fadin Allah ya miki albarka ya baki yara masu miki biyayya inga jikoki na, indo rufe fuska tayi ba tare data amsa ba, amma a zuciyarta ta amsa, mum tayi murmushi tare da fadin bari inje in duba A Majeed inga ko ya tashi, indo da mamaki take kallonta, Mum kaman tasan abunda take tunani tace nasa an kawo shi nan dan in kula Dashi, Indo cikin murya wacce ya dashe tace ya jikin nashi Mum tace da sauki, bayan fitan Mum ne indo tayi ta tunani akan maganganun Mum, tabbas abunda ta fahimta Mum har gobe tana sonta da dan nata, kai indo ta girgiza tare da fadin ba haka Mum ke nufi ba kawai tana son in yafe mai abunda yayi min ne da wannan tunanin indo tafi yarda dan haka ta tashi itama ta fita, motsi taji a kusa da dakin Mum din dan haka ta shiga Mum ce a ciki tare da A Majeed wanda yake kwance idonshi a lumshe kaman mai bacci amma idonshi biyu, kanshi ke mishi ciwo sosai ga zazzabin yaki sauka, Mum tace aysha inaga asibiti zamu gskya, jin an kira sunan wacce yake burin gani yasa ya bude ido a hankali, dai2 lokacin ta matso kusa da gadon idanshi a kanta yana mata murmushi, dakewa tayi domin irin kallon da yake mata yasa take jin wani iri, murya na rawa tace mai ya jiki?amsawa yayi da fadin kaina kaman zai fashe tanan gefen tare da nuna mata yana maganan ne dakyar, tashi tayi ta fita tare da cema Mum bari in duba shi, jim kadan sai gata da abun gwada VP, wayan mum ne yayi kara ta dauka tare da barin dakin, a hankali ta zauna gefen gadon tare da fadin Kawo hannunka,wannan ne karo na farko data mishi magana tunda ta dawo kasar, kaman dama jira yake ya mika mata jallabiya ne a jikinshi mai gajeran hannu ta daura abun a hannun lumshe ido yayi ga kamshin turarenta na dukan shi, idanta ya sauka a inda ta cijeshi domin taga shaidan hakori wani iri taji a ranta, jin muryanshi tayi yana fadin haka kike ma mutane a hspt kina taba su…….

STORY CONTINUES BELOW

Taku maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      135to140

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Mamaki maganan ya bata dan haka bata kulashi ba sai fara danna abun takeyi tana dubawa, jin tayi shuru yasa ya bude idonshi daya canza kala daka fari zuwa ja, ido suka hada gabanta taji ya fadi domin ganin Yana yinshi, tayi saurin kawar da idonta tana dan kallan abun, dai2 lokacin Mum ta shigo dakin hakan yama indo dadi, Mum tace aysha ya jikin nashi? Ni inaga muje hspt kawai, indo tace Mum VP dinshi ne yahau sosai, zaro ido Mum tayi tare da matsowa kusa da tilon dan nata tace Abdul Majeed, maike damunka haka da har jininka zai hau, idonshi a lumshe suke amma ji yake kaman yace ma mum aysha ce matsalata amma bazai iya ba dan inda zai iya da tun tuni ya fadama Mum din domin yasan shida kanshi bazai tunkareta da zancen ba dan abunda ya aikata… Mum ce ta katse shi da fadin son ka tashi muje hspt, kai ya girgiza tare da fadin a’a Mum aysha zata kula Dani, indo wacce sai yanzu ta kuma magana tace Mum za’a amso mishi magani bari inje driver ya kaini, da sauri yace No kiba driver din yaje, Mum wacce tasan kanin zancen tace rubuta maganin aysha sai driver ya amso mishi, tace To Mum, fita indo tayi daka dakin jim kadan sai gata ta dawo Mum tace ina takardan? Indo tace na bashi ya siyo dan murmushi Mum tayi tare da fadin maimakon kizo in baki kudi sai kika bayar, aysha shuru tayi ba tare da tace komai ba, A Majeed idonshi lumshe amma kirjinshi kaman ya fashe dan takaici, kishin aysha yake ji bai san dawa take mu’amala ba a hspt, jin kirjinshi na zafi sosai yasa hannunshi yana dan dannawa amma kaman karawa yakeyi, duk abunda yakeyi idon indo na kanshi ta dan tausaya mai ko Ba komai dan Mum ne dole ta tausaya mai, dan haka ta tashi ta fita jim kadan sai gata da Ruwa da Cup da kankara a cikin wani bowl ruwan ta zuba a Cup din tare da kankaran, wajanshi ta nufa jin kamshin turaren Nata kaman kusa Dashi yasa ya dan bude ido, fuskanta babu yabo babu fallasa tace ga Ruwa kasha zai rage maka zafin, kin amsa yayi sai ido daya kura mata wanda hakan Yasa take jin wani iri, Mum tace A Majeed ka tashi kasha mana, kai ya girgiza alaman a’a, indo cikin muryanta karama tace ka daure kasha zaisa kirjin ya rage maka zafin kafin a kawo maganin, ganin yanda take maganan kaman za tayi kuka yasa ya tashi yana cije baki ya amsa tare da shanyewa duka, kallonta yayi yana dan murmushi a hankali ya furta thank for care, bata bashi amsa ba sai barin dakin da tayi, jim kadan sai gata da ledan maganin lokacin Mum bata dakin idonshi a lumshe jin kamshin turaren da yake sashi cikin wani hali yasa ya bude ido dan yasan tana wajan, idanshi akan nata murmushi ya sakar mata fuskanta a daure tace ga maganin, kallonta yake yi yanda ta wani tamke fuska, sai yaga ta kara mishi kyau, mika mai maganin takeyi bai amsa ba sai fadi yayi plz bani ruwan da zansha, ajiye maganin tayi a gefe tare da bude goran faro ta zuba mai a cup, bashi tayi ya amsa jiki babu kwari kallonta yayi tare da fadin plz ki taimaka kiban maganin insha bazan iya budewa ba, dan tsaki tayi kadan wanda bata san zai fito ba har yaji, sai jinshi tayi yana fadin kiyi hakuri nasan na takura miki, but dan Allah za kiyi min, wani iri taji dan haka tayi saurin bude ledan maganin ta fara bashi yana sha, harya gama ya kalleta yace ngd da kulawa, tace no need ina maka hakan ne a matsayina na Dr wanda zan iya yima kowa ma hakan tana fadin haka tabar dakin, ido ya lumshe cikin jin zafin kalaman nata, zan iya yima kowa ma hakan, wani irin kishi yake ji tare dajin zafin maganan nata sosai, duk yanda yaso ya cire abun a ranshi ya samu yayi bacci ya kasa, sai juyi yake tayi ga kirjinshi na mishi zafi sosai dan ma maganin da yasha yasa ya dan ragu amma still yana mishi zafi.

STORY CONTINUES BELOW

Itako dakinta ta fada ta shiga toilet tayi wanka tare dayin alwala dan yin sallah magrib da aketa kira,bayan ta idar da sallah dinne ta zauna akan kujeran dakin tana tunanin kauyensu wani hawaye taji yana zuban mata Allah sarki inna jamila ko kina nan har yanzu a gidan mu? Abubuwan da suka faru a baya suka dunga dawo mata, gaba daya hankalinta taji yayi Gida ko Ba komai ya kamata ace yanzu taje duk da bata son zuwa garin amma kodan taga inna jamila dako sata sami labarin Dan uwanta dole taje,cikin wannan hakin Mum ta shigo ta sameta, kiran sunanta tayi tare da fadin wai ni kam aysha miye matsalanki ne kwana biyu nan, dan shuru tayi tana tunani tana son zuwa Kaduna da garinsu amma bazata iya fadama Mum yanzu ba saboda ciwan dan nata dan taga hankalin Mum ba’a kwance yake ba, kaman Mum tasan abunda take tunani tace aysha nasan kina Tuna baya ne bayan dazu mun gama magana, amma inaga ki shirya jibi sai kije garinku ki duba su inaga hankalinki zai dan kwanta, indo kai ta girgiza tare da fadin Ba yanzu ba mum sai nan gaba, Mum tace akan wani dalili kin fiso kiyi ta damuwa kullum koh? Tace Mum inaso inje amma zan bari sai A…. Shuru tayi wanda kuka yaci karfinta Mum tace kiyi hakuri aysha kibar wannan kukan, shuru indo tayi tana sauke ajiyan zuciya haka Mum taita bata baki akan ta shirya taje jibi din,tace Mum shikenan amma sai naga yanayin jikin nashi tunda ni nake duba shi, Mum tayi dan murmushi tare da fadin karki damu amma Idan kin bukaci hakan sai ki daga tafiyan, tace toh mum kiran sallah isha’i ne yasa Mum barin dakin indo tashi tayi dan yin sallah, bayan ta idar ta zauna amma saita tsinta kanta da zuwa duba A Majeed din dan haka ta tashi ta nufi dakin a zaune ta ganshi akan dadduma alaman ya gama sallah ne, kallo daya tamai ta kawar da idonta gefe tace kirjin ya daina maka zafi? Ido ya kura mata komai nata yana burgeshi a natse, yace ya daina sai dai ina cikin damuwa, kallonshi tayi caraf suka hada ido tayi saurin kawar dakai gefe dan murmushi yayi tare da tashi dakyar ya koma kan gadon dakin, cikin taushin murya tace gobe zan gwada maka VP din inga koh ya sauka sannan ka cire ma kanka damuwa indai Kana son lafiyanka,ido ya kura mata yanda take mai bayani abun har mamaki yake bashi, dan shuru tayi alaman ko zai ce wani abu jin shima din yayi shuru yasa ta juya zata fita, sunanta ya kira da aysha cikin wani irin murya tsayawa tayi ba tare da ta waiga ba, yace plz ki dan dawo ki zauna ko zan iya bacci, waigawa tayi tana mai wani irin kallo shiko murmushi yake mata, kaman bazata koma ba komai ta tuna kuma ta dawo tare da zama akan kujeran dakin tace zan zauna a matsayina na doctor mai burin inga wanda nake dubawa ya samu Lafiya, ido ya lumshe da alama maganan nata ya mishi zafi, amma saiya daure yace babu komai a hakan ma nagode, bata kulashi ba illa wayanta da take latsawa shiko idanshi na kanta ji yake kaman yaje yayi hugging dinta ko zaiji sanyi a ranshi, wayanshi ne yayi kara wacce yake gefen gadon, hannu yasa ya dauka bakuwar number ne, kuma na waje ko ba’a fada ba yasan cewa zainab ce tunda ta tafi bai kirata ba itama haka sai yau, dan haka ya dauka tare da sawa a Kunne, ban san mai take fada mai ba naji dai yana fadin kin san baki isa ki rabani da mahaifiya taba koh, dan haka ki dinga sanin kalaman da zaki fada a kanta yana fadin haka ya kashe wayan gaba daya cikin bacin rai, indo dake zaune tana saurara duk sai taji ya bata tausayi a karo na farko, dan tasan matarshi tafi karfinshi yana mata son daya wuce kima, dan lumshe ido tayi tana tuna abubuwan da suka faru lokacin datai zama a gidan nashi, haushin shi shida matarshi taji yana kara kamata, dan tsaki tayi kadan wanda sai kana gab da ita zaka iya ji, A Majeed da idonshi ke kanta yana lura da duk abunda takeyi jin muryanshi tayi yana fadin aysha dan Allah ki daina tuna baya ki bani second chance, ina mai baki hakuri akan……  Ya isa haka ta katse shi cikin bacin rai, shuru yayi yana kallonta taci gaba da fadin kar kaga dan daman dana baka yasa kaji koh akwai abunda nake nufi a kanka, karka yaudari kanka ya kamata ka bude idonka daka baccin da kake shirin yi, duk wannan abun ina makane a matsayina na doctor sannan kuma ka kasance kai dan Mum ne sai yasa har nake dubaka kar hakan ya baka daman wuce gonarka……  Wani irin hawaye taji yana zubar mata wanda yasa ta kasa karasa maganan dan haka tabar dakin da sauri……

Taku maryam obam😘*💅 TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

STORY CONTINUES BELOW

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      140to145

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

A Majeed idanshi ne ya kada yayi ja kaman garwashi ga kirjinshi na faman tafarfasa, gaba daya ji yayi zaman gidan ma ya isheshi domin magananta yake taji a kwakwalwanshi yana mai yawo, lumshe ido yayi yana mamakin irin son da yake mata Lokaci daya, hawaye ya fara zuba a idonshi tare da karayin nadaman abunda yayi mata, tabbas duk yanda kaga mutum karka taba wulakanta shi, domin baka san irin baiwar da Allah yayi mishi ba, tashi yayi dakyar ya fita daka gidan, security din gidan sunyi mamaki da suka ganshi dan sun san bashi da lfya gashi kuma yana tafiya dakyar, bude gate din gidan yayi, wani daka cikin security din yace sir where are you going in dis condition, bai kulashi ba dan bata shi yake ba, fita yayi daka gidan yana tafiya dakyar taxi ya tsayar dakyar ya iya furta mai inda zai kaishi, direct gidanshi aka kaishi zaro kudi yayi wanda bai san ko nawa bane ya bashi sannan ya karasa kofar gidan yana bugawa mai gadin gidan ya leko duk da dare ne akwai haske tako ina, ganin ogan nashi yasa ya fito da sauri yana fadin wlcm sir, baibi ta kanshi ba sai shigewa da yayi,dakinshi ya wuce direct ya fada gado yana hawaye kaman wani karamin yaro, tabbas Allah yakan jarabci bawa ta hanyoyi da dama, bai taba tunanin zaiso indo a rayuwanshi ba, sai gashi lokaci daya Allah yasa mishi azababban sonta tare da kishinta ada idan yaji labarin halin da masoya sukan shiga har haushi yake ji sai yaga kaman karya ne, sai gashi yau ya faru a kanshi, lallai ikon Allah ya wuce wasa, gaba daya ya kuma birkicewa ya koma abun tausayi duk saboda son wacce ya kira yar kauye wacce bata waye ba, gashi sonta na neman hallakashi, ido ya lumshe wanda hawaye ke zuba, tare da burin barin kasar ko zai dan sami sauki domin duk yanda yakai da sonta bazai matsa mata ba, tunda bata bukatar hakan, dakyar ya janyo wayanshi ya kira wata number, kana jin maganan shi kasan yana cikin wani hali, fadi yayi zan sami visa na London gobe nake So, ban san mai aka fada mishi ba ya jefar da wayan gefe tare da lumshe ido kanshi na mishi wani irin juyi.

Koda indo ta shiga daki itama kukan take tayi, wai mai yasa rayuwa yake zuwa mata a haka ne? Da farko nasha wuya wanda ban taba kawo wa zanji dadi ba, sai gashi nayi aure an kaini Gidan mijin da yake guduna yana kyamar nunama duniya ni matarshi ce, ya maidani baiwar kishiyata ya kirani yar aiki a gabanta tasa ni bauta kaman ba gobe, Allah ya kubutar dani daka gareshi mai yasa saida na fara jin dadin rayuwa na yake son fito min da wani bakon abu mai yasa hakan yake faruwa Dani ne……  Kukan da takeyi ne ya kara karuwa…..  Dan shuru tayi yayin da wata zuciyar take ce mata haba aysha mai yasa zaki dauka da zafi haka aiko da zaki rama abunda ya miki bai kamata kiyi mai a cikin wannan yanayin ba, karki manta kefa doctor ce dan mai yasa zaki fadama patient dinki kalaman da zai kara samai wani ciwon da sauri ta tashi kaman an tsunguleta fita tayi ta nufi dakin da yake amma baya ciki dan zama tayi dan tana tunanin ko yana toilet jin ta dade a dakin bata ga ya fito ba yasa ta koma dakinta akan da safe zata dawo, koda ta koma kwanciya tayi tana ta juye2 sai tunanin da take tayi yanda zata Kawo karshen abun tun Kafin ya fito fili, lallai dole in fito da koma waye inyi aure duk da bata da burin yin auren a yanzu amma tana ganin hakan shine zai kawo Mata duk wani karshen matsalanta wanda A Majeed yake shirin tsokano mata domin indai harya furta abunda yake ranshi koda Mum bazata bada goyan baya ba, tabbas ita zata bada domin bazata taba gudun wani Abu na Mum ba, yanda take jin Mum babu wani nata da zaice yana son abu a wajanta ta kasa yi domin Mum Mace ce wacce babu irinta koda za’a samu sai ansha wuya, wani hawaye taji yana zubar mata a ido lallai ya kamata tasan abunyi.

Washe Gari da safe Mum ta shiga dakin da d’an nata yake amma bata ganshi ba, zama itama tayi dan tana tunanin ko yana toilet jin shurun yayi yawa yasa ta tashi ta nufi wajan toilet din, ganin babu alaman mutum yasa ta bude taga wayam, cikin damuwa take fadin ina yaje ne haka? Fita tayi a hanya suka hadu da indo tana kokarin zuwa dubashi tayi shiri da alama fita za tayi, Mum duk da tana cikin damuwa tace aysha fita za kiyi tace eh mum an kirani a hspt ne akwai wanda aka Kawo zan duba shi, Mum tace toh Allah ya taimaka, kinga A Majeed kuwa? Indo dan shuru tayi Kafin tace baya cikin dakinshi?  Mum tace baya nan, indo taji wani iri amma saita daure tace kodai ya fita ne? Mum tace bari in kirashi shida yake jin jiki ina zashi kuma, kiran layin tayi akace switch off kallon indo tayi tace wayan ma a kashe indo taji wani iri musamman yanda taga Mum din nata, na cikin damuwa, toh ina zashi? Shida yake cikin wani hali ido ta lumshe gaba daya jikinta yayi sanyi, Mum ce ta katseta da fadin bari inje in tambayi security ko sunga fitan shi, tare sukai kasa ita da indo din tambayan security tayi ko sunga A majeed, bayan Sun gaidata ta amsa suke shaida mata jiya da daddare ya fita gashi kuma hjy kaman yana jin jiki sosai wlh, Mum shuru tayi amma ranta a jagule indo itama kasa magana tayi horn din da akeyi yasa aka bude gate din mai girma sanata ne ya shigo da mukarrabanshi, ganin matar tashi a tsaye ita da indo yasa ya fito yana tambaya koh lafiya? Nan Mum ta fada mishi abunda ke faruwa, kiran layin A Majeed din yayi amma a kashe, security dinshi ya tambaya ko akwai mai number din security din dan nashi? Wani yace yana dashi nan ya karanto ma senator bugu daya security din ya dauka tare da fadin Hello waye akan layi cikin turanci, Dad yace mahaifin A Majeed ne, cikin girmamawa kaman yana gabanshi yake gaidashi bayan Dad ya amsa nan yake tambaya koh A Majeed yazo Gida, yace eh amma gskiya sir yana cikin wani hali kaman bashi da lfya sosai wayan a speaker yake duk suna ji indo hawaye taji ya zubo mata da sauri tasa hannu ta goge hawayen Dad ya kashe wayan tare da kallon matar tashi bari inje inga halin da yake ciki, tace suje tare Dad yace ok Mum ta Kalli indo tace kije driver ya kaiki hspt din bari muje muga halin da yake ciki indo kafa babu kwari ta nufi mota driver yaja suma su Mum suka fita zuwa gidan dan nasu.

Koda indo ta karasa asibiti jiki a sanyaye ta shiga ciki, nan aka kawo Mata patient din da zata duba a kan keke kallon mutumin tayi cikin tausayawa tare da kallon wanda yake turashi din ganin yana mata murmushi yasa itama tamai tare da tunanin ina ta sanshi lokaci daya ta tuna da wanda ya biya mata kudin abinci dai2 lokacin wata mata ta shigo Office din daka gani matarshi ce bayanta wani saurayi ne ido indo ta kura mai da  sauri ta nufeshi tana nunashi lokaci daya kuma ta rungumeshi wanda mamaki ya hanata magana sai kuka haka shima ta gefenshi yazeed dake gefe yana kallon ikon Allah tare da mamaki a ina tasan Yusuf ga zuciyarshi dake mishi zafi ganin irin runguman da tayi mishi ……..

TAMBARIN TALAKA 💅*

*NA*

*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

145to150

*DEDICATED TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Kuka take sosai dan sake shi tayi ta dago da fuskanta ta kalleshi wanda idanshi na kanta shima tace mai yasa baka nemeni ba tsawon wannan lokacin yaya yusuf, Yusuf yace aysha, indo da sauri ya kara riketa yana hawayen murna dan sakinta yayi tare da fadin Alhmdlh, aysha…. Yama rasa abunda zaice murmushi take tayi tare da komawa ta zauna dan ta duba wannan bawan Allah da yake zaune akan kujera,dan kallonshi tayi tare da fadin Baba maike damunka? Matar tace hawan jini ne yake fama dashi kwana biyu yaki sauka na rasa mai yake tunani haka, dazu muna tsaye kawai ya fadi kasa, koda ya farfado ya kasa koda daga hannu… Ta karasa maganan cikin damuwa, nan indo ta tashi ta nufi inda mutumin yake ta dan dubashi, sannan ta dawo inda take tayi yan rubuce2 sannan ta kalli mutumin tace Baba ina yake maka ciwo, da baki yake magana amma baya iya daga komai nashi, yace gaba daya jikina bana jin dadinsa ji nake kaman jikina baya tare Dani, magani ta rubuta mai tare da fadin za’a dinga Kawo shi duk sati daya ana mishi gashin kafa domin jikinshi ne ya shanye amma idan akayi Sa’a …… Matar kuka tasa cikin damuwa nan yusuf ya karaso inda take yana fadin kiyi hakuri ummi komai zaizo da sauki insha Allah zai warke, indo ta amshe da fadin insha Allah kawai abunda za’ayi yanzu shine ku dinga bashi Magani akan lokaci, sannan ku dinga Kawo shi duk sati dayan, duk wani abu da zai sashi tunani a kauce ma abun nan taita basu shawara shiko mutumin babu abunda yake sai hawaye, abun ya daure ma indo kai ganin dan uwan nata shima yana hawaye toh miye alakansu da wannan mutumin? Jin muryan yusuf din yasa ta dawo daka duniyar tunanin data shilla, yace Sis yanzu sai kizo mu tafi tare koh? Dan ya kamata ki dauki excuse, tace dama saboda duba wannan bawan Allah aka kira ni, nan suka fita tare wannan karan yusuf ke tura mutumin, har wajan jibgegiyan motarsu mai kiran jeep yusuf da yazeed suka kamashi suka saka shi cikin motar, matar ta shiga gaba yusuf wajan driver, indo suka shige baya ita da yazeed domin kalan jeep din nanne mai shigen seyana, mai kujera baya tsakiya da gaba, yazeed kallon indo yake tayi tare da lumshe ido yana jin kamshin turarenta a hankali yake jin sonta na kara kamashi gashi yau yana farin ciki sister din abokinshi ce duk da yana cikin rudani akan ya suka rabu, itako ta gefen indo murna take sosai na ganin dan uwan nata gefe daya kuma tana tunanin wani hali A Majeed yake ciki, jin an taka birki ana horn yasa ta kalli inda suke wani katoton Gida ne sukai parking lokaci daya mai gadi ya wangale Gate din suka shiga, Nan masu aikin gidan suke ta faman zuwa gaida Alhaji da matar tashi, yusuf bayan ya fito haka itama indo da yazeed, kama mutumin sukayi Suka shiga cikin katon falon gidan, har zasu kaishi ciki yace a ajiye shi a falo zaiyi magana hakan koh akayi wata yarinya ce ta fito kyakyawa hannunta dauke da Baby daka gani bata dade da haiyuwa ba, da sauri ta nufi wannan mutumin tana mai sannu daka gani babanta ne, Alhaji yace kowa ya zauna, zama sukayi su duka banda yazeed da yake musu sallama akan zai wuce, mutumin yace shima ya Zauna a gabanshi za’ayi komai, kallon yusuf yayi yace miye tsakaninku da wannan dr din ko itace kanwar taka? Yana magana ne amma daka ji yana jin jiki, yusuf yace eh kanwata ce abba itace indo da nake fada muku, yusuf ya kalli indo yace aysha ban taba tunanin zan sake ganinki ba a rayuwa tun da nabar taraba na shigo garin abuja na fara wanki da guga ina samun albashi duk da bawai yana isana bane tunda a ciki nake ci insha, domin basa bani abinci, gashi ina dan tara wani abu dan inci gaba da karatu, kullum da tunaninki nake kwana nake tashi gashi bani da ikon inje in ganki dan gargadin da mai Gari yayi min wanda shairi aka kulla mana ni dake wani hawaye mai zafi ya zubo mai a fuska, sannan yaci gaba da fadin gidan da nake wanki wata rana ina dakin da aka bani saiga matar mai gidan ta turo a kirani koda naje dan shuru yayi na wani lokaci kafin yace ta nema in bata hadin kai naki amincewa, na nuna mata hakan haramun ne tare da dan mata nasiha shuru tayi kaman ta dauki nasihar sai ji nayi tace wlh dole saina biya mata bukatan ta yana magana yana hawaye, da dai taga bazan yarda ba tasa masu gadin gidan suka Fara jibgata da yake sodoji suke gadin gidan, summin duka sosai ba tare da tace musu ga abunda nayi mata ba , mijinta baya zama washe garin ranan sai gashi ya dawo gari nan yasa a kamani a kara min duka dan shuru yayi yana kuka Kafin yaci gaba da fadin ranan na daku sosai har da karaya suka min wai naje ina son inma matarshi fyade, haka suka daukeni suka jefani cikin daki aka rufeni ga karaya a kafa da hannu, gashi babu abinci balle ruwa indo kuka tasa sosai dan tausayin dan uwan nata, yaci gaba da fadin Allah yasa inada sauran kwana a gaba, ranan dana cika sati suka daukeni suka jefar Dani a bakin titi tare damin kashedin karsu kara ganina, Ashe duk abunda ya faru lokacin da aka jefar Dani a idon Abba ne lokacin zai koma Gida nan yasa driver dinshi ya faka, dan a zaton shi yan yanka kaine suka kamani sukayi tsafi Dani amma ganin ina numfashi yasa suka kamani shida driver dinshi suka kaini asibiti nan Dr suke ta fada akan ya za’a bar mutum ya karye har a barshi Ya dauki lokaci ba’a daurashi ba, nan abba yaita basu hakuri, Dr ya fadama abba idan akayi daurin Allah yasa yayi abba yace dan Allah suyi ko nawa ne zai biya amma daurin yayi kyau, nan Dr suka ce babu damuwa gobe za’ayi, abba ya tausaya min ranan shiya koma Gida shi daya driver dinsa yasa ya kwana dani, washe gari sai gashi da matarshi da yarsu sunzo lokacin har an fara min daurin nasha wuya sosai lokacin harna gwammaci in mutu, haka akayi daurin na koma gidan abba ina zama ana jinya na, yarinyar abba wacce ita daya ya mallaka zaliha kullum tana dawainiya Dani ita da ummi, nayi zaman jinya sosai lokacin da aka kwance ni hannun ya gyaru amma kafar akace akwai matsala sai an sake min aiki, haka aka sake min wani aikin aka sa karfe a wajan nasha wuya sosai lokacin har zan iya cewa gwara na farkon ma, na jinyatu sosai, kuma duk wannan zaman da nakeyi a gidan abba bai san ko daka ina na fito ba, tunda ya tambaye ni iyayena nace mishi sun rasu bani da kowa, haka naita zama ana jinya Na, har Allah yasa na warke, lokacin ne nace zan tafi domin inzo in nema kudi inje inga yanda kike ciki koda kuwa za’a kashe ni tunda a lokacin na cire rai da duniya dan nasha wuya, Abba ya hanani tafiya inda ya nemi yasan daka garin dana fito ban boye mai komai ba na fada mishi harda abunda akamin lokacin daya sameni, nan ya tausaya min yace kar inje garin namu yanzu in zauna na wani lokaci a nan, haka naita zama yana sani cikin harkan kasuwancin shi na canji da saida motoci ganin yanda na rike Mai amana gashi na iya kasuwanci yasa ya kara sona gashi Mace daya Allah ya bashi bai kara haiyuwa ba yasa ya turani london karatu inda na karanta kasuwanci a nan muka hadu da yazeed komai tare mukeyi yazeed yayi min taimako sosai wanda ban san damai zan saka mishi ba, dan ya wuce abokina ya zama dan uwa Na, shekara uku na dawo Gida, cike dason inje in ganki lokacin dana dawo abba yaban jari sosai inda muka hada da yazeed duk da kudinshi yafi yawa ninkin nawa wajan uku, amma idan aka samu riba biyu yake rabawa yaban rabi shima rabi haduwan da nayi da yazeed yasa na samu kudi sosai domim bashi da mugunta ko kadan samun irinshi sai an tona….TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      150to155

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Dan shuru yayi sannan yaci gaba da fadin lokacin da naje taraba direct gidan Mai gari na nufa lokacin bai ganeni ba, saida na mishi bayani yayi mamaki kwarai dagaske tare da bani hakuri akan abunda ya faru, nan yake shaidamin kinyi aure ya bani labarin yanda abun ya kasance nayi takaici lokacin sosai haka nabar garin ba tare da naje Gida ba, domin nasan har yau babu abunda ya canza daka zuciyar kawu akan kiyayyar da yake mana, duk da mai gari ya fadamin wanda kika aura hankalina bai sa ya kwanta ba lokacin saida nayi bincike sosai akai naji dan sanyi kullum ina da burin inje in ganki amma babu dama domin shiga gidan governor ba abu bane mai sauki, haka na hakura duk da a lokacin inda na fadama abba zaisan yanda za’ayi in ganki amma sai nayi shuru nabar abun a raina, ana cikin haka abba yaban auren zaliha muka tafi london saboda karatun ta, inda nima naci gaba da masters dina a yanzu haka mun kammala ta haiyu yau kwana biyar jibi suna, indo cikin muryan kuka tace gskiya yaya yusuf kasha wahala a rayuwa sosai amma Allah da yake mai rahma ne saiya hadaka da masu tausayama, ta Kalli abba dake zaune tace Allah ya saka maka abba samun mutum irinka zaiyi wuya a rayuwa Allah ya baka lafiya, duka Suka amsa da ameen, sannan ta kalli yazeed tace yaya yazeed kaima Allah ya biyaka, murmushi yazeed ya mata, sannan ta kalli ummi tace ummi Allah Ya saka muku da gidan Aljanna, tashi tayi da sauri ta dauki yaron yayan nata dake hannun zaliha, Tana kallonshi cike da kaunar yaron dan uwan nata, tace anty zaliha yaron da yaya yake kama zaliha murmushi tayi tare da fadin kai sister wannan son kai haka, dariya duka suka sa, yusuf yace sister yanzu a ina kike yaranki nawa? Dan shuru tayi tare da hawaye tace yaya yusuf bani da aure yanzu, yace mijinki fah maiya faru? Nan ta bashi labari da irin abubuwan da suka faru tun daka kauye har haduwanta da Abdul da irin taimakon daya mata shida Mum, amma ta boye musu irin abunda A Majeed ya mata sai dai tace sun rabu ne a bisa kaddara wanda haka Allah ya tsara yazeed jin haka yasa ya saukar da ajiyan zuciya wanda tun sanda yaji yusuf yace an Mata aure ya shiga damuwa, yusuf yace gskiya sister kema kin hadu da mutane musu kirki tabbas na Allah basa karewa duk da akwai marasa kirki amma Na Allah sunfi yawa marasa kirkin kadan ne,sai dai Sunfi kaurin suna, yau ina cikin farin ciki mara misaltuwa daya sake hadamu, indo ce ta tashi tare da fadin Bros inaga zan tafi sai gobe zanzo, kallonta yusuf yayi tare da fadin sister har zaki Iya tafiya kibar ni Ai bazan yarda da hakan ba, zadai kije ki dibo kayanki ki dawo Gida na, sannan Kafin ki dawo zanje inyi musu godiya duk da nasan kalman godiya tayi kadan, sai a lokacin ummi tayi magana tare da fadin haba yusuf ai hakan inaga ba daidai bane ace lokaci daya tabar su, ai hakan ba adalci bane, abba yayi gyaran murya shima yace hakane ka barta tayi shawara da kanta Akan abunda ya dace tayi, yusuf yace shikenan abba, indo tayi dan murmushi tare da fadin Bros yaron Mum ne bashi da lafiya nan ta basu labarin yanda ta fito ta barsu, yusuf yace subhanallah Allah ya bashi lafiya kije kiji yanda ake ciki gobe nima zanzo insha Allah, yazeed ne ya tashi shima Amma ranshi a dan jagule dan ya gane A Majeed shita aura suka rabu kuma gashi Tana wani nuna damuwa akanshi dan baida lfya… Yusuf ne ya katseshi da fadin kaima tashi kayi, yace eh nan sukai sallama indo da yusuf da yazeed suka fita, yusuf yace ya ajiye indo a Gida plz baya son barin abba shi daya hakan akayi motar yazeed ta shiga bayan sunyi exchanging number da dan uwan nata, Tana gaba yazeed na tuki yana ta dan janta da hira sama2 take bashi amsa har suka karaso inda ya nemi ta bashi number dinta shima bata musa ba ta bashi sannan sukai sallama ta shiga Ciki.

Kai tsaye falon gidan ta shiga babu kowa, haurawa sama tayi bata ga kowa ba, dan haka ta kira Mum bugu daya ta dauka tare da fadin aysha…..  Indo tace Mum na dawo ban ganki ba, Mum tace aysha wlh gani gidan A Majeed tun dazu muke fama dashi akan muje hspt yaki, kana jin muryan Mum kasan Tana cikin damuwa, wai babu inda zashi aysha na rasa gane mai yake nufi…..  Indo tace gani nan zuwa Mum, indo jiki a sanyaye ta fada toilet tayi wanka tare dayin alwala tayi sallah La’asar dan ankira tun dazu batayi ba, wata doguwar riga tasa ta fita taxi tahau bata jira driver ya kaita ba kai tsaye gidan aka nufa da ita, jiki a sanyaye ta fita taba mai mota kudin, tayi wajan minti uku Tana dan tuna abunda ya faru baya a cikin gidan hawaye ne ya silalo mata tasa hannu ta goge ta nufi Gate din Tana bugawa kirjinta nata dukan uku2,mai gadi ne ya leko duk da bawai ya santa bane ya bari ta shiga, a falo taga dady yasa hannu akai alaman damuwa, indo ta gaidashi cikin sanyin jiki, yace aysha sannu tare da fada mata Mum na ciki direct dakin ta shiga wanda yau ne ta taba shiga duk zamanta a gidan a baya, Tana bude kofar ta hangoshi kwance akan gadon da alama bacci yakeyi daka shi sai singlet Da 3quater jeans ya rame lokaci daya hannunshi an makala mai drive, wani hawaye ne ya zubo mata a fuska lokaci daya tare dajin tausayin shi, dai2 lokacin Mum ta waigo tace aysha karaso mana, karasa shiga tayi tare da fadin Mum ya jikin nasa? Mum tace toh da sauki dai na musulunci, tunda muka zo muke ta fama muje asibiti yaki yarda wai mu barshi kawai….. Hawaye ne ya zubo ma Mum cikin damuwa taci gaba da fadin aysha A Majeed shi daya gareni gashi a kwance yana fadin a barshi kar’a kaishi asibiti wai mutuwa zaiyi, indo itama hawayen take, Mum tace dakyar ya bari akasa mishi wannan Drive din wlh aysha A Majeed yayi mugun d’agamin hankali a yanda muka sameshi yanzu anyi mishi alluran bacci tunda akamai har yanzu bai farka ba, indo tace Mum kiyi hakuri zafin ciwo ne kawai insha Allah zai tashi babu abunda zai sameshi, mai Dr yace akai, nan mum ta bata wata takarda da Dr yace za’ayi mishi scan da test din da Dr yayi mishi da dan rubuce2 da akayi, indo amsa tayi ta fara dubawa, kallon Mum tayi kaman za tayi magana kuma tayi shuru, wata nurse ce ta shigo dakin danta duba ko ruwan ya kare, indo tace mata ta bata number din dr din nurse din ta fadama indo ta rubutu, fita waje tayi dan ta kira Dr din, dialing number din tayi bayan an dauka ta fadama Dr din koh ita wacece inda ta rokeshi akan ya tura mata sauran bayanan ta email dinta yace mata ok, jingina tayi a jikin motar Dad, Tana tunani, lokaci daya tace no hakan bazai faru ba, nasan dai matsalan matarshi ne yake damunshi duba wayanta tayi taga an tura mata dan haka ta fara karantawa harta gama, fita tayi daka gidan, bata dade ba sai gata ta dawo da leda a hannunta, Dad yana falo har yanzu yace aysha zoki zauna inada magana dake, zama tayi a gefen kujeran tare da sunkuyar da kanta a kasa, Dad yace aysha miye tsakaninki da A Majeed?  Dam taji gabanta ya fadi dai2 lokacin Mum ta fito Tana fadin aysha tashi ki shiga ciki, Dad ido yabi Mum Dashi cikin mamaki indo tashi tayi Tana mamakin mai Dad yake son Sani, bata karasa dakin ba taji Mum na fadin haba mai yasa za kayi haka, karka manta irin abubuwan da suka faru a baya nida kaina ina son aysha da abdul-majeed amma dan Allah karka fada mata karta daukemu  marasa adalci masu san kammu da yawa, duk da a yau ina cikin damuwa ga tilon dana a kwance rai a hannun Allah bazai sa ince aysha ta aureshi ba, tunda nayi hakan a farko maiya haifar koda kaji yana fadin aysha ina sonki karka manta yana cikin zafin ciwo ne bai san inda kanshi yake ba……. Indo data tsaya tana ji da sauri ta shige dakin da A Majeed din yake an cire mai drive din, yana kwance abunshi, kuka ta fara mai tsuma zuciya zama tayi a kan gadon Tana kallonshi yayi mugun ramewa sosai jin hannunta tayi cikin nashi ya rike da sauri ta kalleshi amma taga har yanzu bacci yakeyi, kallon hannun Nata tayi wanda ya rike da karfi, wani hawaye ya zubar mata mai zafi lallai Mum ta cika uwa ta Gari mai sadaukar da ran nata dan ta faranta ma bare, wani hawaye ya kuma zubar mata mai zafi dan harga Allah bataji zata Iya aurenshi a karo Na biyu domin har yanzu ta kasa cire abunda ya faru a ranta ,jin kaman yana magana Yasa takai kunnenta dan taji mai yake fada dayan hannunshi yasa ya riketa dole yasa ta kwanto a jikinshi wanda maganan da yakeyi kaman mafarki ne tunda bacci yakeyi, wani irin kasala taji ya kamata ta fara kokarin tashi amma sai taji ya kuma rikota yasa dayan hannunshi ya rungomota dakyau  kirjinta ya shiga bugawa da Sauri……..TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      155to160

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Saukan numfashin shi take taji akan fuskanta, fuskanshi ta kalla ta gefen idonta amma taga idonshi a rufe alaman dai bacci yakeyi bai san abunda yakeyi ba, dan ajiyan zuciya ta sauke tare da rike dayan hannunshi ta sauke daka rikon da yayi mata, tazo zata sauke dayan taji yana magana kadan2 saida ta saurara dakyau taji yana kiran sunanta Aysha I really love you, da sauri ta cire hannun nashi daka jikinta ta tashi ta koma kan kujeran dakin Tana mai sauke ajiyan zuciya, kanta ta kifa a kasa tare da lumshe ido anya A Majeed ba gamo yayi da aljana mai sunanta ba, wannan wani irin So ne wanda ban taba jinsa ba sai a film koh a littafan hausa, dama hakan yana faruwa dagaske mutum ya zauce akan Mace kaman yanda marubuta suke fada a littafin su, wani irin hawaye taji yana zubar mata data tuna da maganan mum, gskiya Mum ta cika uwa ta Gari Wanda irinsu kalilan ne, wata uwar zata iyasa kowa cikin kunci dan nata yayi dariya, sai gashi ita Mum dan wani takeso yayi farin ciki akan nata, A Majeed yakai namijin da duk wata Mace zatai burin aure sai dai kash matarshi tafi karfinsa dan yana mata son da baya ganin laifinta koh kadan, wani hawaye ne ya kuma sauka a kan fuskanta tunawa da yanda ya kaskantar da ita a gaban matarshi wai yar aiki ya Kawo mata, jin karan bude kofar ne yasa tayi saurin goge hawayen fuskanta tare da dago kanta, Mum ce ta shigo dakin ganin fuskan aysha yasa Mum tace aysha lafiya Kuwa?  Indo tace lafiya Mum? Mum kallon gadon dan nata tayi wanda yake bacci har yanzu dan Dr yace zaiyi baccin wajan awa 6, sannan ta maida idonta kan indo wacce take dan murmushin yake dan kar Mum ta zargi wani abu, Mum tace haba aysha ai duk wanda yaga fuskanki yasan kinyi kuka, nifa mahaifiyarki ce dan mai yasa zaki dinga boyemin damuwar ki, indo tace Mum babu komai kawai ina kukan murna ne yau naga dan uwana, Mum da sauri ta zauna kusa da indo Tana tambaya a ina? Nan indo ta bata labarin inda suka hadu, Mum ta taya ta murna sosai tare da fadin ina fata dai baza’a gujeni ba koh?  Dan murmushi indo tayi a dai2 lokacin A majeed ya farka yana mika tare dayin salati, gaba daya idonsu ya sauka a kanshi wanda shima din su yake kallo, da sauri Mum ta tashi ta nufeshi Tana fadin son ya jikin naka? Dan murmushi yayi ba tare da yace komai ba, Mum ta tashi tare da fadin bari in kira Dad dinki, indo ganin kallon da yake mata yasa ta karaso wajan gadon Tana fadin sannu ya jikin naka? Yace ai baki damu da kisan halin dana shiga bah yana maganan ne cikin murya irin na mara lafiya dake jin jiki, za tayi magana su Mum suka shigo dakin, Dad zama yayi kusa da dan nashi yana tambaya son ya jikin naka hope ka warke? Kai ya girgiza alaman a’a yace Dad bana tunanin zan warke har sai na samu abinda nake So, Dad kallon Mum yayi kalan kinga ni koh, Mum yi tayi kaman bata jiba, Indo kuma wani hawaye ne ya zubo mata wanda yasa tabar dakin da sauri, ganin indo tabar dakin yasa Dad fadin kinji dai da kunnanki koh? Mum tace dan Allah kabar wannan maganan mu nemi lafiyar yaron nan kawai, A Majeed da baisan akan me suke maganan ba yasa ya lumshe ido, Mum matsawa tayi kusa Dashi tasa hannunta a gashin kanshi wanda duk ya yamutse tana shafawa bude ido yayi a hankali Mum tace son muje gidan mu saika zauna acan kafin muyi arranging na fita dakai waje, kai ya girgiza tare da fadin No Mum am OK ni nasan miye matsalata babu Dr din da zai bani Magani sai Dr aysha ki bari ita tai treatment dina, Mum taji tausayin dan nata sosai, duk da tasan shiya jama kanshi yanzu ga matar tashi nan da yake Bala’in so bata ma san baida lafiya ba tunda bata kirashi ba ko Mum taji ya yake ba, Mum taji zuciyanta na mata suya, mum dakyar ta lallaba shi akan yazo su koma gidanta toh, security din Dad ne suka kamashi akai mota dashi, wanda indo dake zaune Tana kuka a wajan ganin an fito dashi yasa hankalinta ya tashi, Mum tace mata tazo su tafi jiki a sanyaye tace ma Mum bari in dauko abu a ciki ledan maganin data shigo dashi ta dauko sannan ta shiga motor da Mum ta shiga wanda shima A Majeed din yana cikinta, Mum ce kusa dashi yasa kanshi a jikinta, gaba daya kamshin turaren Indo yake ji a motar duk da yasan tana ciki wani irin mugun sonta yake karaji yana shiganshi, sai dai yasan duk santa da yakeyi a yanzu bazai iya matsa mata akan ta soshi dole ba, itako indo gaba daya jikinta yayi sanyi, sai dai duk da haka bata tunanin zata iya aurenshi domin tana ganin kaman Akwai abunda yake shiryawa akanta shida matarshi tana ganin kaman So yake ta koma gidansa yaci gaba da azabtar da ita a matsayin yar aikin su shida matarsa da yake Bala’in so, wani hawaye ya zubar mata wanda tasa hannu ta goge da sauri dan kar a gani, idan A Majeed dake kwance cikin Mum yana ganin duk abunda takeyi wani iri yaji domin baya son ganin damuwanta a yanzu, bayan Sun karaso aka shigar dashi har dakin da yake da, Dad bai shigo ba dan anata kiran sallah magrib ya tsaya yayi sallah, itama indo alwala tayi dan tayi sallah,bayan ta sallame ta tsinta kanta da yima A majeed addu’a akan Allah ya bashi lafiya, bayan ta shafa addu’a ta dauki wayanta da ledan Magani tare da sauran kayan aikinta ta nufi dakin, Mum na ganinta tace yauwa dama So nake naje nayi wanka da sallah tunga gaki bari ki zauna Dashi kafin in dawo, tace toh Mum, bayan fitan mum ne indo ta matsa kusa dashi tana fadin yanzu mai kake ji yana damunka? Yace ke, tace mene? Yace ina nufin kece matsalata aysha nasan ban kyauta miki ba, kuma duk wani hukunci da kika dauka akai na kinyi dai2 dan na fusknci hukunci fiye da abunda kike min a yanzu, sai dai ke a wajanki ba komai kike daukan hakan ba, amma ni a wajena hakan da kike min…..  Dan shuru yayi alaman ciwo na damunshi kafin yaci gaba da fadin hakan zai iya shafan rayuwa na, da sauri ta kalleshi dan ta tabbatar shi dinne yake magana ganin ita yake kallo yasa tayi kasa da kanta, aysha a da ban taba tunanin zanzo wata mace ba sai zainab, amma a yanzu Allah ya jarabce ni da sonki wanda ko Dashi aka barni na horu ban taba jin kishin wata Mace ba kaman yanda nake jin naki sai yasa na bada aikin gina miki asibiti dan banso kina aiki a karkashin wani namiji sai dai ayi a naki,  dan shuru yayi yana kallonta ganin Tana hawaye yasa yace aysha dan Allah ki yafe min koh Allah muna masa laifi ya yafe mana,  jikinta yayi mugun sanyi ganin ita yake kallo ysa ta daure tace zan gwada maka VP in gani ko yyi normal, dan murmushin yake yyi tare da fadin No ki barshi kawai bana bukata, kallonshi tayi taga idonshi a rufe, tace lafiya shine komai mai yasa kake son horar da kanka da ciwo? Idonshi a rufe yace bani nake son horar da kaina da ciwo ba kece kike neman horar dani da ciwo aysha ko kin san sonki zai iya zama ajalina? Bazan iya rayuwa in ganki da wani namiji ba Face ni ba, cikin siririyan muryanta da tasha kuka tace A majeed ni nasan ba sona kake ba akwai abunda kake nufi dani amma daka yau ina tunanin zan bar gidan nan May be idan nayi nesa dakai zaka tashi, amma ina rokan ka da kabari in duba ka,jin yayi shuru yasa ta matsa kusa da gadon tare da zama akai bude ido yayi wanda suka hada ido wani irin shock taji tayi saurin kawar da kanta gefe, yace Aysha keda za kiyi nesa dani mai yasa kike son dubani? Baki damu dani ba mai yasa kika damu da ciwo na? Aysha kiban amsa? Tace saboda ina son ka warke kaci gaba da rayuwa kaman da dan Allah karka kara tambaya na ka bari in duba ka, yace bana bukatar wani koh ke ki duba ni, har sai kin fada min amsan tambayar da zan miki, jin hanunshi tayi cikin nata wani abu taji tun daka sama har kasa, kokarin cire hannunta tayi daka nasa amma ya rike sosai dan haka ta hakura ,yace aysha ki kalleni ki fadamin cewa bakya so na, indai kika min haka na miki alkawarin zan cireki a raina har abada tare dayin nesa dake, kuka ta fara mai sauti gashi hannunta yana tare da nashi babu daman tabar wajan, shiko jin kukan yake har cikin ranshi amma babu yanda ya iya dole yana bukatan amsar ta,cikin kuka tace dan Allah ka sakemin hannu, baice komai ba haka kuma bai saki ba, Dad ne ya shigo dakin ganin Dad yasa ya sakar mata hannun to tashi tabar dakin da sauri tana kuka, dakinta ta nufa ta fara hada kayanta domin bazata iya ganinsa a hakan ba kuma ba zata iya yarda da abunda yake bukata a wajanta ba duk da har yanzu ta kasa gane mai zuciyarta to yanke akai amma d Best tin shine tabar gidan cikin daren nan hakan zai bata daman ci gaba da rayuwa cikin salama shima idan yaga ya daina ganinta tasan zai tashi yaci gaba da rayuwa…. Hmmmm ku biyoni sannu a hankali TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      160to165

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Gaba daya ta gama sa abunda zata bukata cikin akwati, duk da ba komai ta dauka ba, fita tazo yi amma saita tsinta kanta da kasa bude kofar dakin, domin tunanin alkawarin da tayi ma Mum ya fado mata, bani da yawan dangi koh yara, naso ki zauna dani har abada sai dai hakan bamai yuhuwa bane dan za kiyi aure May be Ma mijin da kika aura ya hanaki hulda dani, sakan akwatin tayi tana kara rusar kuka, tunawa tayi da amsan da taba Mum, bazan taba barinki ba mum duk mijin dazan aura dole ya soki a matsayin Mum dina, zama tayi a wajan tana kuka gwanin tausayi, mai yasa talaka bashi da gata mai yasa wanda bashi da iyaye yafi shiga irin wannan matsanacin rayuwan mai yasa, A Majeed mai yasa kake son Sani cikin kunci koda yaushe mai yasa maina maka, ni nasan bawai dan kana sona dagaskiya kake wannan abunba, kanayi ne dan wata manufa taka ta daban, dan shuru tayi kaman Tana dan nazari lokaci daya kuma ta lumshe ido hawaye na zuba jin karan wayanta ne yasa to bude ido Bros taga an rubuta da sauri ta dauka tare dayin sallama, bayan ya amsa yace sister lafiya Kuwa?  Naji muryanki kaman mai kuka, dan murmushi tayi na karfin hali Kafin tace lafiya qalau bros, yace ya mai jikin da fatan dai da sauki koh?  Tace eh Alhmdlh da sauki bros, nan suka taba dan fira kafin sukai sallama akan cewa gobe zaizo gidan, yana kashewa kiran yazeed ya shigo wayanta, kaman karta dauka harya kusa tsinkewa ta dauka tare da fadin Hello, daka gefenshi shima ya amsa da fadin barka da dare, dan lumshe ido tayi tare da fadin barka kadai, yaka koma Gida? Ya amsa da lafiya dan shuru ya biyo baya, jin muryanshi tayi yana fadin aysha tun ranan dana ganki Allah yasa min sonki a raina, sai dai kuma a lokacin baki bani lokaci ba dan kin nuna kina sauri, amma haka zuciyata taci gaba da tunaninki duk da ban san inda zan kuma ganinki ba, sai dai nabar ma Allah komai sai gashi kuma ya kara hadamu cikin sauki wanda ina fata wannan karan zai zama shine hanyar da zamu kasance har abada, domin dai ni bada wasa nazo ba, dagaske nake aurenki zanyi sannan bana son ya dauki Lokaci mai tsawo, amma fah inkin amince dani, dan shuru yayi alaman yana jiran amsa, kanta ne ya kulle tama rasa abunda zata ce mai jin muryanshi tayi yana fadin ban samu karbuwa bako? Tace a’a yaya yazeed na amince Allah yasa hakan shine alkhairi, cikin jin dadi ya amsa da ameen, tare da fadin insha Allah zaki farin cikin kasancewa mata2 sannan dan Allah inaso kar aja da tsawo inaso ayi komai nanda wata biyu, bata iya cewa komai ba dan tama rasa abunda zata cemai tadai yardan mishi ne kawai badan tana sonshi ba ko Tana jin wani abu a kanshi ba, sai dai auren nashi zaisa tabar gidan nan gaba daya hakan zaiba A Majeed daman tashi tare da wargajewar wani abu da yake nufi a kanta, jin tayi shuru yasa yazeed ya kira sunanta tare da fadin gobe zanzo sai muyi magana, tace Allah ya kaimu tare da kashe wayan, Mum ce ta shigo dakin ta ganta a bakin kofa ga akwati a gefenta, kallon akwatin tayi sannan ta Kalli indo wacce fuskan ta tayi ja ga idonta duk ya kumbura dan kuka kun san farar Mace, Mum tace aysha lafiya kuwa? Maiya sameki wannan akwatin fah? Badai kina nufin Zaki barni bane,? Wannan tambayar duk a lokaci daya Mum ta mata shi, indo gaba daya kunya ya hanata magana dan bata so Mum ta shigo dakinba ba tare data maida komai wajanshi ba, mum ta tsugunna tare da kiran sunan aysha tace aysha mai aka miki da zakiyi irin wannan danyan aikin, koh wani ne ya bata miki rai? Indo kuka ta kuma saki tare da fadin Dan Allah mum kiyi hakuri wlh na rasa abunyi ne, gaba daya komai ya jagule min Mum dan Allah karki min wani fahimta ta daban….  Kuka yaci karfinta dan haka tayi shuru ba tare data karasa abunda tayi niyan fada ba, Mum janyota tayi jikinta Tana shafa mata baya tare da fadin aysha na fahimce ki, amma mai yasa ba zaki iya fadamin abunda yake damunki ba, saiki yanke hukunci dakanki? Cikin murya mai sanyi tace Mum A Majeed yana son kara bata min rayuwa Mum……  Shuru tayi dan tunawa dawa take magana, jin muryan Mum tayi Tana fadin aysha kiyi hakuri A Majeed bai isa yasa kiyi abunda baki niya ba, bashi da iko akanki, sannan ba zamanshi kike ba, kiyi shuru ki daina damuwa da komai kinji, bazan bari ya kara miki wani magana makamancin hakan ba, sannan idan kina da wanda kike So ki bashi dama ya fito kinji? Ido kasa amsa ma mum tayi dan gaba daya jikinta yayi sanyi, tare dajin kunya yau gashi Tana nuna bata son jinin Mum, wani hawaye mai zafi ya zubo mata sai dai hakan bazai sa ta canza ra’ayi ba, dan tasan bawai sonta yake ba, yaudara ce kawai irin tashi, shida yake da zee mai zaiyi da ita, gata yar masu arziki nida ba yar kowa ba, bazan iya kishi da itaba …. Wata zuciyar tace mata sai kace ba Mace ba, ai indai Mace ce ko wacece zaki iya zaman kishi da ita, ido ta lumshe ba tare data gamsu ba, Mum ce ta katse mata tunani tare da fadin tashi kije kiyi wanka ki sauko kici abinci, tashi tayi ta nufi toilet Mum kuma tabar dakin, ta nufi dakin dan nata dan taga ya yake ciki.

Mum bayan ta shiga dakin taga dady a kusa dashi yana dan mishi fiffita duk da akwai AC a cikin dakin, amma zufa yakeyi, cikin damuwa tace zafi yakeji? Wajan gadon ta nufa taga yanda yake zufa, hannu tasa a fuskanshi Tana share mai zufan fuskan nashi, tare da fadin son, idonshi dake lumshe ya bude, ya kura ma mum din ido, gabanta ne ya fadi ganin irin ramar da yayi lokaci daya, tace mai yake Damunka? Dad yace wannan wani irin tambaya ne fatima bayan kin san komai, tace dan Allah ka bari yaban amsa domin inaso inji da bakinshi kuma cikin hayyacinshi, Dad shuru yayi amma ranshi a bace yake dan gaskiya abun yana matukar damunshi wai tilon dan nashi ne yake kwance babu lafiya gashi yaki bari a kaishi asibiti, duk da ya bayyana matsalanshi amma Mum tana nunawa kaman bata damu ba, lallai komai ya samu danshi laifin Mum ne…. Jin muryan A Majeed ne ya katseshi da yake fadin Mum babu abunda yake damuna Just kawai ina son inbar kasar jibi shine kawai nake So, Dad yace son indai zaka cire komai a ranka a gobe ma zaka sami flight, yace yes Dad plz inason fita london, I need to rest for some month , Dad yace shikenan amma sai kamin promises zaka ga Dr a can? Yace I promise Dad, cikin jin dadi Dad din yace shikenan saika shirya,gobe 6 in d morning zaku tashi, inda badan dare yayi ba da yau zaka tashi, A  Majeed yaji dadin hakan duk da zuciyarshi a tunkushe yake yana son ganin aysha ko zaiji dadi sai dai bazai nemeta ba dan Yana son yayi nesa da ita ko hakan zaisa ya Manta da ita, dan lumshe ido yayi yana mai jin zafi a ranshi, Mum kam kasa magana tayi gnin Dad ya fita daka dakin yasa ta kalli dan nata tace mai zaka ci son?kai ya girgiza alaman babu komai, Mum tace haba son ya zaka zauna kana ciwo kaki cin komai, plz tell me mai kke son ci? Yace aysha plz am o…. Bai karasa ba yayi shuru dan jin sunan daya kira Mum din nashi dashi, Mum dan murmushi tayi tare da tashi ta fita daka dakin, tashi yayi dakyar ya nufi toilet, ya dade a ciki sai gashi ya fito da towel a kanshi alaman dai yayi wanka, yana tafiya kaman babu jini a jikinshi domin gaba daya babu kwari a jikin nasa, jallabiya yasa, tare da zama akan gadon kayan aikin indo ya gani da sauri ya kawar da kanshi Dan baya son gninsu dan So yake ya manta da komai nata, duk da yasan hakan ba abu bane mai yuhuwa, kwanciya yayi ta baya yana ganinta a idonshi yana cikin haka Mum ta shigo dauke da tray a hannunta ajiyewa tayi akan Side drawer, tace son tashi kaci abinci koh kadan ne kaji? Tashi yayi yana kallon Mum sannan yace Mum bana jin yunwa, tace Abdul-majeed ka daina horar da kanka, wannan abunda kakeyi bashi zai kawo maka karshen wannan matsalan da kake ciki ba, kallon Mum yayi da sauri ta daga mai kai alaman eh, zaiyi magana tace mai Ya Isa haka tare da bashi Tea din data Kawo mai da snack, amsa yayi ya fara ci tare da tunanin mai Mum ke nufi, suna cikin haka Abdul ya shigo dkin hankali a tashe, ganin A Majeed din yana shan Tea yasa ya sauke ajiyan zuciya tare da fadin kama warke Ashe, karaso wa yayi ya gaida Mum, inda take tambayanshi kwana biyu yace wlh Mum naje Kaduna ne amma wannan karan anyi nasara komai ya daidaita yayar yarinyar Ashe wai Tana tsoran bata mai kudi ne saboda gudun wulakanci dakyar dai aka shawo kan matsalan, ni da farko ma nasha ko rikonta take Ashe yayarta ce, Mum tace toh Alhmdlh yanzu saura musha biki kawai, dariya yayi ba tare da yace komai ba, Mum fita tayi ta barsu,Abdul matsawa yayi kusa da abokin shi, yace kai Man irin wannan rama haka gskiya kaji jiki fah, wai maike damunka ne haka? A Majeed yace aysha, Abdul yace aysha kuma? Kai ya daga mai alaman eh, Abdul dariya yayi tare da fadin wai mai kake nufi ne? Kodai ka sami wata chicks ne, dan tsaki yayi kalan na mai jin jiki, kafin yace kana da matsala Abdul wace aysha nake nufi inba matata ba, abdul yace wannan yar kauyen? Cije baki A Majeed yayi tare da ajiye Cup din Tea din ya kwanta, Abdul yace haba Man magana zaka yi, A Majeed cikin murya irin name jin jiki yace, Abdul joke apart ina son aysha sosai duk wannan abunda nake ciki saboda sonta nake cikinsa, ban taba jin wani abu akan wata Mace ba kaman yanda nakeji akanta, Abdul nayi nadaman abubuwan dana mata duk da a lokacin wani abun bada san raina nake mata ba, dan Allah ka tayani bata hakuri dan nasan zata iya jin maganan ka, bance lallai saita soni ba amma ta yafe min,ta cire komai dana mata a ranta duk irin son da nake mata bazan matsa mata akan dole saita soni ba, dan bazan iya auren macen da bata jin wani abu a kaina ba, am not dat selfish, koda sonta zai kashe ni bazan matsa mata dole ba dat Why na yanke decision akan inbar kasar ko zan manta komai duk da nasan ba abu bane mai sauki, but I will try, domin gaba daya bata san ganina kaman yanda na fahimta indai nesa da ita da zanyi will make her happy, I will do anything just to c her happy …. Dan shuru yayi domin jin zafin da kirjinshi yake yi, Abdul ne ya tabashi tare da fadin karka damu Man zan mata magana and I knw baza tayi rejecting dinka ba, abunda naji dadi shine ka fahimci abunda Mum take nuna maka akan aysha din,wanda tun farko kaki ka fahimta saida lokaci ya kure but i will try inga komai ya koma normal insha Allah…….  Toh fah ku biyoni kuji ynda zata kaya…TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      165to170

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Dan murmushin karfin hali yayi tare da fadin I wish so, abdul yace plz Man kabar maganan tafiyan nan, I promise zan Kawo ma karshen duk wani damuwanka, but saika tashi ka fara komai kaman da zaka sami aysha tunda naga ka fada sosai, wani irin kallo A Majeed yayi mishi tare da fadin bana tunanin haka domin she really hate me, abdul yace kiyayya na zama so ai kaima gashi ka gani tunda gashi ya faru akanka, lumshe ido Am yayi tare da fadin hakane but sai nake ganin kaman……  Abdul ya katse shi da fadin karka damu just kawai kayi Cancel tafiyan ka, A Majeed girgiza kai yayi tare da fadin No Abdul dole inyi tafiyan nan gobe, Abdul Shuru yayi yana tausayin abokin nashi, tashi yayi tare da fadin bari ni zan wuce sai gobe zan shigo, A Majeed yace flight din 6 zanbi zadai muyi waya kawai, abdul yace tare da kokarin fita daka dakin muryan A Majeed yaji yana tambaya ya wannan yarinyar da kake so da ta taraba dinnan, Abdul wani iri yaji amma saiya dake yace tayi aure, yana fadin haka yabar dakin, A majeed gaba daya ya kasa bacci sai juye2 yakeyi tare da tunanin indo wanda yayi kokarin ya cire amma ya kasa.

Haka itama ta gefen indo din sai kaiwa da komowa take a daki, tama rasa maiya kamata tayi, gaba daya kanta ya kulle zuciyarta ta tunkushe da tunani kala2 tama rasa maiya kamata tayi,wani hawaye taji yana zubar mata tare da fadin Allah sarki mahaifiya mai dadi yau inda mahaifiyata na raye da itace zata zamemin abokiyar shawara amma gashi yanzu na rasa mai bani shawara, kwanciya tayi akan gadon dakin tare da lumshe ido, magananta da yazeed ne yake ta dawo mata, a halin yanzu Tana da bukatan hutu wanda Tana ganin yin auren ne zai Kawo Mata Karshen duk wani wahala da take ciki, sai dai kuma Tana da bukatan ta auri wanda take so yake sonta, mai yasa nayi saurin amsa ma yazeed bayan banajin wani abu a kanshi, wata zuciyar tace haba aysha karki Manta da cewa kin amince mai kuma ya yarda da hakan, kodan abunda yama dan uwanki aiya kamata ki soshi, wani hawaye taji yana zubar mata yanzu idan na amince mishi A Majeed fah ya zanyi Dashi? Anya banyi butulci ba, zuciyarta taita tuno mata abubuwan da suka faru a baya, gskiya Mum uwace da babu irinta a kullum ina neman hanyar da zan saka mata da irin abubuwan da tamin na alkhairi a rayuwa na, nan zuciyarta tace inko hakane ki yarda da bukatan danta domin shine babban alkhairin da zaki mata sannan hakan zai sata farin ciki, kaita girgiza tare da fadin Mum hakan bazai sa taji dadi ba tunda ta nuna itama bata sona dashi, kuma ta fadamin hakan, lokaci daya kuma ta tuna maganan da taji Mum da Dad nayi inda Mum ke fadin nima harga Allah ina son aysha da A Majeed sai dai hakan bamai yuhuwa bane, kenan Mum tana sona Da A Majeed? Toh mai yasa ta nunamin a gabana bata sona dashi? Gaba daya kanta ya kulle tama rasa abunyi, ranan dai bacci barawo ne yayi gaba da ita.

Washe gari kaman yanda Dad yace haka akayi, A Majeed ya danji karfin jikinshi duk Da zuciyarshi a tunkushe take dason ganin aysha, amma babu yanda ya iya dole ya tafi, itama ta gefenta tunda ta tashi da asuba tayi sallah, sai tunani take tayi kala2, tsintar kanta tayi dason zuwa kitchen dan ta hada breakfast tasan A Majeed zaici indai tayi, tunda ta lura bawai wani abinci yake ciba, koba komai dan Mum ne dole in nuna kulawa Na a gareshi, ta fito zata kitchen shima a dai2 lokacin ya bude kofar ya fito, nan suka tsaya kallon juna,yaji dadin gnin nata, shine ya fara kawar da kanshi, ganin haka yasa taji wani iri, a hankali ta furta ya jikin ka?mai makon ya bata amsa sai matsowa da yayi gab da ita yana mata magana kaman mai rada amma ba radan bane kawai ciwo ne yasa muryan ta dashe, yace aysha am leaving now I just want to see you happy am leaving d country just to c you happy, sai dai all I want u to knw is…… Dan Shuru yayi kaman yana nazarin abunda zaice dan ja baya yayi kadan tare da kallan fuskanta idanta a lumshe kura mata ido yayi tare Da yaba duk wani abunda ke jikinta yace just keep dis on ur mind dat I love you, my life is nothing without you, yana fadin haka yabar wajan a falo ya tarar da Dad shida Mum daka gani jiranshi suke yana tafiya ne kaman mai rangaji, Mum tace son dan Allah kabar wannan tafiyan ka zauna anan sai kaga Dr, dad yace a’a ki barshi yaje nama Dr magana idan ya sauka ma direct hspt zashi, har airport suka kaishi tare da daya daka security din dady suka tafi, babu abunda ya tafi Dashi na kaya dan yace acan zai siya, saida jirginsu ya daga su Mum suka dawo Gida, indo koh tunda taji ya tafi zuciyarta ta kara tunkushewa mai yake nufi ina zashi? Gaba daya ta shiga wani irin hali daki ta koma jiki a sanyaye, wayanta ta dauka ta kira Abdul bugu uku ya dauka tare da fadin aysha lafiya kuwa? Tace Abdul dan Allah A Majeed zaiyi tafiya ne? Abdul yace eh, tace ina zashi? Abdul yace aysha nima ban san inda zashi ba yayi tafiyan ne dan yayi nesa dake, cikin tashin hankali tace saboda wani dalili? Abdul yace bari zanzo anjima kadan muyi magana, yana fadin haka ya kashe wayan, indo sai juyi take akan gado to maina tsare mishi da zaiyi tafiya saboda ni? Haka taita tunani har wajan karfe Tara ta kara kiran Abdul yace gani a bakin Gate fito plz banso in shigo, tashi tayi tasa hijab, sai kuma ta tsinci kanta dajin kunyan fita, domin bata san haduwa da Mum koh Dad amma hakan ta fito cikin sanda tayi Sa’a babu kowa a falon, ta fice a cikin mota taga Abdul, bude gaba tayi ta shige, bayan ta shiga ta gaidashi, amsawa yyi tare da fadin haba aysha ashe haka kike da riko ban Sani ba? Tace yaya Abdul Mai nayi?  Yace A Majeed duk ya fadamin abunda ya faru, haba aysha mai yasa bazaki iya yafe mai ba bayan ya roki gafaran ki, karfa ki manta ko Allah muna masa laifi ya yafe mana sai mune zamu ce ba zamu yafe ma wani ba danya mana abu, ko badan shiba aiko dan Mum yaci albarkacinta, aysha nasan waye A Majeed tunda kikaga ya shiga wannan halin har yana rokanki akan ki yafe mishi wlh duk abunda ya fada dagaske yake har cikin zuciyanshi, aysha ina sonki Da Abdulmajeed domin shine wanda ya dace dake koh kin san saboda sanki yasa yake wannan ciwon? Har yabar kasar nan dan yace bakya son ganinshi a kusa dake, haba aysha aiko dan Mum zaki tausaya mai shine dan Mum fah guda daya data haifa bance dole kiso shiba amma ya kamata ki yafe mai, kuka ta fara Tana fadin yaya abdul wlh na yafe mai saidai bana tunanin zan iya aurenshi a karo na biyu saboda matarshi yaya abdul matarshi bata Da imani koh kadan har yau na kasa mantawa Da abunda tamin, amma indai Mum za tayi farin ciki zan aureshi, Abdul yace haba aysha ina ruwanki Da matarshi zamanta za kiyi koh zaki bari ne ta kara miki wani abu? Sannan idan kika amince da auren Mum sai tafi kowa murna, sannan bana So ki aureshi saboda Mum dan soyayarshi zaki aureshi kunya taji tare Da dan rufe ido tace yaya Abdul na yarda zan aureshi, abdul yace Alhmdlh, Allah yasa hkan shine alkhairi wannan karan ba zakiyi dana sani ba insha Allah, nan ta bashi labarin gnin yayanta ya taya ta murna sosai inda ya bukaci ta bashi number din dan uwan nata domin ya kirashi, bayan ta bashi ta fita tare dayi mishi sallama, koda ta koma dki kuka tasa domin tunawa da alkawarin da tama yazeed, anya bazai ce ta yaudare shiba? Sai dai bata jin komai a kanshi hankalinta yafi kwanciya da auren A Majeed duk da shima din bawai Tana sonshi bne dan Mum da yayanta Abdul zata koma gidansa, cikin wannan halin Mum ta shigo ta ganta, cikin damuwa take fadin aysha Maiya faru? Kunyan Mum ne ya kara kamata cikin kuka tace Mum dan Allah ki yafe min na yarda zan koma gidan…..  Shuru tayi domin jin nauyin maganan da take son fada, Mum tace aysha gidan wa? Rufe fuska tayi tace gidan A Majeed, Mum wani irin farin ciki ne ya ratsa ta, amma saita ce mata aysha karki yanke hukunci da sauri ko dan tunanin wani abu, rayuwan aure anayi ne na har abada bawai ace yau anje an dawo ba, ya kamata ki nutsu, tace Mum har cikin raina na yanke wannan hukuncin, Tana fadin haka ta tashi ta shige toilet Da sauri, Mum dadi ne ya kamata, tashi tayi tabar dakin dan ta fadama mijin nata dake fushi akan Mum ce ke zuga aysha din, a daki ta sameshi yana danna śystem, zama tayi kusa dashi Tana fadin maganan bikin aysha da A Majeed sai ayi ma dan uwanta magana ayi komai cikin watan nan, kallonta yayi cikin mamaki tare da fadin ban gane ba, nan ta fada mishi yanda sukayi da aysha din tare da fadin abunda yasa kaga naki bada goyan baya bawai dan bana son auren bane saboda yarinyar zata ga bamu mata adalci ba,zata ga kaman munfi san namu akanta, kadai ga abunda ya faru a baya ,Dad yace hakane kin san ganin halin daya shiga yasani shiga damuwa, tunda ta amince yanzu Alhmdlh, sai ayi komai Mum tace hakane, Dad yace saiki amso min number din dan uwan nata in nemeshi, Mum tace ok tare Da fita, dakin indo ta koma ta ganta itama zata fito, tace ina zaki? Yaya yusuf ne yazo Mum tace shine baki gaya zai zoba? Dama number dinshi nazo amsa, shigo dasu ciki, tace toh Mum, koda indo ta fita ta ganshi tare da yazeed jiki a sanyaye ta gaidasu tare da fadin su shigo yazeed idanshi akan indo yana ta sakar mata murmushi…TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      170to175

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Har cikin babban falon gidan ta kaisu, nan masu aikin suka cika musu gaba da kayan ciye2, indo sama ta haura dan ta shaida ma mum sun shigo, bata karasa zuwa wajan dakin Mum dinba sai gata itada Dad sun fito, indo cikin jin kunya take gaida Dad, ya amsa tare da fadin sun shigo? Tace eh, nan suka koma tare, Yusuf yana ganin Dad ya tashi domin girmamawa Dad ya mika mai hannu suka gaisa sannan ya mika ma yazeed dake zaune yana kallonsu, Dad cikin sakin fuska yake fadin aysha koh ban tambaya ba wannan shine dan uwanki danga kama nan sai dai kin fishi fari, dariya duka sukayi sannan Dad yace ma yusuf ya zauna mana, bayan sun zauna yusuf ya fara yima Dad godiya akan rike mai yar uwa da sukayi, Dad yace haba2 ya isa haka ai babu zancen godiya tsakanin mu, sai dai fatan daurewan zumunci muke fata ya kasance na har abada, Mum tace hakane domin a gaskiya ban san rabuwa Da Aysha dan tana da hankali da nutsuwa, yusuf yaji dadin yaban da sukema kanwar tashi yanda ya fahimci su Mum mutanan arziki ne, nan Dad yace musu bismillah naga baku ci komai ba, Yusuf ya dauki drink Ya zuba a cup tare Da zubama yazeed shima, nan Dad yaita jan yusuf da fira Mum tace ya mai jego gobe suna koh?dad yace waye ya haiyu nan Mum tace matar yusuf Dad shima barka yamai, Dad saida yaga yusuf ya kammala sannan yayi gyaran Murya, a dai2 lokacin wayan yazeed yayi ringing ya dauka tare Da fita daka falon, Dad yace ina mai bada hakuri akan abubuwan daya faru a baya na rabuwan auren aysha da mijinta, wanda rashin fahimta ne yaja hakan, amma yanzu sun fahimci juna ina mai rokan a barta ta koma dakinta, yusuf dan shuru yayi tare da kallon indo wacce take ta kasa Da kanta ganin irin kallon da yake mata yasa tabar wajan da sauri, murmushi yayi wanda a dai2 lokacin yazeed ya dawo inda yusuf yake fadin cewa babu komai tunda sun yanke zata koma gidan mijinta Allah yasa hakan shine alkhairi ya basu zaman lafiya, nan mum ta amsa da Ameen, yazeed dai bai fahimci abunda ake nufi ba saida Dad yace banso a dauki abun da tsawo danshi yana London inda So samu nema a daura auren sai tabi mijinta yusuf yace duk yanda kuka tsara koh kuma ince yanda aysha din suka tsara gaban yazeed ne ya fadi tare da shiga cikin wani irin hali, bai kara tsinkewa bama saida yaji Mum tace aida an bari ya dawo sai ayi bikin koh? Dad yace a’a baza’ayi haka ba, nan Dad ya zaro kudi cikin aljihu yace mlm yusuf ga sadakin aysha nan,yusuf yace dady inaga da an bari dan abbana zan wakilta akai yace toh shikenan kayi tunani mai kyau Allah yayi albarka yusuf ya amsa da Ameen, yazeed gaba daya ya shiga damuwa mai yasa aysha ta amsa min bayan ta daidaita da mijinta? Wani iri yaji yana ji dan haka ya tashi yace ma yusuf inka fito ina mota, sannan yama su Mum sallama ya fice,dad yace zaizo wajan abban Yusuf din, shima yusuf din bai wani dadeba ya fito inda Mum ta kira aysha dan suyi sallama, a waje ta gansu yazeed Na cikin mota shiko yusuf na waje bayan ta fito Yusuf yace amarya bakya laifi, dan rufe fuska tayi tare Da fadin kai bros, dariya yayi tare da fadin dama naso muje taraba So yanzu sai mu bari bayan bikin ki koh gwara kije kina da aure nima ga ciwon abba bana son yin nesa dashi, tace toh yaya yusuf duk yanda kace hakan za’ayi, ya jikin abba din? Yace da sauki Alhmdlh tunda ya fara shan Magani yace ya rage jin zafin jikin, tace Alhmdlh bari ya gama sha muga yanayin jikin sai ku dinga Kawo shi gashin kafa duk sati din, Yusuf yace insha Allah, yazeed dake mota gaba daya ji yayi kaman yasa ihu dan takaici, sallama sukayi da dan uwan nata sannan ta leka cikin motar tace yaya yazeed sai anjima kai kawai ya daga mata, sannan yusuf ya shiga yaja suka wuce, ta shiga Gida jiki a sanyaye su Mum na falo ita da dad, Mum tace aysha ko kina da wani abun da zakiyi na bikin naku? Tace a’a Mum duk yanda kuka yanke nima yamin, Mum taji dadi sosai indo dakinta ta wuce Tana tunani kala2 wayanta ne yayi kara alaman shigowan message, budewa tayi ganin yazeed ne ta fara karantawa *haba aysha mai yasa kikamin haka? Ko kin san yanda naji a lokacin da ake maganan za kiyi aure a gabana bayan kin amince min, dama zaki iya yaudara na aysha namiji bashi da tabbas duk da ban san maiya hadaki Dashi ba har kuka rabu tun farko ba, komawa gidan nasa bakya tunanin zaiyi miki abunda ya faru baya, aysha mijinki da zaki aura bawai sonki yake ba inda yana sonki da tun farko bai rabu dake ba kiyi tunani akai karki lalata rayuwanki a banza* wani hawaye taji yana zubar mata akan fuska lallai maganan yaya yazeed gskya ne A Majeed bawai yana sonta bane tunda a baya ya gujeta bana tunanin yanzu zai soni sai dan wani manufa nashi, lokacin da nake indo na ya nuna yana jin kyamana tare da gudu Na saida yaga na zama wani abu zai nuna min So, anya banyi babban kuskure ba na komawa gidan nasa ba, kuka ta Saki mai sauti tunawa da tayi da sulaiman mai sonta tsakani da Allah tun bata wayewa yake sonta lallai Sulaiman kaine masoyina na gskiya duk da kaima ka juya min baya, amma har gobe ina jinka cikin raina, kiran yazeed dinne ya shigo waynta kashe wayan tayi gaba daya dan bata son damuwa dan shima Tana ganin bawai yana sonta bane inda Ya ganta a yanda take da tasan koh kallonta bazai yiba, kwanciya tayi tare dajin haushin yazeed din Da A Majeed wanda tafi tsana a yanzu, zazzabi ne ya rufeta ta kudun dune a bargo, Mum jinta shuru yasa ta shiga dakin taga halinda take ciki cikin tashin hankali take tambaynta lafiya kuwa ,indo tace Mum zazzabi nakeyi cikin rawan sanyi Mum tce bari muje hspt indo tace a’a zata sha paracetamol kawai Mum dauko mata tayi ta taimaka mata tasha, sannan ta koma ta kwanta, Mum ranan taita zirga zuwa dakin dan taga jikin indo din, babu laifi zazzabin ya saketa sai dai damuwa dake damunta domin tunda taga sakon yazeed taji bata san auren da zatayi duk da dama ta amsa ne badan tana so ba, anya bazan fadama Mum na fasa ba? Wata zuciyar tace karki kuskura ma ki kara wannan tunanin, ranan dai a daki ta wuni washe Gari dakyar ta shirya suka tafi sunan yayanta ita da mum, inda aka amshesu cikin mutunci Mum tayi ma baby siyayya da yawa,haka akaci suna yaron yaci sunan abban zaliha suna kiranshi Da irfan, indo jiki a Mace domin tunani taitayi Mum duk Tana lura da ita, amma ta bari sai sun koma Gida zata mata Magna indai auren ne bata so sai a fasa, koda suka dawo Gida mum ta sameta a daki ta zabga tagumi tace aysha bataji ba har saida ta tabata, tayi firgit, Mum tace aysha anya lafiya kuwa tun jiya da akayi maganan aurenki kika shiga wani hali dan Allah aysha idan bakya son wannan auren ki fadamin karkiji komai ko nauyi Na wlh bazanga laifinki ba duk hukuncin da kika yanke, aysha hawaye ne ya zubo mata tace Mum bazan taba kin jininki ba, koda kuwa ya yake mum kinmin abunda bazan taba mantawa Dashi ba a rayuwa bani da abunda zan saka miki Dashi Mum sai addua Mum tace ya isa haka,tare da rungume indo Tana sa mata albarka.

Yau alhamis kuma a ranan dady ya hadu da abban yusuf ashe sun ma san juna nan suka tattauna bayan saduwa inda dady yake tambayan abba maiya sameshi, abba yayi ajiyan zuciya tare Da fadin wlh jarabawa ne ya sameni na tura wajan rabi Da kwata na kudina a kawo min kaya har an shigo Da kayan costume suka rike wai an sami hodar iblis a ciki gashi driver din ya gudu, nida aka Kawo min motoci maiya hadani da wata hodar iblis, nan dady ya jajanta mishi tare Da fadin zaiyi wani abu a kai insha Allah, sannan Suka fata tattauna akan maganan daya Kawo su inda abokin dady Da sukaje tare ya bada sadaki abba yace gobe juma’a sai a daura auren, hakan koh akayi, Dad bayan ya koma Gida yake tambayan Mum sunyi waya Da A Majeed kuwa yakira? Tace wlh bai kira ba gashi babu number dinshi tacan Dad dan shuru yayi tare Da fadin gobe za’a daura auren nasu, Mum tace haba aida an bari an shirya, Dad yace No gwara a daura dan harna turama mutane Da txt kawai kiyi addu’a kawai Mum tace Allah ya sanya alkhairi yasa ayi a sa’a, Dad ya amsa Da ameen.

LONDON

A majeed bayan ya sauka direct asibiti ya wuce gado suka bashi ana kula Dashi, kwananshi uku ya dawo gidan da zai sauka tare Da Magani Da aka bashi, kwata2 baya son kiran koda iyayenshi dan So yake ya manta komai amma abun yaci tura dan kullum aysha Tana ranshi ganin kaman a nan din yafi tunanin nata yasa ya fara tunanin dawowa Gida, duk da yayi alkawarin yin nesa Da ita amma yaji bazai iya ba yadai yanke gobe zai dawo Gida ko zaiga ayshan shi yaji dadi.

Yau juma’a bayan an idar Da sallah juma’a aka daura auren A Majeed Da Aysha a central mosque dake abuja, daurin auren Da mutane da dama suka shaida ciki harda president dan shima Dad ya mishi bayani kuma ya hallara sai dai addu’a zaman lafiya.
Hmmmm muje zuwa TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      175to180

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Duk wannan abunda akeyi indo bata sani ba, balle shi A majeed din,bayan Dad ya dawo Gida yasa Mum ta kira mishi indo din, bayan tazo ta gaida mum ta zauna tare da dan takurewa Mum tausayinta take dan Tana ganin kaman bata san auren ta daiyi ne kawai danta faranta musu, duk ta rame, Dad ne ya katse Mum daka tunanin data fada yace aysha yau aka daura aurenki keda abdulmajeed, Dam taji gabanta ya fadi dan batayi zaton za’ayi auren a wannan lokacin ba, toh amma mai yasa aka Mata haka? Hawaye taji yana son zubo mata tayi saurin goge idon dan karya zubo, wayan Dad ne yayi kara ya dauka tare da fadin shigo mana yusuf, bayan Yusuf ya shigo ya gaida Mum itama indo gaidashi tayi ya amsa ,bayan ya zauna ya dauko kudi tare da fadin Aysha ga sadakin ki nan tashi yayi ya mika mata, tace a’a yaya yusuf ka barshi a wajanka, yace a’a wannan ba Hakki na bane naki ne, amsa tayi tare da zubar da hawayen da take makalewa, yusuf murmushi yayi tare da yima su Dad sallama, Dad yace a’a ya tsaya suci abinci, yace Alhmdlh yana So yaje yaga abbanshi ne, sallama yayi musu ya fita, indo tashi tayi tabi bayanshi itama, har wajan motarshi, tsayawa sukayi a gefe, ya kalleta fuskan duk ta cabe da hawaye, sunanta ya kira da fadin aysha kin san zaman aure hakuri ne, basai na fada miki miye hakuri ba ke zaki fadama wani ma miye hakuri idan kin tuna rayuwanki a baya, So inaso ki kara akan nada, dan Allah sis karki bani kunya mutanan Da alkhairi suke sanki ki duba yanda suka rikeki kaman yarsu ta cikin su, dan Allah a wannan karan kema ki nuna yar halak ce ta hanyar Hakuri da kawar da zuciya nesa, sannan nasa ayi oder din kayan dakinki duk da dady yace a barshi amma nafi son a kawo miki yace yasa komai a gidan dan wani saban gidanshi ne daya gina zaki zauna keda mijin naki, kayan idan an Kawo za’a ajiye miki a wani waje, Allah ya bada zaman lafiya, kuka yaci karfinta ta kasa magana ganin tana son karyan mai da zuciya yasa ya shige mota ya wuce yana tausaya mata, saida ta goge fuskanta sannan ta shiga Gida, a falo ta tarar da mum, har zata wuce Mum ta kira sunanta ta amsa Mum tace kizo kici abinci, kaman zata ce ta koshi komai ta tuna kuma ta nufi dinning ta zuba abinci kadan taci, baifi 3spoon taci ba ta tashi ta wuce dakinta Mum duk tana kllonta amma bata ce mata komai ba, koda ta shiga daki babu abunda take sai kuka domin tana ganin kaman da wani manufa Ya aureta lallai hakan nema maganan da yazeed ya fada mata, dafarko ya nuna baya sonta yanzu kuma mai zaiyi da ita, shida yake da kaman Zainab a Gida mai zaiyi da ita, haka taita tunani tana kuka.

Karfe biyar dai2 jirgin su A Majeed ya sauka a airport, mutane suka fara fita ciki harda A Majeed kallo daya zaka masa kasan ya rame ya kara haske da kyau, kaman balaraban kasar dubai, direct wajan motarshi ya nufa dan yama driver magana akan yazo Ya daukeshi, baya ya zauna security din dady na gaba, kai tsaye gidansa yace a wuce dashi, bayan sun karasa ya shiga cikin falon duk yayi kura, dan tsaki yayi dan baya son kazanta ko kadan, fita yayi ya shiga mota yace a kaishi gidan Mum din nashi, kai tsaye gidan suka nufa, wayanshi dake kashe a hannunshi ya kunna message suka fara shigowa har zai share sai yaga na Abdul dan haka ya bude, *man ya zaka tafi baka kirani ba har yanzu kasan bani da number dinka na can, To congratulation aysha an daura muku aure yau* da sauri ya kara karanta message din yana mamaki dan yasan basa irin wannan wasan da abdul, fita yayi daka motar tare da doka ma Abdul kira inda yaji line busy, tsaki yayi tare da kara duba message din da aka turomai duk na congratulations ne akan auren nashi, da sauri ya shige cikin gidan nasu dan yasan duk amsan da yake nema zai samu a ciki, babu kowa a falon dan haka ya haura sama direct dakin Mum ya nufa, mum na zaune akan gado tana waya, taga mutum ya shigo Da sauri ta kashe wayan tare da tashi tana fadin son, sai kuma tayi shuru tana dariya da sauri ta nufeshi tayi hugging dan nata tana fadin mai yasa baka kiramu ba son? Dan sakinshi tayi tana kare mai kallo tace son ka warke kuwa? Dan murmushi yayi tare da fadin da sauki Mum, ina Dad? Tace yana dakinsa muje hannunshi rike da nata suka nufi dakin mahaifin nashi, inda suka sameshi yana danna system, shima ganin dan nashi yasa ya tashi yana yar dariya irin ta murna, yace son ya jikin naka? Yace Dad bana tunanin zan warke har sai abunda naji ya tabbata, Dad Da Mum suka Kalli juna lokaci daya kuma suka kalli dan nasu, Mum tace mai kaji, babu kunya ko tsoro yace Mum aysha wai da gaske an daura……  Shuru kuma yayi tare da sosa kai, Mum ta sakar mai harara Dad yayi gyaran murya tare da fadin zauna son, gabanshi yaji ya fadi bayan ya zauna Dad yace son hakane yau aka mayar Da aurenku kaida aysha, wani irin ajiyan zuciya yayi har iyayen nashi naji, Dad yaci gaba Da fadin son inaso kaji tsoran Allah kayi adalci a tsakanin matanka, ka daiga abunda ya faru baya, da irin abubuwan da suka faru yanzu, aure ba abun wasa bane….. Dad dai yayi mishi nasiha sosai mai ratsa jiki, inda Mum ta amshe tare da fadin ka dai san bazan yarda a wulakanta min yaba koh, wlh idan naji wani abu saina saba maka, itama ta daura da nata nasihan, inda Dad ya bashi keys din gidan da zasu zauna, ya amsa yayi godiya mum tace tarewa kuma sai nan Da sati biyu, wani iri yaji danshi harga Allah yanzu yaso a bashi matarshi, anya zan iya jira har sati biyu kuwa, Dad ne ya katse shi da fadin naji ance kana gina asibiti? Kai ya dan sosa tare da fadin eh Dad na aysha ne bana So tana aiki a karkashin wani, Dad yayi dariya irin tasu ta manya yace hakane hakan yana dakyau, tashi yayi dan yaje ya huta Mum tace Gida Zaka tafi? Yace No Mum ina nan zanje in huta ne, tace badai a gida naba koh? Yace Mum can gidan yayi kura kin san babu kowa a ciki, Mum tace matar taka har yanzu bata dawo ba? Kai ya daga alaman eh dan baya so ayi mishi maganan Zainab din dan yana ciki da ita sosai tunda ta kirashi sau daya bata kara kiranshi bah, shima haka bai nemeta ba, fita yayi daka dakin Mum ta girgiza kai tare da fadin Allah dai ya kyauta Dad yace da akayi me? Tace ina mamakin irin wannan auren Na abdulmajeed, na rasa wani irin So yake ma Zainab da baya ganin laifinta baya iya kwaba mata idan tayi ba dai2 ba, Dad yayi murmushi tare da fadin ki kawar da idanki a kansu ki masa addu’a kawai, Mum tace toh Allah yasa mu dace, Dad yace ameen.

Koda A Majeed ya shiga daki murna yaitayi wai yau shida aysha suna matsayin mata Da miji, ikon Allah, wayanshi ya dauka ya kara kiran Abdul ringing daya ya dauka, abdul yace angon aysha yaushe ka dawo? A Majeed yace yau wlh Kana ina? Abduk yace ina gidana, A Majeed yace ya kamata kazo kasa ta fito in ganta, Abdul dariya yayi sosai tare da fadin kaida matarka, A Majeed yace plz ka bari ni nasan halin kayana sai an lallaba, nasan har yanzu bata sauko ba wai ya abun ya kasance ne ma wlh mamaki nakeyi, nan Abdul ya bashi labari, A Majeed wani irin nishadi yake ji tare da fadin Abdul wlh tunda naji an daura mana aure da aysha naji kirjina ya warke kaman an cire min wani dutse,  Abdul dariya yayi sosai tare da fadin kace yau akwai cin amarci, dan tsaki A Majeed yayi tare da fadin Mum tace sai nan da sati biyu zata tare,ni yanzu kawai kazo ka daukeni muje inga gidan da Dad yaban in babu wani abu in kara dan yace yasa komai, abdul yace ok gani nan zuwa, yana kashe wayan aka kirashi da No din waje ko bai tambaya ba yasan ko wacece kaman bazai dauka ba ya dauka tare dasa wayan a speaker tace A Majeed wai labarin da naji gaskiya ne?  Yace name? Tace dagaske wai ka Kara aure?  Yace hakane Zainab amma inaso ki sani aure…….  Ta katse shi da fadin wannan karan kayi babban kuskure wlh I will teach you a lesson da koda nan gaba akace maka ga Mace tsirara ba zaka kalla ba balle kayi tunanin aurenta, duk da nasan mamanka ce ta shirya wannan makircin itama……..  Daka mata tsawa yayi tare da fadin keee Zainab u have to be very careful akan kalamanki akan mum dina, cikin fushi tace toh karya nayi ai itace ta shirya komai koda yake bani da tym din magana dakai gobe zan dawo dan haka ka shirya domin zan baka babban kyauta kaida amarya tana fadin haka ta kashe wayan..

TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      180to185

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Gaba daya ranshi yaji ya baci sosai, sai huci yakeyi kaman tana gabanshi, wata irin iska ya furzar mai zafi, tare da kwanciya ya lumshe ido yana mai jin zafin kalaman nata, tuna irin soyayyan da sukayi da yayi Zainab macece mara caring da nuna I don’t care akan abubuwa masu muhimmanci, yaushe raban da yayi kwanciyan aure da ita tun kafin ta tafi shima d way yanda ta mishi itace take bukata, wani irin zafi yake ji a ranshi miye dan na kara aure niban kasance mazinaci ba, ina da bukata sosai nima mutum ne ba dutse ba, karan wayanshi ne ya fargar Dashi daka tunanin daya lula, Abdul ne yace Man gani a waje ka fito muje, A Majeed yace ka shigo mana, idan mukayi magrib sai mu wuce, abdul yace OK, horn yayi aka bude mai gate din gidan ya shiga, a falon Gidan ya zauna babu kowa a cikinsa, A Majeed wanka yayi tare dayin alwala yayi wajan 30minute kafin ya fito wai dan ma ana jiranshi ne, masallacin kofar gidan suka nufa, sukayi sallah, bayan an idar Abdul ya gaisa da mai girma sanata, sannan suka wuce, wuse2 suka nufa inda gidan yake a kofar wani dangareren Gida suka faka,fita dukansu sukayi inda A Majeed ya bude gidan suka shiga, gidan kato ne sosai ga fulawowi gwanin Sha’awa, Abdul yace kai gidan babba ne kaman ma na mata biyu ne ginin dan kaga can gefen Da can, A Majeed yace aysha na ita kadai zata zauna ban san a takura mata, dariya abdul yayi, sannan suka shiga cikin  falon, hmm fadan kalan tsaruwan falon bata lokaci ne, kujeru kala biyu ne a falon kuma manya2 masu tsadan gaske, kofofi uku suka gani a falon, dayan kitchen ne dayan bedroom ne dayan kuma wani karamin falo ne, sama suka haura, bedroom hudu ne a saman sai falo guda daya shima mai kyan gaske komai dai yayi babu abunda ake bukata, sauka sukayi Suka zaga baya ta kofan kitchen bukka ne a wajan Da garden, ga kujerun robobi a wajan abun Sha’awa,haka shima dayan gefen komai iri daya sai dai shi ba’a sa kaya ba, Abdul yace Man gskya Gidan nan yayi sosai, A Majeed yace hakane babu abunda yake bukata, nan suka fita tare da rufe gidan, A Majeed yace plz kasan yanda zaka sa aysha ta fito in ganta, Abdul yace kai nifa babu abunda zan karayi maka na gama nawa, A Majeed yace Kana da problem Abdul, dariya Abdul yayi tare da fadin ai gaskiya na fada, bayan sun karasa gidan Mum a lokacin ana kiran sallah isha’i masallaci suka nufa, bayan sun idar Abdul ya wuce duk Da A Majeed yaso su shiga amma yaki yace akwai masu jiranshi, koda A Majeed ya shiga baiga kowa a falo ba, dakin Mum ya nufa yaga bata ciki har zai wuce dakinshi yaji maganan Mum din a dakin da aysha din take tsayawa yayi tare dayin baya, shiga dakin yayi yaga Mum din a zaune gefen gado aysha din na kwance daka gani zazzabi takeyi, da sauri ya matsa tare Da fadin Mum maike damunta indo dake kwance taji maganan nashi kaman a mafarki dan bata san ya dawo ba, dan bude ido tayi wanda a dai2 lokacin ya karaso wajan sukai ido biyu kirjinta taji ya buga, Mum tace fever ne kaman, yace bari muje hspt sai a dubata Mum tace na kira Dr yanzu zata zo, kallon aysha din ya kuma yi tare da fadin sannu ya jikin kai kawai ta daga mai ba tare data amsa ba, Mum tashi tayi tabar dakin tare da fadin bari in jira Dr din a falo, ganin Mum ta fita yasa ya zauna akan gadon idanta a lumshe jin hannunshi tayi a saman goshinta wani iri taji tare da bugawan zuciya,batai aune ba taji hannunshi a wajan wuyanta yana tabawa tare da dan daddanawa cikin muryanshi mai kama da kasala yace jikin naki da zafi sosai tun yaushe kike jin zazzabin bata kulashi ba, sai bugawan da kirjinta yake mata tare dajin haushin taba ta din da yakeyi,dan har yanzu hannunshi na wuyanta ,idanshi gaba daya yana kanta ji yake kaman ya jita a jikinshi, cire hannun nashi yayi daka jikin nata dai2 lokacin Mum ta shigo ita Da Dr, nan ta fara dan dubata tare Da fadin fever ne Dr Aysha kina Dr ya zaki bari fever ya kamaki haka baki sha Magani ba, indo murmushi kawai tayi ba tare da tace komai ba, nan taba indo Magani, sannan ta wuce Mum tace bari in hado miki tea sai kisha kafin kisha maganin, A Majeed ganin kowa ya fita yasa ya koma kusa da ita ya zauna yana mai jin tausayinta, Mum bata dadeba ta dawo, dauke da tea din, ganin A Majeed din a wajan yasa ta bashi tea din tare da fadin tashi kisha ina zuwa fita tayi tabar dakin dan taga dan nata nason nuna fitsaranshi a gabanta, ajiye tea din yayi tare da dagota ya zaunar da ita, idanta a lumshe maganar shi taji a wajan kunnenta yana fadin plz gashi kisha bude ido tayi taga yana kallonta yana sakar mata murmushi da sauri ta kawar da kanta gefe dan murmushi ya kuma saki komai tayi kyau yake mata Cup din yasa mata a baki dan haka ta fara sha, bata wani shada yawa ba, ta kawar da kanta duk yanda yaso ta kara amma taki, Magani ya bata tasha aiko Tana sha ta amayoshi kusan rabin aman a jikinshi duk da bamai yawa bane,dan bata kaunar Magani ko kadan, duk da tana cikin yanayi na ciwo saida gabanta ya fadi ganin tamai amai a jiki, amma ga mamakinta sai taga koh a jikinshi saima rudewa da yayi yana mata sannu tare da daura hannunshi a bayanta yana shafawa a hankali, ganin kaman aman ya tsaya yasa yace tashi in tayaki ki gyara jikinki, wani irin kallo tamai wanda yasa shi murmushi duk da yaso ya dake, hannunshi ta ture daka jikinta tare da tashi dakyar tafiya ta farayi kaman mai koyan tafiya ido ya bita Dashi yana jin sonta na fisgarshi, ganin ta shige toilet yasa ya tashi ya fita,daya daka cikin masu aikin gidan ya kira yace suje su gyara mata daki, sannan ya nufi dakinshi dake gidan toilet ya fada yayi wanka koda ya fito shiryawa yayi yasa jallabiya, fita yayi dan yaga jikin nata kafin ya kwanta, koda ya nufi dakin ya bude kofar a rufe ya jishi, babu yanda ya iya dole komawa yayi badan ranshi yaso ba.

Koda ya koma daki kasa bacci yayi domin tunanin halin da take ciki yaita yi, wayanshi ya dauko danya kirata, lokaci daya kuma yayi tsaki tare da ajiye wayar dan bashi da number dinta, ido ya lumshe yana mai jin takaici na rashin number din nata, gashi yanzu idan ya kira Abdul yace ya bashi sai yayi ta mishi surutu May be ma ya Tuna mai baya, haka dai ranan yaita tunani bai san Lokacin da bacci ya daukeshi ba, ta gefen indo zazzabin ya dan sauka kadan ita da kanta ta rufe kofar gudun kar yace zai kara shigo mata ile sai gashi Tana jin lokacin da ake kokarin bude kofar dan tasan ba mum bace tasan shine, sai yasa bata bude ba kuma batai magana ba, domin bata bukatar ganinshi kusa da ita dan haushin shi takeji sosai, daka ta ganshi take tunawa da messages din da yazeed yai mata wannan dalilin yasa ta kara tsananshi fiyeda nada.

Tunda A Majeed yayi sallah asuba bai dawo gidan ba, direct gidanshi ya nufa tare da wasu masu aikin daya dauko dan sumai gyaran gidan, domin yace gwara ya dawo Zainab ta sameshi a nan dan yasan ba kunya ya isheta ba zata iya cewa itama zata biyoshi gidan Mum din nashi duk da yasan Tana shakkar Mum a gabanta bata wani abun, gidan yayi mugun kura da datti haka suka share gidan tare Da cire cottons din gidan suka sa wasu ko ina an gyara yayi fes2 komai dai yana Son gyara, A Majeed ya sallamesu da kudi masu yawa tare dayi musu godiya dan gidan ya koma kaman bashi ba,ga Gida har Gida amma duk yayi kura saboda tsaban kishi ta kori masu aiki, tsaki yayi tare da shiga toilet yayi wanka yasa kananan kaya tare Da feshe jikinshi da turare tako ina, baka jin komai sai kamshi Key din motarshi ya dauka ya nufi gidan Mum, bayan ya karasa yayi horn mai gadi ya bude mai gate ya shiga a falo yaga Mum ita daya Tana breakfast gaidata yayi tare da dan sosa kai dan yana son ya tambayeta aysha amma yana jin kunya kaman tasan abunda yake tunani tace ka duba aysha kuwa? Da sauri yace a’a ya jikin nata? Mum tace da sauki, sama ya haura, mum da kallo ta bishi harya bace mata, sannan taci gaba dacin abincinta, koda ya shiga dakin indo a zaune ya ganta amma tasa blanket ta rufe jikinta daka gani dai sanyi takeji, ganin ya shigo dakin yasa ta kawar da kanta gefe tare da tamke fuska, zama yayi kusa da ita, yana kallonta, juyar da fuskanta tayi ta dayan gefen, abun dariya ma ya bashi amma saiya dake hannunshi ya daura akan kafadarta ya janyota jikinshi, tare da sa dayan hannunshi a wajan wuyanta yaji da zafi, yace aysha ko zamu hspt ne kinga jikin naki har yanzu? Bata kulashi ba sai kokarin fara jan jikinta daka nashi tayi, Amma ya riketa da kyau ta kasa janye jikin a hankali yace haba my baby plz ki tashi in tayaki kishirya muje hspt kinma sha maganin ki kuwa? Ledan Maganin ya gani a  gefe ya dauko tare da ciro maganin yaga bata sha ko guda daya ba tun wanda tasha jiya, kallonta yayi tare da fadin haba Baby ya zaki ki shan Magani? Taya zaki warke saketa yayi tare da tashi ya fita daka dakin, jim kadan sai gashi da breakfast, kallonshi tayi tare da kawar dakai tana mamakin irin abubuwan da yake mata wanda tasan tsaban yaudara ne kawai, jinshi tayi kusa da ita yana fadin gashi kici ko kadan ne, daure fuska tayi kalan ka barni dinnan, ganin bata da niyan amsa yasa ya saka mata Cup din a baki, da sauri  taja baya dan tea din akwai zafi, hannu tasa a baki tana gogewa shi kuma duk ya rude yana mata sannu tare da fadin bansan zai miki zafi ba, wani irin kallo tamai wnda yasa yayi dan murmushi, tare da fadin gashi kisha toh a hankali, bata Musa ba ta amsa dan bata son yanda yake Mammane mata, kadan tasha sannan ya bata paper chicken kai ta girgiza alaman a’a, yace plz Baby kici kadan plz, kawar dakai gefe tayi ba tare da tace komai ba, magani ya dauko ya bata ta amsa Tana mai jin takaici dan bata san magani ko kadan sha tayi dan Tana ganin zai barta in tasha amma sai taga bashi da niyan tafiya, wayanta dake gefe yayi kara dauka tayi tare da fadin Hello, ban san mai aka fada mata ba naji tace ok gani nan Tana maganan ne irin namai ciwo, shiko A Majeed ido ya kura mata yana kallon ikon Allah, tashi tayi ta shiga toilet jim kadan ta fito ta dauki kaya a wardrobe ta koma toilet, bata dade ba ta fito hada ido sukayi taji gabanta ya fadi tunawa da tayi yanzu Fa mijinta ne dole saida yardanshi zata fita gashi emergency ake nemanta a hspt, kuma bata tunanin zata iya tambayan shi, zama tayi akan kujeran dakin tare da tamke fuska, kallonta yayi tare da fadin mai yasa kika zauna kuma? Ba fita za kiyi ba? Shuru tayi ba tare da tace mishi komai ba, tunanin irin yanda akace mutumin najin jiki ta farayi sai yasa har ta yarda ma zata fita duk da bata jin dadi, toh yanzu ya zanyi in fita? Nidai bazan tambaye shiba dan bana san wani abu Ya hadani Dashi ko kadan shiko A Majeed kallonta yake tayi dan yasan Tana jiran izinin shine kafin ta fita shi kuma yace bazai mata magana ba har sai ta tambaye shi, tashi yayi tare da fadin ban baki izinin fita ba har sai kin tambaye ni, dan haka in Kin shirya tambayan ina bukka yana fadin haka ya fita daka dakin……TAMBARIN TALAKA 💅*

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      185to190

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Dan murmushin takaici tayi tare da fadin what did he mean? Tsaki tayi tare da fadin abunda kake So inma bazan yiba, infact ma ai ba tarewa nayi a gidansa ba balle yamin wani iko da Isa, wayanta ne ya kara ringing ta duba taga daka hspt ne kin dauka tayi, harya tsinke, rasa abunyi tayi dan wlh bata ji zata iya ma mishi magana balle harta nemi alfarma a wajanshi, shuru tayi Tana nazari tace yes Mum, tashi tayi ta nufi dakin Mum amma bata ganta ba, gaba daya ta shiga damuwa, jin muryan Mum tayi Tana haurowa daka ji waya takeyi da sauri ta nufi hanyar, Mum na ganinta tace bari zan kira tare da kashe wayan, tace aysha ya jikin? Tace da sauki Mum, Mum tace ina zaki? Tace Mum a hspt ne aka kirani emergency, Mum tace keda bakya jin dadi aysha, Indo dai shuru tayi Mum tace toh kisa driver ya kaiki saiya jira ki gama ya dawo dake, tace toh Mum, tare da fita cikin jin dadi koh ba komai A Majeed zaisha mamaki tunda Mum ta bata izini ai bata da matsala, mota ta shiga driver yaja sukai hspt.

A Majeed na zaune a bukka yana jiranta tazo amma yaji shuru, dan dama yana tunanin hakan, dan yasan dakyar tazo, dan har yanzu yasan wannan tsanan da tamai yana nan, lumshe ido yayi tare da fadin you will love me bck soon My dear, ya dauki lokaci mai tsawo a wajan yana tunani, gaba daya dauriya yakeyi domin wlh hakurin shi ya kare yana cikin matsanacin Sha’awan Mace, duk da yana yawan yin azumi dan gudun fadawa halaka, amma dai jiki da jini, gashi Mum ta hanashi matarshi tace sai nan da sati biyu shi baiga amfanin zaman nata a nan ba, kawai a bashi matarshi inda Mum tasan halin da yake ciki aida ta bani matata, tashi yayi dan Ya koma yace tazo suje Ya kaita hspt din, koda ya shiga dakin nata bai ganta ba, fita yayi ya nufi dakin Mum dan yana tunanin ko ta shiga can, bayan ya shiga yaga bata ciki sai Mum ita daya, tace son ya akayi? Yace mum dama dama tace dama me? Aisha naga bata daki? Mum tace eh taje hspt, yace hspt kenan saida ta fita without my permission, mum ce ta katse mai tunani da fadin an kirata emergency ne nasa driver ya kaita dan nasan bata jin dadi, yace OK tare da fita yabar dakin yana mai jin wani iri, tsaki yayi tare Da fadin I will punish u for dis, wayanshi ya dauka ya doka ma Abdul kira bugu daya ya dauka Abdul yace ango kasha kamshi, tsaki ya danyi tare da fadin kasan hspt din da aysha ke aiki? Abdul yace kaida matarka ni ina……  A Majeed ya dakatar Dashi tare da fadin inka sani ka….  Bai karasa ba ya kashe wayan tunawa da yayi Mum tace ma da driver ta tafi, wayan driver din ya kira yace suna ina? Yace ina hspt ina jiran hjy ta fito nan yace driver ya fada mai asibitin bayan ya fada mai ya kashe wayan tare da shiga mota ya nufi asibitin kiran Abdul ne ya shigo wayanshi tsaki yayi tare da kashe wayan dan karya dameshi, asibitin ya nufa ya hango motar gidan nasu, parking yayi ya fita ya nufi wajan motar yace ma driver din yaja tashi ya kai mai Gida, sannan ya amshi Key din ya tafi shi kuma ya shiga wacce aka Kawo ta, bai dade ba, ta fito ta shiga gaba kaman yanda ta saba, bata ko kalli inda yake ba, tace muje, A Majeed ya tada motar suka tafi, jin kamshin turaren nashi ya mata yawa kuma dai tasan baya wajan yasa ta dan dago ta kalli driver din, ido ta bude tare da faduwan gaba, amma duk da haka bata furta komai ba dan tsoro, shima hakan baice mata komai ba har suka karasa wajan gidan da zasu zauna, fita yayi ya kulle motar yaje ya bude gate din, gabanta sai fadi yake tare da fadin ina ya kawo ni kuma?…  Shiga motar yayi yaja sukai cikin gidan, fita ya kumayi ya rufe gate din, sannan ya bude gefenta tare da fadin fito muje, wani kallo tamai na babu inda zani, hannunta ya kama tare da janyota ta fito, yana rike da hannunta har Suka shiga ciki, kallon falon ta tsaya yi, kallonta shima yakeyi sannan yace ki duba ki gani in akwai abunda kike bukata sai a sa miki, sai yanzu ta fahimci inda zasu zauna ne, mai makon ta duba gidan kaman yanda yace saita sami waje ta zauna a kan kujeran falon, kallonta yayi tare dayin murmushi, zama yayi kusa da ita yana shafa fuskanta daure fuska tayi tamau, shiko bai fasa abunda yake ba saima ci gaba da yakeyi, bata ankara ba taji hannunshi duka biyun a jikinta ya rungumota, tureshi ta farayi tare da kokarin son ta tashi, saketa yayi ta tashi da sauri tare da fadin ka mayar dani Gida, murmushi yayi yace haba My baby nan fa gidan kine, hannunta ya kamo yana fadin mai yasa kika fita ba tare da kin fadamin ba kaman yanda nace, shuru tamai ganin tayi shuru yasa ya Kara rungumeta a jikinshi yana fadin plz karki kara zuwa ko ina ba tare da yarda naba, I really love You bana son ana kallemin ke My baby, ina kishin ki sosai, irin runguman daya mata yasa jikinta ya fara sanyi duk da bawai so take ba, dan sakinta yayi yaga ta lumshe ido, bakinshi yasa cikin nata ya fara tsotsa tun Tana tureshi harta kasa dan yanda yake shan bakin kaman yana shan lollipop, gaba daya jikinta ya mutu kafanta ya mata sanyi ta kasa rikesu kasa tayi shima yayi kasan bakin nasu a manne har yanzu yayi wajan minti hudu yana kissing dinta tare da manneta cikin jikinshi,gaba daya ya fita hayyacinshi dama a bukace yake hannunshi yasa a kan kirjinta yana murzawa wani irin yanayi ya kara shiga jin karan kukanta yasa ya tsaya daka abunda yakeyi, cikin murya irin ta kasala yace plz stop it bana son kukanki, tureshi tayi duk da jikin nata ba kwari, amma ko gezau baiyi ba, yace aysha plz allow me am your husband, kukan ta kara saki ganin haka yasa ya saketa tare da tashi yabar falon mota ya shiga ya lumshe ido cikin wani irin hali, ya rasa wani irin So yake mata,yayi wajan 30mnt a mota kafin ya dawo normal, falon ya koma ya ganta a yanda ya barta Tana kuka, wajanta ya nufa tare da dagata sama yace aysha am so sorry, idan na ganki bana iya controlling kaina dauriya kawai nake but sorry bazan kara miki irin haka ba, plz, ganin bata daina kukan ba yasa yace plz ki daina wannan kukan kinga u r sick karya kara ja miki wani ciwon, share hawayen fuskan nata tayi sannan ta gyara riganta da gyalenta daya fadi ta dauka ta yafa, fita tayi shima ya rufa mata baya, motar ta bude ta shiga,saida ya bude gate sannan ya fitar da motar, tafiya suke babu mai yima wani magana ko wanne da abunda yake tunani a ranshi, har suka karasa Gida, bayan yayi parking ta bude kofar ta fita sannan ta tsaya tace nasan dama bani kake soba akwai abunda kake nufi amma Allah ya fika, insha Allah ba zaka taba samun nasara a kaina ba, Tana fadin haka ta wuce shuru yayi lokaci daya kuma ya fara dariya tare da fadin what did she mean? Am her  husband inada right inyi komai a kanta, dan murmushi ya kara saki tare da fadin I will teach her a lesson nxt Time, fita yayi ya shiga Gidan yaga Mum a falo ita daya sallama yayi mata sannan ya wuce, dan yau zainab zata dawo kaman yanda tace mishi….TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      190to195

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Gidan da Zainab din take ya nufa, a falo ya zauna tare da lumshe ido yana Tuna abunda ya faru shida Baby dinshi, murmushi yake tayi cikin jin dadi yana mata wani irin so wanda bai san lokacin daya fara yi mata shiba, lokaci daya ya kara sakin wani murmushin dan romance dinta kawai nayi amma na samu nutsu, idan ina tare da ita ina samun nutsu da nishadi, ji yake kaman ya janyo sati biyun dan ta tare a gidanshi, haka yaita tunani har Gari ya waye zainab bata dawo ba hakan bai dameshi ba dan ya kira layinta Tana ta samai Bussy daka karshe ta turo mai txt na zagi tare da fadin ina nan tafe zaka sha mamaki na, tsaki yayi tare da goge message dinma,

Indo tunda ta shiga daki take ta sauke ajiyan zuciya, tayi wajan minti 30 a zaune tana Tuna abunda ya faru tsakaninsu, tsaki ta sake tare da fadin dama abunda yakeso kenan, kuma bazan taba barinka ba, kaje ka zauna da matarka I hate you so much, tashi tayi ta fada toilet tayi wanka, Mum ce ta shigo dakin yace ya jikin? Tace Mum na warke dan fitan da nayi naji dadi, Mum tace dama wani lokacin zama waje daya nasa ciwo, gobe Maryam zata zo da Hafsat za Su fara miki gyaran jiki, indo cikin jin kunya tace toh, Mum tayi murmushi ta fita, indo duk da bata son gyaran jikin Tana jin dadi zata ga inna maryam, haka itama ta kwana cikin jin dadi.

Washe gari tunda indo ta tashi ta nufi kitchen jikinta ya mata sauki bata jin komai, girki ta fara kokarin daurawa dan taran su inna maryam, saida ta fara hada musu breakfast, ta jera a dinning, Mum ta fito cikin shiri tare da hijab a jikinta ita da dady, Dad da Fara’a yace aysha kin warke kenan ya jikin naki? Amsawa tayi da fadin da sauki Dad, tare da gaidasu cikin jin kunya, nan Suka zauna sukai breakfast, indo ta koma kitchen dan tayi girki, Mum ta shigo kitchen din tana fadin sannu aysha ke daka warkewa sai fara aiki, murmushi kawai tayi, Mum tace zamu Zaria amma yau zamu dawo, matar abokin Dad dinku ne ta rasu, indo tace Allah sarki Allah yaji qanta Mum ta amsa da ameen, munyi waya dasu Maryam sunce Sun taso kudi ta dauko taba indo tare da fadin gashi koda wani Abu zai taso, amsa tayi tare da fadin Allah Ya kiyaye hanya, har wajan mota ta rakasu saida suka fita sannan ta dawo ciki, kitchen ta koma ta daura tuwan shinkafa tare da miyan egusi, falo ta koma ta zauna tana danna wayanta, tare da kallo jefi2 saka wayan tayi a kunne tare da fadin haba Bros shine ka wani shareni koh? Yace sorry sister aiki ne yamin yawa kin san yanzu ni nake kula da komai Na abba, tace ya jikin nashi?  Yace da sauki tare da fadin jiya munje hspt anyi mai gashin kafa, tace nazo ma ai hspt din jiya, yace eyya amma maganin da kika bashi yana da kyau dan gskya yace baya jin ciwan jikin nashi kaman kwana biyu da suka wuce, tace nasan yama kusa karewa koh? Yace eh bashi dai da yawa wanda Ya rage, nan tai ta kara bashi shawara akan yanda za’a dinga kula Dashi, yaji dadi sosai inda yake tambayanta ina A Majeed? Dan shuru tayi ba tare da tace komai ba, yace sister lafiya kuwa? Tace lafiya Bros yana lafiya ta amsa ne dan kar ya zargi wani abu, sunyi dan fira kadan kafin sukai sallama, kitchen ta koma ta fara tuka tuwan, ji tayi an riketa ta baya da sauri ta saki kara cikin tsoro, dariya Ya fara yana fadin ki nutsu is ur husband, ajiyan zuciya ta sauke tare da hararanshi taja jikinta daka nashi Tana kara sauke ajiyan zuciya dan tamke fuska yayi tare da fadin baby plz yunwa nakeji, bani wani abu mana inci, cikin yar siririyan muryanta tace aiba ajiye ni kayi ba da zaka ce in baka, ido ya kura mata yana kallon yanda take magana, ganin irin kallon da yake mata yasa ta juyar da kanta, janyota yayi tare da fadin kara fadin abunda kika ce, gabanta taji yana fadi amma duk da haka saida ta bude baki tace nace aiba……  Ganin ya kura mata ido yasa tayi shuru domin Ya Mata kwarjini, dan murmushi yayi tare da fadin u r hardhearted, mai yasa bakya yafiya plz my Baby u have to change fada baya miki kyau, daure fuska tayi tare da fadin plz ka sakeni, hannunshi yasa akan fuskanta yana shafawa tare da fadin yaushe zaki zo muje ki zabi kayan akwatin ki, kin san Nafi son ki zaba da kanki, shuru tayi ba tare Da tace komai ba, saketa yayi tare da fadin plz kiban breakfast am hungry, fita yayi yabar kitchen din tsaki ta sake tare da fadin sai yayi ta taba mutane, kwashe tuwan tayi tare da sakawa a kula, fita tazo yi ta hangoshi a dinning alaman yana jiranta komawa tayi tare dayin tsaki daukan sauran abincin dasu Mum sukaci tayi dan dama ita bata ciba, chips nd egg ne da plantain, sai farfesun naman rago, a plate tasa mai ta zuba mai farfesun a cikin wani bowl, sannan ta hada mishi tea ta jera a Tray ta dauka, tunda ta fito ya kura mata ido harta karaso ta ajiye mai, a hankali ya furta thank dear, har zata wuce ya kira sunanta tsayawa tayi cak ba tare data waigoba yace aysha dan Allah kiban 5mnt za muyi magana ne kaman karta tsaya taji ya kara cewa dan Allah, komawa tayi ta zauna a gefen kujera breakfast dinshi ya fara ci harya gama, sannan ya nufi kujeran da take tare da zama a gefe, yace aysha mai yasa kike min haka?  Mai yasa har yanzu kika kasa yafe min? Aysha trust me wlh ina sonki sosai,plz tell me miye matsalanki Dani, kanta a gefe tace matsalanka Dani shine bana sonka ji yyi komai nashi ya tsaya cak, tashi tayi tabar wajan, idanshi ne ya kada yana mai zafi ga knshi dake mishi ciwo lokaci daya, dakyar ya tashi yabar gidan dan baya son zama a ciki kai tsaye gidansa ya nufa, dakyar ya karasa Gida, yana zuwa ya fada kan kujera tare Da lumshe ido, yana mai jin zafin maganan nata, har zata iya fadamai bata sonshi a gabanshi, lokaci daya ya shiga cikin wani hali mai ysa ta yarda ta aureni bayan bata sona Why? Wani irin hawaye mai zafi ya fito mai wanda bai san ya fito ba, lallai yana son aysha amma baya tunanin zaiyi posing nata akan taso shi, duk san da yake mata baya tunanin zai iya zama da ita bata sonshi amma zai fita daka hanyar ta harta tare domin su nema ma kansu mafita.

Inna Maryam tazo indo tayi murna sosai, an farama indo gyaran jiki sosai ga Magani ana bata masu kyau, yau sati daya da zuwan su inna maryam wanda rabon A Majeed da gidan shima yau sati daya bai zoba, inna Maryam Tana lura dako waya basayi, yau indo na daki inna Maryam ta shigo indo tayi Bala’in kyau gyaran Da ake mata, inna Maryam tace aysha tunanin mai gidan akeyi? Indo tayi dan murmushi wanda bai kai ciki ba, inna Maryam tace aysha inaso muyi wata magana wai miye tsakaninki da A Majeed, na dauka kun fahimci juna kafin aka maida auren idon indo ne ya ciko da kwalla tace hakane inna, inna maryam tace aysha fadamin gskiya karki boyemin komai, indo cikin kuka tace wlh har yanzu na kasa gane miye a zuciyata inna ina cikin rudani…TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      195to200

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Inna Maryam tace aysha ki fadamin mai kike ji, tace inna kin san abubuwan da suka faru a baya, har yanzu na kasa mantawa har yanzu inajin haushin abun, inna maryam tace aysha kina son A Majeed?  Indo tace inna bana sonshi domin idan ina ganinshi har gobe ina tuna baya, inna Maryam tayi dan murmushi tare da fadin mai yasa kika yarda kika aureshi toh Aysha? Tace inna bazan iya kin dan Mum ba, sai yasa na yarda na aureshi, inna Maryam tace amma shine zaki ce bakya sonshi inaga idan kika fadama Mum bakya sonshi ba zata miki dole ba, amma aysha inaso in baki shawara kiyi Hakuri ki rike mijinki hannu biyu, ki nuna mai kulawa sannan duk wani abu daya miki a baya ki Manta dashi Allah ma muna masa laifi ya yafe mana, indo tace inna nifa abunda matarshi tamin nake jin…..  Shuru tayi inna Maryam tace na fahimta aysha amma ni a ganina ki manta komai ki nuna mata yanzu bada bane kiba mijinki kulawa, karki ji tsoranta koh shakkarta, indo shuru tayi tana nazarin maganan anya zata iya kishi da Zainab kuwa? Kai dakamar wuya gskya A Majeed ya gama dani, inna maryam ce ta katse mata tunani da fadin aysha wlh kinfi matar tashi kyau nesa ba kusa ba, gaki kaman balarabiya kunyi mugun dacewa keda A Majeed, indo dan murmushi tayi tare da fadin kai inna wani kyau ni Zainab ta fini kyau sosai, inna Maryam tace wlh ko kadan kin fita kyau nesa ba kusa ba, sai dai kawai ta nuna miki ita yar president ce, sai yasa nake cewa kiyi Hakuri ki nunama mijinki so yanda zaki nunama duniya kece matar So, indo shuru tayi tabbas hakane amma bata jin zata iya hakan sai dai zata gwada, haka inna Maryam taita bata shawara da yanda zata kara sonta a zuciyar A Majeed din,  Mum takira A Majeed akan maganan tarewan indo gobe, yace yana sane nan Mum tayi ta mishi nasiha tare da fadin yaji tsoran Allah inda yaba Mum hakuri akan maganan akwati saita tare zai mata coz yafi son ta Zaba da kanta, Mum tace aita siya komai ta bayar an kawo, yaji dadin hakan nan suka taba dan fita inda daka karshe sukai sallama ya wuce baiko nemi indo ba dan yana So yayi dan nesa da ita duk da yana dauriya ne kawai shi kadai yasan mai yake ji.

Yau Saturday kuma itace ranan Da indo zata tare gidan mijinta, anyi taro a gidan Mum sosai anci ansha indo zazzabi ne ya kamata tare da zullumin mai zata je ta tarar a gidan nashi, yau rabanta da ganinshi kwana nawa gashi koh waya babu, hawaye ne ya zubo mata a ido, gskyan yazeed ne dama bawai yana sonta bane, akwai wani abu a ranshi, mutumin da yake da kamar Zainab mai zai nema wajan wata Mace, wani hawaye mai zafi ya zubar mata, a haka Inna maryam tazo ta ganta tana hawaye jin muryan inna maryam a kanta yasa ta fara goge hawayen da sauri, inna Maryam tace haba aysha mai yasa kike haka ne, kwata2 kinki fitowa kin zauna kina kuka a daki, ganin tayi shuru inna Maryam tace aysha ki daina tunanin komai karki manta shifa aure rai ne dashi in lokacin shi baiyi ba babu mai raba shi, haka zalika idan lokacin yayi sai kika an rabu ba tare da wani dalili ba, koma wanki gidan A Majeed a karo Na biyu bakya tunanin akwai wani alkhairi a cikin sa, aysha ni Na hango miki alkhairai da dama a ciki kuma kema da kanki zaki gani nan gaba, bata kofi tayi tace gashi kisha, amsa tayi ta shanye duka,tana dan goge baki dan akwai dan bauri2, inna Maryam tace ki tashi kije kiyi wanka ki shirya Mum in taga kin saki jiki zata ji dadi, tashi tayi ta shiga toilet tayi wanka, wata atamfa tasa ash colour, dinkin riga da zani duk da batayi makeup ba tayi kyau sosai, inna maryam ta shigo tace kai tubarkalla, gskya kinyi kyau, muje ki gaisa da mutane, fita sukayi tare indo tana ta gaida mutane wanda suka hallara bikin, suna ta fadin yarinyar kyakyawa ce, Mum taji dadi yanda taga ta saki jiki, haka akaci akasha karfe 7 dai2 motoci Na daukan amarya suka zo, nan su inna maryam suka shiryata cikin wani les mai shegen kyau, gashi anyi mata makeup tayi kyau sosai abunda sai wanda ya gani, dakin Mum Aka kaita dan suyi sallama, Mum tayi mata nasiha kaman yanda uwa take ma yarta,  babu abunda indo take sai kuka haka aka tafi da ita, da yake ba kawaye gareta ba ita da inna Maryam suka zauna mota daya wanda Abdul ne yake jansu, sauran motocin kuma mutane ne wanda suka zo taya Mum murna wasu ma bata sansu ba, bayan ankai gidan inna Maryam tace indo ta shiga da kafar dama da bismillah hakan tayi suka shiga cikin katon falonta wanda ya hadu ga kamshi yana tashi, dakinta akayi da ita, nan inna Maryam ta kara ba indo wasu maganin wanda zata dinga sha tare dayi mata nasiha akan hakuri da juriya, sannan sukai mata sallama suka fita indo babu abunda take sai kuka.

A Majeed sai wajan karfe daya ya shigo gidan shi daya, direct dakinta ya nufa ya bude kofar tare da sallama, a kwance ya ganta tana sheshekar kuka,jin muryanshi yasa ta dan tsagaita, da sauri ya nufi inda take tare da dagata yana fadin aysha maiya sameki, takaici tambayan nashi ya bata, in banda wulakanci tun dazu an Kawo mai mata bai shigo ba sai yanzu dama tasan za’a rina yanzu kuma yazo yana wani tambaya ko lafiya, katse mata tunani yayi da fadin kiyi hakuri aysha banzo da huri ba, plz ki daina wannan kukan kar knki yayi ciwo, ki sauko kizo muje kici abinci kafin ki kwanta, kin tashi tayi ganin haka yasa ya Fara kokarin daukanta da sauri ta tashi dariya ma ta bashi yanda tayi Amma saiya dake, bayan ta tashi ya rukota suka nufi parlour, dinning suka nufa, bayan ta zauna ya dauko plate a kitchen ya saka mata kaza a ciki guda biyu tare da dauko mata drinks a fridge da Cup, shima sawa yayi a plate ya fara ci amma ita ta kasa ci dan bata jin zata iya ci, ganin bata ci yasa ya dawo kusa da ita yazo zai sa mata a baki ta kawar dakai gefe yace plz mai dear kici mana, tunawa da irin nasihan da inna Maryam ta Mata yasa ta yarda taci shi yake ta bata harta koshi, ta kawar dakai, kuka tasa mai ya rude yana tambaya lafiya? Cikin dashewan murya tace kaina ke ciwo, yace sorry bari inje in nemo miki paracetamol ina Dashi a Gida bari inje in dauko kaman tace mai a’a ya barshi amma kan na mata ciwo sosai, fita yayi tare da nufa gidan zainab dan dauko mata paracetamol, daki ta koma ta fada toilet tayi wanka, bayan ta fito ta feshe jikinta da turare tako ina sannan tasa rigan bacci kanta keta kara sara mata dan yau taci kuka, zama tayi a gefen gadon, ta daura hannu a fuska tana tunani ko wani irin zama za suyi oho, bude kofar yayi ya shigo hannunshi dauke da ruwan roba da paracetamol, blanket ta janyo ta rufe jikinta Dashi, bata maganin yayi tasha sannan shima ya zauna ta gefenta tunda ya shigo ya ganta gaba daya ta jagula mai lisafi dauriya kawai yakeyi ga kamshin turaren ta na Dada fisganshi, a hankula ya furta kan ya lafa, kai ta daga mai alaman eh, yace ki tashi kiyi alwala muyi sallah Dam taji kirjinta ya buga, tashi yayi tare da fadin kiyi alwala kafin inzo, bayan ya fita ta tashi tayi toilet dan yin alwala, shiko dakinshi ya nufa yayi wanka tare dayin alwala, koda ya dawo dakinta yaga ta shimfida dadduma, yace tazo suyi bata Musa ba ta tashi sukai raka ‘a biyu sannan ya daura hannunshi a kanta ya fara mata addu’a bayan ya gama ya fita jim kadan sai gashi da fresh milk kaman karta Sha amma hakanan ta daure tasha kirjinta sai bugawa yake, har shima ya lura da a tsorace take, tashi tayi jiki ba kwari ta nufi gado kwanciya tayi tare da rufe ido, tana mai zullumin karya mata wani abu, hannunshi taji a jikinta ya matseta yana shakar kamshinta, tana ta danjan jikinta amma shi sai kara matseta yake, ya fara kissing dinta tun daka saman goshinta har zuwa wuyanta, gabanta sai fadi yake domin tasan indai yayi abunda yakeso shikenan zai fara mata wulakanci, bakinshi yasa cikin nata ya fara tsotsan bakin kaman yana shan lollipop tare da murza mata orange dinta shafawa yake tako ina tun tana tureshi harta kasa domin jikinta ya mutu, shiko gogan kara birkicewa yayi domin a yunwace yake gashi tare da aysha wacce yake jinta kaman ranshi, a hankali ya zare mata rigan baccin dake jikinta bakinshi yasa kan boob dinta ya fara tsotsa baka jin karan komai saina saukan nishi saida ya tabbatar ta fita hayyacinta gaba daya kafin yai mai gaba dayan wani irin ihu ta Saki mai ban tausayi amma shi gogan bai masan tanayi ba, domin gaba daya he is out of service baka jin komai sai karan sambatun shi tare da albarkan dayai ta sakar mata…….. A Majeed bai kyaleta ba har sai da yaga kaman bata motsi kun san zakin da yake jin yunwa yau ya sami abinci dan bubbugata ya farayi amma shuru cikin tashin hankali ya kunna wutan dakin yaga jini ya bata zanin gadon cikin tashin hankali ya fara kicicin daukarta.

TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      200to205

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Daukanta yayi kaman yanda ake daukan jariri, sai kaiwa da komowa yakeyi gata a hannunshi yama rude ya rasa maiya kamata ya mata, toilet ya nufa da ita tare da ajiye ta cikin bath ruwa ya zuba a ciki mai dan dumi, a hankali ta sauke ajiyan zuciya lokaci daya kuma ta rungumoshi tana fadin ka barni ka barni, wani irin tausayinta yaji ya kamashi tare da kara sonta ya kara shiganshi a hankali ya furta sorry Baby na barki, bari in taimaka miki, bude idanta tayi ta ganta a toilet, hada ido sukayi tayi saurin rufewa lokaci daya abunda ya faru ya fara dawo mata, wani hawaye mai zafi ya fara zubar mata tare da fadin maina aikata haka, mai yasa na amince na bashi jikina, shikenan yanzu zan fara ganin wulakanci kala2, jin hannunshi tayi akan fuskanta yana goge mata hawayen tare da fadin aysha plz stop it bana son kukan ki plz my baby, wani irin haushin shi taji yana kara shiganta, shiya taimaka ya mata wankan ta Danji dama2 zugin da takeji kuma ya ragu, fita yayi domin tayi wankan tsarki, bayan ya fita ta fashe da kuka mai ban tausayi tare dayin dana sani dan tasan bawai yana sonta bane kawai jikinta yake so kuma ya samu sai yanda ta gani yanzu, shiko bayan ya fita gyara gadon yayi tare da canza wani zanin gadon, dauke wannan yayi yasa a washing machine ya wanke tare da busar dashi, harya dawo dakin bata fito daka toilet ba, kaman ya shiga ya dubata amma saiya zauna tare da fadin bari ta fito, yayi wajan 10mnt zaune bata fito ba, tashi yayi ya nufi toilet din, ganinta yayi ta kife kanta da giwa tana kuka, cikin tausayawa ya nufeta tare da dagota ya daura mata towel, sannan ya fito da ita, akan gadon dakin ya zaunar da ita, wata rigan Bacci ya kuma dauko mata, ganin bata da niyar sawa yasa ya saka mata Da kanshi, sannan ya kwantar da ita tare da rufeta da blanket, har yanzu Tana jin zafi amma ba sosai ba, shima kwanciya yayi akan kujeran dakin yana mai Tuna abunda ya faru, lallai mata suna suka tara irin nutsuwan da yaji tare da aysha bai taba jiba a wajan Zainab, lumshe ido yayi yana mai kara godema Allah daya bashi aysha a matsayin mata bacci ne ya daukesu duka basu farka ba sai wajan asuba, tashi yayi tare da nufan gadon hancinta Ya danja a hankali ta bude ido, murmushi ya sakar mata tare da fadin tashi kiyi sallah, kokarin tashi ta farayi ya kamota tare da mikar da ita, Jan jikinta tayi daka nashi ta nufi toilet tana tafiya a hankali murmushi yayi shima ya fita daka dakin.

Tunda indo tayi sallah, ta kwanta bata farka ba sai yanzu, ganin haske ta wajan window yasa ta gane gari ya waye sosai, wayanta ta tuna ta tashi ta fara tafiya jinta tayi fayau kaman an cire mata wani abu a jiki, wata jaka ta dauko ta ciro wayanta ta kunna karfe 10:35 ta gani a hankali ta furta Ashe lokaci yayi nisa haka, ji tayi anyi hugging dinta ta baya dan kara ta Saki alamun jin tsoro, dariya yayi tare da fadin morning my princess, banza Dashi tayi sai kokarin kwatar jikinta takeyi daka nashi amma ta kasa, a hankali yace muje kiyi breakfast, dan nasan you r hungry,  dan tsaki tayi wanda bata san zai fito ba, murmushi yayi tare da fadin idan kina fushi bakya kyau my baby, ganin yaki sakinta yasa ta yarda ta bishi duk da rigan bacci ne a jikinta, dinning suka nufa bayan ya taimaka mata ta zauna ya hada mata tea tare da zuba mata farfesun naman rago, da chips nd egg, tea din ta fara sha, bata wani sha Da yawa ba ta ajiye ba tare data kuma cin komai ba, idanshi a kanta yace inzo in baki?  Daure fuska tayi tamau, yace I should come, ganin zai iya kuma inya taso saiya bata yasa ta girgiza kai tare da fadin na koshi, tana maganan ne kaman za tayi kuka, yace toh kici naman ko kadan, babu yanda ta Iya haka taci tana gamawa ta tashi tayi daki toilet ta fada tayi wanka, tana cikin shafa mai sai gashi ya shigo fake ya mata a bayanta tare da fadin I love you my Baby baki ta turo tare da fadin mayaudari amma a cikin zuciyanta, zama yayi akan gadon yana kallonta yanda take abu cikin nutsuwa, harta gama ta tashi ta dauki kayanta ta nufi toilet dan tasa, dariya abun ya bashi sosai, harta gama ta fito wata doguwar riga tasa na yar kanti ya mata Bala’in kyau komai nata ya zauna das a cikin rigan, ta daura wani karamin Gyale a kanta, tunda ta fito idanshi ke kanta wani irin sonta ke kara shiganshi, wayanshi ya dauko ya fara daukanta hoto hannu tasa ta rufe fuskanta, dariya yayi tare da tashi ya nufota riketa yayi tare Da zaunar da ita akan kujeran dakin, hannun nata ya cire a fuskan ya manneta da jikinshi ya fara daukansu tare, duk da fuskanta a daure yke sunyi kyau sosai, nuna mata ya farayi, kallo ta farayi ta gefen ido, sai yanzu taga hasken data kara, gskiya hafsat da inna maryam sun Iya gyaran jiki, ji tayi ya kamo hannunta tare da kiran sunanta yace aysha what r you thinking? Ajiyan zuciya ta sauke tare da kawar da kanta gefe, tashi yayi ya dawo ta inda tasa kan nata yace Baby plz Luv me back, kallonshi tayi suka hada ido tayi sauri tayi kasa da kanta, yace aysha I love you so much plz ki daina tunanin komai ki yarda dani plz, shuru tayi tana nazarin maganan shi, amma ta kasa yanke wani hukunci akan shi, har yanzu zuciyarta taki gane Maita yanke.

A Majeed yana nunama indo tsantsar So da kauna wanda a cikin tsanar da take mishi ya ragu sosai sai dai har yanzu bata jin sonshi a ranta, yau satinta daya a gidan kuma har yanzu wani abu bai kara hadasu ba, dan yana jin tausayinta duk da a matse yake yana dauriya ne kawai, yau dai ya yanke zai nemi hakkinsa dan ya gaji da hakurin, indo na falo ita daya sai gashi ya shigo da basket daka gani daka gidan Mum ne, kaman ta tashi taje ta amso amma sai taki, ajiyewa yayi akan dinning tare da nufanta yana fadin Baby come and hug me am so tired, kin tashi tayi harya karaso inda take, zama yayi kusa da ita tare da daura kanshi akan jikinta yana fadin Baby na gaji yau, jin tayi shuru bata da niyan mishi magana yasa ya fara shafa mata boob dinta yana wasa dasu, da sauri tace ka bari plz, dariya yayi tare da fadin Ashe za kiyi magana, dan turo baki tayi tare da kokarin dagashi daka jikinta, amma ta kasa, ganin haka yasa ta hakura, janyota yayi ya hade bakinshi da nata Ya fara tsotsa tun tana kokarin ta hanashi harta sake ta barshi dan bazata iyaba jikinta Ya fara weak, shiko gogan lokaci daya idanshi ya kade, a hankali ya zare mata zip din riganta da yake riga da skirt tasa, aiko gaba daya kirjinta suka bayyana, dan sometimes bata sa bra dan a tsaye suke kam, kara rudewa yayi tare da daura bakinshi a kai ya fara tsotsa yana wani irin nishi, haka itama ta gefenta tunda yasa bakinshi akan boob dinta takejin wani abu tun daka kanta har kasan yatsanta, wanda lokaci daya ta kasa gane tana wani duniyar ne, hannunshi yasa cikin private part dinta ya fara wasa Dashi, lokaci daya ta Saki wani irin kara Wanda bata san ya fito ba, tare da kara matseshi a jikinta dan tana jin dadin abun, saida ya bari ta fita hayyacinta gaba daya yayi babban aikin baka jin komai sai karan TV dana nishin su sai surutan da yakeyi, Ya dade yana abu daya kafin ya barta, kwanciya tayi akan carpet din parlour tana mai sauke ajiyan zuciya, shiko kallonta yake tayi yana kara sonta, ya dade yana kallonta har bacci ya dauketa, ganin kaman tayi bacci yasa ya dauketa yayi daki da ita tare da kwantar da ita akan gado, ya rufeta da blanket, toilet ya shiga yayi wanka sannan ya fito yana gyara gashin kanshi, wayanshi ne yayi kara dauka yayi yaga Zainab ce da number dinta na Nigeria, tashi yayi yabar dakin dan karya tashi aysha dinshi, har wayan ya tsinke ta kara kira dauka yayi tare da fadin Hello, tace Kana ina? Yace ina gidan amarya na, tace ok tare da kashe wayan, zama yayi a falon yana kallo, nocking yaji anayi da karfi,tashi yayi yana fadin waye haka bude kofar yayi yaga Zainab ce cikin riga da wando ta yafa wani shara2 Gyale, tace gani nazo saika zaba ni koh ita, janta yayi suka koma baya, tace dallah sakeni munafiki ai wlh yau sai anyita ta kare sai ka zaba Zainab ko yar iskan daka aura kaida kanka kasan nafi karfin in zauna da wata Mace a matsayin kishiya, indo dake daki taji kaman hayaniya sama2 da sauri ta tashi ta leka ta window ta hangosu cikin tashin hankali da tsorata tace Zainab, lokaci daya kuma ta Saki wani irin kuka tare da fadin abunda take gudu kenan gashi ya fara faruwa, toilet ta shiga tayi wanka amma har yanzu tanajin hayaniyar tasu muryan Zainab kawai takeji tana fadin ya barta ta shiga ciki, da sauri indo tasa kaya tare da yafa gyale, fita tayi daka dakin, direct waje ta nufa ta bude kofar amma taji a rufe alaman yasa key ta waje, zama tayi akan kujeran dakin tare da takaicin abunda yake faruwa taso data fita data Kawo karshen abun dan sai tasa ya saketa yau domin bazata zauna Dashi ba gwara ya zauna da zainab dinshi kawai dan ita bata son tashin hankali, jin shiru yasa ta leka taga dukansu basa nan, jim kadan taji ana bude kofar tashi tayi taga shine ya shigo abunda taso ce mishi saita tsinci kanta dajin nauyin fada dan wani irin kwarjini taga ya mata, yace aysha kiyi hakuri da abunda ya faru yana fadin haka ya wuce dakinshi, sai taji ya bata tausayi a karo na farko kenan, zama tayi a falon duk sai taji wani iri tama rasa abunyi.+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      205to210

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Daura hannu a fuska tayi alaman tagumi, toh ni daba ni akama haka ba nashiga damuwa ina gashi, zuciyarta ta fara mata tunani kala2 mai yasa baibi matarshi ba ya dawo nan, ina ita zainab din take? Tana cikin wannan tunanin taji hayaniya tare da buga kofar parlour din, bude kofar tayi Zainab ce tare da sodoji mata Da maza, kallo ta karema indo dashi Tana mamaki dama balarabiya ya aura, lokaci daya ta cakumi wuyan indo tare da fito da ita waje tayi jifa da ita, indo tayi tangal2 zata fadi amma sai ta fada jikin motar dake pake a wajan, Zainab tace dan ubanki sai kin koma kasarku da kafanki shegiya yar Iska can kasar taku kin rasa mijin aure ne da zaki aure min miji yar Iska, saina canza miki kamanni yau sai kin san kinyi babban kuskure nufanta ta kuma yi, ta wanketa da mari a dai2 lokacin A Majeed ya fito yaja Zainab da karfi tare da wanke mata fuska da mari itama kallonshi ta tsaya yi da mamaki abunda bai taba yi mata ba, kai zama ta iya rantsewa da cewa A Majeed bazai iya dukan ko wace mace ba domin baya daya daka cikin maza masu dukan mata, hannun indo ya kamo tare da fadin bata ji miki ciwo badai koh? Indo babu abunda take sai hawaye tare dajin takaicin abunda Zainab ta Mata yau, jan hannunta tayi daka nashi dai2 lokacin Zainab ta kuma zaburowa tare da fadin nika mara A Majeed akan wata Mace ka Manta wacece ni? Dan murmushi tayi tare da fadin u will regret it, kallon sodojin da tazo dasu tayi tace ku kama min wannan yar iskan kuyi ta duka har sai nace ku barta, matan ne suka fara tawowa alaman zasu bigeta din, A Majeed Ya daka musu tsawa tare da fadin get out of My house tare da nuna masu hanya, Zainab tace baka isa ka basu command ba sai abunda nace kallonsu tayi tace what r you waiting? A Majeed yace duk wanda ya kara wani step a cikinku sai an cire mai uniform dukansu suka tsaya domin sun rasa maganan wa za subi, A Majeed yace wlh idan kika kara wani abu I will teach you a lesson, tace kai waye baka isa kayi min komai ba kuma wlh sai sunci ubanta yau, indo zagin da ake mata ranta ya baci sosai dan idan da ta tsaya ana zaginta yanzu ba zata bari ba, nufan Zainab tayi tare da fadin ki kwantar da hankalinki indai mijinki ne gashi nan dan baya gabana tana fadin haka tabar wajan A Majeed kam ranshi ne ya baci dajin kalaman indo din, Zainab kam shewa ta Saki tare da fadin toh kaifa kaji saika sallameta ashe yar Nigeria cema shegia zabiya, A Majeed Da ranshi ya baci sosai baibi ta kanta ba ya wuce ciki, itama binshi tayi tana fadin ai wlh sai ka koro shegiyar tabar gidan nan, zama yayi a falo ranshi a bace, yama rasa abunyi gaba daya ga ranshi dake a mugun bace, tace kafa tashi kaje ka koro wannan shegiyar, indo ce ta fito ta yafa Gyale a kanta Zainab tace Yar Iska sai kinyi dana sanin auren min miji, sadaka yalla, indo ranta ya gama baci hakurinta ya kare abunda tai niyan yi saita tsinta kanta da fasawa, tace dafarko naga dai baki ganeni ba bari kiji nice dai kishiyar ki wacce aka miki tun farko yanzu kuma gani a gidanki a karo na biyu, Zainab kallon Indo take tayi tabbas sai yanzu taga kaman wani uban ashar ta saki tare da fadin dama na dade ina neman irin wannan daman da Allah zai hadani dake yanzu kam gani ga ki, cakuman indo tayi da nufin dukanta indo ta tureta da karfi tare da fadin karki kuskura yanzu bada bane sannan inaso ki sani ni aysha zan zauna a matsayin kishiyarki indai hakan kike so in kuma kin canza zan zauna a matsayin yar uwarki, Zainab tace yar uwar uwarki A Majeed tashi yayi yaja hannun Zainab yayi hanyar waje da ita ta fara kokarin kwacewa tare da fadin ka sake min hannu, saida ya kaita waje ya rufe kofar sannan ya dawo yace ma sodojin subar mai Gida fita sukayi tana ganin an bude gate din ta kara shigowa Da gudu tayi hanyar falon shima rufa mata baya yayi yana shiga yaga suna kokowa ranshi ya kuma baci ya fizge Zainab din tare da wanketa da mari har biyu wani uban ihu ta Saki tare da fadin akan wannan yar matsiyatan ka mareni abdul-majeed wlh ka mari Bala’i ke kuma ki jira dawowa Na, fita tayi fuuuuu tabar parlour shima rufa mata baya yayi tana fita ya kalli mai gadin yace karya kara barin kowa ya shigo mai Gida, yace ok sir ciki ya koma koda ya koma baiga indo ba bai bi ta kanta ba dan yana fushi da ita itama dan maganan data fada yafi mishi ciwo akan abunda Zainab tayi ni mijinki baya gabana, kwanciya yayi akan gado tare da lumshe ido yana mai jin zafin abun,  itama ta gefenta kuka take tayi tare dajin haushin shi domin tana ganin duk shine yaja komai tunda ya nace saiya aureta gashi abunda take gudu ta fara gani, wata zuciyar tace kai karki ce haka yana sonki dagaske baki ga yau harda marin Zainab yayi saboda ke ba, ya kamata ki sallama kema ki soshi domin son tsakani da Allah yake miki, lallai hakane tunawa ta farayi da abubuwan da suka faru Baya duk abunda Zainab tace baya iya ce mata No, tuna abunda inna Maryam ta fada mata tayi tace kinga yanda zaki kwace mijinki inma kina tunanin wai yana son matarshi fiye dake, ki dinga mishi abubuwan da kika san bata mishi……  Misali kaman wajan kwanciyan aure duk wani abu da kika san yana so ki dinga mishi karki ji kunya ki zama karuwa number daya sannan kisan yanda zaki dinga magana da miji kar kice waike ranki ya baci bari ki fada mishi komai ko kice bari in tura mishi txt din rashin mutunci karki kuskura namiji baya mantuwa koda kuwa kun shirya zai dinga kallanki da abun wata rana koda kun samu rashin fahimta sai kiji yana fadin ina jiran sakon cin mutunci dama Kin saba kinga mutuncin ki ya ragu, sannan keda kike da kishiya idan kika lura ranshi a bace yake kisan hanyar da za kibi danki faranta mishi rai May be itace ma ta bata mishi ran kinga idan kina sashi cikin farin ciki koda baya gidanki zaiyi ta Alla2 Ya dawo gareki sannan kullum kina cikin ranshi, sannan koda shine ya miki laifi bishi ki bashi hakuri shida kanshi zaiji kunya gobe zai rage abunda ya miki sannan karki Bari mijinki ya kwanta cikin fushi kice aishi ya sani babu ruwana yar uwa kinyi babban kuskure a duk sanda kikaga mijinki na fushi bishi ki rarrashe shi har kiga Ya sauko irin haka zaisa miji ya kara manne miki dan yana samun nutsuwa wajanki…. Ajiyan zuciya indo ta sauke tare da tashi ta shiga toilet tayi wanka zama tayi tasa wata night gown gaba daya jikinta ana gani ga wani irin rikitaccen kamshi da takeyi saida ta gama ta bude kofa zata fita saita tsinci kanta dajin Kunyan zuwa wajanshi komawa tayi ta zauna dan bataji zata iya, tashi ta karayi ta dauko hijab tasa sannan ta nufi dakin nashi budewa tayi a hankali kofar ta bude akan gadon dakin ta ganshi yayi rub da ciki, jikinta a sanyaye ta karasa inda yake a hankali tace in Kawo maka abinci?  Bai bata amsa ba sannan kuma bai dago ba, kara nanatawa tayi in Kawo maka abinci? Dagowa yayi idanshi yayi ja yace aysha mai yasa bakya sona? Aysha bani da abunda kike bugata gana mijin da kike burin aure ne? Mai yasa kika tsaneni haka? Aysha dan Allah ki fadamin miye bani dashi wanda bakya sona? Shuru yayi tare da kifa kanshi a kasa, jikinta taji ya mata sanyi ta kasa furta komai sai zuciyarta dake faman buga mata, a hankali yace aysha nine bakya so right? Plz kiban amsa yau inaso in kawo karshen komai koda kuwa Kin yanke hukuncin rabuwa dani ne, ni na yarda sonki ya kashe ni zan miki abunda kike so indai zaki farin Cik……. Karan kukanta ne yasa yayi shuru tare da kallonta ganin tana kuka sosai gashi baya son jin kukan nata domin jinshi yake har cikin zuciyarshi tashi yayi ya janyota jikinshi tare da rungumeta yana shafa mata baya cikin murya irin namai rada yace plz stop it bana son kukan ki, ki fadamin abunda kike bukata and I promise zanyi miki duk abunda kike So cikin daren nan, kukan ta kara saki mai karfi saketa yayi tare da dago mata kanta bakinshi yasa cikin nata ya fara kissing dinta sosai gaba daya jikinta yayi weak kafanta ya kasa riketa lokaci daya sukai kasa tare saida ya bari ta fada sosai kafin ya saketa dan dama yana bukatan nutsuwarta ne, a cikin kunnanta ya furta do you love me? Shuru tayi tana mai sauke ajiyan zuciya a cikin kunnenta ya kara furta tell me plz, ki fadamin miye bakyaso a tare dani, idanta na rufe ta kasa furta komai sai tunani takeyi harga Allah a yanzu dai bata jin zata iya cewa tana sonshi ko kuma tace bata sonshi ba dan zuciyarta gaba daya ta kasa gaya mata mai takeji akanshi, katse mata tunani yayi da fadin tel me plz, a hankali tace kana Da duk wani abu dana miji akeso a ganshi a tare Dashi duk abunda nake son in samu a wajan namiji kana dashi sai dai abu daya na rasa shine kai baka sona…… Bakinta ya rufe da hannunshi yace mai zan miki ki tabbar ina sonki?  A hankali tace kayi nesa dani  cikin wani irin murya yace ban gane ba, tace inaso kayi nesa dani na wani lokaci, yace ok tunda haka kikeso zanyi miki indai zaki farin ciki, saketa yayi ya tashi tare da bude wardrobe din dakin ya fara diban kayan da yake bukata yana sawa a karamin akwatin shi, tana kwance harya gama ya kalleta yace ga ATM dina tare da fada mata pin din yace duk abunda kike bukata ki dauka sannan inaso kiji tsoran Allah dan zaki cutar dani, yana fadin haka ya kama hanyar fita.TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      210to215

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Fita yayi tare da rufe mata kofar dakin, kirjinta ne ya fara buga mata da sauri ganin ya fita din, yana fita yasa akwatin cikin mota tare da shiga ya tada motar yabar gidan, da sauri ta tashi ganin ya tada mota dan batayi zaton zai fita dagaske dinba, hanyar fita tayi ko kafin ta karaso yabar gidan wani irin ihu tasa mai karfi tare da sakan kuka lokaci daya, dama nace baya sona tunda harya tafi dagaske inda yana sona bazai tafi ba, zama tayi a falo tana ta rusar kuka har kanta ya fara ciwo lokaci daya kuma taji wani irin kishi na shiganta dama nasan gidan matarshi yake son zuwa sai yasa bai musa minba ya tafi, gaba daya ta kasa rintsawa domin wani irin azababban kishin shi takeji dan tana ganin kaman yana can wajan matar tashi, wata zuciyar tace toke ina ruwanki keda ba sonshi kike ba, kai ta girgiza tare da fadin miji nane dole in damu akan komai nashi, ranan gaba daya kasa bacci tayi sai juyi take tayi a parlour har aka kira sallah asuba, kuka ta kuma Saki tare da rufe kofar parlour ta haura Sama dan tayi sallah tsintar kanta tayi da rokan Allah akan yasa mijinta Ya dawo gareta yanzu, yasa mishi sonta fiye dako wace Mace, taita addu’a tana kuka a wajan baccin wahala ya dauketa.

Shiko tunda ya fita yake jin wani iri mai yasa aysha bata sona haka, wani irin kiyayya takemin har haka, anya zata soni kuwa a rayuwa, wannan shine kaddara na ban taba tunanin zanso macen da bata sona ba, hotel ya kama dan anan yake ganin zai iya samun hutu dan baya tunanin ma zuwa wajan Zainab a wannan lokacin, shima bacci dai gagaranshi yayi gaba daya domin zuciyarshi gaba daya a jagule yake bashi da wani buri Face yau ace aysha ta amince Dashi a matsayin miji wanda take so, amma yasan hakan bamai yuhuwa bane tunda ta nemi yayi nesa da ita hakan zaiyi duk da yasan zaiji jiki sosai kuma baya iya tunanin zai iya tsawon lokaci baya tare da ita dan ganinta kawai yana sashi cikin farin ciki tare da nutsuwa, wani irin hawaye mai zafi ya zubar mai a ido wanda bai san fitar suba, bai taba tunanin zaiso Mace bayan zainab ba, yau gashi son wacce ya raina yake mata kallon yar kauye wacce bata wayeba gashi sonta na neman zautar dashi, lallai babu kyau raina halittar Allah a duk yanda yake, yasan abubuwan daya mata a baya yasa take mishi haka a hankali ya furta aysha mai yasa bakya yafiya mai yasa ba zaki iya yafemin ba, nasan nayi miki laifi amma hukuncin naki yayi tsauri da yawa wannan laifin nawa bai kai wannan hukuncin da kike min ba, kanshi yaji yana sara mai gaba daya ya rasa maike mishi dadi shiba dadi yake ji wajan Zainab ba gashi itama aysha wacce take nuna mai kiyayya baro2 haka yaita tunani har aka kira sallah yayi, bayan Ya idar ya kira Abdul bugu uku Ya dauka cikin muryan bacci yace ango kasha kamshi A Majeed yace Abdul kana ina? Yace Gida mana A Majeed yace zoka sameni inda nake yanzu plz, Abdul yace kana ina nan ya fada mishi abdul yace OK gani nan, bayan Sun kashe wayan abdul ya tashi domin zuwa wajan abokin nashi tare da tunanin mai yakeyi a hotel toh, koda abdul ya karasa dakin da yake yayi nocking dakyar Ya tashi ya bude mai Abdul da ido ya bishi ganin yanda yake tafiya, yace Man maike faruwa ne?  A Majeed bayan Ya zauna ya kalli abdul tare da fadin Mai yasa aysha bata sona? Abdul mai zan mata ta yafe min laifi na tasan cewa dagaske ina sonta? Abdul yace ban gane ba nan ya fadama abdul abunda ya faru harda wanda zainab tayi, ajiyan zuciya abdul yayi tare da fadin dafarko dai zance ka kara hakuri akan abunda zainab tayi wannan dama dole ne duk wata Mace ta nuna kishi idan aka mata kishiya sai dai ko wacce da irin nata, sannan aysha bata kyauta ba amma kayi Hakuri zan mata magana, A Majeed yace No ka barta karka ce mata komai na riga na yanke bazan koma gareta ba koda kuwa santa zai kashe ni dan Allah karka je wajanta ka barta, Abdul yayi shuru na wani lokaci kafin yace ok yanzu ita Zainab din fah? Yace ban san inda take ba bama na bukatan insan inda take for now, ina bukatan hutu zan manta dasu dukansu Na wani lokaci, Abdul yace haba Man laifin wani baya shafan wani yau fah 8dyz dayin aurenka kuma a ka ida 7dyz zaka ma aysha saika koma gidan zainab kaga Kana cikin kwananta ne ya kamata ka nemeta in baso kake kaci hakkinta ba, nan Abdul yaita mai nasiha tare da nuna mai yayi adalci ya danji sanyi a ranshi ba kaman da ba, harya amince zai nemi Zainab din, koda abdul zai tafi yace su tashi su tafi tare, A Majeed badan yaso ba ya tashi suka wuce direct gidan Zainab din suka nufa koda sukaje kofar parlour a bude yake shiga sukayi suka ganta a parlour Tana bacci, A Majeed sai yaji ta bashi tausayi ko ba’a fada ba yasan anan ta kwana dan ja mata hanci yayi tare da hura mata Iska ido ta bude a hankali ganin A Majeed yasa ta tashi da sauri tare da fadin mai ya kawo ka nan? Lokaci daya kuma tasa kuka mai ban tausayi tare da fadin ka fita kaban waje ka koma wajan wacce mamanka ta baka dama nasan mamanka ta tsaneni gashi tayi nasara tasa kamin kishiya har Kana marina a gabanta, Abdul yace haba Zainab komai ya faru kiyi hakuri tunda kika ganshi yanzu yasan yayi laifi, tace Abdul kalli fuska na yanda ya kumburu babu wani wanda ya taba saka hannunshi a jikina da sunan duka sai jiya kuma namijin da nafi so a rayuwa shine ya mareni saboda wata yar Iska, A Majeed cikin tsawa yace Zainab ki iya bakin ki, ya kamata kisan abunda zaki dinga fada, tace na shiga uku abun naka har yakai haka yanzu baka sona ka tsaneni kuka ta kuma Saki wanda ya hanata karasa maganan, matsawa yayi kusa da ita tare da janyota jikinshi abdul ganin haka yabar gidan dan ya basu waje ya rarrashi matar tashi, matseta yayi sosai yace control your self plz, cikin kuka tace A Majeed ka rabu dani, yace bazan iyaba Zainab ina sonki keda kanki kin san haka, Zainab ya kamata kimin adalci kin san ni dan adam ne 9 nake ban cika goma ba sannan karki manta duk abunda bawa yayi haka Allah ya tsara mishi a rayuwanshi remote din na hannun Allah mu munayin yanda akayi damu ne, so ki daina fadin wai bana sonki sannan ban mareki ba saida kika min laifi abunda kikayi jiya is out of sense sannan zaki sa yarinyar ta rainaki yaka mata ki kama girmanki, Zainab wlh ina sonki sosai na rasa a ina kika samo wasu halaye da baki dasu da kika daurama kanki,plz ki dawo yanda na sanki…  A hankali tace indai kana sona kaman yanda kace toh ka Saki matar da aka daurama, dan murmushin takaici yyi tare da fdin Zainab ki saurare ni ina sonki kaman yanda nace miki sannan kuma hakan bazai sa in rabu da ita ba, kokarin fara jan jikinta daka nashi ta farayi tare da fadin sun kwace min kai sun rabani dakai sunyi nasara, ina sonka A Majeed amma bazan iya zama da wata a matsayin matarka ba, yace Zainab ki dinga tunawa da ko ke yar waye, yanzu ba abun kunya bane ace kina kin kishiya tace so what koma yar waye ni kawai bana so, yace zainab zauna muyi magana, bata motsa ba ganin haka yasa ya kamota ya zaunar da ita yace zainab ina sonki bazan iya rabuwa dake ba haka ita aysha bazan iya rabuwa da ita ba yakama ki fahimci haka sannan ki rige girmanki a wajanta, sanan inaso ki canza halinki plz mu zauna lafiya, shuru tayi tana nazari can tace shikenan na yarda amma zaka hadamu Gida daya coz naga gidanta gidan mata biyu ne, dan shuru yayi can yace keda bakya son takura kaman wajan ya miki kadan, tace eh ina son mu zauna tare yaji dadin hakan yace ok zansa a miki oder din kaya sai a sa miki, shuru tayi tana tunani tare dajin kishin mijin nata wai yau itace akama kishiya har zasu zauna Gida daya, ganin tayi shuru yasa bakinshi cikin nata ya fara kissing tun tana sharewa harta fara mayar mishi da martani baka jin karan komai saina nishin su ranan Zainab ta Saki jiki ta nuna mishi tsantsar so shida kanshi yayi mamaki dan yaji canji sosai, bayan Sun dawo hayyacinsu ta tashi ta nufi dakinta toilet ta fada tana wanka tana kuka yanzu ita A Majeed yama kishiya amma ba komai zan dauki mataki koba yanzu ba, haka tayi wanka ta fito tasa wata riga da wando tayi kyau sosai, tana cikin sa Turare ya shigo dakin daka ganin shi Shima kasan yayi wanka, rungumota yayi ta baya tare da fadin uwar Gida ta, dan murmushi tayi wanda bai kai ciki ba, ranan bai fita koh inaba sai masallaci da yake zuwa hakan yama Zainab dadi harta sake dashi tare da rage radadin da zuciyarta ke mata kuma tana lura bai kira amaryar tashi ba hakan ya mata dadi harta yarda da cewa ita yakeso kawai yayi auren ne dan haka Allah ya tsara mai, ranan duk wata kulawa ta bashi ta gefen A Majeed kuma gaba daya tunanin indo yakeyi koh wani hali take ko taci abinci gaba daya dauriya yakeyi kawai Dan kar Zainab ta lura da hakan.

Indo iya tashin hankali ta shiga tun da ta tashi tayi wanka tasa English wear masu kyan gaske dan tana tunanin zaizo amma taji shuru gashi har yamma tayi shuru, kuka ta farayi tare da fadin dama baya sona karya ne kawai da yaudara tunda ya sami abunda yakeso ai na shiga uku yanzu, wani irin kishin shi takeji wanda kwana daya da bata ganshi ba yasa ta kasa cin abinci tare da yarda cewa tana sonshi daukan wayanta tayi danta kirashi ta bashi Hakuri ya dawo, lokaci daya ta kuma sakin kuka mai karfi tunawa da tayi bata da number dinshi, kuka take sosai tare da tausayin kanta dan yanzu tasan babu komai a ranta sai kaunar mijin nata wanda ya mata kaura, ta gefe daya kuma taji tana kara tsanar Zainab tunawa da tayi itama matar shice wanda take tunanin yanzu suna tare yana ririta ta, kanta taji yana sara mata kaman zai fashe dan ciwo, hannu tasa a kan tare da fadin innalilahi’wa inna ilahira jiun, dama haka so yake mai yasa tun farko ban gane ina sonshi ba sai yanzu mai yasa na kamu da sonshi bayan shi ba sona yake ba haka ta kwanta a falo kaman jiya ga yunwa ga damuwa da ciwan kai, washe Gari da safe dakyar tayi sallah ta kwanta a wajan dan zazzabi takeji sosai ga jiri na dibanta.TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      215to220

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

A Majeed yau kwanashi biyu bai fita ko inaba sai masallaci, Zainab kwana biyun da yayi bata ga fitanshi ba yasa ta saki jiki dashi tana nuna mai Luv dan kawai kar yayi tunanin zuwa wajan indo, shiko tunani ne fal ranshi yana tunanin koya aysha ke ciki yanzu, wani lokacin kuma sai yayi tsaki tare da fadin mai yasa zan damu tunda ita bata damu dani ba, duk yanda yaso ya cire tunanin ta a ranshi ya kasa amma yayi alkawarin bazai koma gidan ba har sai ta nemeshi din kaman yanda tace mishi dan yana ganin hakan zai bata daman yarda da cewa yana sonta tunda yabi umarninta, sai dai yanzu ya rage takaici tunda Zainab ta sauko harta fahimce shi, jin hannun zainab yayi a saman kanshi tana wasa dashi murmushi ya sakar mata tare da janyota jikinshi ya hura mata iska a ido dariya tayi tare da lumshe ido, lokaci daya kuma ya mata peck a goshinta tare da furta I love you my darling bude ido tayi a hankali tare da kallonshi tace miye bakaso a tare dani? Tambayan nata ya bashi mamaki amma bai bari ta ganeba amma tunda ta bukaci ta sani zai fada mata komai da yake damunshi a game da ita, hannunta ya rike tare da fadin…..  Zainab kece first love dina and you know dat ina sonki sosai and b4 we get married munyi ma juna alkawari da dama amma daka baya duk kin watsar kin dauko wasu halaye da ban sanki dasu ba, ni namiji ne inada bukatan Mace amma ke gaba daya bakya bani hakki na dake kanki sai kinga dama kuma sai inyi wata biyar shida banyi sex dake ba and kuma ke da kanki zaki iya bada shaidana akan bana neman mata bana zina, in zaki duba ki gani kin san irin wannan abubuwan da kikeyi kina cuta na nifa mutum ne bawai dutse ba inada feelings Zainab idan kika duba karin aure ya wajabta a kaina tunda bakya iya daukan bukata na kwata2 ke bakya tunanin haiyuwa dan baki taba min magana akai ba, sannan bakya respecting dina a matsayin miji in zaki fita bakya neman permission dina fita kawai kikeyi Zainab duk yanda nakai da sonki dole inji kin fara fitar min a rai, sannan bakya respecting Mum dina and You knw itace ta haifeni indai kina sona dole ki sota, bayan haka ni namiji ne mai kishi bana son irin wannan dressing din da kikeyi kina fita dashi, wannan abubuwan sune suke bata min rai dake kuma bana so, a hankali ta dago kanta Tana hawaye tace hakane nasan ban kyauta maka ba, yanzu dama duk soyayyan da yake tsakaninmu zan iya fitar maka a rai? Janyota yayi jikinshi yace Zainab ko daya har gobe ina sonki indai zaki gyara halinki zaki tabbatar da hakan, shikenan zan gyara amma inaso ka sani haiyuwa nima inaso Allah ne bai bani ba, tashi tayi tabar dakin da sauri Tana kuka, jikinshi yaji yayi sanyi tare dajin tausayinta, tana shiga daki ta tabe baki tare da fadin zan gyara zanyi abunda kake bukata wlh saika Saki matar da uwarka ta aura ma zan nuna maka irin tawa kissan sannan haiyuwa kuma ban shirya ba dan bazan zama tsohuwar karfi da yaji ba inacin ganiyar kuruciya na ahem, jin karan bude kofar ne yasa ta kuma rushewa da kuka harda shesheka shiko ganin haka ya kara shiga damuwa yaita bata hakuri tare da gaya mata kalamai masu dadi dakyar tayi shuru sai narke mai takeyi a jiki shiko gogan irin sukuwar da takemai yasa tsigar jikinshi tashi tare da banana dinshi lura da wandonshi da tayi yasa ta fara kokarin tashi kamota yayi tare da jona bakinsu waje daya ya fara kissing itama martani ta fara mayar mai dan tasan dama indai ya fara dole ta biye mai dan yasan sirrin sarrafa Mace, shafata yakeyi tako ina tana wani irin nishi tare da kara kankame shi kissing dinshi itama ta fara tako ina tare da wasa da Banana dinshi lokaci daya ya janyota ya cire mata komai nan akayi mai gaba dayan bayan sun gama bacci ne ya dauke Zainab shiko toilet ya shiga yayi wanka shiryawa yayi yasa kananan kaya yayi kyau sosai ga kamshi na tashi ganin tana bacci baya son tashinta yasa ya dauki Key din motarshi ya nufi gidan Mum dinshi, tuki yake amma zuciyarshi cike take dason ganin Aysha yana tunanin ko wani hali take harya karasa gidan Mum koda ya shiga a falo yaga Mum ita daya, tana ganinshi ta saki murmushi tare da fadin son kaine da yamman nan, yace wlh Mum nan ya gaidata tare da zama kusa da ita amsawa tayi da fadin ina aysha? Yace tana gida Mum, mum tace ina fatan dai komai lafiya koh? Yace eh lfya qlau tare da tambaya ina Dad? Tace yana Sama yanzu ya haura, yace Mum dama magana za muyi harda Dad tace toh saika tashi muje, haurawa sukayi tare har dakin Dad din, bayan sun shiga A Majeed ya gaida mahaifin nashi amsawa yayi cikin Fara’a tare da tambayanshi ya iyalan nashi yadan sosa kai tare da fadin lfya Dad, shuru ya dan biyo baya kafin A Majeed yace Dad dama inaso in fada muku zan hada aysha da Zainab Gida day……  Tun kafin ya karasa Mum tace karka kuskura ko wacce ka barta a inda take bana son a takura ma yata ahem, dad yace haba fatima mai yasa zaki dinga fadin irin wannan maganan ba tare da kin jira munji dalilin shi nayin hakan ba, shuru tayi ganin haka Dad yace mai yasa kake son hadasu baka ganin rigima ne zai biyo baya? Yace Dad hadasu waje daya shine zai kawo zaman lafiya tsakaninsu tare da gudun zargi sannan Dad ita Zainab da kanta ta bukaci hakan.. Mum tace toh kaji koh? Bazai taba sabuwa ba Dad ne ya katseta tare da fadin fatima hadasu waje daya abune mai kyau shi kanshi zai sami kwanciyan hankali sannan duk wani zargi da zai dinga shiga ransu zai kawar ni banga laifin hadasu ba gidan aysha ai na zaman mutum biyu ne dan haka saika gyarama Zainab din dayan wajan itama, yace toh Dad, Mum tace wlh idan akama aysha wani abu saina saba maka, tunda zaka Sama  Zainab kayan daki dama ni nayi ma aysha akwati dan haka saika mata naka akwatin Dad yayi murmushi tare da girgiza kai yce fatima kenan ,A Majeed yace Mum dama inason inyi mata tace yafi maka kwanciyan hankali sannan maganan aikinta fah? Yace an gama aikin asibitin nayi oder din kaya May be cikin week din nan su iso, tace Allah ya kaimu dad yace toh baki tambaya ba ita Zainab din maiya mata tunda anyi ma yarki asibiti, Mum tace aiki ya hanata kaga kam dole ya nema mata wani inko yace bazai gina bama ai dole ya barta tayi aikin, ita Zainab din inda zata fara aiki ai zai nema mata dai2 irin nata a gina mata Dad yace Fatima baki da dama Mum tace ai gaskiya ne dan naga shirin cutar aysha akeyi shine zai wani kawo zancen hadasu waje daya, shidai A Majeed tashi yayi tare da musu sallama, Mum ta bishi da harara, bayan ya fita Dad yace mata ba’a haka duka matanshi ne kuma duk yana sonsu dan haka ki daina nuna banbanci a tsakani Mum tace niba banbanci nake nunawa ba nasan halin matar nashi ne baida kyau Dad yace addu’a zaki dinga yi musu tace insha Allah.

Tuki yake yana tunani jin karan wayanshi yasa ya dauka yaga zainab ce, murmushi yayi tare da dauka yace Baby gani nan zuwa tace ok tare da kashe wayan kai tsaye gidanta ya nufa, bayan ya shiga tayi hugging dinshi tare da fadin ina kaje Baby, yace naje gidan mum ne, tace ya Mum din? Yaji dadin tambayan yace lfya nan ya zauna tare da fadin mai zaki bani inci? Tace babu komai nasha mako zaka siyo mana ne, yace Baby ya kamata ki faramin abinci ina cin naki, tace Baby kaifa da kanka kasan ban wani kware ba sosai a girki kai ya girgiza alaman takaici, kiran Abdul ne ya shigo wayanshi dauka yayi tare da fadin gani gidan aysha bakin gate security yace min wai kwananka wajan uku baka zoba, haba Man sannan kasan yau gidanta kake, A Majeed baya son Zainab ta gane yace ka jirani gani nan zuwa, bayan ya kashe ya kalli zainab tare da fadin zanje wajan Abdul sannan daka nan zan tafi gidan aysha kin san yau can nake, ga mamakinsa sai yaji tace inka je kace ina gaidata, hakan ya mishi dadi tare da ganin girmanta peck ya kai mata a goshi tare da fadin I love You har mota ta rakashi yana fita ta dawo Gida ta fara kuka tare da fadin wlh saina illata ki saina nuna miki kinyi kuskuren auran min miji akanki zan koya ma duk wata mce mai gigin auran mijin wata darasi ni Zainab nayi alkawarin bata miki rayuwa sai nasa kin tsani kanki banga wacce zan zauna da ita a matsayin kishiya ba kuka take sosai tana surutai.

Koda A Majeed yaje kofar gidan yaga motar abdul a gefe shima bai shiga ba fakawa yayi a gefe tare da fitowa ya bude motar Abdul ya shiga tare da fadin wato kai har lisafamin kwanaki kakeyi koh? Abdul yace haba Man gskya kaban mamaki wannan ne son da kake fada Kana ma aysha haba dan Allah kwana uku baka leko kaga halinda take ciki ba, kai dan tacema kayi nesa da ita shine zaka biye mata bayan kasan mata karancin tunani garesu kuma suna da rauni haba Man, A Majeed yakai mai duka irin na wasa tare da fadin kaida kanka kasan ina sonta sanda nake mata shine yasa ma har nake biye mata, nake daukan duk wani abu da tace, Abdul yace Man duk irin sonda kake ma Mace idan ta kawo abunda baiyi dai2 da hankali ba karka biye mata wlh ni nazo nema inci abincin amarya dan nasan Kana nan yau Ashe kai Kana can, A Majeed yace sai kazo muje Ai, abdul yace ina ai badani zaka shiga ba next time dai zan dawo yanzu dai kaje kaga halinda matarka take ciki, fita yayi a motar abdul ya shiga nashi tare dayin horn Mai gadi ya bude, Abdul shima ya wuce, bayan yayi parking ya fito tare da kulle motar ciki ya shiga kofar falon a bude yake bata falo direct dakinta ya nufa yaga bata ciki har zai juya yaga kaman mutum a kasa da sauri ya nufi wajan ya ganta bata ko motsi, cikin tashin hankali ya fara kiran sunanta tare da bubbugata amma ko gezau batayi ba hankalinshi ya tashi matuka hawayen da yakeyi ne Ya sauka fuskanta wani irin nishi tayi mai karfi ganin haka yasa ya tashi da sauri ya dibo ruwa ya fara shafa mata a jiki, ido ta bude tana ganin dishi2 ganin kaman A Majeed yasa ta kara bude idan sosai jikinta babu kwari ta Kasa tashi sai kallonshi da takeyi shima ita din yake kallo, lokaci daya kuma tasa kuka mai karfi……TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      220to225

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Dagota yayi tare da hadata da jikinshi ya matseta da karfi tare Da shafa mata baya yana mai jin zafin kukan nata, a hankali ya saketa tare da zaunar da ita akan gadon dakin, har yanzu bata daina kukan ba, fita yayi jim kadan sai gashi da Tea a Cup ya shigo dashi, ganin tana kukan yasa ya kura mata ido hannu yasa yana goge mata hawayen tare da fadin plz stop it kin san bana son kukanki sa mata Cup din Tea din yayi a baki ta fara sha tunda ta kafe kai bata cire ba har saida ya kare ta kawar da kai, tausayi yaji ta bashi sosai dan yasan tana tare da yunwa, bayan ya ajiye Cup din a gefe yace aysha maiya sameki? Mai makon ta bashi amsa saita kuma fashewa da kuka tare da kokarin tashi daka wajan jin kaman jiri yana kokarin dibanta yasa ta zauna tare da daura hannu a kai alaman yana mata ciwo, sauke mata hannun yayi tare da fadin plz tell me my princess maiya sameki haushi tambayan nashi ya bata wato shi baima san maiya faru ba bayan yasan abunda yayi, cikin kuka tace dama nasan baka sona sai yasa kayi nesa dani, dan murmushi yayi tare da fadin Baby kina so in zauna kusa dake ne? Jin tayi shuru bata da niyan bashi amsa yasa yaci gaba da fadin nabi umarninki ne kaman yanda kikace and you know ina sonki sai yasa nakeyin duk abunda kikace koda kuwa zai cutar dani, yanzu ma nazo ne inga halin da kike ciki duk da baki bukaci ganina ba, amma kiyi hakuri zan tafi har sai kin nemeni din yana maganan Tana kara fashewa da kuka shima yana fadin hakan ne dan akwai abunda yake son ya fahimta a tare da ita, tashi yayi tare da fadin kiyi Hakuri zan tafi amma ki dinga kula da kanki bazan dawo ba har sai kin kirani da kanki tafiya ya farayi har yakai kofa yaji ta rungumeshi ta baya Tana kuka tare da fadin karka tafi ka barni ina bukatanka kusa dani bazan iya kara juran kayi nesa dani ba, kuka yaci karfinta sosai shiko yanda yake baiko motsaba mamakin kalaman nata yakeyi dan bai taba zatan zasu fito daka bakinta ba, komai yayi tsit bakajin karan komai saina kukanta wanda yake jinshi har cikin ranshi a hankali ya furta aysha mai yasa kike sona kusa dake bayan bakya sona? Cikin kuka tace sonda nake maka yasa bana so kayi nesa dani da sauri ya waigo tare da kara janyota jikinshi yace mai kika ce? Ido ta rufe tare da furta I love You I want you to stay with me forever dnt ever think of leaving me again, wani irin farin ciki ne ya lullube shi tare da mamakin jin kalman nan daka bakinta lallai yau yaji abunda bai taba zato ba, a hankali ya kira sunanta bude ido tayi Suka hada ido wani irin murmushi suka sakar ma juna mai cike da nuna tsantsar soyayya tare da tabbatar ma juna dagaske suna son junansu, idanshi nakan nata yace aysha ban taba tunanin zanji wannan kalman daka bakinki ba yau inaji nafi kowa cikin farin ciki zan nuna miki ina sonki fiye da tunaninki, idanta ta kara lumshewa ganin haka ya sakar mata peck akan lebanta da sauri ta bude ido Tana kallonshi murmushi yayi tare da fadin come on Baby zoki fadamin maiya sameki dan bugunshi a kirji tayi irin na shagwaba tace bakai bane, ido yadan Zare tare da fadin ni yana nuna kanshi, tace eh bakai bane ka gudu ka barni inata tunaninka na kasa cin ko abinci, ido ya kura mata yana kallon bakinta yanda take magana daura hannunshi yayi akan kafadanta yace zomu zauna ki fadamin inji yaushe aka fara sona, hannu tasa a fuska ta rufe Tana dariya, shima dariyan ya fara bayan ya zaunar da ita yace oya a cire min hannu akan fuska inason ganin face din babyna dariya ta kuma yi tare da cire hannun tace yunwa nakeji murmushi yayi tare da fadin gani eat me yana maganan yana kashe mata ido, da sauri ta daura kanta a giwa Tana fadin nifa ba mutum zanci ba abinci nakeso, dariya yayi tare da fadin to ki tashi ki shirya muje muci, da sauri ta tashi ta shiga toilet, binta yayi da ido yana murmushi shima tashi yayi ya nufi dakinshi kafin ta shirya, yau A Majeed yana cikin farin ciki sosai ya rasa wani irin so yake ma aysha wanda kwata2 baya ji ta gundureshi a kullum yana son kasancewa kusa da ita, shima wani kayan ya canza tare da zama yana tunanin Baby dinshi wai itace yau ta bude baki tace Tana sonshi, lumshe ido yayi yana jin dadi har cikin ranshi, ji yayi ansa mai hannu a ido an rufe mai murmushi yayi tare dasa hannunshi ya cire mata hannunta ya janyota ta fada jikinshi dariya ta Saki tare da rufe idanta da hannu alaman kunya, murmushi yayi tare da daura fuskanshi a wuyanta da kasan riganta domin a ko da yaushe kamshin jikinta na rikita shi, murya irin na mai cike da shauki da tsantsar soyayya yace Baby ina son kamshin turaranki, tashi tayi daka jikin nashi Tana mai fadin ngd ya kamata mu tafi kasan ina jin yunwa yace hakane Baby muje fita sukayi yace badai haka zaki ba? Jikinta ta kalla taga riga da skirt ne na atamfa sai gyale amma bamai girma sosai ba, tace a haka zani mana, yace No ban yarda da hakan ba kisa hijab muje ko kisa jallabiya, baki ta dan turo alaman shigar tata batai komai ba ai ganin haka yasa ya matso kusa da ita batai aune ba taji bakinshi cikin nata tsotsan bakin yakeyi kaman lollipop saida ya tabbatar ya cire mata jan bakin da tasa kafin ya barta yace kinga yanzu na rage miki makeup din dariya ta Saki lokaci daya ido ya bita Dashi yana mamakin mai takema dariya hannunshi ta kama sukaje wajan console fuskanshi ya kalla shima dariyan ya fara domin janbakin nata duk ya goge mai a kasan lips dinshi, kallonta yayi tare da fadin oya zoki goge min kai ta noge alaman a’a ganin yana matsowa kusa da ita yasa tayi daki da gudu dariya yayi tare da girgiza kai yayi dakinshi shima dan ya wanke wajan, itama canza kaya tayi da sauri tasa wani dogon wando da top sannan tasa hijab, tayi kyau sosai a falo ta sameshi kallonta yayi tare da fadin anya ba zaki zauna inje in kawo miki abunda kike soba, baki ta dan turo tare da fadin nidai tare zamu tafi, yace gskya bana son a dinga kallon minke kalla yanda hijab dinnan ya miki kyau, gsky kisa nikaf ido ta zaro tare da fadin dan Allah kayi hakuri karka daura min sa nikaf, hancinta ya lakuta tare da fadin mai yasa kike da kyau sosai, tace nidai bana son sa nikaf plz, yace ok amma karki dinga kallon mutane dariya tayi tace na yarda sannan suka fita tuki yake ga wakar akon dake tashi yana tuki yana bin wakar har suka karasa wani hadaddan restaurant wanda sai mutum ya isa yake zuwa wajan fita sukayi sannan suka jera hannushi na rike da nata duk wanda ya gansu sai yaji sun burgeshi wasu dauka ma sukeyi larabawa ne su dan kaman larabawa sak ga kyau ga hasken fata abun dai sai wanda ya gani, Kin yarda yayi su zauna wajan da akwai mutane gudun kar ayi ta kallan mai mata private waje suka zauna sannan suka fara duba list din abincin indo tace a kawo Mata fried chicken and rice, sannan drink a bata Chapman, shima kalan nata yace a kawo mishi, koda aka Kawo indo ci takeyi sosai dan Tana jin yunwa tsayawa yayi yana kallonta yanda takecin abinci duk sai yaji ta bashi tausayi ganin irin kallon da yake mata yasa tayi dan murmushi tare da fadin tunani ya hanani cin abinci, yace tunanin me?  Uhm uhm kawai tace tare dashan Chapman idanshi Na kanta yace Baby tel me tunanin maiya hanaki cin abinci tashi tayi tare da fadin idan munje Gida zan fada maka dariya yayi tare da fadin wayau koh itama dariyan tayi tare da fadin mu tafi, biyan kudin yayi sannan suka fita wani boutique suka shiga kaya ne kala2 English wear shadda wanda aka dinka da atamfofi dinkakku da sauran kayan bukata na mata komai suna dashi ready made, hannunsu a manne dana juna suka shiga gwanin ban Sha’awa bayan sun shiga yaja ta gefen hijab kallonta yyi tare da fdin gashi ki zaba wanda kike so inma duka kike so saimu siye kallonshi tayi tare da fadin ni guda daya ymin kasan nafi son gyale y….. Baiko tsaya sauraranta ba yyi gaba tare da fara jidan mata hijab dariya tayi ta bishi tare da fadin haka ya isa fah yace Baby nifa bazan yarda da fita babu hijab ba harda nikaf zan siya miki yanzu dan kin san banaso ana kallon min ke, murmushi tayi tare da matsawa gefen English wear wani 3quater ta dauka guda biyu da wata top mai budaddan hannu in mutum yasa baifi ya tsaya wajan cibiya ba dan a dangale yake jin muryanshi tayi ta wajan kunnanta yana fadin zai miki kyau Baby na in mun koma shi Zaki samin da sauri tayi gaba Tana dariya, daukan mata English wear din yayi da yawa sannan ya tura basket din sukai wajan biya ko wanne akwai kudinshi a makale Dashi haka ya bada ATM dinshi aka cire suka fita da kaya niki2 harda ma’aikatan wajan suka kwasan musu akasa a mota direct Gida suka nufa shita bari da kwaso kayan domin shigewa tayi ta barshi haka yaita kwaso kaya yana shigar dasu itako toilet ta fada tayi wnka koda ta fito taga kayan a Dakin murmushi tayi tare da nufan dress mirror ta fara shafa mai da tura ruka kala2 kamshî ya bide ko ina tashi tayi ta bude wardrobe dan daukan kayan da zata sa taji an rukota ta baya magananshi taji yana fadin ban bukatar asa min ko wani kaya sai wanda na zaba ido ta lumshe Tana dariya juyo da ita yayi tare da fadin muje in nuna kayan da za’a sa, wajan kayan suka nufa suka fara budewa wannan top din ya dauko tare da 3quater yace tashi in sa miki ido ta bude tare da noke kai alaman a’a dariya yayi tare da matsawa kusa da ita ganin dagaske yake yasa ta dauki kayan ta nufi toilet Da gudu dariya yayi, jim kadan sai gata ta fito ido ya bita Dashi domin ganin yanda kayan ya mata mugun kyau wani irin Sha’awanta yaji lokaci daya, tashi yayi ya dauko wayanshi ya fara daukanta dariya take tayi matsowa yayi kusa da ita ya fara daukansu tare sunyi kyau sosai, a hankali ya jata zuwa kan gado tare da zaunar da ita yace tel me tunanin maiya hanaki cin abinci? Kallonshi tayi taga irin kallon da yake mata tayi saurin kawar da kai Tana murmushi tare da fadin baka manta ba? Yace taya zan manta da wani abu daya shafi lamarinki plz tel me Baby a hankali tace tunaninka ya hanani cin abinci, dago mata kai yayi tare da goga hancin shi akan nata yace I love You itama a hankali ta furta mai I love you too, Lokaci daya yasa bakinshi cikin nata ya fara kissing dinta tare da shafata tako ina itama ganin yanda yake mata yasa ta fara mishi irin yanda yake mata saida ya bari ta kamu sosai kafin ya saketa tare da dagota jikinshi nan akayi babban aiki baka jin komai sai karan AC da nishin su sun dauki lokaci daya suna abu daya kafin suka dawo hayyacinsu, kowa kwanciya yayi ta gefe tare da sauke ajiyan zuciya cikin jin dadi da nishadi janyota yayi jikinshi tare da matseta da karfi a hankali yace I need more dan ture mai hannu tayi alaman ya barta dariya yayi tare da fadin ina son yau in baki gift din baby’s ne, dariya tayi tare da fadin ba yanzu ba ni, yace nikam yau zan baki Baby May be ma ya shiga tun ranan farko kokarin tashi ta farayi dan Tana jin kunyan zancen nashi dariya yayi tare da janyota jikinshi yace idan kika tashi bazan iya bacci ba, babu yanda ta Iya haka ta dawo ta kwanta a jikinshi, har bacci yayi gaba dasu, basu tashi ba sai gab da asuba shiya fara tashi yayi wanka tare da alwala motsin shine ya tasar da ita itama wankan tayi tare da alwala, bayan ta fito yace Baby bari inje masallaci tace ok, fita yayi itama tayi sallah bayan ta idar kitchen ta nufa dan ta daura breakfast Dan tana ganin ya dace ta fara girki, koda ya dawo motsinta yaji dan haka ya nufi kitchen din jeans ne da top gajeran hannu tasa sai hula, kallonta yake tayi yanda take aiki komai cikin nutsuwa rungumota yayi ta baya ta saki kara dariya yayi tare da fadin sarkin tsoro ajiyan zuciya tayi tare da fadin nifa ban san ka dawo ba hancinta ya lakuta tare da fadin muje mu kwanta kin san bana jin dadin bacci ni daya dariya tayi tace breakfast din fah?  Yace you r my food ai rufe fuska tayi da hannu tare da tureshi alaman ya saketa, dariya yayi yace plz let go and slp, tace bari in gama sai muje kaje inna gama zanzo kin tafiya yayi yace sai dai suyi tare dariya tayi ganin kaman wasa yakeyi amma ganin ya amshi knife din data dauka ya fara fere dankali kallonshi take tayi ganin yanda yake zaftarewa lokaci daya kuma tasa dariya kallonta yayi tare da fadin kinga na iya koh? Tace bafa haka akeyi ba janyota yayi yasa ta a gaba tare da manneta ta baya yace toh gashi ki koyamin in gani daukan wukan tayi ta farayi yana kallo amsa yayi amma still zaftarewa yakeyi daka firan dankali zance ya fara canzawa domin gogan jikinta da yakeyi yasa stick dinshi ta fara harbawa dama yana bukata nan ya fara romancing dinta tun tana dan sharewa dan tana son hada breakfast harta fara mayar mishi da martani a kitchen dai akasha love, indo tana mamakin mijin nata yanda ya iya sarrafa Mace da juyata ta yanda yake bukata yanda duka zasu ji dadi,sannan tana mamakin yanda baya gajiya idan yana sex, shiko ta gefenshi yana kara jin sonta a ranshi domin tana mishi yanda yake so sannan ya lura tana da dauriya sosai, hannunta ya kamo sukai falo zamar da ita yayi tare da fadin ki bari anjima sai muyi breakfast din yanzu ki huta kin san bamu ci amarci ba sosai, zaro ido tayi tare da tashi da sauri tayi dakinta dan taga idan ta biye mishi sai yayi ta abu daya ba tare daya gaji ba, murmushi yayi tare da tashi yabi bayanta, koda ya shiga a kwance ya ganta kwanciya yayi kusa da ita tare da fadin Baby ya kamata muje honeymoon London dariya tayi tare da fadin Wow ina so inje London kuwa, yace shikenan cikin month dinnan zamu tafi…. Dan shuru yayi can yace Baby Zainab zata dawo gidan nan zata zauna a dayan gefen can Dam taji gabanta ya fadi wani irin abu taji yana taso mata……..

TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      225to230

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Ido ta lumshe wanda takeji yana mata zafi, ga kirjinta dake mata zafi shima saboda tsabar kishi dan mai yasa zaice zata dawo nan gidan? Harya manta abunda ya faru kenan lallai namiji dama gidanta yaje ya manta Dani shikenan yanzu zan fara ganin wulakanci kala2 wani hawaye taji ya zubo mata anya banyi kuskuren fadawa sonshi ba? Haba so mai yasa kamin haka mai yasa kasa na kamu da son wanda baya sona, jin tayi shuru yasa ya katse mata tunani da fadin Baby kinyi shuru karki sa wani abu a ranki Zainab ta fahimci tayi kuskure ta bada hakuri kuma so ita ta bukaci ku zauna Gida daya saboda hadin kanku, sannan inaso kisa a ranki babu abunda zai faru insha Allah plz ki bani hadin kai dan Allah, dan janyota yayi jikinshi tare da lakutan hancinta kasancewan dakin da duhu baiga hawayen da takeyi ba amma taba hancinta da yayi yaji hawaye tashi yayi da sauri ya zauna tare da fadin aysha kukan mai kikeyi? Bata kulashi ba saima juya Mai baya da tayi nan hankalinshi ya tashi dan baya son damuwanta,a hankali ya kira sunanta tare da fadin banyi zaton wannan abun zai Saki damuwa ba na dauka kema mai son zaman lafiya nane haba aysha karki manta……  Katseshi tayi da fadin ni bance maka komai ba kayi duk abunda kake ganin ya dace gidanka ne ban Isa in hanaka yin duk wani abu da kayi niya ba, ni nasan komai daya faru kaddara ne haka Allah ya tsara ina cikin wanda ba za suji dadi ba wahalan kishiya dana miji shine zai kashe ni mai yasa kake son kunna wuta a gidanka bayan kasan abubuwan dake faruwa kai a tunaninka hadamu Gida daya shine zaman lafiya? Inko haka kake tunani sam ba haka bane wlh idan ka hadamu Gida daya rigima ka hada da rashin kwanciyan hankali ni nasan dama baka kaunata kullum burinka ka kuntata min zanci gaba da zama dakai har Allah ya dauki rayuwa na tunda tawa kaddaran kenan tana fadin hakan kuka yaci karfinta tashi tayi da sauri tabar dakin tana kuka, hmmmm iya tashin hankali ya shiga tare dajin tausayinta inama zai iya bude mata zuciyarshi taga yanda soyayyarta ta mamaye ta, mai yasa aysha bazaki fahimce ni ba mai yasa kika kasa gane ina sonki da yawa, ido ya lumshe yana mai jin takaicin rashin fahimtan da take mai amma duk da haka bazai canza magana ba Zainab dai zata dawo gidan kaman yanda ya yanke shima tashi yayi yabar mata dakin ya nufi dakinshi baibi ta kanta ba.

Kitchen ta nufa tana ta faman aikin kuka tare da kokarin daura breakfast, fere dankali takeyi tana fadin mai yasa zai hadamu da Zainab bayan yasan abunda ta mata a baya da wanda tayi kwana biyu daya wuce dama nasan baya sona so suke su hadu suban wahala kara ta Saki tare da jefar da wukan kasa Hannu ta rike wanda yake zubar da jini domin ta yanke da wukar a yatsa A Majeed dake daki ya fito da sauri kasa ya nufa yaji gunjin kukanta a kitchen shiga yayi da sauri yaga ta rike hannu Jini na zuba, da sauri ya nufeta tare da riko hannun yana tambaya garin ya haka ya faru a hankali ta fara kokarin jan hannunta kallonta yayi tare da fadin plz ki daina baki ta turo kai ya girgiza tare da kamata sukai Sama yace kina da spirit banza Dashi tayi dan tasan spirit yana zafi a ciwo, dakinshi yayi da ita zaunar da ita yayi akan gadon dakin ya shiga toilet jim kadan sai gashi da kwalabe guda biyu da auduga spirit din ya fara zubawa tare da fadin muga hannun kai ta girgiza alaman a’a yace plz idan akasa zai daina zafi miko hannun tayi yana sawa ta Saki ihu tare da fashewa da kuka, dariya yayi tare da fadin u r a doctor fah shine kike irin wannan kukan, tace toh ba abun bane da zafi, yace toh sorry babyna zoki kwanta, tace ni bazan kwanta a nan ba a hankali tayi maganan yace mai kika ce, shuru tayi ba tare data kara nanatawa ba, yace Baby kina da rigima come on ya kamata ki fahimci mijinki na sonki kinga yanzu kinje kina bata ranki gashi kin yanke, a hankali tace toh bakai bane kaja, dan murmushi yayi tare da fadin Baby inaso ki fahimci wani abu yanzu da dah ba daya bane abubuwa sun canza basai na miki bayani ba keda kanki kin san hakan sannan idan Zainab ta dawo gidan nan gefenta daban naki daban kinga babu mai ganin wani sai in kunso hakan so ki daina tunanin wani abu kinji Baby na, hannunta ya kamo tare da fadin kice wani abu Baby, tace shikenan tunda ka riga ka yanke babu damuwa Allah ya kawar da fitina ya baka ikon yin adalci hugging dinta yayi tare da fadin ameen my baby nan yace suzo su koma bacci taki yarda wai zata koma kitchen dakyar ya barta tare da fadin kar tayi amfani da wukan kar ta kara yankewa tace ta yarda, duk da tasan dole nema tayi amfani Dashi din, wajan karfe goma ta gama komai tare dayin wanka tasa wasu English wear riga da mini skirt tayi mugun kyau kunyan fita taji tanayi tana tunanin ta shiga dakinshi haka koh tasa hijab bude kofar dakin yayi ya shigo ido ya kura mata domin tayi mugun kyau dan kunya taji yanda ya ganta a haka amma saita dake tare dayin baya ta zauna akan gadon dakin murmushi yayi tare da fadin u always look so pretty My angel, a hankali ta furta kalman thanks, karasowa yayi inda take tare da kwanciya yasa kanshi Akan cinyanta dake bude lumshe ido yayi domin jin kamshin jikinta a hankali yace Baby am hungry, tace muje dinning na gama breakfast, bude ido yayi tare dayi mata peck a ciki dariya tayi tare da kokarin tureshi shima dariyan ya fara sannan ya dagata suka nufi parlour kan dinning suka zauna tea ta hada mishi tare da zuba mai meat ball da sultan chips and egg sai parfesun naman rago, kallonta yayi tare da fadin Baby ke daya kikayi wannan aikin kai ta daga mai alaman eh, yaji dadi sosai yau zaici abinci a gidansa kuma matarshi ce ta dafa mai abunda yake buri yaga Zainab tayi kenan amma ta kasa sai son jiki gashi girkin ma bata iya ba, cin abincin ya fara yana lumshe ido dan yaji dadin meatball din sosai yaci da yawa ita ko indo tea tasha da Egg, tashi yayi yazo inda take ya fara bata meatball din bata da niyan ci amma dole yasa taci harta ture kai alaman ta koshi sannan ya barta, kujeran falon suka koma suna fira gwanin Sha’awa duk da hankalinta ba’a wajanshi yake ba Tana tunanin irin zaman da za suyi da Zainab idan ta dawo gidan, ido ya kura mata ganin bata magana a hankali ya hura mata Iska a fuska ido ta lumshe lokaci daya kuma ta bude ido yace tunanin mai akeyi Baby? Dan murmushi tayi tare da fadin tunaninka nakeyi dariya yayi yace are u sure? Tace yes haka ta saki jiki sukai ta fira gwanin Sha’awa.

STORY CONTINUES BELOW

An kammala komai na asibitin indo harda doctors din da za’a su fara aiki a asibitin an tanada A Majeed yace bazata fara aiki ba har sai Sun dawo daka honeymoon Zainab ma ansa mata komai a gefen da zata zauna yana mamakin saukin kai da hakuri da Zainab ta koya lokaci daya sai yasa duk wani abu da yasan zai kyautata mata yakeyi yau zaibar gidanta kuma a yau dinne zai mata magana akan tafiya honeymoon da yakeso yaje da indo, tana zaune akan kujera yana ta gefenta yace dear inason inyi tafiya na 2week tace zuwa ina? Yace London zani dan shuru yayi itace ta katse shurun da fadin ya kamata ka tafi da amarya sai aci amarci a can dakyau, kallon mamaki yake mata ganin haka yasa tace yes dagaske nake my dear, tashi yayi ya kamo hannunta tare da fadin I love you Baby u r a darling, dan murmushi tayi tare da fadin I love you too, fira suka dan taba kafin tace yazo ya wuce kar aci hakkin amarya mamakin canjin Zainab yakeyi tare da kara ganin girmanta lokaci daya, kai tsaye gidan indo ya nufa a falo ya ganta cikin wata doguwan riga na less tayi kyau sosai hannu ya bude alaman tayi hugging dinshi dan murmushi tayi ba tare data tashi ba, yace shikenan bari in koma tunda am nt welcoming, da sauri ta tashi tayi hugging dinshi dariya yayi tare da fadin Baby kinfa kara kyau anya babu ajiya na a jikinki dariya tayi cikin jin kunya taja jikinta daka nashi tare da fadin muje ka zauna zama yayi tare da fadin am so tired kallonshi tayi tare da fadin mai kayi, murmushi yayi tare da fadin zirga2 tace plz yaushe zaka kaini gidan Mum yau fa wajan 1mnt fa, dariya yayi yace sai kinyi 3mnt zaki je ,dan bata fuska tayi tare da fadin haba mana 3mnt yayi yawa wlh ina missing Mum, yace toh naji amma sai anyi min abunda nake so da sauri tace mai kake so matsawa yayi kusa da kunnenta ban san mai yace mata ba naga ta tashi da sauri tana dariya kitchen ta nufa shima dariyan yayi, drinks ta kawo mai tare da fadin oga sir ko zaka dawo dinning ne, tashi yayi ya nufi danning din ta zuba mai tuwan semo miyan danyan kubewa yaji nama da dry fish ga farfesun naman kaza ,yana ci yana santi tare da fadin Baby kodai restaurant zan bude miki ne a fasa hspt din? Dariya tayi tace eh a bude indai zaka yarda in dinga yi, bata fuska yayi tare da fadin babu mai cin girkin Babyna sai ni daya hspt dinma dan anfi karfina ne yasa na yarda zaki aiki din, ni dama zaki hakura dana dinga miki albashi, tace haba ya zakace haka karka manta fah aikin asibiti taimako ne gaba dayanshi kuma ga lada, yace hakane amma ni bana so ana kallan min Mata, dariya tayi tare da fadin babu mai kallo na, yace da wannan kyan naki ni gskya nikaf zaki fara sawa daka yanzu ma, tace ni wlh bana son nikaf plz Dan tamke fuska yayi tare da fadin saboda a dinga kallan min ke koh? Tace nifa babu wani mai kallo na ni wlh nikaf in nasa zafi yake min, yace oh dama kin taba sawa koh? Tace toh ba’a Egypt bane nasa, nan sukai ta magana akan sa nikaf inda ya dage in zata asibiti sai da nikaf ita kam tana ta bashi hakuri akan karya daura mata sa nikaf.

A Majeed yayi musu komai da komai na tafiya, ana gobe zasu tafi ya kaita gidan Mum ba karamin dadi taji ba gata ga Mum wajan wata daya kenan sai dai waya, Mum taji dadin yanda taga indo ta koma ta kara kyau haske da fresh duk wanda ya ganta yasan tana cikin kwanciyan hankali bayan sun gaisa da Mum A Majeed yake tambaya ina Dad tace baya nan yana Kaduna sunje Kai sadakin Abdul kasan bikin ansa nan da wata daya ne, A Majeed yace shine bai gaya min ba, Mum tace kunfi kusa ai taja hannun indo sukai ciki shiko kiran Abdul yayi tare da fadin kana ina ne? Abdul yace ina office kai kwata2 bama ka zuwa office din, A Majeed yayi dan tsaki tare da fadin ina hutu ne ni bama wannan ba ansa bikin ka shine baka fadamin ba, abdul yace sorry Man so nake sai ankai komai kafin inzo muyi arranging, yanzu kana ina? A Majeed yace ina gidan Mum, yace ok gani nan zuwa, basu dade da gama wayan ba saiga abdul yazo nan suka fara tattaunawa inda yake fadamai gobe zasu bar kasar shida indo, Abdul yace Zainab ta yarda kuma? A Majeed yce itace ma tace yakamata muje tare da aysha din, Abdul yace kai Zainab tayi sauki ,A Majeed yace sosai kuwa ni har mamaki take bani wlh dariya suka sa su duka, bayan mum da indo an shiga daki Mum ta kalli indo tace aysha badai ya miki wani abu koh? Tace eh Mum baya min komai tana maganan ne cikin jin kunya ,mum dai tana zargin indo tana da ciki dan tayi mugun haske da kyau sai dai kuma bata tabbatar ba dan tasan amare suna irin wannan kyan musamman idan hankali a kwance yake yau idan akace aysha nada ciki ban san irin murnan da zanyi ba zanga jika na, A Majeed ne ya katse ma mum tunani daya budo kofar tare da fadin yanzu dai Mum ni baki da lokaci na dariya tayi tare da fadin toh yau kuma tanan aka bullo shima dariyan yayi tare da fadin Mum bari muzo mu wuce, Indo bata so ba dan basu wani dade ba, mum tace inkun dawo daka tafiyar nan saiku shirya kuje garin su aysha kaga danginta dan baka sansu ba yace hakane Mum, bayan sunyi sallama ne Mum taba indo su dambun nama dasu snack taso ta bata Magani amma Tana tsoro kar ace tana da ciki ya zube, bayan sun fito Abdul ya gaida Mum sannan suka gaisa da indo, inda take tsokananshi da angon watan gobe dariya yayi sannan suka fita su duka, A Majeed direct gidan Yusuf ya kaita taji dadi sosai tare da mamakin dama yasan gidan ne, kiran Yusuf yayi tare da fadin gamu a gate yace ku shigo mana bayan Sun shiga yusuf yasa aka musu tarba mai kyau indo tace yaya Yusuf ina Anty na? Yace Tana gidan abba bata san zaku zoba ma, tace ya jikin abba din yana shan Magani kuwa? Yace eh da sauki har ya fara dan jan kafa kinga sauki ya fara samuwa,tace Alhmdlh Yusuf ya kalli A Majeed yace a tayani yima dady godiya yasa an sako ma abbana kayanshi da costume suka kama, A Majeed yace Allah ya taimaka nan suka fara fira inda A Majeed yake Cema yusuf idan Sun dawo daka tafiya zasu garinsu yusuf yace Allah ya dawo daku lafiya nima inason inyi maka magana akan ya kamata aysha taje, yace tare ma zamu insha Allah sunyi fira sosai kafin suka koma Gida, a falo duka suka zauna A Majeed ya kalli aysha tare da fadin Baby wai miye labarinki ya akai kika san Mum? Dam taji gabanta ya fadi amma saita dake tace baka san koni wacece ba harka yarda ka aureni? Yace aysha plz tel me kin san yanda auren namu ya kasance tun farko inaso inji daka bakinki plz hawaye ya fara zubar mata……

Taku Maryam obam😘
TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      230to235

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Janyota yayi jikinshi tare da rungumeta yace Baby plz tel me ina bukatan sanin labarinki, a hankali ta fara magana zan fada maka….. Labari ta fara bashi da irin wahalan da tasha da yanda ta hadu da abdul har zuwa sanda akayi aurensu, A Majeed shuru yayi cikin matsanacin tausayin matar tashi lallai tasha wuya sosai amma zai zame mata uwa uba zai zame mata gata wani irin sonta yaji yana kara shigarshi lokaci daya lallai Abdul aboki na kwarai ne dama aysha ce yarinyar da zuka zubar ma kayan tallah Ashe itace abdul yake so amma ya bar mishi ita, kara matseta yayi a jikinshi tare da fadin kibar kuka Baby lallai labarinki abun tausayi ne insha Allah duk wani wahala ko maraici ya Kare dan zan zame miki uwa da uba zan baki gatan daba kowa ke samu ba, a hankali ta furta kalman nagode cikin kuka, hannu yasa ya fara goge mata hawaye tare da fadin ya kamata ki bude association na taimaka ma marasa galihu da wanda ake zalinta, tace inason inyi hakan amma nasan bazaka barni ba, yace zan barki baby jin labarinki yasa na kara yarda da matata nasan bazakiyi abunda zai ban kunya ba na yarda dake nasan zaki karemin mutunci na a duk inda kike, tace nagode da mijina ya yarda dani, yace amma ki bari komai za’ayi sai mun dawo hannunshi yasa akan kirjinta yana fadin ya naga suna kara girma anya babu ajiya na a jikinki? Dariya tayi tace babu komai tare da tashi ta haura Sama shima binta yayi yana fadin muje in duba in gani, sukai ciki.

Washe gari wajan karfe biyu jirginsu ya daga zuwa London, bayan sun sauka a airport suka hau taxi duk da Dad dinshi yana da Gida a London yace a hotel zasu sauka, direct hotel aka kaisu,indo taji dadin yanayin kasar tare da ganin tsaruwan kasar, bayan sun sauka a dakin da suka kama mai kyau ga girma dakin kaman ciki da falo ne akwai wajan kujeru idan ka kara shiga wata kofa bedroom ne da toilet a ciki, indo akan kujeran dakin ta kwanta dan ta gaji kallonta yayi tare da fadin Baby lafiya kuwa? Tace na gaji da yawa dan murmushi yayi tare da cire mata takalmin kafanta ya ajiye a gefe yace come on muje kiyi wanka sai kici abinci sai mu huta gaba daya dariya tayi tare da fadin anjima zanyi bacci nakeji yanzu ni bana jin yunwa, kallonta yayi, ganin dagaske bata da niyan tashi yasa ya dauketa yayi toilet da ita dariya takeyi tare da fadin plz ka saukeni anjima zanyi bayan sun shiga toilet dinne tace ya fita tayi wankan yace shi zai mata tunda ta gaji babu yanda batayi ba amma haka nan ya cire mata komai tare da kokarin yi mata wankan amma zancen saiya canza salo dan ganin kirjinta wanda yake rudashi dan yana son orange sosai gashi aysha Tana dasu, shafawa ya farayi yana wasa dasu tare da murzasa ido ta Fara lumshewa cikin wani yanayi mai wuyan misaltuwa sucking din boob din ya farayi da karfi ta rikeshi tare da shafa mishi bayanshi da kanshi Tana sauke ajiyan zuciya tare da nishi…….  Saida suka dawo hayyacinsu sannan sukai wanka tare da alwala suka fito sallah sukayi ta tashi ta duba jakanka,kallonshi tayi tare da fadin babu cream din dazan shafa, yace yanzu kizo muje mu siya sai muci abinci in mun fita, tace bacci nakeji fah kallonta yayi tare da fadin bazan bari ki kwanta ba har sai kinci abinci baki ta turo sannan ta tashi ta canza kayan jikinta tasa wata doguwar riga tare da boyfriend jacket ta yane fuskanta da Gyale, fita sukayi a kafa suna dan tafiya Tana makale a jikinshi har suka karasa wani super market gefe kuma akwai wajan cin abinci wajan cin abincin suka nufa bayan sun zauna yace mai zaki ci?tace burger nakeso yace ba snack ba abinci wannan sai a siya idan kinci abinci, tace ni shi zanci, babu yanda ya iya shi yasa aka kawo mata shidai yaci nashi abincin, bayan sun gama yasai mata su snack da yawa suka fita super market din suka shiga yana tura keken kayan Tana daukan abunda take bukata har suka gama ya biya suka dawo, suna shiga ciki ta kwanta sai bacci dariya yayi tare da girgiza kai falo ya koma yana kallo tunawa yayi bai kira Zainab ba dan haka ya dauko wayanshi yasa sim dinshi na London doka ma Zainab kira yayi bugu uku ta dauka tare da fadin dear I miss you so much, cikin jin dadi yace nima haka dear ya kike? Tace lfya qlau ya sister dina? Yace Tana lafiya nan sukai fira cikin kulawa daka karshe sukai sallama yana mai kara alfahari dajin dadi domin burinshi kullum yaga Zainab ta canza yanzu gashi ta canza din, Mum ya kira suka gaisa tace ina aysha din yace Mum Tana bacci tace OK inta tashi a gaida min da ita sannan sukai sallama.

STORY CONTINUES BELOW

Tunda suka zo London kullum indo bacci basu samu sunyi yawo ba kaman yanda taso gashi bata son cin wani abinci sosai sai dai abu daya bataso A Majeed yayi nisa da ita dan tace Tana son kamshin jikinshi duk da ta fahimci abunda ke damunta amma tayi shuru dan bataso ya sani yanzu, shiko abun na damunshi yawan baccin da takeyi ga zaban abinci yau tace wannan gobe wannan, yana zaune a falo ta fito cikin shiri tasa riga da wando tare da daura suwaita a kai mai tsawo, hannunta tasa a gashin kanshi Tana yamutsawa tare da fdin my one tashi muje yawo kasan bamu je ko ina ba, kallonta yayi tare da fadin yau babu baccin? Dan murmushi tayi tare da fadin yau banaji, tashi yayi suka fita ranan sunyi yawo sosai tare da siyayya da yawa sai dare suka dawo suna shiga tayi toilet tayi wanka tare da alwala doguwar riga tasa tayi sallah Tana idarwa ta kwanta a wajan ta fara bacci shigowa yayi ya gnta a kasa Tana bacci dariya yayi tare da fdin bby gskiya gobe dole in kaiki hspt wannan baccin yana cutana, daukanta yayi ya kwantar da ita akan gado tare da rufeta da blanket shima kwanciya yayi kusa da ita tare da janyota jikinshi ya rungumeta a haka bacci ya daukeshi shima…..washe Gari duk yanda yaso suje hspt taki yarda haka ya barta domin ta dage lafiyanta qalau haka taita daurewa suna fita yawo tare da siyayya satinsu biyu cif suka fara kokarin komawa Gida, ana gobe zasu koma suka kuma fita siyayya sosai.

Karfe biyar Suka sauka a Nigeria inda driver gidan Mum yazo daukansu direct gidan Mum suka nufa an shirya musu abinci kala2 Mum tayi mamakin ganin yanda indo ta koma ta kara haske kyau har dan jiki tayi gwanin Sha’awa jikin yayi bul2 Mum yanzu ta tabbatar da abunda take zargi sai dadi takeji tama rasa mai zata bata Mum tace aysha muje kuci abinci bayan sun nufi dinning indo tace ita ta koshi A Majeed ya kalleta tare da fadin wai mai yake damunki ne aysha kwana biyu kallon Mum yayi tare da fadin Mum ki mata magana muje hspt haka tun a can bata cin wani Abu sai snack ga bacci yanzu sosai, Mum tace aysha ya kamata kije a dubaki indo dai shuru tayi dan ita tasan maike damunta, jin Mum tayi Tana fadin bari in kira family Dr dinmu daukan wayanta tayi ta kira family Dr dinsu ita kadai take duba Mum haka Dad Shima yana da nashi, bata dade ba sukazo nan suka gaisa tare da fadin Dr aysha Ya aiki Tana kallon indo wanda kallo daya ta mata ta gane Tana da ciki, nan Mum ta mata bayani akan canjin da indo tayi Dr tayi dariya tare da fadin bari in duba ta Dr aysha muje ciki, tashi indo tayi suka shiga ciki, ta bukaci ta bata fitsari indo tace Dr basai kin gwada ba dan nasan ciki dinne Dr tayi dariya tare da fadin shine kika ki gaya ma mum, tace wlh kunya nakeji yanzu saiki fada mata, fita Dr tayi jim kadan sai ga A Majeed cikin farin ciki da murna a zaune ya ganta a dakinta na da rungumeta yana fadin aysha u r pregnant Alhmdlh Allah na godema ashe nima zanga dana ina sonki Baby ban taba jin labarin da yasa ni farin ciki irin haka ba tun bayan da kika furtamin kalman I love you surutai na soyayya ya dinga mata ji yake kaman ya goyata dan murna haka Mum ta shigo ta samesu ganin Mum yasa ta fara kokarin jan jikinta shima sakinta yayi indo ko kunya taji Mum ta fahimci hakan amma saita basar tare da fadin yanzu dai Dr tace zaki hspt kiyi scan kiga lafiyan jikinki dana Baby Mum tana maganan ne cikin farin ciki duk wanda yaganta yasan Tana murna A Majeed yace Mum bari mu wuce Gida saiki bamu masu aiki ko mutum biyu ne, Mum tace ok amma daka barta in an gyara gidan sai ta koma ko zuwa gobe, babu yanda ya iya dole ya yarda duk da ba hakan yaso ba wucewa yayi masu aiki kuma driver yakai su, A Majeed gidan Zainab ya nufa tayi murnan ganinshi duk da ranta na mata daci tare da kishin mijin nata a hankali ya furta dear baki da lafiya ne? Tace maika gani yace kin rame dariya tayi tare da fadin lafiya na qalau kawai nayi missing dinka ne, peck ya sakar mata a goshi tare da fadin nima nayi missing dinki my dear, ranan dai a gidanta ya kwana amma bini2 ya fita ya kira yaji lafiyan aysha, yace ma Zainab itama gobe zata tare a gidanta ta nuna jin dadinta sosai, washe Gari kaman yanda yace haka kam akayi Zainab bata dauki komai ba sai kayanta na sawa shima saida aka kira mai mota dan kayan suna da yawa, bayan Sun karasa ya nufi gefen Zainab din komai an gyara yayi kyau sosai komai ansa sabo kal, hugging dinshi tayi tare da fadin gidan yayi kyau sosai, nan aka fada duniyar love dama an dade ba’a hadu ba, a kullum yana mamakin yanda Zainab ta yarda take bashi jikinta, fita yayi tare da fadin zaije ya dawo gidan Mum ya nufa dan dauko Indo amma Mum tace ya barta ta kara kwana biyu dan sunje hspt dazu ance cikin wata daya ne da kwanaki Tana bukatan hutu dan cikin baiyi kwari ba abu kadan zai iya sawa ya zube, A Majeed babu yanda ya iya kodan lafiyan matarshi da Baby dinshi dole ya hakura yace Mum kwana nawa za tayi? Tace ban sani ba sosa kai yayi tare da fadin inaso ne dama in dauko mata kaya Mum tace Tana da kaya a nan, shuru yayi tare da fadin yauwa na siya kayan akwatin ta zuwa gobe koh jibi zasu iso kayan sai a kawo mata nan mum tace hakan yayi, kaman yanda yace an Kawo akwatin tare da kayan tsaraban da sukayi akwati guda 18 ya mata ko wanne cike yake makil da kaya gana tsaraban da sukayi mum tace bari a cire mata wanda zata bukata sai akai mata sauran Gida hakan akayi kuwa.

Yau satin indo biyu gidan Mum A Majeed kullum yana sintiri gidan shi duk ya kosa matarshi ta dawo Gida itama ta gefen indo din hakane dan Tana son ta jita jikin mijinta musamman kamshin jikinshi da take masifar so, yanzu ta rage yawan bacci sai dai kwadayi dason abu mai yaji, Tana zaune A Majeed ya shigo dakin da take tace yauwa my one rogo nakeso plz, yace rogo dan shuru yayi tare da tunanin miye shi dan bai san abun ba, tace eh yace a ina ake saidawa? Tace nima ban sani ba ni kawai shi nakeso, yace toh naji wani iri ne abun  nan ta Fara fadin zaka ganshi fari kaman doya ana saidawa a kwano yace oh na ganeshi baby plz ban san ciye ciyen irin wannan abun kar yaja miki matsala, bata fuska tayi tare da fadin nima babu abunda zai min kawai ka siya min, kallonta yayi yanda take wani daurewa yace ok naji toh zan siyo sai a dafa miki a nan tace toh tare da sakin murmushi tashi yayi ya fita driver yaba kudi ya siyo mata bayan an kawo yasa aka dafa mata bayan ankai mata ta fara ci sosai kallonta yake tayi yanda take ci Tana jin dadi kaman wani nama amsan kwanon yyi tare da fadin ya isa haka tace plz ka bani wlh ban koshi ba, mum ce ta shigo Tana fadin lafiya yace Mum tun dazu take tacin abun nan kar ya mata wani abu, mum tayi murmushi tare da fadin kaga ka bata kayanta taci babu abunda zai mata badan yaso ba ya bata ta zabga yaji da garin kuli, yace mum kin gani koh dariya Mum tayi tace babu abunda zai mata kasan duk mai ciki akwai abunda take so bai dade ba ya wuce, Gida ya nufa Zainab ta tareshi tare da fadin wai ina aysha ne tunda nazo ban ganta ba, yace Tana gidan Mum bata jin dadi cikin kulawa tace waiyo maike damunta? Yace she is pregnant wani irin duhu ta gani tare dajin wani dum lokaci daya kuma ta Saki kuka tare da fadin shikenan na rasa ka har abada bazaka taba dawowa gareni ba har abada kallonta yayi tare da fadin Zainab Wannan wani irin magana ne haka? Tace Ciki fah kace Tana Dashi shikenan yanzu zanga canji a gidan nan tunda ni Allah bai ban ba kamota yayi tare da rungumeta yace kiyi hakuri Zainab haiyuwa na Allah ne kema karki fidda tsammani Allah bai manta dake ba insha Allah kema zaki sami ciki ki haiyu kaman kowa, nan yaita rarrashinta tare da fadin idan aysha ta haiyu zai bata rikon dan data haifa, jinshi kawai take amma zuciyarta babu komai sai takaici da bakin ciki tare dayin dana sani nashan maganin hana daukan ciki da takeyi dan a yanzu taji Tana sha’awan haiyuwa tunda akace Indo nada ciki, tashi tayi tare da nufa daki danta kwanta binta yayi yana kara bata hakuri akan zata samu itama insha Allah…….  Watan indo daya cif ta dawo Gida ranan A Majeed ji yake kaman ya goyata dan murna Mum ta bata masu aiki har biyu wanda zasu dinga mata aiki, bayan ta shiga gefenta tayi wanka tare da zama dan ta shafa mai da sauri ta rufe dan taji warin mai din har kanta lokaci daya kuma tayi toilet tana kwarara amai a wannan halin ya shigo ya sameta hankali tashe yaita mata sannu idanta yayi ja dan wuya cikin tausayawa ya wanke mata fuska da baki sannan ya kamota suka fito waje bayan ya zaunar da ita ya koma toilet din dan ya gyara wajan, saida ya gama ya fito sannan ta kalleshi tace my one ka siyo min wani mai nawa yayi expire, yace ba akwai mai cikin akwatin dana miki ba tace oh na manta bude wardrobe yayi ya janyo mata akwatinan tare da budewa har ya bude namai ciki harda kalan wanda ta bude yasa ta amai shita dauka aiko Tana budewa ta jefar tare dayin toilet da gudu amai ta kuma sakewa shigo hankali tashe yace Baby muje hspt kai ta girgiza alaman a’a tace wannan ma yayi expire wari iri daya sukeyi dauka yayi ya duba expire date din yace da saura baiyi expire ba, bude mata Vaseline yayi na oil yace shafa wannan shiya fara shafa mata tace kaga wannan baya wari dariya yayi tare da fadin dama Mum tace yanzu abubuwanki ba irin namu bane sai kin zaba dariya tayi tare da ture mai hannu tace toh ba Baby dinka bane yasa na canza yace kar ayi ma baby  dina shairi dariya ta Saki yanda taji yayi maganan wai nan ya kwaikwayeta ne, wayanshi ne yayi kara dauka yayi tare da karawa a kunne yace ok shigo bari ta sauko, kallonta yayi tare da fadin Zainab ce tazo gaidaki gabanta taji ya fadi amma haka ta daure tasa wata doguwar riga ta fito masu aikinta tace suje su jera mata kayanta cikin wardrobe na cikin akwati, a falo taga Zainab kallon2 sukama juna kafin indo tayi murmushi tare da fadin sannu da zuwa, amsawa tayi duk yanda taso ta boye kishinta saida ya fito domin taga indo ta kara kyau duk da sau daya ta ganta ran da sukayi rigima amma hakan bai hana ta gane ta kara kyau ba kishi kumallon mata bata wani dadeba ta tashi tare da fadin idan kina bukatan wani Abu saiki fadamin in Kawo miki dan nasan masu ciki akwai ciye2 indo dariya kawai tayi shiko gogan yaji dadi sosai Zainab na fita ta Fara kuka tare da alwashin saita zubar da cikin indo kota wani hali.TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      235to240

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Ranan Zainab taci kuka tare da tunanin hanyar da zata salwantar da cikin indo domin tunda ita bata haiyuba haka indo ma bata isa ta haiyu ba sai dai kowa ya rasa a hakan ma yata Kare balle ace aysha ta haiyu tsanar indo take taji tare dana Mum wacce take ganin duk ita ta shirya komai dake faruwa yanzu a hankali ta furta saina rabaki da dan naki inga ta tsiya haka taita kuka Tana sambatu

Indo kam duk wani kulawa Tana samu wajan mijinta da mum sai Zainab da itama take nuna mata ta2 irin kulawan duk da indo bawai ta saki jiki da ita bane, A Majeed yana lura da yanda aysha keyi ma Zainab ranshi nadan baci komai Zainab ta Kawo Mata bata ci domin ita ba yarda tayi da ita ba domin wanda ya kika da safe dan yace yana sonka da yamma karyane yaudara ne kawai, indo na zaune a falo Tana cin dankalin hausa dafaffe yasha mangyada da yaji sosai, A Majeed ya shigo kallonta yayi tare da nufanta ya kwace kwanon yace haba aysha wannan man gyadan da yajin yayi yawa bakya tunanin zai iya sa miki wani ciwon daban? Tace ni babu abunda zai samin dan Allah ka bani inci wlh yanzu fa na fara ci kuma tun jiya nake son ci sai yanzu na samu, yace gskiya bazan baki wannan abun kici ba, hawaye ta farayi tare da fadin nifa kasan yanzu ba komai nake ciba idan wannan abun ya fitar min a rai ban san Mai zanci ba yanzu, ido ya kura mata tare da share Mata hawayen fuskanta yace toh naji amma  oil din yayi yawa da yajin bari a Kawo miki wani, tace ni wannan nake so babu yanda ya iya haka ya mika mata ta Fara ci kaman Tana cin nama har wani lumshe ido takeyi dariya ma ta bashi yace Baby ki barshi haka ai kinci da yawa, ido ta dan zaro tace nifa banci sosai ba da sauri ta fara ci dan kar yace zai amsa dariya yayi tare da fadin ci abunki a hankali, kitchen ya nufa tare da samun masu mata aiki yace su daina cika mata mai da yaji cikin abinci sukace ita da kanta take sawa yace toh su dinga fada mata yayi yawa in zata sa sukace toh, falon ya dawo yace Baby ban san kina shiga kitchen komai kike So kiyi magana a baki kinji kai ta daga alaman eh, saida ta cinye ta Fara kokarin shanye mai din ya tashi ya amshi plate din tare da fadin ya isa haka baki ta turo yasa hannunshi akan bakin tare da fadin wannan bakin ya koyi kwadayi dariya tayi shi kuma yakai plate din kitchen, bayan ya dawo tace yaushe zamu garin namu? Wani irin kallo ya mata tare da fadin ba yanzu ba,tace mai yasa? Yace taya zan bari kiyi tafiya kina dauke da babyna, tace wato nice baka so koh? Hancinta ya lakuta tare da fadin kinfi kowa sanin ina sonki Baby, kawai ban san muyi tafiyan ne yanzu tunda kina da ciki kiyi hakuri har ki haiyu sai muje, kinga hakan ma yafi koh, tace duk yanda kace ni mai biyayya ce, yaji dadin maganan ta tare da fadin Baby kwana biyu ban duba babyna ba ya kamata muje aban mu gaisa, dariya tayi tare da rufe fuska dan ta gane nufin shi Kin tashi tayi ganin yanda yake mata gashi masu aikinta zasu iya shigowa duk da in yana nan basa zuwa falon sai ya fita suke gyarawa amma tasa Su mata alale tasan zasu iya shigowa su gansu dan haka ta mike tayi daki shima ya rufa mata baya, suna shiga ya fara kissing dinta tako ina tare da shafa mata jikinta har suka kai gado kwanciyar da ita yayi tare da cire mata rigan jikinta yasa kunnenshi akan cikinta yana fadin Hello Baby is ur dad say hi to ur daddy dariya ta farayi ganin yanda yakeyi jin bakinshi tayi akan boob dinta yana tsotsa kaman swty ido ta lumshe daka nan akai mai gaba dayan saida suka dawo cikin hayyacinsu sannan sukai wanka tare tun Tana jin kunyan yin wanka Dashi harta daina dan ta saba yanzu *Note yin wanka tare da miji yana kara muku son junanku sosai yar uwa a cire kunya maganan aure babu kunya in kika tsaya jin kunya zaki dana sani domin duk ranan da mijinki ya kara aure ya auri wacce take mishi abun da bakya mishi kin bani*

STORY CONTINUES BELOW

Zainab duk yanda taso taga cikin indo ya zube tayi amma cikin na nan daram Dam har Magani tasha zuba mata cikin juice ta kai mata bata san indo bata sha ba, domin bata yarda da Zainab din ba duk da yanzu ta Dan Saki jiki da ita ba kaman da ba, cikin indo ya kara girma sosai idan ka ganta zaka dauka ya isa haiyuwa dan cikin yayi mugun girma sosai kuma kwata2 wata biyar yanzu cikin da yan kwanaki A Majeed siyan kaya yake tayi kaman hauka na mata dana Maza so yake ma su fita shida zainab dan ayi siyayya amma baya so abar aysha ita daya dan ko nan da can baya son yaje saboda aysha balle kuma yabar kasar yadai yanke zai sa a turo mishi kayan baby’s kawai, bikin Abdul ya taso anata shirye2 indo kam jiki yayi nauyi A Majeed ya hanata yin komai dan karta wahala duk yanda indo taso tayi a bikin Abdul hakan ba dama dan jikinta yayi nauyi sosai duk da cikin ya mata kyau amma Tana jin nauyinsa sosai an mata scan ance guda daya ne Baby din, amma girman cikin naba kowa mamaki an Fara shagalin bikin Abdul A Majeed anata shirin zuwa kaduna dan daurin aure duk da bayaso yayi nisa da aysha amma tunda ga Zainab nan zai barta da ita hakan ko yayi ya shiga gefen zainab yace ta dinga kular mai da aysha karta bari tayi wani aikin wahala tace toh babu damuwa zaka dawo ka sameta lafiya, yayi dariya tare da shafa mata fuska sannan ya wuce bayan sunyi sallama da aysha sannan ya nufi kaduna shi daya dan Abdul shi yana can, tunda ya tafi indo ta rufe kofarta dan bata son damuwa domin tunda suka dawo gidan bai taba yin tafiya ba sai yau sai dai ya fita ko yaje office ya dawo, Zainab ce ta fito hannunta dauke da plate ta nufi gefen indo dashi nocking tayi tare da budewa taji kofar a rufe tsaki tayi domin tasa Magani cikin dambun da tasa a kawo mata dan taba indo ance idan mai ciki taci naganin wlh sai dan ya fito koda cikin yakai wata tara kuma babu rai zai fito, kara buga kofar tayi taji shuru komawa tayi Tana ta sambatu tare da fadin ai gobe na nan tsaki ta sake lokaci daya tunawa da tayi duka maganin ta juye bata rage ba wata zuciyar tace mata kiyi hakuri mana har dan yazo duniya sai ki bashi abu yaci ya mutu, da sauri ta girgiza kai alaman bazan iya ba haka taita tunanin hanyar da zata zubar da cikin.

Washe gari karfe daya da rabi aka daura auren Abdul da amaryan shi fatima Zarah a Sultan bello mosque dake kaduna, bayan an daura aurene akace za’a tafi da amarya hakan ko akayi ango ya dauki matarshi sauran yan uwanta kuma driver ya daukesu mota biyu suka je, shiko A Majeed ana daura auren ya wuce dan ya kosa ya koma yaje yaga ya Baby dinshi take, wajan karfe biyar saura ya isa Abuja, direct gefen indo ya nufa yayi nocking masu aikinta suka bude tare da gaidashi ya amsa tare da tambayan ina aysha sukace Tana ciki, haurawa yayi Sama ya ganta Tana ta faman Daura dankwali murmushi yayi tare da rike mata hannu kara ta saki dan bata zaji shi bane amma jin kamshin turaren shi da take mutuwar so da kuma dariyan shi yasa ta saki ajiyan zuciya tace shine baka fadamin ka taso ba yace sorry baby gani yanzu na dawo zaunar da ita yayi akan kujeran dakin tare da fadin bari in gaisa da Baby na nayi missing dinshi, dariya tayi dai2 lokacin yasa kanshi akan cikin nata yace Hello baby is ur daddy do you miss me dariya ta saki mai karfi tare da fadin tell your Baby yayi sauri ya fito yasa nayi girma sosai, hancinta yaja tare da fadin kin kara kyau sosai, tace an Daura aure lafiya ina ango? Yace lafiya qlau yanzu shirin dinner zanyi ma tace nima zani plz, yace nop babu inda zaki ban san yawo gashi bake daya ba tace plz bikin Abdul nefa dakyar ya yarda yace ta shirya suje bari yama Zainab magana itama fita yayi ya nufi gefen Zainab din ya ganta a zaune Tana danna waya daka gani chatting takeyi kallonshi tayi cikin kulawa tare da fadin saukar yaushe kuma? Yace ban dade ba ta mishi ya hanya bayan ya amsa da lafiya yace ta shirya suje dinner din Abdul tace yaje kawai kanta na ciwo nan ya fara tambaya tasha Magani tace eh haka ya fita ya barta tsaki ta Saki tare da fadin Magani bashi bane matsalata burina inga wannan yar iskan tabar gidan nan gaba daya, koda ya koma yaga aysha ta shirya cikin wani doguwar rigan material duk da batayi makeup ba tayi kyau sosai yace Baby kinyi kyau, ido ta lumshe lokaci daya kuma ta bude tare da fadin a haka yace Baby kona fada ko ban fada ba kina da kyau murmushi tayi cikin jin dadi domin Tana son yaban da mijinta yake mata kiran sallah magrib akayi yace bari inyi sallah sai mu tafi fita yayi itama tayi alwala tayi sallah tunda ya fita bai dawo ba har sai da aka kira isha’i yayi kafin suka tafi wani katon hall ne wanda an tsarashi sosai amarya itama tasha makeup tayi mugun kyau sosai A Majeed wajan Abdul ya nufa aysha na makale Dashi Tana dan tafiya dakyar nan indo ta mishi murna tare da addu’an zaman lafiya suka gaisa da amarya, nan suka sami waje ya zaunar da aysha shima ya zauna ana ta kida tare da ciye2 A Majeed ya lika musu kudi kaman ba gobe indo taso tayi likin itama ya hanata wai kar a bige mishi Baby haka ta hakura badan ranta yaso ba, sai wajan 10 A Majeed suka wuce taro dai yayi kyau anci ansha sai sam barka.

A kwana a tashi ba yuwa cikin indo ya cika wata tara Mum tace a dawo da ita gidan ta duk da baiso hakan ba amma babu yanda ya iya domin baya tsallake umarnin Mum, masu aikinta suke ta hada mata kaya ita kam Tana falo ita da gogan nata ya tamke fuska wai shi a dole baya so ta tafi, hannunta tasa cikin nashi tare da fadin my one plz kabar fushi kasan a gidan Mum zanfi samun kulawa sosai sannan idan Kana wannan fushin sai inga kaman bazan tashi bane inna zo haiyuwa da sauri ya toshe mata baki tare da fadin karki kara irin wannan maganan kin san bazan iya rayuwa ba tare dake ba, dan murmushi tayi tare da fadin haka zaka ce amma ni nasan zaka rayu ko bani danko yaranka zaka so ka rayu, yace aysha plz ki daina min wannan maganan bana son jinta, tashi muje in kaiki murmushi tayi kawai tare da tashi zata haura Sama yace ta zauna bari ya duba ko sun hada kayan haurawa yayi yaga sun gama hada komai yace Su fito Dashi sunkai komai mota sannan ta shiga gefen Zainab wannan ne zuwanta na farko, bayan sun gaisa indo tace Zan tafi gidan Mum nazo muyi sallama idan Allah yasa na tashi toh in kuma ban tashi ba ki rike min yara na amana dan Allah hawaye ne ya zubar mata a ido da sauri ta fita Zainab kam jikinta itama yayi sanyi, ta kasa ko motsi duk yanda takai da kin indo ba zata so ace ta mutu ba burinta kawai tabar mata mijinta, A mota ta sameshi yana jiranta ganin Tana hawaye yasa ya fara fada haba aysha wai miye haka ne mai yasa kike son tadar min da hankali ne plz ki barni haka inji da abun da yake damuna mana, shuru tayi Tana ajiyan zuciya ganin haka yasa ya fara rarrashinta  tare da fadin aysha idan Mace zata haiyu bashi bane wai mutuwarta duk da yana da kyau mutum ya dinga Tuna mutuwa koda yaushe irin yanda kike yi yanzu baki san zaki Iya sa rayuwa na cikin wani hali ba aysha koh kin dauka son da nake miki wasa ne, wlh aysha ban taba jin son wata Mace ba kaman yanda nake jin sonki bana tunanin zan iya doguwar rayuwa ba tare dake ba Dan Allah aysha ki bar wannan maganan in baso kike ni in fara tafiya ba, shuru tayi ba tare da tace komai ba jiki ba kwari ya tada motar babu Mai cewa wani abu haŕ suka karasa gidan Mum, bude kofar tayi ta fita shima binta yayi a baya har cikin falon gidan mum na zaune ita da Dad suna fira sai gasu sun shigo mum tace sannu aysha ganin idanta a kumbure gashi yayi ja yasa ta gane tayi kuka tace aysha maiya faru dake haka, A Majeed yace Mum aysha nason sani cikin damuwa tun dazu take ta fadin wai kaman ba zata tashi ba shuru yayi yana hawaye da sauri yabar falon Mum da Dad suka bishi da ido Mum tace haba aysha ki daina fadin haka zaki tashi insha Allah dan murmushi tayi tare da gaida Mum da Dad suka amsa cikin kulawa sannan Mum tace ki zauna mana, zama tayi dakyar tare da tunanin halin da mijinta yake ciki yanzu, a yanda takeji Tana ganin kaman zaiyi wuya ta rayu domin ita tunda ta zama Dr tasan wahalan da mata ke sha wajan haiyuwa take tsoran ta haiyu gashi yanzu haiyuwa yanzu ko anjima ko gobe wani hawaye taji ya zubo mata tare da tausayin yaranta idan akace yau ta mutu bata raye wani irin rayuwa za suyi tunawa da tayi da rayuwanta na baya wanda maraici ne yasa ta haka,shiko A Majeed mota ya shiga amma ya kasa ja sai hawaye da yake ta faman yi sai driver mum ne ya kaishi Gida gefen Zainab ya nufa a falo ya ganta Tana hawaye Tana ganinshi tayi hugging dinshi Tana fadin komai dai lfya koh?wayanshi ne yayi kara dauka yayi yaga Dad ne yace son ka samemu asibiti aysha zata haiyu Da sauri yace toh Dad gani nan kallon Zainab yayi yace zani hspt aysha zata haiyu da sauri tace bari in dauko Gyale muje tare da sauri tayi daki jim kadan sai gata suka fita tare shine mai tukin kaman zai tashi Sama har suka karasa hspt din, koda suka karasa Tana labour room A Majeed gaba daya ya kasa zama haka Mum da Dad Zainab kam kuka takeyi domin ta tausaya mata bata so ta mutu, ta dauki lokaci mai tsawo Tana nakuda amma shuru Dr ce ta fito tace gsky sai an mata Cs dan bazata iya haiyuwa da kanta ba jikinta yayi weak, A Majeed akaba ma takarda yayi signing dai2 lokaciñ Yusuf da zaliha suka zo hspt din gnin irin tashiñ hankalin da suke ciki yasa suka zauna suma amma basu ce komai ba, an Fara shirin aikin indo tayi wani irin nishi mai karfi sai ga yaro ya fado lokaci daya kuma tayi wani nishin yarinya ta fado can kuma ta sake wani sai ga yaro ya kara fadowa lokaci daya kuma ta Saki hannunta komai nata ya tsaya cak.TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      240to245

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

Kwashe yaran akayi ganin kaman bata motsi yasa aka sa mata oxygen amma baya moving gaba daya Dr din sun sadakar ta rasu lokaci daya kuma oxygen din ya fara tafiya alaman Tana da rai tayi doguwan suma ne, nan sukayi kanta ana dubata tayi wajan 30 mnt Tana numfashi a lokacin an kimtsa yaran sannan Dr din da kanta tasa nurse suka tayata kamata akai toilet da ita dakanta Dr din ta mata wanka har lokacin idanta a lumshe yake bata bude ba da duka alamu bata cikin hayyacinta har Dr din ta gama gyara mata jiki Sannan tasa mata wata doguwar riga daka cikin kayanta da suka zo Dashi tare da pad, Dr din ta fita da sauri A Majeed ya matsa kusa da ita yana tambaya tace congratulations ur wife give birth to triple yace yan uku, Dr tace yes a hankali yace itafa hope babu abunda ya sameta? Dr tayi shuru ba tare da tace komai ba yace Dr ta mutu ta mutu koh Dr tace bata mutu ba amma har yanzu bata farfado ba jikinta yayi weak Allah yasa ta haiyu da kanta ba’a kai dayi mata aikin ba yanzu sai mu jira kadan muga yanda abun zai kasance, da sauri yace Dr zan Iya ganinta tace eh amma ka bari a kaita dakin hutu nurses ne suka fito da yaran Mum da Dad suka amsa Zainab ta amshi daya itama A Majeed kam ko kallon yaran baiyi ba danshi burinshi yaga matarshi kawai yaran kyawawa kaman babansu sak gasu farare tas dasu duka kamansu daya sai dai macen ta fisu haske sosai, Zainab wani irin hawaye ne ya zubo mata wannan ne rana ta farko da taji Sha’awar haiyuwa domin yaran sun burgeta dana sanin shan maganin hana daukan ciki duk taji ya kamata lallai itama Tana bukatan haiyuwa duk da lokacin da tasan indo nada ciki ta daina shan maganin amma har yanzu batai ciki ba dole taje hspt a dubata dan itama Tana da bukatan haiyuwa a yanzu, fito da indo akayi akan gadon marasa lafiya ana turata hankalinsu duka ya koma kan gadon A Majeed Da sauri ya nufi gadon tare da rike mata hannu yana hawaye kaman karamin yaro har dakin da za’a kaita suka shiga hannunshi na manne da nata yana hawaye tare da fadin get up aysha tashi kiga yaranki plz kowa dake wajan yaji tausayinshi musamman yusuf da yake ganin gudan kanwar tashi a kwance bata motsi iya tashin hankali shima ya shiga Mum ce ta dafa ma A Majeed baya tare da fadin son kayi hakuri insha Allah zata tashi rungume Mum yayi yana kuka Mum nata bashi baki lokaci daya indo ta bude ido Tana ganin wani irin dishi2 a hankali ta Gama bude idan ta ganta a kwance mutanan dakin ta fara kallo lokaci daya kuma abunda ya faru ya dawo mata ido ta kuma lumshewa sannan ta bude karaf ya sauka akan na A Majeed Da sauri ya kira sunanta da aysha murmushi ta sakar mai da sauri yace mum ta tashi Alhmdlh nan Yusuf ya fita ya kira Dr ta dubata tace komai normal dama ta tsorata ne sosai tun farko shiya ja mata suman da tayi yanzu dole ta kwana dan muga yanayin jikin, sai a sannan A Majeed ya kalli yaran tare da amsar wanda ke hannun mum ya mika ma indo tare da fadin kinga dani suke kama dariya tayi kowa ya fara mata sannu tare da barka fita Su Mum sukayi aka barta ita da mijinta zainab kam Gida ta wuce nan A Majeed ya fara fadin aysha dama nasan ba zaki mutu ki barni ba dariya tayi tare da fadin hakane nima bazan so in tafi in barka ba kodan yarana ma zanso in rayu dan kar suyi rayuwa irin nawa, matseta yayi da karfi a jikinshi yana fadin I love You baby macen ce ta tsala ihu da sauri ya Saki indo ya dauketa yana jijjigata Mum ce ta shigo ta amshi yarinyar tare da bama indo ita tace yunwa take ji, indo kunyan amsan yarinyar tayi mum tace amsheta mana aysha babu yanda ta Iya dole ta amsa tare da fadin Mum ina kayana? Mom ta janyo mata akwati ta Dan tashi kadan ta dauko hijab tasa sannan ta Fara bama yarinyar nono Mum dariya tayi tare da barin dakin ganin Mum ta fita yasa A Majeed komawa kusa da matar tashi yana ma sauran yaran wasa, inna Maryam ce ta shigo dakin ita da mum hannunsu dauke da basket bayansu mai aikin Mum ce dauke da flask da kayan tea indo tace inna Maryam saukan yaushe? Tace yanzu nan indo ta gaidata inna maryam ta amsa tare dayi ma indo barka, inna Maryam ta hadama indo Tea mai kauri tare da zuba mata farfesun naman rago amsan yarinyar tayi ta ajiyeta sannan taba indo Tea din da naman amsa tayi ta Fara ci duka naman ta cinye inna Maryam tace bari a karo miki tace a’a ya isa, A Majeed yaso ya kwana wajan matarshi Mum ta korashi inna Maryam ce ta kwana da ita Yusuf suma suka shigo suka kara yi mata barka tare da sallama suka wuce washe Gari wajan karfe 7 A Majeed yazo asibitin nan inna Maryam take ta tsokananshi wai yayi sammako shidai babu abunda yake yi sai dariya wai yau shine yake da yara har uku, ikon Allah, mum itama tazo asibitin tare da abinci nan aka zuba ma indo shima zama yayi suna ci tare Mum fita tayi dan taga dan nata wani sabon fitsara ya koyo, Abdul Da matarshi suma sun zo asibitin Sun dade kafin suka tafi A Majeed babu abunda yake sai daukar yaran hoto sai wajan karfe 5 Dr ta sallamesu dan taga jikin da sauki, gidan Mum suka nufa direct, A Majeed sai kashe kudi yake tayi akan yaran Zainab bata kara zuwa ba tunda tabar asibiti dan tace sai ran suna zata ta gefen Mum ma sai kashe ma yaran kudi take tayi……… Yau akayi sunan yaran inda aka kashe naira kaman babu gobe namijin yaci sunan dad muhd suna kiranshi da irfan dayan kuma Aminu sunan mahaifin indo suna kiranshi arfan macen kuma sunan Mum fatima suna kiranta da zarah Zainab itama tama yaran kaya na kece raina duk da tana jin kishi amma Allah yasa mata son yaran sosai a ranta, haka akaci suna aka watse kowa nasan barka, saida indo tayi arba’in sannan ta koma gidanta Mum tasa an hada mata ita sosai yanzu da masu aiki uku aka hadata dasu, koda ta koma Gida taga dakin da aka ware ma yaran an kashe kudi sosai komai ansa na wasan yara kala2 ga gadajensu nan guda uku kowa da nashi ji tayi an rikota ta baya ihu tasa a hankali ya furta kin cika tsoro Baby dariya tayi tare da turo baki kuma yace mai nene kuma? Tace nayi missing dinka yace really toh muje a amshe ni ido ta zaro tare da fadin ba irin Wannan missing din ba yace toh ni nayi wata nawa banji dumin jikinki ba dariya tasa tare dayin dakinta da gudu shima binta yayi a dakin yaga yaran ko wanne adan gadonshi mai keke yana tura Su, yace Baby nikam mai zan miki kiji dadi a rayuwa? Dan shuru tayi can tace inaso inje garinmu domin inga inna tani da Baba Musa, shuru yayi kafin yace banda wannan mai kuma kike so dariya tayi tare da fadin soyayyan miji na, yace ai kin samu tun tuni yace plz tell me mai kike so? Tace kaman yanda nace inason zuwa garinmu da kuma soyayyarka, yace shikenan ki bari yara suyi kwari sai muje kinji kai ta daga alaman toh nan aka shiga duniyar da yara basa zuwa sai sun girma😝 ranan dukansu Sun san sunyi missing din junansu sosai watan indo biyu da haiyuwa ta fara aiki a hspt dinta lokaci kadan tayi suna sosai danta kware a aikinta abban Yusuf ya sami lafiya sosai babu inda baya zuwa gashi Yusuf ya rike Mai amana na dukiyarshi dan lokacin da yake ciwo Yusuf yake ta juya dukiyar gashi an sami riba sosai ganin haka yasa yace Yusuf yaci gaba da juya kudin sannan ya dinga raba riban uku biyu na Yusuf daya nashi Yusuf rasa bakin godiya yayi dan murna a lokacin zaliha Tana dauke da ciki itama na wata 7 Yusuf ya kara kudi sosai ya kara kyau da girma.

STORY CONTINUES BELOW

*Bayan shekara daya*
Indo ce cikin wani tsaddan leshi anyi mishi dinkin doguwan riga tayi kyau sosai yaranta suka nufota suna dariya su ukun duk wanda ya gansu zai ce sun wuce shekara daya dan sunyi girma sosai da wayau, rungumeta sukayi suna dariya ita dariyan tayi tare da fadin karku fadar dani dai2 lokacin A Majeed ya fito yana fadin muje yaran daddy yau zaku kauye koh? Kai suka daga duk da basu san mai yake nufi ba, fita sukayi indo Tana fadin ni garinmu ba kauye bane murmushi yayi sunyi ma Zainab sallama wacce har yanzu burinta bai wuce ace A Majeed ya Saki indo ba, fita sukayi cikin wata katuwar jeep driver ke tuki suna baya shida yaranshi da matarshi da yake kalan jeep din nanne mai baya biyu, wayanshi ne yayi ringing Yusuf ya gani dauka yayi tare da fadin mun fito yanzu kuna ina,ban san Mai yace mishi ba naji yace ga munan zuwa, Sun hade da Yusuf da matarshi da yaranshi biyu abba da Hauwa, suma a tasu motar tafiya sukeyi kaman zasu tashi Sama har suka karasa garin taraba yaran duka sunyi bacci indo tunda suka zo garin gabanta ke fadi amma ganin Sun wuce yasa ta kalleshi tare da fadin ina zamu yace jalingo gobe zamu dawo taraba yamma yayi yanzu ya kamata mu huta bata kara cewa komai ba har suka karasa gidansu na jalingo gidan da aka fara kawo ta nan suka sauka Yusuf dai yace hotel zasu sauka dan bazai kwana gidan kanwarshi ba duk da A Majeed bai soba haka suka tafi kafin su shiga gidan saida yasai musu abinci bayan ya dauki yaran ya kaisu falo masallaci ya nufa dan anata kiran sallah magrib, ita kam indo abubuwan daya faru a gidan ne yake ta dawo mata sai dariya take tayi da yake Tana fashin sallah a haka ya dawo ya sameta Tana dariya kallonta yayi tare da fadin maman uku lafiya kuwa turo baki tayi tare da fadin baban uku driya yayi sosai tare da fadin kina tuna baya ne koh?  Lokacin da kike tsoran tv dariya tayi mai karfi tare da tashi takai mai dukan wasa a kirji wajan ya rike tare da fadin ashhh Baby akwai zafi fah, tace toh bakai bane kake tsokana na, yace toh na daina kar a hanani abun dadi ido ta rufe da hannu Tana dariya, yace wai yaushe zaki gama wannan abunne nifa gskya a matse nake tace yaranka dai na wajan dariya yayi tare da fadin bari ma in tashe su suci abinci sai su kwanta tashin su ya farayi bayan Sun tashi shida kanshi ya basu abinci sannan ya kaisu daki ya musu wanka tare da sa musu kayan bacci suka kwanta fitowa yayi daka ganin alama shima wankan yayi yace ma’am kema muje in miki wankan tace nagode bana bukata yace kinma isa dariya tayi tare da fadin kazo muci abinci yunwa nake ji yace ohkey nan suka Fara ci har suka koshi suka nufi daki Dan su kwanta su huta.

Washe gari bayan Sun tashi sunyi breakfast wajan karfe 9 Yusuf yazo suka nufi taraba, kauyansu suka shiga yana nan yanda yake babu wani canji har yanzu dai basu da wuta sai dai wasu gidan an danyi gyare2 ta wajan gidan mai gari suka wuce nan ta hango SULAIMAN cikin wasu matasa duk ya rame kaman bashi ba wani irin hawaye taji yana son zubar mata amma ta dake dan tasan yanzu gogan nata zai fara tambaya idan kuma yaji akan abunda take kwallan tasan zaiyi fushi dai2 kofar gidansu Yusuf ya tsaya dan haka driver dinsu shima ya tsaya gidansu yana nan yanda yake sai kwanon daya cire akasa kalan abun itacen nan gidan ya tsufa sosai, indo ce ta fito Yusuf yace ta shiga taga gidan, gabanta na fadi ta nufi gidan babu kowa saida tayi sallama sannan wata ta fito cikin wasu kaya kaman tsumma saida ta kalleta dakyau sannan ta gane abu ce ita koh abu kallon indo takeyi baki sake tana mamakin kyanta tare da fadin anya mutum ce kuwa Baba Musa ne ya fito ganin abu bata dawo ba shima bakin ya Saki cikin wata shadda duk ta kode gashi tasha faci duk da hakan akwai wajan daya yage, hannunshi daya yana makale a kirji daka gani wani gefen jikinshi ya shanye ne yace hjy wa kike nema ne? Tace Baba musu indo ce cikin kuka yace karya kike yi indo ba haka take ba tace wlh nice baba shima kukan ya Saki yana fadin na gode Allah da bai dauki rayuwa na ba iya tsawon wannan lokacin yau gashi na ganki zan roki gafararki duk da akwai aiki a gabana ban san inda zan sami Yusuf ba, cikin kuka tace Baba tare muke Dashi da sauri yace kice ya shigo mana nan ya shiga daki ya dauko tabarma duk tayi datti ita kam abu mutuwar tsaye tayi dan ta kasa ko motsi, Yusuf tare da A Majeed suka shigo da yara da zaliha A Majeed babu komai a ranshi sai tausayin matarshi dama a irin nan tayi rayuwa, indo batai zaton mijin nata zai zauna akan tabarman ba amma sai taga ya zauna, Abu ce ta fashe da kuka Tana fadin dan Allah indo ki gafarta min nayi miki laifi babba a rayuwa duk kuma shairin tani ne da xugani da takeyi dan Allah ki yafe min nima gashi tun a duniya na fara ganin abunda na shuka, indo tace karki damu Abu na yafe miki ina inna tani? Abu tace Tana ciki nan abu ta shiga ta dauko tani dake daki Tana jinsu Tana kuka ana kawo ta duka suka toshe hanci ta rame ta Side babu kyan gani ga ciwo wajan nononta daka gani cancer ne dan wajan yayi kaman donut yayi rawun, tani ta Fara fadin yusuf indo sai kuma ta kara sakin kuka tare da fadin dan Allah ku gafarta min kunga yanda Allah yayi dani koh, duk da abunda ya faru baisa na hakura ba haka naita bin malamai dan mijinki ya koroki ya auri abu wata rana naje wani daji na fadi na soke nonona tun daka lokacin ya fara ciwo harya fara ruwa nasha Magani har na gaji tun ina iya tafiya har na kasa gashi ance sai nayi na asibiti wai daji ne gashi babu kudi mun so mu saida gidan nan mai Gari ya hana wai naku ne duk da a lokacin muna ganin munma yusuf shairi yabar gidan ai gidan ya zama namu Ashe ba haka bane gashi duk yanda naso Sulaiman ya Saki abu lokacin yaki dan nayi mishi mugun sihiri kafin ya yarda ya auri Abu ya rabu dake danginshi tunda suka san asiri aka mai ya auri Abu suka tsaneta sosai shiko kullum santa yake yi kaman ranshi ina ta zugata taita hadashi fada da yan uwanshi harta uwarshi baya Raga mata akan Abu ganin abun nata na yawa yasa suka tashi tsaye wajan addu’a har kadarin mu ya karye kuka ta Saki sosai kafin taci gaba da fadin ranan naga tashin hankali domin aljani aka tura mai yasa ya auri Abu rannan ya fita ya fadi aka dawo dashi Gida yana ta sambatu nan aka gane iska ne aka kira liman ya fara karatu nan aljani yayi magana tare da fadin karku konani dan Allah nima aiko ni akayi nan ya fada musu wanda ya aiko shi nan ya fita koda sulaiman ya farfado aka fada mishi abun daya faru wanda yayi kuka ya farayi tare da fadin yaushe na auri wannan mara tarbiyan ni ban ma san nayi auren ba tashi yayi cikin fushi ya nufi dakin Abu…….TAMBARIN TALAKA 💅*

+

                     *NA*

                    
*MARYAM ALHASSAN DAN’IYA*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*Vote me on wattpat* *@maryam-obam*

*WWW.maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

                      245to250

*DEDICATED  TO….*

*NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO*

*LAST PAGE*

Koda ya shiga ya rufe kofar ya fara jibgarta Tana ta ihu jin ihun nata yasa iyayen shi suka nufi dakin akan ya bude kofar amma ina baibi ta kansu ba sai faman jibganta yake saida mai Gari ya kira matasa suka balla kofar aka fito da abu ya mata jina2 ko gani batayi dan ya kumbura mata fuska jini ta hanci ta baki duk fuskanta ya canza ya kumbura sumtum ko kuka ta kasa dan azaba ga hakori biyu daya cire mata nan take yace ya saketa Saki uku tare da fadin tabar mai Gida kafin ya fito ya kara ganinta haka ta tawo Gida jina2 hankali na ya tashi naji raina ya baci duk da bani da lafiya haka na nufa gidan dan in musu tujara duk da ana tsoran mai Gari koda naje na tarar da mamanshi da yan uwanta na fara Bala’i haka suka taru suka min duka wanda shine silan kara durkushewa na ciwo yaita kamari tun daka lokacin na daina tafiya kuka ta saki tare da fadin nasan ba komai bane sai hakkin ku ganin ciwo naci na gashi babu Magani nace musa ya saida gidan nan mai gari da yaji labarin zamu saida gidan yace karmu fara haka muke ta zama gashi babu abinci abu kuma idan ta fita aita jifanta wai Tana bin boka haka muke ta zama a Gida Mlm gashi babu Sana’a gashi bintalo sunyi gobara sun kone ita da mijinta da yaranta, mutane sun tsanemu a kauyen nan wlh raban mu da muci abinci kwana uku kenan sai ruwa dan Allah indo ku yafe mana dan Allah wlh hakkin kune yake cin mu Abu itama kuka ta Saki tana kara roqan indo, Yusuf yace inna kiyi shuru mun yafe miki duniya da lahira tunda gashi abunda kika mana yasa mun hadu da arzikin mu, indo da fuskanta ya jagule da kuka tace inna ina inna jamila fah? Tani tace sun tashi daka nan Abu fita ki fada mata ga indo tazo, da sauri Abu ta dauko wani bakin hijab ta fita indo tace Ashe sun tashi? Tace eh jamila ta kasa zama saboda mun hanata sakat tunda tabar gidan nan bata kara lekowa ba, mlm musa ne yayi magana tare da fadin yusufa dan Allah ku yafema kawunku wlh duk shairin tani ne ita ta sani yin duk wani abu dana aikata wlh da badan wani abu ba dana rabu da ita da sauri indo tace kawu kayi hakuri karka rabu da inna ka yafe mata kaman yanda muma muka yafe ko Allah ana Mishi laifi ya yafe balle mu,yusuf ya amshe da hakane mlm musa yace naga bakin fuska su waye? Yusuf yace ga mijin aysha da yaranta ya nuna yaran da suka manne a jikin babansu dan tsoran ciwon tani suke ga iyali na ya nuna zaliha, mlm musa ya mika ma yaran indo hannu da nufin suzo suka noke kaman za suyi kuka yace kuzo yan nema, ya miko hannu kaman zai daukesu suka sa kuka tare da kankame babansu dariya Mlm Musa yayi tare da fadin kuyi hakuri bazan daukeku ba tunda baku sanni ba, ganin ya koma ya zauna yasa sukai shuru tare da yin ajiyan zuciya, A Majeed dariya shima yayi tare da fadin toh ya isa haka baza a daukeku ba, dai2 lokacin inna jamila ta shigo gidan ta kara tsufa amma babu laifi Tana cikin shiga mai kyau duk da kauye ne, indo da sauri ta tashi ta rungumeta Tana kuka inna jamila ma kwallan takeyi tare da fadin aysha Ashe zan sake ganinki a rayuwa, indo tace innata gani inna ta tana maganan Tana kuka sun dauki lokaci a haka kafin suka zauna inna jamila tace Ashe zan sake ganinki sai yasa naki barin garin nan dan kullum ina sa ran ganinki Allah Sarki indo na aysha indo Allah kenan mai yin yanda yaso inda a hanya na ganki bazan ganeki ba Ashe haka kike da kyau da fari kauye da wuya duk sun boye miki, dariya indo tayi tare da fadin innata ga Yusuf fah tace Allah Sarki Yusuf nan suka gaisa harda A Majeed kamo hannun zarah tayi Tana fadin kai tubarkallah yarinya kyakyawa Zarah batai mata kiwa ba ganin zarah a hannunta yasa su arfan suma zuwa wajanta suko su tani suna ta kallon ikon Allah yaran da suke manne jikin babansu amma yanzu sunje wajan jamila, Tani tace Abu ba’a basu koh ruwa bah, Yusuf yace a’a inna barshi mun gode, nan A Majeed ya ciro kudi bandir din kudi yan dubu daya2 yaba inna tani bandir daya dubu dari kenan yace gashi inna kusai kayan abinci yaba mlm musa bandir din guda uku yace gashi Baba ka rike wannan a hannunka mlm musa da tani sai washe baki suke, tashi yayi yace ina zuwa fita yayi jim kadan sai gashi ya dawo tare da karamin leda a hannunshi kudi ne cike a ciki inna jamila yaba dubu dari biyu yace gashi ta rike kafin su dawo nan taita godiya tana fadin Allah ya saka da alkhairi dubu dari yaba Abu itama Tana ta murna, Yusuf yayi mai godiya sannan yace aysha inaso a kira liman ya raba mana gidan nan domin ni nawa zan barma su Baba tace nima abunda nake shirin yi kenan amma ban Sani ba koh mijina zai amince? A Majeed murmushi yayi tare da fadin baki da matsala aysha duk abunda kika yanke nima na amince nan mlm musa yaita rafka godiya harda kuka itama Tani harda kuka Tana godiya Yusuf yace zansa a gyara gidan zanje wajan mai gari inbar komai a wajanshi sannan zaku koma wani gidan kafin a gama nan, inna ke kuma zamu asibiti dake a duba ki, tani kuka take sharbe2 Tana godiya tare da fadin su yafe mata tayi kuskure *hmmm rayuwa kenan sai yasa hausawa ke cewa d’a na kowa ne baka san mai rikeka ba duk Yaron da aka baka rikon shi kiji tsoran Allah ki rikeshi amana dan baki san gaba ba May Be shine zai rikeki kar kice wai kina da yara zasu kula dake bafa lallai bane yaran nan naki in Sun girma suji qanki ba, inma sun tausaya koda ciwo ya kamaki sun biya kudin Magani akwai laluran fitsari bayan Gida kuma idan lokacin yazo ga girma ga ciwo kina bukatan kula ba lalle bane yaranki su miki komai ba wlh sai yasa wlh muji tsoran Allah musamman ma mu mata ni wlh wasu matan mamaki suke ban mata fah mune aka sani da tausayi amma saboda an baki riko sai ki cire tausayinki akan dan rikon kita gana mishi azaba haba mata ina tausayin namu yake, sannan maza kuma kuji tsoran Allah ku daina kama maganan Mace har sai kunyi bincike domin wlh mata akwai iya kulla makirci ko shaidan na tsoran kaidin Mace idan Mace ta zauna ta tsara karya sai kaji namiji ya dauka har an fara Bala’i Dashi wlh ko mamanka ta fada maka magana akan wata yana dakyau kayi bincike akai sosai kafin ka dauki hukunci domin wlh rashin bincike akan abu zai sa mutum daya san, akwai kiraye2 da dama da nake samu akan irin wannan matsalan musamman mata masu zama Gida daya da uwar miji  zan danyi bayani kadan akwai wacce ta turo min txt wai Tana zaune Gida daya da uwar mijinta komai tana mata na biyayya amma uwar mijin ta tsaneta taita tsangwamanta Yaron duk yana lura da irin biyayyan da take ma mamanshi kuma yana kyautata ma matar tashi dan yana jin tausayinta akan abunda mamanshi take Mata gashi kuma ita tana Mata biyayya wai yanzu uwar mijin taita kulla mata shairi wajan mijin tun baya kamawa har ya fara yarda yanzu ta hadasu rigima har tasa ya saketa Saki daya gashi yana son matarshi ta hanashi ya dawo da ita wai ya kara aure…..  Haba mata mai yasa idan danki yana da Mata sai kibi ki tsani matar karfa ki manta kema fah Mace ce shin dama ciwon y’a Mace da ake cewa na y’a Mace karya ne tunda gashi yanzu dan Mace na auren danki saiki tsaneta karki manta fah kema kina da yara mata idan aka musu abunda kike ma matar danki zaki ji dadi koh da baki da yara mata Ai kina da yaran yan uwa mata wanda na tabbata idan aka musu abunda kike ma matar danki ranki zai baci dan Allah mata mu dinga kawar da idonmu akan matan yaranmu da yan uwanmu domin duk abunda kama dan wani sai anma naga majority mata basa son uwar miji saboda irin wannan matsalolin sannan mata masu tsanar uwar miji ku daina domin itama uwarku ce tunda ba zaki so danta ba kice ita baki sonta dan ance maso Husaini yaso hassan Allah yasa mu dace* su Yusuf sunje wajan mai Gari inda suka sami su Sulaiman a can shi baima gane indo ba bayan an gaisa nan Yusuf ya gabatar da kanshi mai Gari yace au Yusuf ina tama kallon sani kai kuma tunda kazo sai ka tafi kaki dawowa kaga kanwar taka? Yace eh ga tanan mai Gari indo ce wannan haka sai a sannan sulaiman ya kara dagowa ya kalleta danshi a zaton shi larabawa ne suka zo ya bude baki zaiyi magana yaji yusuf na fadin ga mijinta nan da yaranta sulaiman hawaye ya fara fita a fuskanshi ya tashi yabar wajan indo itama ido ta bishi dashi domin sulaiman ne masoyinta na farko wanda ya sota tsakani da Allah ganin yabar wajan yana hawaye yasa itama guntun hawayen da take boyewa ya fito da sauri tasa hannu ta goge dan kar mijinta ya gani, nan mai gari suka gaisa da A Majeed inda Yusuf yace zai bada a gina masu gidansu a rushe wannan yace MA mai gari zai bada amanan komai a wajanshi A Majeed yace Yusuf ka barshi ni zanyi komai nan ya dauko wani akwati yaba mai gari tare da fadin 6mil ne a fara aikin mu gani mai Gari yace ai yayi yawa gidan bashi da girma A Majeed yace a fara toh sannan a nema musu wani gidan su zauna kafin a gama, nan mai gari ya amsa da toh tare da kallon Mlm musa yace mlm musa ka gode Allah yarannan basu rikeka ba mlm Musa yar guntun kwallanshi ya fito yace hakane shairin shaidan ne da kuma makiran matar dana samu , suna cikin magana sai ga dan jummai wasû samari sun rukoshi sun mai jina2 ga jummai kuma nata kuka mai gari yace lafiya? Matasan suka ce kanwar mu yama fyade kuma yasan yana da HIV nan mai gari ya Saki salati tare da kiran yan sanda aka tafi Dashi jummai nata bada hakuri akan a barshi mai gari yace idan ta kara magana sai an hada da ita taja baki tayi shuru tare da kokarin barin wajan mlm musa yace jummai ga indo koh baki ganeta ba ashe Allah ya taimaketa da yanzu danki ya kashe ta da sauri ta kalli indo sai kuma ta kara fashewa da kuka tace Allah sarki wlh yaso ya aureta lokacin nice na shiga na fita na hana auren mai gari yace kinga koh kin taimaketa ga tarin zunubi da kika tara ma kanki haka jummai tabar wajan jiki a sanyaye, Yusuf yace tunda A Majeed ya dauki komai shima ya bari ya samu lada yakai Tani asibiti hakan akayi a ranan aka samo mota aka tafi da ita asibiti su indo kuma suka koma Abuja dan A Majeed yace baza su kara kwana ba, bayan sun Isa Abuja taga A Majeed ya wani tamke fuska bata kulashi ba taja hannun yaranta sukai ciki tunda suka dawo bai shigo ba Dan yau gidan zainab yake, ta mishi uziri dan tace May be gajiya yayi ga yaranta sun dameta dady dakyar ta samu sukai bacci washe gari har wajan 5 bai shigo ba gashi ta kirashi yaki dauka sai wajan isha taji ihun yara suna daddy lokacin Tana kitchen batai fushi ba ta fito domin bai taba mata haka ba tace daddy lafiya kuwa inata kira kaki picking kodai gajiyan ne yasa haka? Wani irin kallo ya mata Da yasa tayi shuru Tana mamakin mai tayi wasa yayi da yaran sannan yaja su dakinsu yasa musu kayan bacci yace suyi bacci dare yayi dan kullum haka yake musu sai yasa jiya da bai zoba Suke ta rigima, bayan Ya fito ne ta nufeshi amma kallo daya ya mata ya kauda kai tace my one tafiya yaci gaba dayi bai tsaya ba da sauri ta nufeshi tayi hugging dinshi Tana kuka tare da fadin mai nayi mijina yake fushi dani kukan nata yaji har ranshi a hankali ya rikota tare da dago mata Kai yace aysha mai yasa kike kuka lokacin da kika ga saurayinki ya tashi dama har yanzu kina sonshi tace haba My One kasan Kai daya nake so dama akan wannan abun kake fushi kawai tausayi yaban saketa yayi tare da fadin sai kiyi tajin tausayin nashi ai kara rikeshi tayi ta fara rarrashin shi dakyar ya hakura tare da fadin baya son ma ya kara jin tayi maganan sulaiman dariya tayi sosai tace ta yarda ankai Tani da kwana biyar asibiti ta rasu wanda yasa indo dole ta koma kauyen kasancewan an fara aikin gidansu a gidan mai gari ake zaman makoki sam A Majeed yaki yarda indo ta kwana wai jalingo zasu koma hakan akayi dan su biyu suka zo yaran na wajan Zainab dan ta yaye su nono bai damesu ba, kwanan su uku suka koma taso ta dauki Abu amma yusuf yace gidanshi zata koma da zama tare da Abu Yusuf ya koma abuja, duk wannan abunda ake indo nada ciki bata sani ba dan tana period dinta rannan suna zaune da A Majeed yace Baby anya ban baki ajiya ba kalli yanda kika kara cika da kyau tace haba My One yanzu idan nayi ciki ai na shiga uku banfa manta wuyan da nasha ba  kuma su zarah ko shekara biyu basu yi ba kaga aiko su sun ishemu yace Baby nifa ina son yara wannan ma Mum so take mu bata su naki ga Zainab itama Tana So kinga idan kika kara haiyuwa sai aba Mum da zainab tunda yan uku nake baki dariya tayi tare da fadin Na yafe tashi tayi ta nufi daki dan itama Tana dan jin canji aiko gwajin farko data gwada taga Ciki ne cikin tashin hankali ta koma inda ta barshi tace my one na shiga uku wlh ina da ciki dan Allah muje a zubar wlh banso in kara haiyuwa yanzu, daka mata tsawa yayi tare da fadin wlh idan kika zubar min da ciki saina Saba miki wlh yana fadin haka yabar falon rai bace ita ko kuka ta Saki mai karfi tare da fadin wlh bazan yarda ba inna mutu aishi kenan dama ba sona yake ba kuma ciki ne wlh bazan yarda Dashi ba koda A Majeed ya fita dakin Zainab ya nufa ya ganta Tana kuka da sauri ta Fara gogewa kallonta yayi tare da fadin Zainab lafiya kuwa? Cikin kuka tace A Majeed na kasance ina son haiyuwa naje asibiti da dama ina amsan Magani dan in haiyu duk bada saninki ba Amma daka baya sai akace bazan iya haiyuwa ba wai mahaifata ta sake inko na samu ciki komai zai iya faruwa Dani duk da bama sa iya tunanin zan haiyu kullum inna Tuna da wannan abun nakanyi kuka ina dana sanin shan……  Shuru tayi dan tunawa da tayi dawa take magana, yace Zainab shan me??  Shuru tayi lokaci daya kuma ta kara sakin kuka tace A Majeed shan maganin hana daukan ciki ya jefani cikin wannan Bala’in dan Allah ka yafe min wlh nayi maka laifi ina shan Magani ba tare da saninka ba gashi yanzu ina son haiyuwa ido rufe amma babu dama kukan da takeyi ne duk da ranshi a bace yake yasa ta bashi tausayi har ya fara rarrashinta tare da tunanin aysha na gudu ita gashi wannan Tana nema duk da ita taja ma kanta.

STORY CONTINUES BELOW

A Majeed fushi yake da indo sosai Dan har yanzu Tana kan bakanta na zubar da ciki har Zainab ta gano suna fada hakan ya mata dadi kuma tasan dalilin fadan tare da alkawarin saita zubar da wannan cikin na indo tunda baiyi kwari ba rannan ta shiga dakin indo takai mata kunun aya indo ta amsa tasha Tana fadin yayi dadi tasha da yawa Zainab dadi takeji sosai ta tashi tabar dakin indo ta koma nata dakin A Majeed koda ya dawo gefen Zainab ya nufa kaman yanda yakeyi yanzu IN baya dakinki inya dawo wajanki zai fara zuwa kafin yaje inda zai kwana Tana hangoshi yana zuwa ta window ta fara wayan karya tare da fadin wlh kin San dai ni ance bazan haiyu ba amma kinga yar uwata aysha ta haiyu yanzu ma ciki gareta amma kin san wani abun mamaki wlh maganin zubar da ciki naga tasha dazu dana shiga gidanta kalan wanda kwanaki kika sha lokacin da mijinki yace ki zubar da cikin ki koya sakeki, ni wlh tausayin A Majeed nake…….  Bai karasa shigowa dakin ba ya nufi gefen indo koh gani ba yayi aiko yana Zuwa ya ganta a falo kafanta duk jini ranshi ya kara baci kenan dagaske ne ta zubar mai da ciki baiko lura da halin da take ciki ba yace aysha sai yau na tabbatar da bakya kaunata bakya sona Allah ya isa tsakani na dake kinji darajan yaranki amma dayau sai nasa an kulleki saboda kin zubar min da jini na ban taba tunanin har yanzu akwai sauran kiyayya naba a cikin ranki ba, aysha ki tashi kibar min Gida bana bukatar in kara ganinki a rayuwa na zanyi yaki da zuciya na in cire sonki kije ki auri saurayinki wanda kike so ki fitar min daka Gida yanzun nan kuka takeyi ga azaban da takeji tace wlh ban zubar ba banyi komai akan cikin nan ba fita yayi fuuuuu yaranshi ya kwasa dake waje sukai mota ya fita fuuuu daka gidan Zainab kam murna ya kamata tare da fadin Alhmdlh, indo dakyar ta tashi tayi toilet ta gyara jikinta tasa pad tare da daukan wasu kaya dasu ATM dinta da kudaden dake wajanta duk wasu abu mai amfani ta dauka dakyar take jan akwatin ta fita daka gidan Zainab na kallonta ta window tana ta tsallan murna burinta ya cika yau, shiko koda ya fita yama rasa inda zashi kai yaran yayi wajan snack yasai musu sannan ya dawo Gida ranshi a jagule koda ya shiga gidan bai ganta ba dakin yaran ya kaisu yasa musu kayan bacci yace su kwanta, dakinshi ya shiga ya kwanta tare dajin zafin abunda aysha tayi mai yasa mai yasa aysha mai yasa kika zubar min da jini na Aysha mai yasa kika tsaneni har haka laifin da na miki shine har yanzu kika kasa yafe min aysha mai jini na ya miki kika zubar min Dashi bayan ni zaki hukunta bashi ba kuka yake sosai tare da takaici ranan ko bacci ya kasa sai tunani duk da yana so ya cire ma kanshi tunanin ina ta nufa yanzu amma ya kasa,  ita ko indo koda ta fita hotel ta kama washe Gari da safe ta shiga motar taraba ta nufi garinsu wanda har an gama gyaran gidan sai wajan karfe 4 takai nan mlm musa yayi murna da ganinta yace aysha ina yaran damai gidan? Nan tasa mishi kuka cikin damuwa yace aysha lafiya kuwa nan ta fada mishi abunda ya faru tare da rantsewa akan bata zubar da cikin ba, yace kai abu baiyi dadi ba amma kiyi hakuri muga zuwa nan da kwana biyu zan nemeshi dan nasan yanzu yana fushi kiyi hakuri insha Allah zai fahimta kema aysha dole ya zargeki ai tunda kin nuna bakya son cikin amma kiyi hakuri komai zai wuce tace toh Baba, ginin gidan anyi 2bed room sai daki daya a waje da toilet nan indo tace zata dinga kwana akwai gado a dakin gidan yayi kyau sosai inna jamila kullum Tana gidan dan mijinta ya dade da rasuwa kullum Tana kwantar ma indo hankali tare da bata baki Mlm musa ya amshi number din A Majeed ya jishi a kashe wasa2 yau satin Indo biyu wayan A Majeed kuma a kashe, indo ta rame ga kewan yaranta da take yi, indo kullum Tana jin wasu abubuwa a jikinta ta fadama inna jamila tace suje asibiti hala cikin bai zube ba dan yana haka aiko indo ta shirya suna zuwa asibiti aka duba ta tare dayin scan nan aka gano cikin na nan bai zube ba amma sun bata bedrest dan Tana bukatar hutu saida tayi sati biyu aka sallameta tare da bata Magani jikinta yanzu ya mata karfi ta dai rame ta kara haske dadinta daya da cikin bai zube ba, Abu daya ke damunta yanda yaki bata uzuri yaki sauraranta gashi yanzu ya shareta wayanshi a kashe wani hawaye taji yana zubar mata dama ba sonta yake ba, sallaman Mlm Musa ne yasa ta fito ganin wanda suke tare yasa ta koma daki da sauri Tana kuka yaranta ne suka shigo dakin suna fadin Mummy suna tsalle najin dadi, jim kamshin turaranshi yasa ta gane ya shigo dakin rikota yayi ta baya yana fadin am so sorry nayi kuskurem da ban saurareki ba duk da a lokacin kona saurareki bazan yarda dake ba dan abunda naji nan ya bata labari tare da fadin yanzu ma Zainab Tana gidansu na saketa Saki daya cikin kuka tace mai yasa yace saboda na gano itace ta baki drink kika sha tasa miki Magani Da sauri tace taya ka sani yace naji Tana fadama kawarta ne, indo tace wlh ranan taban kunun aya nasha yace naji komai kiyi hakuri ki yafe min tace naji amma saika yarda zaka dawo da Zainab zan hakura bata fuska yayi tare da fadin plz kar kisa nayi abunda banyi niya ba, tace plz My One Zainab na sonka kuma san naka yasa tayi duk abunda tayi dakyar tayi convincing nashi yace zai dawo da ita din mlm musa ya kara musu nasiha inda indo tace Baba ina neman alfarma yace name fah tace Baba zamanka babu mata hakan yana sani cikin damuwa babu mai kula da Gidan da gyarawa yace hakane aysha nida na tsufa ina ni ina aure tace Baba dan Allah ka auri inna jamila dariya yayi na manya yace toh saiki mata magana inta amince indo tashi tayi ta nufi gidan jamila duk da A Majeed bai so ta fita ba ta mata bayani dakyar inna jamila ta yarda wai ita ta wuce aure a ranan mai gari ya daura aure A Majeed yaba mlm musa kudi masu yawa wai ya fara Sana’a dasu a kalla yakai million biyar itama inna jamila ya bata kyautan kudin, a ranan ya dauki matarshi suka koma Abuja kwanansu biyu tasa yaje ya dawo da Zainab wacce a yanzu tayi dana sani kuma ta gane duk wani abu da zata kulla ko tayi bazata canza yanda Allah ya tsara ba gashi duk kudin nata da mulkin babanta gashi Tana zaune da kishiya wacce take ganin tafi karfinta gashi duk kudinta da mulkinsu bazai bata yara ba ko soyayyan miji wanda tasan yanzu baya sonta kawai dai yana zama da ita ne sai yanzu tasan kudi da mulki bashi bane komai mutunci yafi kudi tunda kudin nata bai tsinana mata komai ba saima tozarci.

Bayan shekara uku indo yanzu yaranta 7 zarah arfan irfan, sai kuma ta kara yan uku duka maza adnan farhan anan, sai Mace daya yar auta yusra yanzu zarah ta koma wajan Zainab wacce yanzu ta dauki indo matsayin kanwa kuwa abokiyar shawara indo tayi suna sosai ta kware wajan aikinta Tana daya daka cikin doctors din da ake alfahari dasu a Nigeria, Zainab da indo kuma sun hada kasuwanci sunayi tare, Abu itama tayi aure ta auri yazeed itama yanzu an waye kuma ta shiga makarantar never give up harta gama ita yaronta daya aka samai musa sunan babanta suna kiranshi da aryan, matar Abdul ma yaranta biyu sunyi ma indo takwara aysha sai muhd,sulaiman ma A Majeed ya samar mishi aiki, yusuf shima yanzu ya kara kudi ba kaman da ba, A Majeed ya Kara samun kwanciyan hankali ga kudi sosai da yake samu yanzu dan yanzu yabar aiki ya koma kasuwanci kudi kota ina suna shigo Mai ga kwangilan da mahaifinshi ke bashi da wasu ma, ya gina musu wni mahaukacin Gida babba gefen yara daban ga wajan kayan wasan su nan kala2, indo ce zaune ita da A Majeed tace nikam ina son zuwa Egypt inga ummi da abba yace gskya ya kamata kam nan aka musu visa harda Mum da yara duka da Zainab suka wuce Egypt sunyi yawo sosai indo har gidan kawarta fatima taje sukai zumunci sati biyu sukayi suka dawo indo taji dadin ganin ummi da da abba duk da sun kara tsufa sosai, haka a taraba mlm musa da jameela suna zaman lfya suna cin mai kyau su sha mai kyau dama ance *TAMBARIN TALAKA* cikin sa, sai yanzu yasan yayi aure, rayuwan indo da mjinta sai dai muce Alhmdlh nima dai a nan zance ALHAMDULILLAH.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *