TANA TARE DANI CHAPTER A

 TANA TARE DANI CHAPTER A

ANAS

     K’auyen Bama dake jihar Maiduguri, Borno.

            Da yammacin ranan Asabar misalin k’arfe biyar da mintuna aka. Ruwan sama akeyi me ni’iman gaske, ga wani iskan dake hurawa me kad’a bishiyoyi da flawoyi, ko ina ya d’au sanyi. Tsit kukeji a garin, yara da manya, maza da mata kowa na cikin gdajensu, masu tafiya akan hanya kuwa sun faka gu d’aya, motoci dabasu fi a k’irga ba ke wucewa time-to-time. Can k’ark’ashin wata bishiyar ’yim na hango wasu samaruka guda hud’u wanda barasu gaza kuma barasu fi shekaru 17-18 ba.

        Daga nesa nake, amman hakan be hana ni tantance kyakkyawan cikin wad’annan samarukan ba. Wani kyansan ma sanda na gama k’arisowa, fari ne yellow shar da gashi kwance a duk sassan jikin d’an Adam da akasan na tsirar da gashi. Gashin kansa nada yawa saidai bawai afro tayi ba saboda tsantsin gashin bai tsayuwa, luf-luf yake kwance a kansa, bak’i k’irin yana yalk’i wane yasha mai.

      Saje ne kwance akan farar fatar fuskarsa wanda da ace yanada gemu da sun had’e. Gashin girarsa ba a cike take erin thick dinnan ba, silky yake a kwance d’an siriri wane yayi carving nasu. Dogayen eyelashes nasa wanda suke kallon k’asa santsi ne dasu. Bashida dara-daran idanunu, idanun nasa suna nan madaidaci da k’wayoyin idan nasa light blue wane na bature.

          Nasha jin ana cewa a Africans akoi masu blue eyes ban tab’a yarda ba sanda naga wannan saurayi. Hancinsa ma ba dogo har bakan nan bane, daidai yake cikin ‘yar fuskarsa wanda yakasance shi ba dogo ba bakuma gajere ba. Bakinsa light red yake d’an madaidaici cikin fuskar tasa. Dukda cewar ya d’aure fuska hakan be hana dimple na kumatun damarsa lotsewa ba wanda babu hakan a na hagun.

   A zaune yake amman hakan be hanani tantace tsawonsa ba, dogon na miji ne, yanada faffad’ar k’irji duk da cewar siriri ne. Ofcourse ana cewa d’an Adam bai cika goma but za’a iya kiran wannan saurayi hallitar data cike goma bansani ba halan ya gaza ta hali amman inde ta hallita ne kam masha Allah, Allah yabasa, ban tsammanin akoi macen da zata ga wannan saurayi bata kuma kallonsa ba. I mean ba mace kad’ai bama kowa in all.

      Sanye yake da mint blue T shirt wanda ya mugun amsar farar fatarsa, jeans na jikinsa kuwa tad’an kod’e alaman tasha ruwa. Rik’e yake da kara a hannunsa yana wasa dashi da siraran yatsunsa wanda suke nan kan ba na miji ba.

      Gefensa saurayi ne me kama da shi sak, saidai komi na wannan kyakkyawan yafi nasa, kuma shid’in be kai kyakkywan fari da k’war jini ba, duk yadda akayi wansa ne na jini saidai na kasa tantance wane babba cikinsu. Sauran biyun k’arshen kuwa chocolate skinned suke, saidai still d’aya yafi d’aya haske.

     “ANAS na mata kenan!” Cewar d’an bak’i na k’arshen tare da kewayo da kallonsa kan kyakkyawan cikin nasun wanda nake da tabbacin shine ANAS d’in yana mai murmushi wanda hakan ya bayyano da brown teeth nasa, tabbacin kanuri ne shi kenan. “Uhm uhm fa BAANA!” cewar me haske na gefen d’an bak’in da yayi magana yanzun kenan. BAANA yace, “ah’ah barni in tsokanosa de.” Shide kyakkywan nasu da ake kira da ANAS be tanka saba, hasali, yi ma yayi kamar besan ana magana a gefensa ba se b’antare karan dake hannunsa yakeyi yana kallon yadda ruwan saman ke sauk’owa.

        Wanda nake kyautata zaton wan Anas d’in ne yace da d’an bak’in gefen nasa “barsa de KASHIM, neman magana yake yau gun ANAS.” KASHIM ya karkato da kallonsa kan BAANA “aikam naga alama rad’au a fuskarka, kuma wallahi kasan inya shak’ure ka bame k’wato ka, kasan halin mazan namu. Ko mata ma bai ragar masu ba bale kai,” ya d’an yi shiru sannan ya k’arisa “gardi” Yafad’a cike da gatsine.

     BAANA yace, “hummm zagen dai, naga kap nan gardawa ne har Shettima k’anin mun ma(k’anin Anas knan)” Duk suka k’yalk’yale da dariya illa shi wannan kyakkywa da suke kira da Anas wanda yayi burning face sekace besan me kalmar dariya ba.

        Niko miemie na matsu injiyo muryan wannan kyakkyawan da suke kira da Anas. Yawancin anacewa wanda yafiye kyan fuska bai fiye zaqin murya ba kuma hakan ne sanda na jiyo muryan Anas na k’aryata wannan batu.

        “You see, ruwan nan na tsayawa barama kuganni anan ba to talk more of kumin tsiya mtschww.” Cewar Anas tare da watso musu harara sekace mace.

      Lallai! Allah yayi murya anan, muryar Anas sautin na miji ne da anji amman saidai ba tattausar murya bace, zaqi ce ga me sauroro, bakuma zaqi erin ta mata ba saboda yadda muryar ke cracking a hankali in yana magana.

       “Toh Anas meyayi zafi daga fad’in gaskiya? Ai gaskiya ce wallahi kap ‘yan matan garin nan basu san wani na miji sekai, narasa menene kake dashi bamuda, ni da bansanka bama se ince asircesu kayi.” Cewar Baana yana nuna yadda abin ke damunsa.

      “Ahhh lallai Baana ka soma zarewa” cewar Kashim cike da mamaki. “Yanzu har seka tambayi ko mesa matan garin nan basu kula kowa se Anas? Bakada ido ne?” Shettima ya karb’esa “gaskia da alama.” Kashim ya cigaba, “k’warank’wasa ace yau ni mace ce nima sena so Anas wanga blue eyes sekace bature, ko ka manta teacher’n English namu da ke sansa.” Suka sake sheqewa da dariya at once kuma sukayi shiru suna jiran tsiwar Anas to thier suprise be ce masu ko uffan ba miqewa yayi da niyar tafiya dukda cewar ruwa akeyi fuskarsa a tamqe kwata kwata abin be basa dariya ba.

        “Haba maza yi hak’uri mana karka fad’a min cikin ruwan nan zaka tafi!” Cewar Shettima wansa tare da rik’o shirt na Anas. Harara Anas ya galla masa da nufin ya sake masa kaya, kafin ace me k’arfin ruwan saman ya dad’a k’aruwa ba yadda ya iya dole ya koma ya zauna. “Wai zanso inga Anas yayi aure wataran, muga ya zena controlling wannan uban temper’n nasa da matarsa.” Cewar Baana. Take Shettima ya juya ya kallesa tare da zaro masa ido yana me masa warning.

         Dukda cewar Anas be tanka sa ba amman fuakarsa takoma ja alokaci d’aya ya had’e girarsa gu d’aya kallo d’aya za’a masa asan ransa ya b’aci ko dan meh oho? Kodan kiran kalmar ‘aure’ da abokin nasa yayi ne?

      Cikin tsiwa yake maganar ba alamar walwala a tattare dashi. “Baana don’t push it, nasha fad’a maka time without number bana san kana min maganan aure ko kuma ‘yan mata in muna tare, that goes to both of you” ya nuna Kashim da Shettima. “Banaso! Banaso! Inhar kuna sona yaci ace kundena for goodness sake!” Shettima ya dafe kafad’arsa “toh maza we are sorry.” kallonsa yayi ba tare da yace masa komi ba sannan ya kau da kai. Baana ya numfasa sannan yace, “toh ka fad’a mana why mana, kullum se kace bakasan kalmar aure ko budurwa amman baka tab’a gaya mana mesa ba, as friends we have to know ko bahaka ba Kashim?”

      Kashim ya giad’a kai “sosai mah kayi gaskiya.” Shettima kuwa dayasan mesa wan nasa bayasan wannan kalmomi guda biyu kawai ya kad’a kansa cike da nadama, yayi yayi ya ganar da d’an uwansa gaskia yakuma sa ya yafe wa mahaifiyar su amman ina abin ya gagara sam saboda abinda tayi ta sa Anas ya kariya, zuciyarsa a toshe take da bak’ar kiyayya is hardly aga Anas yana dariya, murmushin ma se in abu yakai ya kawo ne yakeyi.

      “I can’t tell you guys, I’m sorry saboda talking about it makes me sick kawai ni kudena tareraya ta da wannan magana banaso give me a break please.” Baana ze sake magana Shettima ya dakatar dashi ta aza yatsa kan lips nasa. In akoi abinda yafi damun wannan abokai guda biyu, (Baana da Kashim) befi wannan halin abokin nasu ba, ace da an kira kalmar aure se mutum ya b’ata rai, aure da ta kasance sunnah me k’arfi wanda kowani d’an Adam keda burin cikata. Gaskiya da abun duba.

     Kashim yakasa hakura shikam sanda ya kuma tambaya “Anas munsan baka san maganan nan amman ka dage ka fad’a mana, who knows! we might be of help.”

     Juyowa Anas yayi ya kalle sa tare da wata murmushin takaici ta gefen lips nasa wanda a sakamakon hakan ya bayyano da fararan hak’waransa da suke kamar an daidaita tsawonsu “help? Hmmm, k’arshen k’ok’arin da zaku iyayi shine ku dawo da ita kuma koda kunyi hakan ma barinyi appreciating ba saboda tafita a raina, bana san sake sata cikin idanu na, ta cuceni ta cuci two siblings d’ina Shettima da Amal, and most of all ta cuci Abuu (mahaifinsu). I don’t want her ever in my life.”

      Cike da mamaki Baana yace, “subhanallah wa kenan?” “Bade mahaifiyarku ba?” Kashim ya tambaya. Anas bece dasu komai ba Shettima ne ya giad’a masu kai da nufin eh mahaifiyar su Anas ke nufi. “Subhanallah! Subhanallah! Anas be kamata kana maganar mahaifiyar ka da ta kawo ka duniya haka ba, uwa uwa ce. Kome tayi maka ka tuna ita ta kawo ka duniyah.”

   “Thats my point!” Anas ya fad’a a masifanche. “Ita ta haifeni, ita ta kawo ni duniyah abin dayafi ban haushi fiye da komai kenan. Taya matar da ta kawo ni duniyah zata tafi ta bi wani na mijin daban ta bar family’nta a baya, How? Why? Mesa mata basuda tausayi? Mesa Allah yayi su mugaye masu san kai da abin duniyah mesa? Mesa basuda Imani? Mesa tayi breaking heart na Abuu haka? Har yau yakasa trusting wata ‘ya mace a duniya. Why does it have to be this way? Why? Mstchww!” yaja tsaki cike da haushi.

       “We are sorry” Kashim yafad’a cike da tausayi, so wannan grudge d’in Anas ke holding a zuciyarsa har yanzu saboda abinda mahaifiyarsa da Shettima tayi musu. Yau shekaru kusan bakwai kenan da sanin junansu amman be tab’a sanin mesa Anas ke cikin k’unci ba, kullum ba walwala a tattare dashi se yau. Tun ba yau ba yakeson jin me tarihin Anas amman Anas ko kad’an baisan maganar haka zalika ya hana wansa Shettima fad’a ma kowa. Yau d’inma halan saboda sun tak’ura masa ne yasa ya fad’a.

         Tun da suke a secondary school haka Anas yake, ko erin secondary school dating da akeyi d’innan Anas be tab’ayi ba hasali betab’a showing koda slightest interest akai ba ma. Unlike his brother Shettima daya d’au komi as k’addara yake living life nasa peacefully cikin walwala da dariya.

       Tunanin ya zeyi ya karkato da hankalin friend nasan kan gaskiya yake. Gyaran murya yayi sannan a hankalche yace “Anas we are all here for you, we are like brothers yanzu. Nasan how hard this must be for you amman dole kayi haquri ka rungumi qaddara kamar yadda Shettima yayi.”

       “No Kashim, I can’t baran iya ba. Karka had’ani da Shettima, Shettima was a small kid back then time da abin yafaru, definately ya manta komai bare iya tuna koda abu ba, but me? Da wayona da komai na wannan matar ta tattara kayakinta, we were all begging on our knees muna roqarta karta tafi… Mschww I don’t want to talk about it banasan ciwon kai, you two have heard enough.” Anas ya fad’a tare da miqewa daga mazauninsa. “Finally ruwan ya tsaya” yayi qoqari canza topic d’in, yana miqa wanda a sakamakon haka joints na jikinsa suke sakar k’ara. “Shettima lets get going, yakamata mud’an taya Ummee da aiki kafin Maghrib yayi” (Ummee; k’anwar mahaifinsu wacce takasance tamkar uwa a garesu tunda mahaifiyarsu ta tafi ta barsu take kula dasu).

        Shettima ya mik’e shima suka d’anyi manly shake da juna, “alright! Se mun had’u a masjid” Anas yace da Baana da Kashim da suke zaune har yanzu sannan ya juya shida Shettima suka soma tafiya.

     “Huh!” Kashim ya numfasa, “ina tausaya wa abokin nan namu, like sosai. Zuciyarsa ta riga ta toshe da tsantsan k’iyayya.”  “Sosai fa Kashim, but tsaya kaga wani abu yanzun nan ze dawo” cewar Baana yana murmushin jin dad’i. “Bade ya manta blessing d’inba?” (Yaren da masu shaye shaye ke amfani dashi wajen kiran ‘wiwi’). Baana yace, “Yup!” Tare da d’aga girarsa sama yana murmushi.

© miemiebee

TANA TARE DA NI… PAGE 02

BY MIEMIEBEE

Tafiya suke a sahu d’aya, tsayin nan nasu na nan d’ai da kad’an Anas ya d’ara Shettima inba wai ance ya da k’ani bane za’a zata agemates ne. Daidai lokacin da suka yanko wata corner kenan Anas yasa hannu a aljihu yaji wayam ba komai, cak ya tsaya hakan yasa Shettima tsayawa shima. “Ya maza lafiya?” “Ba lafiya ba, go ahead I’ll catch up nayi mantuwa.” cewar Anas. Shettima ya tsaya ya k’are ma d’an uwan nasa kallo sannan yace, “bade blessing d’in ba.”

      Anas ya kallesa da gira d’aya d’age sannan yace, “toh meh? Kadega yadda su Kashim suka sani tono maganan chan definately nasan ciwon kai ze kamani and despite that, yadda akayi ruwan saman nan I’m gonna enjoy sleeping.” tare da d’anyin murmushi wanda ya sake bayyano da kyansa tare da lotsar da dimple nasa dake kumatun dama. “Kona yau baraka hak’ura ba?” Shettima yasake tambaya. “Se in na amso karka sha” cewar Anas.

       Dariya kad’an Shettima yayi “zan d’an tab’a mana, naji ance da akoi dad’i cikin tea.” Anas ya dafe kafad’arsa “lets go?” Da d’aga kan da Shettima yayi suka juya suka dawo gun Kashim da Baana. Suna iso wurin nasu, Anas yace, “maza bani!” Baana yaci fuska “ban gane baka ba, mezan baka?”  “Wai me ka maidani ne? Give me!” Anas ya fad’a a little bit pissed. Dariya Kashim yayi “basa please kaga har yafara losing temper.”

     Nan Baana yasa hannu a aljihu yaciro wata leda ya raba into two saidai d’aya yafi d’aya yawa sannan ya mik’a wa Anas kad’an din. “Are you serious? Naga fa wannan abu ni nasaya da kud’ina so kabani me yawan ko in hanaka duka.” Baana yace, “haba! Anas namu na kanmu, kap qauyen nan fa kai kad’aine me blue eyes yi hakuri mana. Aikasan da inada kud’i dana siya nima.”  “Toh ni na hanaka yin noma ka samu kud’i? Abeg give me and stop wasting my time.”  “Dan Allah fa nace” Baana yafad’a pleadingly. “Okay naji talaka kawai semun had’u a masjid then.”

      Daidai sunkai ga shiga corner’n gdansu kenan wata budurwa tafito daga wani gida, sanye take da hijabi iya guiwarta, dududu barata fi shekaru 15-16 ba. Idanunta suna sauk’a kan Anas ta sakar dawata murmushi. Tsuka Anas yaja yasa qaninsa a gaba yana tunkud’esa dan suyi sauri subar gun shiko Shettima daya gano haka tuni ya rage saurin tafiyarsa dukda tunkud’in da Anas kemasa.

     Se k’arisowa wajen nasu wannan budurwa ke. “Anas kamar kayi bak’uwa ko? Wannan ba Aisha bace? Ka tsaya kaji me zatace mana.” Cewar Shettima yana murmushi. “Wallahi in bakayi shiru ba zan mareka, kuma barakayi tafiya bane?” Daya wani tunkud’a gaba Shettima besan sanda yasoma matching dasauri sauri suka bar wurin ba.

     Isarsu gidah keda wuya suka tarar da Ummee a tsakar gidah tana tsince shinkafa. Da sallama suka shiga ta amsa da fara’arta. ‘yar dattijuwa ce wacce barata fi shekaru 45 a duniya ba, tanada haske sosai amman bara’a kirata da fara ba, ga kyau daidan gwargwado masha Allah!. “Ohhh mazan nawa sun iso ne? Sekuma ruwa ya tareku a hanya ko?”  “Eh Ummee” cewar Anas yana k’arisowa wajen da take. “Me kikeyi haka?”

     “Tsince nake baba na, tuwon shinkafa Abuu keson ci gashi har ruwan ya tafasa ban gama ba.”  “Toh Amal fa mesa bata tayaki ba? Anyways kawo in tayaki Ummee.”  “Kai Baba na kaide Allah shi maka albarka” ta d’ago kai tana kallon Shettima dayayi kamar besan ma me suke fad’i ba. “Kai yanzu Shettima koda aiki ze taru ya kasheni ba ruwanka da bari ka tayani ko? Baka ganin wanka ne?”

    “Toh Ummee fisbailillahi ina aka san maza da tsintar shinkafa.” Baki wangalau ta bud’e tana kallon Shettima dududu shekarunsa sha shida ne fa da abu aka yake wannan tsiyar bayan ga wansa Anas me shekaru sha takwas bece komi ba. “Ehh hakane, sannu fa” tafad’i cike da gatsine. “Oyoyo Ya Anas” cewar wata kyakkyawar yarinyar da baratafi 8years ba fitowarta daga wata d’aki, ba shakka itace sistersu da suke kira da Amal, kyakkyawace sosai kamar sauran yayun nata bata gama kai Anas fari ba amman tafi Shettima. Su uku kap kamanninsu d’aya.

          (Bayan tafiyar mahaifiyarsu daga gdansu da wata takwas ta turo da Amal da wasiqa na cewa tabar gidan da cikin Amal ga ’yarsu nan ta haifota, kwanan ta d’aya a duniya kenan) sanadin haka Anas yake mutuwar san Amal duk rashin kunyarta bata masa saboda duk fitar da zeyi seya siyo mata abun k’walama unlike Shettima da cikinsa kawai ya sani thats the reason why basu shiri da Amal kullum cikin fad’a sukeyi duk sanda Anas yazo kuma seya bata gaskiya, wani sa’in har taran dangi suke masa.

     “Oyoyo my angel” yafad’i tare da bud’e hannunsa tazo da gudu tayi hugging nasa. “Ina sweet d’ina ya Anas?” kafin ya amsa mata ta zira hannu cikin aljuhunsa taciro ’ya’yan wiwin da Anas ya amso gun Baana sekuwa idan Ummee yakai kai. “Baba na meh wannan!?” Ta tambaya tare da zaro idanu waje. Nanfa Anas yasoma kame-kame can yace, “laaa Shettima kalli wannan abin da abokin Baanan can yace na rik’e masa” yama Shettima ido. Shettima yace, “ohh yamanta be karb’a ba kenan?”

      “Gashi anan kuwa!” Cewar Anas. “Anyways meh abun nema?” ya amshi daga hannun Amal. Ummee tace, “maza ka mayar masa wannan abu shaye shaye akeyi dashi, mayar masa maza!”  “Toh Ummee amman bansan ina gdansu ke ba, agidansu Baana muka had’u.”  “Nide koma me ka mayar masa.”  “Toh Ummee bari in muka fita Maghrib zan bawa Baana ya mayar masa.” Anas yafad’i a hankali

“Toh” tace tare da numfasa. “Ya Anas to ina sweet d’ina toh?” Cewar Amal.

      “Angel bansamu na saya miki ba, shops d’in duka a rufe I promise gobe kinji?” A hankali ta giad’a kai tare da turo baki. “Tsaya kiji wani batu” nan ya daidaita tsawonsa yakamo nata tare da rad’a mata wata magana a kunne aikuwa tahau tsalle suna ido hud’u da Shettima ta galla masa harara. “Wallahi Amal niba sa’anki bane wa kke harara? Maras kunya kawai.” Kafin Ummee ta masa magana Anas yace “ah’ah karka zagarmin k’anwa now go inside okay? Anyi ruwa kar mura ya kama ki.” Tana tsalle takoma ciki.

     Ba tare da b’ata lokaci ba Anas yataya Ummee suka gama tsince shinkafar banda Shettima daya tsaya kansu yana kallonsu cike da mamaki yarasa meke burge Anas a aikin kitchen bama aikin kitchen kad’ai ba. Bayasan ganin abinda ze tab’a Ummee ko Amal, he is so protective of them, duk abinda zeyi zeyi inhar it will keep them save and happy.

   *****

        Bayan sunfito daga masallaci iyayensu sukayi gaba a yayinda Shettima, Anas, Baana da Kashim suke tafiya a bayansu suna tattauna warsu ta maza. Wata budurwa ce ta b’ullo gabansu, dakatar dasu. “Ina wuni?” ta gaishesu duk suka amsa illah Anas dake neman any chance yabar wajen. “Anas ina wuni?” tasake fad’i cikin wata anniyar murya ganin shine be amsa ba. Shiru yamata, “Shettima ko nama Anas wani abu ne baimin magana?”

      Murmushi k’adan Shettima yayi sannan yayi k’arya “ko kad’an Hafsah mura yake saisa bai iya magana.” Wani kallo Anasa ya watsa masa wanda shi Shettima yamayar da murmushi. Kafin yace wani abu Hafsah tace, “dama zuwa nayi na tayaka murna ne kan scholarahip daka samu cewa nanda ‘yan kwanaki zaka London shine na had’o ma wannan pepper soup sekuma gashi kana mura I’m sure ze d’an wassakar maka da muran ma. Gashi please ka amshi”

        Ganin Anas baida niyan karb’a Shettima yasa hannu ya amsa “kai sannu Hafsah kamar kinsan mura na damunsa kika kawo wannan.” Shettima ka tabatta Anas yasha please ze taimaka masa sosai.”  “Aii karki damu” cewar Kashim “consider it done, zamu tabbata yasha.”

      Da murmushi a fuskarta tace, “toh nagode seda safenku.” Sanda ta sake kallon Anas sannan ta fice. Nan Anas ya finciko Shettima tare da kama masa kunne ya murd’a da iya k’arfin da Allah ya basa. “Awchhhh!” Shettima ya sakar da k’ara. Karb’e kulan abincin Anas yayi ya soma tafiya. Baana yace, “ya haka kuma? Nad’au ai baraka ci ba.” Duk suka k’yalk’yale da dariya. Bece dasu komi ba yacigaba da tafiya, “anji kunya” cewar Shettima nan ma be tankasu ba. Yana isa gida ya tarar da Ummee tana ‘yan wanke-wanke kafin ya b’oye flask d’in har ta riga ta gani.

       “Baba na me wancan kake k’ok’arin b’oyewa?” Cewar Ummee da murmushi fal a fuskarta. “Oh wannan!” Ya d’ago flask d’in sama “erm… Erm… Na-”

      “Iyye baba na manya har ‘yan matan naka sun soma kawo maka abinci ne, to yayi kyau. Me aciki?”

    Kamar ya mata k’arya sekuma ya fasa, “pepper soup ne nakawo wa Amal ko kema zaki tab’a?”  “Noo haba! Budurwa takawo wa Baba na kaji kuma se inci je kaci abinka.”  “Kai Ummee da Allah bafa budurwata bace.”  “Hehe!” tayi dariya sosai “yanzu uwar taka kake jin kunya?”  Rashin sanin me zece mata yasa ya wuce ta kawai ya kira Amal suka wuce d’akinsu ya bud’e masu suka sha pepper soup nasu. Ni miemie nace Anas ba kunya yanzu sha yake!? Lol

       Sun ci kusan rabin kazan Shettima yashigo senishi yake da alama gudu yayi ya iso nan. “Yanzu Anas cinye kazan nan zakayi da wannan maras kunyan baraka d’an bani ba nima?”  “Eh bara’a bayar ba” cewar Amal “Ya Shettiman nan shegen kwad’ayi wallahi ko Ya Anas?” Ta sake p’antarar kazar ta kai baki. “Sosai ma Angel” Anas ya amsata. “Wallahi Amal ki kiyaye ni” gwalo ta masa sanin in Anas na gefe da ita ba abinda Shettima ya isa ya mata.

          “Ka kwantar da hankalinka bari mu fita sallan Isha har gidansu Hafsah zanje in fad’a mata ka cinye kazan kap ko k’ashi baka bari ba.” Murmushi kad’an Anas yayi “to ai ko ka fad’a mata ba yadda zatayi ba saboda ban bata fuska ba.” Haka ya dake sanda suka cinye kazan tas shida Amal, pippike da wuya suka ragar sannan Anas ya ceda Amal ta mik’a ma Shettima da yawunsa ke d’iga k’asa.

      Itako ta d’aga ta ajiye mai “gashi Ya Shettima.” Hannunta ya rik’e tare da danna mata nank’washi aiko tasaki kuka harda na munafirci take Anas ya k’ariso ya rama mata.

     ***

     Haka ma da suka dawo sallan Isha Aishar d’azu ta tsaresu tare da masu sallama kap suka amsa illa Anas. Sak batun da Hafsah tayi haka Aisha ma tayi sede nata chips da omalet ne, itama na taya Anas murnan samun scholarship da yayi. Anas na jiran Shettima ya amsa kamar na d’azu aikuwa yak’i. “Dan Allah kayi hak’uri ka karb’i Anas ni badan kasoni na kawo ma ka ba, consider it as a friendship gift please.”

      D’ago blue eyes nasa yayi ya kalleta ciki ciki wanda tuni ta soma shaking tare da kawar da kanta. Ajiye flask d’in tayi a k’asa “dan Allah ka d’auka se da safenku.” Aiko tana shigewa cikin gdansu ba kunya Anas ya d’aga yakama tafiya. Baana yace “andeji kunya” haka suka ta masa tsiya amman ko a kolan rigarsa, duk yasan so suke suci kuma bayarwan ne bareyi ba. Nanma dashi da Amal ne suka cinye wannan karan ko ragowar ma ba’a baiwa Shettima ba.

    **

        Da misalin k’arfe goman dare bayan kowa ya kwanta a gdan. Anas da Shettima suna kwance kan seperate gadonsu bayan sun gama shan wiwinsu cikin tea. Shettima daya zura wa Anas kallo na kusan mintuna yace, “tunanin me kake haka?”

      “Anas?” Nanne ya dawo hankalinsa “yes! kace me?” Shettima ya kuma nanata kansa “nace tunanin me kake?”

     Murmushi sosai Anas yayi wanda yasa dimple nasa lotsewa sosai, kad’an daga cikin fararen hakwaransa suka bayyano. “My dreams are about coming true.”  “Wani dream kenan?” Shettima ya tambaya tare da tasowa ya zauna kan gadonsa tare da jingina bayansa a jikin kan gadon.

      “Don’t tell me bakasan dreams d’ina ba! Ofcourse to be a billonaire se in samu inyi breaking hearts na thousand of women by then kaga na ramawa Abuu abinda mamarku ta masa.”

    “Wai wace erin magana kakeyi Anas? Wai yanzu kana ganin in Abuu yaji wad’annan munanan kalamu daga bakinka zeji dad’i? Haba mana kai baka yafiya ne?”

      “Yafiya! Har yau bansami defination na word d’in a dictionary ba plus in wa’azi kakeson yi kaje masallaci kayi, kagannin nan? Banasan jin wannan wa’azi allow me to get some sleep yadda nasha ’ya’yan wiwin nan.” Nan yaja bargo tare da rufe kansa ciki a hankali bacci me nauyi ya daukesa.

© miemiebee

 TANA TARE DA NI…

TANA TARE DA NI… PAGE 03

BY MIEMIEBEE

FANNAH

      ‘kauyen Bama dake jihar Maiduguri, Borno.

       Kyakkyawar budurwa ce zaune cikin wata ‘yar k’aramar d’aki bisa gaban wata ‘yar madubin da aka mak’ala a jikin bango. Ba komai bane a d’akin illa katifan dake shimfid’e a k’asa seda bakunan sa kaya da leather carpet ciki. Ba shakka basu da arziki. Dududu wannan ‘yar budurwa baratafi 15 years old ba. Tanada haske sosai, da sirirn hanci dakuma plumpy lips, idanunta ba laifi ‘yan manya ne dadai. Gashin girarta acike yake mekyawun gaske ba ruwanta da zana artificial gira [ba erinsu ni ba;( ] in kuwa aka k’are mata kallo sosai za’a ga alamar had’ewar girar ta guda biyu gu d’aya sede be munanta taba hasali kyau ma yak’ara mata. Gashin idanunta a cike suke kuma dogaye, saje ne a fuskarta kwance luf-luf wane na miji (kaman nawa, lol) gashin kanta dana girarta sun had’e dan yawansu. Hannunta gashi ne a kwance dogaye masu mugun kyau.

           Siririya ce de tanada tsawo daidan shekarunta, tana sanye da wata atamfa maroon da torches na white and green, se murza wata ‘yar jan baki pink take a lips nata hankalinta kwance da anganta ansan batada matsala. A lokacin da wayarta k’irar Nokia Asha dake kan cinyarta tayi k‘ara, a hanzarce ta duba tana ganin sunan daya bayyana kai Ya Ahmad tayi murmushin jin dad’i sannan ta bud’o sakon ta karanta kamar haka;

    my Fannah I’m outside waiting for you yanzu shigowa na gari ko gida ban lek’a ba just wanted to see you

            “yeyy!!” Ta fad’a a fili tana murna. Data gama sa jan bakin ta shafa powder tareda sa kwalli a fararen idanunta take ta dawo wata balarabiya. A garin mike’wa d’an kwalinta ya since ya fad’i k’asa tare da ribbons data k’ukk’ula gashin nata dashi. Fans ko kunsan ya gashin buzayen Maiduguri yake? Erin bak’i k’irin me santsi da tsawo kamar haukan nan? Haka gashin wannan ‘yar budurwa yake.

     Ni kaina miemie dana gani sanda na tsorata dukda cewar ita kad’ai ce a d’akin hakan be hanata yin saurin tattara ribbons d’in gu d’aya da sauri ba tasoma k’ok’arin faka gashin nata gu d’aya saidai dan cikar gashin ta kasa, hannun nata suna nan sirara ba fad’i ga uwa uba gashi har tsakiyar bayanta. Kamar wacce zatayi kuka tafito d’akin “Mami! Mami!” Shiru kukeji wani mutum ne wanda bara’a kirasa da dattijo ba danko befi shekaru irin 44-45 dinnan ba ya lek’o daga wata d’aki wanda ya kasance opposite daga d’akin da Fannah tafito da alama mahaifinta ne dukda cewar basu kama kuwa. “Fannah uwata ya akayi? Tsaya mesa kike yawo da kanki a bud’e haka?”

     Kamar wacce zatayi kuka tace, “Baba ribbon d’in ne yafita kuma nakasa d’aure gashin, Mami nake nema ta tayani.”

         “Shine zakiyi kuka uwata?” Cewar mahaifin nata “Mami batanan tashiga mak’ota.”

          “To baba Ya Ahmad fa yazo yana jirana a waje ko gida be wuce ba ya zosa nan.”

      “Oh! Keda Ahmad d’inkin nan se Allah. Ina Afrah da Aiman toh?”

         “Sun tafi islamiya Baba.”

     “Yoh! Kekuma fah?”

         “Kai Baba wai yanzu so kake kace ka manta sauk’an nawa? Abinda har Hajji kaje da kujerar da aka bani danayi na biyu.”  “Haka fah, taho to in kama miki kan.”

         “ Yawwa Baba na.” Da gudu taje ta zauna gabansa shima sanda yayi dagaske sannan ya kama uban gashin nata gu d’aya. Banda tsawon gashin gu d’aya. Wawan cika ne dashi saisa Fannah batta iya kamawa. “Toh nagode Baba.”  “Yawwa ‘yar akbarka se ganin Ahmad ko?” Ta giad’a masa kai. “Ki sa hijabi fa tukun kuma kice ya gaishe min da mahaifinsa naji wai ya d’anyi rashin lafiya kwana biyu kuma ban samu na lek’a sa ba.”  “Toh Baba zan fad’a masa in shaa Allah.”

      D’akinta takoma tad’au wata maroon hijabi wanda ya sake ciro da hasken ta tasa, tare da d’aukar wayarta sannan tafito waje idanunta suna sauk’a kan Ahmad nata ta sakar dawata murmushin jin dad’i. Ahmad saurayi ne me k’imanin shekaru 23. Chocolate skinned yake, yana da kyau dadai gwargwado gasan murmushi. Tsayyayen na miji ne masha Allah!

     “Ga sarauniyata ta fito.” Ya fad’a yana mai murmushi. “Gaskiya wankan nan yayi kyau sosai Fannah, kin ganki kuwa? Looking so take away.”

           “Ya Ahmad kaide kullum seka riga zolayata. Ina wuni? Ya hanya? Gashi ko ruwa ban samu na d’auko maka ba duk na k’osa in ganka.”

          “Laaa ai sarauniyata bata laifi ae, karki damu ni ganinki kad’ai ya kashe min k’ishi.” Hannu tasa ta tare fuskarta a kunyance. “To ya Ahmad mu zauna anan mana kar ka kaji a tsaye.” ta nuna wat benchi.

        “Haka sarauniyar tawa tace? “Haka to za’ayi.” Bayan sun zauna Fannah tace, “ya hanya toh? Ya makarantar?” Hannu yasa ya dafe goshi sannan yace, “so hectic fa Queen, biochemistry akoi wahala. Ga Maiduguri zafi like hell”

       “In shaa Allah ka kusa gamawa, Allah baka sa’a yaya na.”  “Ameen sarauniyata.” Kefa ya school ‘yan matan ss2 koh?”

          “Kai yaya! School alhamdulillah” Ta fad’a tana murmushi. Hira suka d’an tab’a na ‘yan mintuna. Shi Ahmad ba abinda yake sake jan ransa kan Fannah kamar san addininta dakuma yawan yarintar ta dakuma sa sa dariya da takeyi in suna tare. Fannah batta magana d’aya biyu seta sa alhamdulillah, subhanallah, masha Allah ko jazakallahu bikhair ciki. Yarinyace me tarbiyan gaske, ga hankali da girmama na gaba da ita koda wasa bata tab’a kiransa da sunansa gatsau ba dole seta sa yayan nan kuma bawai they are related bane tsantsan girmamawa ne kawai.

     “Toh yaya na kar na ta jan ka da surutu nasan su Mama duk suna jiran ganinka, kaje gida ka huta.”

            “Toh sarauniyata” hannu yasa cikin jakarsa yaciro wata leather sannan ya mik’a mata.

       “Me wannan kuma yaya na?” ta tambaya suprisingly.

        “ ‘yar tsarabar Maiduguri ne nace barin kawo wa sarauniyata, yi hak’uri ba wani abu me tsada bane.”

         “Yanzu yaya karatu kakeyi amman seka rik’a kashe kud’inka a kaina? Ni gaskia kadena banso nafison kana kula da kanka a school.”

       “Ko kad’an Fannah baran iya zuwa nan ba tare da na kawo miki komi ba. I prmise you this duk sanda na fara earning salary’n kaina I will spend it on you, ina sonki sosai Fannah ta.”

             “Nima ina sonka yaya na. Nagode sosai, jazakalllahu bikhair Allah taimaka ya baka sa’a yaya.” nan ta mik’e.

     Mik’ewan yayi shima “ameen my Fannah inasan addu’o’in ki agareni, ba k’aramin taimaka min suke ba.”

         Ai saisa kullum nake including d’inka cikin prayers d’ina. Baba na naka sannu dazuwa also, yace ka mim’a gaisuwan sa gun Abba da jiki”

          Toh my Fannah, I’ll tell him so se munyi waya ko?” kai ta giad’a a hankali. Wai! Ai na manta kun kusa fara exams ma, barinso jn hana Queen d’ina karatu ba”

        “Haba mana yaya ko wayan minti ishirin baramuyi ba?”

     Da murmushi a fuskarsa yace ai baki tab’a neman abu kirasa guna. Allah kaimu daren toh”

     “Yawwa yaya bo-bye” tamasa murmushi. Murmushin ya mayar mata “bo-bye Queen.” Ahaka tashigo ciki.

      Tun kafin ta yo d’aki ta soma bud’o ledar, abaya ce me kyan gaske ga stones kota ina. “Wowww!” kukeji tana fad’i kamar Ya Ahmad yasan yadda nakeson abayah. Nan ta hau gwada wa kan kayarta bayan ta cire hijabin nata. Aiko daidanta tazo gwada yafa gyalen se kud’i ya fad’i daga ciki tana irgawa taga dubu biyar. “Yanzu Ya Ahmad wannan d’inne zece ba yawa. Baba! Baba!” Ta k’olla masa kira tana nufo d’akin nasa.

     “Ya akayi uwata ta kaina?” Ya tambayeta a kishingid’e tare da kashe radio’n dayake ji. “Wannan kaya fa daga ina?”

       “Masha Allah Ya Ahmad ne yakawo min yanzu kaga harda dubu biyar kuma.”

        “Kai Allah shi mashi albarka, shi kullum cikin wahala yake miki? Gashi ko kayan yamiki kyau kika fito kamar balarabiya.”

      “Kai! Baba dagaske?” Ta tambaya tana tsalle. “Sosai ma kuwa uwata.” ya amsata. Nan ta irga dubu biyu ta mik’a masa “gashi Baba ka rik’e wannan, Mama ma dubu biyu nida Afrah da Aiman kuma semu raba wannan.”

       “A’a uwata rik’e abinki kinji? Ki saya abubuwan da bakida dashi” ya mik’a mata.

        “Baba ni komai danake buk’ata inadashi ka karb’a kaji? Ko cafani sekayi dashi.”

     “Toh nagode uwata, Allah miki albarka ya cigaba da kare min ke.” “Ameen Baba zan koma d’aki.” Nan ta fice, isarta d’aki bada jimawa ba k’annenta Afrah da Aiman suka dawo.

     Atare suka shigo d’akin d’ayan tana nan kamar Fannah baratafi 13 years old ba whereas d’ayan kuma dududu intayi shekaru shine 3. “Ke wai Aiman kullum ne sekin tsaida mu akan hanya da sunan fitsari?” cewar ‘yar babban (Afrah) kenan. “Anyin!” cewar Aiman yarinya ‘yar shekara uku se uban baki.

    “Ni kike ma rashin kunya? Iyye?”

       Fannah dake kwance kan katifa tana karatun History ta d’ago ta zauna “wai ke Afrah me damuwarki? Shikenan yarinya bara  tayi fitsari ba?”

        “Ya Fannah ni ban tsoma bakinki ba, nida Aiman nake magana.”

     “Aww rashin kunya zakimin? Dama d’azu Ya Ahmad yazo ya bani kud’i nayi niyan baki kad’an daga ciki amman tunda rashin kunya zakimin na fas-”

      Afrah ta katse ta, “a’a yi hak’uri Ya Fannah ta.” Da gudu ta haura kan katifar “yaushe Ya Ahmad d’in yadawo?”

      “D’azu bakiga abayan daya kawo min ba!” Nan ta mik’a hannu taciro daga cikin wata bako take Afrah data kusan kamota tsayi ta amshi zata soma gwadawa Fannah ta k’wace “kefa bakida seti, akawo min kaya kiwani ce zaki gwada?”

        “Su Ya Fannah manya masu samari.”

          “Samari? Ai Ya Ahmad ba saurayi na bane miji na ne, kinga yana level 5 yanzu ina ss2 ina ss3 yana neman aiki ina gamawa se muyi aure by then yasamu aiki in shaa Allah”

     “Ahh lallai fa soyayya ruwan zuma. I’m envious.” Cewar Afrah.

      “Don’t be, kema lokaci ne beyi ba Allah ze had’aki da mijin dayafi Ya Ahmad sona.”  “Allah sa!” Afrah tafad’a da sauri “Ameen habibti” cewar Fannah.

       ****

     “Fannah! Fannah! Zo da sauri da Allah” kirar Mami. “Na’am Mami gani zuwa.” Sunnah take da niyar yi kafin tayi nafilar Maghrib kasancewar lokaci ya kusa yi amman dan kirar Maminta ta fasa tajeta. “Gani Mami”

        “Fannah yi hak’uri ki siyo min maggi ashago nan kusa wallahi bansan ya akayi ba har ya k’are ban sani ba yi hak’uri kinji mamana?”

      “Yanzu Mami aike zakiyi shine sekin had’ani da Allah harda bani hak’uri. Ina kud’in?”

       Nan Mami taciro hamsin ta mik’a mata. “Kinga ai kece babba Afrah yakamata in aika amman shegen yawonta tashiga nan mak’ota ganin jaririyar da Ameenatu ta haifa.”

       “Ayya ba komai Mami barin yi sauri kafin su rufe shagon.”

      “Toh Allah kare.”  “Ameen” ta amsa sannan ta fice.

ANAS

    “So Anas sauran ka 3 days kafire London kenan?” Cewar Shettima suna zaune a kan wata benchi a bak’in k’ofar gidansu. “Gonna miss me?” Anas yafad’a yana d’aga gira.

      “Eh mana I will miss you, nide Anas wallahi ka canza tsoron zuwanka London d’innan nake nan da Bama ma kana shaye shayenka a b’oye bale ace kaje can inda ba idan kowa.”

      “Toh yau kuma wa’azi zaka min? Kagannin nan yanzu haka akoi inda mukayi appointment da su Baana I will have my last drink a Bama yau kasan gobe zamu wuce Maiduguri, so kaga dole in sha in bugu tunda na k’arshe ne.”

     “Amman kasan Abuu nagari ko? In ya ganka a buge fah?”

      “Make up stories for me then, kamar yadda ka saba kace masa fad’a mukayi da wani. I’m going now.”

     “Toh masallaci fah?” Cewar Shettima.

      “Sena dawo zanyi sallar.” Daga nan ya fice inda suka saba had’uwa in zasuyi shaye shayensu ya je chan suka bugu like never, ko sanin ina suke in aka tambayesu ba sani zasuyi ba.

         Daidai Anas ya tashi ze tafi gida kenan aka soma wani erin masifaffen ruwa ba yadda Baana basuyi dashi yajira ruwan yad’an tsaya kafinnan ma hankalinsa yad’an dawo jikinsa ba amman sam yak’i jinsu ana ruwan yasoma tafiya, yazo ma besan ina yake dosa ba dan yadda ya bugu.

    **

FANNAH

     “Oh No! Shagon Ya Wakil a rufe gashi Mami battada maggin da zata yi amfani dashi dole in k’ara gaba” haka tatayin gaba duk shagunan a rufe amman still bata hak’ura ba. Bada jimawa ba aka soma ruwa me k’arfin bala’i gashi daga can tana hango wata shago a bud’e ta koma gida ba maggin kuma battaso. Cikin ruwan ta cigaba da tafiya daidai ta shiga wata lungu taga wani na miji daga gani a buge yake, duda acikin duhu ne hakan be hanata tantance kyansa da blue eyes nasa daya d’ago yana  kallonta ba. Take ta soma b’ari Allah sa ba gamo tayi ba. Mutum da blue eyes.

      Addu’o’in kariya tasoma yi jikinta se rawa yake gu d’aya ta tsaya jiran yazo ya wuce tayi gaba itama. Daidai yazo kusa da ita seya tsaya hannu ya d’aga yakai kan fuskarta tuni Fannah ta soma kuka tunda take ba d’a na mijin daya tab’a tab’ata inba Babanta ba. Ga k’arfin ruwan saman koda tayi ihu bame jinta shagon data gani a bud’en ma har sun rufe.

©miemiebee

 TANA TARE DA NI…

TANA TARE DA NI… PAGE 04

BY MIEMIEBEE

Cikin kuka tace, “dan girman Allah bawan Allah kayi hak’uri I beg of you please.” Jikinta se rawa yake tana hawaye. “Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri I’m just 15 ba abinda zan iya baka have mercy on me please dan Allah.” Ko k’adan be saurareta ba hijabin jikinta yasoma k’ok’arin cirewa. “Wayyo Allah Mami na! Baba! dan Allah kuzo ku taimakeni! ihu take sosai.”

     Hannu yasa ya rufe bakinta. “Duk mata haka kuke, mesa zanji tausayinki? Data gudu tabarmu ta tausaya mana neh? Why will I have mercy on you? I hope you tell her abinda zan miki yanzu saboda itama ta d’and’ana little daga cikin bak’in cikin data sanyamu time da ta tafi ta barmu” Yana d’aga hannu daga bakin nata ya yaga hijabin nata into two. Ihu ta sake sakarwa “bawan Allah dan Allah kayi hak’uri karka lalatani dan girman Allah, kaji tausayi na I’m just 15 years dan Allah ka rufa min asiri karka b’ata min future”

     “Data tafi ita taji tausayin mu ne?”

       A rikice bakin ta na rawa tace, “ww..wa ce? Ni bansan wacce kake fad’a ba bawan Allah ban tab’a ganinka ba seyau kayi hak’uri dan Allah, karka lalata ni.” Be saurareta ba ya yaga kayanta. Nan ta shiga tare k’irjinta kuka sosai Fannah takeyi tana rok’an wannan bawan Allah’n haka ba tausayi ba inani yayi raping (fyad’e) nata.

     Tun tana iya jure zafin har ta sume wajen, kaca-kaca yayi da ita sannan ya fice yabarta ruwan sama ma dukan sumemmiyar jikinta. Shi kansa besan ya akayi ya isa gida ba a daren, kawai ganin kansa yayi bisa kan gado.

 

             A hankali ya bud’e blue eyes nasa wansa Shettima yagani a kansa. Tunanin meya faru yakuma yake nan ya soma lokacin da aka soma ruwa yace dasu Baana ze tafi sukayi k’ok’arin hanasa amman ya k’i jinsu ya hau tafiya can cikin wata lungu.. Wata lungu… Daga.. Can kwata kwata seya kasa tuna meya sake faruwa.

         “Anas how are you feeling? Sanda na fad’a maka karka bi su Baana kak’i kasan yadda ruwan saman nan yamaka duka kuwa? In akayi wasa seka kamu da mura.” cewar Shettima fuskarsa a d’aure

     “Ina Abuu?” Anas ya tambaya. “Ka gode wa Allah be ganka ba sanda nashigo dakai nan. Anas fisabilillahi mesa baraka rungumi k’addara ka manta da zancen Ummimi (mahaifiyarsu) a rayauwarka ka yafe mata ba? You’re blaming yourself for her mistakes, misleading your life in the process. Haba mana Anas. Saboda Ummimi kasoma shaye shaye me haka please? Yanzu saboda ita ka kusan kashe kanka, abinda tayi ya riga ya wuce se mu rungumi k’addara mu barta da halin ta.”

        “No Shettima I can never do that, tariga ta juya min rayuwa, my life can never be normal kamar yadda kakeso, I can never move on barni haka kawai inta misleading rayuwar nawa har zuwa sanda zan mutu. Images of yadda ta tafi ta barmu will never leave my head, they are stuck in it forver”

       “Anas wai kai mesa bakajin magana ne ko dan ni k’aninka ne kafisan babba ya maka magana? Bari Abuu ya dawo I think is about time yasan gaskia shima, I’ve been keeping your secret for how many years now? A ganina with time zaka mance komai amman tunda you are not ready to change, tunda baka iya rungumar k’addara ba zan fad’a wa Abuu komi idan ya dawo.”

             Sede daya juyo ya kalli Anas yaga ko k’adan ma hankalin sa ba a gunsa yake ba, yayi nisa cikin duniyar tunani.

     “Anas?” Ya kira sunansa. Shiru Anas yayi be amsa ba dan haka ya d’an jijjik’a sa. “Yarinyar…” Anas yace fuskarsa cike da damuwa. Se yanzu ya tuna yaga wata yarinya acikin lungun. Amma sam ya kasa tuna ya fuskarta take ko fara ce ko bak’a ko kyakkyawa ko munana, ko doguwa ko gajeriya shide yasan yaga yarinya cikin lungun.

         “Wata yarinya kuma Anas? Yau kai ke kirar mace cikin gidan nan?”

     “Yarinyar Shettima ina take?”

    “Wai wace yarinya Anas, me kake fad’i?” Shettima ya fad’i fuskarsa cike da mamaki

           “Yarinyar Shettima, ina take? Ina ka tsince ni?” Cewar Anas.

             “Can gaba da gidan gona and also meya sami kayanka duk jini na duba ka banga ciwo ba.”

     “Jini fa kace? Ina kayan nawa?” Anas ya fad’a a rikice.

    “Na wanke already.”

     “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.” Abinda Anas keta nanatawa kenan duk yasa Shettima kid’imewa.

    “Wai meke faruwa ne Anas? Wani abu ne?”  “A’a nothing thanks please in baraka damu ba I want to be alone in d’an huta thanks.” Shettima na fita Anas ya rufe ido so yake ya tuna fuskar wannan yarinya amman ya kasa, “ina take? Mena mata? Mesa Shettima yace yaga jini ajikin kayana. Oh no! Nayi blaming yarinyar da batasan komi ba akan laifin da Ummimi tayi. Oh no! Nayi raping d’inta subhanallah shikenan nazama mazinaci, Ummimi baran tab’a yafe miki ba abinda kika min, kin cuceni” Dakyar bacci yayi gaba dashi…

**

FANNAH

       “Malam wallahi aiken maggi nan shagon bakin titi nace taje mun kuma har yanzu bata dawo ba, wayyo Allah inaji a jikina abu yasamu Fannah tah.”

      “Maman Aiman ki kwantar da hankalinki Fanmah yarinya ce me hankali tasan abinda takeyi barata tab’ayin abinda zesa mu cikin damuwa ba.”

     “Abin da nake nufi kenan Malam” Mami ta fad’a cike da tashin hankali.

          “Fannah bara ta tab’a yin abinda ze samu cikin damuwa ba saidai in za’a tilasta mata.”

    “Me kike nufi kenan Maman Aiman?”

         “Malam wallahi ji nake a jikina Fannah ba lafiya ba wayyo Allah tun kafin Maghrib fa na aiketa yanzu har Isha bata dawo ba, Allah ba lafiya ba nashiga uku!”

    “Maman Aiman ki kwantar da hankalinki yanzu d’auko hijabinki ga lema anan muje mu duba nan mak’ota ko halan tashiga tana jiran ruwan saman ya d’an saurara.” Nan ta d’auko hijabi sunzo fita kenan Aiman ta fito daga d’aki “Mami ina zakuje?”

         Idan Mami cike da hawaye tace, “nemo Ya Fannah zamuyi Aiman, bata dawo gida ba tun d’azu” daidai lokacin Afrah ma tafito “zan biku Mami.” tace idanta cike da hawaye tunda take bata tab’a shiga tashin hankali kamar na yau. Fannah ba mutumiyar yawo bace, ba inda take zuwa banda boko tunda ta kammala haddan Al~Qur’aninta. Dole ne wani abu yasameta a hanya, fatansu Allah sa ba sharri bane.

       “A’a Afrah ki zauna da Aiman a gida in shaa Allah yanzu zamu dawo.”

      “Mami what if something bad ya samu Ya Fannah fa? Please kibarni inje” tafad’a hawaye na tsiyaya a idanunta cike da tausayi da tsoro.

       “In shaa Allah ba abinda ze sameta” cewar Baba “ku zauna yanzu zamu dawo.”  “Toh Allah kare” Afrah tace. “Ameen” Mami da Baba suka amsa a tare sannan suka fice cikin ruwan sama. Aiman ce ta rik’o hannun Afrah, “Ya Afrah me ze samu Ya Fannah?”

        Murmushin dole ta k’irk’iro “in shaa Allah ba komai karki damu kinji? Ya Fannah will be alright.”

          *

         “Malam suka ce Fannah bata shigo nan ba innalillahi malam dan Allah ina zataje? Ina aka kaimin ‘yata?!”

          “Maman Aiman panicking is never a solution kizo mu dudduba kusa ko zamu ganta cikin shagu nan bakin titi” Haka fa iyayen Fannah suka ta duba sak’o sak’on unguwar tasu ba Fannah ba alamarta har sun fidda rai se Mami ta tuna shagon dake gaba da wata lungu a sabuwar unguwa tace suje su duba, sunayin wajen kuwa sega Fannah kwance a k’asa half naked ruwan sama yamata tsinannen duka ko numfashi battayi.

          “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!” kawai ke tashi gun both Baba da Mami were shocked hawaye gangara suke daga kumatunsu suna kallon yadda aka walak’antar masu ‘yarsu. Mutuwan tsaye Mami tayi Baba ne yayi k’arfin hali yaja zanin ta dake gefenta ya rufe mata jikinta dashi tare da rungumota yana kiran sunanta sam bata amsa ba dake ko numfashi battayi. Alokacin Mami ta sakar dawata erin k’ara    

              “FANNAAAHHHHH!!! WAYYO ALLAH!” Da gudu tayo kansu tare da jefar da leman ta karb’e Fannah tareda rungumota tana kiran sunanta “FANNAH! FANNAH! Dan Allah karki tafi kibarmu dan Allah kitashi wayyo Allah!” Kuka kenan!

         Mota Baba yasamu da k’yar aka sa Fannah ciki suka wuce babban asibitin dake hukumar Bama. Nan take akayi emergency da ita sam Mami ta kasa daina kuka shikansa Abba kuka yakeyi duk yadda yayi ya hana kan sa kuka ya kasa. Hannun Mami ya rik’e yana bata hak’uri tana kuka tace, “mesa Malam? Mesa se Fannah ta za’ai wa haka? Hankalinta yayi yawa ace an mata wannan tsiya. Malam shikenan an rusa wa ‘yata future Allah ya isa ma duk wanda ya mata wannan d’anyen aiki barin tab’a yafe wa ba…” ta fashe cikin wata erin matsanancin kuka.

       Rungumota Baba yayi yana bata hak’uri shima yana kukan. “Nima kaina abinda ke d’aure min kai kenan, wani azzalimi ne kawai yayi taking advantage na innocence nata saboda Fannah bawai tana mu’amala bane da maza bale ace saurayi ne yamata wannan abu, Ahmad ne kawai ke zuwa wajenta kuma nasan Ahmad bare tab’a aikata mumunar abu kamar haka ba.”

**

3 hours later

   K’ofar d’akin da Fannah ke ciki ya bud’u likita ya bayyana daga bayansa. Da sauri su Mami suka taresa. “Ya ‘yar tamu likita ya jikin nata?” cewar Mami da Baba a tare. Kai ya k’ada a hankali fuskarsa cike da tausayi. “Likita dan Allah karka fad’a min ta rasu, dan girman Allah” Mami ta fashe da kuka Baba yana bata hak’uri.

      “Iyayen Fannah kuyi hak’uri amman munyi duk iya abinda zamu iya dan ceto ran ‘yarku, mun kasa, ya gagare mu, mun kasa at all ruwan saman ya mata duka sosai har na fitan hankali, yabi ta kunnenta da hanci har baki, bayan haka kuma ga raping nata da akayi wanda aka mugun ji mata ciwo. Zafin datayi witnessing yafi k’arfin jikinta yafi k’arfin shekarunta. Yarinya ce sosai. Kuyi hak’uri dan Allah amman kar kuyi losing hope anyi waya dawani likita daga Maiduguri Teaching Hospital gobe da sassafe ze iso ya dubata inhar da abinda ze iya toh se mu godewa Allah.”

        Mami dake kuka kamar zata cire ranta tayi k’arfin halin fad’in “likita me kake nufi kenan? har yanzu ban fahimce ka ba ‘yar tawan tana raye ne kokuwa ta mutu?”

 

           “Maman Fannah ni kaina banda amsar wannan tambaya zuciyarta na bugawa yana aiki amman kuma bata numfashi, mun samata oxygen munyi komi still ba progress, kwata kwata bata responding to stimuli.”

              “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un. Malam sun kashe min ‘ya shikenan Fannah ta tafi ta barni, ta barmu Malam” takuma fashewa da wata masifaffiyar kuka Baba na bata hak’uri, shikansa hawaye yake zubdawa shar shar.

   “Baban Fannah ‘yarku bata gama mutuwa ba tunda tana numfashi, duk me numfashi aikuwa nada rai kenan.  Addu’a kawai zaku sata ciki sosai, Allah sa tayi making it through the night in shaa Allah in gobe likitan yazo seya duba ta. Allah bata lafiya ya k’ara maku hak’uri. Excuse me please.” Nan ya fice. Har k’asa Mami ta sauk’a tana kuka.

     In ta rasa Fannah ta rasa komai a duniya cikin yaranta uku ba wacce takai Fannah hankali, ‘yar da zaka aiketa sau d’ari a rana barata b’ata rai ba bara kuma tayi fushi ba. ‘yar da kana ce mata bari ta bari kace yi kuma tayi. ‘yar da is ready to sacrfice the last kobo she have just to make her parents happy. Barata iya rayuwa ba Fannah ba. If only zata iya bada ranta asawa Fannah da tayi.

      Kuka take sosai, abin tausayi, tanayi Baba nayi tabbas shima kap cikin ‘ya‘yan sa babu kamar Fannah. Kalmar son kai ko k’adan Fannah bata sani ba, she can give up her own happiness for others…

©miemiebee

 TANA TARE DA NI…

TANA TARE DA NI… PAGE 05

BY MIEMIEBEE

       “Malam baran iya shiga ganin Fannah ba, if only zan iya bata raina wallahi zanyi.”

           “Addu’a zamu mata Maman Aiman kinsan dole ke zaki kwana da ita.”

     “Yanzu Malam kud’in asibitin fa? Taya zamu biya? Wallahi duk d’an iskan da yama Fannah wannan abu be kyauta ba.” Ta kuma fashewa da kuka hak’uri Baba ke ta bata. “Karki damu da wannan, zan sayar da shanu na in shaa Allah zamu biya bills nata dashi, fatan mu Allah bata lafiya”

               “Shikenan yanzu dama shanun nan kad’ai muka mallaka, Allah ya isa wallahi.” A sanyaye suka mik’e zuwa d’akin Fannah, Baba na bud’e k’ofa suka hango Fannah kwance kan gado ba alaman nishi a tattare da ita.

        Da gudu Mami tayi kanta ta tsuguna tare da rik’o hannunta se kuka take zubawa. “Maman Aiman addu’a zamu mata kuka baida amfani barin koma gida in d’ibo muku abubuwan da zaku buk’ata, kiyi hak’uri” ahaka ya fice isarsa keda wuya ya tarar da Afrah se safa da marwah take a parlour tana ganinsa tayo kansa. “Baba ya kun sami Ya Fannah?” Kallon daya mata yasa jikinta yayi sanyi take idanunta suka cike da hawaye “Baba dan Allah meya sami Ya Fannah?” ta tambaya tana kuka.

           “Afrah da rungumar k’addara aka san musulmi, mun samu Fannah amman yanzu haka tana asibiti.”

          “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un Baba me kake nufi? Meya samu Ya Fannah?”

          “Bata da lafiya Afrah, mun… Mun…” Sekuma yayi shiru hawaye na cika a idanunsa sakamakon hakan ya sake tada ma Afrah hankali. Tana kuka tace, “Baba dan Allah ka fad’a min meya samu Ya Afrah.” Zaunar da ita yayi ya bata labarin komai kuka Afrah keyi sosai kamar zata cire ranta sam tace seta bisa asibitin taga yarta.

        Ba yadda Baba beyi ba dan hanata amman ta dage setaje. Aiman kuwa ta jima da bacci, bayan sun gama had’a abubuwan da zasu buk’ata Baba ya rakata ya tsara mata abin hawa sanda suka b’ace ya dawo ciki. Tafiyar minti 15 ya isar da Afrah asibitin, bayan ta biya sa kud’insa tashigo ciki direct d’akin Fannah ta wuce.

      Tana bud’o k’ofar taga Mami tsugune gefen Fannah se kuka takeyi take itama wani kukan ya faso mata da gudu taje ta rungumi Mamninsu suna kuka sosai. Sunjima suna abu d’aya sannan Mami ta tambayeta “Afrah me kkeyi anan ina Babanku?”

       “Mami yana gida na zo ne in tayaki kwana.”

       “Afrah bekamata kiga yarki a wannan yanayi ba da kin koma gida.”

      “Haba Mami! Ya Fannah fa yayata ce taya zakice haka?” Nan ta jiyo tana kallon Fannah wacce take kamar gawa. Wani sabon kukan tasoma ta rungumeta, tana kuka “Ya Fannah dan Allah karki mutu ki barmu, Allah ze sak’a miki in shaa Allah.” Da kyar Mami ta lalasheta tayi shiru.

       Mami ko kayan tean da Afrah ta had’o musu susha tea ma takasa sha hankalinta duk yabi ya tashi. Afrah bata tab’a ganin Maminsu cikin tashin hankali irin wannan ba.

     Kwana Mami tayi tana nafilfilu tana rok’an Allah haka itama Afrah bawanda yayi bacci cikinsu.

     ****

     Washegary da safe misalin k’arfe 8:00AM babban likita daga TH na Maiduguri ya iso. Aikin kusan awa uku akayi kan Fannah sannan likitan yafito. Baba, Mami, Afrah da Aiman dake rik’e a hannun Afrah duk sukayi kansa “likita ya jikin ‘yar tawa?” Cewar Mami jikinta se b’ari yake.

       “Ku kwantar da hankalinku in shaa Allah ‘yarku zata samu sauk’i tana cikin state of coma ne yanzu within 5-7 days in shaa Allah zata farfad’o.”

     “Alhamdulillah!” kukeji a wajen. “Likita amman har kwana biyar? Kana nufin barata san inda take ba har nan da tsawon kwana biyar ko bakwai?”

     “Eh Hajiya, she’ve been through alot, raping at this tender age ba k’aramin abu bane, tamugun jin jiki, gakuma ruwan daya mata duka again yasa ta kamu da pneaumonia but in shaa Allah inta farfad’o everything will be alright za’a bata magani karku damu.”

     “Toh likita mungode sosai Allah biya.”

       “Ba komai” ya fad’i sannan ya fice.

       A hankali Umma ta soma kuka “Malam yanzu har kwana biyar ko sati ‘yata zatayi batasan inda take ba? Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.”

      “Maman Aiman godiya yakamata muyi tunda Allah yabar mana ita be karb’i abinsa ba, mu cigaba da addu’a in shaa Allah zata samu sauk’i.”

   

       *ANAS*

    _Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri kar ka lalata min future, wallahi baran iya baka abinda kake nema ba I’m just 15 dan Allah karka lalata ni kayi hak’uri ka rufa min asiri_

    Firgit Anas ya farka daga bacci yana numfashi da k’arfi sosai wanda hakan yasa Shettima tashi shima daga bacci tun jiya yaga yanayin wansa ya canza koda ya tambayesa meh kuwa ce masa yake ba komai, wannan karan ne na farko da Anas ya soma b’oye masa abu. Gadonsa ya bari yaje yasamu Anas tare da dafe kafad’arsa. “Anas lafiya? Ka jima fa bakai mafarkin Ummimi ba, meya faru kuma yau?”

    “Ba mafarkin Ummimi nayi ba.” cewar Anas yana raba ido.

      “Mafarkin me kayi toh?”

      “I don’t want to talk about it karka damu its okay.” Anas yayi k’ok’arin calming kansa.

      “Its not okay Anas, tun jiya nake lura da kai, something is bothering you and you’re keeping it to yourself. Tell me.”

      “Nace maka ba komai” Anas yayi insisting. A hankali ya mik’e ya wuce bayi. Tun shigarsa bayin ba abinda yakeyi se tunanin mafarkin dayayi akan yarinyar jiya, ko kad’an besamu yaga fuskarta ba a mafarkin. Ruwa ya riga watsa wa a kansa sannan yayi wanka yafito ya shirya kayakinsa da komai dake yau ze tafi Maiduguri, gobe ya wuce Abuja daga can kuma se London.

      Yana fitowa daga d’akin nasu ya rufo k’ofar yana juyawa sega Amal idanunta sunyi ja “my Angel waya tab’aki?”

      “Ya Anas wai yau zaka tafi baraka sake dawowa ba se nan da 5 years?”

      “Waya fad’a miki haka?” Ya fad’a yana wasa da gashin kanta.

     “Ya Shettima ne kuma wai kana barin gidan nan ze dakeni wai dama tarani yake, Ya Anas dan Allah kar ka tafi” ta rungumesa da tsayinta daidai kunkuminsa. Sama ya d’agata “stop crying kinji Angel? very soon zan dawo kuma duk sanda Shettima ya tab’aki ki d’au wayan Ummie ki kirani I promise in na dawo zamu rufesa a d’aki mumasa dukan tsiya.”

     “Dagaske Ya Anas? Zamu masa duka?”

     “Sosai ma bulala zan baki ki zanesa se yayi kuka.”

   “Yeyyy!” Hugging nasa tayi “I love you Ya Anas.”  “I love you too Angel. Sauk’o to muje wajen Abuu.”

     “O’o ni muje a haka ka d’aukeni for the last time.”  “Okay Angel” ya manna mata kiss a goshi sannan yaja akwatinsa suka fice. Suna isa parlour ya sauk’eta tare da gaishe da Abuu sannan Ummie.

     Breakfast suka ci bayan sungama Abuu ya zaunar da Anas.

       “Anas kaga karatu zakajeyi ba hutu ba kuma kafi kowa sanin wahalar da mukayi kafin muka samo maka wannan scholarship I’ll be very angry inhar baka je kacika mana burinka na zama architecture ba.”

     “In shaa Allah Abuu” cewar Anas dake kallon kan carpet.

       “Kasani kuma duk abinda kakeyi Allah na kallonka, kowa yasan ya rayuwar London yake, inbanda iskanci ba abinda sukeyi, ba ruwanka da zuwa beach bale kaje kaga abinda ze hana ka d’aukan karatu. Qur’ani shine guidance naka, karka kuskura kabari rana ya wuce ka baka d’au Qur’ani ka karanta ba. Ba ruwanka da ‘yan mata ko friends na banza. Ba ruwanka da shaye-shaye Anas. Kajini ko bakaji ba?” ya gargad’i Anas tare da rik’e kunnensa.

    “Naji Abuu na gode in shaa Allah zan kiyaye duk wannan abubuwan daka lisafo, nagode.”

    “Toh Baba na nikam nasan ko ban ja maka kunne ba kasan what is right and wrong, ban tab’a doubting tarbiyarka ba. Allah baka sa’a ya kareka daga kowani irin sharri Baba na.” Cewar Ummie.

    “Ameen Ummie nagode.”

**

         “Amal kukan me ne kuma haka sekace mutuwa yayan naki zeyi? Makaranta fa zasa in shaa Allah ze dawo.” Cewar Ummie tana lalashin Amal dake ta kuka.

      “Bar shakwab’a de Ummie ke kike biye mata ma ai, tayi kukan jini tagadama ta mutu.” Shettima ya fad’i yana ma Amal dariyan mugunta. Harara ta watsa masa me rai da lafiya “toh nak’i kukan” tasa hannu ta share hawayerta “kaine zaka mutu mugu kawai.”

      “Ke! Rashin kunya kike min?” Ya mik’a hannu ze finciko ta daga jikin Ummie, hannu Ummie tasa ta make hannun nasa da k’arfi “okay dan Amas yatafi zaka soma cin zalin Amal ko? Toh kasani Anas yace duk sanda ka tab’a ta in kira sa a waya in fad’a masa dan haka ka mayar da hankalinka. Kai kullum kata biye wa ‘yar yarinya duk kabi kasa ta raina ka.”

      Gwalo Amal tamasa harda sa hannu kan kunnenta. “Ni shikenan Ummie kullum ma wannan maras kunyan zaku na ba wa gaskiya wallahi kicigaba Allah kawo rananda za’a barni dake gidan nan.” ya cize yatsa.

     “Karki kula sa Amal taho muje mu siya miki sweet ga kud’i nan dayawa Anas ya ajiye miki.” Juyawa tayi tasake ma Shettima gwalo sannan suka fice da Ummie.

***

Da misalin k’arfe 1:00pm Ummie ta kira wayar Anas ringing kad’an yayi ya d’aga “hello Ummie” yafad’a cikin muryarsa me dad’in gaske.

   “Baba na ya gajiyan hanya?”

      “Alhamdulillah Ummie tun d’azu muka iso ai, ina gidan chairman ahaka.”

       “Toh yayi kyau, Babana kaji abinda Abuu ya fad’a maka ai? Nasan kanada hankali kuma kasan abinda ya kamata kar kayi abinda ze haddisa mana matsala kaji ko Babana?”

     “In shaa Allah Ummie karki damu, ina Angel d’ina?”   “Tana parlour tana kallo barin kai mata.” Nan ta mik’e takai wa Amal “ga Ya Anas nasan yanason ku gaisa.”

     “Ya Anas ina wuni?”

   “My angel ya kike?”

     “Lafiya, har kun isa London d’inne?”

    Murmushi kad’an yayi wanda hakan yasake bayyano da kyansa. “A’a Angel da saura sosai ina Maiduguri ne yanzu se gobe zamu wuce London.”

     “Okay! Nagane. Ya Anas kaga d’azu Ya Shettima ya nank’washeni akai dan yaga baka nan.”

       “Shettiman? Bari ki riga irgamin duk mugunta daya miki ina dawowa zamu masa duka.”

    “Yeyy! Ya Anas I love you ina kallon frozen se anjima.”

      “Yawwa Angel d’ina bo-bye.”

  FANNAH

    6 days later…

       “Mami kukan ya isa mana dan Allah, ki dubi yadda kika rame dan Allah.” Cewar Afrah dake rik’e da Mami itama tana hawaye.

      “Afrah kiyi hak’uri ba san ra’ayi na bane nima, yau kwanan ‘yar uwarki shida bata san inda take ba taya baranyi kuka ba. Gani nake kamar zata tafi tabarmu. Allah ya isa, haka kawai Fannah bata masa komai ba ya zab’i ya wulak’an ta ta. Allah ze sak’a mata.”

       “Shhh Mami dan Allah karkiyi magana haka, in shaa Allah Ya Fannah zata farfad’o lets not lose hope Mami.”

*

     Da azahar misalin k’arfe 1:30PM wani dattijo yashigo cikin asibitin, kallo d’aya za’a masa asan wan Baban su Fannah ne. Zekai shekaru irin 50 a duniya. Baba dake zaune a bakin k’ofar d’akin Fannah ne ya hango wan nasa nan ya mik’e “sannu da zuwa Ya Khaleel.”

        “Sannu dazuwa fa kace? Ashe iskancin da ‘yarkan tayi kenan shine ka b’oye min kak’i gaya mun, toh Allah ya sanar dani gaskia.”

     “Haba ya Khaleel ya kake magana haka? Kafi kowa fa sanin halin Fannah ba halinta bane tarayya da d’a na miji.”

       “Ni ba abinda nake nufi ba kenan, my point is adena kirar ‘yata kariya. Alhj Suleiman kai da d’anka zaku iya tafiya, abincin wani gub’an wani kamar yadda ka k’yamaci Fannah haka wani zeji kamar ya mutu mata. Ahmad Allah had’aka da rabonka, ka kasance masoyin Fannah na hak’ik’aamman there is nothing you can do now dole ka hak’ura kabi umarnin mahaifinka, in zakumin uzuri, I need to see my daughter.” Yana kaiwa nan ya shige d’akin Fannah.

       Idanun Ahmad take suka kad’a sukayi ja, koda wasa be tab’a tsammanin akoi abinda ze shiga tsakaninsa da Fannah ba, yana santa fiye da yadda yake san kansa. “Abba dan Allah kar muyi haka, wallahi nasan Fannah is innocent.”
      “Ahmad kaji na rantse maka kasake min maganan wannan kariyan zan tsine maka, ai saisa akace a bincike mutum shiru-shiru. Maza mu wuce gida, Alhj Khaleel nagode sosai Allah bar zumunci.”

      “Bakomai Alhj Suleiman, ita gaskiya haka take daga k’in jinta kuma se b’ata. Allah rufa mana asiri.” Da fad’in “ameen” Ahmad dake hawaye shida mahaifinsa suka bar asibitin. Suna ficewa ya Khaleel ya b’alle da dariyar mugunta. “Ai dama nace in shaa Allahu ‘yarka barata auri wani ba inba d’ana ba. Kyakkyawar mace me addinin muslinci Farouq ya cancanta kuma ba kowa bace illa Fannah saboda haka tana warkewa zanje in samu Baba (mahaifinsu) in masa magana.”

      Gida ya zarce yana isa ya soma k’olla ma d’ansa Farouq kira. “Farouq! Farouq! Zo nan” alokacin ya zauna kan wata tabarma bada jimawa ba Farouq d’in yafito da angansa an ga d’an iska wata shegiyar crazy wando ne a jikinsa da singlet. Ba laifi yanada kyau dadai dakuma tsawo. Bayan ya zauna yace, “gani Baba.” Ya Khaleel ya kallesa sannan yace, “d’ana ka kwantar da hankalinka Fannah ta kusan zama taka, Fannah taka ce! Yanzu ana sallamota daga asibiti zan wa kakanka magana.”

       “Baba dagaske!” Farouq ya tambayi mahaifinsa cike da jin dad’i. “Da dana ce maka seka auri Fannah ka d’au wasa nake maka ne? Ai Fannah taka ce.”  “Kai Baba na gode amman da akoi matsala Baba.”
      “Ina jinka Farouq mecece matsalar yanzu in warkar maka da ita?”
       “Fannah… Bata so na Baba ko kad’an zan iya irga sau nawa muka tab’a magana da ita, sam bata sona ta tsane ni.”
      “A da kenan…” Ya khaleel ya fad’a yana murmushin mugunta.
      “Ban gane a da ba kenan Baba.” Farouq ya fad’a a little bit confused.

      “A da datake da tabbacin cewa akoi masu santa amman banda yanzu data rasa budurcinta, kap ba na mijin da ze so ta yanzu, ta zamo tamkar k’azantar da akeson a yasar ne yanzu. Ko baka gane ba?”
      “Sosai na gane Baba na gode.”
  
    *
       Afrah ce tsaye kan Fannah tana kallonta hawaye suna gangara kan kumatunta a yayinda Baba da Mami suke zaune kan wata kujera, Aiman kuwa an mata shimfid’a a k’asa tana bacci. Hannu Afrah ta mik’a dan ruf’e Fannah mekyau da  bargo taga kamar Fannah tad’an motsa.

     “Barin je in kama ruwa” cewar Mami “ina zuwa yanzu.” Kai Fannah ta kad’a a hankali again. “Ya Fannah! Baba! Mami! Fannah tayi motsi.” Kafin su Mami su k’ariso Fannah ta soma bud’e ido a hankali tagama bud’e idanun nata ta sauk’esu kan family’nta dake tsaye a kanta suna murmushi da zubda hawaye a lokaci d’aya, murmushin tayi k’ok’arin mayar masu da k’yar.

     “Ya Fannah!” Cewar Afrah
     “Fannah! ‘yata” cewar Mami.
      “Mama na!” Cewar Baba.

      Kallonsu take a hankali cikin wata dashasshiyar murya tace, “Mami, Baba, Afrah.” Dad’a k’aruwa murmushin fuskarsu yayi Baba yace, “Afrah jeki kira nurse kice mata Fannah ta farfad’o.” Bayan minti d’aya Afrah dawata nurse suka shigo d’an dube-dube tayi wa Fannah sannan taceda su Mami “Alhamdulillah condition na ‘yarku is stable. Inda hali a had’a mata tea me kauri tasamu tasha se abata magunanta. Excuse me.”

     Hugging nata sukayi one-by-one kowa na muranan dawowarta. “Ina Aiman?” ta tambaya a wahalance kusan a tare suka amsata “gata can tana bacci.” “Fannah ya jikin naki?” cewar Mami
      “Da sau… Argh!” Tasaki k’ara.
     A rikice Mami tace. “ina ke maki zafi Fannah?” Take idanunta suka cike da hawaye, “k’asa na Mami, zafi.” “Malam ko zaka d’an bamu waje dan Allah” cewar Mami cike da tausaya wa ‘yarta. Bayan Baba yafita Mami ta umarci Afrah ma da tafita ba gardama ta fice.

       “Fannah kiyi hak’uri dole k’asarki ya miki zafi anji miki ciwo.”
     Tana kuka tace “Mami ya rabani da budurci na ko? Mami banida martaba yanzu.” Ta fashewa dawata erin matsanancin kuka.

     “Fannah ‘yata dan Allah kiyi hak’uri kukan nan k’ara miki rashin lafiya zeyi, kiyi hak’uri. Ki d’au wannan k’addara ce Allah ya turo miki.”

      Cikin kuka tace, “Mami yanzu akoi d’a na mijin da ze yarda ya aureni? Nasan ko Ya Ahmad ze gujeni.”
       Shiru Mami tai batace komai ba hakan ya sake tabbatar wa Fannah zancenta. “Yama riga ya tafi ko Mami?” Har yanzu Mami batace da ita komi ba se kuka ba sautin da takeyi. “Mami talk to me please, ki fad’a min gaskia.”

     “Fannah kiyi hak’uri wannan jarabawa ce Allah keson gwada ki, in baki rungumi k’addara ba seki fad’i. Ahmad be k’i ki ba mahaifinsa ne ya tilasta masa se ya rabu dake saboda Kawu Khaleel yace masa saurayin kine ya miki wannan abu.”
       “Mami amman ai k’arya ne, wallahi bansan shi ba acikin lungu kawai ya tsareni wallahi ban tab’a ganinsa ba inba ranan ba.”
      “Shhhh! Fannah basekin min bayani ba sanin kanki ne Kawu Khaleel tinba yau ba baya sanki, yayi hakan ne kawai dan ya shiga tsakaninki da Ahmad dan yaga Ahmad nasanki tsakani da Allah.”

       “Mami me na masa ya tsaneni haka? Mena ma wannan saurayin daya k’wace min martaba ta Mami? Shin na kasance mutumiyar banza ce da duk munanan abubuwa suke faruwa dani?” Hannu Mami tasa ta goge mata hawayen dake gangara kan kumatunta, “ko kad’an habibti, ita duniya haka take mutane masu kind heart su Allah yake jarabta saboda ya gwada nauyin imanin su. Wannan jarabawa ce Fannah you have to be strong.”

     *****
     *ANAS*

       D’aki ne babba da gadaje guda uku ciki, haka wardrobe ma, sannan da bathroom aciki. A d’aya daga cikin gadajen Anas ke kwance akai da earpiece a kunnensa wanda ke had’e da wata sabuwar Iphone 6s ajiye kan cikinsa. Sanye yake da ¾ wando da vest bak’a ya zura wa ceiling ido se tunani yake. Bada jimawa ba wasu samaruka guda biyu suka shigo wanda suke nan sa’anin Anas, da angansu anga ‘yan hutu. Gado d’add’aya suka d’auka suka kwanta kai har alokacin Anas besan da shigowarsu ba.

      Pillow d’ayan ya wulla masa a firgice ya mik’e ya zauna ganin su ne yasa ya sauk’e ajiyar zuciya. “Mehn! Yaushe kuka shigo bansani ba.”

      “Well kayi nisa a tunani taya zakayi noticing shigowarmu?” cewar na k’arshen. “Waima tunanin me kake haka? Kullum fa cikin tunani kake ko ka bar mata da ‘ya‘ya ne acan gda 9ja?”
  
     suka k’yalk’yale da dariya illa Anas daya tsaya yana kallonsu.
     “Musty waikam meke damun Anas ne?” cewar d’ayan.
     “Ji Abdul de da wata magana budurwarsa ce ni da zan sani?”
     “Oh oh no please banda maganan budurwa anan” Anas ya fad’a in an angry tone.

        “Wai Anas kai kullum haka kake ne? Ban tab’a ganin kayi dariya ba wallahi, whats wrong with you? And anytime aka kawo maganan girlfriend you seem so moody.” Cewar Abdoul.

    “Nima de, abin have been bothering me.” Hannu yasa yaja d’aya daga cikin bedside drawer’n gadonsa tare da ciro wani syrup ya wulla wa Anas karap ya cafke. “Meh wannan kuma?”

    “Wannan!” yad’an murmusa “lets say anti-problem kokuma problem reliever.” Shida Abdoul suka kwashe da dariya. Kallaon syrup d’in Anas yayi sannan ya ajiye kan bedside drawer’n nasa “no thanks barin sha ba.”

     “Chill bro!” cewar Musty. “It’ll ease all your problems just give it a try.” Haka suka ta cika masa baki kan in yasha ze manta yanada problem ko d’aya akansa seya d’auka ze sha seya tuna wa’azin da Abuu yamasa amman kuma problems sun masa yawa right now gana Ummimi gakuma na yarinyar daya yi raping. Rufa ido kawai yayi daga k’arshe yasa kwalban syrup d’in a baki. “Dude (maza) karka shanye duk-” be k’are maganar ba Anas ya kauda kwalban syrup d’in daga bakinsa sanda ya kwankwad’e tas.

     Fuska ya yamutsa trying to adjust and in just 3 minutes Anas ya fad’a bacci, baccin daya jima beyi ba in a lifetime.

     _7 hours later_

     Daidai 8:30PM Anas ya tashi, ko sallan la’asar, maghrib da Isha beyi ba duk yini yayi yana bacci. “Holy shit!” Ya fad’i. Sede kuma kap ya nemi problems nasa ya rasa, da yayi niyan bare sake shan syrup d’inba amman dan yadda ya masa aiki he can’t resist it. Daidai ya mik’e ze shiga toilet Musty da Abdoul suka shigo da angansu anga wad’anda suka dawo daga party, dan aikinsu kenan. “Ya dude har ka tashi ne?” Musty ya tambayi Anas yana k’ok’arin zama.

         “How did you like the syrub? Your problems will all be gone for good two days and after that seka nema ka sake sha, continiously” Abdoul ya ma Anas bayani tare da fad’awa kan gadonsa da baya.

     “Great!” Anas ya ce, “I can’t remember any of my problems now saidai nata bacci ko sallan la’asar banyi ba.”
     Tsuka Abdoul yaja “yanzu dan kawai yau ka rasa sallolin nan shine wani abu? Kaifa Anas kanada case, wannan blue eyes naka basu taimake ba. Nifa the first time I saw you nad’au American ne kai to seme dan ka share sallolin yau?”

    “Tell him bro” cewar Musty. D’an murmushi Anas yayi lallai duk iskancin mutum dubu sun fisa, can a Bama sune ‘yan iskan gari nan kuwa a tafin hannun su Abdoul yake be sauraresu ba yashige toilet yayi alwala yafito ya rama sallolinsa.

  Da misalin k’arfe 11:30PM su Musty suka kuma yin wanka suka yi shiri tsaf a yayinda Anas keyin zanen project da aka basu a school. Da suka zo fitane suka juya suka kallesa tare da kad’a kai. “Anas wai kai ko kad’an baraka gwada zuwa clubbing d’innan bane? Wallahi its fun, more fun than wannan jakin project da kakeyi na 5 marks kacal.” Cewar Musty ransa a b’ace.

     “No kuje kawai, I have to get this done, maybe next time.” Anas ya sanar dasu yana d’an murmushi.
   “Dude listen to him, ko na yau ne kazo muje club d’innan.” Cewar Abdoul. Kai kawai ya kad’a masu bayan sun fice yayi rounding up abinda yakeyi ya kira Ummie bayan sun gaisa yasa ta mik’a ma Angel nasa suka ta hira abinsu. Anas na mutuwan san Amal badan komai ba dan abinda Ummimi ta mata.

     Ace yarinya kwanan ta d’aya a duniya amman dan rashin imani tasa a dawo da ita gida ko shayar da ita batayi ba.

_2 days later_ 

         Da misalin k’arfe 12:30PM Anas na kishingid’e kan wata couch (kujera me fad’i da akan iya bacci akai) yana bacci. Ya soma mafarki;

    _“Ummimi dan Allah karki tafi kiyi hak’uri indan plates dana fasa ne I promise baran sake ba. Ummimi I am sorry dan Allah karki tafi. Abuu ka hana Ummimi tafiya dan Allah kace mata I will be a good boy from now on.”_

       _“Yanzu Aysha bara kiji tausayin yaranki ki hak’ura ki zauna dasu ba. Kalli yadda suke kuka fa?_

    _“Mstww wannan kuma ku ya shafa nagaji da zama cikin talaucin nan, ace kullum se atashi ba’a san me za’a karya dashi ba gaskia nagaji daman tun farko sanda Abba na yace kar in aureka matsiyaci ne kai amman nak’i sauraronsa. Ga can miji Allah yamin har k’asar waje ze kaini saboda haka ban ga abinda zesa in cigaba da zama a wannan gidan ba.” Jakarta ta ja ta soma tafiya da sauri naje na kama k’afarta ina kuka ina rok’arta wani wawan ball tayi dani da k’afa sanda na ji ciwo a elbow na…”_

“UMMIMI!” Anas ya kira da k’arfi a yayinda ya farka daga baccin dayakeyi duk zufa yakeyi se nishi yake da k’arfi ganin mafarki yake yasa hankalinsa yad’an kwanta. Wani erin mahaukacin bacci yakeji saboda jiya kwana sukayi a studio amman saboda duk sanda ya rufe idansa mafarkin Ummimi yake yasa ya kasa baccin abu d’aya ne yasan inyasha ze gusar masa da problems nasa which is syrup na problem reliever (giya) da Abdoul ya basa ranan.

     Kash! Saidai basu gida sun fita yawo gashi bacci yakeji. Gwada jirarsu yayi na ‘yan mintuna ganin basu dawo ba yasa ya kira sa a waya kai tsaye ya tambayesa ina yake ajiye syrup daya basa ranan yana san sake sha. Dad’i sosai Abdoul yaji finally Anas is ready to change, bayanin ina yake ajiye wa ya masa yakuma tabbatar masa in zasu dawo gida ze sake siyowa tunda wanda ya rage kad’an ne.

       Exactly inda Abdoul yamasa kwatance yasamu syrup d’in bud’e sabon kwalb’a yayi yakafa a baki sanda yashanye tas, ko cikakken minti biyu beyi ba yasoma jin bacci me nauyin gaske tsalle kawai yayi ya fad’a kan gadonsa yasoma wani erin mahaukacin bacci me uban nauyin gaske

           *© miemiebee*

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 07
BY MIEMIEBEE

        FANNAH

      3 days later…
  
     Kwanan Fannah uku a asibiti tasamu k’arfin jiki aka sallamesu, ayau suke shirin dawowa gida, Alhamdulillah jikin nata da sauk’i sosai saboda anti-biotics datake sha masu k’arfi ne sosai. Baba ya sayarda shanunsa da shi ya samu ya biya kud’in asibitin ta da kuma na magunanta.

     Daidai sun sauk’o daga keke na pep kenan se ga irin almajiran unguwan nan sunzo sun tsaya gabansu.

         “Fannah! Dama ashe ke d’in kariya ce me bin maza, sekitayin abu kamar ‘yar malam saliha to Allah ya tona miki asiri tunda saurayi yayi miki ciki.” Hannu Mami ta d’aga ta wanke sa da mari. “In na sake jin wannan munanan kalamu daga bakinka kaji na rantse seka kwana a asibiti, bakai kad’ai ba dukanku nan. Fannah ba kariya bace abinda ya sametan nan k’addara ce. Maza ku fice min daga kallo.”

    Baya sukayi kad’an sannan suka soma wak’a “kariya! Kariya! Fannah kariya Fannah kariya!” Hannun Fannah kawai Mami taja suka shiga ciki a yayinda Baba ya koresu.
    Kuka Fannah keyi sosai. “Yanzu shikenan Mami kallon kariya za’a na mun? Shikenan rayuwata ta lalace Mami.”
        “Shhh karkiyi magana haka, karki saurare wad’ancan almajiran basu masan me suke fad’i ba.” Hugging nata tayi har sanda Fannah tayi shiru.

      Da yammacin ranar around k’arfe 4:45PM Ya Khaleel da d’ansa Farouq suka shigo gidansu Fannah. Mami da Afrah suna had’a girkin dare suka masu sannu da zuwa, ba abinda Afrah ke masu se harara. “Ke Afrah jeki kira min mahaifinku dakuma ‘yar ku kariyan can.” cewar Ya Khaleel.

           “Kawu Khaleel bamuda kariya a gidan nan.” Ta fad’a stubbornly.
          “Ke ni keke gaya wa magana? Iyye?”
     “Kawu kayi hak’uri Afrah kibasa hak’uri kije ki ma Babanku da Fannah magana.” A sanyaye ta mik’e taje ta kira Baba sannan takira Fannah a tare suka fito. Fuskar Baba a tamk’e ya zauna kan tabarman da Ya Khaleel da d’ansa ke kai ba tare da ya musu magana ba.

       “Ina wuni kawu?” Gaisuwar Fannah.
        “Yawwa sannu an sallamoki kenan. Se a kiyaye aukuwan na gaba kafin wani saurayin yasake fiad’e ki.”

     Har tsakiyan kanta tajiyo wannan kalamai ba ita kad’ai harsu Baba da Mami da Afrah. “Ya Khaleel in kasan batun daya kawo ka gidana dan kaci zarafin ‘yata ne dan Allah kayi hak’uri na had’aka da Allah ku tashi ku tafi.”

       “Ba seka koremu ba yanzu zamu tafi. Magana d’aya biyu na zoyi nan saboda haka nakeson ku bud’e kunnuwanku ku saurareni. Kunfi kowa sanin yadda ake k’yamatan kariya a gari, ba uban da ze so d’ansa ya auri macen da batada budurci. Fannah kuwa ‘yata ce dukda abin kunyan da ta mana ina san ta saboda haka zan bata wa d’a na Farouq.”

     “What!?” Baba yayi exclaiming.

     “Bari na gama mana k’ani na. Na riga nayi wa Baba magana kuma ya goyi bayan zancen d’ari bisa d’ari bawai nazo nan bane in baku choices saboda bakuda choice inbanda ku yarda mu rufa wa kariyarku asiri dan na tabbata kap garin nan bame san aurenta. Kinji ai Fannah? Ga Farouq nan mijinki, kina k’are secondary ze rufa miki asiri ya aureki zaki iya gode masa saboda wannan jahadi yayi. Auren kariya ba wasa bane.”

     D’ago jajyen idanunta tayi ta azasu kan Farouq dake ta mata murmushi. Hawaye se gangara suke kan kumatunta, kuke take sosai. Tasani a yanzu kam kamar yadda Kawu ya fad’i ba na mijin da zeso aurenta saboda ta rasa budurcinta martabatar ta, amman duk da haka gomma ta mutu batai aure ba data auri Farouq. Farouq baida tarbiyya ko kad’an d’an iska ne ba aikinsa se bin mata Allah kad’ai yasani ko baida cutar k’anjamau ma. Ba yadda za’ayi ta auresa.

       “Kawu dan Allah kayi hak’uri ni baran auri Ya Farouq ba, dan Allah ka rufa min asiri.”

        “Ji shashasha dabadan Farouq nada imani bama jinki ze yarda ya aureki ne? Ajinki a kariyan da kike yanzu zaki samu na miji kamar Farouq yace ze aureki ne? Inba mahaukaci ba wallahi ba na mijin de so ya aureki gara ma tun wuri kinsan ina ke miki ciwo”

      “Enough Ya Khaleel!” Cewar Baba a fusace. “ ‘yata barata auri wannan d’an iskan ba. Mungode da alfarman da kuka bamu amman bamuso da in aura wa ‘yata d’an iska kaman Farouq na gommaci kartayi aure a duniya. Yaro ko gaishe dana gaba dashi be iya ba. Ku tashi kubarmin gida zanje in samu Baba in masa magana yaja da baya da wannan zance. Fannah bata san Farouq saboda haka barin tilasta mata ba.”

      “Aww haka kace kenan? Yanzu har zaka bud’e baki ka kira d’a na Farouq d’an iska? Kariyarka kuma fa? ai nakega sede ace mata ‘yar guguwa, aure tsakanin Fannah da Farouq kuma consider it done bari ta k’are shirmen secondaryn nan kuga ikon Allah. Wawiya ana taimaka miki kina wawanci mschww Farouq tashi mu tafi da Allah.” Suna ficewa Fannah ta ruga d’aki da gudu ta baje kan katifar ta tana kukan cire rai. Afrah ce tabiyo bayanta itama kukan take tabbas Fannah tana cikin tsaka me wuya duk wanda ya aikata mata ta’addancin can ya cuce rayuwarta har a bada.

       Tun ba yau ba Fannah ta tsani Farouq taya za’ace shi zata aura? Kasheta akeson yayi?

     “Yi hak’uri Ya Fannah dan Allah kibar kukan nan in shaa Allah baraki auri Ya Farouq ba.” D’ago jajayen idanunta tayi “Afrah shikenan ni haka rayuwata zata k’are cikin k’unci da bak’in ciki? Mesa se ni Afrah? Mena tab’ayi da ba kyau to deserve all this? Duk abinda addini na yace inyi inayi wanda kuwa ya haramta ina k’ok’arin nisantar kaina daga aikatasu. Mesa seni wancan saurayin zeyi raping? Mena masa Afrah? Mesa seni za’a ce zan auri Ya Farouq kinfi kowa sanin halinsa. Kullum yana nan a bayan gari yana kwanciya da mata, Afrah dan Allah ki taimaka min.” Ta kuma fashewa cikin matsanancin kuka.

     Itama Afrar kuka take ta rungumi yarta tana bata hak’uri.

     ****

        “Malam dan Allah kayi wani abu karka bari Kawu ya cimma burinsa na aura wa Fannah aure da Farouq kafi kowa sanin halin Farouq so nawa ake kamasa a bayan gari? Dan Allah kaji k’an ‘yarmu Fannah. Ko kad’an she’s not to blame for what happened to her fiad’e aka mata munyi iya binciken da zamu iya mun kasa samun waye ya mata wannan d’anyen aikin.” Ta fashe da kuka.

      “Maman Aiman in shaa Allah barin bar Fannah ta auri Farouq ba. Yanzun nan zanje in samu Baba in masa magana kishiga ciki kibata hak’uri ki kwantar mata da hankali dan Allah. Ni na wuce…”

**

     “Ina wuni Baba?” Gaisuwar Malam Aliyu Babansu Fannah ga mahaifinsa da Ya Khaleel.
       “Lafya Aliyu, ya jikin Fannan?”
      “Da sauk’i Baba.” Ya amsa yana kallon wansa Khaleel da d’ansa dasuke zaune a gefen mahaifin nasu.
       “Nasan maganan daya kawo ka Aliyu saboda wan ka Khaleel yamin bayanin komi yanzu. Kasani wan ka bare tab’a maka abinda ze cutar dakai ko iyalinka ba. Kafi kowa sanin halin da ‘yarka tashiga kallon kariya ake mata agari me bin maza-”

      Malam Aliyu katse mahaifin nasu “amman Baba ai duk munsan ba haka asalin abar take ba, fiad’e aka mata.”

      “It still will not change anything Aliyu, in mu mun yarda da hakan mutane fa? Baramu iya fahimtar dasu ba. Kap garin nan ba mahaifin da ze b’ar d’ansa ya auri wacce batada budurcinta tattare da ita kasani Aliyu. Allah ya kawo mana sauk’i gida ga wan ka nan Khaleel he is ready ya rufa wa ‘yarka asiri ya d’au d’ansa ya aura ma ‘yarka dukda ba cikakkiyar mace take ba yanzu amman har ka bud’a baki kace bakaso? Ina zaka zo ka kai ‘yar taka?”

    “Baba in shaa Allah, Allah ze kawo mata miji wanda ze sota a yadda take.”

     “Har tsawon yaushe kuma zaka tsaya kana jiran wannan rana da bakasan ranan zuwanta ba? Iyye Aliyu? Bana sake jin wani zance, Fannah zata auri Farouq wannan shine san da muke mata bamusan tak’are rayuwarta batayi aure ba.”

      “Baba dan Allah kayi hak-”

   Baba ya katse sa. “Aliyu wannan shine karo na farko da kake k’ok’arin bijire min, kar muyi haka da kai. Farouq.” ya waiwayo da kallonsa kan Farouq

    “Na’am Baba.” cewar  farouq.

    “Kanason Fannah zaka aureta koda bata da budurcinta a tattare da ita?”

        “Eh Baba ina santa k’anwa tace koda duniya sun k’ita ni baran k’ita ba.”

    “Masha Allah” Baba yace. “Kaikuma fa Khaleel ka yarda d’anka ya auri macen da tarasa budurcinta?”
  
      “Na yarda Baba” cewar ya Khaleel. “Fannah ‘yata ce matuk’an ina raye zanyi duk iya abinda zan iya dan in kula da ita in rufa mata asiri.”

   “Toh masha Allah kadeji Aliyu. In nine kai godiya zanyi wa Khaleel da Farouq.”

    “Baba amman Fannah batasan Farouq, bata tab’a sansa ba, taya zamu tilasta mata auren wanda bata so.” Cewar Malam Aliyu.

      “Wannan kuma ba me wuya bane, in suka soma ganin junansu a hankali zasu shak’u. Allah dad’a had’a kawukan ku.”
    “Ameen” Ya Khaleel ya amsa banda Malam Aliyu dake ji kamar yayi kuka.

**

     “Sannu da dawowa Malam” cewar Mami tana k’ok’arin shimfid’a masu tabarma. Bayan sun zauna take tambayarsa ya had’uwan nasu ya gudana. Kai ya kad’a a hankali take jikinta yayi sanyi.

      “Maman Aiman Ya Khaleel ya riga ya saye Baba nuna masa yayi intensions nasa are clean tsakani da Allah yakeson ya aura wa Fannah Farouq saboda tsantsan tausayi.”

    “Malam amman ai duk munsan badan haka bane.” Mami ta katse Baba. “Tun ba yau ba idanun Kawu suke kan Fannah shikansa yasan tana da tarbiyya mekyau da hankali so yake ya aura wa Farouq Fannah saboda ta giara masa d’a ita kuma tasha wahala in the process.”

        “Ba k’arya cikin magananki Maman Aiman ni kaina abin nan ya dameni bansan ya zanyi ba, tausayi Fannah take ban matuk’a yarinya me hankali ace arasa ma wa za’a d’aura wa k’addara erin wannan se Fannah.” yaja numfashi.

   “Uhn uhn Malam kayi istigifaar kar kayi sab’o. Wannan Allah kad’ai yasan mesa ya d’aura wannan mumunar k’addara kan Fannah bekamata muyi ma Allah shisshigi ba.”

     “Hakane Maman Aiman Astaghfurullah.”

     “Yanzu Malam shikenan sede mu zuba ido muna ganin ‘yarmu zata auri wannan d’an iska? Ba abinda zamu iya mata? Innalillahi!”

     “Da akoi abinda zan iya da nayi Maman Aiman banasan Fannah ta auri Farouq ko kad’an. Ran Baba ya b’aci ya dage se Fannah ta auri Farouq inhar na hana aikuwan wannan aure, zamu iya samun sab’ani da mahaifina.”

       Fannah dake lab’e ajikin bango tana sauraronsu ba abinda takeyi se hawaye. Daidai lokacin wani yaro yashigo gidan bayan ya gaisheda Mami da Baba yace “wai Fannah tafito inji Farouq.”  “Barata fito ba” cewar Baba a fusace. “Kace masa barata fito ba inji mahaifinta.” Nan Fannah dake lab’e tafito “kace masa ina zuwa.”  “Fannah!” Mami da Baba suka kira a lokaci d’aya.

         Tana kuka tana maganar, “Baba naji duk abinda kuka fad’a barinso saboda ni kasamu matsala da Baba ba. Muyi hak’uri mu rungumi k’addara fatarmu Allah sa hakan shi yafi alkheri, Allah sa auren Farouq ba sharri bane a gareni, addu’an da nake so kumin kenan. Barinje kirarsa kar yaje yasamu Baba ya fad’a masa wani abu daban yajawo maka matsala.” Tana kaiwa nan ta fice.

     Kuka me k’arfi Mami ta fashe da shikansa Baba sanda ya zubda hawaye, babu kamar Fannah, yarinya me hak’uri da hankali dole yasan abinda zeyi ya hana aukuwan wannan aure.

     Tana fitowa taga Farouq zaune kan benchin da take zama kullum da Ahmad nata take hawaye ya ciko mata a ido. “To ke kuwa Fannah haka ake hira? Haka kika sabayi ne in samarukan ki sunzo wajen ki? Taho nan mu zauna mana.”
       Kafin tace meh Farouq ya taso ya cafke hannunta da sauri ta waske hannun nata daga rik’onsa. Tana kallonsa da jajayen idanunta.

    “Meh haka kuma? Yau na miji ya soma rik’e hannunki ne? Kinga nifa ki sake jikinki dani tunda nasan ciki nasan waje ba sekin tsaya kina proving min innocence ba.” Hannun nata yasake rikowa da k’arfi sannan ya aza d’ayan hannun sa kan fuskarta yana shafawa. “Ji laushin jiki wai a haka ma kinbar samaruka suna tab’awa kenan.”

       K’ok’arin k’watan kanta take amman ta kasa se hawaye take yi “Farouq kasake ni bana so, kadena tab’ani.” K’in saketa yayi “meh aciki dan na tab’a mata ta ko kin manta a matsayin mijinki nake yanzu.” Matso da fuskarsa yayi sosai kusa da nata. Numfashinsu yana had’uwa. Kafin ya hankara Fannah ta tsinke sa da mari wanda besan sanda ya saketa ba.

     Hawaye take sosai “karka kuskura ka sake tab’ani in kai d’an iska ne toh ni ba ‘yar iska bace, in ka saba tab’a mata anyhow ni ba d’aya daga cikin ‘yan matan da kasaba tab’awa bane.”

   “Dallah can kariya kawai, keda kike bin maza kowa ya sani, zaki wani zo kina min zak’in baki. Kuma barikiji in fad’a miki duk sanda kika kuskura kika sake marina wallahi kinji na rantse sekin sake kwana a asibiti. Humm!” ya sakar da wata shu’umar murmushi “bari a aura min ke zaki yaba wa aya zak’inta. Se gobe ko baby, ki kula min da kanki please karki sake bin wani har abu yakuma shiga tsakaninku nasan you are itching to be with a guy.”

© miemiebee

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 08
BY MIEMIEBEE

Kasa cemasa komai tayi, kallonsa kawai take hawaye na gangarowa kan kumatunta, kuka ne yafi k’arfinta juyawa tayi tashiga gida da gudu ta tsaya daga wata lungu ta share hawayerta sannan ta k’arasa ciki. Mami da Baba ta tarar zaune yadda ta barosu. Basu ce da ita komai ba dan haka tashige d’akinsu da Afrah ta fashe da kuka bata san da wanne zata ji ba da rabata da akayi da budurcinta martabarta na k’arfi da yaji ne kokuma da auren wannan monster me suna Farouq tun be aureta ba ma yasoma mata rashin mutunci yana zaginta bale ace in sunyi aure, kwata kwata baida slightest regard mata.

     Bada jimawa ba Mami ta aike Afrah shago siyo man giad’a tun kafin Maghrib yayi gudun kar abinda ya faru da Fannah yakuma samun Afrah. Afrah ne tashigo d’aukan hijabi a d’akinsu, Fannah dake kwance a kan katifa da Qur’ani tana karatu ta d’aga kai tare da tambayarta. “Ina zakije haka?”
      “Shago fa Mami ce ta aikeni siyo man giad’a.”
      “Okay, jirani muje tare nagaji da zama nan shiru ni kad’ai.”
     “Toh sanya hijabinki muje Ya Fannah.” Nan Fannah tasa hijabi suka fito tare, “ya haka ina zaki Fannah?”  tambayar Mami ga Fannah.
      “Zan bi Afrah ne Mami nagaji dazaman cikin.”
     “Toh Allah kare dan Allah in har babu anan shagon Ya Wakil dana mak’otansa karkuyi nisa ku dawo gida kawai, kunji?”
     “In shaa Allah Mami” cewar Fannah sannan suka fice. A shagon Ya Wakil suka samu man giad’an sun jiyo zasu fice sega yaran unguwa sun taru suka soma wak’a

        “Fannah kariya me bin maza Fannah kariya me bin maza.”

         Hawaye tasoma yi bata tab’a tsammanin zatayi witnessing rana kamar ta yau ba, ranan da za’a ce tafita waje ana binta ana zaginta me bin maza.

          “Ku wai bakuda hankali ne?” cewar Afrah “wanj irin ‘yan iska ne ku? Wallahi in baku bar nan ba zan jefe wannan munanan bak’ak’en kankun da dutse, jahilai kawai. Bara ku matsa bane?”

        Ko ajikinsu ma magana ake masu  wak’an su suka cigaba dayi. Mari wani ya sake ma babban cikin nasu Tasss! Kukeji a fuska take ya soma kuka saurayin na juyawa suka had’a ido hud’u da Fannah take ta kau da kanta. Kolar rigarsa Ahmad ya rik’e da hannu d’aya “kanajina in sake jin ka kira Fannah ko wata mace a garin nan da kariya kaga abinda zan maka ba kai kad’ai ba dukanku nan” ya nunasu da yatsa. “Kunjini ko bakuji ba?”

     Baki na rawa babban yace, “munji dan Allah kayi hak’uri.” Ahmad na sakesa suka kwasa da gudu suka bar wajen. K’arisowa gabansu Ahmad yayi “Fannah kiyi hak’uri kibar kuka dan Allah, karki bari maganan yaran nan to get to you.”

         “Ya Ahmad dan Allah kayi hak’uri” Fannah tace tana hawaye hannu kawai tasa ta rufe bakinta ta ruga a guje se kiran sunanta Ahmad yake ko sauraransa batayi ba. Juyawa yayi ya kalli Afrah da itama idanta suka cike da hawaye. “Afrah kiyi sauri ki bita kar wani abu ya sameta. Tell her tayi hak’uri ta rungumi k’addara in shaa Allah, Allah ze sak’a mata kuma kice mata I will never stop loving her koda ban aureta ba, da santa zan mutu kice mata tayi hak’uri, ina kan mata addu’a.” Kai kawai ta giad’a masa tabi bayan Fannah da gudu.

      Tana isa gida ta tarar da Mami a tsakar gida se safa da marwah take.    “Mami ga man giad’an.”
        “Afrah meya samu Fannah tashigo tana kuka ta rufe k’ofar d’akinku nayi nayi da ita ta bud’e tak’i wani abu ne?”
        “Mami wallahi Ya Afrah tausayi take bani, yanzu fitan mu almajirai suka taru suna mata wak’a suna kiranta da munanan suna Mami.” Ta k’are maganar tana hawaye.

     “Allah sarki Fannah” cewar Mami itama tana hawayen, “Afrah inda zan iya karb’e pain da Fannah ke feeling danayi wallahi, it hurts me seeing my daughter in a horrible situation like this kuma ba abinda zan iya mata.” Hannu tasa ta share hawayerta addu’a zamu mata Afrah ko a islamiya ki fad’awa Malamanku su sata cikin add’ua kinji?”
          “In shaa Allah Mami barinje in sameta.” Tana tashi taje ta k’ofar d’akinsu tun daga bakin k’ofar take jin sautin kukan Fannah. “Ya Fannah dan Allah kibar kukan nan batada amfani, addu’a zamu dage dayi, bud’e k’ofar kinji? Ya Ahmad yabani sak’o in isar miki, yi hak’uri ki bud’e.”

    Fannah na jin Ya Ahmad ta tsananta kukanta haka ta tayi kusan na minti ashirin sannan ta tashi ta bud’e ma Afrah k’ofar bayan sun zauna Afrah ta isar mata da sak’on Ya Ahmad, se kuka Fannah ke Afrah na bata hak’uri. Comb ta d’auko da mai ta shafa ma Fannah a gashi sannan ta taje ta kama mata da k’yar, rabuwan gashin Fannah da giara tun kwanciyar ta a asibiti.

      Haka fa rayuwa ta cigaba da kasance wa Fannah, bak’in cikin yau daban na gobe daban, sam bata fita daga gida yanzu saboda duk sanda ta fita se yaran unguwa sun taru suna mata wak’a. K’arshen yawonta bakin k’ofar gidansu ne in Farouq matsiyacin yazo. Makaranta ma ko ina tashiga nuna ta akeyi da yatsa haka suka gama exams nasu batasan me take rubutawa ba.

       Kwata kwata ta fita daga kamanninta tayi duhu ta sake rama. Abinci ma ba kullum take ci ba rayuwa de takoma upside down wa Fannah baiwar Allah ba abinda ke mata dad’i ciki, Allah sarki!

     _One year later…_

       Alhamdulillah Fannah is trying to move on from her past. Hasken ta ya d’an dawo, ta rage tunani yanzu addu’a sosai ita da iyayenta suka dage dayi. Abun da yaran unguwa suke mata kuwa yanzu da sauk’i sosai seta fita kusan sau uku-hud’u ba’a samu matsala ba. Watanni uku da suka wuce akace su Ahmad sun bar garin Bama, koda yazo mata sallama k’in fita tayi badan komai ba wai dan ita a ganinta she don’t deserve him anymore bata san ma ya sake ganinta bale yaji yana santa. Shekarunta goma sha shida yanzu this year ta gama secondary school.

        Baba kam sanda ya kamu da ciwon zuciya saboda erin wahalar da suka sha wancan shekarar, sak abinda ake ma Fannah haka ake masa in ya shiga cikin jama’a shima, ga bin abu a zuciya haka sanda ya kamu da ciwom zuciyan. Yanzu haka gasu nan ne kawai d’an aikin kanikancin dayake d’an yin ma yadena banda ciwon zuciyan dayake damunsa ga hypertension da ciwon sugar sam da angansa za’a tausayawa masa gashi ba kud’in kaisa asibiti a masa aiki.

        Bakuma komai bane ya haifo masa da hypertension d’innan banda halin wansa Ya Khaleel, sam ya dage seya aura wa Fannah Farouq, abinda Baba bayaso kenan ita Fannan da za’a mata auren ma ta hak’ura ta rungumi k’addara yanzu tunda duk saurayin da ya soma zuwa wajenta tun gama makarantar ta se ‘yan unguwa sun korasa, daga yazo yau gobe bara a sake ganinsa ba.

     Farouq kuwa ba kalan walak’ancin da baya wa Fannah musamman ma dayaga yanzu Baba bayida lafiya ko magana be cika san yi ba. Fannah kuwa dama ba mutumiya ce me hayaniya ba haka zezo ya zageta yazagi Babanta ba abinda zata ce masa illa tayi kuka, maganan aurensu kuwa Ya Khaleel ya dage se shiri yakeyi.

        Yau ranar ta kasance Asabar, Mami, Afrah da Aiman sun je gidan suna a unguwar noma Fannah kuwa tana zaune a gida saboda bata san shiga cikin mutane gudun kar a fara nuna ta da yatsa ana kiranta da sunan data tsana wato kariya. Wanke wanke take tajiyo knocking bam bam bam a bakin k’ofa kafin ta wanke hannu tasa hijabi ta duba ko wayene already meshi ya shigo Farouq taga tsaye da alama ya bugu baya cikin hankalinsa.

          “Ya Farouq me kakeyi anan a buge? Dan Allah ka tafi gida” Cewar Fannah murya na rawa.

    Bece komai ba sanda ya iso inda take, atake ta soma b’ari incident daya faru da ita shekara d’aya daya wuce ya soma yawo a kanta shima wancan mutumin daya rabata da martabatan ta a buge ya zo mata, gashi ko hijabi batada. Baya baya take Farouq na matsowa kusa da ita sanda suka kai bango. Hawaye ke tsiyaya daga cikin idanunta “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri kabari.”

      “In bari ko in fara? Ai kinsha yi da samarukan ki se me dan nayi dake yau? After all ni zan aureki.”
      “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri kabari.” Hannu ya aza kan gashinta me uban yawa yana shafawa. “Baba dan Allah kazo ka taimakeni Ya Farouq dan Allah kabari.” Kuka take tana had’asa da Allah. Finciko gashinta yayi da k’arfi “kice kina sona!” Ya daka mata tsawa.

        “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri ka sake min gashi da zafi.”
      “Who cares? Tell me you love me!” Yayi demanding.
      Bakinta b’ari yake se hawaye take zubarwa. Gashin nata yakuma ja fiye da yadda yayi d’azu, k’ara ta sakar. “Nace tell me you love me and you’ll marry me ko in miki kaca kaca anan anyways dama ni zan aureki.”

     Baba dake kwance a d’aki jikin sa yatashi sosai ko motsi dak’yar  yake yajiyo muryan Farouq. Ja da ciki yayi yafito zuwa bakin k’ofar ya d’aga labile. “Farouq… Dan Allah kayi hak’uri kabar ta.” Cewar Baba a wahalance.

     “Nak’i hak’urin Baba, seta ce tana sona kuma zata aureni wacce erin uselsess budurwa take ‘yan matan waje na ma suna cemin suna so na se ita wannan kariya me bin mazan.” Gashin nata ya sake ja “tell me you love me and you’ll marry me for the last time.”

      “Farouq yanzu magana nake maka baraka jini ba?”
      “Da Allah Baba ka rufa min baki da mata ta nake magana bada ubanta ba.”

     “Farouq ina sanka zan aureka dan Allah kayi hak’uri ka sake min gashi” Fannah ta fad’i tana kukan azaba.
       “Banji ba sake fad’a min.” Shiru tayi tana jan hanci se b’ari take ga shi yak’i sakar mata gashi. “Farouq dan Allah ka sake ta, mesa baka ji ne?”
       “Baba nace kamin shiru ko? Kai bakasan addini bane? Ana shiga tsakanin mata da miji ne?” Yadawo da kallonsa kan Fannah “nace tell me you love and you’ll marry me ko sena rage miki kayan jikin kine?”

     “A’a dan Allah karka min haka, kayi hak’uri.”
     “Ke kariya kike kome baraki fad’a min abinda nakesan ji bane?”
     “Ya Farouq ina sanka zan aureka, Ina sanka zan aureka dan Allah kayi hak’uri ka sake min gashi.” Murmushi yayi sannan ya sake ta tare da cusa ta jikinsa k’ok’arin k’watan kanta take amman takasa ga jikinsa duk warin giya. “Yawwa my beautiful Fannah I love you too, karki damu nan da ‘yan watanni za’a mana aure.” Kuka take sosai “Ya Farouq dan Allah ka sakeni.” Yasar da ita yayi a k’asa sannan ya juya yana tafiya nan da can ya fice.

     Kuka sosai Fannah keyi so helplessly shi kansa Baba kuka yakeyi bare iya barin Fannah ta auri Farouq ba there has to be a way. Farouq besan darajar Fannah ba be kamata ace an barsa ya aureta ba inbanda wahala ba abinda zata sha a gidansa. “Fannah mama na dan Allah kiyi hak’uri in shaa Allah baraki auri Farouq ba, kiyi hak’uri barin iya tashi in taimakeki ba.”

       Hannu tasa ta share hawayenta “karka damu dani Baba kabar kuka kar jikinka ya k’ara tsananta.” A sanyaye ta mik’e zuwa d’akinsu ta baje kan gado tana kuka kamar zata cire ranta.

**
      Da dare around k’arfe 8:30PM.
    “Abinda d’an mayen yazo yayi ma Fannah kenan Malam? Wallahi abun nasa yayi yawa gaskia k’ara zan kai wajen me gari.” Cewar Mami cikin tashin hankali. Bata tsaya jin me Baba ze fad’a ba ta fire zuwa d’akinsu Fannah a kwance ta sameta tana bacci a wahale numfashinta se sama sama yake dan yadda tasha kuka. Take idanunta suka cike da hawaye tayi kan ‘yarta tare da zura mata ido. “Fannah dan Allah kiyi hak’uri wallahi in shaa Allah baraki auri Farouq ba, zanyi duk abinda nasan zan iya in hana aukuwan wannan aure.”

     _“Bawan Allah dan Allah karka lalata min rayuwa kayi hak’uri ka rufa min asiri I’m just 15.”  “Nak’i baran hak’ura ba. Ita da ta tafi taji tausayin mu ne? se na k’wace abin yau yaso seki je ki fad’a mata, banga abinda ze hanani miki wannan abu ba yau.”  “Dan Allah kayi hak’uri. Wayyo Allah Mami na ze kasheni…!!”_

     Firgit! Fannah ta farka daga baccin da takeyi se nishi takeyi me nauyi, zuciyar ta na bugawa da k’arfin gakse jikinta duk yayi zufa se b’ari take. Mami na tab’a ta, ta k’urma wata erin ihu. Daga nan Mami tagane mafarkin incident na ranan tayi dama haka yake mata duk sanda tayi mafarkin seta tashi tana b’ari tana kuka da an tab’ata kuma seta tsala ihu. Yau k’imanin shekara kenan kusan kullum se Fannah tayi mafarkin daren da aka rabata da budurcinta martabarta.

      “Fannah Mami ce ba abinda zan miki, Mami ce” a hankali ta sake gwada tab’a Fannah wani ihun ta kuma b’urmawa. “Mami ce Fannah, Maminki” a hankali ta tab’a hannunta sekuma batayi ihun ba hugging nata Mami tayi a hankali tana shafa kanta.

      “Mami mutumin… Dan Allah kice karya dawo.”
    “Shhhh! Mafarki ne Habibti mutumin yatafi bare sake dawowa ba. Mafarki ne kinji? In kawo miki ruwa?” Kai Fannah ta giad’a a tsorace Mami na mik’ewa taja zaninta “Mami dan Allah karki tafi, ze dawo. Ki zauna dani dan Allah.” Zama Mami tayi Fannah ta rungumeta gamgam wane za’a k’wace mata ita tana hawaye.

© miemiebee

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 09
BY MIEMIEBEE

United Kingdom, London
ANAS

                 _shima bayan shekara d’aya…_
  

             Acikin babban Beach dake waje da London, Anas ne mik’e kan wata doguwar kujera da blue sunglasses a fuskarsa kwata kwata short nicker ne kad’ai ajikinsa seda headphone dake kansa wanda ya had’a da wayarsa yana nin cool music. Kallon sama yake yayi nisa cikin tunani.

       Bottled wata aka wulla masa a firgice ya mik’e ganin Musty ne yasa yayi murmushi wanda ya bayyano da fararen hak’waransa. “Kai! Abdoul where are you? Yau Anas yayi murmushi harda ciro hak’wara. Tell me why do you seem so happy?”

     Murmushin ya sake, “my dreams are coming true one-by-one.” cewar Anas.
      “Wani dream kenan Anas?” Musty ya tambaya.
     “Humm!” yakuma murmusawa ta gefen da dimple nasa yake. “Ni dreams d’ina guda uku ne kacal a duniyan nan.”
     Musty ya giara zama “ina jinka!”
     “Kaga na farko to be a billonaire not a millonaire but a billonaire. After that kaga in nayi kud’i I can toy with women hearts, saboda one thing I’ve learnt in life is ba abinda mata sukeso fiye da kud’i a duniya, zanyi amfani da wannan damar in saye zuk’atarsu dashi, akan kud’i they are ready to sacrifice everything I mean everything harta family’nsu, kaga ko in nayi kud’i nasan ba macen da zata k’i ni ko akoi?” Ya tsaya ya tambayi Musty.

     Musty dake jin dad’in wannan labari yace, “ai ko a yanzun ka ma ba macen da zata k’ika Anas you’ve got the looks and the blue eyes also.” Murmushi sukayi dukansu “ehemm. Ina jinka…”

      “Yess! As I was telling you, inason inyi wasa da zuqatan ‘yan mata a k’alla 100-200. So nake na karya musu zuqatansu ta yadda barasu sake san kawo na miji cikin rayuwarsu ba, so nake su d’and’ana how it feels to be left alone.”

     Kai Musty giad’a a hankali alaman yana gane abinda Anas ke nufi “so in ka karya masu zuqatan nasu what will you benefit from it?” Daidai lokacin Abdoul yazo ya zauna dawata American babe kan cinyarsa tasha bikini (pant and bra) “Hi Fauzy!” Tace da Anas sunan da ake kiransa dashi a can London kenan kasancewar su turawa sun saba da kiran mutum da family name nasa (ANAS IBRAHIM FAUZY)

          Ba tare da ya kalleta ba yace “hey.” Abdoul ya d’ibi k’asa me laushi dake beach d’in ya watsa wa Anas. “Budurwar tawa ma seka ja mata aji ne? Kaifa Anas daban kake I keep on telling you.”
      “Abdoul kaga magana muke da mazan nan kuma kallon wannan me farin gashin kusa dani amai yake sani so please ka koreta kokuma ku tafi tare.” Cewar Anas batare da ya nuna damuwa ba.

    “Allah…!” Abdoul ya fad’i cike da mamaki wai ace baturiya ma bata burge Anas ba to wace zata burge sa!? Dariya sosai Musty ya fashe da ba k’arya maganan Anas ya sasa dariya. Baturiyar ce ta tsargu danko ba jin yarensu take ba. “Hey Auwal (family name na Musty) whats funny why you laughing?”
    Dariyan yake har yanzu “ohh Emily its nothing don’t worry.” Bayanta Abdoul ya shafa “excuse us babe I’ll be right back.” Kiss ta manna masa a cheek sannan ta tashi ta fice.

     Fuska Anas ya yamutsa a k’yamance yana mamakin Abdoul wai har baturiya yake bari tana masa kiss. “Seka sake fuskarka ai tunda na miji da na miji kaga suna kiss ba.” Cewar Abdoul a little bit pissed off. Murmushi kad’an Anas yayi “LOL mamaki kawai kuke bani, I can’t waste my time on girls. They aiint worth it”

         “Aini Anas da ban sanka ba senace gay ne kai.” Cewar Abdoul “anyways what are you two discussing about da kuka sa na kora Emily.”
       “Labari Anas ke bani” cewar Musty yana jin dad’i. “Ehem ina jinka continue.”

      Komawa yayi ya jinginu jikin kujerar sa yana kallon sama sannan ya cigaba “kace what will I benefit in nayi breaking hearts na mata?” Musty ya giad’a kai dukda ba kallonsa Anas yake ba. “I will benfit everything, zan ramawa Abuu abinda Ummimi ta masa, dukda ba direct kan Ummimin zan d’au revenge d’inba atleast ‘yan uwan ta mata zasuji jiki tunda ciwon ‘ya mace na ‘ya mace ce.”

     Cikin rashin fahimta Abdoul yace, “wait wait nade san waye Abuu mahaifinka ba? what of Ummimi? Wace ita? As far as am concerned Ummie nasani mamanka har kana bamu waya muna gaisawa.”

     Numfashi Anas yaja “well apart from my family you guys are the first people da zan bawa wannan labari so listen closely after na baku labarin seku fad’a min ko inada laifi in nace mata are evil creatures da be kamata a tausaya masu ba.”

      _[Abuu kamar yadda kuka sani mahaifi na ne kanurin Bama ne dake jihar Borno. Ummimi kuwa mahaifiya tace unfortunately, asalin shuwa arab ce daga Maiduguri. Mu uku ne gun iyayenmu nine babba I’m 19 years old, followed by my brother Shettima shikuma he is 17½(sha bakwai da rabi) yanzu. Shekara 1½ (d’aya da rabi) ne tsakanin mu sekuma little sister’nmu my angel Amal she’s just 9 years old.]_

     _[Base on yadda Abuu yabani labari auren soyayya shida Ummimi sukayi. As you guys know scholarship nasamu nazo nan school d’in not like you guys da iyayenku suke biya muku da kansu. Abuu bashida wani arzikin azo agani, yanada arziki ne dadai na rufin asiri a yanzu haka in za’a kira masu arzikin garinmu Bama nasan definately za’a sa Abuu amman dekam bade da kafin sui aure da Ummimi ba. Shi da kansa yake bamu labarin irin rayuwar talaucin da sukayi shida Ummimi kafin a haifemu harkuma da aka haifemu so dayawa ana tashi a gidanmu ba’a sanin me za’a ci.]_

    “You guys must be wondering ya akayi Ummimi shuwa arab da uban san kud’insu ta auri talaka kamar Abuu na ko?” Ya juya ya kalli abokansa. Kai suka giad’a a tare murmushi ya saki kad’an “well you don’t have to.”

    _[Alokacin da Abuu yaje Maiduguri yin diploma ne ya had’u da Ummimi tana sayar da abinci a school nasu a lokacin iyayenta sun kasance talaka sosai amman kunsan shuwa arabs koda su talaka ne se masu kud’i sukeso unlike Ummimi back then, dukda tasan Abuu baida kud’i makaranta yake hakan be hanata falling masa ba kamar yadda shima ya juma da falling mata dan kyan ta dakuma hali, sosai Ummimi kyakkyawa ce kap mu yaranta kamanninta muka dauka sede nafi kama da ita fiye da Shettima da Amal wanda har yau in na tuna da haka se inji kamar inje inyi plastic surgery in canza kamanni na sam banasan abinda ze sa ina tunawa da ita but anytime I look at myself in the mirror ita kawai nake gani…]_

    Musty da Abdoul da suke duhu sukace “ban gane ba” a tare. “Mesa ka tsani mahaifiyarka haka Anas?” Cewar Musty.  “Shin yanzu bata gidanku ne?” Abdoul ya tambaya.

         “Zakaji reason dayasa na tsaneta Musty, bata gidanmu Abdoul Allah kad’ai yasan ko tana nan aduniya ko  lahira.”
     “Babbar magana!” cewar Abdoul “kanada picture’nta inasan ganin ta.” Hannu Anas ya mik’a ya d’aga wallet nasa daga kan wata ‘yar table ya bud’o sannan ya ciro wata hoto “wannan family picture’nmu ne Abuu, Ummimi se nida Shettima time d’in ba m’a haifi Angel ba. Sede bara ku gane fuakarta sosai ba saboda na dirje da biro.” Nan ya mik’a wa Abdoul sosai kam ya dirje fuskar Ummimi a hoton se ansa ido sosai za’a d’an ga kutsirin fuskarta amman ko a hakan ma za’a gano kamanninta da yaranta musamman ma da Anas kamar yadda ya fad’i bayan Abdoul yagama gani ya mik’a wa Musty, shima daya gani yayi returning wa Anas, amsa yayi tare da mayar wa cikin wallet nasa sannan ya cigaba;

  
_[Sun yi shekaru biyu suna soyayya batare da sanin iyayensu ba lokacin da Abuu yagama polythecnic ne ya sanarda da iyayensa kan yasamu mata kuma yanasan ya aura dukda cewar ba aiki yake dashi ba. Kowa murna ya tayasa seda akaji batun Shuwa Arab ze aura ne hankalin kowa ya tashi gudun heartbreak da suke masa dan sunsan for sure in iyayen Ummimi sukayi learning truth about status na Abuu barasu yarda suba d’ansu wa talaka ba sunfi san wanda ze kawo masu gwala gwale yakai su Hajji da umara.]_

       _[As expected da Ummimi tayi introducing Abuu wa iyayenta sam sukace ‘yarsu barta auri talaka ba suka masa kaca-kaca sannan suka koresa. Amman dan erin soyayyan da Ummimi kema Abuu yasa ta bijirewa iyayenta tace ita sam inba Abuu ba zata kashe kanta kuma she was serious duk suka tsorata ba yadda suka iya dolensu suka yarda mata saboda ita kad’ai ce ‘ya a garesu. A munafirce mahaifinta ya tura ‘yan uwansa suka tsare Abuu a hanya suka masa tsinannen dukar mutuwa basu barsa ba sanda suka ga baya numfashi jinyan wata d’aya Abuu yayi kafin ya samu sauk’i alokacin Ummimi ta tada borin inba a aura mata Abuu ba zata fad’a rijiya dole aka musu aure iyayenta wane bak’in ciki ya kashe su]_

     _[Bama ta biyo Abuu aka basu BQ a family house nasu Abuu. Aiki Abuu yashiga nema dan earning living and to make his beautiful wife happy but  kunsan yadda k’asarmu take sam be samu aiki ba haka ya soma noma, safe, rana, yamma, dare. Duk sanda yayi harvesting shuk’ansa once in a year yakan kai maiduguri ya siyar a wannan lokacin ne yake samun kud’i ya ma Ummimi siyayya and duk abinda ya kawo mata tana appreciating. Bayan shekara d’aya da aurensu aka haifeni Abuu yace ni ko ragon suna ba’a min ba sanda nayi wata uku tukuna. Sam basu ji dad’in haifan Shettima da akayi bayan shekara d’aya da rabi da haifa na ba dukda cewar kowani d’a da arzikinsa amman talaucin nasu yayi over. So dayawa ana wayen gari ba’a san me zamuci ba. Mahaifin Abuu ke turo mana abincin dazamu ciki.]_

      _[Daga bayan Shettima kuwa Ummimi bata sake samun ciki ba. Shekarana goma a duniya lokacin Ummimi tasoma staying late at night seta fita tun safe bata dawowa se dare abin ba k’aramin damun Abuu yake ba. Da ya d’anyi bincike kuwa se aka gano wani Alhaji ne daga Yola take had’uwa dashi. Attajiri ne sosai yanada kud’i Abuu yace kullum cikin canza mota yake. Yana ganin Ummimi kuwa ta masa kyau ya fara nemanta ita kuma  saboda cin amana tak’i fad’a masa tanada aure. Soyayya sosai suka fara sam Ummimi tadena kula damu kullum cikin dukan mu take kamar ba yaran cikin data haifa ba.]_

     _[Koba abin duka ba seta bugemu musamman ma a weekends lokacin da wannan Alhajin nata ya koma Yola ba me bata kud’i. Ranar lahadi da sassafe baran tab’a mantawa da wannan rana ba. Da misalin k’arfe 8:00AM Ummimi ta tashi se had’a akwati take sam nida Shettima bamu damu ba acewarmu ko tafiya zamui duka sede naga kayakinta kad’ai take ta had’awa dana tambayeta in zataje kuwa ba kunya ba tsoron Allah ba tausayi ta kalli cikin idanuna tace min *talaucin mahaifinku ya isheni tattara kayakina nake saurayi na zezo ya d’auke ni in tafi inbar nan* atake kaina naji ya soma juyawa wace erin magana Ummimi take dama mata masu aure sunayin saurayi ne? Danni ban tab’a jin malamin islamiyan mu ya fad’a mana ba. Sema na d’au wasa take na shareta mukaje muna ta wasa nida Shettima. Abuu na zaune a Parlour ya tambayeni. Anas Baba na ina mamarku? Ko yau d’inma ta fita ne? A’a Abuu tana d’aki tana shirya kayakinta tace min wai saurayinta ze zo ya d’auketa. Take Abuu ya mik’e what!? Niko na sake nanata masa. Bada dad’ewa ba sega Ummimi tafito tana jan akwatinta.]_

       _[Aysha ina zakije haka?_
     _Aww d’an naka bai fad’a maka bane? Tafiya zan saurayi na na jira na._
    Haba! Aysha wace erin magana kike? Wani erin saurayi kuma? Cewar Abuu]
     _[Ai kasan sa Alhajin Yola, shi nake nufi, rayuwar talaucin nan ya isheni ni tafiya zan inje inji dad’in rayuwa na nima.” For the first time naga idan Abuu yacike da hawaye kafin in hankara naga yana kuka take nima na fara same goes to my brother. Rok’arta na soma haka Shettima ma banda Abuu dayayi mutuwan tsaye.]_

     “Huhhh!!! Nagaji I’ll continue some other day.”
     “Haba! mana maza da Allah k’arasa mana.” Cewar Musty.

    “Nace maku I’ll continue tomorrow or later I promise, baki na yagaji da surutu kunfi kowa sanin ban cika magana ba ai nayi k’ok’ari ko?”

    “Sosai kayi Anas namu me blue shining eyes. Yi hak’uri ka gama mana amma” Abdoul ya fad’i yana masa zak’in bak’i.

    “Okay toh siyo min soda sena cigaba ishi nake ji.” Ba musu Abdoul ya tashi ya siyo masa ya dawo da sauri. “Gashi toh cigaba muna jinka please.” Bayan ya bud’e sodan ya kwankwad’e tas sannan ya cigaba kamar haka;

©miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 10
BY MIEMIEBEE

         “Last words da mukayi exchanging da ita are forever stuck up in my head.”

_[“Ummimi dan Allah karki tafi kiyi hak’uri indan plates dana fasa ne I promise baran sake ba. Ummimi I am sorry dan Allah karki tafi. Abuu ka hana Ummimi tafiya dan Allah kace mata I will be a good boy from now on.”]_  “Haka nata had’ata da Allah ko saurarena batayi ba”

       _[“Yanzu Aysha bara kiji tausayin yaranki ki hak’ura ki zauna dasu ba? Kalli yadda suke kuka fa?”]_ cewar Abuu

    _[“Mstww wannan kuma ku ya shafa nagaji da zama cikin talaucin nan, ace kullum se atashi ba’a san me za’a karya dashi ba gaskia nagaji daman tun farko sanda Abba na yace kar in aureka matsiyaci ne kai amman nak’i sauraronsa. Ga can miji Allah yamin har k’asar waje ze kaini saboda haka ban ga abinda zesa in cigaba da zama a wannan gidan ba.” Jakarta ta ja ta soma tafiya da sauri naje na kama k’afarta ina kuka ina rok’arta. “Ummimi please don’t leave us we love you dan Allah karki tafi, Abuu will find a better job dan Allah karki tafi…” wani wawan ball tayi dani da k’afa nafad’i na ji ciwo a elbow na har d’inki sanda aka min wajen…”]_

        “Kun ga ci won?” Ya mik’o hannunsa ya nuna masu Musty. Ciwo ne babba sosai ace yau shekaru kusan goma amman hakan besa ciwon ya rage girma ba. Komawa yayi yasake kishingid’a.

   _[ko waiwayo wa ta dubani batayi ba jakarta taja ta fice, asibiti Abuu yayi rushing d’ina. Tun daga ranan Abuu ya rasa walwala, Abuu da mukasani da fara’a da murmushi ya koma wani abu daban. Kullum cikin tunani, nida Shettima tun tafiyar Ummimi muka rasa gatanmu, kakarmu bata raye bale ace ita zata kula damu, abinci ma waninsa’in mancewa ake damu haka zamu kwana da yunwa Ummie sister’n Abuu ce data dawo daga Maiduguri tayi alk’awarin zama damu. A lokacin ina primary 5 zamuyi common entrance, ikon Allah ne kawai yasa nayi passing exams d’in saboda tafiyan Ummimi yayi affecting d’ina psychologically, mentally and socially.]_

     _Tun daga lokacin na canza, na dena dariya, nadena wasa koda da Shettima ne kullum cikin tunani nake har wani psysho psycho na soma zama. Ganin haka Kaka yabawa Baba shawara akaini Maiduguri Boarding school a tunaninsa in ina cikin yara zan sake, unfortunately koda aka kaini can abun nawa be ragu ba sede worse da yayi ma, bana cin abinci bana magana da kowa karatu na kawai nakeyi saboda blue eyes d’ina yasa yara dayawa suna san zama friends dani ace warsu ma ni bature ne sam bana basu chance guda biyu ne sukaci galaba a kaina Baana da Kashim, su biyu kawai suka samu na sake dasu muka zama friends.]_

    _[A lokacin da mukayi second term hutu bayan na dawo gida na tarar da Ummie da jaririya kuma a iya sani na Ummie bata da aure. Tambayarta nayi ko ‘yar wace me kama dani haka amsar data bani ne ya mugun sake tada min hankali.]_
      _[“k’anwarka ce Anas, uwar ku d’aya uban ku d’aya. Shekranjiya Ummimi tasa wani almajiri ya turo ta cikin wata basket da wasik’a.” Zafaffun hawaye ne suka soma gangarowa kan kumatu na. “Mesa Ummimi zatayi haka Ummie? Mesa barata tausayawa wa baby’n nan ba? Me tamata itakuma da zata rabata da d’umin jikinta? Mesa Ummimi ta tsane mu haka Ummie?”]

    _[“Anas nima bansani ba hak’uri zakayi, I’m here for you guys, bar kuka Baba na.” “Ina wasik’ar Ummie?”_  Na tambayeta. Acikin wata drawer ta d’auko ta mik’a min na karanta kamar haka…]_

   [_ Ibrahim ‘yar da ke cikin wannan basket, ‘yarka ce da cikinta nabar gidanka. Allah ya taimakeni nasamu na haifeta ga abinka nan na kawo maka, banasan abinda ze sake had’ani da kai ko da ‘ya‘yanka…_]

         [Hawaye ne suka soma sauk’owa kan kumatu na hannu na mik’a na amshi sister na da ko suna Abuu be sa mata ba dan tashin hankali. Hawayen idanuna na d’iga kan fuakarta ta bud’e idanunta a hankali tana kallo na se kamar Ummimi nake gani, Amal na kirata dashi ina hawaye. Daidai lokacin Abuu yashigo. “Amal kasa mata Anas?” Alokacin ban fahimce abinda yake nufi ba sanda na tambayesa yake fad’a mun yak’i sa mata suna ne saboda ni yake jira nayi naming nata tunda nace mata Amal sunan ta Amal kenan. Tun daga ranan na d’au alk’awari zanyi protecting Amal da raina, zan zame mata uwa.]_

        _[Ban tab’a jin inason d’an Adam kamar Amal ba, simply because of tausayin da take bani har yau bata san tanada wata mahaifiya bayan Ummie ba, rok’ar Abuu nayi kar a fad’a mata gaskia banasan rayuwarta ta tab’arb’are kamar yadda nawa yayi. Komai ni nake wa Amal har noma nafarayi tun ina d’an yaro in nayi harvesting se in siya wa Amal kaya da kauan abinci as Abuu har a lokacin be samu aiki ba. Tun tana k’arama take sona ko kuka takeyi ina amsarta zatayi shiru kwana ma tare mukeyi da ita, ko yawo zanje da ita nake zuwa. Sam banso komawa makaranta ba da hutun mu yak’are gudun kar nayi missing nata. Ba yadda na iya haka na koma amman kullum da tunaninta nake kwana in tashi.]_

_[Ina jss 3 aka sa Shettima a school namu, jiki na jasa sosai ko kad’an bana barin school bullies su tab’a sa. Abokai na abokansa ne. Alokacin Abuu ya samu aiki rayuwar mu yasoma canzawa a hankali ya gina mana gida Amal kuwa se girma takeyi a lokacin tana da shekaru biyu da abu akai. Amal completes me, kullum tare muke da ita duk sanda nazo komawa school setayi kuka tace seta bini. Har dan haka nad’au alk’awarin barin sake dawowa gida ba se nagama school d’in gabad’aya bana san ganin kukan Amal. 3 years later nagama secondary school I was 16 years then Shettima kuwa yana ss1 time d’in. I can’t believe Amal dana ganta she was 5 years then, ta girma sosai in na ganta kaina kawai nake tunawa da muguwar Ummimi.]_

     “Tun daga lokacin na cigaba da kula da sister na har ila yau. Ummimi kuwa bamu sake jin labarinta ba tunda ta bar gidanmu yau about 10 years kenan.” Numfashi ya saki tare da tasowa daga kan kujerar ya mik’e tare dayin mik’a “kunji labarina you guys are the first to know. Kunji dalilin dayasa na rasa happiness d’ina, dalilin dayasa na tsani Ummimi da kowace mace banda mata guda ukun nan; Amal, Ummie seda yarinyar danayi blaming nata akan laifin Ummimi har nayi raping nata wanda har yau ban san ya take ba, bansan kona kasheta ba bansan irin ciwon dana ji mata ba. I can’t ever forgive myself for what I did to her har se ranan dana ganta na nemi gafararta ta yafemin. She was just 15”

             “Anas stop blaming yourself, ba’a cikin hankalinka kayi mata abinda ka mata ba in shaa Allah bata mutu ba someday in the future zaku had’u kuma zata yafe maka inhar ka bata labarin ka. Gaskia Anas kasha gwagwarmaya a rayuwarka, kayi witnessing bak’in cikin rayuwa at a very tender age. Ummininku sam bata kyauta muku ba.” Cewar Abdoul cike da tausayawa wa Anas ashe saisa kullum yake cikin tunani baya dariya, he has been through so much ba laifinsa bane because of how he is now.

          “Anas if only zan iya taimaka maka da nayi, you’ve had such a horrible past just know that when ever you need a shoulder to cry on we are here for you.” Musty yayi assuring  nasa.

     Kallonsu Anas yayi tare da ciri sunglasses nasa rana ya haska blue eyes nasa da skin nasa yayi kyau sosai. Murmushi ya saki kad’an wanda ya bayyano da fararen hak’waransa “thank you guys, so now what? Kun ga laifi na saboda nace na tsani mata barin yi aure ba?”

     Kai duk suka kad’a “wallahi ko k’adan Anas you have every single right ka tsani mata fiye da komai sede inda zaka yayyafa wa zuciyarka ruwan sanyi you can find love in your own way I’m sure Allah ze sak’a maku abinda Ummimi ta muku by kawo maku matan da zasu kula daku su soku tsakani da Allah badan kyanku ko kud’inku ba but tsakani da Allah and barasu tab’a barinku ba kai da wanka Shettima se mutuwa.” Cewar Musty. “Sosai dude Musty is absolutely right.” Abdoul ya mara wa Musty baya.

         “Ofcourse you guys are right, but niko kad’an I don’t have faith in love to talk more of marriage, I wish to finish my life single ba senayi aure ba. Dama ai ana aure ne dan a haifafa I have Amal, she is like a daughter to me.” Musty ze sake magana Anas ya katsesa by changing topic of discussion d’in. “Yau da kuka sani na tono past d’ina dole se na sha 2 bottle na syrup d’incan if not barin iya bacci ba and also I

Bayan tafiyan Ya Khaleel bada jimawa ba su Mami suka dawo gida, Fannah na d’aki tana kukan cire rai bata ma ji shigowansu ba kawai ganin Mami tayi tsaye a kanta take ta soma share hawayenta “sannu da zuwa Mami, yaushe kuka dawo?”
          “Habibti kukan me kuma kike? D’an mayen can yazo ne?”

        “A’a ba kuka nake ba Mami, inasu Afrah?”
          “Fannah ga idanunki sunyi ja sun kunbura, fad’a min meneh? Keda waye?”
        “Ya Khaleel ne yazo…” Nan ta irga mata duk abinda yafaru tana kuka.
        Rungumota Mami tayi “Shikenan yi shiru in shaa Allahu Kawu da d’ansa barasu k’arisa da duniya lafiya ba, mugayen mutane kawai bar kuka kinji? Akoi Allah Fannah always have this at the back of your mind, in shaa Allah baraki auri Farouq ba.”

     Hannu tasa ta share hawayenta,    “Mami ni nasan zan auri Farouq ba abinda zamu iya Ya Khaleel yariga ya gama komi.”
      “Fannah kin cire rai daga Allah kenan?” Kad’a kai Fannah tayi “toh ki bar fad’in haka, Allah ba azzalimin bawansa bane. Allah da kansa yace a Qur’ani auren mazinaci se mazinaci aikinsani koh?” Kai Fannah ta giad’a “toh kibar kukan ya iso mik’o mai in taje miki gashinki.” A sanyaye ta mik’e ta d’auko mai da comb mama ta taje mata gashinta takama mata gu d’aya sannan ta bata waje tasa kaya. Itakuwa ta fice zuwa d’akin Baba.

Kwance ta samesa, “Malam ya jikin?”
    Baki na k’yarma yace, “da sauk’i.”
          “Sannu, Malam ko kanada labari d’azu Kawu yazo ya cicci mutuncin Fannah? Duk nazo na sameta se kuka take.”
        “Eh..Mam.. Maman Aiman saisa yazama dole in siyar da gwalagwalen da Umma (mahaifiyarsa) ta tab’a bani dana ajiye kan duk sanda Fannah tazo aure se in sayar mu mata kayan d’aki amman tunda ga yadda abu ya kasance dole mu siyar yanzu…” Tari ya tsaya yayi sannan ya cigaba.
        “K’ark’ashin wancan akwatin akoi d’an kunne da sarqa da zobe dakuma warwaro guda hud’u na gwal, da ace ina da lafiya da a gobe zan jeni Maiduguri in siyar amman gajan haka yasa dole seke zaki Maman Aiman.”

    “Ina jinka Malam, in mun siyar me zamu da kud’in?”

     “Gidan nan zamu bari, garin nan zamu bari gaba d’aya mukoma Maiduguri inason bayan kinje kin siyar da gwala gwalen ki kama mana gida me arha koda 2 bedroom ne kawai wanda zamu iya affording, sekuma da essential abubuwan da zamu iya bu-” tari ne ya tsaida sa sosai.

    “Malam shikenan ya isa nagane kar jikin ka ya tsananta. Amman Malam bara mu tafi da kayakin mu ba? Inaga zefi mana sauk’i inda hali ma gidan nan se mu siyar.”

     Gyaran murya yayi sosai “inaaa… hakan bame yuwu wa bane Maman Aiman mukayi haka ai kamar mun fad’awa duniya zamu bar garin Bama ne kisani no one must know about this. Fannah kawai na yarda ki fad’a mata itanma dan mu cireta daga damuwa ne kuma ki gargad’e ta karta kuskura ta fad’awa Afrah kar da baki taje cikin jama’a ta tona mana asiri. Dan maganan nan na fitowa fili shikenan namu ya k’are dole Fannah zata auri Farouq, ni na fad’a miki.”

        “In shaa Allah Malam, Allah kaimu goben zan wuce Maiduguri dan kasan matsalar samun gida, in bamu soma nema a kan lokaci ba zamu makara har lokaci ya k’ure we have just a month.”

  **

        “Fannah habibti. Fannah!” Kirar Mami dake tsaye daga bakin k’ofa.
    Sanda Fannah takai k’arshen ayan datake karantawa sannan ta amsa “na’am Mami am sorry bansan yanke ayan ne.”
    “Bakomai karatu kike ne?”
    “Eh Mami wani abu ne?”
     “Ina Afrah da Aiman?”
      “Suna can parlour suna assignment.” Fannah ta amsa a takaice.
           “Oh toh magana daman nazo miki.”
         “Toh bismillah Mami” nan Mami ta k’ariso ciki tare da rufo k’ofar tayi joining Fannah kan katifar sanan a hankali ta sanarda Fannah abinda ita da Baba ke da shirin yi. Sosai Fannah taji dad’i harda hawayen nin dad’i.
  
       “Mami dagaske kike? Zamu koma Maiduguri barin auri Ya Farouq ba?”
         “Sosai Habibti ai dama na fad’a miki koda bamuda komai munada Allah, kuma Allah ba azzalimin bawa  bane kamar yadda na fad’a miki gobe zani Maiduguri.”
    “Toh Mami in bi ki mana muje tare.” Cewar Fannah tana share hawayen jin dad’i.

         “A’a Fannah kinsan Kawunki wane bodyguard haka yake kusan kullum seya zo gidan nan inkuma yazo bani ba ke kinsan dole yayi bincike the moment asirin mu ya tonu kuwa kinga dole sekin auri Farouq. Saboda haka ni kad’ai zanje addu’a kawai zakimin Allah sa inje a sa’a in dawo lafiya.”

          “In shaa Allah Mami Allah baki sa’a. Nagode sosai, keda Baba kun gama min komai aduniya Allah biyaku da gidan aljannah.”

         “Ameen Habibti barin koma in had’a akwati na.”
    “Toh muje in tayaki shiryawa.”
       “A’a Habibti zanyi dakaina, go on da karatunki.”
      “Toh Mami.” Har Mami takai bakin k’ofa Fannah ta danna mata kira da   
      “Mami!”
      “Na’am Fannah.” Ajiye Qur’anin dake hannunta tayi ta ruga gun Mami da gudu tayi hugging nata “Jazakumullahu bikhairan keda Baba nagode sosai, Allah sak’a muku da gidan Al-Jannah.”
       “Ameen Habibti Allah miki albarka kema.”   “Ameen” ta ce sannan ta sako Mami tana kallonta har sanda ta shige d’akinsu da Baba. Sujjada tayi tana gode wa Allah sannan tashiga bayi tayi alwala tayi nafila raka’a biyu tare da sake gode wa Allah ji tayi kap matsalolinta sun gushe. Kan katifar su ta fad’a se murmushi take.

**
4 days later…

        “Oyoyo Mami! Oyoyo Mami!” cewar Aiman tana daka tsale. “Oyoyo auta ta” Mami ta d’aga ta sama. Nan su Fannah suma sukazo suka mata oyoyo. Kwanan Mami uku a Maiduguri tadawo, tafiyar ta kuwa was a success kap addu’o’insu Allah ya amsa musu. Kud’in data samu bayan ta sayar da gwala gwalen ta kama musu gidan haya 2 bedroom dashi a unguwar jiddari polo, na shekara, seda katifu guda biyu da d’an kayan abinci da kayan kitchen. Alhamdulillah!

2 weeks later…

      Farouq ne tsaye bakin gidansu Fannah shi a dole yazo ganin matarsa nan da sati d’aya da ‘yan kwanaki zata zama mallakinsa tsabagen iskanci ba abinda yake imagining illa first night nasa da Fannah. Wani almajiri ne yazo wucewa take ya tsaida sa “kai shiga nan kace wai inji Farouq matarsa ta fito.” Da “toh” yaron yashiga gidansu Fannah suna zaune tsakar gida suna tsintar shinkafa ita da Afrah.

    Ita kanta Afrah mamakin yadda Ya Fannah ke walwala kwana biyu ke bata kukan data sobayi safe rana dare yamma duk tadena yanzu, dukda batasan reason nayin hakan ba itade tana ma yarta murnan dawowar farin cikinta.

     “Assalamu Alaikum” cewar almajirin. “Wai inji Farouq wai matarsa tafito” dadai lokacin Mami tafito daga kitchen. “Me kace?”
     “Farouq ne ya aiko ni wae matarsa ta fito.”
    “Dan ubansa kace barata fito ba yaushe tazama matartsa? Fice kabani waje.”
      “Almajiri tsaya” cewar Fannah “kace masa ina fitowa.” Kallo Mami ta watsa mata “Fannah baraki fita ba kinsan wannan d’an mayen yanzu seya saki kuka ki zauna.”
        “A’a Mami kibari inje ai ba abinda ya isa yamin a waje a idan mutane, kiyi hak’uri.” Mami zata sake magana Fannah tace, “please Mami.” Da d’aga kan da Mami tamata Fannah ta shiga ciki ta d’au hijabinta sannan ta fice a zaune ta samesa kan benchi da alama yau ba a buge yake ba.

         “Ke zo nan kizauna yaci ace kin saba dani yanzu, nan da ‘yan kwanaki zaki zama tawa.” A zuci Fannah tace, _taka? never! Allah ya riga ya kare ni daga auren mazinaci kamar ka._ Kawai jin hannun sa tayi kan kumatunta firgit ta matsa baya. Yasake matsowa kusa da ita “wai tunanin me kike haka? Kode tunanin first night namu?” Ya d’an murmusa “karki damu I’ll take it easy on you” batace dashi komai ba illa kallonsa da take.

        “Ke wai yau azumin magana kike ne?” Juyawa tayi zata tafi ya danna mata kira cak ta tsaya bata tanka sa ba. “Kiyi sha’aninki iya san ranki kimin rashin mutunci iya san ranki amman kisani nan da sati d’aya da ‘yan  kwanaki ni zanna ja miki aji. You can go daman nazo inga kyakkywar fuskarki ne kafin na wuce bayan gari.” Kai kawai takad’a tashige ciki.

      Tsaye ta tarar da Afrah da Mami da damuwa karara a fuskarsu. “Ya haka Mami wani abu ne?” Ta tambayesu

         “Farouq fa inade be miki komai ba?” Cewar Mami.
        “Kai Mami da Allah ki kwantar da hankalinki Mami, kema haka Afrah ba abinda Ya Farouq yamin banda suratan banzan daya saba wai yanzu haka ma bayan gari zasa.”
         “Shege mazinaci” cewar Mami. “In shaa Allahu baraki auresa ba.”
        “Amman Mami yau fa sauran sati d’aya da kwana uku ne bikin anya akoi abinda ze hana aukuwan wannan aure?” Afrah ta fad’i cike da damuwa.
       “Akoi Allah Afrah, always have this at the back of your mind. Jeki huta Fannah nida Afrah zamu gama girkin.”
       “Toh Mami, ina Aiman tazo mu mata tsifa.”

     _3 days later…_
   Ana saura sati bikin Fannah da Farouq. Ya Khaleel ne tsaye cikin tsakar gidansu Fannah. Mami, Fannah da Afrah suna tsaye kansa. “Toh nide nafad’i nawa tun ana wata bikin nan na fad’awa Fannah ta sanar dake batun gadon nan gashi har yau baku sai ba wallahi zakusha mamaki dan kuwa amaryarku kan tabarma zata kwana. Wasu erin matsiyata ne ku? Ace ‘yarku zatayi aure ko gado kun kasa yi mata? Wai ahaka ma dan na d’auke maku nauyin kayan kitchen. Allah wadar in erinku wallahi.”

        “Kawu kayi hak’uri nan da ‘yan kwanaki zan kwashe adashe na se in sai wa Fannah gadon dan Allah ka k’ara hak’uri.” Cewar Mami.

         “Wannan kuma ku ya dama, ko ku sai gado ko amaryarku tayi kwanan tabarma. Ni na tafi.”

    Yana ficewa Mami taja hannun Fannah sukayi d’aki gudun kar Afrah ta fahimce wani abun. Itade Afrah tasoma zargin abu da a da ne Kawu yayi wannan magana definately Fannah zatayi kuka sega yau ko nuna damuwa batai ba.

   Da daren ranan Fannah da Afrah suna zaune d’akinsu Aiman tayi nisa a bacci. Afrah tafi minti biyu tana kallon Fannah har sanda tasa ta tsarguwa. “Afrah wannan kalo haka?” Cewar Fannah tana duba pages nawani Government text book.

    “Ya Fannah kallen.” D’ago fararen idanunta tayi wanda suka sha bak’in kwalli ta azasu kan Afrah. “Na kallekin” tace. “Kina b’oye min wani abu kinsan na sanki fiye da yadda nasan kaina I can tell in kina b’oye min bu.” Cewar Afrah

           “Me zan b’oye miki Afrah? Kawai de inajin dad’i ne.”
       “Dad’in me fah? Dad’in zaki aura Ya Farouq??” Ta tambaya tare da d’age gira.
     Dariya kad’an Fannah ta saki “ko kad’an Afrah ina murna ne saboda inaji ajikina barin auri Ya Farouq ba.”

      “Toh Ya Fannah Allah sa, kinsan happiness naki ya fiye min komai a duniya.” Hugging junansu sukayi cike da so da k’aunar juna.

  
**
Ana saura kwana biyu biki… 
Da misalin k’arfe 8:00AM
      “Farouq! Farouq!” Kiran Ya Khaleel yana zaune kan tabarma. “Na’am Baba” Farouq ya amsa yana isowa sannan yasamu waje ya zauna.
         “Ni ya jiya ka had’u da Fannah kuwa? Mahaifiyarta tace mun cikin satin nan zasu kawo gadon gashi saura kwana biyu bikin naku basu aiko ba. Anya mutanen nan lafiya kuwa?”

       “Ni Baba kawai mu share zancen gadon nan kafa san basuda kud’i ni Fannah ta zamo mata ta shine babba ban damu ba ko kan tabarma zamuna kwana bale ma ai ina gado se in tafi mana dashi.”
    K’eyarsa Ya Khaleel ya tand’e “ai dama kai wawa ne, taya mu zamu masu komai tashi muje gidan nasu yanzu.” Ba gardama Farouq yabi bayan Babansa suka fice zuwa gidansu Fannah.

         “Salamu alaikum!” Cewar Ya Khaleel a yayinda Farouq kuma ke knocking shiru kukeji ba amsa “waiko wannan matsiyatan bacci suke ne?” Ya Khaleel ya tambayi Frouq. “Toh ya zansani Baba inba wai shiga zamuyi ba.” Sa kai sukayi a tare Ya Khaleel na sallama sede har da suka iso tsakar gidan ba amsa dan haka Ya Khaleel yayi d’akin Baba yayi knocking nanma shiru hannu kawai yasa ya bud’e k’ofar yaga d’akin wayam! Daga katifa se katifa ba bakunan kaya ba komai. “Tashin hankali!” ya kira a fili. Farouq dake tsaye tsakar gidan yace, “lafiya Baba?”
       “Ba lafiya ba” cewar Ya Khaleel “zo kaga ba kaya a d’akin nan. Tsaya duba d’ayan d’akin yaran tukunnah” nan Farouq yaje ya bud’e same story. “Nan ma ba kaya Baba.”

            “Tashin hankali! Bade Aliyu da iyalansa sun gudu sun bar garin Bama ba.” Y fad’i cike da tashin hanakli. “Amman ai basuda inda zasu ma, through out rayuwarmu anan mukayi, baida ma kud’in biya masu kud’in mota bale ace ya kama masu gida a inda sukaje. Dole suna cikin garin nan suna b’oye cikin wani gida taho muje mu sami kakanka mu irga masa.”

    Bayan sunje sun samu kaka Ya Khaleel ya irga masa komai. Matuk’a Baba yasha mamaki. “Tunda haka d’an uwanka yayi deciding, mu barsa mu ga iya gudun ruwansa. Mun nuna masa halacci ya nuna mana butulci. Ni badan komai na amince da wannan maganar ba dan kar ‘yarsa ta rasa mijin aure ne amman tunda haka yace se mu barsa.”

        “Haba! Baba haka zakace!? Nida na d’au tsine masa zakayi. Guduwa fa yayi Baba ya bijire wa umarnin ka.”
          “A’a Khaleel ba maganan tsinuwa anan fatan mu Allah sa hakan dayayi shine mafi alkhairi garesa da ‘yarsa dakuma iyalansa gaba d’aya.” Ko “amin” d’inma Ya Khaleel be amsa ba shida yagama sa rai Fannah zata haifo masa kyawawan yara ace sun gudu basu gidansu. IMPOSSIBPLE. “Tashi Farouq yau ko shadda suka shiga suka b’uya semun tonosu bayan nagama bazawa a gari zakayi aure se ace amarya ta gudu wallahi k’arya ne tashi nace. Aliyu be isa ba yau duk inda suke a b’oye sena nemo su!” Baba na k’olla masa kira ko a jikinsa yaja hannun Farouq a fusace suka bar gidan.

   *Masu karatu kui hak’uri yau bansamu nayi typing kamar yadda na saba ba, severe back pain ke damuna in shaa Allah gobe zanyi dayawa. I love you guys!*

   *©miemiebee*

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 12
BY MIEMIEBEE

Da misalin k’arfe 7:30AM su Fannah suka isa garin Maiduguri daga can suka tsara taxi se sabon gidansu. Ba laifi gidan gaskia yayi arha d’akuna biyu ne da bayi biyu dakuma  kitchen. Fannah takasa b’oye murnanta, finally barata auri Ya Farouq ba.

     Ya Kaheel da d’ansa Farouq kuwa haka kaman zararru suka riga bin gida one-by-one a Bama su a dole suna neman Fannah da family’nta sam hankalinsa be basa Maiduguri su Fannah suka tafi ba. Har dare suna neman su Fannah ganin ba mahalicci se Allah yasa suka hak’ura suka dawo gida disappointedly.

     Fannah kuwa yanzu rayuwa yasoma mata dad’i, a hankali ita da family’nta suke settling a Maiduguri hankalinsu akwance basuda wata tsoro yanzu, Government school me kyau Mami tasamu aka zuba Afrah da Aiman. Fannah kuwa ko kad’an bata sa rai kan zata cigaba da makaranta ba se sanda Baba yayi suprising nata kud’in daya kamata abiya akaisa asibiti ya yafe kan Fannah tayi proceeding karatun ta. Admisson aka nemo mata a Polythecnic course na Business Administration.

         Sosai taji dad’i. Koda ta soma zuwa makaranta kuwa kullum cikin hijabi da nik’af take, mazan makarantar su basu ma san ya fuskarta take ba bale ace su gano kyawunta su soma binta. Haka Allah ya cigaba da yima rayuwar Fannah albarka, karatu take sosai ba wasa, Mami tana d’an sayarda irin gwanjon kaya hakan nan dashi suke cafanin gida. Baba kam jiki se worse yake ba kud’in kaisa asibiti a kullum burin Fannah ta gama karatu tasamu aiki ta kai Babanta asibiti.

     Ya Khaleel kuwa koda ya kira Mami a waya bata d’aukawa haka yagaji ya bari. Rayuwa de alhamdulillah…

  
★★★★
        4 YEARS LATER…
★★★★

             Abubuwa da dama sun gudana a both rayuwar Fannah da na Anas. Fannah tanada k’imanin shekaru ishirin a duniya yanzu. Kyanta yagama fitowa, hips nata da dukiyar fulaninta daidai jikinta beyi yawaba kuma be kasa ba masha Allah. Fannah takai mace duk inda ake neman mace,  shekarunta kusan biyu da gama poly tayi graduating under Business admin da excllent result. Sede aiki ne har yau babu ta kasa samu, duk wad’anda ake bata ba related to course nata bane daga baya dole ta hak’ura ta karb’a aiki as a waitress (me serving abinci ko drinks a shago kokuwa wajen taron jama’a) a wani babban coffee shop. Dad’in abin Coffee shop d’in nasu sananne ne sosai cikin garin Maiduguri yawancin meetings kokuma party ko biki da akeyi a Maiduguri a Coffee shop nasu Fannah ake zuwa a d’ibi waitresses kuma duk lokacin da akayi haka kud’i suke samu sosai. Da wannan take samu ta biya kud’in school fees na Aiman dana Afrah, amman de yanzu Afrah itama tagama makarantar tana neman kusan shekara da gamawa.

       Fannah na k’ok’ari sosai dan tasa Afrah a makaranta sede abun ya gagara, jarin Mami ya jima da karyewa lokacin da jikin Baba yatab’a yin tsanani dole ta tattara ribanta da uwarkud’in business natan duka aka kaisa asibiti. A takaice de yanzu Fannah ce breadwinner’n family’nta duk akanta sukayi depending. Allah sarki Fannah ‘yar Albarka Allah cigaba da miki albarka, ameen.

       Samari kuwa ba ta kansu take ba, sau afi a k’irga in aka d’ibesu serving food and drinks a meetings alhazai masu ji da naira suka ganta sesun neme ta amman saboda duk sanda ta tuna da past nata, ta tuna bata da  budurcinta martabarta setaji barata iya k’ara yin soyayya ba saboda definately randa aka gano gaskia ita ba budurwa bace za’a guje ta abinda bataso kenan. Bature yace prevention ia better than cure sesa tun farko ma bata sa kanta cikin soyayyar. Daga wanda zata musu k’arya tace takusa aure se wanda zata ce musu tanada aure.

         Zancen mafarki kuwa har yau bata dena ba kusan kullum setayi mafarkin mutumin dayayi raping nata wai ya dawo ze sake raping nata, Mami kullum ke calming nata in tayi mafarkin rananda Mami batta kusa kuwa haka zata riga kuka tana b’ari har wayewan garin Allah, Allah sarki!

       K’arfe 2:00PM…
      Dadai lokacin tashin Fannah daga aiki kenan kafin ta tsari napep ta dawo gida kuma 2:30PM yayi. Tana shigowa gida Aiman dake carafke tsakar gida tasoma mata “Oyoyo Ya Fannah” cewar Aiman dake da shekara 8 kenan baki kam masha Allah. “Oyoyo Aiman” cewar Fannah tare da hugging nata. “Ina sweet d’ina Ya Fannah?”
    “Laaa kinga yau na mance ban siyo miki ba in shaa Allah zan siyo miki gobe, yi hak’uri kinji?”
     “Ai dama haka kike cewa kullum inda saurayin kine ai baraki mance ba.” Cewar Aiman tana guna-guni.
      “Ya SALAM!!!” Fannah ta zaro ido “ban hanaki maGanan saurayi ba? Ni narasa ina kikejin wanga zance.”
    
        “Sekin tambaya ne Ya Fannah?” cewar Afrah data fito daga d’aki “wannan maras kunyan kuma.”
         “Ai wallahi Ya Afrah ko kiyi shiru ko in fad’awa Ya Fannah batun wancan saurayin dayazo wajen ki d’azu da Mami batta gida.”
    Kai Afrah ta dafe “banza! ai kin riga kin fad’a matan kuma wallahi kisani baran sake baki chocolates ba in yakawo min.”
        “Wait wait wait Afrah saurayi kika soma kawo wa gida bada sani na ba?” Cewar Fannah in a serious tone.
       “Ya Afrah fa ba saurayi na bane munafircin wannan munafukan ne, Ibrahim nefa classmate d’ina na secondary school.”
          “Meaning? Afrah bawai zan hanaki yin samari bane kawai becareful karki yarda da maza so easily zasu kaiki ne su baro ki.”
      “In shaa Allah ya Fannah I’m very vigilant.”

6 hours later…
      Mami da su Fannah ne zaune a d’akinsu suna d’an tab’a hira. “Fannah nace wannan karan se ankai har k’ashen wata za’a biyaku?”
         “Eh Mami” ta amsa da fara’arta “wani abu ne?”
        “Fannah Habibti nasan kina mana sosai in ba ke family’n nan would have been dead by now, mungode sosai Allah cigaba da miki bud’i ya miki albarka kuma.”

        “Ameen Mami dan Allah kidena min godiya, you guys deserve all that I’m doing for you. We are family. Kina buk’atan kud’i ne? Kaman nawa?”

        “San samu dubu biyu kinga Maman-”
    Katseta Fannah tayi “a’a Mami ba sekin min bayanin me zakiyi da kud’in ba” nan ta ciro wallet nata ta irga N4000 gashi jiya mun samu ankai mu wani meeting da akayi na commissoners so anbiya mu kud’i. “Nan N4000 gashi zdmiki aiko?”

        “Fannah N2000 ma ya isheni dan Allah ki rik’e sauran kema kinada buk’atunki ai.”
      “Mami dan Allah ki amshi ai ni na baki.” Hannun Mami tabud’e tasa mata kud’in ciki. “Nagode Habibti Allah miki albarka yakuma k’ara bud’i.”
       “Ameen Mami nagode da addu’arki Jazakillahu khairan. Barinyi sallah in kwanta k’arfe bakwai zan fita gobe akoi meeting da za’ayi muzamuje muyi serving abinci can.”
      “Toh ki huta gajiya nima barinje in samu Babanku. Seda safe.” A tare Afrah da Aiman da Fannah duk sukace “Allah bamu alheri” sannan Mami tafice bayan ta amsa da “Ameen karku manta kuyi addu’a”

     Ya Fannah zan d’an samu d’ari biyun kati ne? Cewar Afrah tana b’oye fuskarta.
     ‘Yar murmushi Fannah tayi “saboda kisamu na kiran samari ba”
      “Haba! Dan Allah Ya Fannah wallahi a’a.”
     “Toh Allah kaimu gobe zan baki, kwanan nan bana spending much muku kuyi hak’uri tara kud’in nake ne Afrah inason kai Baba asibiti kinde san ya jikin nasa yake.”
     Kai Afrah ta giad’a alaman tasani sosai. “Mun gode sosai Ya Fannah Allah k’ara bud’i.” Da amsar “Ameen” suka kashe wuta suka kwanta.

   ★★★★ 
ANAS

      Sosai Anas ya k’ara kyau, fari da fresh, shekaru sun k’aru yazama cikakken saurayi yanzu me shekaru ashirin da uki (23) a duniya. Jikinsa muscular yake, packs nasa na nan guda hud’u dadai ba guda shida irin na wrestlers ba. Tsayayyen na miji yake yad’an k’ara kauri kad’an kan sirancinsa wanda yasake fito da kyansa. Sede kam hali na nan na shaye shaye dukda cewar har a yau Abuu da Ummie basu san yanayi ba, duk wanda yaji ance Anas na shaye shaye ma bare yarda ba saboda erin hankalin dayake nuna wa mutane, kominsa a b’oye yake. A da se in yayi mafarkin Ummimi ko na yarinyan dayayi raing yake sha amman banda yanzu, haka kawai in ya rasa abin yi ze kurb’a abinsa. Allah shirya.

    A wannan shekaran yagama makarantarsa na London. Tun tafiyarsa be dawo gida ba sanda ya k’are shekaru biyar d’in cur! Cikin ikon Allah kuwa  yafito da excellent result, school nasu sunyi dashi ya soma musu aiki dan iya zanen Anas as an architecture amman sam yak’i saboda san cika burinsa na karya wa mata zuqatansu, yafisan yayi da matan Nigeria kaman sa ba tsinannun turawa ba. Amal tasa ta girma sosai shekarunta 13 yanzu, ba abinda ya rabata da Anas kyau kawai ya d’ara ta da kad’an. Amal an d’an soma wayo amman har yanzu halin autan ta nanan dakuma rashin kunya da rashin shiri da Shettima. Shettima har yau besan ya girma ba shekarunsa ishirin da d’aya da abu a ka amman hakan be hanasa papiro Fannah da gudu in tamasa rashin kunya. Cat and dog Ummie ke ce musu.

         Anas kuwa saide in bai gida sarai fa yasan Amal ce da laifi amman haka zebata gaskia yabawa Shettima laifi se in sun keb’e yake basa hak’uri. Sosai Anas yaya ne me hankali, yana kula da k’annansa ba kamar da ba kuma yanzu in yana cikin family’nsa yana murmushi da walwala sosai seda Amal ne kawai yake dariyan da har za’a ga fararen hak’waransa tas. Su Baana da Kashim ma suna nan sun bud’e ‘yar sana’a tare and alhamdulilah Allah na sa musu albarka. Shettina kuwa yasa san jiki a gaba, sam bayasan yin abu wa kansa yayi depending da Abuu kawai ‘cause yanzu masha Allah Abuu arziki se bunk’asa yake tunanin komawa Maiduguri ma yake sede har yanzu nothing is certain yet.

     A yanzu haka Anas yana garin Maiduguri yazo neman aiki kwanansa uku kenan yau yakeda shirin fara fita neman aikin, Allah bada sa’a.

     Construction industries yasoma bi sede yawancin su se suce basu d’iban masu aiki yanzu ya dawo bayan wasu ‘yan watanni dukda kyan result nasa kuwa haka ya gama yawo a ranar farko besamu aiki ba. Ranar biyu ma haka ya jera kusan sati yana neman aiki kap babu har yayi giving up kan monday ze koma Bama ze huta yanzu a weekends a gidan chairman daya sauk’a.

      Yana kwance a guest room kan gado Iphone nasa yayi ringing yana kai dubansa yaga “My angel” Amal kenan. Da murmushi kan fuskarsa ya d’auka.
       “My Angel” ya fad’i.
   “Na’am Ya Anas d’ina ina wuni?”
       “Lafiya qalau Angel ya kike ya school?”
      “Lafya qalau Ya Anas, yaushe zaka dawo baka samu aikin bane har yanzu?”
       “Ban samu ba Angel ina kan nema har yanzu amman nakega monday zan dawo. Kinasani cikin addu’a ko Angel?”
         “Sosai Ya Anas yanzu ma dana idar da sallah sanda nasaka ciki”
          “Yawwa My Angel ya Ummie toh?”
   “Lafiyarta qalau. Ya Anas kaga Ya shettima d’azu ya mareni.” Ta fad’i kamar zatayi kuka.
     Yana kishingid’e jin Amal tace Shettima ya bugeta yasa ya zauna tare da zaro blue eyes nasa. “Ya mareki? A dalilin meh?”
       “Wallahi ba abinda na masa Ya Anas kawai fa abokansa ne sukazo yace in gaishesu nikuma nak’i saboda hak’ori na na ciwo shine bayan da suka tafi ya mareni a bayana wajen har yayi pink.”
       Sarai yasan Amal da rashin kunya daga ji ba k’in gaishe da abokan nasa kad’ai tayi ba in aka bibiya halan har zaginsu ma tayi.
      “Toh yi hak’uri Angel yanzu zan kirasa in sissilesa na dawo kuma zan rama miki.”
   “Yawwa Ya Anas ba-bye.” Ding! Ta kashe.

     Komawa yayi ya kwanta tare da zira wa ceiling ido yana murmushi wa kansa daidai lokacin wayarsa tayi k’ara yana kai dubansa yaga number ke kira, zurawa screen d’in ido yayi yana nazarin wacece can yace wannan number Meenor ce. Sanda ya kusa tsinkewa sannan ya d’aga batare da yace komi ba wata murya ce me zak’in gaske ta soma magana a hnakali dukda cewar cikin tashin hankali kuwa take.

     “Haba dan Allah blue eyes, menayi kuma wannan karan? Tun jiya nake ta trying number’nka sarai kana gani ignoring d’ina kawai kake.”

    “Toh nayi, zaki iya yin wani abu ne?” Gatsau ya bata amsa.

     “A’a dan Allah blue eyes kar muyi haka dakai I’m sorry, I love you.”

     “Meenor nomore of that we are done, karki sake kira na please ko kin kira ma barin d’auka ba.” Karap ya katse wayar. Kafin ya ajiye ta soma kira again sa number’n nata yayi a call divert tare da sakar da murmushi hakwaran samansa suka bayyana. “7 of  100 kenan.” ya cize light red lips nasa. Ma’ana cikin mata d’ari daya d’au alwashin ze kariya masu zuciya yaci nasara kan guda 7 wannan ma tun kafin yasamu aiki yazama billonaire kenan!

© miemiebee

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 13
BY MIEMIEBEE

washegari…
      Kasancewar yau Asabar bayan Anas yayi wanka yayi breakfast yayi shirinsa na kullum T shirt da pencil trousers ya feffeshe da turare tare da taje gashin kansa yayi styling nasa me kyau sannan ya rataya jakar laptop nasa da credentials nasa ke ciki. D’an fita ganin gari zeyi tunda Monday ze koma Bama.

      Tafiya yake cikin unguwar Old GRA yana d’an kalle-kalle yadda kowa yake aikin gabansa can yaga mutane sun taru gu d’aya se hayaniya ke tashi wajen, a hankali ya taka izuwa wajen shima dan ganin meke faruwa. Yawancin architects ne awajen seda masu construction kuma zane ne babba a gabansu se musu suke sun rasa gane ya zasu gudanar da aikin. Daga wata gefe kuwa wani dattijo ne zeyi erin shekaru 65 d’innan yayi tagumi ya zuba musu ido sunata shirmeh. Kallo d’aya Anas yayi wa zanen wajen ya gano zanen babban gini ne ko erin company ko industry haka. Daya sake kallo kuwa seya gano matsalar da suka samu wajen zanen murmushi yayi sannan yayi giaran murya “may I interrupt?” yace dasu.

     Tas kowa wajen ya juya yana kallonsa, wasu suna admiring kyansa wasu kuma mamakin blue eyes nasa suke kode bature ne? Amman kuma farin sa bekai na turawa ba toh fah. Na zaunen ne yace “sure please” tare da mik’a ma Anas paper’n. Dattijon kuwa har yanzu na zaune yana kallonsu. Amsar pencil da cleaner Anas yayi yad’an goge wani waje a zanen ya giara daga k’asa sannan yayi haka ma daga sama. Yana gamawa ya juya paper’n yana kallon babban nasu na zaunen bayan ya d’an kalla aikuwa sega abinda suke san sucire d’in yafito, building d’in is in perfect position. “Wow!” Yayi exclaiming “saurayi you are incredible! ku tafawa wa wannan saurayi please.”Nan take duk mutanen wajen suka d’iba da tafi suna hailing Anas.

     Dattijon dake zaunen ne ya taso da karar tafiyarsa irin na gayu me kan gwal d’innan ya iso wajen a hankali. Cikin muryar manyanta yace, “meke faruwa anan?” Babba na zaunen ne ya juya da paper’n yana nuna masa “gashi Mr Muh’d toilet da ake buk’ata a last floor d’in yafita building d’in is in perfect position yanzu.” Kai Mr Muh’d ya giad’a a hankali “good.” yace. Babba na zaunen ya cigaba da cewa “wani saurayi ne anan yanzu ya giara yana zuwa kawai ya amshi papern ya d’anyi goge goge kawai ya fitar he must be a genius. Ina kake ne?” Yana dubawa kuwa se ba Anas har ya juya ya cigaba da tafiyarsa.

         “You two” Mr Muh’d ya nuna yaran aikinsa guda biyu “ku bisa ku kira min shi.” A papare suka yi inda Anas yabi suna gudu suna binsa can suka gansa ya tsaida taxi ze shiga “hey! Hey! Bawan Allah ka tsaya” sam be jisu ba gashi basu san sunan saba. Can d’ayan yace, “me blue eyes!!!” da k’arfi cak Anas ya tsaya ya juya yana kallon inda yajiyo kiran. Bada jimawa ba suka iske sa. Hannu d’ayan ya mik’a masa suka gaisa. “Uhm I’m Kacallah wannan co-worker nane Yunus mune wanda kayi saving building drawing namu yanzu. Thank you”

         “Oh!” Anas yad’anyi murmushi, “that was nothing kar ku damu” ya juya ze shiga taxin. Yunus ya tsaida shi “erm dan Allah d’anyi hak’uri ka tsaya Boss na wajen aikin mu neh CEO’n Flames Enterprises babban company’n dake Maiduguri keson maka magana.”
       Zaro blue eyes nasa yayi “me?” Ya nuna kansa cike da mamaki.
      “Eh” Kacallah yace “you! You did what muka kasayi duka for that yanason ya maka godiya and am very sure zeyi honouring naka saboda Mr Muh’d mutum ne me kirki.”
     “Okay” Anas yace… Har yanzu ji yake kamar a mafarki wai CEO’n Flames Enteeprises keson masa godiya, sosai yasan Enterprise d’in kullum cikin NEWS se anyi maganan enterprise d’in yadda suke successful. Shi koda yake neman aiki ma be lek’a can ba a tunaninsa ma barasu kallesa ba bale su d’auke sa.

     Kacallah ne ya katse masa tunani, “blue eyes baka ce komai ba.”
     D’an murmushi Anas yayi “you can call me Anas, suna na Anas.” Kacallah yace, “wow suna me dad’i but still I prefer blue eyes sorry to ask muslimi ne kai?”
       Kallonsa Anas ya tsaya yi daman ina kama da christians ne? Ya tambayi kansa.
      Ganin Anas be amsa saba yasa ya giara zancen nasa “uhm don’t feel offended please bawai kamin kalan arne bane kawai your eyes…” ya nuna idanun Anas da yatsa “nad’au bature ne kai.”
      Sosai Anas yayi mrmushi, “toh ai ban kaisu fari ba” yace.
          “Eh nasani ko irin black Americans d’innan ne kai.”
         “To ka kwantar da hankalinka ni nan da kake gani na kanuri ne daga Bama dangi na kap ba christian.”
       “Ohhhh!” Kacallah da Yunus suka fad’i a tare suna giad’a kai. “Ikon Allah!” cewar Yunus. “Kanuri amman zallah? Baka had’a dawani yare ba?”
      Toh fa an tab’o gogan namu, ya washi yakira yaren Ummimi amman ya ya iya dasu? dole ya fad’a musu ko zasu bar kallon da suke masa.

          “Mahaif-” se zece mahaifiya ta seya gagara dan koda wasa baisan kiran Ummimi dasunan mahaifiyarsa shi Ummie yasani mamansa ba Ummimi ba. Ganin sun zura masa ido yasa kawai yace, “mahaifiyata shuwa arab ce, mahiafina ne kanurin.”

      “Aihoooo aiko da alama” cewar Kacallah “sesa kake da kyau haka, masha Allah. Toh blue eyes muje Boss namu nasan ganinka.” Sallamar me taxi d’in yayi sannan ya bisu har gaban Mr Muh’d suka kaisa. “Mr Muh’d gashi nan” suna fad’in haka suka ja da baya duk suka bar wajen ya rage daga Anas se Mr Muh’d.
      “morning sir?” Anas ya gaishesa tare da durk’ushewa har k’asa mutumin be amsa ba illa kallon Anas dayake har Anas ya shiga tsoro daga bisani Mr Muh’d yace, “morning boy, get up please.” Nan Anas ya mik’e yana kallon k’asa. “I will first of all like to thank you for saving my men and company in all.”

      Anas na murmushin dole yace, “ba komai Sir, don’t make an issue out of it.” Cike da mamaki Mr. Muh’d ke kallon Anas jin yayi hausa. “Kanajin hausa kenan?” ya tambayesa.
     Mamakin erin tambayan Anas ke wai dagaske aka gansa bara’a d’au yana jin hausa bane? Dole ya sai black lens (k’wayan ido) a kasuwa ya soma sawa.
      “Sosai inaji Sir d’an nan ne ni ai, kanuri nake daga Bama.”
     Sanda idan d’an dattijon ya warwaru. “Kaid’in?” Ya tambaya in disbelief.
      “Eh sir” kafin Mr Muh’d yasake wata maganar Anas yace, “nasan you must be wondering ya nake da blue eyes haka aka haifeni amman d’an nan ne ni kuma muslimi ne ni my name is ANAS IBRAHIM FAUZY.”

     Kai Mr. Muh’d ya giad’a alamam ya yarda. “Toh masha Allah Mr. Fauzy kanada kyau tubarkallah.” Murmushi Anas ya masa “na gode Sir.”
      “Kana kirana da Baba, I once had a son as you.” Sekuma mood nasa ya canza.
      Nan Anas ya gano rasuwa d’an nasa yayi kenan. “I’m sorry Sir.. I mean Baba.”
     “Bakomai Mr. Fauzy. Aeroplane crash ne ya samemu time da zamuje hutu Paris nida d’ana Sultan da matata sekuma da iyayena, bayan jirgin yayi crashing atake duk suka rasu ni kad’ai nayi surviving a family na dukda nima naji ciwo sosai a sanadin haka na rasa k’afata na hagu anyi aiki sosai amman ina yak’i gyaruwa sesa kaga ina tafiya da stick (sanda).”

     Tausayin bawan Allah’n nan Anas yaji ya kamasa, sarai yasan how it feels to be alone, not to have a family shi Ummimi kawai suka rasa amman rayuwarsu ta tab’arb’are bale shi nasa da ya rasa komai. “I’m so sorry Baba Allah ya jik’ansu da rahmah.” “Ameen Mr Fauzy sede ana nema na awani meeting yau gashi har…” Ya d’aga hannunsa ya kalli agogon hannunsa “8:30 yayi.”

        “Ba komai Baba I’ll sit here in jiraka its my honour meeting with you, nasha ganinka a NEWS you’re such a successful man.” Murmushi kad’an Mr. Muh’d yayi “lets go” cike da rashin fahinta Anas yace, “excuse me?”
     “Lets go to the meeting together.”
     Blue eyes nasa ya zaro “Baba thank you for the offer but I’m not invited kar inje a koreni.”
    “Hahaha!” Mr. Muh’d yayi dariyan manya. “Not in kana side d’ina so lets go?”
      Kai Anas ya giad’a masa. Waya Mr. Muh’d yayi bada jimawa ba wata prado 2016 bak’a tasha wanki har kamar mirror jikinta yake ya zo yayi parking a gabansu. Fitowa wani yayi daga gaba ya bud’e k’ofar baya, hannu Mr Muh’d ya nuna wa Anas da nufin ya shiga a sanyaye ya shiga tare da rik’e jakar laptop nasa daya rataya a kafad’arsa kan cinyarsa, bayan shigansa Mr. Muh’d ma yashiga a hankali driver’n yasoma tuk’i.

     Basu tsaya ko inaba se wata babban conference hall tun fitowarsu daga motar mutane suka soma layi jiran su gaisa da Mr. Muh’d. Mamaki ne yacika Anas mutane kamar su cinye Mr. Muh’d wasu kuwa tambaya suke kowaye Anas amsar dayake basu ne yasa Anas shocking wai “he is my son.”

       Wajen VIP aka zaunar da Mr. Muh’d shima Anas yasamu kujera a gefen sabon Babansa (lol). Tambayoyi sosai Mr. Muh’d ya riga yi ma Anas kan ina yayi karatu? Sheraunsa nawa? Tambayoyi de turum. Daga k’arshe ya buk’aci Anas da ya nuna masa CV’nsa dan yagani Allah yaso Anas kullum yana yawo dashi nan ya ciro yamasa presenting.

      **
      “Fannah! Fannah” kirar Boss na wajen aikinsu. “Yes Boss” ta fad’i bayan da ta iso. “Ga can table na VIP Mr Muh’d ne CEO’n Flames Enterprises.” Ido Fannah ta zaro tare da kewayo wa tana kallonsa ba shakka tana ganinsa a NEWS kap Maiduguri ba wanda yakaisa kud’i.   
       “Kinga saboda kinfi sauran ‘yan uwanki fasali yasa ke zanbawa chance d’innan kije kiyi serving nasa drinks dashi da saurayin gefensa dukda cewar yau na soma ganinsa naji ance wai Mr. Muh’d da bakinsa yace d’ansa ne kinga ko sekije kid’an tatso mana su. Kiyi amfani da kyanki ki ja attention na d’an nasan.”

     Fuska Fannah ta d’aure ko juyawa ma takalli saurayin da akace d’an Mr Muh’d d’in batai ba. “Ya Suleiman wai mesa kake magana haka ne? Nikama b’ata min rai nafasa kai musun gasu Asma’u ka kira sukai masu.”
           “Haba Fannah ke bakisan wasa bane? Ai wasa nake miki. Ungo ga plate nasu na shirya yi hak’uri ki kai musu.” Kallo ta watsa masa sannan ta d’aga ta fice. Murmushi yayi haka suke cikin fad’a kullum shida Fannah sarai yasan batada interest cikin samari shikuwa yata neman taokanarta, in aka ajiye wannan agefe kuwa shida Fannah suna shiri sosai tamakar sister’nsa ya d’auketa. Shine d’an me coffee shop na wajen aikin su Fannah’n. Saboda haka duk wani aikin da akeyi shike bada orders.

     Tunda Fannah ta soma tafiya zuwa table na Mr. Muh’d dan kai masu drinks da d’ansa bata d’aga kai ba. Kanta a k’asa tana isa table d’in ta gaishe da Mr. Muh’d da fara’arsa ya amsa sannan ta ajiye mishi cup nasa, ta mik’a hannu ta ajiye wa Anas nasa shima. A yayinda yake answering call ko d’aga ido ya kalli wacece ma beyi ba kawai “thanks” yace. Fannah itama da kanta ke k’asa bata d’aga kai ta kalle sa ba kawai de tasan waya yake. Ta juya zata tafi kenan Mr. Muh’d ya kira ta da “waitress” cak ta juyo “yes sir.”  “Take this away” ya nuna cup na gaban Anas dake kan waya har yanzu ko kallon direction nasu baiyi “ki kawo masa irin nawa”  “okay” tace sannan ta d’aga tana juyawa taga Asma’u sekuwa gashi kan plate nata akoi erin na Mr. Muh’d nan ta d’aga ta aza kan table d’in. “Here you go Sir” tace sannan ta juya zata tafi dakatar da ita yayi sannan ya zira hannu a aljihu ya ciro bundle na d’ari biyar ya mik’a mata. “Gashi ko mungode.”

     Fannah tasha jin ana cewa Mr. Muh’d nada kyauta bata tab’a tabbatar da hakan ba se yau. Amsa tayi hannu bibbiyu ta masa godiya. “Ba komai wannan nakine bawai na baki bane kije ki kai wa boss naki, wancan na zuwa daban. Keep this”
         Murmushi take sosai “Thank you sir! Thank you” nan ta fice daidai lokacin Anas ya katse wayar dayake yi tare da kewayo wa. “Kai da waye ne?”
         “Nida Abuu ne mahaifina.” Ya amsa a takaice.

          “Okay gashi an canzo maka tunda you are allergic to wancan flavour’n.”   “Thank you” yace “gashi ban samu na bata hak’uri ba nasa ta tayi sahu biyu.”
       “Bakomai don’t worry.” Atare suka sa cup nasu a baki suka d’anyi sipping sannan suka mayar suka ajiye. “So Mr Fauzy naga credentials naka you have such an excellent result, I’m ready to offer you a job a Flames Enterprises as my Personal Assistance (PA) akan albashi N500,000 (dubu d’ari biyar) dakuma weekly allowances N5000 (dubu biyar) kowani sati for a start kenan inhar naga ka iya aiki kana kiyayye komai kuma naji dad’in aiki dakai there will be additional salary for you. So? Will you accept my offer?”

     Anas ji yake kamar a mafarki albashi dubu d’ari biyar? “Yes! Yes Baba nagode sosai, in shaa Allah zaka sameni me kiyaye duk wani dokokin da ka kafa min. This is amazing nagode sosai yau sati na a nan Maiduguri ina neman aiki ban samu ba segashi ka bani wanda ban tab’a zaton zan samu irinsa ba I can’t wait in kira Abuu in sanar daahi. Nagode sosai Baba Allah saka da alkhairi.”

     Kallonsa Mr. Muh’d yake yana murmushi he made Anas happy, kawai tunawa yake da d’ansa.

  
     *© miemiebee*
NAGODE LOADS FOR THE WARM CONCERN YOU GUYS HAVE SHOWN ME, I LOVE YOU ALL!
     
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 14
BY MIEMIEBEE

      “Hello Abuu?” Cewar Anas ta waya.
       “Anas Baba na ya kake?”
      “Lafiya Abuu I have a suprise for you”
     “Toh inaji Baba na.”
        “Nasamu aiki!” Anas yayi exclaiming.
     “Ahh toh Alhamdulillah a ina haka?”
     “A Flames Enterprises Abuu, kuma as Personal Assistance na CEO’n wajen.”
      “Wai wai! Kana nufin Alhaji Muh’d Muh’d??” Abuu ya tambaya cike da mamaki.
     “Shi Abuu salary na N500,000 da weekly allowances N5000.”
       “Kai Baba na namaka murna barin fad’awa Ummie se add’ua take ta maka.”
      “A’a bari Abuu I’ll call her dakaina banasan Amal tasan she is not the first person I called to tell.”
     “Uh!” Abuu yayi exclaiming “kai da wannan ‘yar takan.”
     Murmushi Anas yayi “Aikam Abuu ina karb’an first salary na shopping zankai Amal.”
     “Toh Allah maka albarka Anas yacigabada bud’i congratulations.”
    “Thank you Abuu se mun sake magana.”
     “So yanzu zaka shigo Monday d’in still?”
    “Eh zan shigo saboda in d’iba kayakina I have untill next week inyi resuming office.”
    “Okay toh yayi kyau, welldone.” Ahaka sukayi sallama.

      Anas na cikin searching contact na Amal wayarsa ta soma k’ara number ke kira bayan yad’an zura wa number’n ido ya gano Teema ce. Murmushi yayi sannan ya d’aga batare da yace komi ba.

     “Hello angelic blue eyes” cewar budurwar.
    “Yes” ya amsa ba tare da ya nuna damuwa ba.
     “Blue eyes fad’a muke ne? Tun jiya nake expecting call naka shiru.”
    “I have far worth important stuffs to attend to than you Teema.”
    Har tsakiyar kanta ta jiwo wannan zagi amman ta danne zuciyarta. “Blue eyes dama so nake in sani ko you are free zuwa anjima da yamma inason mu fita ne, like a date.”
     “What are you implying Teema? Kina nufin ni bansan abinda yakamata ba se kece zaki bani time da zamu fita date dake?” Ya fad’a a tsawace.
     “Blue eyes please calm down ba abinda nake nufi ba kenan naji kace gobe zaka koma Bama I want to spend some time with you kafin ka tafi.”
     “Huh!” Ya saki numfashi. Tare da jawo kad’an daga cikin gashin kansa yana wasa dashi da wata mirmushin mugunta a fuakarsa. “Nikuma banaso kinsan me Teema? Lets just end it bana sonki anymore lets break up, we are done karki sake kira na ko kin kira barin d’auka ba.”
    “Blue ey-” bata k’are maganar ba ya katse nan take ta sake kira kalan abinda yama Meeno ya mata. 8 of 100 ya murmusa sosai wanda ya mugun k’ara masa kyau.

    Amal nasa ya kira ya fad’a mata yasamu aiki. Tsalle ta riga dakawa haka suka sha hira sannan yace ta kai wa Ummie wayar. Sosai Ummie ta masa. Shettima ne k’arshe ya kira ya fad’a masa aikin daya samu, sosai Shettima uwar san jiki yamasa murna at long last ze soma jin dad’i dan yasan halin Anas be iya rowa ba inba wai dagangan zeyi ba, mutum ne me kyauta amman fa ma wanda yaga dama.

    ★★★★

           Da misalin k’arfe 3:30PM Fannah ta dawo gida da ledoji manya manya hannunta siyayya tama family’nta sosai. Mami, Afrah da Aiman duk suna tsaye tsakar gida hankali tashe a tunaninsu ko wani abu ne yasamu Fannah saboda duk sanda zata wani waje daga gun aiki tana kiran Mami ta sanarda ita wanda yau batayi ba.

     Tana shigowa Mami tayi kanta tare da rungomata “Fannah ina kikaje? You made us worried sick gashi nata kiran wayarki akashe.”
        “Wallahi game natayi seta mutu, kubar tada hankalinku please in shaa Allah ba abinda ze sameni. Kasuwa na wuce nad’an mana siyayya.”
    Nan Afrah da Aiman suka k’ariso tare da karb’an ledojin akan tabarma suka zauna tare da zazzage kayakin.

       Kitchen utensils ne, food items, seda sweets da chocolates dakuma atamfofi guda hud’u masu kyan gaske seda shadda guda biyu, se sauran k’ananun abubuwa irinsu tissue, toothpick da sauransu. “Fannah ina kika samu kud’i haka ko har anbiyaku albashin ne?”

        “Ko kad’an Mami, ina meeting dana fad’a muku za’a kaimu serving d’insu yau?” Mami ta giad’a kai “ashe harda Alhaji Muh’d Muh’d CEO’n Flames Enterprises.”
      “Haba keh!” Cewar Mami.
     “Ya Fannah kap Maiduguri fa ba wanda yakaisa kud’i!” Cewar Afrah.
    “Ya Afrah shine wanda muke gani a NEWS yawancin kullum?” Aiman ta tambayi Afrah. “Eh shi” Afrah ta amsa ta a takaice.
  
         “Toh shida d’ansa sukaje ni akace na kaimusu drinks nasu bayan nakai nakega se d’an nasa yace baya shan flavour’n drink d’in baban nasa ya kirani na canzo masa nazo tafiya kawai Alhj Muh’d d’in ya kirani ya mik’a min bandir na N500 kyauta bayan da aka k’are meeting d’inkuma da muka raba kud’in da aka bamu na tashi da dubu goma albashi na na wata fa kenan ga kuma dubu hamsin. Daga can na wuce kasuwa namana d’an siyayya dududu kayan dubu talatin ne anan.”

      Aiman mathematician har an buga lisafi “sauran miki N30,000 kenan.”
   Kallonta Fannah tayi tana murmushi “welldone ashe surutun nan naki ba’a banza bane tunda kin iya math haka.”
    “Math d’in ‘yan primary three ba” cewar Afrah tana duba zannuwan. Aiman zatayi magana Afrah tace, “Ya Fannah wannan zannuwa fah?”

      “Namu ne biyu na Mami ta zab’a ciki, guda biyu iri d’ayan kuma naki da Aiman.”
       “Haba Ya Fannah mena siya min turmin zani iri d’aya da wannan maras kunyan.”
        “Yo! Ked’inma ance miki inasan yin anko dake ne? Ya Fannah mungode sede har yanzu banga sweet d’ina ba.” Cewar Aiman.

      Nan Fannah ta bud’o jakarta ta ciro packet na sweet “ungo wannan duka naki ne kika rabawa ‘yan ajinku kuma ni ba ruwa na.” Amsa tayi tana tsalle “nagode Ya Fannah ai ko Ya Afrah ma barin bata bale ‘yan ajinmu masu kwad’ayin nan, wallahi Falmatan nan har k’wai na sanda taci ranan” Zani biyu iri d’ayan ta d’au d’aya tashige d’akinsu dashi. “Ke dawo nan waya ce miki ki d’auka?” cewar Afrah jan d’ayan tayi itama ta ruga tabi Aiman cat and dog kenan.
  
        “Fannah Allah miki albarka, Allah k’ara miki bud’i yaci gaba da kare mana ke. Mungode matuk’a da d’awainiyan da kike mana dukda kuwa ba responsibility’nki bane wannan aiki na ne da Babanku amman kinayi. Kiyi hak’uri.”
     Hannun ta Fannah ta rik’e bibbiyu cikin nata “Ameen nagode da addu’arki Mami amman dan Allah kidena min godiya ba godiya tsakani na daku Mami. Na ware dubu ishirin cikin kud’in gobe seki kai Baba asibiti a duba shi ko magani a basa tunda baramu iya affording aikin da za’a masa ba.”

        “Toh Fannah, sannu da k’ok’ari Allah miki albarka.” “Ameen” tace “barin je in samu su Afrah ciki, ki d’au zannuwa biyu anan shaddojin kuma na Baba ne.” “Toh mungode sannu.”

     Fannah na shigowa d’aki tasamu Afrah da Aiman se dambe suka dak’yar ta rabasu zani de gasu iri d’aya amman ahakan ma se anyi fad’a. Bayan ta rabasu ta kori Aiman dawayo in bahaka ba sun hau wasan habaici kenan. Ana kawo wuta ta had’a wayarta a charging. Kayakinta na cikin wardrobe take shiryawa a yayinda Afrah ke kishingid’e kan gado tana game a wayarta. Can ta nisanta sannan takira Fannah. “Ya Fannah!” “Na’am Ya Afrah, mene kuma yanzu?” cewar Fannah tana ninke kayakinta.

       “Kikace d’azu kinga Alhaji Muh’d Muh’d?” Kai Fannah ta giad’a batare da ta kalleta ba. “Okay da d’ansa kuma kikace sukaje wajen?” Afrah ta fad’i kalma d’ai d’ai.
     Barin abinda takeyi tayi ta juyo ta kallon Afrah “what are you implying?”
    D’an dariya Afrah tayi “guilty concious?? Ni bance komi ba kawai cewa nayi kinga d’an Alhj Muh’d?”
     “Nope ni bangansa ba.” Fannah tabata takaicaccen amsa.

     “Wow! Yau me hana mutane k’arya keyi? Hilarious.” Cewar Afrah tana mocking smile.

       “Kuma se akace miki k’arya nake. Allah ban ga d’an nasa ba.”
        “Toh ikon Allah kuma ke fa ke kika kai musu drinks nasu? Kodan had’ewarsa yasa baki gansa ba?”
    “Ke wallahi Afrah suratan banza sun miki yawa. Ni ko zaki samin wuk’a a wuya bansan kalar fatar sa bama bale insan ko kyakkyawa ne ko mumuna. Muryarsa kawai naji.”

      “Haba!” Afrah ta daka tsalle tare da baro inda take ta matso kusa da Fannah. “Ya muryar tasa take Ya Fannah? Fad’amin please kinsan su yaran masu kud’i muryarsu ma daban take.” Shiru Fannah tayi tana nazarin muryar Anas dasuka d’au d’an Alhj Muh’d ne. “Well ba hassada muryarsa nada zak’i irin zak’i ta mazan nan and yana cracking hakan nan. Barin miki bayanin yadda zaki gane kinsan muryar Lancelot nacikin season film Merlin ba?” Kai Afrah ta giad’a sau uku. “Toh haka murayarsa take sede kamar zatafi na wancan d’inma dad’i. Toh kinji, matsa min nacigaba da abin dake gabana.”

      “Iyye! Har kinsa na fara imagining wannan d’an billonaire nasan definately zeyi kyau sesa hakan ma ba’a nuna sa a NEWS gudun kar ‘yan mata su bisa.” Kallo Fannah ta bita dashi “kefa wallahi surutun banzanki sunyi yawa.”

         “Hummm! Afrah taja numfashi “Ya Fannah kenan. Kinsan muryarsa meaning kunyi magana kenan.”
      “Wai meke damunki bamuyi magana ba acewarki yaran da ubansu billonaire suna magana wa mutane anyhow ne? Ko kallona ma beyi ba dana ajiye masa drink d’in kamar yadda nima ban kallesa ba thank you kawai naji yace.”
   “Iyye! Amman daya miki magana fa? Zaki amsa?”
      “Ke qaniyarki, Afrah kika sake maganan wancan saurauyin bake ba kud’in kati se next month.” Tsit Afrah tayi bata kuma cewa komi ba, ahaka Fannah tasamu tagama had’a kayakinta cikin wardrobe.

           _One week later…_
    
           Anas ne tsaye gaban dressing mirror a d’akin da chairman yabasa. Yau ze soma zuwa office he is feeling nervous sosai. Sanye yake da mint blue shirt me long sleeves da cufflinks, seda jean trousers. Simple shiri ne amman yamugun amsar sa he is looking way smart. Jakar laptop nasa ya d’ago yasa laptop d’in ciki da sauran takardu kad’an sannan yasake kallon kansa jikin madubin sannan ya fice bayan ya karya ya wuce office.

       Yana isa gaban building d’in da za’a iya kira da mini sky scrapper ya tsaya. A k’alla floors za suyi 7-8, dogon gini ne sosai wanda jikin bangon yake glass. Building ne babba bakin k’ofar an rubuta FLAMES in caps. Wani button ya danna k’ofar glass d’in ya bud’u yana shiga k’ofar yayi scanning nasa bayan ya tabbatar baya d’auke da makami sannan wata k’ofar ta sake bud’uwa nan ne mutanen cikin ginin suka bayyana. Maza da mata kowa se aikin gabansa yake very organised. Wajen shiru ba hayaniya. Wajen dayaga an rubuta RECEPTION ya k’arisa mace ce tsaye wajen gabanta telephone ne da pack na pencil da biro seda files kuma. Tun kafin ya mata magana tace dashi “Hi” tana washe 32 inta acewarta taga bature.

       “Hello” ya gaisheta back, “erm I want you to direct me to Mr. Muhd’s office, the CEO.”

     “Okay American’s most handsome” tace dashi. “Whats your name?”

     “Anas Ibrahim Fauzy.” Ya amsata a takaice. Baki tasake wangalau wai dama ba bature bane?

   “Excuse me, I mean your name. Name.” dan bata yarda muslimi bane.

   “Yes Anas Ibrahim Fauzy. Ko kema kin d’au Joseph ko Andrew ne sunan nawa? My name is Anas for goodness sake.” ya fad’a a tsawace.

        “I’m sorry blue eyes” ta fad’a tare da kashe masa ido. Tsuka yaja tare da kawar da idanunsa daga kanta.

      “Uhm are you two having an appointment with the CEO yasan da zuwanka?”

    “What nonsense? Da inbe san da zuwa na ba zanzo nan ne? Take me to your CEO” yayi demanding ba alaman dariya a tatare da fuskarsa. “Mesa yawancin kyawawan mutane basuda hali ne?” Cewar receptionist d’in a hankali aikuwa Anas ya jiyota harara ya watsa mata bayan d’an dube-duben da tayi a system dake gabanta tace, “I’m sorry Mr. Fauzy seems like ba sunanka acikin wad’ana zasu ga Mr. Muh’d yau maybe next time.”

           “Kinsan wani abu? Tunda nake a duniya ban tab’a ganin senseless mutum kamar ki ba.” Dadai lokacin elavator ya bud’u Mr. Muh’d ya fito daga ciki. Taku d’ad’ai kamar yadda ya saba yayi yatako zuwa gabansu Anas cike da girmamawa Anas ya gaishesa.

        “Ya Anas me kakeyi baka shigo ba har yanzu? I’ve been waiting for you”
        “Baba wannan receptionist d’ince ta rik’eni wai baran shiga ganinka ba.”
    “No Sir ba hak-”
   Katse ta Mr. Muh’d yayi rai a b’ace “this should be the last time da zaki sake hanasa shigowa nan he is Anas my son, copy that!” ya daka mata tsawa.
   “Yy..yyess sir, my aplologies please.”

     “You apologise to him not me.”
     Kallon Anas take yana mata murmushin mugunta, “Mr. Fauzy I’m sorry.” Harara ya watsa mata sannan yace, “apology accepted.” Nan Mr. Muh’d yaja hannunsa “come lets go in nuna maka office naka.” A floor na k’arshe yakai Anas inda aka rubuta Mr. Fauzy a bakin k’ofar d’akin. Office ne babba da split AC ciki, office kujeru ne manya guda biyu da table d’aya. Akoi telephone da flat screen desktop kan table d’in seda notepad, da pen dakuma pencil pack. Gefe guda kuwa fridge ne seda plasma TV. “This is your office, inda abinda be maka ba let me know se a giara” Godiya sosai Anas ya masa tun daga ranan Anas ya soma aiki.

     He is very punctual, duk meetings da schedule na Mr. Muh’d shi yake maganing kasancewar duk Enterprise d’in ba architecture’n daya kai Anas duk sandq za’ayi zanen project Anas keyi.

  © miemiebee

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 15
BY MIEMIEBEE

★★★★★
    5 months later…

               Shak’uwa ne me k’arfin gaske ya shiga tsakanin Anas da Mr. Muh’d, ladabi da biyayya kam Anas ya iya duk wanda yaji ana cewa Anas na shaye-shaye ze k’aryata zancen. Basu tab’a samin matsala da Mr. Muh’d ba aikinsa duk yanayi me kyau tun da yayi joining enterprise d’in abubuwa suka sake improving fiye da da. Family’n Anas a yanzu haka sun dawo Maiduguri da zama a unguwar New GRA. katafaran gida Abuu ya sai masu da taimakon Anas. Gida ne mansion d’aki kota ina. Rayuwa alhamdulillah yanzu, ansa Amal a Ruby Springfield College. Shettima kuwa ya soma attending UNIMAID a inda yake karanta accounting.

     Anas yayi introducing family’nsa wa Mr. Muh’d sosai suka shak’u da juna. Sanin yadda Anas keson Amal yasa shima Mr. Muh’d yakeson Amal sosai, musamman yadda take sasa dariya duk sanda suke tare in su Anal sunyi hutu kullum tana office wajen Mr. Muh’d datake kira da grampa, wane family haka suka zama. A birthday’n Anas Mr. Muh’d ya basa sabuwar mota pil cikin leather k’irar mercedes-benz SLK. Tunda Anas yayi mota walak’anci ya k’aru ahaka yanzu a list nasa yanada mata 33 da yayi breaking hearts nasu. Leaving life nasa yake to the fullest duk sanda su Baana suka shigo Maiduguri kuwa shan giyan ranan na daban ne. Suna waya sosai da friends nasa Abdoul da Musty.

     Yau ranar ta kasance Monday as usual ya soma shirin office, Shettima da ba lectures se da rana se bacci ake sha. Amal da ba office zata ba amman ta riga Anas tashi tare suka had’a breakfast su biyunsu sukaci bayan sun gama ta rakasa har parking lot yashiga cikin sabuwar motarsa sukayi ba-bye da juna sannan ya fice. As usual yashirya wa Mr. Muh’d schedule nasa na ranan yakai masa. “Welldone Anas, kana k’ok’ari sosai nace zanen project d’incan kasamu kayi kuwa? Kasan mutanen daga Ghana zasu zo yau akoi board meeting da za’ayi by 4:00PM zamu masu presenting.”

      “Eh Baba nayi yana nan ajiye cikin shelf a store room floor 2.”

      “Good, se meeting d’in zanbar care d’in a hannunka. Akoi inda ake samun professional waiters a Fahmaz coffee shop (inda Fannah ke aiki) kayi waya da masu wajen kamana booking.
  
    “Okay Baba, I’ll be going” nan ya zarce office nasa inda ya kira number’n me Fahmaz coffee shop d’in.

    ***
     “Ya Suleiman ga call from Flames Enterprises.” Fannah ta danna kira wa Ya Suleiman dake waje. “Ki d’aga kiji meneh, I’m busy here.” Hannu tasa ta d’aga tare da yin shiru bata ce komai ba. “Hello?” Anas ya fad’i cikin muryarsa me tafiya wa kowace mace da imani. “Hello” Fannah ta fad’i in return. This is Fahmaz Coffee shop, how can I assist you?”

      Jin muryar mace ne yasa ransa ya b’aci take. A fusace yace, “ai nasan Fahmaz Coffee shop d’inne saisa na kira so just shut up plus haka aka koya miki wajen aikin naku in kun d’au waya kuyi shiru?”

         “Lalle ma wannan mutum anyi d’an iska” cewar Fannah a zuci “shi ya kira kuma yana jiran nice in soma yin magana?” Dukda bame san magana bace amman taji barata iya hak’ura ba so take ta sa koma waye ne shi in his rightful position sekuma ta tuna wannan business related matter ne she shouldn’t take it personal.

       “I’m sorry. How can I assist you?”
    “Mstchww” yaja tsuka sannan ya cigaba “we need 5 waitresses and 5 waiters from your coffee shop here at Flames Enterprises by 4:00PM.”

     “Okay copied” tace.
        “Bama tolerating late coming you guys should make sure 4 d’in ya muku anan.”
       “Lalle ma wannan mutumin” cewar Fannah a zuci.

        “Ko baki ji bane?” Zatayi magana ya katse dagangan.  Ciro telephone d’in tayi daga kunnenta tana kallon wayar cike da namaki wannan wani irin bawan Allah ne me uban jijji dakai haka? Mstcw taja tsaki daidai lokacin Asma’u ta shigo “yau Fannah ke tsaki? Keda waye ne haka?” Ta bud’e baki zatayi magana Flames Enterprises d’in yasake kira sanda ya kusan tsinkewa sannan ta d’aga “yes.”

       “Don’t use that tongue with me young lady” cewar Anas in a serious tone daya tsorata Fannah kum tayi shiru. “Incase clueless mind naki be baki idea ba, you have to be here now saboda coffee zakuyi serving ba drinks ba. So zakizo in baki details d’in plus don’t be late bana jiran mutum sede a jirani.” Shiru tayi tana mamakin wannan bawan Allah. “Are you there? Cause bana repaeating kaina twice”

        “Yes I’ll be on my way.” Nan ya katse wayar. Tsuka takuma ja “lallai akoi arrogant people dayawa a duniya what is he feeling like? D’an Adam de ba wanda yafi wani we are all equal.” Asma’u dake kallonta tace, “ji yadda kike magana sekace bakisan Anas ba.”

     Fannah tace, “Anas? Waye shi?”
     Asma’u tace, “no wonder sesa kike tada jijiyoyin wuyanki haka, ni rananda ya kira na d’aga bakiga zagin duniyan daya min ba aike yamiki mutunci ma.”
     “Toh waye shi? Whats he feeling like?”
      “Shine PA’n Mr. Muh’d na Flames Enterprises kuma ance Mr. Muh’d nasan sa tamkar d’an cikin daya haifa, cewa ma yake Anas d’in d’ansa ne.”
     “Ikon Allah! Lallai kam.” cewar Fannah cike da mamaki.
     “You better go kafin yasake kira ya balbale ki.” A sanyaye Fannah ta fice bata tsaya ko inaba se Flames Enterprises can akayi directing nata zuwa office na Anas tsaye take a bakin k’ofar office nasan takasa shiga zuciyarta se bugawa take musamman ma data d’aga kai taga ansa *Mr. Fauzy* asaman. Tafi minti biyu tsaye a wajen sannan jiki na k’yarma hannu na b’ari tayi knocking k’walli d’aya tal jin ba’a amsa ba yasa ta k’ara d’aya “come in” taji muryan na miji ya fad’i authoritatively. Tabbas tasan wannan murya shine wanda yace mata thank you rananda Mr. Muh’d ya bata bandir na N500 kawai haka taji zuciyarta na bugawa tarasa dalili.

BY MIEMIEBEE
*ASSALAMU ALAIKUM MASU KARATU, INASON INYI AMFANI DA WANNAN DAMA IN FAHIMTAR DA MASU K’ORAFI KAN LITTAFI NA, NACEWA INA YAWAN SA TURANCI CIKI. RIGHT FROM THE START NASO DAMA IN YI MAKING IT CLEAR KAN ZA KUNA YAWAITA GANIN TURANCI CIKIN LITTAFIN NAN AMMAN KUMA SENA FASA. GANIN ANASON A MAIDA ABIN SUBJECT OF DISCUSSION YAZAMA DOLE INYI MAKING IT CLEAR YANZU. IN KUKA LURA BAWAI NA K’WARE A HAUSAN BANE, KOYO NAKE HAR YANZU, BA BAHAUSHIYA CE NIBA ‘YAR MAIDUGURI CENI, YOU GUYS KNOW RIGHT ‘YAN MAIDUGURI BA’A SASU CIKIN JERIN HAUSAWA. INDA NA K’WARAI A HAUSAN AI BARIN NA SIRKAWA DA TURANCI BA. KUGANE PLEASE KUNA MIN UZURI. MOREOVER, A CHAPTER’N BAYA CHAPTER 15 KENAN, NAGA SHINE NASA TURANCI SOSAI SABODA A OFFICE SUKE, SANIN KANKU NE MASU K’ORAFI BA’A CIKA YIN HAUSA A OFFICE BA, ENGLISH UNIVERSAL LANGUAGE AKE SPEAKING. INA FATAN DAGA YAU MUNYI SOLVING WANNAN ISSUE. THANK YOU SO MUCH, I LOVE YOU GUYS HAVE FUN READING!!!*
   
         Ba tare da ya kalleta ko yace da ita komi ba yacigaba da abinda yakeyi cikin laptop dake gabansa. Tafi minti biyu tsaye sannan ya ciro wata paper daga drawer ya ajiye kan table d’in. “Here is the coffee description, sugar should be minimum.” K’arisowa tayi ta d’aga paper’n lallai ma d’an wannan order’n ne bare irga min ta waya ba seya sa nazo all the way here.
 
           “Sir is that all? Naga ai irin wannan orders muna d’aukawa ta waya.”
           Ba tare da ya kalleta ba daka tsawa “just shut up and leave please!” Har tsakiyar kanta tajiyo wannan tsawa rabuwanta da a daka mata tsawa haka tun barinsu Bama. Take tajiyo hawaye na ciko wa idanta daman ita ba me daure masifa bane, batare da tace komi ba tajuya ta kama tafiya tana share hawayenta nan ne ya d’ago kai yana kallon bayanta har ta bud’e k’ofar ta fice.
       Da misalin k’arfe 3:50PM su Fannah suka iso conference hall d’in komai is in place. 4 on the dot su Anas suka hallaro hall d’in. Fannah na ganin sun shigo ta fice ko sa Anas a ido batai ba, bata masan wani kalan kaya yake sake da ba, se sanda za su soma serving coffee’n ne ta dawo kanta a k’asa take tafiya dan karta jawo attention, haka table by table take bi tana ajiye coffee’n. Table nasu Anas takai k’arshe a hankali ta d’aga kai dan sasa a ido saidai ba direction nata yake kallo ba ya juya yana magana da d’aya daga cikin mutanen kan table nasun. K’eyarsa kawai tagani yadda yayi styling gashin kansa me tsawo wane na bature.
    Bayan ta gama ajiye musu tajuya zata tafi kenan taji familiar voice ya kirata da “waitress” gam ta rufe idanta a hankali ta juya “yes sir” lokacin kuma Anas ya juya yana magana da wasu, k’arisawa tayi ta tsaya daga gefensa “yes sir!” Ba tare da ya kalleta ba yace, “take this away I don’t take coffee.” Kallo ta k’are masa sannan ta d’aga ta fice. Mamaki ne yacika ta wai waye wannan Anas ne ko me sunan san yake feeling like.
      Bayan taron ya watse suka raba kud’in da suka samu sannan ta dawo gida d’aki ta wuce direct. Afrah tasamu se faman chatting take bayan ta mata sannu dazuwa seta karinci kamar wani abu na damun Fannah. “Ya Fannah lafiya?”
          “Wani irin lafiya? wallahi wannan d’an Alhj Muh’d d’in ji da kai ya masa yawa. Bakiji yadda yake ma mutum magana ba ke ko kallon mutum ba yayi.”
      “Kina nufin Anas Ibrahim Fauzi?” Cewar Afrah.
      “Eh wai haka naji sunan nasa amman ya akayi kika sani?”
       “Yanzun nan aka nuna sa a NEWS nake gama meeting d’inda kuka jen ne. Yasa black suit da white shirt da black necktie ko?” Cike da mamaki Fannah ke kallon Afrah. “Eh haka” ta amsa ta.
      “Ya Fannah baki ga kyansa ba wallahi kamar bature.”
     “Toh ai kyansa be amfana sa ba tunda baida hali me kyau.”
      “Ya Fannah waya keta hali? Ke bakiga fuskarsa bane?”
         “Bangani ba kuma bansan gani, ni mubar maganarsa ma he is so arrogant. Barinje inyi wanki kafin Maghrib yayi.”
      Wankin ta takeyi hankalinta kwance tajiyo kiran Afrah daga d’akinsu Baba. “Ya Fannah! Ya Fannah! kizo da sauri.” Nan ta bar abinda take ta ruga a guje ciki acewarta kowani abu ne yasami Afrar dan su Mami basu gida takai Baba asibiti Aiman ta rakata. “Afrah lafiya?” Ta bankad’o labulen d’akin zaune tasamu Afrah gaban TV “Ya Fannah gashi nan! Anas d’in” kafin  Fannah ta kai dubanta kan TV’n har ya juya sede taga kamar ta ga fuskarsa kamar kuma bata gani ba. “Mstw tun d’azu nake kirar ki gashi ai har ya kau da kansa”
       “Yanzu Afrah fisabilillahi akan ganin wannan Anas d’in kika kirani all the way here nafa d’au ko wani abu ne ya same-”
      Bata k’are maganar ba Afrah da hankali ke kan TV tasomsa sabon ihun “gashi nan! gas-” karap NEPA suka d’auke wuta. “Oh damn it! NEPA bakuyi ba.” Tsuka Fannah taja sannan ta koma ta cigaba da aikin dake gabanta.
     
      Wattani da dama sun shud’e…
         Rayuwa ta cigaba da kasance wa Fannah daidai ba abinda ya sake had’ata da Anas. Tana zuwa gun aikinta kullum. Baba kuwa magunan da aka basa a asibiti cikin ikon Allah yana samun sauk’i sosai. Tsoron Fannah d’aya ne rananda magunan zasu k’are bata san ina zata samu kud’i asake sai masa ba. Kullum cikin add’ua take.
   
      Ta b’angaren Anas kuwa abu sunan yadda suke shaye shaye dakuma breaking up da ‘yan mata kullum yana kan yi. Saidai ba kamar da ba, d’an watannin baya da suka wuce sam yadena mafarke mafarken daya saba na Ummimi da kuma yarinyar dayayi raping but kwanan nan sede be kwanta ba seyayi mafarkin yarinyan dayayi raping d’in wai ta dawo garesa. Syrup nasa yake kwankwad’a bayan kwana biyu yasake tashi da mafarkin ji yake yarinyan is somewhere close to him. To kode tana d’aya daga cikin ‘yan matan daya tab’a breaking up dasu ne? Kai! A’a da k’yar ai ita wancan a Bama take. To ina take??
      Shettima dake tsaye a kansa ne yayi ihu dagangan dan tsoratar dashi. “OMG!” cewar Anas da hannu dafe kan k’irjinsa. “K’aniyanka kasan yadda kaban tsoro kuwa!” har yanzu nishinsa be dawo dadai ba. Dariya sosai Shettima ke “hahaha! Kaga fuskarka kuwa? Anyways tunanin me kake har na shigo d’akinka baka sani ba.”
         “Kajima anan ne?” Anas ya tambaya yana k’ok’arin daidaita numfashinsa.
    “Yup about 2 minutes ago” cewar Shettima.
    “Babu, ba tunanin da nakeyi.”
     “Oh common! Ya Anas kama dena min k’arya kasan ko lokacin da ka b’oye min lamarin abinda kama wancan yarinyar a Bama nagane so just tell me what is it now?”
      Tasowa yayi ya zauna, shima Shettiman ya zauna kusa da wansa “tell me ina jinka.”
    Nishi Anas yaja “kasan wani abu ne? Its been long banyi mafarkin wannan yarinya ba but yanzu anytime na kwanta tunanin ta kawai nake ji nake kamar _TANA TARE DA NI_ I don’t know whats wrong kullum cikin tunaninta nake Shettima I can feel it yarinyar bata mutu ba.”
      “Toh fahhhh” cewar Shettima dan ko besan me zaice ma wansa ba he is speechless.
    “Fad’a min Shettima what are you thinking?”
        “Well, Anas maganar gaskia bansan me zan ce maka ba. Yarinyar nan fa a Bama take theres no way zata dawo Maiduguri kuma kai da bakinka kace she was 15 time da abin yafaru who knows ko bata rayu bama an-”
   
        Katse sa Anas yayi “No Shettima I can feel it, bata mutu ba” hannu yasa cikin gashinsa “I don’t know what to think anymore, inasan ganin yarinyar in nemi gafararta Shettima.”
     Kafad’arsa Shettima ya dafa “komai will turn out perfect karka damu, wayasani ko ta kasance d’aya daga cikin ‘yan matan da kake wasa dasu. Saboda baka san fuskarta ba.”
        “But I’m sure ita tasan nawa ai, in ta ganni zata gane ni tunda ita ba’a buge take ba time d’in.”
 
          “Tsab ko zata iya mancewa da fuskarka Ya Anas, katuna da dare ne ranan kuma ruwa akeyi, in har ta rikice beyond imagination alokacin sosai tsab zata mance da kaman ninka. Allah desa bata kasance d’aya daga cikinsu ba.”  “Ameen” Anas yace sannan ya koma ya kwanta tare da zura wa ceiling ido. Wayarsa ya soma k’ara yana kai dubansa yaga family doctor’nsu ne, ba tare da b’ata lokaci ba ya d’aga “Hello Dr Mansur?”
     “Hello Anas kabar duk abinda kakeyi  kazo gidan Babanka yanzu.” ya fad’i cike da tashin hankali sannan karap ya katse wayar.
     “Hello..? Hello…?”
   Zabura yayi yajawo jacket nasa yasa tare da d’auko key’n motarsa ya fice a 360. Bayan ‘yan mintuna ya iso gidan Mr. Muh’d. Sama ya haura direct zuwa d’akin Mr. Muh’d can yasamu Dr Mansur tsaye a bakin k’ofar. “Dr Mansur whats wrong? Meya samu Baba?”
       “Anas is about time kasan gaskiya Babanka yata b’oye ma gaskia saboda bayasan ya saka cikin tashin hankali amman yanzu da lokaci yariga ya k’ure I have to tell you.”
    Take idanun Anas ya cike da hawaye “meke faruwa Dr. Mansur? Meya samu Baba?” ya tambaya murya na rawa.
     “Anas calm down tunba yau ba Baba ke suffering da cutar cancer.”
      “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” Anas ya saki salati. “No thats not true please karka ce haka Baba baida cancer.” Kuka yasoma yi sosai.
      “Anas thats why nace maka you need to calm down yanzu ba lokacin musu ko kuka bane addu’a zaka masa. Kasan shi matsalar cancer ba’a cika discovering na sa da wuri ba bale ayi maganinsa saboda bai da symptoms cin jiki yake sosai the moment ya kama mutum. Haka yasamu Baba ma, yau shekara kenan yana fama da cutar a iya sani na kenan. Duk sanda kaji Baba yace maka zeyi tafiya to ciwon nasa ne yatashi.”
     “Dr Mansur niba wannan ba dan Allah” yasa hannu ya share hawayensa. “Do something to save him please.”
    “I’m so sorry Anas but its too late, saisa nace maka addu’a zamu masa yanzu lokackin Baba yayi, be a man please, kai kad’ai Mr. Muh’d keda bayida wani family bayan kai, you have to be strong.”
       Inaaa Anas se kuka sun shak’u da Baba sosai wane Abuu. Kuka yake sosai Dr. Mansur na basa hak’uri ganin ba mahillici se Allah yasa ya share hawayen sa a hankali ya bud’e k’ofar d’akin Mr. Muh’d. Kwance yagansa rai a hanun Allah wani kukan yasake faso masa jiki a sanyaye ya k’arisa gaban gadon nasa ya tsuguna tare da rik’o hannunsa yana kuka.
          “Baba dan Allah kar ka tafi kabarni, kar ka tafi kabar Enterprise naka we need you.” Magana ciki ciki Baba yace, “shhh Anas, bar kuka ni zan tafi amman na bar musu kai. Kai na mallakawa Enterprise d’ina da duk wani abinda na mallaka”
      “Noo… Nooo please Baba” Anas ya katse sa.
      Baba yacigaba “na riga nayi signing komai under your name Anas, kamar yadda nasan ka da hankali da hardworking ka cigaba da kula da Enterprise d’in koda a bayan raina, naka ne yanzu banida ikon in fad’a maka abinda zakayi dashi, just do what is right. Ban samu naga su Abuu da Amal ba tell them am sorry.”
      “Baba please kabar magana haka in shaa Allah zaka tashi baraka mutu ba please.”
      Wani irin numfashi Baba yasoma yi da k’arfin gaske.
      Gamgam Anas ya rik’e hannunsa yana ihu “No! No! Baba dan Allah karka tafi Dr. Mansur! Dr. Mansur!” a guje Dr. Mansur ya shigo saidai shima ba abinda ze iya tsayawa yayi daga gefe d’aya yana kallon yadda Baba ke nishi. “Dr. Mansur do something to save him please karka bari ya mutu.”
        “Anas I’m so sorry amman ba abinda zan iya masa, lokacinsa ne yayi.”
      “La ila ha illallah muhammadur-rasulillah salla-” be k’are ba numfashinsa ya yanke kap. Ihu Anas ya k’urma “Noooooo! Baba you can’t die please” hugging Baba yayi yana kuka yana jijjik’asa Dr. Mansur ne yazo yana k’ok’arin d’aga sa daga jikin gawan Baba amman ya kasa haka ya zuba wa Anas yana kukan cire rai yana basa hak’uri. Sun musan minti talatin sannan Anas ya tashi a garin yin haka wayarsa ta fad’i kasa “Ina zakaje Anas?” Cewar Dr. Mansur.
    Idanunsa sunyi jazir wane barkono blue eyes nasa sun k’ara shiga. Batare da ya kalle sa koya ce dashi komi ba yafice be tsaya ko inaba se bar (gidan giya) inda yaje ya bugun buguwa. He can’t take it mesa Baba ze mutu ya barsa?
      Wayarsa Dr. Mansur ya d’aga ya kira Abuu ya sanar dashi halin da ake ciki salati kawai kukeji. Bayan ya ajiye wayar ya rufe gawan Baba sannan ya fito a ranan aka ma Baba wanka aka sallace sa aka bisine sa. Kuka sosai kowa yake, ‘yan Maiduguri sun mugun jin mtuwan Mr. Muh’d. NEWS na ranan kap Mr. Muh’d aka yini ana nunawa.
     Ba inda ba’a nemi Anas ba an rasa ina yashiga se Allah, gashi wayar sa bata gunsa. Ranar de ta kasance a very bad day wa mutanen Maiduguri all in all.
     Se washegari da safe Anas ya dawo gida Allah yaso daya dawo Abuu da Ummie basu nan Shettima kad’ai a gida shi ya kula da Anas. Sosai Anas ya bugu ko d’aga k’afa bai iyawa Allah kad’ai yasan ya yadawo gida lafiya. Bayan Shettima ya tayasa rage kayan jikinsa ya kwantar dashi tare da rufe sa da bargo. Bacci sosai Anas yayi se shabiyun rana ya tashi. Shettima yagani zaune a gefensa yana karatu.
     Kansa ya rik’e yana k’ok’arin zama. Nan ne Shettima ya jiyo ya kallesa cike da tausayi. “How are you feeling Ya Anas?”
       Kallonsa kawai yayi ba tare da ya amsa sa ba.
     “Ya Anas hak’uri zakayi Baba lokaci yayi, zuwa gidan giya ka bugu is not a solution. Ba abinda ze amfanar da Baba kamar yadda bare amfanar dakai ba kaima. Addu’a ya kamata ka masa.”
 
         “No Shettima bara ka gane ba, baraka tab’a ganewa ba. Why is my life always like this? Se lokacin dana soma jin dad’i Baba ze tafi ya barni da burden na Enterprise nasa. Baran iya ba Shettima I can’t manage his company.” A hankali ya soma kuka kamar d’an yaro.
 
    © miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 17
BY MIEMIEBEE
 
      “Oh common please Ya Anas, kowa yasan how you must be feeling, hak’uri zakayi ka d’au wannan ma wata k’addara ce.” Cewar Shettima yana shafa bayan Anas dake kuka. Daidai lokacin su Abuu da Ummie da Amal suka shigo kan gadon Anas Amal tayi. Ganin wanta na kuka itama tuni ta fara “Ya Anas bar kuka kaji? In shaa Allah Baba is in a better place yanzu.” Rungumosa tayi yana kuka ajikinta kamar d’an yaro.
          “Anas hak’uri zakayi, munsan yadda kaji mutuwan Alhj Muh’d amman yazama dole kayi tawakalli ga Allah kayi masa addu’a lokaci ne yayi. Yabar duk wani prperty’nsa maka inda hali zuwa anjima ‘yan jaridu sunasan magana dakai dangane da faruwar wannan abu.”
       “Noo Abuu please, ni baran iya kula da enterprise na Baba ba baran iya ba, kabawa ‘yan press hak’uri baran samu zuwa ba. Ni Enterprise nasan ma baran iya handling ba, I can’t.” Ya sake fashewa da kuka.
     Ummie ce ta k’ariso ta karb’esa a hannun Amal, “yes you can Anas, zaka iya. Babanka bare ji dad’i ba inda ze dawo yanzu yaji abinda kake cewa, ya bar maka company’nsa ne saboda ya yarda da kai da abilities naka, he is sure zaka iya cigaba da gudanar da lafiyar conpany’n saisa yabaka karka basa kunya Baba na. Kayi hak’uri kukan nan baida amfani gacan abinci na had’aka maka kaci kaje mutanen suna jiranka a TV station ko muce suzo ne?.”
     Kai ya kad’a yana kuka sosai. Bayi ya fad’a dan yin wanka amman wankan ma yakasa damuwa sun masa yawa shower kawai ya kunna ruwan nata zuba kansa kusan na minti ishirin sannan yafito yasa kaya yafice zuwa dining inda Amal ke zaune tana jiransa itama idanun nata sun kumbura sunyi ja. Serving nasu abincin tayi kamar yadda suka saba a plate d’aya sukeci. Sede ko kad’an yau Anas baici. “Ya Anas kayi hak’uri dan Allah kaci, karka zauna da yunwa.” cewar Anas.
        Hawaye taga na cikowa idanunsa, hannu tasa ta tare “Ya Anas kasan baran iya jure kukan kaba please kayi hak’uri.” Be iya yace mata komi ba hannu kawai ya aza kanta tare da mata murmushin dole sannan ya kai spoon d’aya baki bayasan jin Amal na had’asa da Allah kwata kwata spoon biyar yayi yace mata ya k’oshi. Yabari su Abuu su raka TV station d’inma yak’i yana isa wajen ‘yan press tunda ga waje suka soma binsa har sanda ya shiga ciki.
    Bayan an basa kujera ya zauna suka soka jero masa tambayoyi wanda kad’an daga ciki ya amsa sauran kuwa kuka suka sa sa haka fa kamar d’an yaro Anas ya bud’e dandalin kuka a TV station su kuwa se recording suke direct ana uploading a news Nigeria’s most youngest billonaire.
      Ba’a gama interview d’in bama yatashi yafice dan yadda kuka yafi k’arfin sa. He wanted to be strong amman ina bare iya ba, besan dawani damuwa ze fara handling ba, na Ummimi ne ko kuwa na ‘yar dayayi raping ko na mutuwan Baba kokuwa na managing babban enterprise da Baba ya bar masa. Yakasa tunani giya kawai ne in yasha ze warkar masa da wannan damuwa gidan giyan ya koma ya sake buguwa sannan yafito ya kwanta cikin motarsa har bacci me nauyin gaske ya iske sa.
    ****
        “Ya Fannah yi sauri kizo kiga abin tausayi, hurry!” Afrah ta danna wa Fannah dake kitchen kira. Wanke hannu tayi tafito da wuri.
      “Kiga yadda d’an Alhj Muh’d ke kuka, Allah sarki.” cewar Afrah. Fannah na kai dubanta kan TV’n taga Anas zaune kan kujera da hanky rik’e a hannayensa biyu ya rufe fuskar sa dashi se kuka yakeyi kamar d’an yaro se kace besan da camera kota ina a gaban sa ba. “Allah sarki!” tace “Allah jik’an Alhj Muh’d, yasa k’arshen wahalarsa kenan.”
     “Ameen” Afrah dake jin kamar tayi joining Anas suyi kukan tare. “Kinsan kuma me worse part d’in? Fannah ta kad’a kai. Akace a idan Anas d’in Baban nasa ya rasu, yana ji yana gani mutuwa ta musu katanga, Allah sarki!”
     Tausayi Fannah taji yabata jibi yadda yake kuka sekace bashine mara mutunci me gasa wa mutane magana ba, sekace ba shine me uban jijji dakai ba Allah sarki rashi. Dan yadda Anas ke kuka yasa ta fito daga d’akin ko fuskarsa yakasa bari agani tasan sarai ta k’ara minti d’aya a d’akin kuka zata soma dan hawaye bai bata wuya ga kuma uban tausayi…
        Haka fa tun daga ranan rayuwar Anas ya lalace yafi na da worse ba aikinsa se shaye shaye barin gida ma gabad’aya yayi ya kama hotel yadda yake shaye shayensa hankalinsa kwance.
       Safe, rana, yamma, dare Anas na rik’e da bottle na giya a hannu yana sha. Da rasuwan Baba yau sati biyu kenan amman Anas ji yake kamar yau yau d’innan Baba ya rasu sau kusan kullum yake kai ziyara gidan Baba, masu aiki ya nemo dasuna kula da gidan, a rana se anyi shara da mopping sau biyu wane akoi mutum ciki. Tun rasuwar Baba kuwa ya rufe company’n har yau ba’a bud’e ba masu aiki a wajen ba yadda basuyi dashi ba ya bud’e su koma aiki amman yak’i shi a tunaninsa bare iya handling ba bayasan ya b’atawa Baba koda k’wayan zarra ne cikin company’nsa. Allah kad’ai yasan wahalar dayasha kafin yasamu ya gina wannan sky scrapper saboda haka yake jin tsoro sosai kar yayi wani abu yayi ruining abu ciki.
Kusan sati uku ake nema yau Anas yak’i bud’e company ga on going projects dayawa nan barkate. Daga k’arshe sanda ‘yan manya manyan wajen suka je suka ma Abuu bayanin komai sannan ya ce musu zema Anas d’in magana. Bayan tafiyar mutanen, Ummie dake taya Amal tsifa tace, “Ya Ibrahim wallahi Anas tausayi yake ban, ba laifinsa bane yaro yake har yanzu dudu shekarunsa 24 nefa, he is still young.”
    “Saisa yakamata ya bud’e office  d’in, yayi hak’uri ya rungumi k’addara k’in bud’e company’nsa ba taimakasa masa zaiba kin deji abinda masu aikin nasa sukace akoi on going projects dayawa  kuma koba dan wannan bama yau ace Alhj Muh’d na raye ai bareyi farin ciki da abinda Anas keyi ba. Kowa ya tausaya masa shiima yayi hak’uri ya tausaya wa kansa.” Shiru Ummie tayi ta giad’a kai. Amal kuwa idanta tuni suka cike da hawaye rabuwanta da sa Ya Anas a ido har tamanta tun da yabar gidan kota kirasa wani sa’in ma bai d’ agawa yadda zakusan lallai Anas yashiga wani erin yanayi kenan. Ace Amal ma gabad’aya yak’i picking call nata. Allah sarki!
 
         Anas na zaune k’asan carpet a hotel room nasa da giya hannunsa se sha yake ba makawa, gashin kansa ya tarwatse wane na mahaukaci, d’akin duk warin giya yake. Ko ina kwalb’an giya kuke gani ko masu giara sunzoyi bai barinsu su shiga. Kan gadon ne kawai kenan tsatsaf shima d’in saboda ya k’aurace wa kwanciya kai ne a k’asa yake kwanciyarsa yanzu. Wayarsa dake kan gado ya soma ringing haka yana ji amman yakasa koda d’aga k’afa bale yaga kowaye. Haka ya d’aga giyan hannun san yakai baki sanda ya kurb’e tas sannan ya wurgar a k’asa kamar yadda ya saba. Bajewa kawai yayi a k’asan tare da zira wa ceiling ido. Can wayar tasan ta soma ringing again nanma yanaji be d’aga ba se a karo na uku yayi rarrafe ya d’aga idanunsa wani dushe dushe suke gani mai yama kasa gane wake kira kawai picking up yayi ba tare da yace komi ba.
      “Hello Anas?” Cewar Abuu shirun dayaji yasa yasake fad’in “hello? Anas baka ji ne? Hello?”
      Ai kawai Anas ya fashe da kuka cin wayar kamar d’an yaro. Hankalin Abuu in yayi dubu be tashi ba gashi basu san wani hotel Anas ya kama ma. “Anas! Anas until when zaka koyi rungumar k’addara ne wai? Kasani Babanka ya riga y rasu duk wannan abinda kakeyi ba dawo dashi zeyi ba. Haba! Mana Anas sekace bana miji ba, man up please. Kap kowa jira yake ka bud’e company’nka amman kak’i se yaushe wai? Iyye?”  Shiru kukeji ba response ko kukan ma yadena ji. “Hello? Anas!” Aikam tuni Anas yayi hanging up call d’in se kuka yake ba makawa. Shi har yanzu be yarda cewa Baba ya tafi ya barsa ba, Baba yatafi yabar masa company’nsa daya kula dashi. Yana cikin kukan Shettima ya kira yanaji yak’i d’agawa kusan missed calls biyar sannan ya d’aga nanma shiru yayi bece komi ba.
      “Hello Ya Anas” muryan Shettima ya jiyo. “Ya Anas kana ina?” Shiru yayi be amsa saba. “Ya Anas dan Allah kana ina? Wallahi duk mun damu ka fad’amin inda kake.” Amsar wayar Amal dake kuka tayi “Ya Anas yanzu seka tafi kabarmu dan Allah ka dawo gida” ta kuma fashewa da kuka. Jin kukan Amal yasa sa magana bayan ya daidaita muryarsa dan kar tagane a bige yake. “Shhh! Kinji Angel bar kuka, zan dawo amman ba yau ba.”
“Toh kana ina?” Ta tambaya.
      “Ina nan cikin Maiduguri.” Amsar wayar Shettima yayi “Ya Anas tell me ina kake inzo in sameka.”
     “Nooo bareyi kazo ba right now am drunk banasan su Abuu da Ummie suzo…” Aiko ya fara magana kamar zararre “kar su zo sugan ni ahaka sukamu da cancer” bama ciwon zuciya ba. Yad’anyi dariya “wayasani ko suma su mutu.”
         “Ya Salam!!!” Shettima ya fad’i. “Me ya same sa Ya Shettima?” Amal ta tambaya tana  kuka. “Ba komai” Shettima ya mata k’arya “jeki ina zuwa.” A sanyaye ta tashi ta fice. Tana fita Shettima ya dawo kan wayar.
        “Ya Anas what are you saying? Yanzu fisabilillahi tun tafiyar ka can kata shaye shaye? Ina kake yanzu.”
     “Chill little bro! Karka damu am somewhere safe.”
       “Ya Anas ka fad’amin inda kake inzo in duba ka please kaji?”
      “Saboda kazo dasu Ummie da Abuu sugane ina shaye shaye?” Anas yafad’i idanunsa suna kakkafewa besan sanda yabada address d’inbama kawai ya zarce bacci. A gurguje Shettima ya fito ya samu su Abuu a parlour duk hankalinsu ya tashi. “Ya haka? Ina zuwa?” Abuu ya tambayi Shettima. “Wajen Ya Anas zani Abuu.” yabasa amsa.
       “Tsaya muje tare toh mana.”
       “A’a Abuu please kayi hak’uri yace inje ni kad’ai bareji dad’i ba in ya ganmu duka kubar damuwa Ya Anas is somehwere safe.”
        “Anya kuwa Shettima?” Cewar Ummie cike da damuwa. “Kabari muje duka mu gansa dan Allah.”
      “Ummie please kar mu fara ce in ce, Ya Anas made it clear to me ni kad’ai yakeson in je kuyi hak’uri.”
    “Bakomai Shettima Allah kare kakuma isar masa d sak’on.” Abuu ya fad’i.
       “Toh Abuu” nan ya ja mota ya fice. Daidai ya isa harabar hotel d’in yafito bema san room number’n da Anas ke ciki ba, ko daya tambayi Anas d’in kuwa shima ce masa yayi besani ba tsantsan yadda ya bugu kawai.
     Reception ya wuce yayi tambaya k’in fad’i masa tayi acewarta ko yazo cutar dashi ne. “‘kaninsa ne ni can’t you tell? Bakiga muna kama bane?” ya daka mata tsawa. “Now tell me his room number.” Kallon fuskarsa tayi a tsorace sannan taga eh fa suna kama “I’m sorry sir room 21 CEO’n Flames Enterprises yake.” Da gudu ya haura sama zuwa room 21. A bud’e ma ya tarar da k’ofar yana sa kai warin giya ya masa sallama. Salati kawai yake yana bin d’akin da kallo kwalb’an giya sekace na siyarwa. Toshe hancinsa yayi tare da rufo k’ofar akan gado ya tsinci Anas yayi ruf da ciki se bacci yake. Kwata kwata singlet ne a jikinsa seda short nicker. Gashin kansa daya tarwatse ya rufe kad’an daga cikin fuskarsa. Juyar dashi Shettima yayi tare da kiran sunan sa. Shiru kukeji ba amsa. “Ya Anas! Kana jina?”
     “Uhmmmm” ya fad’i idansa rufe yana bacci. Giara masa kwanciya Shettima yayi tare da rufe sa da bargo sannan yakoma k’asa yakira masu aiki suka kimtsa d’akin tsaf aka sa room freshner me uban k’arfi da dad’i dan kora warin giyan.
    Baccin awa uku Anas yayi sannan ya farka a hankali ya soma bud’e ido ya saukesu kan Shettima. K’ok’arin zama yake Shettima ya taimaka masa.
      “Ya Anas how are you feeling?”
    “Yaushe ka shigo nan? Ya kasan ina nan?” Tambayar da ya masa kenan.
       “Kai kafad’a min, but it doesn’t matter. Ya Anas this has to stop. Ya isa fisabilillahi me damuwarka ne? kai bakasan meh k’addara bane a rayuwa? Kashe kanka kakeson yi kwalaban giya kusan 30 a d’akinka hauka ne kuma abin?”
      Ba tare da ya amsa saba yace, “inasu Abuu kataho dasu ne?”
       “Ban taho dasu ba amman believe me ina komawa gida zan sanar dashi da Ummie wannan halin naka na shaye shaye tunda you are not ready to change. Ina ka tab’a jin dan an ma mutum rasuwa seya soma shaye shaye haka? Haba mana Ya Anas.”
         “I’m sorry” ya fad’a a hankali cike da jin haushin abinda yayi. “Shettima I’m sorry, giyan ne kawai in nasha nakejin problems d’ina sun tafi. Shettima kubar ganin laifi na please abubuwa ne sun min yawa I’m just 24 baran iya managing babban Enterprise kamar na Baba ba. Baran iya ba, it is beyond my will.” Sekuma ya fashe da kuka. Da had’in Allah da Annabi da kuka sannan Shettima yasamu yayi convincimg Anas kan bud’e company’n.
       Wanka yasa sa yayi yana fitowa ya masa ordering abinci sosai Anas yasamu yaci. “Thank you Shettima, bansan ya zanyi ba without you.” Hugging nasa Shettima yayi “me too brother dan Allah ka rage shaye shayen nan kar alcoholic level naka ya haura yazama toxic, dan Allah.” Hugging nasa back Anas yayi “in shaa Allah zan rage.” Bayan sun sako juna Shettima yace, “lets go ga kayakin ka nan duk na shirya maka.”
     Tare suka sauk’o bayan Anas ya biya bills nasa suka dawo gida cikin motocin su. Amal na zaune bakin k’ofa tun d’azu tana jiran dawowarsu gate taji an bud’e da sauri takai dubanta ganin motan Ya Shettima k’aramar benz C230 yasa ta koma baya ta zauna tana sake juyawa kawai taga motar Ya Anas tsalle ta daka tayi wajen parking da gudu yana fitowa sukayi huggibg junansu sosai. “I miss you Ya Anas” tace tana hawaye.
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 18
BY MIEMIEBEE
     “I miss you too my Angel, bar kuka barin sake tafiya ba, I’m back forever.”  “Yeyy!” tasake hugging nasa. Bayan sun shigo su Abuu da Ummie duk sukayi hugging nasa sun mugun jin dad’in dawowansa. “Sannu da zuwa Baba” na cewar Ummie, “kar ka sake tafiya dan Allah.”
       “In shaa Allah Ummie.” Anas yayi assuring nata.
      “Erm Anas I’m sure Shettima ya sanar dakai halin da ake ciki koh? Ma’aikatan company’nka har gidan nan sukazo suna rok’o na in maka magana sukoma office.”
     “In shaa Allah monday zan bud’e Shettima ya fad’a min komai. I’m sorry baran sake barin gidah ba. Problems ne suka min yawa Abuu bansan ta ina zan fara solving ba.”
         “Anas just know we are here for you running is never a solution.”
        “In shaa Allah Abuu barin shiga daga ciki.” Amal dake mak’ale kan cinyarsa ta tashi tare da k’ara mak’ale hannunta a nasa. “Kekuma Amal ina zaki?” cewar Ummie. “Zanbi Ya Anas d’akinsa.”
   “A’a kinga Ya Anas ya gaji yana neman hutu da bakin kinnan zaki damesa.”
     “Ummie mana, barinyi surutu ba” tafad’a tana bubbuga k’afa.
     “Don’t worry Ummie, taho muje my Angel.” Gwalo Amal tama Ummie sannan tabi Anas d’akinsa.
 
    Bayan ya rage kayan jikinsa ya haura gado tana zaune kan couch “Ya Anas ina kaje daka tafi?” Ta tambayesa.
    “Hotel Angel.”
    “Ohhh! kasan kowa yayi kuka daka tafi, tunba ni ba we all miss you blue eyes.”
Ido ya zaro “Amal ina kika san sunan nan?”
    K’arya tayi “babu kawai ni na had’a.”
      “Yau ni kike ma k’arya? Saboda kinsan password d’ina kika fara min shisshigi a waya ko?” ya tambayeta.
      “A’a fah Ya Anas ranan ne wata ta turo message lokacin ina game a wayan shine… Shine..” Sekuma tayi shiru.
     “Shine kika bud’e kika karanta koh?”
     “I’m sorry Ya Anas please karka canza password d’in.”
    “Toh naji barin d’an kwanta koh?”
     “Okah ba-bye” nan ta mik’e ta fice.
        Washegari…
Yau ta kasance Monday da safe Anas ya tashi ya shirya cikin black suit, black shirt da white necktie wanda yamun masa kyau bayan yayi  breakfast yaja benz na sa ya fice zuwa office. Daidai k’arfe takwas ya isa mutane turum ya tarar bakin k’ofar duk shi suke jira yana fitowa sukayi kansa suna gaishesa da “Boss” bayan ya bud’e office d’in ya shiga  elevator zuwa last floor inda new office nasa yake. Kallon office d’in kawai yake se gani yake kamar Baba ze shigo ya zauna kan office. Ba abin arzikin dayayi ranan inbanda  tunanin daya tayi seda signing papers da ake ta kawo masa. Sosai su Kacallah da Yunus suka yi condoling nasa kamar yadda duk sauran ma’aikatan suka masa. Sam be saba ba in suna kiransa da Boss. Aranan akayi renovating office d’in yakoma komai na ANAS IBRAHIM FAUZY.
     Office ne babban gaske me ciki biyu wanda harda d’aki ciki. Fridge, California bed, TV ba abinda babu ciki.
     Da yamma da misalin k’arfe 4:00PM daidai lokacin da suka tashi bayan Anas ya tattara stuffs nasa Kacallah ya shigo. “Uh sorry Boss bansan har ka tashi ba, wallahi seda aka tashi Ahmaz investment daga Kaduna suka kawo wannan kuma gobe zasu koma. “I’m so sorry please.”
   “Bakomai” Anas ya fad’i yana murmushi “kawo inyi signing.”  “Thank you Sir! You’re so kind.” Nan Anas ya zauna bayan yayi signing Kacallah ya sake masa godiya yakai da bakin k’ofa Anas yace, “uhm Kacallah are you free?”
     “Yes Sir wani abu ne?”
      “Ba abinda zanyi yau nace ko zakazo mud’an fita maybe muje muyi having snack tare I need someone to talk to.”
     “Oh yes ofcourse Sir barin kai wannan kafin su tafi.” Kai Anas ya giad’a masa “thank you”
    “The pleasure is mine sir.” Nan yafice bada dad’ewa ba ya dawo suka shiga elevator tare. A motan Anas suka fice, “so ina kakeso muje?” Anas ya tambayesa.
 
       “Duk inda kace will be fine Sir.” Cewar Kacallah cike da girmamawa.
    D’an murmushi Anas yayi “in mu bibbiyu ne kana cemun Anas kawai.”
      “I’m sorry sir amman baran iya ba, girman ka yayi yawa ace na kiraka da sunan ka. I’m sorry please.”
    “Tun da haka kace fine, so ina zamuje.”
     “Muje Fahmaz coffee shop Sir.”
   “Fahmaz Fahmaz…” Anas ya tsaya nazarin abu “ohh sune wanda in an kirasu waitresses nasu basua magana a wayan nan koh?”
   “Ahha Sir nakega basu gane ko kai waye bane. Muje chan d’in please you’ll like their services.” Ba musu Anas ya tuk’asu zuwa coffe shop nasu Fannah.
    Bayan yayi parking suka fito suka shiga tundaga bakin k’ofa aka fara tarerayar su Anas anga Nigeria’s most youngest billonaire. A special table suka zauna. Ya suleiman ne yazo ya musu sannu dazuwa da kansa sannan ya d’auki order’n su. “Mr. Fauzy is my honour having you here at my coffee shop what can I get you?” Ya fad’i yana washe 32.
   Kai Anas ya giad’a masa sannan ya dawo da kallon sa kan Kacallah. “Me zamuyi ordering?”
     “Sir nikuma zan mana ordering please do, ni ai duk abinda ka mana ordering I’m fine with it.”
    “No Kacallah I insist ka mana ordering. Feel free with me please.”
        “Tunda kace haka sir OK. Akawo mana caf`e lat`e.”
     “Unfortunately bana shan coffee.” Anas ya fad’a yana kad‘a kai.
     “Ohh sorry sir but da ka gwada gaskia nan coffee shop suna k’ok’arin yin coffee.”
     “Yes Sir” cewar Ya suleiman “ka gwada coffee’n mu I’m sure you will not regret it, please.”
       “Tunda kunyi insisting okay. Get us two caf`e lat`e.”
      “Thank you sir” sannan ya fice yana shiga ciki ya soma k’olla wa Fannah kira. Nan tafito tana daidaita hijabinta. “Yes Boss!” Ta fad’i cike da gatsine. “Yawwa yau zo ke zaki had’a coffee’n nan. Inason ki had’a coffee’n da baki tab’a had’awa ba.”
        “Tohhh d’an shugaban k’asa ne yazo coffee shop namun?” Ta tanbaya tare da d’age gira.
     “You will find out in kika kai musu. Two cups, ki had’a yayi kyau please Fannah give it your best. Table 03.”
   “Okay Sir” tace tana dariya. Nan ta hau had’awa bayan 3 minutes ta gama ta aza kan tray sannan ta fice. Kanta a k’asa tana kaiwa zuwa table 03 ta gaishesu tare da ajiye wa a gabansu.
 
     “Thank you” Kacallah ya fad’i nan ne ta d’aga kai ta kallesa “you’re welcome” ta masa murmushi jin d’ayan bece komi ba yasa ta juya ta kallesa lokacin kuwa hanky Anas ya cire yana goge fuskarsa se bata samu ta gansa ba. Tana ajiyewa ta fice.
      Anas na kai coffee’n baki yaji k’amshi sosai. Dayasha kuwa yaji dad’insa sosai tunda yasan kansa be tab’a shan coffee me dad’i ba kamar na yau ba last time dayasha a London kwata kwata be masa dad’i ba sesa yabar sha ma. Be cire cup d’in daga bakinsa ba sanda ya kurb’e duka. “Wow! coffee’n nan yayi dad’i sosai, this is the first time coffee yamin dad’i. In ba damuwa inason in k’ara.”
   Murmushi sosai Kacallah yayi “I told you sir. Waiter!” Ya kira wani na miji me uniform “caf`e lat`e zaka k’aro wa Boss d’ina.”
     “Okay” ya fice nan da nan yaje ya had’o ya kawo saidai da Anas ya tab’a ya ji na d’azun yafi dad’i. Da kyar ya had’e dan yadda ya yamutsa fuska yasa Kacallah tambayan ko lafiya.
    “Sir are you okay?”
    Ajiye cup d’in yayi “ba wannan nasha d’azu ba. Irin na d’azu nakeso.” Anas yace.
     “Sir” cewar waiter’n. “Caf`e lat`’n daka buk’atan nefa kalan na d’azu.”
   Tsawa Anas ya daka masa “No!” “nace ba eri d’aya bane kaje ka sake had’o min irin na d’azu.”
  “But sir-”
     “I said now.” Anas ya sake daka masa tsawa. A tsorace yabar wajen.
    “Sir I’m so sorry please” cewar Kacallah. “Is okay ba komai.” Anas ya tabbatar masa.
    Shigar waiter’n ciki yasamu Ya Suleiman. “Ya akayi Harauna?” Cewar Ya Suleiman.
    “Ya Suleiman CEO’n Flames Enterprises ne yace na had’o masa caf`e lat`e na had’o masa kuma wai ba irinshi yakeso ba, wai ba irinsa yasha d’azu ba.”
     “Omg!” Ya Suleiman yayi exclaiming.
  “Ina Fannah? Jeka kirata ita ta had’a masa kace tazo ta barinje in basa hak’uri” da “toh” suka rabu. Isan Ya Suleiman cikin shop d’in yayi kan table nasu Anas. “Sir please kayi hak’uri anje kiran yarinyan data had’a na farkon ne yanzu zata zo kayi hak’uri dan Allah.”
      “Make it quick inada abinyi please.” Cewar Anas nan Haruna yafito “Ya Suleiman Fannah bata nan ta tafi yanzu Asma’u ke fad’a min.”
    “What!?” Cewar Ya Suleiman. “Taya zata tafi? This is the first time take barin nan bata fad’a min ba.” Nan ya kewayo da kallonsa kan Anas.
    “Mr. Fauzy I’m so sorry please yarinyar data had’an ta tafi gida nakega emergency ne yataso but akoi wata itama ta iya had’awa sosai barin mata magana.”
   
      Ran Anas tafasa yake, “then make it quick!” Yafad’a a tsawace.
    Bayan ‘yan mintuna Asma’u tafito da coffee’n Anas. Tana ajiyewa ya d’auka yayi sipping nan ma taste d’in be masa ba wurgi ma yayi da cup din coffee’n ya zube a yayinda cup d’in ya tarwatse b’ari Asma’u ta soma. “Wai ace nan cofee shop amman ba me iya had’a coffee?” Ya Suleiman ne yafito yana ganin irin b’arnan da Anas yayi shi bama wancan ba kar Anas yasa ayi sueing coffee shop nasu.
    Hak’uri ya soma basa. “Mr. Fauzi wallahi wanda ta iya had’awan ne ta tafi gida.”
    “Wacece ita?” Anas ya tambaya rai b’ace.
   “Fannah ce Sir Fannah Aleeyu.”
    “Koma wace ita call her now kace mata ta dawo and make me coffee.”
      “Yyesss sir” Ya Suleiman ya amsa baki na rawa. Wayarsa ya ciro ya kira Fannah har ta tsinke bata d’aga ba se a karo na biyu. “Hello Fannah ina kikaje? Ki dawo please is urgent.”
      “Ya Suleiman jikin Baba ne yatashi yanzu haka asibiti zamu kaisa bareyi in dawo ba.”
   
     “Fannah dan Allah su Mama barasu iya kaisa ba? Nasan lafiyan Babanki means alot amman you are needed here rashin zuwanki ze iya jefa lafiyar coffee shop in mu cikin matsala please.”
     “Ya Suleiman if only I can come, baran iya barin Baba ba dan Allah kayi hak’uri I have to go” karap ta kaste wayar. Fuskar Ya Suleiman kad’ai amsa ce ga tambayar Anas. “So?” Ya tambaya
     “Sir we are so sorry amman yarinyar barata samu zuwa ba.”
     Kallonsa Anas yake “kasan ko ni waye ne? Nace ka kira Fannah take ko meh and tell her tazo ta had’a min coffee.”
       “Mr Fauzi mahaifinta ne ba lafiya saisa barata iya zuwa ba.” Anas najin ance mahaifinta yaji ya hak’ura. “Okay” yace tare da ajiye musu N1,000 kan table d’in yaja jakarsa a yayinda Kacallah yabi bayansa.
      Mamaki ne yacika Ya Suleiman da Asma’u daga jin ance mahaifinta kawai ya canza mind nasa ga kuma dubu d’aya daya ajiye musu ba tare da ya amshi chanji ba. Shide gode wa Allah yayi.
   _Wahsegari…_
     Da misalin k’arfe uku da rabi Anas ya zo coffee shop nasu Fannah shi kad’ansa. Tun jiya ya kasa bacci dan kwad’ayin coffee’n dayake tayi. Sam yarasa meke masa dad’i duk abinda yasa a bakin sa bai masa dad’i shi coffee d’in kawai yakeso duk ya k’osa yasake sha. Bayan yashigo aka karb’esa da girmamawan daya cancanta, nan yayi ordering caf` lat`e. Bayan yaron ya juya Anas ya kirasa “and kace Fannah… Fannah Aleeyu ce ta had’a and no one else okay?”
   “Okay” yaron yace masa. Yana shiga yasamu Fannah zaune tana buga gamw a wayarta yakai mata order’n ba tare da ta kallesa ba tace, “wai nikad’ai kake gani anan ne Boy? Ga Asma’u da Allah ka kai mata kaga game nake yi hak’uri.”
     “Ya Fannah shi wanda yabada order’n ne yace ke zaki had’a.”
   Baki wangalau Fannah ta bud’e lallai ma “yaushe aka fara wannan sabon salo? Coffee ba coffee bane waikam. Koma waye ne yayi hak’uri barin had’a ba tunda ba shift d’ina bane, Asma’u da shift nata ne ta had’a.” Daidai lokacin Asma’u ke shigowa cikin kitchen nasun. “Yawwa gara ma da kika shigo. Gashi caf`e lat`e zaki had’ama wani kiyi sauri.”
     “Waye ne?” Asma’u ta tambayi yaron. “Nima bansan sunansa ba.”
   “Ya yake? Fari ne yanada blue eyes?”
 
     “Eh” yaron ya giad’a kai. “Fannah dan Allah kiyi hak’uri ki had’a masa wallahi shine wanda yazo jiyan.”
    “Wai waye shi duk kika bi kika tsure haka?”
     “Fannah wallahi shine, Mr Fauzi d’an marigayi Alhj.  Muh’d.”
    “shi???” Fannah tafad’i tare da zaro ido.
      “Fannah dan Allah wallahi naki kawai yakeso, jiya nida Haruna muka had’a masa coffee wulli yayi dashi, please Fannah” ta k’are maganar kamar zatayi kuka.
    “Chabdi!” Cewar Fannah “ai gara ke ni da kike gani nannan wallahi banasan abinda ze sake had’ani da Anas d’innan ranan har kuka sanda yasani.” Daidai lokacin Ya Suleiman yashigo ransa b’ace “wai Fannah meke damunki ne? Bakisan da abinda kikeyi zaki haddisa mana problem ba? Wuce ki had’a masa coffeen kinsan ko waye shi?”
      “Ya Suleiman amman shift na Asma’u ne fah.”
   Katse ta yayi “amman kuma ke Mr Fauzi yakeson ki had’a masa off you go.” Zata k’ara magana ya daka mata tsawa “now!” hawaye taji na ciko mata a sanyaye ta mik’e ta had’a masa takawo gaban Ya Suleiman ta ajiye. “Gashi.”
      “Aww nikuma zan kai masa? Kikai masa yana san miki magana.”
     “Ya Suleiman dan Allah kayi hak’uri kaba wata ta kai masa wallahi banasan magana dashi dan Allah.”
     “Fannah I can’t say no to him kawai kije ki rufa wa coffe shop namu asiri.” Zata sake magana ya fice juyowa tayi ta kalli Asma’u da take ta kau da kallonta elsewhere. Miyau ta had’iye sannan ta fice kaiwa Anas kujerun ta duba sannan can ta hangesa dukda bata ga fuskarsa ba amman daga farinsa ta ganesa. A hankali ta k’arisa kan table d’in ta ajiye a lokacin yana kan waya yana kallon window. Tana ajiyewa ta juya zata tafi holding wayar yayi “Boss naki be fad’a miki inasan miki magana bane?” Ya fad’i authoritatively ba tare da ya kalleta ba. Cak ta tsaya tare da kewayo wa…
    © miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 19
BY MIEMIEBEE
Wayar da yakeyi ya cigaba da, tafi minti uku tsaye sannan yayi hanging, ba tare da ya kalleta ba ya d’au coffee’n ya kai baki be cire ba sanda ya kwankwad’e tas mamaki ne ya cika Fannah datayi mutuwan tsaye tana kallonsa cike da mamaki waiko d’umi d’umin coffeen ma baiji? “I will appreciate it in zaki bar kallo na haka kinemi waje ki zauna.” cewar Anas. Miyau ta had’iye wai shi ya yake gane mutum na kallonsa ne? A kunyace taja kujera ta zauna d’an nesa dashi har yanzu be d’ago kai sunsa juna a ido ba. Bayan ta zauna ya d’ago kyakkyawan fuskansa ya aza blue eyes nasa kan Fannah.
      Idanunsu na had’uwa Fannah ta saki salati. “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!” tare da dafe k’irjinta. Kallonta Anas yake cike da mamaki. Kallon cikin ido suke ma juna shide baya manta fuska yau ya soma sa Fannah cikin ido mesa take kallonsa kamar ta sansa? “Hey!” Ya fad’i da kallon ya ishesa. “Are you okay?”
     Shiru har yanzu tayi tana kallonsa tana tuna ina ta tab’a kallonsa, wannan idanu tasan ta tab’a sata cikin idanunta amman takasa tuna a ina. Tayi tayi amman takasa. Table d’in ya buga firgit ta kyafta idanunta tadawo reality. “Aljani kika gani neh?” Ya tambayeta. Kai ta kad’a masa. “Better” ya fad’i relieved.
     “So kece kike had’a wannan coffee?” Shiru tayi bata amsa ba se kallonsa take wanda har yafara feeling uncomfortable. “Please na kiraki nanne to give you an offer bawai ki tsaya kina kallo na ba, hold it after natafi you can admire me.”
    Kut lalle ma wannan Anas, jijji dakai ya maka yawa, well kanada kyau amman ni ba kyanka nake kallo ba cewar Fannah a zuci. “Ba kallonka nake ba” ta fad’a tare da kawar da kanta daga ganinsa. “Allah sa you mean what you said just now. So ke kike making coffeen nan?”
    Kai ta giad’a. “See Fannah kike koh?” Nanma kai ta giad’a.
      “Damn it!” Ya buga table d’in a tsorace ta d’ago kai tana kallonsa. “I hate it in ina wa mutum magana yana using body signal, kimin magana as I do you, clear?” B’ari take ta giad’a kai take tace “eh.” “Good” yace sannan ya cigaba “maganan gaskia I like your coffee.”
    “Thank you”+ tace a hankali.
      “And inason ina sha kullum like safe rana yamma dare all the time.”
     “Sir but coffee shop namu k’arfe shida muke rufewa kuma ni 2:00PM -3:30PM ship d’ina yake k’arewa.” Tafad’i tana kallonsa
     “Exactly! sesa na taho miki da offer yau. And for the last time kidena kallo na will you?”
     Kau da kanta tayi da alqawarin barata sake kallonsa ba so take ta tuna ina ta tab’a ganinsa sarai tasa wannan blue eyes nasan sede ta rasa a ina ta tab’a ganinsu.
      “So kinsan ni waye ne ba sena fad’a miki ba Anas Ibrahim Fauzi CEO’n Flames Enterprises inason inyi offering naki better job a company na kina making min coffee 24/7 meaning duk lokacin da nakeson shan coffee I’ll give you a call and komin me kikeyi a lokacin zaki bari kizo ki had’a min abinda kawai zaki na min kenan and zanna biyanki ko wani k’arshen wata da salary me kyau. So what do you say?”
        “Mr. Fauzi nagode da wannan dama but am sorry baran iya karb’a ba saboda as you can see ina da aiki a nan kuma am satisfied with it. In zakayi excusing d’ina zankoma aiki.” Tana k’ok’arin mik’ewa ya daka mata tsawa “sit! This should be the last time, ba’a dismissing d’ina sede inyi dismissing mutum clear?”
      “I’m sorry” tace “now sit.” Ba gardama takoma ta zauna ita bata ga mesa zesa tama wannan arrogant mutumin aiki ba, ita tausayawa masu aiki k’ark’ashinsa ma take. Mutum kullum cikin tsawa da masifa ba dariya? Chabdi!
      “Nawa ake biyanki anan? I mean whats your salary?” Tambayarsa ne ya dawo da ita daga duniyar nazarin data fad’a.
   
     “Mr. Fauzi me zakayi da albashi na, naga kamar its personal.”
    “Zaki fad’a min salary’n kine kokuma sena sa an rufe coffee shop nakun?”
     Zaro ido tayi wai wannan wani irin mutum ne? “N10,000 (dubu goma) ne.”
    D’an murmushi yayi baki rufe wanda kawai dimple nasa ne kad’ai ya lotsa. “N10,000 kad’ai salary’nki? Work for me I’ll pay you double.” Zaro ido tayi. “Ko ya kasa? N30,000 then.” K’ara ciro ido tayi waje “N40,000 toh.” Kai ta sosa “induk yakasa miki toh N100,000 inshima ya kasa tell me ko nawa kikeso I’ll pay you as long as zakina making min coffee.”
     Mamaki ne yacika Fannah lallai wannan Anas baida matsala jibi yadda yake irga kud’i sekace dutse?
    “So, you accept my offer?”
    “Mr. Fauzi kayi hak’uri inasan aiki na anan dukda albashin bame yawa bane amman Allah nasa min albarka kuma i’m satiafied.”
   “Oh common Fannah karki yaudari kanki dubu goma bare rik’e ki har na wata ba, dubu goman da ake kashewa in just a minute? accept my job ko nawa kikeso I’ll pay you.”
       “Mr. Fauzi I’m sorry please, nagode zan tafi.”
     “Kiyi tunani Fannah anytime kika canza mind naki you can call me” hannu yasa yaciro card nasa tare da ajiye mata kan table d’in. “Koda zaki kira karki kira around k’arfe 5:00PM to 8:00PM.” Be jira me zatace ba ya d’au jakarsa ya fice.
     Hararan card nasan tayi, ta ja tsaki sannan ta d’aga ta karanta, phone numbers nasa biyu tagani kai. “Aiko nasha giyan wake barin kira ka ba, bana buk’atan dubu d’ari d’arin ka mschww” d’aga katin tayi da nufin yagawa karap Asma’u tasa hannu ta wabce. “Ke bani!” cewar Fannah.
      “Nak’i barin bayar ba. Ke yanzu Fannah Mr. Fauzi gabad’aya yabaki card nasa shine kike k’ok’arin yagawa? Meya sa yabaki?”
     “Oho! kiya tambayesa ni bakisan wani abu ba tsoro yake bani wannan da blue eyes nasa kuma kinsan wani abu? ji nake kamar na tab’a ganin sa awani waje kuma kamar yadda muka had’u bawai irin yamin mutunci bane kamar… Sharri” Tayi shiru tana kad’a kai “ya Allah a ina nasan wannan bawan naka?” Ta tambayi kanta.
         “Kefa Fannah anyi mutum yanzu Mr Fauzin ne harzaki wani tambayi a ina kika sansa ko kika tab’a ganinsa? Abinda har office nasa kin tab’a zuwa aikunsha had’uwa.”
     “A’a Asma’u duk had’uwar mu dashi bamu taba had’a ido dashi ba se yau kuma ayau d’in naji na tab’a had’uwa dashi wani wajen amman nakasa tunawa.”
   “Kide tuna” cewar Asma’u. “Seki tashi lokacin tafiyar ki yayi.” A sanyaye Fannah ta mik’e, Asma’u tabi bayanta. “Ina jakarki Fannah?” Akoi wayata ciki in cire.
    “Yana chan kan counter a kitchen please kifito min dashi” murmushi Asma’u tayi sannan tafice zuwa kitchen chan ta d’au jakar Fannah ta bud’e daman bawani wayarta ciki, card na Anas tasa cikin jakar cikin wata zip sannan ta rufe takai wa Fannah.
        Isar Fannah gida keda wuya ta tarar da Afrah kad’ai a gida har su Mami sunkai Baba kenan ta fadi a zuciya. “Sannu da zuwa Ya Fannah ya haka kuma yau? Tun shigowarki kinyi shiru.” Bayan ta zauna kusa da Afrah tace, “wallahi Afrah wani abu ke damu na.”
     “Wani abu kenan Ya Fannah?”
    “Yau Mr Fauzi yazo coffee shop namu-”
     Katse ta Afrah tayi “dan Allah!? Omg! Kunsamu kunyi magana? Wayyo Allah!”
        Marinta Fannah tayi a hannu “da Allah kimin shiru. Kinaji ba?” Afrah ta giad’a kai Fannah ta cigaba; “I mean jiya ma yaje shagon namu to da yasha coffee na seyace wai yamasa dad’i yau ma yadawo na k’ara had’a masa.” Afrah zatayi magana Fannah ta katse ta “please kiyi shiru kiji ni.”  “Ina kaiki, bayan na kai masa…”
Nan ta kwashe labarin komi tabawa Afrah sosai Afrah tasha mamakin erin sokancin da Fannah tayi. A yadda suke shan bak’ar talaucin nan ne har za’a bata aikin dubu d’ari tace battaso? Lallai kam.
    “Afrah kinyi shiru.” Cewar Fannah
      “Saboda kin ban mamaki ya Fannah at thesame time kuma kin ban haushi yanzu har a baki aikin dubbai kice bakiso? Seyau nasan bakisan Baba yasamu lafiya gaskia.”
    “Afrah wace erin magana kike haka? Baki tsaya kinji dalilin dayasa nak’i aikinsan ba fah.”
    “Toh ina jinki wani dalili ne haka?”
   Hannunta Fannah ta rik’o. “Wallahi Anas baida mutunci kinfi kowa sanin yadda nake tsoron masifa da tsawa banasan amin masifa shiko Anas ba aikinsa se ma mutum masifa wallahi ko yau danne zuciyata nayi banyi kuka ba daya daka min tsawa. Bayan haka kuma kinga ai bareyi inbar aiki haka kawai da su Ya Suleiman ba, bareji dad’i ba mun saba najima ina aiki dasu kawai dan an bani aiki me kyau se na mance dasu? Na kyauta kenan?”
       “Haba Ya Fannah mesa masu aiki suke barin gun aikinsu in sun samu me kyau? shi kansa Ya Suleiman inhar yana sanki murna ze miki dan wannan promotion. Dan Allah Ya Fannah ki karb’i wannan aiki, for once a rayuwarmu muma muji dad’in da akeji, Baba yasamu lafiya.”
     Kad’a kai Fannah tayi “Afrah niba wannan bama. Afrah inada wrong idea da feeling akan Mr. Fauzi yau na soma sasa a idanu na amman kuma ji nake kamar natab’a ganinsa wani waje kuma kamar had’uwan mu sharri ne, Afrah bansan meke damuna ba.”
      “Lallai! Ya Fannah ai dama kin sha kallonsa mana, ko kin manta shi kikaje office nasa ranan?”
     “A’a Afrah believe me wallahi duk had‘uwar mu dashi bamu tab’a had’a ido hud’u dashi ba.”
     “Toh in banda abinki ranan ai na nuna miki shi a TV.” Shiru Fannah tayi tana nazarin abu..
    “Kuma fa haka ranan kin nuna min shi a TV lokacin da Babansa ya rasu” zata k’ara magana sekuma tayi shiru “amman fa kaman bangansa ba ma ranan na tuna bangansa ba”
    “A’a Ya Fannah kituna dakyau kin gansa koda kad’an ne, kinsan dama wani sa’in ai haka ne sekaga kamar baka ga mutum ba amman ka gansa next in kuka had’u kuma seka ta wondering ina kuka tab’a had’uwa. In bahaka ba ina ke ina had’uwa da Anas d’an billonaire ko kin manta a ture can London yayi rayuwarsa. Bansani ba ko kema kinje London d’in a mafarki” Afrah ta fad’a taja dariya.
    Maketa Fannah tayi “LOL kuma fa kinyi gaskia nakega hakan ne a TV na gansa ranan in bahaka ba kam ina zan had’u da mutum kan Anas.”
    “Yawwa ‘yar garin so yanzu zaki karb’i aikin?”
    “Eh” tama Afrah k’arya dan kar taji haushinta amman kam har cikin ranta bata san amsar aikin, kuma bataga abinda ze sa ta amsa ba. Gara ta soma neman sabon aiki datayi aiki k’arkashin Anas, mutum ne kullum cikin masifa baya murmushi bale dariya. Sekace dodo!
      Da daddare da misalin k’arfe tara bayan su Fannah sun idda sallah suna shirin kwanciya wayarta ya soma ringing tana kai dubanta taga Ya Suleiman cike da mamaki ta d’aga dan kuwa be tab’a kirarta warhaka ba se addu’a take Allah sa ba magana ze mata gameda Anas ba.
     “Assalamu Alaikum Ya Suleiman.”
    “Ff… Fannah!” Se jin muryar tasa tayi na rawa.
     “Ya Suleiman meya faru? Wani abu ne? Ya muryarka ke rawa?”
   “Fannah shagon mu… Shagon mu Fannah!!”
   “Ya Suleiman dan Allah meya sami shagon namu please tell me” hankalinta tashe take maganar. Afrah dake gefenta itama ji tayi zuciyarta na bugawa.
     “Shagon mu yakama da wuta Fannah k’urumus ya k’one ba abinda aka samu aka cire. Wutan NEPA ne yasoma gobarar kafin akira fire service k’urumus komi ya k’one.”
      Salati Fannah keyi ba makawa. “Innalillahi!” take idanunta suka cike da hawaye “Ya Suleiman kayi hak’uri mud’au wannan a matsayin jarabawa dole kayi hak’uri ka rungumi k’addara innalillahi! Gobe in shaa Allahu zan fito dare yayi yanzu dana fito am so sorry kayi hak’uri dan Allah.”
    “Nagode Fannah” ahaka sukayi sallama.
   
       “Ya Fannah meya faru?” Cewar Afrah.
     “Afrah shagonmu ya k’one wutan NEPA ne yasoma gobarar.” Salati Afrah tayi sannan tayi calming Fannah dake hawaye down. “Daman kinada niyyan barin aikin segashi dalili kwararre ya zo ayyah, Ya Fannah da rabon Allah baisan kiyi witnessing a day without a job.” Kallonata kawai Fannah take cike da damuwa ita shikenan nata ya k’are mesa hakan ze faru da shagonsu? Yanzu ya zatayi da kud’in asibitin Baba? Dole a gobe taje tasoma neman aiki.”
      Washegari da sassafe ta tashi taje ta shagonsu  k’urumus komai ya k’one abin tausayi. Ya Suleiman da Babansa da angansu anga wanda suka kwana suna kuka. Condoling nasu tayi gashi dama k’arshen wata yayi jiran albashi take ta k’arisa biyan kud’in asibitin Baba gashi yanzu da abinda yafaru ba su ba albashi dan koda za’a bata ma barata amsa ba da wannan masifar daya same su.
    One week later…
      Yau k’imanin sati kenan Fannah na neman aiki ba rana ba dare amman har yau ba labarin aiki, abin har kuka yake sata ga kud’in asibitin Baba ‘yan asibitin sun dameta harda cewa in bata k’arisa biya ba zasu kaita gun ‘yan sanda. Abinci ma yasoma k’arewa masu agida abinde ba kyau. Ita nadaman mesa ta yasar da card na Anas ma take ta hak’ura da duk walak’anci da masifan da ze mata inhar ze bata kud’i tabiya kud’in asibitin Babanta. Kuka tasha a waje sannan tashigo ciki. Mami da Baba da Aiman suna d’akinsu. Tana k’arisawa d’akinsu da Afrah ta tare ta zaune kan gado yau ko chatting d’inma battayi dan ba kud’in kati.
      “Afrah ba magana ne?”
      “Ya Fannah me zance miki? Nariga na gaya miki abinda yakamata. Kinada halin da zaki warkar damu daga wannan hali amman kika k’i. Kalli yadda kowa yake shan wahala haba Ya Fannah dan Allah.”
     “Afrah wallahi ba haka bane na miki k’arya dana ce miki zan karb’i aikin da Mr. Fauzi yabani wallahi tun a ranan daya bani card nasan na yasar bansan ya zanyi ba yanzu. Afrah nayi nadamar yin hakan ban zata shagon mu ze k’one ba kuyi hak’uri ina kan neman aiki har yanzu kuyi hak’uri dan Allah.”
     Afrah bata ce mata komi ba. Jakarta ta zazzage kan gado dan tattara credentials nata. Fitsari ne ya matse ta, bayan ta shige bayi Afrah ta lalimo kan gadon tana duba papers d’in dan ko bata yarda da abinda Fannah tace mata ba nacewa ta yaga card d’in. Kap ta duba bata ga komi ciki ba har ta hak’ura se kuma ta d’au jakar ta, dudduba zip nacikin jakar take can tajiyo takarda tana cirowa taga card d’inne daidai lokacin Fannah tafito “Afrah me kike min da jaka.”
    “Ya Fannah me wannan?” Da sauri Fannah ta hauro kan katifar ta amshe card d’in, baki ta bud’e wangalau “aina kka samu?”
    “Ina kuwa? Cikin jakarki? Dama baki yasar ba kenan dan bakisan karb’an aikin ne kika min k’arya kin kyauta.”
   “Wallahi tallahi Afrah kinji rantsuwan muslumi kenan bansan ya akayi abin nan ya dawo jakata ba aida nansan da zamansa da na kirasa tuni nida ake threatning d’ina kan za’a kaini gun ‘yan sanda?” Shiru tayi tana nazarin wani abu can tace, “aikin Asma’u definately ita tasamin cikin jakata” nan taba wa Afrah labarin komai.
  10 minutes later… Dadai k’arfe 5:30PM
    Fannah ce zaune kan kujera d’ayan hannunta katin Anas ne d’ayan kuma wayarta a kunne tana jiran Anas ya d’au wayar. Zuciyarta se bugawa yake bababam! Babam!
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 20
BY MIEMIEBEE
Ringing wayar yake amman ba response, bayan ya tsinke ta sake gwadawa nan ma haka har ta tsinke Anas be d’aga ba.
         Anas na kwance kan gadonsa yana ganin wayan na ringing ko yunk’urin d’agawa beyi ba danko baya d’aukan waya within time d’innan inba wai familiar number yagani ba. D’ayar number’nsa ta zuba nanma two missed calls duk be d’aga ba. Anas na gani nanma yak’i d’agawa. Fuksarta cike da disappointment tajuyo ta kalli Afrah. “Afrah be d’aga ba 4 missed calls na masa be d’aga ba. Omg!” Wayarta ta duba taga lokaci pass 5. “Oh no! Se yanzu na tuna sanda yace min kar na kirasa within 5 to 8.”
     “Toh seki bari se anjiman ai ki gwada.” Kai Fannah ta giad’a mata.
**
     Sosai Anas yayi missing coffee’n Fannah, bayasan shan komi inba coffee’n Fannah ba. Tun ranan da suka had’u yake jiran kirarta amman shiru. Bayan kwana biyu yaje ya duba coffee shop nasun yaga k’urumus komi ya k’one a tunanin sa wai a ranan ko washegari Fannah zata kirasa ta amshi aikin daya offering mata amman ina har yau shiru, k’ok’arin mancewa da coffee’n yake tunda basamu zeyi ba. Inda kuwa yasa a binciko masa ita da a ranan ze sameta amman kuwa girman kai irin nasa bare barsa ba.
     Washegari da safe da misalin k’arfe tara bayan Fannah tagama shiri tasaka atamfa ne ja da baki seda bak’in hijabi wanda yamugun sake fidda hasken ta. Ba makeup kamar yadda ta saba, daga kwalli se kwalli da lipgloss a baki ta d’au credentials nata tana shirin fita zuwa company’n Anas tunda bata samesa ta waya ba zataje ta samesa in person. Koda ta sake kiran sa ajiyan around pass 9 be d’aga ba acewarsa wai ko irin mata masu kiran san nan ne danko kirar yayi yawa.
      Isarta company’n keda wuya. Wannan shine karo na biyu da take sa Enterprise d’in a ido. Bayan tashiga ciki ta tsaya raba ido dan bata ma san ta ina zata fara neman Anas cikin wannan babban building ba, ita bama wannan ba karya ganta ya cicci mata mutunci yanzu danko baida mutunci. Reception ta hango ta k’arisa wajen da fara’arta ta gaishe da receptionist d’in wani kallon bakwai saura kwata ta mata “how can I help you?” Tace da Fannah tana tauna chewing gum bakin nan yasha jan janbaki.
       “Uhm Mr. Fauzi nazo gani please.”
     “Mr. Fauzi?” Cewar receptionist d’in tare da d’age gira. “Ked’in zaki ga CEO? LOL” ta k’yalk’yale da dariya.
       “Eh kwanakin baya ya tab’a offering d’ina aiki yace kan duk sanda na yi making up mind d’ina in zo in samesa. Ki kaini wajensa please.”
      “Ya sunanki?”
    “Fannah Aleeyu.”
    “Kina da appointment dashi ne? Yasan da zuwanki? Is he expecting you?”
     “Actually no amman in ya ganni ze tuna please ki kaini wajensa please.”
     “Uhm Fannah kinga Boss d’ina is a very busy man bareyi in kaiki wajensa ba, ba tare da yasan da zuwanki ba in zaki zauna kijira in masa magana yaso ko zuwa gobe ko jibi se a had’a muku appointment seki dawo.”
     “Ma’am please kiyi hak’uri dan Allah I need this job so badly mahaifina ba lafiya ki taimaka please wallahi ya ganni ze gane ni.”
    “Fannah kinga kiyi hak’uri ki fice daganan dan nan ba gidan bada taimako bane.”
    “Ma’am please.”
     “Security!” Receptionist d’in takira “kuzo ku fita da wannan ‘yar please.” Nan security sukayo wajen suna tambayan meya faru. Daidai lokacin elevator yake bud’uwa Anas ne ya bayyano yana sanye da navy blue suit da blue sunglasses a fuskarsa, gashin nan anyi styling nasa masha Allah, fuskar nan nasa tamk’e ba alaman murmushi. Wani na miji ne a bayansa wanda ga dukkan alamu PA’n sa ne.
   
     Taku yake magestically cike da k’asaita yana duba agogon hannunsa da alaman meeting zasa, tafiya yake kai a sama yakaida wajen su Fannah ta kira sunansa “Mr. Fauzi” cak ya tsaya sannan a hankali ya juya ya kallet
Bayan Anas ya gama shafa maganin kan ciwonsa ya kurb’e coffeen sa hankali kwance. Yana gamawa yasa kaya yaja motarsa zuwa gida. Amal na tsaye bakin k’ofa tana jiransa. Ko gama fitowa daga mota beyi ba tayi kansa tana masa oyoyo a garin haka tad’an fama masa k’onuwansa. K’ara yasaki kad’an.
    “Ya Anas kaji ciwo ne?”
    Murmushi ya mata “a’a angel ba ciwo bane.”
    “Toh Ya Anas kayi ihu fa, mugani.” Tana k’ok’arin d’aga mai T-shirt. Hannunta ya rik’e “don’t worry angel ba ciwo bane.”
     “Toh Ya Anas ina mayafina daka ce ka siya min zaka taho min dashi.” Nan ya tuna mayafin nata ya bawa Fannah. “Ya Anas kayi shiru ko dama wasa kake baka saya min ba.”
    “Angel na saya miki mana, naga bashida kyau ne shine na kyautar ma wata mata akan layi but don’t worry zan k’ara saya miki wani kinji?”
   Kai ta giad’a a hankali tana turo baki.
    Ganin haka yace da ita, “dauk’o mayafin ki muje mu siyo miki wani yanzu, infact shopping ma zan kaiki ki saya duk abinda kikeso.”
    “Yeyy! Ya Anas!” dagudu ta shiga ciki ta d’auko mayafinta suka fice.
    **
    Afrah kuwa ta k’osa Fannah tabata labarin abinda ya faru cikin tsakaninta da Anas d’azu, tun a hanya take ta damun Fannah sanda suka iso gida Fannah ta labarce mata komi. Ido wuru-wuru Afrah ta zaro. “Ya Fannah wallahi Mr. Fauzi na sanki irin wanga kallo haka?”
    “Kefa akuya ce” cewar Fannah “Mr. fauzin yasoni? Impossible tense kenan! bakiga uban rashin mutuncin dayake suburbud’a min bane wallahi.”
     “Ke baraki gane irin san bane-”
   Katse ta Fannah tayi “ni banasan ji sekace baki san banida martaba ba aiko da ace ma sonan yake bare aureni ba muddin yaji labarina kamar yadda nima baran auri masifaffen mutum kamar Mr. Fauzi ba. Kinga tashi ki rakani muje mu siyo wa Baba magunansa tunda mun samu kud’i.”
     “Amman Ya Fannah a gani na ba sekin bar aiki da Mr. Fauzi ba.”
   “Kamar ya Afrah? Ke bakisan Mr. Fauzi bane wai? Ai barin aiki dashi consider it done monday monday’n nan zan fara nema in Allah ya taimakeni nasamu ai na huta.”
   “Tunda haka kikace, Allah sa hakan yafi alkhairi.”
   “Ameen” Fannah tace sannan suka je suka siyo wa Baba magunansa.
      Wahsegari ma haka ya kirata kan taje ta had’a masa coffee a paint house nasa tun 8:00AM ya kirata amman se kusan to 9:00AM ta isa saboda ta raka Mami kai Baba ganin likita daga can ta biya gidan Anas tare da mayafin daya bata, ta wanke sa harda guga. Hijabi har k’asa take sanye dashi yau. Bayan ta danna door bell ta tsaya jira shiru dan haka ta sake dannawa nan ma shiru, yin haka sau uku taga ba motsin mutum gidan ta d’au wayarta ta kirasa alokacin da ya soma ringing kuwa wayan na hannun Amal tana game.
    “Ya Anas coffee maker na kiranka” kafin yace, “mik’a min” ta d’aga “hello coffee maker.” Ido wuru wuru Fannah ta zaro wato ma da coffee maker yayi saving lambarta, Allah shirya toh. “Hello Amal” Fannah ta gaisheta.
    “Laaa kinsan suna na taya ya?”
   “Bani wayar Amal” cewar Anas.
    “Ya Anas gashi ta kira suna na wacece ita?” Nan ta dawo kan wayar “Hello coffee maker ya sunanki?”
    “Fannah ce Amal.”
   “Laaaa! Fannah!!” ta daka ihu “ya kike?”
   “Lafiya, kefah?”
   “Amal kawo wayan nan.” Nan ya mik’e da nufin ze karb’a ganin haka ta mik’e a guje kafin tace me ya kamata ya k’wace wayan.
 
    “Yes? Kud’inki ne baki gani ba komeh?”
  “Mr. Fauzi gidan a rufe ne.”
   “Kin gwada bud’e k’ofar ne kika ga a rufe?”
  Nan tasa hannu taga a bud’e a kunyace tace, “a’a.”
    “Good kud’inki na kan dining table don’t call me again.” Kafin tayi magana ya katse wayar. Kallon wayar ta tsaya yi lallai ma wannan Mr. Fauzi wallahi da girman kai na kisa da ka juma da mutuwa. Tsuka taja sannan ta shiga ciki…
**
     “Ya Anas shine kace min bakasan wace Fannah ba ranan dana tambayeka.”
   Kallon Amal ya tsaya yi yana tunanin wani k’arya ze mata can yace, “eh mana ban santaba, ni banma san asalin sunan ta ba se yanzu, bakiga da coffee maker nayi saving number’nta ba.”
    “Toh Ya Anas mesa ta kiraka?”
    “Aiki zatamin.” Ya amsa ta a takaice.
  “Toh Ya Anas bani lambarta inasan muna waya da ita.”
   “A’a Amal, Fannah is not a good person bana san kuna zumunci da ita.”
    “Mesa Ya Anas?”
   “Just trust me kinji Angel?”
   “Okay Ya Anas” ta masa murmushi “bani wayar in cigaba da game d’in toh.” Ba gardama ya mik’a mata “zan d’an fita in kin gama ki had’amin a charging kinji?” Kai ta giad’a “and also karkiyi recieving min calls, Angel am serious.”
    “Ya Anas barin yi ba seka dawo.”
   “Yawwa Angel!” Be zarce ko inaba se paint house nasa alokacin kuwa Fannah har ta gama had’a masa cikin flask ta ajiye kan dining ta tafi. Dad’i yaji dan ba san ganinta dama yake ba sesa ma yace tazo time da bayya nan. Tun jiya daya ganta ba mayafi ya riga tunaninta wanda ya mugun basa haushi. Nutsuwa yayi ya sha coffeen sa sannan ya taho da flask d’in da ze dawo gida.
      **
     Fannah na zaune ita kad’ai a d’aki tun dawowarta take zaune shiru kasancewar Afrah ma ta tafi yawonta, su Mami kuwa basu dawo ba. Dadai zata d’au wayarta dan buga game kenan wayar ta soma ringing ganin sabuwar lamba ta tsaya nazarin kowaye amman sam bata san lambar ba sanda ta kusan tsinkewa ta d’aga nan ma batace komi ba, familiar voice taji “Fannah” aka kira sunanta.
   “Na’am Amal ce?”
    “Kin gane ni kenan?”
          “Eh!” Fannah ta fad’i cike da mamaki. “Ina kika samu number na?”
    “A wayan Ya Anas karki fad’a masa munyi waya fa kinji? Besan na d’auka number’nki ba.”
    “Toh Amal barin fad’a masa ba. Mesa kika kirani?”
    “Kawai I want you to be my friend.”
    Cike da mamaki Fannah tace, “toh nikuma? Ai na miki babba.”
  “To ki zama big sis d’ina” Amal ta fad’i tana turo baki.
   “To Ya Anas fa bare miki magana ba?”
    “Ai bare ma sani ba dan ni ba fad’a mai zan ba, kamar yadda kema baraki fad’a masa ba koh?”
    “Sosai” Fannah tace tana dariya “toh little sis barin fad’a masa ba.” Hira sosai suka sha suka riga tambayan juna questions akan rayuwarsu suna amsawa se can sukayi sallama.
    Washegari…
     Kasancewar yau Monday Fannah ta tashi tayi shirin zuwa office tare ta taro credentials nata dan daga can tana san ta wuce neman aiki. Takwas da ‘yan mintuna aka ta isa office bayan tayi knocking Anas yace, “come in.” Kanta sunkuye tashiga ta gaishesa be amsa ba bale ya kalleta, matsowa kusa da shi tayi alokacin ne ya d’ago kai yana kallonta.
        Jakarta ta bud’e taciro gyalen daya bata kafin ta ajiye kan table d’in ya dakatar da ita. “Wannan kuma fa? Kar ki ajiye min kan table” Ya tambayeta.
        Cak! Ta dakata “Sir mayafin daka bani shekran,jiya ne thank you, shine zanyi returning maka yanzu.”
          “Inada ido ai, banaso, bana buk’ata. Ko ki cigaba da ajiyewa wajenki ko kuma ki jefar ya rage miki. Make me coffee.” Mamaki ne yacikata bata ce masa komi ba ta mayar cikin jakarta sannan ta ajiye ta wuce ta had’a masa coffee bayan ta ajiye ta kallesa “Sir excuse me zan d’an fita but in shaa Allah zan dawo kafin azahar.”
    Yana sipping coffeen sa tare da duban wasu files “wannan kuma keya dama, iyaka in bakizo on time bane inyi firing naki” ya fad’a mata ba tare da ko ya kalleta ba. A ranta tace ka kwantar da hankalinka ina samun aiki zanyi resiging a nan. Jakarta ta ja ta fice neman aiki ta tayi amman ba sa’a kafin azahar ta dawo ta sake had’a masa coffee.
 
    Haka de tun daga ranan Fannah ta shiga neman aiki ba wasa. Mayafin kuwa ta adana sa gu d’aya dukda bata da niyyar sake sawa. Anas kuwa be canza ba baya shiga harkanta amman ko d’an k’aramin mistake tayi ze balbaleta ya tsawa ta mata, kuka take sosai duk sanda ya masifeta sam takasa sabuwa da masifar Anas, shiko kukanta sam  be d’aga sa bale ya nana sa a k’asa. Shak’uwa sosai yashiga tsakanin Fannah da Amal wanda har yau Anas be sani ba. A yau wata d’aya da sati biyu kenan tana masa aiki.
     Yau ranar ta kasance Wednesday, dawowar Fannah daga aiki kenan idanunta duk sunyi ja saboda kuka.
    “Fannah ya haka?” Mami dake fitowa daga kitchen ta tambayeta.
    Kare fuskarta take “ba komai Mami dutse ne yashiga min ido amman yafita karki damu.” tamata k’arya.
    “Are you sure?”
   “Eh Mami ina Aiman da Afrah?”
   “Sun shiga nan mak’ota.”
  “Okay barin watsa ruwa toh” nan tayi hanyan d’akinsu. Bayan tafito daga wanka tajiyo alert a wayarta tana dubawa taga message daga d’aya daga cikin ma’aikatan datayi applying FCB ltd. Tsalle ta daka ganin aiki suka bata kuma akan abinda ta karanta finally zata samu tayi amfani da ilimin data samu a jami’a.
   Afrah na dawowa ta labarta mata komi sosai Afrah ta mata murna. Ga albashi me kyau daidai N50,000.
       Bayan ta sa kaya taje tayi printing resignation letter’n da zata kaiwa Anas gobe. A hanyar dawowarta gida Amal ta kirata bayan sun gaisa take fad’a mata kan tabar aiki a Enterprise na Anas tasamu aiki. Amal ta mata murna kam sede bataji dad’in barin aikin Fannah gun Anas ba. Sau dayawa tana zuwa office na Anas ita da Fannah su fita suje suta hira ba tare da sanin shi Anas d’inba.
   
     “Ya Fannah amman mesa zaki bar aiki da Ya Anas? Ya miki wani abu ne?”
    Murmushi Fannah tayi sam halin Anas da Amal ba iri d’aya bane, kamanninsu ne kawai d’aya. “Ba abinda yamin Amal kawai nasamu better job ne.”
   “Yanzu shikenan bara mu sake had’uwa ba?” ta fad’a kamar zatayi kuka.
       “Nima banso hakan ba Amal, amman ai zamu na waya ko?”
   “Eh amman its still not enough ko zaki na zuwa gidanmu?”
    Danqaree Fannah tafe a zuci. “A’a Amal bareyi inje gidanku ba saboda Ya Anas.”
        “Ba abinda Ya Anas ze miki dan Allah kinji?”
    K’arya ta mata “naji zanzo in shaa Allah. Ina kan hanya bari in na isa gida zan kiraki.” A haka sukayi sallama.
     Washegari Fannah tasha baccinta a cewarta ta bar masa aiki se lokacin data ga daman zuwa office zata takai masa resignation letter’nta. Da misalin k’arfe 9:30AM Fannah ta iso building na Anas. A first floor ta had’u da Yusuf ta sanardashi great news na aikin data samu sosai yaji mata dad’i kuma ya mata murna. “Barin haura inkai wa Mr. Fauzi resignation letter na ina zuwa.” Da “toh” ta shige elevator. Zuciyarta fal da farin ciki ba me sake sata kuka yanzu dan ta tabbata ba worse Boss kamar Anas. Knocking d’aya tayi a bakin k’ofar yace, “come.” Cike yake da ita wato yau se 9:34AM Fannah taga daman zuwa masa office, she will get it from him.
        Bayan ta k’ariso ciki ta gaishe sa ko amsa ta beyi ba kallo ya watsa mata wanda yasa k’afafunta shaking. Ya bud’e baki ze soma suburbud’o mata masifa kamar an turosa kawai k’ofar office d’in ya bud’u wanda ba kowa ke shigowa haka ba illa Amal. “Ya Fannah!” tayi ihu ganin Fannah tsaye da gudu ta nufa wajenta tayi hugging nata. Baki wangalau Anas ya bud’e yana kallonsu. Wato Amal bata je school ba yau, bama wannan ba yaushe suka san juna da Fannah har suka shak’u haka? Tambayoyin da yayi wa kansa kenan.
     “Ya Fannah yanzu dagaske kike zaki bar aiki nan? Dan Allah kiyi hak’uri.”
     Kunnensa ya bubbuga ko halan ruwa ya shiga yau da yake wanka, barin aiki Fannah zatayi zuwa ina? Ta samu wani aiki ne? Coffee na fa? Bece dasu komi ba sanda suka gama hoge-hogensu. Bayan Fannah ta ciro letter’n ta matso kusa da table na Anas. “Mr. Fauzi wannan resignation letter na ne. Thank you for giving me the oppurtunity to work for you.” Letter’n ya d’aga yana k’arisa masa kallo sannan ya d’ago blue eyes nasa yana kallonta “are you really sure about this? Na barin aiki a nan?” ya tambayeta ba tare da ya nuna damuwa ba dukda kuwa ya damu sosai.
      Kai ta giad’a a hankali. “Kin samu wani aiki ne?” Nanma kai ta kuma giad’awa. “A ina?”
    “A FCB ltd.” ta amsa sa.
   “Ohhh, nawa ne salary’n naki?”
   K’arya tayi masa “nima bansani ba tukunah.”
   “Yayi kyau zaki iya tafiya.” Amal dake kallonsu ne tace, “Ya Anas ka hana ta tafiya ka k’ara mata salary se kar ta tafi.”
    “A’a Angle barta ta tafi. Ni ban hanaki alak’a da ita bama?” Ya tambayeta ba alaman wasa a tattare dashi.
    “Ya Anas kayi hak’uri.”
    “Zan hak’ura if only kika dena alak’a da ita, kingani ai barin aiki tayi.”
  “Mr. Fauzi-” cewar Fannah be saurareta ba ya daka mata tsawa “just go, leave, bana san sake ganinki.”
   “Amal na tafi” nan ta juya.
   “Ya Anas-” itanma tsawa ya daka mata for the first time. “Enough Angel kije ki samu Yunus yakira Shettima yazo ya d’auke ki.”
    Ita kanta tsoro taji sosai bata tab’a ganin mood na yayanta haka ba. Wajensa ta nufa tayi hugging nasa “Ya Anas I’m sorry, bansan me Ya Fannah tayi ka tsaneta haka ba, tanada kirki fah but tunda baka sona tare da ita, I’m sorry.”
     Bayanta ya shafa “is okay je gida ki huta nima I’m sorry for shouting at you.” Bayan Amal ta fice Anas ya d’au resignation letter’n Fannah ya yayyaga into pieces, zuciyansa se tafasa yake. Yarasa me ke damunsa mesa ma nake damuwa dan wata wai ita Fannah tabar min aiki? Nawa suka fi ta komi kuma na koresu, toh se meh dan kin bar min aiki? Mschww dama dan coffee ne kuma akoi masu neman aiki anan dubu. Wayarsa ya d’au ya kira Ahmad. “A buga a news ina neman masu aiki wanda suke da degree inma da hali har da masters kan had’a cofee.” Cike da rashin fahimta Ahmad yace, “Boss coffee kuma? Anayin course akan coffee ne?”
    A fusace Anas yace, “in baka aiwatar da abinda na saka kayi ba a yau a bakin aikinka.”
    Tuni Ahmad ya amsa “yes ofcourse Boss”  “Good, kuma ka turo cleaners suzo share wannan gabbage” yana nuni da resignation letter’n Fannah daya yayyaga “and also ka turo min number’n manager’n FCB ltd”
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 27
BY MIEMIEBEE
Ko cikakken minti d’aya ba’a yiba Ahmad ya turo masa lambar PA’n Manager’n FCB ltd kasancewar Manager’n ya canza number kuma bayi sabon. Nan Anas ya kira PA’n ringing d’aya biyu PA’n ya d’aga gaisuwa ya fara wanda Anas ya dakatar dashi ransa se tafasa yake dan yadda ya b’aci. “Ka kai wa Boss naka wayan” ya fad’a authorititavely.
        “Wa ke magana please?” Cewar PA’n saboda bada layin office Anas ya kirasa ba.
     Ba k’aramin fusatar dashi tambayan PA’n yayi ba. Cike da b’acin rai yace, “Tambaya na ma kake wake magana? Inba wai so kake ka rasa aikinka a yinin yau ba give the damn phone ro your Boss.” Ya sake daka masa tsawa.
    “Sir I’m sorry but ya kamata insan wake magana kafin in maka abinda kake buk’ata.”
     “You’re stupid kajini? Nace you are stupid, ANAS IBRAHIM FAUZI ke magana CEO’n FLAMES ENTERPRISES.”
     “Omg! Sir dan Allah kayi hak’uri wallahi ban san kai bane,my apologies please kayi hak’uri.”
    Tsuka Anas yaja “mschww damuwanka wannan kuma, where is your boss ka kai masa wayan.”
    “Sir d’azu da safe Boss d’ina da family’nsa suka tafi trip zuwa Hungary.”
   “Meaning what? Meaning baraka kirasa kace inasan masa magana ba kenan ko meh?”
   “Sir I’m so sorry amman sanda ya fad’a min koda wasa kar na kirasa in batun aiki ne dan Allah kayi hak’uri. Hutu ya tafi”
     “Lalle kanasan rasa aikin ka nace call your Boss kace masa ina san masa magana.”
   “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri wallahi banasan rasa aiki na.”
    “Damn it!” ya buga hannun sa kan table, “what of business kuna running har yanzu ko shima kun dakatar?”
          Dadai lokacin knock yashigo daga k’ofar office nasa “come” yace bayan an bud’e k’ofar cleaners mata biyu suka bayyana. Tun daga bakin k’ofa suke gaishesa har suka k’ariso ciki. Papers d’in ya nuna masu nan d’ayan ta hau sharewa kallonsu ya tsaya yi bayan yayi holding call dayakeyi da PA’n.
      Har sun kai da bakin k’ofa ya kirawo su, dawowa sukayi suka tsaya gabansa “yyyess Sir” har i’ina suke dan tsoro. “Haka ne kin share nan wajen?” Yana nuna wanda ta share wajen “bakiga wancan paper’n bane?” Ya nuna mata wani piece na paper a k’asa. “Me amfaninki a nan in har shara ma baki iya ba se an koya miki? Eh?? Useless kawai.”
          “Boss dan Allah kayi hak’uri” tana b’ari taje ta share gudan paper’n kallonta yake sannan cike da nuna rashin damuwa yace, “you are fired ki tattara kanki kibar min building kije kisamu Adam yayi settling miki salary’nki. You are dismissed.” Kuka ta fashe da “Boss dan Allah kayi hak’uri wallahi ban gani bane hakan bare sake faruwa ba.” D’ayan ce tasa baki dan ganin yadda ‘yar uwarta ke kuka. “Boss dan Allah kamata hak’uri bada-”
       Mugun kallo kawai ya mata wanda yasa take tayi shiru. “Kekuma waya jefa bakinki cikin wannan matter? Nasan kinada dogon baki ba sekin nuna min ba I have eyes to see. You two dukan biyu are fired, kuje kusamu Adam yayi settling muku albashinku now leave my office.” Suna kuka suna had’asa da Allah amman ko a kwalan rigarsa tashin hankalin Fannah tabar masa aiki bame had’asa masa coffee ke damunsa nan ya dawo kan wayar.
         “Nace kun rufe business naku ne ko kuna running har yanzu?” Ya tambayi PA’n.
    “Muna running Sir komi munayi.”
    “Good” Anas yace, “kwanan nan kukayi hiring ma’aikata koh?”
    “Eh Sir just jiya muka musu sending letter ran monday zasu soma aiki.”
     “Ka bud’e kunnuwanka da kyau kajini. Inasan kaje kabi list d’in kayi firing FANNAH ALEEYU. kajini?”
   “Naji Sir yanzu zanje in samu secretary in masa magana in shaa Allah za’ayi firing natan. Amman mesa Sir?”
           “Wannan kuma ba damuwanka bane, inajiran feedback nanda like 10ninutes”
         “Okay Sir” nan Anas ya katse wayar. Bakinsa ya cize yana murmushin mugunta. Telephone na office nasa ne yasoma ringing nan ya d’aga.
       “Hello Boss an buga a press da jaridu gobe in shaa Allahu masu degree da masters harda PHD ma zasu soma applying batun coffeen”
     “Good banasan failure.”
    “In shaa Allah Boss.” Shide Ahmad mamaki yake har yanzu wai yaushe aka soma yin degree kan had’a banzan shayin da ake had’awa kan tebur akan layi safe rana dare, wani abu se Boss.
   Kai ya jingina jikin kujerar sa yana juyawa a hankali chan ya mik’e ya bud’e fridge tare da ciro barasar sa kusan rabi ya kurb’e ya koma d’aki ya baje ya kwanta ko problem nasa ze d’an tafi. Sanda ya kusan kai minti goma sannan yasamu yayi bacci abinda kullum daya sha befi minti uku bacci ya rufesa. Bacci me nauyi ne ya rufesa wayarsa dake kan table se ringing yake PA’n Manager’n FCB ltd ke kira. Two missed calls yamasa sannan ya hak’ura.
     Bayan minti ishirin da kwanciyar Anas, Kacallah ya taho yana knocking bakin k’ofa se sauri yake kwata kwata ya manta Anas nada board meeting da zeyi attending yau saboda yadda aiki ya masa yawa gashi in less than 10 minutes za’a fara. Knocking yake sosai Anas dake bacci ko kad’an baiji daga k’arshe shiga kawai yayi yana kiransa da “Boss” shiru kukeji. D’akin ya lek’a yaga Anas yayi ruf da ciki se bacci yake sha harda minshari necktie nasa yayi gefe guda takalmansa ma d’aya na kudu da’aya kuwa arewa. Ido ya zaro wuru wuru mekuma yasami Boss nasa yake bacci in the middle of the day.
      K’arisawa cikin d’akin yayi shi kansa tsoron tada Anas yake gudun kar ya rasa aikinsa dan kuwa yaga Hussaina da Zainab da akayi firing d’azu se kuka suke. A hankali ya tsuguna gaban fuskar Anas. “Boss!” ya fad’i murya na b’ari. “Boss!” Nan ma shiru dan haka yad’an jijjik’a sa ko kad’an Anas be motsa ba se bacci yakeyi. “Boss!” Kacallah ya kira sa sosai cikin kunnen sa nan ya yamutsa fuska. “Boss kayi hak’uri ka tashi akoi board meeting da za’ayi wanda yazama dole kaje you are needed please.”
     Cikin bacci yace, “dole? Se a sani inga. Barin je ba leave ko baka ga bacci nakeyi ba?” Pillow yaja ya rufe fuskarsa. Fuskar Kacallah kan wanda zeyi kuka “Boss kayi hak’uri ka tashi please you have to be there.”
     “Wake magana?” Anas ya tambayi Kacallah fuskarsa rufe da pillow dan yama kasa recognising muryar meshi.
   “Kacallah ne Boss, Kacallah ne.”
   “Kacallah kanason aikinka?” Anas ya tambayesa fuskarsa cikin pillown har yanzu.
    “Eh Boss inason aiki na sosai” ya fad’i yana giad’a kai.
    “To ka tashi kabani waje, fita min daga office in na sake jin muryaraka you’ll be fired.”
    “Fired?” Kacallah ya nanata a zuciyarsa. Meyayi zafi harda firing. Da sauri ya tashi ya bar d’akin hak’urin da yakeson badan ma yafasa dan ko Anas yace baisan sake jin muryar sa. Bayan ya isa office nasu na ma’aikata ya zauna kan table nasa tunanin wani k’arya ze had’ama wanda zasui meeting d’in yake chan ya d’au telephone ya kira assistant coordinator’n meeting d’in bayan ya gaishesa ya fara kamar haka;
        “Uhm Sir dan Allah kayi hak’uri for the inconvenience da aka samu.”
   “Wani incovinience kenan?” Mutumin ya tambaya.
      “Boss d’ina ne mahaifiyarsa ba tada lafiya, bareyi yasamu attending meeting d’inba, kuyi hak’uri please.”
     “Toh Allah sawak’e amman gaskia bareyi ace Flames Enterprises basu hallaci wannan meeting ba saboda  na board ne gabaki d’aya, ka turo d’aya daga cikin staffs naku ya ko ta wakilce sa.”
       “Yes Sir thank you so much.” Nan ya katse ya kira wata ma’aikaciya Suwaiba dake 6th floor yamata bayanin komi take ta shirya ta tafi zuwa meeting d’in. Nanne Kacallah yad’an samu peace of mind se addu’a yake Allah sa kar emergency ya taso dan besan ya zeyi ba Boss yace bayasan sake jin muryarsa.
          Bacci sosai Anas yasha kusan to 2:00PM ya tashi da k’yar yayi alwala yayi sallah yayi ordering  kawo masa abinci daga kitchen, a lokacin ya duba wayarsa yaga missed calls from PA. Nan ya kirasa, “hello Sir good afternoon.”
   Ba takan gaisuwar yake ba dan haka ko amsa sa beyi ba, “yes anyi firing natan?”
     “Unfortunately Sir wallahi secretary’n yace ba abinda tayi wai bareyi firing nata ba-”
   “What!??” Anas ya daka tsawa. “Bareyi firing nata ba? Waye shi?” Daidai lokacin knock yazo daga k’ofa ransa b’ace yace, “who is it?”
      Tana b’ari tace, “Boss Leemcy ce abincin ka na kawo”
      “Banaso, get the hell out of my office you are fired kije ki samu Adam.” Aguje ta koma k’asa tana kuka. “Kace meh? Bareyi firing nata ba? Kai masa wayan.” Bayan minti d’aya aka kaiwa secretary wayar.
   “Hello yace.”
   “Hellon k’aniya?” Anas ya tambayesa “kasan dawa kake magana?”
   “A’a seka fad’a” cewar secretary’n.
   “Nonsense you are speaking with ANAS IBRAHIM FAUZI.”
   “Sir! Ran ka ya dad’e kayi hak’uri dan Allah wallahi Kabir be sanar dani wane kai ba.”
    “Yanzu daka sani seka yi abinda ya kamata” amsar da Anas ya basa kenan.    “Yes ofcourse Sir yanzu zan tura mata message d’in.”
   “Good, inajiran feedback nanda 5minutes.” Karap yayi hanging call d’in.
     Nan da nan yasa akayi typing message na Fannah daidai lokacin za’a tura Manager’n wajen ya turo sak’o kan kar a d’iba kuma kar a sakar da masu aiki saboda wasu k’wararrun dalilu. Aiko ba halin korar Fannah. Nan ya kira Anas ya masa bayani.
    “What rubbish are you saying? Ku had’ani da manager’n naku.”
    “Sir wallahi kayi hak’uri nan da sati biyu ze dawo in ya dawo everything will go your way, sosai Boss yana mutunta ka duk abinda kakeso shi zai maka, ka k’ara hak’uri please ni da kaina zan sanar dakai duk sanda yayi landing.” Dan haushi bema amsa sa ba ya katse wayar. Zuciyarsa tafasa yake kamar ze k’one “mstchwww.” Ma akan Fannah da bata kai ta kawo ba yana ta tada hankalinsa inde coffee ne ai yasa job on sale daga gobe za’a fara applying, se meh dan Fannah tabar masa aiki, aikin banza. Tun lokacin tashi beyi ba ya tattara wayoyinsa ya sauk’a. Chan ma by mistake wata ma’aikaciya tasha gabansa saboda saurin da take tayi submitting wasu files take aka buga mata fire! Itama. A ranan Anas yayi firing mutane ba adadi kowa mamaki yake at thesame time being cautious kuma shima kar a koresa. Kacallah de ba halin yima Boss magana dukda there is so much to tell.
     Washegari ta kasance thursday ‘yan garin Maiduguri kap angani kuma an karanta a news cewa Flames Enterprises suna neman masu aikin had’a coffee. Zokuga yadda maza da mata suka taru bakin building na Anas yau. Da k’yar yasamu passage. 10-10 ake d’ibansu ake kaisu kitchen kowa da coffee machine dakuma ingredients na had’awa. First set suna gamawa Mr. Fauzi ya sauk’o tasting na wanda yafi masa dad’i seya samu aiki ya maye gurbin Fannah dan ko bacci ya kasa jiya se tunanin coffeen Fannah yake duk yadda yayi ya mance coffeen Fannah ya kasa, he is addicted to it dak’yar yasamu yayi bacci bayan syrup dayasha.
    Yana kai na farkon baki ya mayar cikin cup d’in “meh wannan? Ruwan wanki ko meh? take her out.”
    “Yes  Sir” cewar Adam. Nan na biyu ta matso itama yana kaiwa baki ya mayar cikin cup d’in “ke kinma san meya kawo ki nan kuwa? Take her out.”
  “Yes Sir.”
    Na uku ma takawo nata shima yana kaiwa baki ya miyar cikin cup d’in. “Take her out bana san sake ganin fuskarta.”
     Haka de bayin Allah suketa shigowa anayin round-round, na mutane 25 maza da mata Anas ya tab’a dukka ba wanda ya masa koda kusa da na Fannah ne.
      “Fire them all, duk ka koresu bana san sake ganinsu. Fire them now!” Yaja tsuka sannan ya shiga elevator’nsa ya haura zuwa office. A ranan yayi firing ma’aikantansa guda biyar plus na jiya abin de ba dad’in ji. Hankalin kowa tashe yake abu kad’an kayi a danna maka fire. Yau yini biyu kenan Anas be sha coffeen Fannah ba amman ji yake kamar shekaru aru aru ne. Yarasa ina ze sa kansa, abinci ma ba sosai yake ci ba koda ya gwada had’a coffeen baya masa dad’i bai ma iya sha gashi wannan karan ko Shettima ma be sanar dashi abinda ke damin sa ba kamar yadda ya hana Amal ma. Kawai in an tambayesa cewa yake rasuwar Baba (Mr. Muh’d) ya tuna.
      Yau k’imanin sati kenan da barin Fannah aiki gun Anas, k’imanin sati be d’and’ana coffeen ta me dad’i a bakinsa ba. Ba yadda beyi ba dan mancewa da coffeen nata amman yakasa shi daga baya nema yagano ba coffee natan kad’ai yake missing ba ita kanta Fannan ma missing nata yake, yes yayi missing Fannah, yayi missing innocent face nata, yayi missing kukanta dakuma muryarta me dad’in gaske, yayi missing kamilallen shirinta na kullum, komai yayi missing akan Fannah. Yabi ya k’osa next week ya iso ya kira Manager’n FCB ltd.
       Fannah kuwa rayuwarta ta juma batayi dad’i kamar yadda take ba yanzu, ba ruwanta da wani tashin hankali, aikinta tana yinsa me kyau ba ruwan asst. Manager’n ta da shiga harkar mutum bale ma ya mata masifa. Sosai take jin dad’i aiki wajen. Amal kuwa duk da erin warning da Anas ya mata ta kasa dena kiran Fannah saboda hankalinta. Wannan shine karo na farko da take sab’awa umurnin Anas.
 
  © miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 28
BY MIEMIEBEE
Da yammacin ranar Juma’a bayan Anas ya dawo daga office yayi firing mutane 6 shida ranan. Kwance yake kan gado a d’akinsa ya zura wa ceiling ido yayi zurfi cikin tunani. Har Shettima yayi sallama ya shigo beyi noticing ba. D’an tab’a sa yayi a hannu firgit ya dawo daga duniyar tunanin daya fad’a. “Ya Anas yaukuma tunanin me kake haka? Na Ummimi kokuma na yarinyan?” ya tambayesa yana k’ok’arin zama kusa dashi.
    “Ko d’aya” ya amsa sa alokacin dayake k’ok’arin zama.
    “Then mene? Kasan ban maka magana bane amman Yusuf yabani labarin abinda kake tayi a Enterprise naka, me yayi zafi ace cikin sati kayi firing mutane 31 haba Ya Anas.”
    “Oh haka shi Yusuf nakan yace? Allah kaimu monday shima ya jira nasa.”
     “Ya Anas wai me haka, friend nawan zaka kora? Wace kuma Fannah?” Cike da mamaki Anas ya kewayo da blue eyes nasa kan Shettima. “A ina kuma kaji wannan batu? Still gun Yusuf?”
    “It doesn matter Ya Anas saboda ita kake firing ma’aikatan ka kana kashe Enterprise naka da kanka, ajinka yanzu in za’a dawo da Baba zeyi appreciating abinda kakeyi ne?”
         “Toh yimin lectures Shettima, please ni banasan maganan nan excuse me.”
    “Saboda yarinyan ne Ya Anas, kanasan ta dawo maka aiki ne? Do you miss her?”
      A fusace yace, “Yes Shettima I do, I miss her.”
     “Toh mesa kake treating nata badly lokacin da take nan? Kaifa kasa tayi resigning tabar maka aiki.”
    “Shettima ni ba abinda yake damuna ba kenan, abinda yake damuna shine tadawo.”
    “Toh ta yaya?”
    “Ta duk yadda nasan zan iya.”
   
        Shiru Shettima yayi yana nazarin wani abu. “What are you thinking of?” Anas ya tambayesa. “Ya Anas kode san ta kake? Yaushe ka fara damuwa da rashin mutum a kusa da kai?”
     “San ta? Are you kidding me Shettima? Me zan so a jikinta? Ni kawai I miss her saboda coffeen da take making min.” Yama Shettima k’arya dan shi kansa yanzu yasan ba coffeen Fannah kad’ai yake missing ba no matter how yayi denying Fannah ta daban ce, kayan duniya be dame ta ba, kyansa dayasa mata suke binsa ma be dameta ba yaci ace Fannah ta kamu da ciwon sansa amman ko kad’an beyi noticing hakan ba a tattare da ita.
           “Amman da akoi abin duba anan mata nawa wanda suka fi Fannah komai suke fad’in suna sanka baka tab’a saurara musu ba hasali ma koda sun shigo rayuwarka k’ok’arin koransu kake amman when it comes to Fannah, ita ta tafi da kanta but kanasan dawo da ita. Ya Anas ina yarinyan dakace _TANA TARE DA KAI?_ Ko hala itace Fannan.”
 
        “Non sense. Wani erin jagual guale kake fad’i Shettima? That girl can’t be Fannah in da ace itace da nayi recognising nata. Ka manta lokacin da abinda ya faru a buge kake?”
     “Toh ita fah? Ai in ni a buge nake ita ba’a buge take ba, da itace da ta gane ni.”
   “Not really” Shettima ya fad’a yana kad’a kai.
        “Noo Shettima wancan yarinyan ba Fannah bace kadena had’ani da Fannah please ni ba wai santa nake ba, batta,da abinda zan gani har ince inaso duk mata ma ba wacce take dashi illa yarinyar dake *_TARE DA NI._* so please kabar had’ani da Fannah, coffeen ta nakeso ba itaba.” Shettima ze sake magana Anas ya katse sa “maganan Fannan kuma ya isa please. Zan kwanta excuse me” kallonsa kawai Shettima yayi ya kad’a kai sannan ya fice.
       “Mesa Shettima zece inasan Fannah? Mesa yake tunanin itace yarinyar da nake nema har yau, eh nasani yarinyar _TANA TARE DA NI_ amman ba itace Fannah ba, banasan Fannah barin tab’a santa ba coffeen ta kawai nakeso. Coffeen ma daga yau zan dena missing saboda in manta da ita a rayuwa na forever”
         Washegari ya kasance Asabar ko tashi daga kan gado Anas beyi ba ya fara tuna Asabar daya kira Fannah zuwa gidansa had’a masa coffee, k’irjinta daya gani tun ranan har yau yakasa deleting image d’in daga k’wak’walwar sa. Kai ya kad’a dan ya gusar da tunanin nan ya mik’e ya shiga bathroom ya kunna shower yabar ruwan na sauk’a kansa. Duk yadda yayi ya mance Fannah ya kasa, yarasa dalili is not as if yasan how it feels to be in love.
   _One week 2 days later…_
      A shekaran jiya Manager’n FCB ltd ya dawo tun a ranan secretary’n yama Anas sending number’n Boss nasa as promised sede abin mamaki har yau Sunday Anas be kira manager’n ba. Kwance yake a d’akinsa da wayarsa a hannunsa ya zura wa lambar Manager’n ido yakasa kira. Anas ya koma wani abu daban. Sati biyu ne tun rabuwarsa da Fannah amman seji yake kamar irin shekara da shekaru. Abin nasa se worse yake dukda maganar da Shettima yamasa amman ina. A yanzu haka yayi firing about 60 something staffs nasa kullum cikin kawo sabi ake, hankalin kowa ya tashi a office sede ba kamar yadda na Anas ya tashi ba. Mutuwa ne kawai beyi ba dan hana kansa tunanin Fannah da coffeen ta. Yanzu haka ma ga number’n Manager’n amman ya kasa kira dan girman kai.
      Seda yammacin ranan ya danna wa manager’n kira, he can’t take it anymore. Manager be d’aga ba a karo na farko se ana biyu nan ma sanda ya kusa tsinkewa.
   “Hello” Manager’n yace bayan ya d’aga.
   “Mr. Azeez, Anas Fauzi ne.”
    “Ohh our youngest billonaire! Kwana dayawa.”
    “Alhamdulillah tun last 2 weeks nake neman ka akacemin ka tafi trip hungary, I had to wait ka dawo.”
    “Taya Kabeer ze maka haka? Besan ko waye kai bane? Ai be fad’a min ba I’m sorry.”
   “Ba komai ya wuce dama aiki nakeson baka.”
   “Toh billonaire inaji…”
  “About last 2-3 weeks kukayi employing ma’aikata koh?”
    “Eh suna nan ma munajin dad’in aiki dasu musamman wata Fannah something yarinyan akoi hardwork ina tunanin k’ara mata matsayi ma.”
      D’an murmushi Anas yayi “ita nakeso kayi firing Mr. Azeez.”
     Ido wuru wuru ya zaro “inyi firing nata kuma billonaire? Mesa?”
   “Saboda ni nace.”
   “Toh nawa kuma zaka bani wannan karan?”
    Murmushi yasaki kad’an again. “Miliyin d’aya yayi?”
   Mr. Azeez lips nasa ya tand’e tas “amman barin samu k’ari ba?” saboda yasan irin kud’ad’en da Anas yakeda.
    “Inde zakayi firing nata zan k’ara maka 1.5 yayi?”
    “Wow! consider it done Mr. Fauzi saisa nakeson aiki da kai wallahi. Gobe gobe za’ayi kamar yadda kakeso.”
   “Good” Anas yace yana me jin dad’i “amman kasan be kamata kayi firing nata haka kawai ba zan turo maka 50k akai se ka bata please make sure ka bata, banaso na bata kud’i dayawa tak’i dawowa wajen aiki”
     “Karka damu Mr. Fauzi zan san yadda zan b’ullo mata da lamarin ta yadda barata fahimci you have something to do with this ba.”
   “Good nagode.”
    “Ai ba godiya tsakanin wa da k’ani. Take care” ahaka sukayi sallama.
    Sosai Anas yaji dad’i dan dolen Fannah ta dawo masa aiki yanzu kuma wannan karan ma better job ze bata yadda bara ta sake tunanin tafiya ba, yasamu yasha coffee iya san ransa. Aiki kamar Personal Assistance nasa tunda dama baida shi. Jira kawai yake gobe ko jibi yayi Fannah ta dawo masa aiki.
    **
       Fannah na zaune d’aki ita da Afrah se hira sukeyi cike da nishad’i. Har wani fresh Fannah ta k’ara dan yadda batta da wani matsala yanzu. Wayarta ce ta soma ruri nan da nan ta duba ganin Yusuf ke kira yasa ta d’aga da wuri. “Assalamu alaikum Yusuf”
   “Wa’alakissalam Fannah ya kike? Ya aiki?”
    “Lafiya qalou, aiki alhamdulillah, naka fah?”
    “Fannah wallahi wajen aiki ya zamo kamar hell.”
   “Mesa kace haka Yusuf?” Ta tambaya cike da rashin fahimta.
    “Wallahi Boss ne Fannah, Boss yazama wani abu daban tun tafiyar ki, da barin ki office d’in wallahi yayi firing mutane sittin da abu ka.”
     “What! Allah shirya!” Fannah tayi exclaming cike da mamaki. “Sittin da abu? Dalili?”
   “Saboda ke mana Fannah, wallahi Boss yayi missing naki frustration na rasa ki yasa yake duk abinda yakeyi.”
    “A’a kam bade ni ba, nikuma me had’ina da Mr. Fauzi? Ai Allah ya riga ya rabani dashi har abada in shaa Allah.”
   “Fannah ki tausaya mana ki dawo please, wallahi kina dawowa komi ze dawo normal.”
  “Yusuf!” Ta kira sunansa cike da mamaki “nima ka tausaya min mana, ashe de baka sona kafi kowa sanin abinda Mr. Fauzi yakemin ni barin aiki dashi shine mafi alkhairi a gareni kukuma Allah k’ara maku hak’uri amman inde dan in dawo aiki k’ark’ashin wancan mugun mutumin ne ka kirani I’m sorry I can’t.” Karap ta katse wayarta.
   “Wani mara imanin ne Ya Fannah?” Afrah dake game a wayarta ta tambayeta.
     “Yusuf ne wai in dawo aiki a Flames Enterprises…” nan de ta labarce mata komi.
   “Ayya amman sun ban tausayi gaskia shege Mr. Fauzi an gasu!” ta fad’a tana dariya. Dariyan itama Fannah takeyi “ai ya gasu ya k’one Allah ya riga ya rabani dashi har abada!”
    Washegary…
 
    As usual k’arfe takwas dadai ya cika wa Fannah a office kap co workers nata suna santa dan hali irin nata me kyau. Chan around 10:30AM tana zaune tana faxing wasu papers aka danna mata kira daga Manager’s office zuciyarta fal taje sam basu tab’a samin matsala dashi ba tun dawowarsa ita ta d’au ma batun promotion dayace ze mata ne. Bayan ta shiga office nasan ta gaishesa cike da girmamawa kamar yadda ta saba da fara’a ya amsata sannan ya nuna mata kujera ta zauna. “Fannah Aleeyu kamar yadda kika sani kina d’aya daga cikin hard working employees d’ina ko kad’an bansan rasaki amman in yazama dole kinga ba yadda na iya.”
   Murmushin dake fuskarta ne ya gushe a hankali. “Bangane ba Mr. Azeez.”
    “Fannah babban matsala na samu da wannan organisation namu wanda yazama dole in rage ma’aikatan da aka d’iba last 3 weeks wanda nakeso da alkhairi kenan wanda kuma ba haka ba, zasu cigaba da aiki nan amman ba albashi. Inasan ki da alkhairi Fannah sesa zan fara sallamar ki and already na riga na samo miki aiki ma me kyan gaske.”
     “Allah sarki Mr. Azeez ni ko ba albashin ‘yan watanni zan maka aiki karka damu, inasan aiki anan sosai.”
    “A’a Fannah” I insist please. “Ga wannan” nan yaciro envelope “dubu hamsin ne ciki albashinki na wata gabad’aya.”
   “Mr. Azeez ai banyi aikin wata ba kayi deducting please seka samu ka biya wasu dashi..”
   “Ni na baki Fannah ki rik’e karki damu”
   “Toh nagode sosai Allah saka da alkhairi, matsalar da organisation naka yasamu kuma Allah takaita.”
   “Ameen” yace yana mata murmushi
  “Toh Mr. Azeez ina ne inda kace ka sama min aikin?”
     “Ba ko ina bane se Flames Enterprises.” Take taji zuciyarta ta buga ai ba Flames Enterprises ba sunan chan wajen, hell shi yakamata ana kiran wajen da.
 
     “Lafiya Miss Aleeyu?” ya tambayeta.
   A kid’ime tace, “a’a, a’a nagode Mr. Azeez gobe in shaa Allah zanje nagode.”
    “You’re welcome, yawwa please karki sanar da wani ko wata maganar da mukayi dake kar su gudu in rasa ma’aikata.”
   “In shaa Allah na gode da erin karamcin da ka min Allah saka.” Da “Ameen” daya amsata ta fice. Jakarta ta d’auka tama sauran ‘yan uwan nata k’arya kan zata gida.
     Bayan ta isa gida ta tarar da duka family member’nta banda Aiman dake school zaune suna hira harda Baba dad’i taji sosai Babanta na samun sauk’i. “Fannah ya haka yau?” Tambayar Mami.
  Murmushi ta musu duka “wallahi matsala aka samu da ma’aikatanmu…” nan de ta zayyana masu komi. Ba wanda yaji dad’i cikinsu saboda sun san wahalar neman aiki.
  “Karki damu ‘yata zamu taya ki da addu’a in shaa Allahu nan da lokaci kad’an zaki sake samun wani aikin.” Baba ya tabbatar mata yana me mata murmushi.
   “Gaskiyan Babanku ne Fannah karki damu akoi Allah.”
   “In shaa Allah Mami gashi kuwa ya biyani albashi na na wata kinga zamu samu mud’an yi siyayya. Afrah zo mu shiga daga ciki.” Shigarsu ciki Fannah tabata labarin aikin da Mr. Kabeer ya nemo mata a Flames Enterprises.
    K’irji ta dafe tare da zaro ido. “Kin gudu baki tsira ba Ya Fannah ya zakiyi yanzu?”
   “Nikuwa na gudu na tsira Afrah banga abinda ze sake sani ma Mr. Fauzi aiki ba. Chab! Aiko Mr. Azeez yazo ya kirani nan gaba ce masa kawai zan nasamu wani aikin daban.”
   Shiru Afrah tayi tana nazarin abu. “Tunanin me kike haka?” Fannah ta tambayeta tare da d’an bugin ta a hannu. “Something smells fishy anan.” Afrah tace tana tunani.
   “Meh kenan?” Fannah ta tambayeta a takaice.
   “Mesa Mr. Azeez ze tura ki Flames Enterprises kinsan me nake gani? Gani nake kamar Mr. Fauzi nada hannu cikin wannan abu.” Shiru itama Fannah tayi tana nazarin abinda Afrah tace. Chan ta murmusa “ko kad’an Afrah kin manta Yusuf yace kullum cikin koran ma’aikata yake ai kinga kuwa dole yana neman masu aiki safe da dare and ko ba dan haka bama I trust Mr. Azeez”
     Kai Afrah ta giad’a nufin ta gane. “Kinyi gaskia kuma fa mude fatan mu Allah baki wani aikin ba sekin wahala.”
    “Ameen Afrah gobe zan shiga nema in shaa Allah.”
***
   Tun k’arfe 9:00AM Fannah tabar gida bayan addu’o’in da su Mami suka ta suburbud’a mata. Mr. Fauzi kuwa yau office nasan ma yak’i shiga yana tsaye bakin k’ofa shi a dole yana jiran isowar Fannah dan tun daren jiya da Mr. Kabeer ya fad’a masa yayi firing nata yakasa hak’ura se Allah Allah yake gobe yayi. Mamaki ne ya cika kowa a building d’in wai yau Mr. Fauzi ke tsaye bakin k’ofa ko wa yake jira se Allah! Ganin har 11:00AM ba alaman Fannah ya dawo ciki da disappointment karara a fuskarsa. Bade ta samu wani aikin ba? In bahaka ba me ze hanata zuwa? Ai sosai Fannah bata wasa da aiki, what could be the problem? Wayarsa ya d’au ya kira Idrees bayan kamar minti biyu Idrees ya iso bayan gaisuwa yace, “yes Boss you called for me.” Giaran murya Anas yayi “aiki nakeson saka and banasan failure, kanajina?”
  “Inaji Boss fad’a min duk abinda kakeso ayi maka.”
 
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 29
BY MIEMIEBEE
 
  “Kasan Fannah Aleeyu ko wacce ta tab’a aiki anan?”
    “Wacce take had’a maka coffee Boss?”
   “Yes ita.” ya amsa sa a takaice.
   “Sosai nagane ta friend na Yusuf ce.”
    “Toh ban tambayeka ba.” Ya tsawata masa.
    “I’m sorry” Boss ya sunkuyar da kansa.
    “You better be, bawani aiki zan baka ba illa spying akan Fannah dana keson kana min, inasan yazamo duk inda zataje dakuma duk abinda take ciki ka sani kana turo min rahoto.”
    “Okay Boss nagane.”
      “Good, karka bari ko da information d’aya ne ya wuce ka, do you get me?”
    “Yes sir.”
   “Good inka min wannan zan baka mak’udan kud’ad’e. Off you go, ga number’nta” nan ya mik’a masa rubucaccen number’n Fannah kan wata paper. “Ka kirata yanzu seka samu kayi tracing inda take.”
     “Yes Sir” nan ya fice.
   _30 minutes later…_
   
     “Hello Boss yanzu Fannah tabar state secreterial.”
    “Good ka shiga ka tambaya min ko aiki suka bata”
      “okay sir.” Nan ya katse wayar ya shiga. Tambayoyi yariga ma receptionist na wajen itako jaka ta riga basa information saboda tagansa kyakkyawa ba laifi, dama da biyu Anas yayi assigining Idrees yin aikin. “Kina nufin har kunbawa Fannah aikin kenan?” Idrees ya tambayeta.
    “Eh Idrees mun bata saboda takardun ta sunada kyau.” Ta fad’a ta na kashe masa ido
    “Okay inasan number’n Manager’n ku if possible.”
   “Sure Idrees” nan ta basa dan sokanci godiya ya mata sannan ya fice “se na kira ki koh?”
   “Okay!” tace masa tana nin dad’i. Aiko yana fita yayi blocking number’nta bata sake ganinsa ba tun daga ranan.
     Anas ya kira “hello Boss nayi tambaya wai eh tasamu aiki a ma’aikatan amman na amso maka number’n boss d’in sekuyi magana.”
     “Excellent! Ka iya aiki” yayi exclaiming “turo min lambar and kacigaba da binta aikinka na kyau.” Bayan minti d’aya Idrees ya masa sendn number’n Manager’n wajen. Da telephone office nasa ya kira Manger’n. Manager’n na ganin Flames Enterprises ya d’aga jiki na rawa.
   “Ranka ya dad’e Mr. Fauzi ina gaisuwa.”
   “Yawwa barka” straight to the point ya wuce “Fannah Aleeyu da kuka bawa aiki yanzu nakeson kuyi firing nata.”
     “Amman Si-”
    Katse sa Anas yayi “zan baka dubu d’ari biyar.”
       “Toh anyi an gama Sir bari in ta dawo gobe ina jiran alert.”
    “Karka damu just do as I say ina jiran feedback.”
       Idrees be bar bibiyar Fannah ba sanda yaga tashiga gida sannan ya kira Anas ya fad’a masa.
     Fannah ta shiga cikin gida da farin ciki fal a ranta ta sanar da family’nta aikin da ta samu sosai suka tayata murna. Washegari ta koma ma’aikatan suka tareta da sad news na fasa bata aikin da sukayi. Zuciyarta taji ya kariya. “Dan Allah kode wani abun nayi kuka hana ni aikin kuyi hak’uri, ina buk’atar aikin nan. Kefa jiya kika kai wa Manager’nku takardu na yakuma yaba, yau kuma kice kun fasa?”
    “Eh an fasa seki k’ara mai please.” Abin tausayi Fannah taja jakarta ta fice wani ma’aikatan ta wuce neman aiki take suma suka bata aiki. Bayan tafiyarta aka koma gidan jiya Idrees yabi sahu yau ma mace yasamu as receptionist d’in ya tsarata yasamu ya ta fad’a masa news dayakeso tare da basa number’n Manager’n.
     Shima kud’i da dama Anas yabasa ya yarda yayi firing Fannah.
    Duk aikin da Fannah ta samu da ta koma washegari se suce sun fasa sun canza mind nasu, sosai abin yake daminta ranan harda kuka. A inda tasamu aiki a k’arshen ne bayan tafiyanta Idrees ya shiga to his suprise yaga wani santalelen gardi as receptionist d’in yasan koda mutuwa zeyi ba basa information da yakeso ze masa ba. Fita kawai yayi ya kira Anas nan ya masa kwatancen ma’aikatan. Meeting Anas yakeda amman yayi cancelling in akan Fannah da coffeen ta ne baya wasa.
    Bayan like 15 minutes Anas ya iso wajen tare suka shigo cikin building d’in atare wajen receptionist d’in suka nufa. Bayan ya gaishesu Anas yace, “take me to your Manager.”
    “Sir I’m sorry amman se in kanada appointment dashi tukuna, me sunanka in duba.”
    “Tambaya ma kake waye shi? Bakasan Mr. Fauzi bane?” Cewar Idrees dake tsaye bayan Anas.
   “I’m sorry Mr. Fauzi amman bakada appointment dashi.”
    “You’re very stupid and zan tabbata an koreka daga aiki anan stupid kawai” Chan ya hango wani na wucewa “hey!” Ya danna masa kira jiki na rawa mutumin ya iso “ranka ya dad’e, sannu da zuwa yau manyan bak’i mukeda a office namu? Kai D’anladi bakasan mutane bane? Ai Mr. Fauzi ba’a had’a masa appointment. Koda yaushe yazo he is welcomed”
    “Ahto gaya masa de” cewar Idrees.
    Kallo Anas ya watsa ma D’anladin sannan ya dawo da kallonsa kan Isah “so nake ayi firing wannan mutumin.” ya nuna D’anladi da yatsa.
    Hak’uri Isah ya soma bawa Anas. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri shekaran jiya ya shigo gari, be sanka bane, kai D’anladi baraka basa hak’uri bane?” Ya daka wa D’anladi tsawa.
   “Kayi hak’uri Sir.” Kallon sa Anas yake cike da rashin isa “sede D’anladin kam. Uhm Isah Mr. Abdullahi na nan kuwa?”
    “Eh Manager na nan mu haura sama please.” Nan sukayi sama kamar yadda Anas ya saba siye mutane da kud’i haka ya siye Mr. Abdullahi. A dad’insa yanzu kap inda Fannah zata samu aiki yayi blocking batada wata option other than ta masa aiki.
  **
   Kuka Fannah take sosai Mami na bata hak’uri. “Haba! Fannah sekace ba muslima ba? Ke da nasanki da rungumar k’addara kiyi shiru kukan ya isa.”
    “Haba Mami abin ba daidai ba, ace duk inda naje se bayan sun d’aukeni in nakoma washegary kuma suce sun fasa.”
    “Ya isa Fannah akoi Allah ki dad’a hak’uri.”
     “Kiyi hak’uri Ya Fannah” cewar Afrah tana bubbuga bayanta a hankali cike da tausayi da damuwa.
    Fannah bata sake lek’a waje ba tun daga ranan. Sosai rashin aikinta yake damunta in kud’in hannunta ya k’are bata san ina zata samu kud’i tabiya kud’in asibiti da magunan Baba ba. Tasan sarai inda a yanzu zata je wajen Anas ze bata aiki amman barata iya jure wulak’ancin sa ba, mutum ne ace ko kad’an baida slightest regard wa d’an adam. Ita dashi har abada in shaa Allah ta gommaci talauci ya kashe ta data sake masa aiki.
 
     _One week later…_
    Haukacewa ne kawai Anas beyi ba yarasa me ke ajiye Fannah har yanzu batazo neman aiki gunsa ba. Gashi koya tura Idrees ce masa yake Fannah bata fita, toh why? Ta hak’ura da neman aiki kenan komeh? Bare iya explaining ya yayi missing coffeen ta ba tun rananda tabar masa aiki har ila yau baicin abinci kamar yadda ya saba ci da. Shi yanzu abu d’aya ne yasan inya aiwatar dolen Fannah zata dawo masa aiki shine in zeje gidansu, gashi dama Idrees yamasa bayanin yadda gidansu Fannah yake basuda arziki. Wayarsa ya d’auko ya kira Ahmad. “Hello Boss good day.”
   “Yawwa kaje ka d’au credit card d’ina cikin mota a bud’e ne kayi duk siyayyan dakasan magidanci zeyi wa family’nsa I mean food items, kayan sawa home appliances komi da komi ka gane?”
    “Yes Boss angama.” Nan ya katse wayarsa. “In baraki dawo ba Fannah I will force you to.”
    5 hours later…
    Anas na zaune a office nasa yana jiran call daga Ahmad baya son se Maghrib yayi, aikuwa a lokacin Ahmad ya kirasa “Hello Boss komai is in place kamar yadda ka buk’ata motan kayan na nan pake a bakin main gate.”
     “Good gani fitowa.” Turare ya sake feshe jikinsa dashi ya giara gashin kansa ya tabbata he is looking okay sannan ya fice. Motarsa ya shiga motan kayan kuwa Ahmad ne ciki yana gaba Anas na biye dashi har gaban gidansu Fannah suka tsaya. Sosai yasha mamaki ashe saisa Fannah batta wasa da aikinta ashe basu da k’arfi ne sosai. Kallon gidan ya tsaya yi dan ko a Bama gidansu yafi wannan kyau.
    Daidai lokacin Aiman ta taso daga islamiya se b’antare charbin Malam dake hannunta take tana nufowa kusa da gidan alokacin data d’aga fuskarta Anas yaga alaman kamannin Fannah tattare da ita nan take ya yanke hukuncin kasancewar ‘yar yarinyar k’anwar Fannah. Daidai tazo shiga gidan ya dakatar da ita ta hanyan kiran ta da “‘yan mata.” A hankali ta d’ago kai tana kallonsa bata gane kamanninsa ba kasancewar yasa sunglasses.
   “Wace ‘yanmatan” ta kalli left and right “ni? Barin d’an maka tambaya bature ne kai please naga kayi fari dayawa”
   Dariya sosai Anas ya tsaya yi sekace ba shi ba, kawai se yarinyan ta tuna masa da Angel nasa Amal.
   “ A’a ni ba bature bane ‘yanmata”
   “ Nifa kadena cemin ‘yanmata, ai Ya Fannah tace ni yarinya ce ba ‘yan mata ba wai ita da Ya Afrah ne ‘yan mata.”
    “Toh Ya Fannah ta miki k’arya ai ‘yan mata ce ke.”
   “Toh kaikuma fa? Samari?” Ta tambayesa tana jefa charbin malam data b’are a baki tare da taunawa.
    “Ni big uncle ne suna na Anas, kinacemin Ya Anas.”
   “Ya Anas.. Ya Anas ni Aiman a ina na tab’a jin wannan suna?” Ta tsaya tana tambayar kanta.
   Yana ciro glasses nasa aiko kamanninsa ya bayyana.
  “Laaaaa!!! Blue eyes na TV. Me kazo yi agidan mu? Ashe ba bature ne kai ba, kazo ne muma asamu a TV’n?”
   Dariya sosai yake wanda ya mugun masa kyau, fararen hak’waransa suka bayyana, dimple nasa d’aya ya lotse. “Kinasan kiga kanki a TV?”
  “Eh mana ai social studies teacher’n mu tace celebrities kawai ake gani a TV nima inasan in zama d’aya.”
   “Toh kar ki damu, yanzu kizo ki kaini cikin gidanku.”
“A’a’a’ahhhh chabdi! Ai Ya Fannah ta hana. Maza basu shiga gidanmu gaskia me blue eyes kayi hak’uri karka sace min iyaye da yayu. You are a stranger.”
   “Kefa kikace kina gani na a TV karki damu b abinda zan miki. Ahmad ina sweet d’incan?” nan Ahmad ya koma mota ya ciro packet na sweet Anas ya amshi, “ungo zo ki karb’a.” Ya fad’i yana mik’a mata.
    “Blue eyes tsakanin ka da Allah baka sa abin sace yara ciki ba?” dariya sosai Ahmad yake.
   “Kice min Ya Anas ba blue eyes ba.”
    “Toh Ya Anas.” Ta fad’a yawunta na d’iga k’asa.
      “Bari kiga” nan ya bud’e ya ciro d’aya tare da sha “kinga ba abinda yamin. Zoki karb’a se ki kaini gidanku. Ya Fannah tasanni, nine Mr. Fauzi. ”
    “Ohhh ashe kaine me sa Ya Fannah kuka.” Yi yayi kamar be jita ba yace, “karb’a mu shiga toh.” Ba musu ta amshi pack na sweet d’in “muje toh Ya Anas.” Bayan ta yabi suka shiga gidan kam ba laifi tsatsaf ba k’azanta.
    “Mami! Ya Fannah! Ya Afrah! kufito munyi bak’o kuma ya bani sweet har packet.” Fannah ce ta soma fitowa ko hijabi batada ‘yar vest ne kawai jikinta tana shan iska.
      “Aiman ban hanaki shig-” bata k’are maganar ba suka had’a ido hud’u da Anas ai a guje ta koma ciki se nishi take. K’wak’walwar Anas sanda yabar functioning na d’an lokaci ganin Fannah ba kayan arziki. “Ke Ya Fannah wa kika gani haka kike wannan nishi” cewar Afrah dake game as always. Kasa magana Fannah tayi kawai waje take nuna mata da hannu. “Meh gamo kikayi?” Kai ta kad’a mata still tana nuna waje. Kafin Afrah ta tashi suka jiyo muryan Mami na masa lale su Mami anga Mr. Fauzi. Lek’awa Afrah tayi tagansa zaune kan tabarma d’aya da Mami.
    Ashe haka bawan Allan keda kyau, yama fi kyau a fili akan a gidan TV lallai Allah yayi hallita. “Ya Fannah Mr. Fauzi nefa! Mr. Fauzi a gidanmu!” ai da gudu tayi wajen sa kayansu taciro kayan sallarta. “Ki sa hijabi mu fita mu gaishe sa. Ma meyazo yi tukun? Halan bikonki” Duk ta kidime se suratai take tayi.
      Hannunta Fannah ta rik’o “ke jakar ina ce? Ina zaki? Meh Mr. Fauzi yazo yi gidan mu? Nashiga uku Allah sa ba sharri ya taho dashi ba.” Afrah ta bud’e baki zatayi magana suka jiyo kiran Mami “Fannah! Afrah! kufito mana Mr. Fauzi nefa yazo.”
    “A’a Mami Anas de” cewar Anas sewani behaving yake kamar d’an arziki. “Kufito da sauri” Mami ta sake k’olla masu kira. “Toh” Afrah tace. “Ya Fannah kiyi sauri.”
  “O’o ni barin fita ba ni yama yasan gidanmu? Ya Allah help me!” Hannunta Afrah ta fisga daga rik’on Fannah ta fice a guje har k’asa ta gaishe da Anas ya amsa da fara’a se murmushin show off yake. “Aiman kawo wa Ya Anas ruwa kinji?”
   “A’a Mami ta bari daga office nake yanzu naci abinci.”
   “Allah Babana ko ruwa bara ka sha ba?”
   “Eh Mami, ina Baba? Ya jikin nasa?” Fannah dake mak’ale jikin window tana jinsa ji take kamar taje ta shak’uresa ji yadda yake abu kamar d’an arziki.
   “Jikin Baba da sauki. Afrah ina Fannah newai? Fannah!” Ta danna mata kira.
     “Na’am Mami” ta amsa kan wanda zatayi kuka. “Kifito mana me kikeyi ne?”
    “Mami gani nan.” Hijabi ta zumbura sewani kumbure kumbure take.
   Koda ta fito bata d’aga kai ta kalli Anas ba shikuwa idanunsa na kan ta rabuwansa daya sata a ido har ya manta.
    “Baki ga Mr. Fauzi bane da baraki gaishe sa ba?” yi tayi kamar bata ji me Mami tace ba.
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 30
BY MIEMIEBEE
Kallon Fannah Mami ke cike da mamaki, wannan ne karo na farko da Fannah ta sab’a wa umarninta bakuma tare da ta nuna damuwa ba.  “Fannah dake fa nake magana, meke damunki ne? Baraki gaishe sa ba?” Ta sake tambayarta. Nan ma shiru tayi, a kunyace Mami tace, “Anas kayi hak’uri bansan meke damun Fannah ba.” Murmushi yake kaman ba shi ba “ba komai Mami maybe bata san yin magana ne” blue eyes nasa ya d’ago yana kallonta sosai, haka kawai yasamu kansa cikin niahad’i in yana kallon innocent face nata, sarai taji yadda yake kallonta amman ko d’aga kai batai ba. “Fannah tunda baraki gaisheni ba ni zan gaisheki ina wuni?”
     Shiru tayi bata amsa ba, Mami de tashiga cikin duhu wai ace Mr. Fauzi na gaishe da Fannah amman barata amsa ba. “Anas kayi hak’uri dan Allah bansan meke damun Fannah ba yau, Afrah ko kunyi fad’a ne?”
   “A’a Mami ba abinda ya had’a mu.” Afrah ta fad’i cike da zumud’i se satan kallon Anas take.
   Giaran murya Anas yayi “uhm Mami nasan kuna mamakin ko me nazo yi anan koh? Bikon Fannah nazo yi, dama misunderstanding muka samu tabar min aiki akan had’a coffeen da take min ne tace ta gaji dayi sede in zan bata aikin daya fisa nikuma alokacin banida aikin da zan bata.”
 
            Baki wangalau Fannah ta bud’e tana kallon ikon Allah yanzu ko kunya baiji yake wannan k’arya. Kut lalle! “Mami walla-” ta gwada kare kanta.
       Katse ta Mami tayi “se yanzu bakin ki yaga daman bud’uwa Fannah? Toh kiyi shiru Anas ya gama, ina jinka Baba na.” Idanun sa ya d’aga yana kallonta, itama kallon nasa take, murmushin mugunta ya saki mata wanda ta murgud’a masa baki in return tare da kawar da kallonta daga garesa. “Yawwa, shine tayi resigning amman yanzu da nake neman Personal Assistant (PA) kuma gashi takardun ta sunada kyau zan d’auke ta aiki. Albashi dubu d’ari biyar da kuma weekly allowances N5,000.”
          “Alhamdulillah!” Mami ta fad’i cike da murna. “Alhamdulillah! Aiki har gida Allah ya kawo miki Fannah, wallahi Anas ba abinda zance sede Allah maka albarka ya k’ara d’aukaka da girma, aiki ba inda Fannah bata nema ba amman seta koma washegari se suce sun fasa, abin de ba dad’i”
    “Fannah ke baki iya godiya bane?” Mami ta tambayeta. Shiru tayi kamar bata jita ba.
    “Mami kibar Fannah yau kawai bata san magana ne, ai mutane yanzu sun sa san kai a gaba, su yasu kawai suka sani. Se hak’uri.” Idanunsa ya d’aga yana kallon Fannah dake tsaye har yanzu ta had’e gira gu d’aya. “So Fannah zaki dawo min aikin? Tunda na canza miki post yanzu”
      “Anas yanzu har seka tambaya ko zata koma ne? Ai komawa ta riga ta koma kawai ka fad’i yaushe kakeson tayi resuming office.”
   “Mami!” Fannah takira sunanta cike da takaici. “Wai me haka?”
    Sanyi yaji a ransa jin muryarta kawai.
       “Eh mana Fannah, a jinki akoi inda zaki samu aiki me kyau haka ne? Gaskia Anas mungode sosai sosai Babansu na bacci da ya maka godiya shima.”
    “A’a Mami ba komai nine da godiya. Gobe nakeson Fannah ta soma aiki.”
      “Allah kaimu Anas, In shaa Allah a goben zaka ganta” Hannu yasa a aljihu ya ciro bandir na d’ari biyu tare da ajiyewa gaban Mami “ga wannan a saya wa Baba magunansa dashi da kuma sweet wa Aiman ko?” ya dawo da kallonsa kan Aiman dake manne a jikinsa se mamakin gashin hannunsa take.
   “Yeyy! Ya Anas nagode. Ya Fannah ba sekin sake min rowan naki ba Ya Anas yace a siya min” kallo Fannah ta watsa mata wanda batasan Anas na kallonta ba.
   “Anas Babana da wahala haka? Toh mungode Allah saka da alheri.” Fannah ji take kamar ta k’urma ihu ita wallahi barata koma masa aiki ba sede sama da k’asa su had’u.
    “Ermmm Ahmad!” ya danna masa kira nan Ahmad dakw waje yashigo bayan ya gaishe dasu Mami Anas yace ya shigo da kayakin. Dama already yariga ya tara almajirai nan suka soma shigowa da kayaki. Ba Mami kad’ai ba har Fannah sanda tasha mamaki wato siye mata iyaye zeyi da kud’i da kayan duniya, lallai kuwa.
      Kap tsakar gidansu sanda aka cika da kayaki tun Mami da Afrah suna godiya har suka gaji sukayi shiru. Addu’a sosai Mami ta riga ma Anas tana suburbud’a masa albarka ga kyautan kud’i ga kuma na kaya, abinde ba’a cewa komi. “Anas kace ko ruwa baraka sha ba? In aika Aiman ta siyo maka ko maltina mana.”
   “A’a Mami ba komai”
     “Gaskiya Anas ba abinda zance maka, ka gama mana komi naso ace idan Babansu biyu wallahi yamaka godiya, Allah saka da alheri ya k’ara  bud’i”
     “Haba! Mami ai ba godiya tsakaninmu, ya isa please.”
   “Toh ina zuwa, Afrah biyoni.”
    “Afrah kad’ai Mami nikuma fah?” Cewar Aiman “ni ma sena bi ku.” Cak ta tashi daga gefen Anas ta bi bayan su Mami zuwa d’akin Baba. Ya rage daga Anas se Fannah itama juyawa tayi zata shiga d’akinsu ya mik’a dogon hannunsa ya cafko ta da hijabi chak ta tsaya ba tare da ta kalle sa ba tace, “Mr. Fauzi ka sake min hijab.” K’in sakewa yayi, ya mik’e tare da shan gabanta yana d’auke dawani murmushin mugunta a fuskarsa.
       “Stop pretending, nasani you miss me.” Yace da ita.
         “Miss you? A dalilin me zanyi missing mutumin da yake sa ni kuka all thetime? Mr. Fauzi kasan meh? Ni barin sake koma maka aiki ba, na bari na bari forever, ko coffee maker’n ka barin sake zama ba bale PA, kuma wannan tarukucan kayakin daka kawo ka tattara ka mayar dasu inda ka kwaso su bama buk’ata.”
      “Ai aiki min kin riga kin dawo k’arfe 8:00AM gobe don’t be late, wannan kayaki kuma anan zasu zauna, tunda kikayi resigning ba tare da kin sanar da ni ba nima haka zan  dawo dake ba tare da sanin ki ba. Karki manta everything can be bought with money kamar yadda na saya family’nki yanzu. Inba wai so kike ki b’ata wa Mami rai ba zaki dawo min aiki gobe.”
     “No Mr. Fauzi you are wrong, not everything can be bought with money, aiki maka kuma na riga na bari ba dawowa.” Hijabin ta ta
“Am I clear?” Ya tambayeta.
   “Yes” tace murya chan ciki-ciki. “Good” daidai lokacin wayarsa ya soma ringing take ya d’aga “okay I’m on my way.” Ding! ya katse. Suit nasa ya jawo yasa yasake feffeshe turare jikinsa, Fannah duk tana tsaye ko kallon direction nasa batayi bale ya chakka mata magana. Wayoyinsa ya kwasa “follow me” yace da ita. A sanyaye tabi bayansa ganin ya nufa wajen personal elevator’n sa yasa ta juya dan bin na public kafin ya mata wani rashin mutuncin, duk abinda tasan ze jawo masu matsala k’ok’arin kiyaye sa take. Sanda ya bud’e yashiga elevator’n sannan yayi noticing Fannah bata biye dashi chan ya ganta tana nufan gun d’ayan elevator’n. “Miss Aleeyu!” ya kira sunanta a tsawace chak ta tsaya tare da juyawa. “Baki ji me nace bane? I said follow me.” Ya sake nanata kansa.
        “Sir-” bata k’are maganar ba ya katse ta “acikin rules d’ina na fad’a miki banasan muna musu.” Kanta sunkuye ta je ta samesa tana shiga ya rufe elevator’n, daidai nan wayarsa ya soma ringing daga side pocket na suit nasa, yana ciro wayar number ya bayyana kai bayan yayi nazarin wake kira ya d’aga danko baya saving number’n ‘yan mata a wayansa in bawai ta kama ba “hello Salmah?”
   “Cute eyes, ya kake?” tace dashi
   “Lafiya” ya amsa ta.
    “Cute eyes godiya nake son sake maka, dress daka kawo min ya had’u sosai, thank you.”
  “Don’t mention hun, zani meeting yanzu zan kiraki later.”
  “Okay cutie.” Nan yayi hanging. Fannah dake sauraransa kai kawai ta kad’a, dan aikinsa kenan a ‘yan satukan data masa aiki kwanaki bata san ‘yan mata nawa yayi dumping ba. Tsantsan so yake nuna masu na ‘yan kwanaki yana gaining trust nasu seyace suyi break up, ita ta rasa wani erin player ne Anas.
    Elevator’n na bud’uwa ya sa kai ya fita itama haka tana biye dashi. Wajen da ake ajiye masa key ya nufa chan yama driver’nsa magana dan yau baya jin driving. Bayan sun isa wajen motar nasa driver ya bud’e masa k’ofa “enter” yace da Fannah. Cike da mamaki take kallonsa kamar ya enter ina yakeson kaita?
    Katse mata tunani yayi, “incase kina wondering ko zan kaiki cin abinci ko shopping ne you are mistaking, you are my PA duk inda zanje dake zanje so get in.” Miyau ta had’iye ta shiga ta wuce can k’arhen gefen motan a yayinda shima ya shiga. Haka kawai taji zuciyarta na bugawa duk sanda ita da Anas suke kusa da juna se tana jin wani eri ba dad’i. Bayanin inda zasu yama driver’n a hankali ya soma tuk’i. Ita Fannah ta rasa wani erin san AC Anas yake, hijabi ne a jikinta amman sanyi takeji, hijabin nata ta duk’unk’une dan sanyi, ganin haka Anas ya saki murmushin mugunta ta gefen da dimple nasa yake. “Moosa ka k’ure AC’n zafi nakeji”
    “Okay Boss.” Nan ya k’ure tas! take motan ya d’au wani irin mahaukacin sanyi kallonsa Fannah ta tsaya yi, wato ya gane sanyi takeji shine dan mugunta ya k’ara, ita ba ma wannan ba, duk sanda tasha sanyi sosai pneumonia’n ta tashi yake tun lokacin da akayi raping nata a Bama ruwa ya mata duka take fama da pneumonia tashi tashi.
      “Don’t break my rules nace miki banasan kallo dayawa.” Bata ce masa komi ba ta kawar da kanta dakuma sake duk’unk’une kanta cikin hijabin. Kansa ya jingina jikin kujeran tare da rufe ido bada dad’ewa ba wayar Anas ya soma ruri ganin wa ke kira ya d’aga da sauri “hello an samun?”
   “Yes sir ga details d’in.” Cewar mutumin
    “Okay d’an tsaya please let me get a paper”  Juyowa yayi ya kalli Fannah, “ina jotter’nki?”
   “Jotter kuma?” Ta tambayesa cike da rashin fahimta.
         “Hold on please” yace da mutumin da suke waya sannan ya dawo kallon sa kan Fannah “yes you are my PA ya kamata duk inda zakije yazamto akoi paper da pen a tattare dake saboda kina jotting down abubuwan da nake buk’ata.”
    “I’m sorry” tace kanta a sunkuye.
    “Sorry? Meaning bakida ko paper knan?”
   “Yes” ta amsa sa.
     “Bakisan yau zaki fara min aiki bane da barakizo da shiri ba?”
   Farar jakarta side bag dake rataye kan shoulder’n ta Anas yasa hannu ya finciko, karap ta kama “Sir excuse me meh zaka min da jaka?”
    “Ki sake nace.” Yana ja tana ja “tunda bakida pape,  rubuta details d’in zanyi akan jakan naki gobe baraki manta ki taho da paper ko jotter ba.”
   “Haba Sir taya zaka min rubutu a jikin jaka?”
     “Haka kikace?” Wayar ya mak’ala a kunnensa tare da tarewa da kafad’arsa kafin ta fahimci me ya ke shirin yi kawai taji yaja hannunta ya bud’o tafin hannunta tare da ciro biro daga aljihun suit nasa. “Yes David ina jinka, tell me the details.”
 
    “Mr. Fauzi me haka? Ka sake min hannu!” K’ok’arin fisgan hannunta take amman takasa dan yadda ya rik’e gamgam kafin ta sake wata maganar har ya fara mata rubutu kan tafin hannu. Hawaye take taji yana ciko mata a ido da k’yar tasamu ta shanye kukan dan nasihan da Mami ta mata jiya na tadena yawan zubda hawayenta gabansa. Hannunta ya mayar kamar paper harda yin cancelation, kallonsa ta tsaya yi sanda ya gama sannan taja hannunta a hankali. “In kika kuskura kika bari ya goge you’ll answer to me.” Sanin santsin hannunta nan da ‘yan mintuna rubutun ze gushe tashiga damuwan Anas again kawai tafito da wayar ta daga jakarta tayi copying duka details d’in ciki. Yana kallonta bece mata komi ba can data gama yace, “Allah sa wannan abin da kike kira waya yayi saving details d’in da kyau in bahaka ba you’ll get it from me.” Bata tanka sa ba ta mayar da wayar cikin jaka ta sake duk’unk’una kanta cikin hijabinta dan sanyi tana kallon window.
    A haka har suka isa destination nasu, nan take tafito daga motar bayan driver ya bud’e wa Anas yafito shima tabi bayansa tafiya take kanta a k’asa duk inda suka shiga gaishe da Anas ake. Chan sama suka haura zuwa wani hall manyan mutane ne ciki tas kowa da suit. A kujerar tsakiya Anas ya zauna take kowa ya gaishesa ita haushi ma mutanen suke bata gashi de almost dukansu sun girme Anas amman wai suna gaishesa ai ba laifin sa bane baya mutunta d’an Adam jibi yadda ya mayar mata da hannu kamar takarda d’azu, tsuka taja wanda bata san sanda yafito fili ba aiko tuni hall d’in ya d’auka kowa ya juya yana kallonta cike da mamaki harda shi Anas d’in. “I’m sorry please” yace da mutanen wajen “excuse us please.” Nan ya mik’e kafin Fannah tayi tunanin wani abu kawai ya fisge hannun ta yaja be tsaya ko ina ba se a bakin k’ofa. “What ia your problem? Meke damunki da zaki ja tsaki haka? Kinsan ko suwaye wad’ancan mutanen kuwa dazaki ja tsaki gabansu?”
   “I’m sorry” tace kanta a k’asa.
   Kallo ya bita dashi sama zuwa k’asa. “You better be, maza mu koma ki basu hak’uri.” Neck tie nasa ya giara ya shige ciki tana biye dashi a baya. Bayan sun shiga tabawa mutanen hak’uri duk suka giad’a kai da nufin sun hak’ura. Daman tsaye take kusa da Anas gudun kar ta sake masa abin kunya ya nuna mata kujera chan k’arshen hall d’in taje ta zauna. Tayi zaman zama gashi ba abinyi, bacci kawai ta mik’e kan kujeran tanayi har aka k’are meeting d’in bata sani ba. Anas ne yazo k’arshen fita chan ya hangeta tana bacci tsuka yaja sannan ya nufa kanta ya tsaya chan ya tsuguna daidai fuskarta tare da k’ure mata ido bacci take a hankali ba alaman tashin hankali tattare da ita, tayi pillow da hannunta ta hanyan aza kanta kan hannayenta biyu. Kallonta yake kusan na minti biyu, chan kad’an daga cikin hijabinta ya fad’o kan fuskarta hannu ya mik’a ze giara aiko daidai lokacin ta tashi a razane taja da baya ganin Anas a gabanta meyake shirin mata? Ina sauran mutanen sukaje?
    Kunya sosai Anas yaji, yanzu setace kallon ta yake ta raina sa. Ni Miemie nace daman me kake?
     “Gomma da kika tashi, da nasa an kawo min ruwa na watsa miki. Ni bansan wace erin lazy PA ce keba, daga zuwa meeting se bacci. Bakisan ya kamata duk abinda akeyi kema kisa kunnen ki kina saurara ba? This should be the last time.”
     Sauraransa kawai take amman d’an baccin datayin nan ya mugun sa mata yunwa. “Lets go” yace da ita nan ta mik’e tare da bin bayan sa. Kamar d’azu haka driver ya bud’e mota bayan ta shiga shima ya shiga. Akan suyi hanyan office nasu seta ga driver yabi wani hanyan daban. Rabin zuciyarta tana ce mata ta tambayesa ina zasuje, rabin zuciyar kuwa na hanata dan ko ta tambayesa ba amsata zeyi ba, banda ya gasa mata magana. Shiru tayi tana ganin ikon Allah.
    Chan gaban wani makeken hotel taga driver yayi parking k’arfin bugun zuciyarta taji ya k’aru meze mata a hotel? Innalillahi nan tashiga tsoro kasa rik’ewa tayi ta tambayesa. “Sir please me zamuyi anan?”
   “Abinda zuciyarki ke saka miki.” ya bata takaicaccen amsa.
    Wani irin tsoro taji ya sake rufeta. “Sir dan Allah kayi hak’uri.”
    “What a dirty mind dake, me da kike tunani zamuyi anan? A tunanin ki d’aki zan kama mana? LOL inma zan kama d’aki nan bada yara kaman ki ba. Abinci nazo chi in kinajin yunwa kuma lets go.” Shiru tayi bata basa amsa ba, ji take kamar ta nitse k’asa dan kunya mesa hankalin ta yaje da nesa haka? Abinci yazo ci bawani abu ba ta tunatar da kanta.
    Tana kallonsa har ya fice daga motar zuwa hotel d’in. Yunwa takeji amman barata ci abinci dashi ba, amman kuma batasan k’arfe nawa ze turata gida ba shida bakinsa yace mata in aiki yayi yawa ze rik’eta fiye da k’arfe 4:00PM. Wayarta ta ciro dan duban time k’arfe 12:30AM taga wai lalle sun sha awowi suna meeting kam. A hankali tafito daga motar zuwa cikin hotel d’in. Ba kowa wajen cin abincin da alama yayi reserving ne. A kujeran dungu ta hangesa da wayansa a hannu da alama jiran order’n sa yake. Har yanzu beyi noticing nata ba se sanda wani security yashigo “Miss kiyi hak’uri please anyi reserving wajen nan, nanda ‘yan mintuna meshi ze tafi seki dawo.”
      “I’m sorry” tace masa, a sanyaye ta juya zata koma cikin mota Anas ya danna mata kira “Miss Aleeyu.” Chak ta tsaya ba tare da ta juyo ba “security let her in.”   “Miss Aleeyu Mr. Fauzi yace a barki ki shiga yana kiran ki.” Idanunta gam ta rufe rabin zuciyarta na ce mata tace wa security’n zata tafi rabi nace mata taje kiran Mr. Fauzi chan tabi zuciyar data ce mata ta koma cikin motan. Taku d’aya ta k’ara ya sake kiran sunanta “Miss Aleeyu!” wannan karan a tsawace b’ari ta soma wai mesa bare na kiran ta da sunanta ba se dana Babanta. A hankali ta juya k’afafunta suna rawa kanta sunkuye a k’asa, sejin idanunsa take a kanta, ignoring kawai tayi ta k’ariso gaban sa. Bata ce komi ba “sit” yace mata.
  Baki na b’ari tace, “Ss… Sir zan koma mota.”
    “I said sit!” Ya daka mata tsawa. Bata san sanda taja kujerar dake kallonsa ba ta zauna hannu ya d’aga waiter’n ya iso “make the plates two.” yace masa.
   “Okay Sir!”
    Tun bayan tafiyan waiter’n suka soma zaman kurame Anas kam se faman latse latse yake a waya. Bayan kamar minti uku abincinsu ya iso aka ajiye wa Anas nasa sannan itama aka ajiye mata nata. Ita kajin kai ne ma yamugun tsorata ta, batada kud’in biyan wannan plate dududu da dubu d’aya ta fito da, gashi already ta kashe d’ari biyu a zuwa kamar yadda zata kashe d’ari biyu a komawa d’ari shida ne kawai ze rage mata wanda tasan ba siya mata plate na gabantan zeyi ba.
    “Uhm please plate d’innan nawa?” Ta tambayi waiter’n. “N1,500 ne Miss.” Ya amsata a takaice yana murmushi. Miyau ta had’iye tare da waro idanunta dariya sosai tabawa Anas wanda da k’yar ya danne tare da yin tarin k’arya sarai ta gane da ita yake. Tace a mayar da plate d’in kuma tsoro take ji chan ta tuna zata je ta tambayi driver’n Mr. Fauzi cikon kud’in yaso ko gobe seta maido masa. Bayan waiter’n ya tafi ta mik’e tare da d’aga plate nata da nufin zuwa wani table.
    Blue eyes nasa ya d’ago yana kallonta. “Ina kuma zakije?”
   Kanta a sunkuye tace, “d’aya daga cikin tables d’in.”
   “Wannan kuma meya samesa?”
  “Babu kawai nag-” bata k’are maganar ba ya katse ta “sit.”
   “But Sir-” nan ma ya kuma katse ta “I said sit!” yafad’a a tsawace. Carap ta zauna tama kasa ko kallon abincin nata se yatsun ta da take murzawa wanda suka had’a gumi. Bayan yaja plate nasa gabansa ya d’au spoon “eat!” yace mata.
   Kai ta d’ago a hankali tana kallonsa shima kallon nata yake “ko cin abincin ne baki iya ba in kira d’aya daga cikin waitresses su baki?”
    “A’a na iya” tace tare da sunkiyar da kanta tana kallon abincin dakuma kajin da suke mata salamu alaikum!
   “Good, then eat nanda 20 minutes zanbar nan kuma ba jiranki zanba” yana kaiwa nan ya ajiye wayarsa yasoma cin abincinsa hankali kwance yakai kusan spoons biyar Fannah bata ko tab’a plate nata ba. Gugugur! Cikinta yayi k’ara sakamakon hakan yasa Anas dariya sosai amman seya danne yayi tari kad’an. Kunya taji sosai kamar ta nitse k’asa. A hankali ta d’au spoon d’in duk Anas na kallonta ta gefen ido.
       Da k’yar ta iya takai spoon d’aya baki sosai abincin ya mata dad’i, da kad’an kad’an tasamu tana cin abincin saboda yadda Anas yayi kamar besan tana zaune ba, abincinsa yake taci be sake kallon ta ba. Ko daya gama be motsa ba, bakinsa ya goge ya d’au wayarsa yana latsawa da wayo yake satan kallonta. Fannah kam ta baje se cin abincinta take, dam ta cika bakinta da fried rice d’in guda gudan salad cream d’in yamata staining baki kunya sosai taji da suka had’a ido da Anas. Take ta ajiye spoon d’in da k’yar ta had’iye abincin bakin nata sannan ta kora da ruwa ta goge bakinta bece mata komi ba yakira waiter’n, ganin haka Fannah tace, “sir excuse me please.”
      Har ta tashi Anas yace, “ba se kinje aran kud’i wajen driver ba I’ll pay for it” kunya sosai taji wai ya ma akayi yasan abinda takeson yi kenan? Wannan Mr. Fauzi se Allah. Cike da kunya da k’yar tace, “thank you.”
   *© miemiebee*
TANA TARS DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 32
BY MIEMIEBEE
Bece da ita komai ba yabiya masu kud’in abincin, ahaka suka dawo cikin motar suka koma office, a lokacin azahar yayi. “Sir excuse me zanje inyi sallah.” Ba tare da ya kalle taba yace, “you have 5 minutes to do so, in kuma kika tsaya hira da Yusuf kikayi delaying d’ina you’ll answer to me.” Kai ta giad’a a hankali ta ajiye jakarta ta fice bayan ta idda sallah suka had’u da Yusuf hira yakeson janta dashi amman sauri take kar ta makara Mr. Fauzi ya samu abin magana kai. “Yusuf kayi hak’uri please, minti biyar Mr. Fauzi yabani ko second na k’ara ze ci mutunci na kabari in aka tashi zanzo musha labari har se sanda ka gaji.”
    “Toh Allah taimaka aiki as PA wa Mr. Fauzi kam seda hak’uri.” yace da ita yana tausaya mata, a haka ta koma office nasa,yana zaune kan kujera yayi focussing kan laptop dayake aiki akai kafin ta zauna yace taje ta had’a masa coffee bayan ta had’a tazo ta ajiye masa. “Kinga flasks biyu da suke can?” Ya nuna da yatsa. “Eh nagani” ta amsa a hankali.
   “Good ki cika min su da coffee.” Ido ta bud’e tana kallon ikon Allah yanzu dan tsiya har flask biyu? Ya kai ina?
   “Bakiji bane?”
   “Naji” ta amsa a takaice. “Good off you go.” Bayan ta isa wajen ta juyo tana kallonsa, shan coffeensa yake hankali kwance yana duban laptop tare da yin wasu ‘yan rubuce rubuce time to time “Sir ba d’an wani babban roba ko kwanon da zan had’a ciki se injuye cikin flasks d’in tunda dayawa zan had’a coffeen?” Ta tambayesa a nitse.
    “Babu kuma koda akoi ma ba barin ki zanyi kiyi amfani dashi ba ga cups nan kina had’awa ciki kina juye har ki cika.” Wannan wace erin mugunta ne kwata kwata cup d’in fa k’ananu ne erin teacups d’innan yaushe har zata cika wannan manyan flasks.
    “Sir hakan ze d’au lokaci ba gara naje kitchen na ari bowl ba.”
    “Bara kiyi ba, kinga banasan musu na fad’a miki stop breaking my rules in zaki had’a good in barakiyi ba kuma in kira Mami in sanar da ita kina min rashin kunya.”
   Chan k’asa k’asa tace, “ba se kanada lambarta ba.” Murmushi kad’an yayi, “haka kikace?” Wayarsa ya d’aga ya kai kan contact na Mami da yayi saving just d’azu data ajiye jakarta zuwa yin sallah. “Zo kiga” bayan ta k’ariso taga eh fah lambar Maminta ne to ya akayi ya samu? Ba tare da tace masa komi ba ta koma ta fara had’a coffeen cikin teacup d’in tana juyewa cikin babban flask d’in. Tayi hakan kusan sau goma amman data gwada jijjiga flask d’in taji har yanzu da saura cikansa ko rabi, gashi ko soma cika d’ayan ma batai ba haka kamar tayi kuka ta samu ta cike d’ayan da k’yar ta zauna dan ta huta.
      “Kin gama ne?” Ya tambayeta
   Kamar wacce bara tayi magana ba tace, “da saura d’ayan.”
   “Well? Me kike jira toh?”
   “Sir hannu na yagaji barin d’an huta please.”
    “Hutu?” Ya tambayeta yana murmushi. “Kin tab’a ganin inda aka huta a office? Get up ki cigaba we have thousand of things to attend to.” Haka kamar ta kashe kanta ta tashi ta soma cika d’ayan har tsayawa take tana mik’a hannunta Anas kuwa ganin haka dad’i yake masa nan gaba zata sake barin masa aiki ba tare da ta sanar dashi ba seya biya duka coffeen dayayi missing time da ta tafi. Tana gamawa ta koma zata zauna, kafin ta zaunan ya kirata fuskarta ta yamutsa kan kashi sannan ta nufa table nasa.
         “Ina details dana rubuta a hannun ki d’azu?” Jakarta ta koma ta ciro wayarta takai kan inda tayi saving sannan ta tura masa gabansa “gashi.” Kallon wayar nata ya tsaya yi sekace bashi ya d’auka ya copy number ciki d’azu ba. “Wannan shi kike kira da waya?” ya tambayeta. Sosai tambayarsa ya bata mamaki haka kuma ya bata haushi taga de wayarta bara a zagesa ba, tecno ce D7 ba abinda bayayi, duk abinda iphone 6s nasa da samsung galaxy 6 edge nasa dayake tak’ama dashi taga nata ma yanayi kawai de d’an cracks ne wanda basu fi uku akai ba. Amsa daidansa ta basa “shine, kuma naga ga details da kake buk’ata a kai.”
    Biro da paper ya mik’a mata “ungo copy it down for me banasan wannan fashasshen screen nakin ya tsaga min hannu.” Kallonsa tayi tare da kad’a kai kamin ta amsa ta yi copying masa neatly bayan data gama ta mik’a masa d’aga wa yayi yana kallo ya d’au batada clear and neat handwriting ne da seya samu abin magana kai se yaga kamar tafi sa iya rubutu ma dan haka ya gwada yin shiru amman shegen neman maganansa bare barsa ba. “I don’t think wannan wayan kin zena recieving calls da emails me kyau yakamata asan nayi.”
  “Sir nifa waya na ba abinda ba yayi, kuma naga ta nan nake answering calls naka da.”
   “Da kikace, ada dakike as my coffee maker yanzu kuma you are my PA abin kunya ne ma in shiga dake cikin jama’a da wannan abin da kike kira da waya.”
      Kasa rik’e bak’ak’en maganganunsa tayi yanzu kam, abin nasa yayi yawa. “Excuse me Mr. Fauzi just because ina aiki k’ark’ashin ka be baka izinin looking down on me ba, I’m not ashamed ko ina zan shiga da waya na tunda ba wani ne yasaya min ba ni na saya da kud’i na.”
      “Wannan kuma ke ya dama na fad’a miki cikin rules naki banasan ina fad’an abu kina fad’a kema ba, I’m your Boss duk abinda na fada koda ba haka bane dolen ki  kiyarda in baki san me kalman respect ba kisani yau.” Telephone nakan table nasa ya ja tare da danna ‘yan lambobi akai “hello? Akoi iphone 6 gold ne a shop naku?”
    On the other side matar tace, “yes Sir akoi.”
  “Good akawo min guda d’aya yanzu the money will be delivered very soon.”
  “Okay Sir thank you.” Kallon sa Fannah ta tsaya yi iphone 6 ma waye? Inma wa ita ne toh ya kwantar da bokatin hankalinsa ba amsa zatayi ba, tecnon ta ya isheta.
    “Stop starring at me” yace da ita yana me cigaba da abinda yakeyi cikin laptop d’in. Bata ce masa komi ba takoma ta zauna shiru tana mamakin hali irin na Anas. Bayan kamar minti goma knock ya shigo daga k’ofar office nasan. “Get the door” yace da ita hankalinsa kan abinda yakeyi. A sanyaye ta mik’e ta bud’e mace tagani sanye da uniform da k’aramar shopping bag na tambarin AA communications a hannunta. Bayan ta gaishe da Fannah ta mik’a mata leather’n, amsa Fannah tayi ta kai wa Anas tare da ajiye masa kan table wani card ya ciro ya mik’a mata da nufin takai wa matar tana kai mata, ta amsa tayi godiya sannan ta fice, ciki Fannah ta dawo kafin ta zauna Anas ya kirata. A gaban table nasa ta tsaya a yayinda ya mik’o hannunsa da nufin ta ajiye masa abu kai. Itako bata gane me yakeso ba dan haka ta tambayesa “excuse me?”
      “Bani wayarki” ya fad’a a nitse. Zatayi magana ya tsawa ta mata “nace bani wayarki! Don’t let me repeat myself.” Tsabagen tsoro bata san sanda ta ajiye masa wayar a tafin hannu ba. Bayan wayar ya bud’e tare da ciro sim nata “Sir meh zaka min da sim card?” Ta tambayesa ko d’aga kansa beyi ya kalleta ba bale ya amsa ta, daman micro sim cikin wayar tatan, nan ya bud’e leather’n ya ciro sabuwar iphone 6 pil daga ciki ya sa sim d’in ciki wayarta kuwa ya jefa a dustbin kusa da shi.
      “Excuse me! Mr. Fauzi taya zaka jefar min da waya a dustbin da kud’i fa na saya in kai bakasan almubazaranci ba kyau ba toh ni nasani” wajen dustbin d’in ta nufa da nufin zaro wayarta karap ya d’aga ya kai d’ayn gefen. “Sir ka bani wayata.” Drawer’n dayake ajiye kad’an daga kud’ad’ensa ya bud’o tare da ciro bandir na naira d’ari ya ajiye kan table d’in “I’m sure wannan yayi kud’in wayarki. Take ita tare da sabon wayanki.” Bandir na d’arin ta d’aga “zanje in sake siyan sabon waya kalan nawa in chenji ya rage zan dawo maka dashi amman ni barin karb’i iphone naka ba bana buk’ata.”
     “Miss Aleeyu!” Ya kira sunanta a tsawace. “Kap building d’innan bame gaya min magana, bame crossing d’ina se ke. Ko a gida in nayi magana ba’a objecting d’ina saboda haka ki mayar da hankalin ki, I’m your Boss not your friend.” Yayi lecturing nata cikin tattausar murya. “Wannan yazama karo na farko nakuma k’arshe da zan miki magana ko in saki yin abu kimin musu. Ki d’au iphone d’in, I don’t care ko kin koma kin sake siyan kalan wancan abinda kike kira  waya dashi all I know is da wannan wayar zamuna business dake, now take it.”
    Shiru tayi chan ta mik’a hannu ta d’aga da kwalin duka. “Good” yace tare da mik’ewa “follow me.” Ba musu ta mara bayansa still a floor na saman yakaita zuwa wata office a saman aka rubuta MISS ALEEYU ajikin kuwa aka rubuta PERSONAL ASSISTANT bayan ya bud’e k’ofar ya shiga still tana biye dashi office ne babba me kyan gaske da table na katakon zamani da kuma kujerun office guda biyu, kan table d’in laptop ne seda telephone, dasu fax and printing machine da cup cike da pencils da biro da sauran office equipments irinsu stepler, pin, glue, dade sauransu. Gefe guda kujerar cushion ne 3 seater dogo me kuma fad’in da za’a iya kwanciya akai se ‘yar k’aramar fridge dakuma dispenser se kuma split AC dakuma toilet a ciki. Sosai office d’in ya had’u ya kuma yima Fannah kyau dan se kallace-kallace take kamar zata karya wuyar ta.
     “Kallon ya isa haka ba sekin karya wuyarki ba” yace da ita cike da kunya ta daidaita kallonta gu d’aya. “Kin iya karatu ba sena fad’a miki ba, nan office naki ne as my personal assistant kamar yadda kika karanta rubuce a bakin k’ofar. Duk wani abinda zaki buk’ata akoi anan, ba kuma na baki office bane dan kisamu wajen yin bacci da hira da saurayin ki aiki ne yakwo ki nan, wancan telephone should stay on always, karki kuskura koda wasa kiyi disconnecting daga jikin plug na bangon saboda dashi zan na miki magana as well as other staffs, clear?”
    Kai ta giad’a “yes.”
    “Good saboda haka yanzu ba ruwanki da office d’ina fashe ni na kiraki, nima zan huta da kallo, for now ki biyo ni akwai aikin da zan baki ki fara dan nasan na barki anan ba abinda zaki amfana se bacci.” Ita tama soma sabuwa da bak’ak’en kalamunsa. Jakarta ta ajiye ta juya tabi bayansa bayan sun isa office nasa ya zauna ya d’ago blue eyes nasa yana kallonta “ina jotter’n ki?”
   “Yana d’ayan office d’in” ta amsa sa a takaice.
    “Okay office d’inne zena d’auka miki record d’in kokuma so kike kicemin ilimi yamiki yawa da duk abinda na fad’a miki zaki iya d’auka akai ba mistake.”
  Share abinda ya fad’a mata tayi tace, “barin je in d’auko”
    “Make it quick” ya amsata yana duban rolex agogon hannunsa bayan minti d’ai Fannah tadawo rik’e da biro da jotter.
 
        Tun kafin ta bud’o biron ya soma bata aiki  “Kije file room acikin first cabinet akoi stack papers type A-D  kiyi printing sekimin e-mailing, bayan haka ina buk’atar neat handwritten version nasu, avoid any mistake. Sekije 5th floor ki karb’a wasu papers a wajen Miss Suleiman kiyi typing nasu a computer kimin e-mailing, take note kowani paper seprate document ne, bayan kin gama typing nasu print them out ki mayar filing cabinet kiyi arranging. You can go now.” Hannun Fannah har b’ari yake dan yadda take rubutun da sauri duk wannan uban bayani da numfashi d’aya Anas yayi dan mugunta, magana yake sauri sauri saboda tayi missing wani abu dan ta buk’ace sa ya koma baya seya samu ya zageta yanzu.
    A sanyaye ta juya ta fice file room 3rd floor ta nufa kamar yadda ya mata kwatance taga a rubuce a sama 1st cabinet papers d’in ta tsakuro sunyi kusan d’ari har yaushe zatayi typing nasu har tayi e-mailing sannan ta zauna ta k’ara rubuta su da hannu? ai aiki ne babba why not kawai in tayi typing tayi printing ai duk d’aya ne. Bayan ta tattara  papers d’in ta haura 5th floor ta amshi papers wajen Miss Suleiman ta haura sama inda office nata dana Mr. Fauzi suke. Office nasa ta soma wucewa dan masa bayani bayan tayi knocking yace, “come in” tana bud’e k’ofar yaga itane sarai yasan meya dawo da ita, so take ta nemi alfarman printing stack papers d’in ba seta rubuta su ba, da gangan dan mugunta daman ya buk’aci ta rubutan dan kawai yayi punishing nata.
    Bayan ta k’arisa gabansa ta daidaita muryarta ko ze d’an tausaya mata ya yarda da k’udurinta. “Sir naje na d’ibo stack papers d’in nace ko ze yuwu kawai nayi printing nasu bayan nayi typing d’in? Ma’ana ba sena rubuta ba.”
        “Miss Aleeyu nan office ne ba gidan hutu ba, yadda nace sekin rubuta sekin rubuta off you go.”
       “Sir but plea-” bata k’are maganar ba ya dakatar da ita “banasan musu just go nima in huta.” Daman tasan ba yarda zeyi ba juyawa tayi ta nufa office nata. Chan ta soma da typing stack papers d’in bayan tagama ta masa e-mailing duka sannan tayi printing papers data amso wajen Miss Suleiman ta sauk’a taje ta jerasu a filing cabinet sannan ta sake haurowa ta koma office nata batasan a wani shekara zata gama rubuta wannan uban papers da suka kai kusan d’ari ba.
      Guda 20 ta rubuta amman wani erin zogi hannun ta yake mata, kuka ne kawai batayi ba haka da k’yar tayi ta huta ta rubuta hamsin saura hamsin. Telephone dake kan table nata ne yasoma ruri tana kai dubanta taga CEO rubuce akai kamar barata d’aga ba kawai ta sa hannu tayi picking. “Yes Sir” tace masa.
    “Kin gama?” ya tambayeta
    “A’a Sir da saura papers d’in fa har d’ari ne.”
   “Good kicigaba da yi in kin gama seki kawo min akoi aiken da zakije min.”
   Kamar wacce zatayi kuka tace, “Sir please kabar aiken gobe wallahi nagaji please.”
    Murmushi yayi cike da mugunta “kin gaji? Ai bakiyi komi ba tukun hurry up nan da one hour ki tabbata kin gama.” Ding! Ya katse. Tsuka taja “mugu kawai.”
    © miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 33
BY MIEMIEBEE
Haka har k’arfe 4:00PM lokacin tashi yayi Fannah bata gama rubutun ba acikin d’ari tayi 77, daga k’arshe ma da gajiyan ya mata yawa bata san sanda  bacci ya sace ta a wahalince ba. Anas kuwa tun 3:50PM awa d’ayan daya bata yayi ya kirata ba iyaka a telephone nata haka har call d’in ya tsinke bata d’agawa se baccinta takeyi daga k’arshe kam ma Fannah unplugging wayar tayi daga jikin bango dan distracting nata da yake, sannan takoma kan table d’in tare da aza kanta ta cigaba da bacci. Haushi ne ya cika Anas dam wato bayan yace mata kar tayi disconnecting wayan shine tayi ko? da kyau. A fusace ya mik’e daga office nasa ya nufa nata, yana isa yayi banging k’ofar bacci sosai Fannah take cike da gajiya ko noticing abinda yayi ma batayi ba.
    Mamaki ne ya cikasa daya ga yadda ta bararraje tana bacci kan table lallai ma! Bece da ita komi ba, bayi ya nufa tare da d’ibo ruwa cikin mod’a yafito dashi sannan yayi kanta sanda ya k’are mata kallo sannan ya sa hannunsa cikin mod’an ya d’iba ruwan cikin hannunsa sanda ya tabbata ya matsar da papers d’in gefe guda sannan ya watsa mata a fuska a birkice ta tashi tana nishi da k’arfi razana tayi ganinsa a gabanta yaushe ya shigo? Yaushe ma tayi nisa a baccin? Na ‘yan mintuna fa tace zata d’an huta.
   
    “Sannu da hutawa ko Fannah Aleeyu? Kin gama aikin dana saki kenan har kike bacci. Bayan haka kuma kikayi unplugging wayar daga jikin bango saboda kar a tada ke daga beautiful sleep naki koh? dukda kinsan na hanaki.” Se yanzu ta tuna lokacin data zare wayar daga bango ma, ita ta d’au duk a mafarki ne. Kasa fad’in komi tayi har yanzu mamakin ya akayi ta fad’a bacci take. “Baki amsani ba har yanzu, kin gama abinda na saki kokuwa in sake watsa miki ruwan ki gama tashi?”
   “Ban gama ba da saura” ta basa amsa kanta sunkuye tana tsiyaye ruwan daya fesa mata a fuska da cikin hijabin ta.
    “Sauran guda nawa?” Ya tambayeta.
   “Saura 23.” Papers d’in ya tattaro gabanta “oya finish them.” Hijabin ta tasa ta sake share ragowan ruwan fuskartan sannan ta soma rubutun bayan ta gama d’aya ya amshi ya rik’e. Tambayar sa tayi “Sir k’arfe nawa ne please? Kar la’asar ya wuce ni.”
       “Nima bansani ba da kika kwanta kina bacci ai baki tambayeni k’arfe nawa ba” yabata amsa takaicacce. A daidai lokacin ta d’aga kai ta sauk’e idanunta kan wall clock aiko taga 4:07PM “nashiga uku! banyi sallah ba” tana gwada yunk’urin tashi Anas ya zaunar da ita “sit! Ai ba inda zaki sekin gama sauran 22 d’in nan gaba in na saki aiki zakiyi bacci.”
    “Sir Sallah fa na gaba da komai, 5 minutes kad’ai ya isheni in na idar se na cigaba.”
         “Wa’azi zaki min? Toh banasan ji. Damuwanki ne dan bakiyi sallah on time ba da waya ce ki baje kiyi bacci?” zama yayi kan table d’in “get on with it, in kin ga kin tashi yin sallah toh se in kin gama rubuta sauran” Zata sake magana yace, “now!” A tsawace. A ranta tace ai wallahi zunubin na kanka. Haka yana zaune akanta har ta gama rubutawa tas sannan ya mik’e tare da tattara sauran ya had’a gu d’aya. “Kin gama aikin ki na yau zaki iya tafiya.” Dad’i sosai taji a cewarta ya manta da aiken dayace ze mata. “Gobe first thing in the morning zaki aiken da nayi niyan miki yau, karki zata ko na manta ne dan kar Mami tayi tunanin na rik’e ki a ranar farko ne yasa nayi hakan.” Yana kaiwa nan ya fice. “Allah raka taki gona” ta fad’i bayan da ta tabbata ya fice “mugu kawai, kuma Allah ze sak’a min” mik’ewa tayi ta shiga bayi chan tayi alwala tayi amfani da mirron ta giara fuskarta bayan tafito ta idda sallah nan ta tattara kayakinta ta fice, koda ta sauk’o bata ga Yusuf ba dad’i sosai taji dan gida takeson zuwa yanzu ba sauraron labaransa ba.
     Kallo d’aya za’a mata asan tasha aiki yau ta kuma gaji. Mami ta soma tararwa a tsakar gida tana sirfen wake. “Sannu dazuwa Habibti.”
“Yawwa sannu Mami” ta k’irk’iro murmushi. “Ya aikin? Yau da alama agaje kike wuce ciki ki watsa ruwa ki kwanta kafin nan mun gama alalen.”
     “A’a Mami zan tayaki sirfen.”
    “A’a Fannah wannan aiki na da Afrah ne itan ma tashiga bayi ne yanzu zata fito karki damu.”
   “Toh Mami sannu da aiki” tana kaiwa nan ta wuce d’akinsu, sosai taga d’akin ya canza kamanni duk an sake cikasa da kayakin da Mr. Fauzi ya kawo musu jiya tsuka taja wanda yasa Afrah fitowa daga bayan wardrobe inda ta lab’e tana chatting. “‘yar munafukai kinzo kina chatting kinbar Mami na aiki ita kad’ai ko?” Cewar Fannah ba alaman wasa tattare da ita.
   
       “Ya Fannah dan Allah kiyi shiru kar Mami ta jiyoki bayi nace mata zan shiga.”
     “Ai wallahi sena fad’a mata gaskia a mayi seizing wayar taki ai nima haka kika sa baki jiya nakoma wa Mr. Fauzi aiki.”
    “Yi hak’uri Ya Fannah dan Allah ya office d’in?”
   Baki Fannah ta murgud’a mata “bansani k’anwar shed’an kawai jibi yadda hannu na ya kumbura shafin paper guda d’ari na kwafe masa ai wallahi Allah ya isa kuma duk laifin ki ne. Mami! Mami!”
    “Na’am Fannah wani abu ne?” cewar Mami da k’arfi yadda Fannah zata jiyota.
    “Ya Fannah dan Allah karki fad’a mata.” Afrah tace k’asa k’asa.
   “Ai wallahi se na fad’a.” nan ta d’aga muryarta “Mami ga Afrah nan ta mak’ale tana chatting ba bayin da ta shiga.”
   “Mami wallahi k’arya take yanzu fitowa na” wayarta ta mayar cikin wardrobe d’in.
   “Fito nan Afrah kinsan zan karb’e wayarki ko?” Gwalo Fannah tamata a yayinda Afrah tafice zuwa samin Mami tana bata hak’uri. Kayan jikinta ta rage ta fad’a bayi dan watsa ruwa.
  **
       “Oyoyo Ya Anas!” Amal tayi hugging Anas a wajen parking lot. “Oyoyo Angel.” Flasks biyun yaciro daga motarsa ya mik’a mata empty’n “ungo wannan rik’emin.” Bayan ta amshi tace, “Ya Anas me acikin na hannunka?”
   “Coffee ne” ya amsata a takaice yana murmushi. “Toh shine har flask biyu.”
    “A’a d’aya ne na riga na shanye d’ayan.” Ido wuru wuru ta zaro “ka shanye?? Duka wannan na hannun nawa?”
    “Eh Amal yunwa a office.”
   “Ayyah Ya Anas to ko zaka soma tafiya da lunch box ne?” Dariya ya d’anyi kad’an “karki damu I can take care of myself mu shiga daga ciki.”
   “Toh Ya Anas.” A parlour suka tarar da Abuu da Ummie suna zauna se tattaunawa suke sannu da zuwa suka masa a yayinda ya mik’awa Amal flask na hannunsa me coffeen kan takai masa d’aki. Shettima kuwa na dining space yana d’iban abinci shima da alama yanzu ya dawo daga school. “Sannu dazuwa Ya Anas.”
     “Sannu maza” ya amsa sa. “Abuu, Ummie sannunku da hutawa.”
    “Yawwa Anas ga abinci can seka d’iba kaci ko akai maka d’aki ne?”
   Shi da yakeda coffeen sa yau har cikin flask me zeyi da abinci? “A’a Ummie don’t worry bana jin yunwa munje meeting naci abinci a hotel d’azu.”
 
       “Ai dama kullum haka kake cewa toh a huta gajiya.”
   “Yawwa Ummie” ya juya ze nufa d’akinsa kenan Abuu ya kira sunan sa “Anas!” chak ya tsaya tare da juyowa “na’am” Abuu ya amsa cike da girmamawa. “D’an zo ka zauna magana nakeson muyi.”
    Ba musu ya k’ariso cikin parlour’n tare da zama kan rug d’in.
Giaran murya Abuu yayi, “ni Anas shin baka da tsarin aure ne a rayuwar ka?”
      Blue eyes nasa ya zaro tare da sake baki wangalau cike da mamaki. Bambarak’wai yajiyo maganar, dududu shekarunsa nawa ne? 24 nede da ‘yan wattani akai shine za’a masa maganar aure? Cikin mates nasa gabad’aya ba wanda yaji ance yayi aure ko Baana me san mata ma beyi ba se shi ne za’a ce yayi aure? Lallai kuwa! ai da fili kawai Abuu yafito yace masa ya gaji da basa abinci ya tattara kayakin sa yabar masa gida, da yafi mai akan yace wani baida tsarin aurene a rayuwarsa.
 
    “kayi shiru Anas.” Abuu yasake tambayar sa.
    Juyi kansa yaji yana masa da k’yar ya iya fad’in, “aure kuma Abuu?”
       “Eh Anas aure” Abuu yasake jaddada masa.
     “Abuu aure fa kace? Ko ka manta shekaruna ne? I’m just 24 fa, Ummie ki tuna masa mana.” Yadawo da kallonsa kan Ummie. Shiru Ummie tayi dan itama sanda ta fad’a wa yayan nata kan kar ya tinkari Anas da wannan zance na aure yayi yaro he is just 24 amman Abuu yak’i sauraranta saboda wasu k’wararun dalilun dayake dashi.
 
        “Ya Ibrahim nakega abar maganan nan, Anas yaro ne” ta fad’a tana b’ari gudun kar wan nata ya masifeta. “Nafeesa munyi maganan nan dake d’azu inhar kinsan baraki bani goyin baya ba to kiyi shiru.” Kum taja bakinta tayi shiru, dawo da kallonsa yayi kan Anas da ransa ke tafasa, blue eyes nasa sun sake shiga jin an ambato masa kalman ‘aure’ abinda ya tsana fiye da komai. Haka kawai yau yana jin dad’insa Fannah ta dawo masa aiki za’a tinkare sa da zancen aure. Mschww!
         “Aure Anas nakeson kayi, kai kanka kasan kalan kud’in da kake dashi, kalan arzikin da Babanka ya bar maka yaro ne kai har yanzu baka gama mallakan hankalin ka ba hanya d’aya ce kuma zata sa ka mallaki hankalin shine ta hanyan yin aure, yazamto kanada mace a gefenka wanda zata tayaka shawarwari da sauransu. Kuma ko ba dan haka bama kai bakasan ace d’an daka haifa ko ‘ya suyi gadon wannan company naka me albaraka? Sanin kanka ne kap a ‘yan gidan nan bame iya kula maka da wannan babban company koda ace yau kafad’i ka mutu, ga kuma yadda ake mutuwa, iyye Anas?” Shettima dake sauraronsu kai kawai yake kad’awa, ma’ana maganganun Abuu na shiga ta nan na fita tacan ne kawai dan ko za’a had’a sama da k’asa Anas bareyi aure ba inama ace yasamu yarinyan dayake neman ne, wacce ya amshi martabarta da se ace da sauk’i halan ya yarda yayi auren.
    Ganin Anas baida niyan magana Abuu yace, “kayi shiru Anas ko bakada abin cewa ne?”
     Giyansa kawai yakeson sha yanzu shi kad’ai ne ze daidaita masa tunaninsa gashi dama ya d’an kwan biyu be tab’a ba. “Abuu aure? Ni nayi aure? Ai in neman me shawara nake ga Ummie gaka ga Shettima. Ko Amal ma zata iya bani shawara gaskia Abuu ni banasan wannan shawara.”
         “Kinji irin rashin hankalin danake fad’a mikin ba Nafeesa?” Abuu yafad’i yana kishingid’a bayansa jikin kujerar dayake zaune kai. “Anas yaro ne kai har yanzu bakasan ciwon kanka ba aure ne kawai zesa ka mallaki hankali, kasan ko kap Nigeria kaine youngest billonaire? Taya kakeson ka rik’e sunan nan in bawai kanada wanda zata na baka shawara ba? A yanzu a hakan ka tsab abokan banza zasu iya juya maka hankali kayi messing up rayuwar campany’n ka amman in kanada mata fah? Barata tab’a barin hakan ya faru ba. Kai yanzu tsakanin ka da Allah komi da kake ciki ne kake sanar dani ko Ummie’nku?”
    Kai Anas ya kad’a a hankali. “Toh! Amman in mata kake dashi komi zakaji kanasan sanar da ita, in kuwa me hankali da tunani ne duk abinda kakeyi ba daidai ba zata jawo hankalinka, ko baka gane ba?” Ko giad’a kan da Abuu ke jiran Anas yayi beyi ba shifa bega abinda zesa yayi aure ba, shida aure sun raba hanun riga.
      “Baraka fahimce abinda yasa nace kayi aure a yanzu ba se a nan gaba, se anan gaba zaka gano so ne yasa na keson kayi aure.”
    “Abuu wai wani irin aure? Ni ban tab’a jin inda me shekaru 24 yayi aure yayi aure a wannan zamani ba, ko kaifa 27 kayi aure Abuu, a da ma kenan”
        “Nonsense, taya zaka had’a kaina da kai? Kuma ai dama baraka ji ba Anas saboda yawancin masu irin shekarunka basuda aikinyi wasu yanzu suke kammala makarantar wasu kuwa sun kammala ba aiki har yanzu to taya zasuyi aure ba aikin yi? A da ne ko ba aiki mata suke yarda su auri maza amman banda yanzu da ‘yan mata suka sa kwad’ayin abin hannun mutum. Kaga ko dole kace baka tab’a jin me shekaru irin naka yayi aure ba. Amman kuwa in kayi la’akari kai naka case d’in daban ne kap cikin mates naka akoi wanda yakaika samu ne? Mu ajiye samu a gefe ma akoi wanda yake da aiki me kyau kamar naka ne? Ai dama abinda yasa ake delaying aure kenan, rashin samu da abinyi. Kaida Allah ya riga ya baka fa? Seka tsaya yin meh? Jira zakayi se sanda mates naka suka soma aure kaima kayi?”
       “Eh Abuu” ya amsa ransa a b’ace.
    “Toh Anas kayi k’arya dolenka kayi aure kodan mutuncin company’nka kai bakasan in kanada aure mutanen da kake alak’a dasu a sauran k’asashen duniya zasu fi baka mutunci da girmamawa bane? Sabida shi aure hankali yake k’arawa dakuma daraja a idan mutane. Ka ajiye k’ank’antan shekarunka a gefe kayi facing reality Anas, aure ne ya kamance ka kodan kare martaban company’n da Babanka yabar maka.”
       “Abuu gaskia ni barin yi aure ba, my company is doing perfectly fine duk abinda nasan ya kamata inayi ba abinda muke lacking, aure ba abinda zemin inbanda raba min hankali.”
     “Anas yau da ni kake yin che in che? Aure zakayi ko kanaso ko baka so, abinda babba ya hango yaro ko ya hau kan tudu bare gani ba wannan kenan.”
 
   Kamar wanda zeyi kuka yace, “Abuu dan Allah karka min haka please, karka sani yin abinda banaso banida interest akan aure I’m not ready, wallahi kabi duk sauran investments da companies da muke aiki dasu kaji, komi ina kiyayewa ina running business d’ina perfectly, na yarda duk sanda kaji ance maka nayi wani abun da be kamata ba ka sani auren, in fact ka nemo min matar da zan auran ma da kanka amman banda yanzu please. Please Abu.”
          “Anas taimakon,ka nakeson yi, trust me barakayi regretting wannan shawara na yin aure ba.”
      “Abuu please fa nace dan Allah-”
   Katse sa Abuu yayi “a’a ya isa Anas,  na d’aga wannan shawara ya zamto umarni yanzu wanda dolenka ka amince ko kanaso ko bakaso, dolenka zakayi aure ko kanaso ko bakaso ni na fad’a maka.”
    “Ya Ibrahim dan Allah kayi hak’uri take it easy on him, yaro ne.”
   “Dakata Nafeesa wannan uban san da kike ma yaran nan ze zamo musu illa wataran, in gaskia tazo dole a fad’eta, ehe!”
   
   *© miemiebee*
BY MIEMIEBEE
Duk ta gama tsorata ta d’au ko farkawa zeyi yako kama ta red handed, se taga kwanciyar sa ya giara, numfashi ta saki tare da godewa Allah. Inda ta mayar da littafin tasake cirowa, third page d’in ta bud’e taga another family photo, wannan harda Amal aciki da alama be jima suka d’auka ba. Gefen mahaifinsu ne taga wata mata wanda a da takeson tace ko matar sa ne sede kuma taga kamanninsu ya b’aci sosai da mahaifin nasu setayi tunanin ko sister’nsa ne amman toh me ze kawo sister’nsa gidansu har su d’au family photo haka? Ina asalin mahaifiyar tasu taje?
          Next page ta juya taga an rubuta da babban bak’i “I REGRET KNOWING AND HAVING YOU AS MY MOTHER UMMIMI.” Ido wuru-wuru ta zaro yau tana ganin ikon Allah, mutum yace yayi nadaman sanin mahifiyar sa toh me dalili? Daidai zata fara karantawa kenan taji Anas ya sake motsawa tare da giara kwanciyar sa. Tana b’ari ta rufe tare da mayarwa yadda ta samu. Gabansa ta nufa ta karb’e giyan a hankali yadda bare tashe shi ba, taje ta zubar a bayi tare da yin flushing. Tanasan giara masa kwanciya amman tuna abinda ya mata lokacin datayi hakan a baya yasa ta fasa ta barsa kwance yadda ta samesa. So take ta karanta abinda yake rubuce cikin littafin d’azun amman kuma tana tsoro kar Mr. Fauzi ya kamata ya cicci mata mutunci da k’yar ta hak’ura ta fice zuwa office nata akan zata dawo anjima inya tashi yayi signing papers d’in. AC ta kunna kad’an ta kwanta kan makeken 3 seater cushion dake office nata a hankali bacci me nauyi yayi gaba da ita se can azahar ta tashi tayi alwala tayi sallah sannan tafito ta nufa office na Anas knocking tayi sau biyu ba amsa dan haka kawai tashiga kwance ta samesa har yanzu yadda ta barosa tin tin d’azu, daidai nan wayarta ya soma ruri tana kai dubanta taga Yusuf ba tare da b’ata lokaci ba ta d’aga “Asssalamu alaikum.”
          “Wassalam, Fannah Boss yayi signing takardun kuwa? Mutanen sunce zasu zo su amsa yanzu sun fasa zuwa goben.”
    “Mun shiga uku Yusuf Mr. Fauzi bacci yake tun d’azu nikuma tsorin tayar dashi nake.”
     “Toh Fannah ya zamuyi? Kisan nayi please yasamu yayi signing.”
   “Toh me zanyi Yusuf? Kazo ka gwada tayar dashi please.”
    “LOL amman fa kin tsane ni Fannah, try your best kawai I’m hanging” nan ya katse.
    Hannunta takai baki tana cin farcenta dan rashin sanin abinyi, chan ta d’ago files d’in da biro ta nufa kan Mr. Fauzi ta tsaya cak tana nazarin abinyi. A hankali cikin siririyar muryarta ta kira sunan sa “Mr. Fauzi!” Shiru be amsa ba. “Mr. Fauzi!” nan ma be amsa ba, biron hannun ta tad’an tab’a sajen fuskarsa dashi daga sama zuwa k’asa, kan nasa ya kad’a yana me cigaba da baccinsa. Haka ta tayi amman sam yak’i tashi da abin ya ishesa biron ya fisga sauran kad’an ya cafke da hannunta. Wurgi yayi da pen d’in. “Mr. Fauzi please kayi hak’uri ka tashi kayi signing papers d’innan.”
    “Wake magana?” Ya tambaya cikin bacci.
    “PA’rka ce Mr. Fauzi, Fannah Aleeyu.”
      “Fannah Aleeyu inhar kinason aikin ki toh ki fita kibar min office, bakiga ina bacci bane?” ya fad’i idansa a rufe yana bacci.
     “Nagani Sir hak’uri zakayi it won’t take long, kawai signing zakayi seka koma baccin, yi hak’uri.” A hankali ya bud’e idanunsa da suka kad’a sukayi ja yana kallonta inda wani ne ko wata daban da tuni yayi firing nasu amman ganin Fannah se bakinsa yakasa furta kalamun “you are fired” wanda ya rasa dalilin hakan.
 
      Kanta ta sunkuyar, “Please Sir signing nasu kawai zakayi I’m sorry for disturbing you” ta fad’a cikin nitsatssiyar murya. Hannu ya mik’a mata da nufin ta basa papers d’in. Murmushi sosai tayi dan dad’in daya ratsa ta yau wata rana Mr. Fauzi be mata masifa ba cikin kyaftawan ido ta d’auko biro ta bud’e tare da mik’a masa, amsa yayi tana nuna masa inda zeyi signing har yayi signing duka.  “Thank you Sir” tace masa a lokacin daya mik’a mata biron. “Sir azahar yayi da ka dage idar seka cigaba da baccin.”
    Kaman wanda bareyi magana ba kuma chan yace, “me ruwanki da sallah na toh? Kabarin mu d’aya ne? Banasan shisshigi you can go tunda na miki signing.”
     “I’m sorry” tace masa tare da juyawa ta fice. Tsuka yaja, tare da sake rufe idanunsa dan cigaba da baccin sede ya kasa kalamun Fannah na “Sir azahar yayi da ka dage ka idar se ka cigaba da baccin” suke ta yawo masa akai ai haka ya kasa cigaba da baccin dukda kuwa yanaji sosai dan dolen sa ya fad’a bayi yayi alwala sannan yafito yayi sallah bayan ya idar ya tsaya mamakin kansa ma. Wai meke damunsa? Taya Fannah zata ce yayi abu kuma yayi? Impossible! Bayan ya nad’e sallayan ya koma kan table nasa ya zauna se yanzu ma ya lura da state na office nasan, sab’anin yadda ya barsa kafin bacci ya sace sa. “Wait! Ina beer na?” ya tambayi kan sa. Office d’in kap ya duba ba alaman kwalban giyansa. Tashin hankali bame masa wannan d’anyen aikin se Fannah. Telephone nasa ya daddana ya kira Fannah tana zaune a office nata da sabuwar iphone da Anas yabata se game take bugawa hankalinta kwance bayan tama Yusuf submitting files d’in. Telephone nata ne ya soma ringing tana dubawa taga Anas ke kira, nan take bugun zuciyarta ya canza Allah sa bawani abun tayi ba.
      Ko k’ala bata samu tace ba bayan ta d’aga Anas ya soma magana cike da tsiwa “Ke ‘yar shisshigi ba? come to my office right away!” karap! ya katse. Miyau ta had’iye dan tasan she is in trouble Allah sa ba ganewa yayi ta karanta masa wancan littafin ba. As soon as possible ta isa office nasa bayan tayi knocking yace, “enter” kanta a sunkuye ta shiga “yes Sir” tace.
    “Ina ragowar beer na?”
    I’ina ta soma dan tsoro “uhm uhm Si.. Sir…”
    “Ina yake nace?!” Ya daka mata tsawa.
    A firgice tace, “na… Na zubar…”
    “Kin zubar?” ya tambayeta cike da mamaki “Ban hanaki ba?”
   Kan wanda zatayi kuka tace, “ka.. Ka hana kayi hak’uri dan Allah.” Kai ya giad’a tare da sakar da wata murmushin mugunta “jeki d’auko pencils naki a office kizo ina jiran ki yanzu.” Kwata kwata bata fahimce me yake nufi ba, meh  had’in pencil kuma a wannan matter? “Bakiji me nace bane?”
   “Nna.. Naji” tace da sauri ta juya tafice bayan minti d’aya ta dawo da pencil pack a hannunta. “Good” yace mata kai ya sunkuyar k’ark’ashin table nasa tare da jawo wata kwali babba. Papers ne ciki ba iyaka hannu kawai yasa ya d’iba dayawa daga ciki wanda sun kusan d’ari biyar. Bayan ya ajiye kan table yace, “d’auka.”
   “In d’auka kuma Sir? In kai ina?”
    “Ki kai wa me k’osan unguwankau shegen suratan banza. Ki duba cikin kowani page a second paragraph akoi mistake da akayi agarin printing, wajen ‘how’ se computer yasa ‘hoe’ inasan ki zauna ki nutsu ki kibi su one by one ki giara mistake d’in.” Ido sosai Fannah ta zaro tare da sake baki.
   “Sir duka?”
   “Yes Miss Aleeyu duka, 500 pieces ne anan yi sauri karki b’ata mana lokaci akoi abinyi dayawa yau.”
   Kamar wacce zatayi kuka tace cikin siririyar muryarta “Sir dan Allah badan hali na ba kayi hak’uri wallahi tun rubutun jiya hannu ya kumbura gakuma yankan danayi d’azu da glass kayi hak’uri please a sake re-printing.”
   
    “A sake re-printing?” Ya tambayeta tare da d’age gira. “Wannan kuma ayi asaran su a zubar kenan ko meh kike nufi? Kefa kikace min almubazaranci ba kyau, ai kuma zubar da wad’annan yazama almubazaranci ko ba haka ba Malama? Kidena sani surutu tattara ki zauna acan ina ganinki ki fara giarawa, off you go.” Fuska ta kuma yamutsawa “Sir please I’m sorry barin sake zubar maka da beer naka ba.”
     Nuni ya mata da hannu “banasan surutu kibar min kai please nima inyi abinda ke gabana.” Haka kamar zatayi kuka ta tattara papers d’ari biyar ta nufa kan kujera ta zauna ta soma neman mistake d’in can gani ta giara ‘e’ na ‘hoe’ zuwa ‘w’ wa ‘how’ kallonta Anas ya tsaya yi a ransa yace daidanki kenan, nan gaba zaki sake wuce gonanki, a karkace ma ta rik’e biron dan ciwon da hannunta yake mata, amman haka ba tausayi bale tsoron Allah Anas ya shareta ya ciro model nasa na ranan ya cigaba dakayi.
     Guda d’ari Fannah tayi amman tagaji lik’is kai ta d’ago tana kallonsa “Sir please kayi hak’uri” banza da ita yayi ya cigaba da abinda ke gabansa.    “Sir I’m sorry barin k’ara ba ka tausaya min please wallahi hannu na naciwo sosai please…” Nan ma bece mata komai ba. Ai kuka Fannah ta fashe masa da a office. Lallai yarinyan nan ya fad’i a ransa a yayinda ya d’ago kai yana kallonta da d’an gyalenta ta tare fuskarta tana share hawayenta ganin se kallonta yake ta sake k’ara k’arfin kukan. “Guda nawa kikayi?” Ya tambayeta.
  Numfashi take ja kamar ‘yar yarinya “guda hundred.”
   “Kacal?” ya tambayeta “you are not serious get on with it.”
   “Sir dan Allah kayi hak’uri na tuba.”
   “Ki k’ara 150 akai then zanyi deciding ko in hak’ura.”
      “Sir 50 please, zan k’ara hamsin akai.”
      “Nace 150 inkuma barakiyi abinda nace ba seki yi duka 500 d’in.”
    “A’a zanyi” kanta ta sunkuyar ta cigaba dayi. Daidai lokacin wayar Anas ya soma ruri sanda ya kusan tsinkewa sannan ya d’aga ganin Salmar ranan ke kira.
    “Hello eye candy, ya kake?”
    “Ba lafiya ba” yabata takaicaccen amsa a fusace. A hankali Fannah ta d’ago kai tare da barin abinda takeyi tana kallonsa bata san da wa yake wayar ba amman daga jin wannan kalan walak’anci tasan da mace ne.
    “Eye candy me ya sameka? Haka jiya na wuni ina jiran call naka shiru.”
      “Eh Salma banida time naki ne shiyasa ban kira ba, ni nagaji dake ma lets just break up.”
     Cike da mamaki Fannah ke kallonsa inba wai ta mance ba wannan itace salman da sukayi waya shekaran jiya har take ce masa ta gode da kayan daya siya mata, ayyah ita shikenan tabi sahu.
    “Blue eyes dan Allah karka min haka, in wani abin nayi tell me.”
    “Tak’uri na da kike min shi yake damuna karki sake kira na fad’a miki we are done.” Ding! yayi hanging. Kallonsa Fannah ta tsaya yi. “Zaki bar kallo na ne kokuwa se na k’ara miki wasu papers d’in.”
    Take ta kau da kallonta daga garesa tare da cigaba da abinda takeyi. Ta gefen idanta taga ya ciro littafin d’azun, d’an rubuce yayi kad’an ciki ya mayar. Toh me ya rubuta ciki? Mesa baya mutunta mata ne? Toh aima ba abin mamaki bane mutumin dayace yayi regreting sanin mahaifiyar sa kam wace mace ce bare wulak’an ta taba? Tayi ta huta tayi ta huta ahaka har tasamu tagama iyaka 150 dayace ta k’ara. Hannunta ya kumbura iya kumbura gashi se wani shaking yake shi kad’ansa dan azaba.
     Bayan ta mik’e taje ta ajiye masa kan table nasa “Sir gashi na gama”
     “Ki k’ara 50 akai, punishment naki na kallo na d’azu.”
    “Sir wallahi baran iya ba hannu na na ciwo kayi hak’uri barin k’ara ba.”
     “Senace ki k’ara d’ari zaki bar nan?”
      “A’a Sir dan Allah kayi hak’uri.” Kuka ta soma masa kamar ‘yar yarinyar da aka k’wace mata sweet. Shark’af shark’af. Blue eyes nasa ya d’ago yana kallonta a yayinda ta rufe fuskarta da gyalenta ta tacigaba da kukan.
    “Kin d’au wai kukanki ne ze sa incanza mind d’ina?”
   Kai ta kad’a masa tana me cigaba da kukan.
      “Toh kimin shiru” yace. Kum tayi tsit. “I’m letting you go for today amman nan gaba na sake kama ki kina kallo na guda 500 gaba d’aya zaki giara kuma in dad’a miki, I hope am clear?”
    Kai ta giad’a a hankali, sekuma ta tuna dokokinsa. “Yes Sir” tace masa.
   “Ina jotter’nki?”
    “Yana office Sir.”
   “Yau ma ko? Ban hanaki ajiye jotter’nki a office ba?”
   “Sir I’m sorry.” Ta basa hak’uri tana share hawayenta.
     “No, you are not Miss Aleeyu d’au ragowar papers d’in kigama giarawa nan gaba baraki manta ba.” Zata soma masa kuka ya tsawatar mata “in kika bari wancan hawayen yafito believe me wasu sabi zan d’auko miki kuma ki giara.” Hadi’ye hawayen tayi duka. “Na baki a minute kije ki d’auko jotter’n the next time kika sake mancewa dashi kuma zakiyi bayani.”
 
    Tun kafin minti d’ayan ya cika taje ta d’auko ta dawo. Sanda ya k’are mata kallo sannan yace, “Good. Kije mail room a first floor ki kawo min important mail d’ina sauran da kika ga basuda ma’ana ko amfani sekiyi watsi dasu. Kije kitchen also kiyi firing Chef Khadija akwai list na wanda suka jima da applying a 3rd floor wajen Ahmed ki karb’a ki musu sending email ta email addresses nasu. Akoi business trip da zanje in 2 weeks time a Morocco have it rescheduled nan da 2 months haka. You can go.”
     Ita duk ba abinda yake damunta ba kenan taya zataje ta fara firing mutum, gaskia barata iya ba. “Bakiji me nace bane?” Ya fad’i tare da dawo da ita daga duniyar tunanin data wula.
      “Naji Sir but please batun firing chef Khadeeja barin iya ba.”
   “Baraki iya ba?”
   “Eh I’m sorry” ta giad’a kai a hankali.
       “Toh sekizo ga 500 papers a nan kizo ki cigaba da correcting mistakes d’in.”
    “A’a Sir dan Allah kahi hak’uri wallahi hannu ya kumbura.”
   “Then kije kiyi firing nata banasan sake jin wani abu, get out!” Kamar tayi kuka ta fice se tunanin ya zata soma firing Khadeeja take har elevator’n ya bud’u. A sanyaye ta fita tare da shiga kitchen d’in.
   *© miemiebee*
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 37
BY MIEMIEBEE
Ita bata ma san wace chef Khadeejan ba, tambaya ta rigayi har ta sameta sam ta kasa fad’a mata abinda ya kawo ta. “Kece Fannah Aleeyu PA’n Boss koh?” Khadeeja ta tambayeta ganin Fannah batada niyan magana.
        “Eh” ta fad’i fuskarta cike da tausayi da damuwa, baiwar Allah Khadeeja kuwa tun ganin Fannah tasan Boss ne ya turo ta tayi firing nata saboda glass cups da suka fashe mata d’azu.
    “Boss ne ya turoki kizo kiyi firing d’ina ko?” Ta tambaya nitse, kai Fannah ta d’ago ta kalleta cike da tausayi. “I’m so sorry Khadeeja inda inada yadda zanyi da nayi ki cigaba da aiki anan.”
    “Ba komai Fannah, ba laifin ki bane kema.”
    “Me kikayi ne?”
      “Glass cups guda biyu ne suka fashe min mistakenly d’azu.”
    “Kawai? Shine Boss zeyi firing naki?” Fannah ta tambayeta cike da mamaki.
      “Wallahi shine kawai kuma ma bada gangan bane dan Allah ki rok’a min shi wallahi na rasa aikin nan bansan ya zan ciyar da yara na ba, miji na ya gudu ya barni da kula da yaranmu guda biyu, please Fannah.”
   
       Fannah uwar tausayi har idanunta sun cike da hawaye. Ai wannan ba adalci bane ita cups nawa ta fasa masa, mesa bece zeyi firing nata ba se wannan baiwar Allar data fita buk’atar aikin. “Karki damu Khadeeja zanyi iya k’ok’arina inga kin rik’e aikin ki barin je in gwada masa magana, bar kuka kinji?”
    “A’a Fannah karki rasa aikin ki a sanadi na kibari kawai.”
    “A’a Khadeeja I insist in shaa Allah barin rasa nawa ba.” Ahaka ta fice daga kitchen d’in takoma last floor inda tayi knocking a bakin k’ofar office nasa da “enter” da yace mata ta bud’e ta shiga a daidai gaban table nasa ta tsaya. “Mr. Fauzi” ta kira sunansa kanta sunkuye.
     “Yes” ya amsa ta “kin gama duka aikin dana bakin ne?”
    “A’a” ta amsa tana kad’a kai.
    “Meh kike jira then? Ko so kike nazo in tayaki?”
    “A’a Mr. Fauzi batun chef Khadeeja ce-” katse ta yayi “aw! Bakiyi abinda nasakin ba kenan?”
    “Mr. Fauzi I don’t think its fair ayi firing nata.” Kallonta yake cike da mamaki, lallai ma! Jingina yayi jikin kujerar sa tare da crossing arms nasa. “Ke ya kamata ayi firing kenan ko?” Ya tambayeta tare da d’age gira.
 
    “Eh!” ta basa amsa tare da d’ago idanunta suna kallon juna. “Mr. Fauzi ni yakamata kayi firing ba Khadeeja ba, sau nawa nake fasa maka glass cups mesa bakayi firing d’ina ba se ita data fasa guda biyu kacal? Mesa barakayi firing d’ina ba?” katse ta yayi a fusace.
      “Dalili kison ji? Nima bansani ba Miss Aleeyu, kina musu dani, kina karya min cup almost everyday, kina fad’amin magana iya san ranki amman na rasa mesa nakasa firing naki.” Ya fad’i a fusace saboda shi kansa abin ya soma damunsa gashi daga ya zauna seya soma tunanin Fannah koda ransa a b’ace ya tuna da ita seya nemi b’acin ransa ya rasa.
      “Toh itama kar kayi firing nata please, be fair and just. Tunda baraka iya firing d’ina ba itama kayi hak’uri kar kayi firing nata please tunda duk d’aya muke aiki muke maka. Bada gangan ta fasa ba, in ka koreta daga nan batasan dame zata ciyar da yaranta ba, please consider this”,ta fad’i tare da sunkuyar da kanta. A hankali maganganunta suke shiga kunnen Anas. Tunda yazama CEO’n wannan Enterprise ba wanda ya tab’a ce masa ga abinda zeyi kokuma yayi abu ba haka akeyi ba se Fannah kuma yarasa meke damunsa ya kasa tsawata mata se kawai yaji yanasan yayi abinda ta buk’ace sa.
      “Je ki ce mata ta cigaba da aikin amman ta kiyaye nan gaba.” Fannah bata san sanda ta d’ago kai tana murmushi ba, bata d’au akoi tausayi cikin zuciyar Mr. Fauzi ba. “Thank you Sir, thank you so much” da sauri tafice taje ta sanar da Khadeeja, har hawayen jin dad’i sanda Khadeeja ta zubar, godiya sosai tayi wa Fannah, itama Fannan taji dad’i ganin ta farantawa ‘yar uwarta rai.
    Mr. Fauzi kuwa yana cikin wani yanayi wai mesa baya iya turning Fannah down? Mesa da ta nemi alfarma wajensa seyaji yanasan yi mata, mesa? Shi bayasan haka, yafisan yana k’untata mata yana sata kuka kullum baya san yana farinta mata kamar yadda yayi yanzu. “Damn it!” Ya fad’a a fili. “What is wrong with me?”
  **
    Bayan Fannah ta isa mailroon ta cicciro mails na Mr. Fauzi tana tantance masu amfani da maras amfani, tana gamawa tayi disposing mara amfanin sannan ta nufa wajen Kacallah inda ta amso duk wani business transactions da meetings na Mr. Fauzi. Komi da komi ya dawo hannunta yanzu tunda itace PA’nsa. Kafin ta shiga office na Mr. Fauzi ta wuce nata dan rescheduling business trip nasa kamar yadda ya buk’ata in 2 months time. Daga nan ta wuce nasa office d’in tayi knocking yace, “come in” nan tashiga. Sede ta karanci yadda ransa yake a b’ace cikin d’an k’ank’anin lokacin nan. Toh meya samesa? “Sir nayi rescheduling trip d’in ga kuma mails nakan.” Ta fad’i tare da ajiye masa kan table nasa.
    Bece mata komi ba yaja mails d’in yana duddubawa bayan yagama dubawan ya d’ago blue eyes nasa “ina mail da Enterprise Bank suka turo min?”
    Hannu Fannah ta aza kan fuskarta tare da toshe bakinta. Wallahi kuwa taga mail d’in ta yasar dan be mata kalan me amfani ba.
    “Tambayarki nake ina yake?”
     “Sir I’m sorry na yasar.”
    Blue eyes nasa ya zaro, “kin meh? Kin yasar? Da hankalinki kuwa?”
    “Sir I’m sorry naga kamar-” bata k’are maganar ba ya katse ta cike da tsiwa “kinga kamar beyi kalan me amfani ba ko? Na baki nan da 5 minutes kije ki nemo min mail d’in duk inda kika kaisa. Mschww!”
      Tana b’ari tace,  “Sir I’m sorry amman an riga anyi disposing.”
    “Meaning what?! Kije ki nemo min, I don’t care, get out!” Hawaye tajiyo yana ciko mata a ido a sanyaye ta juya ta sauk’o zuwa first floor tare da neman waje ta zauna tana kuka batasan a ina zata nemo masa ba bayan motan kwashe shara ya riga ya tafi. Tayi kusan awa d’aya a waje sannan tajiyo ringing d’in wayarta tana dubawa taga Mr. Fauzi d’agawa tayi ba tare da tace komi ba.
     “Kin samun ne?” ya tambayeta.
    “A’a” ta amsa a takaice cikin muryan kuka.
      “Kuma shine bara kizo ki fad’a min ba? Come right away.” Nan ya katse fuskarta taje ta wanke sannan ta shiga elevator zuwa office nasa. Kallonta yake sannan ya karanci kuka taje tayi, sekuma yaji wani iri besan mesa ba presence na Fannah affects him yanzu. “Make me coffee and leave, na sallameki na yau.” Dad’i sosai taji amman bata nuna masa ba, nan da nan ta had’a masa cikin flask sannan ta fice. Bayan ta fita ya taso ya zuba kad’an cikin cup tare da zama kan kujera, seya kai coffeen baki seyaji kuma bayasan sha, wayasani ko san dayake ma coffeen ta ne yasoma dawowa kan Fannah. “No way!” ya fad’a a fili. Coffeen ya mayar cikin flask d’in shi a dole ya fasa sha bada jimawa ba yatashi yasake juyewa cikin cup duk yadda yayi ya hana kansa ya kasa he is already addicted to it.
    Shima bada jimawa ba ya rufo office nasa yayi tafiyarsa, instead yaje gida seya wuce paint house nasa ba tunanin abinda yakeyi sena Fannah ya rasa meke damunsa kwalban giyansa ya d’auko ze sha abin mamaki ya tsaya cak kalamun Fannah na yadena shan giya yasoma yawo masa a k’wak’walwa. “Damn it!” Ya fad’i tare da rufewa ya mayar cikin fridge d’in. Toilet ya nufa ya rage kayan jikinsa tare da kunna shower ruwa na sauk’a jikinsa.
  ***
         Fannah kuwa tun isarta gida ciwon mara ya rik’e ta alaman wata ya zagayo kenan, haka tata fama da ciwon gashi kuma tak’i shan magani. A haka har bacci ya saceta a wahalince. Cikin baccin ta soma yin mafarkinta na kullum akan wanda yayi raping nata yadawo ze sake mata. Firgit ta farka ta soma kuka tana ihu Mami dake tsakar gida ne tashigo a guje da k’yar tasamu tayi calming Fannah tayi hugging nata. “Ya isa Habibti ki cire wannan abu daga ranki, ace yau shekaru nawa sede baki kwanta ba zakiyi mafarkin abin. Ya isa haka mana.”
      “Mami wallahi inaji mutumin ya matso kusa dani wai yana _TARE DA NI_ Mami tsoro nakeji.”
    “Shhh! ya isa mafarki ne in shaa Allah kin rabu da mutumin har abada bashi ba ke, kinji? Ya ciwon marar?”
     “Mami har yanzu yana min ciwo.”
   “Toh kink’i shan magani ba dole ba, kin kwan biyu bakiyi ciwon ba ma ai Allah kawo sauk’i deh, sannu ki huta in jikin be sake kiba gobe barakije aiki ba.”
    Sanyi sosai Fannah taji har cikin ranta, gobe barata je aiki ba.
     Washegari Anas ya tashi da coffeen Fannah yayi breakfast sannan ya nufa office shiru shiru har 8:30AM Fannah bata zo office na “lallai ma yarinyan nan ta gama raina min wayo” yace a ransa tare da ciro wayarsa ya kira lambarta.
   
  **
     Afrah ne zaune kan Fannah suna hira, sosai Fannah taji sauk’i saboda Mami ta tilasta mata sanda tasha maganin jiya amma da taga Mami seta shangwab’e wai jikin ba sauk’i. Wayarta ne ya soma ruri aiko tana kai kallonta kai taga Mr. Fauzi “ungo Afrah gashi ki d’aga kice masa banida lafiya ne kinji? Zan baki 1k kisa kati.”
    “Dagaske?!” ta tambaya tana washe hak’wara.
    “Na rantse” Fannah ta tabbatar mata, ai karap ta d’aga wayar Anas yayi niyan fara suburbud’o mata masifa kawai seyaji muryar da ba nata ba “hello Mr. Fauzi.”
   “Hello” yace cikin sanyin murya kamar ba shi ba. “Afrah ce?” Sanda tasa a handsfree sannan tace, “eh ina kwana Mr. Fauzi?”
   “Lafiya call me Ya Anas kinji?”
  “Toh Ya Anas, kaji Ya Fannah shiru yau ko? Batada lafiya ne.”
    “Batada lafiya meya sameta?” gabad’aya yaji ya damu, a tunaninsa ko hannunta ne da yata sata rubutu jiya yayi worse.”
  “Menstral cramp (mp) ne” ta amsa sa a takaice. Bugi Fannah takai mata a cinya “bakida hankali ne?” Ta fad’a k’asa k’asa yadda Anas bareji ba.
   “Toh meh ba MP’n bane?” Afrah ta bata amsa itama chan k’asa k’asa.
    “Uhmmm toh kun kaita asibiti?” Ya tambayeta shi kansa yaji kunyan zancen. Itama se yanzu taji kunyan abinda ta fad’a masan. “A’a” ta amsa cike da kunya.
     “Toh yanzu zan turo mota se a kaita kinji? Ki sanar da Mami.” Kai Fannah take kad’a mata da nufin tace a’a.
    “A’a Ya Anas karka damu tasha magani yanzu haka ma tana bacci.”
   “Are you sure Afrah?”
    “Eh Ya Anas gobe ma in shaa Allah zata dawo office.”
   “Toh yayi kyau bye.” Yayi hanging.
     “Bakiyi ba wallahi Afrah taya zaki che masa MP ke damuna? Da wani idan kikeson in kallesa gobe mschww! ni wallahi barin koma office ba.”
   “Toh meh? Kefa kikace yanada k’anwa ai itama nasan tanayi, kuma mahaifiyar sa ma tanayi me abin jin kunya? Amman fa Mr. Fauzi I mean Ya Anas ya damu da lafiyarki, ko ince yana sanki ma, baki ji yadda ya damu bane?” Shiru Fannah tayi bata tanka ta ba tunanin ya next meeting nasu da Anas ze kasance kawai take wannan kayan kunyan da Afrah ta mata.
     Ta fannin Anas kuwa ya kasa gane kan ranan gabad’ai coffeen data had’a masa jiyan ma ya shanye tas, haka kawai yaji yana san sata a idanunsa, yau da be ganta ba seji yake kamar yayi asaran wani abu a jikinsa. Hannayensa biyu yasa cikin gashin kansa yana hargitsawa. “What is wrong with me? I am not missing Fannah, I’m just missing her coffee, thats all.” Model nasa ya ciro dan cigaba da yi ko ze d’an manta Fannah da coffeen t, yana aza hannu kan model nasan se tunanin Fannah ya b’ullo masa akai. “Damn it!” Yayi wurgi da super glue dake hannunsa. A fusace ya mik’e ya nufa wajen fridge nasa yaciro kwalba d’aya daidai ya bud’e yakai baki se kawai kalamun Fannah suka soma masa yawo akai. “Ohh!!! What is wrong with me?” Ido ya rufe yasa kwalban a bakinsa sanda yasha rabi sannan ya ciro. D’akinsa ya nufa ya mik’e kan gado nan ma be bar tunanin nata ba musamman ma dayaji bata da lafiya yasha ganin yadda Amal ke kuka in menstral cramp yakamata.
     Haka yayi yayi amman ya kasa bacci, meeting dayake dashi kawai ya tashi ya shirya. Driving ma kasa yi, tuk’asa driver yayi. Ko a wajen meeting d’in yakasa concentrating, har aka tashi besan me suka tattauna akai ba, mutanen kuwa sun karanchi hakan, koda suka tambayesa menene  che musu yayi kansa ke ciwo. Daga chan ma gida yasa driver ya wuce dashi sosai Ummie, Amal da Shettima sukaji dad’in dawowansa, Abuu bai gida da yayi murna shima dan d’an kwana biyu da Anas yayi ba’a gida ba ya fitinesa.
     Da k’yar Ummie ta ja Amal waje daga d’akin Anas dan barin sa ya huta, bada dad’ewa ba Shettima ya shigo har ya zauna Anas beyi noticing ba, sanda ya tab’a sa sannan firgit ya juya yana kallonsa. “Maza yaushe ka shigo?” Ya tambayesa cike da mamaki.
    “About a minute ago tunanin me kake? Tunanin abinda Abuu ya fad’a maka shekaran jiya ne?”
    Shi Anas ya ma manta da wan can batu, se yanzu da Shettima ya tunatar masa.
       “Shettima ni bansan ina zan samu mace in kawo wa Abuu ba I don’t trust in love.”
    “Ya Anas dade kayi hak’uri ka duba cikin ‘yan matanka wacce tafi hankali ko a aura maka Falmata.”
    “Hankali? Ai dukansu bame hankali, they are after my look and money, ba wacce take sona tsakani da Allah saboda kud’i na da kyau suke bina. Ni nasani ba macen da zata tab’a sona tsakani da Allah.”
     “Akoi Ya Anas kuma ina kan maka addu’a, Allah bayyano maka da ita nan da wata shidan da Abuu ya yanka maka. Macen da zata soka tsakani da Allah, wacce bara ta damu da kud’inka ba, ko kyanka ba, wacce barata damu da duniya da abinda ke cikinta ba, she’ll be a decent girl wanda bata shirin batsa ba kuma ruwanta da jan attention na mutane, me tarbiyya da hankali da kuma ilimi, wacce zata na maka wa’azi duk sanda kayi ba dede ba”
     Duk wannan halaye da d’abi’un da Shettima ya lisafo se Anas yaga sak na Fannah kenan. Yaci ace a iya zaman sunnan ta fito tace tana sansa kamar yadda receptionist na sa ta masa da sauran ma’aikatan sa, koda ya bata iphone cewa tayi bataso dan bata da option ne yasa kawai ta amince ta karb’a meaning bata damu da kayan duniya ba kenan.
      “NO!!! SHE CAN’T BE THE GIRL” ya fad’i a fili ba tare dayasan yayi hakan ba.
     “Wace yarinya kenan Ya Anas?” Shettima ya tambayesa. “Yarinya kuma?” Anas ya wayince. “Wace yarinya? Waye ya kira wata yarinya anan?”
    “Kaifa kace ‘no she can’t be the girl’ yanzu. Wata yarinya kak nufi kenan?”
      “Kai kacika suratan banza wallahi ni tashi kabani gu, inji da problem dake damuna na neman matan aure in 6 months time.” Se da Shettima yakai bakin k’ofa sannan yace, “Ya Anas kode Fannah ce?”
    “What?!” Pillow ya d’aga ya wulla masa wanda tuni ya fice yana masa dariya. Mesa hankalin Shettima ze karkato zuwa kan Fannah? Mesa se ita? To kode na fara santa ne?
  “No way” ya fad’i a fili. “I can’t love Fannah, mezanyi da ita? Coffeenta kawai nakeso ba ita ba, kuma shi d’inma daga yau nadena sha. I can’t fall for Fannah.”
  © miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 37
BY MIEMIEBEE
Ita bata ma san wace chef Khadeejan ba, tambaya ta rigayi har ta sameta sam ta kasa fad’a mata abinda ya kawo ta. “Kece Fannah Aleeyu PA’n Boss koh?” Khadeeja ta tambayeta ganin Fannah batada niyan magana.
        “Eh” ta fad’i fuskarta cike da tausayi da damuwa, baiwar Allah Khadeeja kuwa tun ganin Fannah tasan Boss ne ya turo ta tayi firing nata saboda glass cups da suka fashe mata d’azu.
    “Boss ne ya turoki kizo kiyi firing d’ina ko?” Ta tambaya nitse, kai Fannah ta d’ago ta kalleta cike da tausayi. “I’m so sorry Khadeeja inda inada yadda zanyi da nayi ki cigaba da aiki anan.”
    “Ba komai Fannah, ba laifin ki bane kema.”
    “Me kikayi ne?”
      “Glass cups guda biyu ne suka fashe min mistakenly d’azu.”
    “Kawai? Shine Boss zeyi firing naki?” Fannah ta tambayeta cike da mamaki.
      “Wallahi shine kawai kuma ma bada gangan bane dan Allah ki rok’a min shi wallahi na rasa aikin nan bansan ya zan ciyar da yara na ba, miji na ya gudu ya barni da kula da yaranmu guda biyu, please Fannah.”
 
       Fannah uwar tausayi har idanunta sun cike da hawaye. Ai wannan ba adalci bane ita cups nawa ta fasa masa, mesa bece zeyi firing nata ba se wannan baiwar Allar data fita buk’atar aikin. “Karki damu Khadeeja zanyi iya k’ok’arina inga kin rik’e aikin ki barin je in gwada masa magana, bar kuka kinji?”
    “A’a Fannah karki rasa aikin ki a sanadi na kibari kawai.”
    “A’a Khadeeja I insist in shaa Allah barin rasa nawa ba.” Ahaka ta fice daga kitchen d’in takoma last floor inda tayi knocking a bakin k’ofar office nasa da “enter” da yace mata ta bud’e ta shiga a daidai gaban table nasa ta tsaya. “Mr. Fauzi” ta kira sunansa kanta sunkuye.
     “Yes” ya amsa ta “kin gama duka aikin dana bakin ne?”
    “A’a” ta amsa tana kad’a kai.
    “Meh kike jira then? Ko so kike nazo in tayaki?”
    “A’a Mr. Fauzi batun chef Khadeeja ce-” katse ta yayi “aw! Bakiyi abinda nasakin ba kenan?”
    “Mr. Fauzi I don’t think its fair ayi firing nata.” Kallonta yake cike da mamaki, lallai ma! Jingina yayi jikin kujerar sa tare da crossing arms nasa. “Ke ya kamata ayi firing kenan ko?” Ya tambayeta tare da d’age gira.
 
    “Eh!” ta basa amsa tare da d’ago idanunta suna kallon juna. “Mr. Fauzi ni yakamata kayi firing ba Khadeeja ba, sau nawa nake fasa maka glass cups mesa bakayi firing d’ina ba se ita data fasa guda biyu kacal? Mesa barakayi firing d’ina ba?” katse ta yayi a fusace.
      “Dalili kison ji? Nima bansani ba Miss Aleeyu, kina musu dani, kina karya min cup almost everyday, kina fad’amin magana iya san ranki amman na rasa mesa nakasa firing naki.” Ya fad’i a fusace saboda shi kansa abin ya soma damunsa gashi daga ya zauna seya soma tunanin Fannah koda ransa a b’ace ya tuna da ita seya nemi b’acin ransa ya rasa.
      “Toh itama kar kayi firing nata please, be fair and just. Tunda baraka iya firing d’ina ba itama kayi hak’uri kar kayi firing nata please tunda duk d’aya muke aiki muke maka. Bada gangan ta fasa ba, in ka koreta daga nan batasan dame zata ciyar da yaranta ba, please consider this”,ta fad’i tare da sunkuyar da kanta. A hankali maganganunta suke shiga kunnen Anas. Tunda yazama CEO’n wannan Enterprise ba wanda ya tab’a ce masa ga abinda zeyi kokuma yayi abu ba haka akeyi ba se Fannah kuma yarasa meke damunsa ya kasa tsawata mata se kawai yaji yanasan yayi abinda ta buk’ace sa.
      “Je ki ce mata ta cigaba da aikin amman ta kiyaye nan gaba.” Fannah bata san sanda ta d’ago kai tana murmushi ba, bata d’au akoi tausayi cikin zuciyar Mr. Fauzi ba. “Thank you Sir, thank you so much” da sauri tafice taje ta sanar da Khadeeja, har hawayen jin dad’i sanda Khadeeja ta zubar, godiya sosai tayi wa Fannah, itama Fannan taji dad’i ganin ta farantawa ‘yar uwarta rai.
    Mr. Fauzi kuwa yana cikin wani yanayi wai mesa baya iya turning Fannah down? Mesa da ta nemi alfarma wajensa seyaji yanasan yi mata, mesa? Shi bayasan haka, yafisan yana k’untata mata yana sata kuka kullum baya san yana farinta mata kamar yadda yayi yanzu. “Damn it!” Ya fad’a a fili. “What is wrong with me?”
  **
    Bayan Fannah ta isa mailroon ta cicciro mails na Mr. Fauzi tana tantance masu amfani da maras amfani, tana gamawa tayi disposing mara amfanin sannan ta nufa wajen Kacallah inda ta amso duk wani business transactions da meetings na Mr. Fauzi. Komi da komi ya dawo hannunta yanzu tunda itace PA’nsa. Kafin ta shiga office na Mr. Fauzi ta wuce nata dan rescheduling business trip nasa kamar yadda ya buk’ata in 2 months time. Daga nan ta wuce nasa office d’in tayi knocking yace, “come in” nan tashiga. Sede ta karanci yadda ransa yake a b’ace cikin d’an k’ank’anin lokacin nan. Toh meya samesa? “Sir nayi rescheduling trip d’in ga kuma mails nakan.” Ta fad’i tare da ajiye masa kan table nasa.
    Bece mata komi ba yaja mails d’in yana duddubawa bayan yagama dubawan ya d’ago blue eyes nasa “ina mail da Enterprise Bank suka turo min?”
    Hannu Fannah ta aza kan fuskarta tare da toshe bakinta. Wallahi kuwa taga mail d’in ta yasar dan be mata kalan me amfani ba.
    “Tambayarki nake ina yake?”
     “Sir I’m sorry na yasar.”
    Blue eyes nasa ya zaro, “kin meh? Kin yasar? Da hankalinki kuwa?”
    “Sir I’m sorry naga kamar-” bata k’are maganar ba ya katse ta cike da tsiwa “kinga kamar beyi kalan me amfani ba ko? Na baki nan da 5 minutes kije ki nemo min mail d’in duk inda kika kaisa. Mschww!”
      Tana b’ari tace,  “Sir I’m sorry amman an riga anyi disposing.”
    “Meaning what?! Kije ki nemo min, I don’t care, get out!” Hawaye tajiyo yana ciko mata a ido a sanyaye ta juya ta sauk’o zuwa first floor tare da neman waje ta zauna tana kuka batasan a ina zata nemo masa ba bayan motan kwashe shara ya riga ya tafi. Tayi kusan awa d’aya a waje sannan tajiyo ringing d’in wayarta tana dubawa taga Mr. Fauzi d’agawa tayi ba tare da tace komi ba.
     “Kin samun ne?” ya tambayeta.
    “A’a” ta amsa a takaice cikin muryan kuka.
      “Kuma shine bara kizo ki fad’a min ba? Come right away.” Nan ya katse fuskarta taje ta wanke sannan ta shiga elevator zuwa office nasa. Kallonta yake sannan ya karanci kuka taje tayi, sekuma yaji wani iri besan mesa ba presence na Fannah affects him yanzu. “Make me coffee and leave, na sallameki na yau.” Dad’i sosai taji amman bata nuna masa ba, nan da nan ta had’a masa cikin flask sannan ta fice. Bayan ta fita ya taso ya zuba kad’an cikin cup tare da zama kan kujera, seya kai coffeen baki seyaji kuma bayasan sha, wayasani ko san dayake ma coffeen ta ne yasoma dawowa kan Fannah. “No way!” ya fad’a a fili. Coffeen ya mayar cikin flask d’in shi a dole ya fasa sha bada jimawa ba yatashi yasake juyewa cikin cup duk yadda yayi ya hana kansa ya kasa he is already addicted to it.
    Shima bada jimawa ba ya rufo office nasa yayi tafiyarsa, instead yaje gida seya wuce paint house nasa ba tunanin abinda yakeyi sena Fannah ya rasa meke damunsa kwalban giyansa ya d’auko ze sha abin mamaki ya tsaya cak kalamun Fannah na yadena shan giya yasoma yawo masa a k’wak’walwa. “Damn it!” Ya fad’i tare da rufewa ya mayar cikin fridge d’in. Toilet ya nufa ya rage kayan jikinsa tare da kunna shower ruwa na sauk’a jikinsa.
  ***
         Fannah kuwa tun isarta gida ciwon mara ya rik’e ta alaman wata ya zagayo kenan, haka tata fama da ciwon gashi kuma tak’i shan magani. A haka har bacci ya saceta a wahalince. Cikin baccin ta soma yin mafarkinta na kullum akan wanda yayi raping nata yadawo ze sake mata. Firgit ta farka ta soma kuka tana ihu Mami dake tsakar gida ne tashigo a guje da k’yar tasamu tayi calming Fannah tayi hugging nata. “Ya isa Habibti ki cire wannan abu daga ranki, ace yau shekaru nawa sede baki kwanta ba zakiyi mafarkin abin. Ya isa haka mana.”
      “Mami wallahi inaji mutumin ya matso kusa dani wai yana _TARE DA NI_ Mami tsoro nakeji.”
    “Shhh! ya isa mafarki ne in shaa Allah kin rabu da mutumin har abada bashi ba ke, kinji? Ya ciwon marar?”
     “Mami har yanzu yana min ciwo.”
   “Toh kink’i shan magani ba dole ba, kin kwan biyu bakiyi ciwon ba ma ai Allah kawo sauk’i deh, sannu ki huta in jikin be sake kiba gobe barakije aiki ba.”
    Sanyi sosai Fannah taji har cikin ranta, gobe barata je aiki ba.
     Washegari Anas ya tashi da coffeen Fannah yayi breakfast sannan ya nufa office shiru shiru har 8:30AM Fannah bata zo office na “lallai ma yarinyan nan ta gama raina min wayo” yace a ransa tare da ciro wayarsa ya kira lambarta.
 
  **
     Afrah ne zaune kan Fannah suna hira, sosai Fannah taji sauk’i saboda Mami ta tilasta mata sanda tasha maganin jiya amma da taga Mami seta shangwab’e wai jikin ba sauk’i. Wayarta ne ya soma ruri aiko tana kai kallonta kai taga Mr. Fauzi “ungo Afrah gashi ki d’aga kice masa banida lafiya ne kinji? Zan baki 1k kisa kati.”
    “Dagaske?!” ta tambaya tana washe hak’wara.
    “Na rantse” Fannah ta tabbatar mata, ai karap ta d’aga wayar Anas yayi niyan fara suburbud’o mata masifa kawai seyaji muryar da ba nata ba “hello Mr. Fauzi.”
   “Hello” yace cikin sanyin murya kamar ba shi ba. “Afrah ce?” Sanda tasa a handsfree sannan tace, “eh ina kwana Mr. Fauzi?”
   “Lafiya call me Ya Anas kinji?”
  “Toh Ya Anas, kaji Ya Fannah shiru yau ko? Batada lafiya ne.”
    “Batada lafiya meya sameta?” gabad’aya yaji ya damu, a tunaninsa ko hannunta ne da yata sata rubutu jiya yayi worse.”
  “Menstral cramp (mp) ne” ta amsa sa a takaice. Bugi Fannah takai mata a cinya “bakida hankali ne?” Ta fad’a k’asa k’asa yadda Anas bareji ba.
   “Toh meh ba MP’n bane?” Afrah ta bata amsa itama chan k’asa k’asa.
    “Uhmmm toh kun kaita asibiti?” Ya tambayeta shi kansa yaji kunyan zancen. Itama se yanzu taji kunyan abinda ta fad’a masan. “A’a” ta amsa cike da kunya.
     “Toh yanzu zan turo mota se a kaita kinji? Ki sanar da Mami.” Kai Fannah take kad’a mata da nufin tace a’a.
    “A’a Ya Anas karka damu tasha magani yanzu haka ma tana bacci.”
   “Are you sure Afrah?”
    “Eh Ya Anas gobe ma in shaa Allah zata dawo office.”
   “Toh yayi kyau bye.” Yayi hanging.
     “Bakiyi ba wallahi Afrah taya zaki che masa MP ke damuna? Da wani idan kikeson in kallesa gobe mschww! ni wallahi barin koma office ba.”
   “Toh meh? Kefa kikace yanada k’anwa ai itama nasan tanayi, kuma mahaifiyar sa ma tanayi me abin jin kunya? Amman fa Mr. Fauzi I mean Ya Anas ya damu da lafiyarki, ko ince yana sanki ma, baki ji yadda ya damu bane?” Shiru Fannah tayi bata tanka ta ba tunanin ya next meeting nasu da Anas ze kasance kawai take wannan kayan kunyan da Afrah ta mata.
     Ta fannin Anas kuwa ya kasa gane kan ranan gabad’ai coffeen data had’a masa jiyan ma ya shanye tas, haka kawai yaji yana san sata a idanunsa, yau da be ganta ba seji yake kamar yayi asaran wani abu a jikinsa. Hannayensa biyu yasa cikin gashin kansa yana hargitsawa. “What is wrong with me? I am not missing Fannah, I’m just missing her coffee, thats all.” Model nasa ya ciro dan cigaba da yi ko ze d’an manta Fannah da coffeen t, yana aza hannu kan model nasan se tunanin Fannah ya b’ullo masa akai. “Damn it!” Yayi wurgi da super glue dake hannunsa. A fusace ya mik’e ya nufa wajen fridge nasa yaciro kwalba d’aya daidai ya bud’e yakai baki se kawai kalamun Fannah suka soma masa yawo akai. “Ohh!!! What is wrong with me?” Ido ya rufe yasa kwalban a bakinsa sanda yasha rabi sannan ya ciro. D’akinsa ya nufa ya mik’e kan gado nan ma be bar tunanin nata ba musamman ma dayaji bata da lafiya yasha ganin yadda Amal ke kuka in menstral cramp yakamata.
     Haka yayi yayi amman ya kasa bacci, meeting dayake dashi kawai ya tashi ya shirya. Driving ma kasa yi, tuk’asa driver yayi. Ko a wajen meeting d’in yakasa concentrating, har aka tashi besan me suka tattauna akai ba, mutanen kuwa sun karanchi hakan, koda suka tambayesa menene  che musu yayi kansa ke ciwo. Daga chan ma gida yasa driver ya wuce dashi sosai Ummie, Amal da Shettima sukaji dad’in dawowansa, Abuu bai gida da yayi murna shima dan d’an kwana biyu da Anas yayi ba’a gida ba ya fitinesa.
     Da k’yar Ummie ta ja Amal waje daga d’akin Anas dan barin sa ya huta, bada dad’ewa ba Shettima ya shigo har ya zauna Anas beyi noticing ba, sanda ya tab’a sa sannan firgit ya juya yana kallonsa. “Maza yaushe ka shigo?” Ya tambayesa cike da mamaki.
    “About a minute ago tunanin me kake? Tunanin abinda Abuu ya fad’a maka shekaran jiya ne?”
    Shi Anas ya ma manta da wan can batu, se yanzu da Shettima ya tunatar masa.
       “Shettima ni bansan ina zan samu mace in kawo wa Abuu ba I don’t trust in love.”
    “Ya Anas dade kayi hak’uri ka duba cikin ‘yan matanka wacce tafi hankali ko a aura maka Falmata.”
    “Hankali? Ai dukansu bame hankali, they are after my look and money, ba wacce take sona tsakani da Allah saboda kud’i na da kyau suke bina. Ni nasani ba macen da zata tab’a sona tsakani da Allah.”
     “Akoi Ya Anas kuma ina kan maka addu’a, Allah bayyano maka da ita nan da wata shidan da Abuu ya yanka maka. Macen da zata soka tsakani da Allah, wacce bara ta damu da kud’inka ba, ko kyanka ba, wacce barata damu da duniya da abinda ke cikinta ba, she’ll be a decent girl wanda bata shirin batsa ba kuma ruwanta da jan attention na mutane, me tarbiyya da hankali da kuma ilimi, wacce zata na maka wa’azi duk sanda kayi ba dede ba”
     Duk wannan halaye da d’abi’un da Shettima ya lisafo se Anas yaga sak na Fannah kenan. Yaci ace a iya zaman sunnan ta fito tace tana sansa kamar yadda receptionist na sa ta masa da sauran ma’aikatan sa, koda ya bata iphone cewa tayi bataso dan bata da option ne yasa kawai ta amince ta karb’a meaning bata damu da kayan duniya ba kenan.
      “NO!!! SHE CAN’T BE THE GIRL” ya fad’i a fili ba tare dayasan yayi hakan ba.
     “Wace yarinya kenan Ya Anas?” Shettima ya tambayesa. “Yarinya kuma?” Anas ya wayince. “Wace yarinya? Waye ya kira wata yarinya anan?”
    “Kaifa kace ‘no she can’t be the girl’ yanzu. Wata yarinya kak nufi kenan?”
      “Kai kacika suratan banza wallahi ni tashi kabani gu, inji da problem dake damuna na neman matan aure in 6 months time.” Se da Shettima yakai bakin k’ofa sannan yace, “Ya Anas kode Fannah ce?”
    “What?!” Pillow ya d’aga ya wulla masa wanda tuni ya fice yana masa dariya. Mesa hankalin Shettima ze karkato zuwa kan Fannah? Mesa se ita? To kode na fara santa ne?
  “No way” ya fad’i a fili. “I can’t love Fannah, mezanyi da ita? Coffeenta kawai nakeso ba ita ba, kuma shi d’inma daga yau nadena sha. I can’t fall for Fannah.”
  © miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 38
BY MIEMIEBEE
Washegari tun asuba Anas ya tashi saboda kasa bacci da yayi ga kuma rashin abin shaye shayen sa kusa dashi, koda na kusa dashin ma se yayi drama yake iya sha yanzu tun maganan da Fannah ta masa har yau yakasa erasing daga memory’nsa. Bayan yayi wanka ya shirya yafito already Ummie da Amal sun had’a masa breakfast, as usual shida Amal suka karya sede yau Anas ya zage yaci abincin sosai sab’anin yadda ya sabayi danko in be sha coffeen Fannah ba bai iya breakfast me kyau. Se forcing kanshi yake yana ci shi a dole yanasan mancewa da coffeen, a tunanin sa in ya dena shan coffeen ta ze iya mancewa dashi, eventually Fannan ma ze manta da ita seta zama missed call. (LOL)
    “Wai! wai! wai! Ya Anas ai ka cinye abincin bani yau.”
     Murmushi ya mata tare da rufa bakinsa ta hanyan aza hannunsa kai. “I’m sorry Angel yunwa nakeji. Nikam kunyi waya da Fannan office d’ina jiya?” Shiru tayi bata amsa saba gudun karya masifeta. “Angel I’m talking to you.”
     “Ya Anas kayi hak’uri.”
    “For? Amsa min tambayan dana miki mana kunyi waya jiya?” Kai ta giad’a a hankali cike da tsoro saboda Anas ya hanata waya da Fannah.
    “Meh tace miki?” Nan ma shiru tayi.    “Feel free and tell me barin miki komai ba kinji?” Ya d’ago hannunta yasa cikin nasa.
     “Promise Ya Anas baraka sake hana ni waya da ita ba?”
     “Yes Angel I promise.”
     “Tacemun batada lafiya mentral cramp yana damunta.”
     “Tace zata office yau?”
       “Tace min baza ta ba wai seta warke gabad’aya.”
    Kai ya giad’a tare da kewayo da kallonsa daga kan Amal zuwa kan plate na abincinsun “in ta haka menstral cramp d’in da wahala kenan.” Ya fad’i wa kansa kasancewar Amal na kusa dashi seta jiyo sa. “Sosai Ya Anas ni in ya tashi min ji nake kaman zan mutu.”
     Murmushi ya mata “bara ki mutu ba ma in shaa Allah barin wuce office kinji?” Kai ta giad’a masa a yayinda ya bata peck a goshi. “Ummie thank you for the breakfast na tafi” yache da d’an ihu dan Ummin dake kitchen ta jiyosa. “Adawo lafiya Babana” ta mayar masa itama da ihun.
    As usual k’arfe 8:00AM yayi masa a office nasa, Kacallah ya kira ya tambayesa ko yanada meeting yau. Unfortunately Kacallah yace masa ai duk wani schedule nasa na wajen Fannah. “Toh mesa ka bata duka?”
    “I’m sorry Boss but she is your PA, aikinta ne yanzu.”
    “Toh naji” yayu hanging.
  ***
     “Mami ni wallahi barinje office d’inba, barin sake komawa bama gabad’aya. Bakiji me Afrah tace masa jiya bane? Che masa tayi wai MP ke damuna.”
    Baki Mami ta bud’e tana kallon ikon Allah. “Lallai fa Fannah se akayi ya? Abune kowace mace tanayi, basuda mata ne a gidansu? Shi kansa ya riga yasan mene, ni banga abin jin kunya ba a nan ba.”
    Can k’asa k’asa Fannah tace, “ai dama baraki gani ba.”
    “Nima de wallahi Mami” cewar Afrah.
    “Kekuma Afrah kika kuma wannan rashin hankali zan sab’a miki, Aiman ce yakamata tayi wannan sokanci ba ke ba.” Mami tayi lecturing nata. Juyawa Fannah tayi tana mata gwalo a dole an mata masifa itama.
    “Ke kuma Fannah sa hijabinki ki fice kinga already kin makara kuma Anas baya san latti.”
   “Kar yason” tace a k’asa k’asa.
     “Maza- maza! Tashi ki fice Fannah kar muyi fad’a dake da safiyan nan ko inje in sanar da Babanku ne?”
     “Allah sarki Mami dan Allah mana, gobe zanje I promise.”
   “Wannan kuma ke ya dama Afrah taho muje ki tayani shirya kayakin Aiman.” Da gwalon da Afrah ta ma Fannah tasa kai tabi Mami suka fice. Se zumbure zumbure Fannah take ita jiya da bata sa Mr. Fauzi a ido ba, ta wuni lafiya ba tashin hankali amman tasan definately suka had’u yau seya sata kuka, ita da ana shan maganin hana zuban hawaye da tasha. Ganin ba mahallici se Allah yasa kawai taja blue hijabinta me torches fari tasa, ta d’au jakarta ta sak’ala tare da cikasa da duk wani abinda zata buk’ata sannan ta fice ko sallama batayi dasu
    Ba ita ta isa office ba 8:34AM. Tana tsaye gaban office na Mr. Fauzi amman ta kasa shiga seta d’aga hannu zatayi knocking setaji kunya, yanzu yau wani irin kallo ze na mata? “Mschww Afrah ba kiyi ba wallahi” ta sake nanatawa for the hundredth time a zuciyarta. Ai haka ta kasa shiga office nasan, daga k’arshe nata ta zarce kawai taje ta had’a masa schedule (kamar time table haka) na ranan, tayi arranging komi, meeting d’aya yake dashi se mutanen da zasu zo ganinsa na signing contract guda biyu, sekuma na siyan shares na Global investments. Tagama ta ajiye a gefe guda chan ta ciro wayarta tana game itade yau barata had’a ido da Mr. Fauzi ba sekace wanda tayi sata.
      ***
     Anas kuwa yakasa tsinana wa kansa komai banda tunanin Fannah wai anya yau inbe sata a ido ba ze iya kwanciya lafiya kuwa? “Oh No! No! No! Why am I acting in this way? Coffee nake missing ba Fannah ba, coffee ne” ya tunar wa kansa. Ai daga k’arshe kasa hak’ura yayi ya tashi ya nufi office na Fannah koda bare ganta ba yau yaga office nata he is okay with it. Fannah na cikin game taji an murd’a hannun k’ofar office nata ido tasa wa k’ofan jiran ganin ko waye dukda kuwa zuciyar ta na sak’a mata wai Yusuf ne.
         Wayar ta tayi wulli dashi da suka had’a ido hud’u da Anas dama dalilin dayasa ta sako hijabi me hula kenan yau, da sauri sauri taja ta rufe fuskarta. Yin hakan seta tuna masa da incident na jiya seya gano dalilin dayasa take rufe fuskar kunyan sa takeji dan Afrah tace masa MP ke damunta, shi kansa kunyan ta yakeji bama batun MP’nta ba. In kuma tace meya kawo sa office nata fah? Karkuma tagane dan yana missing nata ne yashigo ta raina sa. Ganin batada niyyan magana yasa yayi giaran muryar. “So kinzo shine baki sanar dani ba? Nazo picking wani file ne dama” yayi k’arya yana wani basarwa.
     Da k’yar ta iya bud’e baki ta gaishe sa. “Good morning, wani file ne?” ta tambaye sa cikin siririyar muryarta.
          Rashin sanin wani k’aryan ze sake mata kawai yace, “to my office” chike da isa. Yana fita ta d’ago kai “to my office” ta kwaikwaye sa sannan tad’au jakarta da jotter’nta da pen da pencil tabi bayansa. Bayan like minti d’aya da shigan Anas office nasa Fannah tashigo itama kanta sunkuye a k’asa daidai gaban table nasa ta tsaya tare da mik’a masa jotter’n gabansa “here is your schedule for today, inda akoi abinda za’a giara let me know” D’agawa yayi ya dudduba yaga komai yayi, yaga ta ma fi Kacallah iya amfani da lokaci dan kuwa by 2:30PM ya gama komai nasa yau.
     So yake ya tambayeta ya jiki amman kuma girman kai irin nasa bare barsa ba seya bud’a baki zeyi magana se wani abu ya katse sa. Itako tana nan tsaye kansa har yanzu tana jiran amsar sa in da akoi abinda be masa ba yafad’i seta giara. Can k’asa k’asa almost kamar da kansa ma yake magana yace, “ya jikin ki?”
     Fannah kuwa taji sa amman dan yadda mamaki yaso kasheta se kawai tace hala kunnenta ke mata k’arya yaushe Mr. Fauzi ze tambayeta ya jiki? Karkuma tayi shiru yace ta rai na sa yasoma balbaleta yanzu a nan, dan haka tace, “eh? Excuse me” fuskar nan a rufe da hijabi har yanzu.
      “Ya jikin ki nace” yasake nanatawa with thesame voice level dayayi d’azu.   Se yanxu ta tabbata ba yaudarar ta kunnenta suke ba. “Da sauk’i” ta amsa a hankali duk seji take kamar ta nitse  k’asa dan kunya. Da k’yar tayi managing tace, “thank you.”
     “Bana buk’atar godiyar ki” ya fad’i mata gatsau sekace bashi yanzu yayi magana a hankali ba. Itafa har yau ta kasa gane hali irin na Mr. Fauzi yanzu yanzu seya mata mutunci take wajen kuma ya zagesa yadda yaga dama. Juyawa tayi ta nufa wajen coffee machine dan had’a masa ai bata soma ciro cup d’in ba ya jefa mata tambaya. “Me kuma zakiyi acan?”
    “Had’a maka coffee sir.”
    “Banaso, bana buk’ata just kitafi kije office naki if am in need of anything I will let you know.”
     Wai yau Mr. Fauzi ne ke fad’in baya buk’atan coffee to kode wanda ta had’a masa jiya beyi dad’i bane kasancewar zogin da hannunta yake mata. Shi kansa be zata ze iya fad’in baya buk’atar coffeen ta ba se gashi ya fad’a confidently ma kuwa.
        “Sir indan na jiya beyi dad’i bane I apologise hannu na ke ciwo, will make it better yanzu.”
    “Banaso nace just get out kuma na hanaki ja min wannan hijabin kina rufe fuskarki dashi, me kike dashi da banida? Ja hijabin baya.” Dakewa tayi tak’i ja seda ya daka mata tsawa “ja nace!” Tana b’ari ta giara “now leave” a sanyaye ta juya ta fice tana isa office nata ta zauna kan cushion.
    “Mschww wallahi Mr. Fauzin nan kanada mental illness, yanzu kama mutum mutunci da ‘yan mintuna kuma ka koresa kaman kashi thank god kai kazo har nan ka kirani bani na kai kaina office nakan ba. Wallahi kawai dan na danne zuciyata ne da nayi kuka, sede kata wa mutane masifa kai aikin ka kenan, Allah shirya wallahi ina tausaya wa matar da zata aure ka” (ni miemie nace kina tausaya wa kanki kenan) “ace kullum masifa, masifa. Ni barin cigaba da yin game d’ina ma.” Wayarta ta ciro tacigaba da buga candy crush.
      Kusan to 12:30PM Anas ya danna mata kira ta telephone kan ta shirya zasu meeting. Yau akeyinta ita gaskia bata shirya zuwa meeting ba amman ya ta iya? Bayi ta nufa tayi changing sannan tafito tak’i shiga office nasan ma bale ya mata korin kare kona akuyan daya saba mata. Bayan like 5 minutes Anas ya fito taga ya canza shirinsa yasa navy blue suit, white shirt da ocean blue tie sosai kam yayi kyau ga yadda gashinsa yasha giara kafin ya kamata tana kallonsa tayi saurin kau da kai, bece mata komi ba koda yaganta tsaye bakin office nasan juyawa yayi ya soma tafiya a yayinda take binsa a baya. Driver ne ya tuk’asu har hall da za’ayi meeting d’in sun iso da shiga ya juya ya kalleta “sauran yau ma kiyi tsaki kokuma ki baje kina bacci kinji ba Miss Aleeyu?”
      “Naji” tace ba tare da ta kallesa ba. Kamar ranan yana shiga mutanen suka tashi masa bayan sun gama gaggaisa wa ya zauna a kujerar tsakiyan nufin shine babba ma a meeting na yau kenan.
 
      Duk abinda ke gudana Fannah ta kasa kunne tana sauraro tare da jotting down major points kuma, gajiya tayi da tsayuwan ta zauna still hankalinta na kan meeting d’in. Time to time Anas yake d’ago kai yana kallonta sam idanunsu basu had’u ba.
     Se 2:30PM suka k’are boring meeting d’in, indagin Fannah yayi tsami dan zama bayan sun shiga mota ya tambayeta, “ina abubuwan da kikayi jotting?” Cikin jakarta tasa hannu ta ciro jotter’ta tare da mik’a masa. Se kuwa yaga duk important abubuwan da sukayi discussing akai na had’a kan Flames Enterprises da C&C Enterprises duk tayi jotting down  da kuma abubuwan da zasu amfanar da juna dashi, sosai kuma yaji dad’i. Amman meya kamata yayi wa Fannah? Godiya koba haka ba? But saboda dan girman kai irin nasa ya kasa, “nan gaba in ana meeting seki dena frwoning fuskarki ai kowa yasan meeting d’in ba dad’i gashi ki ajiye zan buk’ata anjima.” abin da yace da ita kenan.
      Sanyi taji sosai a ranta da beyi complaining akai ba amman kuma yak’i mata godiya dan uban girman kai. Sede abin da ta lura yau shine besa an k’ure AC kamar na ranan ba, kad’an kawai yasa driver ya kunna. Shikuwa Anas yayi hakan ne saboda batada lafiya, bayasan ya k’ara mata wani rashin lafiyar akan wanda take fama dashi, tunda ya karanci bame san sanyi che itaba. Yauma daidai gaban wata makekiyar hotel driver ya tsaya tare da bud’e masu k’ofa. Bayan sa tabi a hankali har suka shiga ciki, ba kowa daga su se masu aiki. A ranta tace wato kai baka iya cin abinci se kayi reserving, lallai kud’i ya maka yawa. A table daya zauna ta zauna itama, ko da waiter yazo d’aukan order’nsu Anas ne yamasa bayanin komi ita batace ko uffan ba ,wasa da siraran yatsunata kawai take tana kallon yankan da tayi shekaran jiya a yayinda Anas ke latse laste kan wayar sa. Bayan 3 minutes abincin su ya iso sede taga combination na yau yafi na ranan yawa, ba abinda babu kan plate nata k’wai ne kaza ne, kayan ciki na, pepper soup ne bade abinda babu shiko Anas kalan abincin ranan ya sake ordering.
      Toh mesa? Mesa za’a bani wannan babban plate cike da abincin kusan dubu biyar? Na Mr. Fauzi kuma na N1,500? Kode waiter’n yayi b’atan kai ne? “Uhm Sir are you sure wannan shine abincin nawa?” Ta tambayi waiter’n a yayinda yake zuba mata drink.
     “Yes Miss your Boss asked me to bring it for you.”
    “Boss?” Ta nanata a ranta tare da juyawa ta kalli Anas. Sam yi yayi kamar bema san maganar da sukeyi ba yakai spoon bakinsa a hankali. Bayan waiter’n ya tafi still Fannah ta kasa tab’a abincin ta dan bata yarda ba har yanzu.
     Anas kuwa dalilin dayasa ya sai mata abincin dubu biyar yau shine akoi time da ya tab’a kai Amal asibiti da menstral cramp ya tab’a rik’eta bayan da likita ya dubata ya bata maguna seyake cewa Anas a tabbata tana cin abinci me kyau saboda asaran jinin jikinta da take in tana period same goes to Fannah, sesu samu suyi restoring energy’n jikinsu. Itama saboda bleeding da takeyi yazamo dole taci abinci me kyau dan lafiyarta sesa ya siyo mata wannan abinci me kyau kuma me tsada.
   Ganin batada niyyan chi yasa ya dakata tare da kallonta, “well? Bara ki chi bane? Kinsan ba jiranki zanyi in na gama bako?”
     Baki na rawa tace, “S… Sir yayi yawa. In kace ni zan biya bansan ya zan biya ba.”
   Kallo ya watsa mata “last time da mukazo ke kika biya? Kin cika surutu, mschw. In zakici fine in bara ki chi bama fine” ya cigaba da chin abincinsa. K’in ci tayi wane ita abincin dubu biyar. Miss Aleeyu eat! Ko sena sab’a miki zakici? Ko kici kokuma in muka koma office inciro miki 500 papers kiyi zaman giaransu”
    Ai a hankali ta d’aga spoon nata ta soma ci a hankali, ta tab’a nan ta tab’a can sosai abincin ya mata dad’i. Bata san lokacin data baje ta fara ci kamar ba gobe ba Anas dake satan kallonta se mamaki yake mutum gata ba k’iba amman se aukin chi. Duk uban girman plate nata sanda taci morethan half, data jita dam tukuna ta goge bakinta ta kora da juice. Kallonta yake cike da mamaki har yasa ta jin kunya.
     “Kin k’oshi ko a k’ara?” Kai ta kad’a masa cike da kunya da nufin a’a. Waiter yakira ya biya kud’in plates nasu sannan suka kama hanyan dawowa office.
   *© miemiebee*
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 38
BY MIEMIEBEE
Washegari tun asuba Anas ya tashi saboda kasa bacci da yayi ga kuma rashin abin shaye shayen sa kusa dashi, koda na kusa dashin ma se yayi drama yake iya sha yanzu tun maganan da Fannah ta masa har yau yakasa erasing daga memory’nsa. Bayan yayi wanka ya shirya yafito already Ummie da Amal sun had’a masa breakfast, as usual shida Amal suka karya sede yau Anas ya zage yaci abincin sosai sab’anin yadda ya sabayi danko in be sha coffeen Fannah ba bai iya breakfast me kyau. Se forcing kanshi yake yana ci shi a dole yanasan mancewa da coffeen, a tunanin sa in ya dena shan coffeen ta ze iya mancewa dashi, eventually Fannan ma ze manta da ita seta zama missed call. (LOL)
    “Wai! wai! wai! Ya Anas ai ka cinye abincin bani yau.”
     Murmushi ya mata tare da rufa bakinsa ta hanyan aza hannunsa kai. “I’m sorry Angel yunwa nakeji. Nikam kunyi waya da Fannan office d’ina jiya?” Shiru tayi bata amsa saba gudun karya masifeta. “Angel I’m talking to you.”
     “Ya Anas kayi hak’uri.”
    “For? Amsa min tambayan dana miki mana kunyi waya jiya?” Kai ta giad’a a hankali cike da tsoro saboda Anas ya hanata waya da Fannah.
    “Meh tace miki?” Nan ma shiru tayi.    “Feel free and tell me barin miki komai ba kinji?” Ya d’ago hannunta yasa cikin nasa.
     “Promise Ya Anas baraka sake hana ni waya da ita ba?”
     “Yes Angel I promise.”
     “Tacemun batada lafiya mentral cramp yana damunta.”
     “Tace zata office yau?”
       “Tace min baza ta ba wai seta warke gabad’aya.”
    Kai ya giad’a tare da kewayo da kallonsa daga kan Amal zuwa kan plate na abincinsun “in ta haka menstral cramp d’in da wahala kenan.” Ya fad’i wa kansa kasancewar Amal na kusa dashi seta jiyo sa. “Sosai Ya Anas ni in ya tashi min ji nake kaman zan mutu.”
     Murmushi ya mata “bara ki mutu ba ma in shaa Allah barin wuce office kinji?” Kai ta giad’a masa a yayinda ya bata peck a goshi. “Ummie thank you for the breakfast na tafi” yache da d’an ihu dan Ummin dake kitchen ta jiyosa. “Adawo lafiya Babana” ta mayar masa itama da ihun.
    As usual k’arfe 8:00AM yayi masa a office nasa, Kacallah ya kira ya tambayesa ko yanada meeting yau. Unfortunately Kacallah yace masa ai duk wani schedule nasa na wajen Fannah. “Toh mesa ka bata duka?”
    “I’m sorry Boss but she is your PA, aikinta ne yanzu.”
    “Toh naji” yayu hanging.
  ***
     “Mami ni wallahi barinje office d’inba, barin sake komawa bama gabad’aya. Bakiji me Afrah tace masa jiya bane? Che masa tayi wai MP ke damuna.”
    Baki Mami ta bud’e tana kallon ikon Allah. “Lallai fa Fannah se akayi ya? Abune kowace mace tanayi, basuda mata ne a gidansu? Shi kansa ya riga yasan mene, ni banga abin jin kunya ba a nan ba.”
    Can k’asa k’asa Fannah tace, “ai dama baraki gani ba.”
    “Nima de wallahi Mami” cewar Afrah.
    “Kekuma Afrah kika kuma wannan rashin hankali zan sab’a miki, Aiman ce yakamata tayi wannan sokanci ba ke ba.” Mami tayi lecturing nata. Juyawa Fanna

Haka har da aka tashi Anas be sake neman Fannah ba. So yake ya nisantar da kansa daga gareta as possible enough as he can, saboda ya soma ji kamar maganganun Shettima gaskia ne. Saboda when it comes to Fannah he is weak abubuwa dayawa take masa wanda yaci ace ya koreta koya hukunta ta amman seyaji bare iya mata komai ba. Yasoma yarda eh he is feeling something for Fannah amman ba love bane tausayi ne kawai, yana tausayawa mata sede ko daya tambayi kansa tausayin me take basa yakasa answering. Fannah is his weakness.

Fannah kuwa dad’i taji da be sake nemanta ba dan da wannan kayan kunyan da tama kanta na masa shisshigi harda karance diary’nsa bata san da wani idan zata sake kallonsa ba. Ita abinda yafi bata mamaki ma shine yadda Anas yabata hanky wai ta goge hawayenta bayan abinda ta masa, shin meke damunsa yau? Ta d’au atake zeyi firing nata kokuma ya mata wani abu makamancin haka amman seyayi sab’anin abinda take expecting. He is acting wierd yau, bata tab’a ganinsa haka ba shida yake fad’in kukanta bai damunsa segashi yau bayasan ji.

Hanky’n ta ninke tasa cikin jakarta sannan ta mik’e tare da rufo k’ofar ta dan ganin lokacin tashi yayi. Ta rufe k’ofar office nata ta juya kenan sega Anas shima yafito suna had’a ido tayi saurin kawar da kanta. Public elevator tabi a yayinda Anas ke binta da kallo so yake yace mata ta zo su shiga elevator’nsa amman kuma girman kansa bare bar sa ba, wai mesa ma yakesan su shiga elevator’n sa bayan abinda ta masa d’azu? Sanda ta b’ace sannan ya nufa nasa ya shiga shima, kafin ya sauk’o kuwa tuni Fannah ta k’ara mai. A d’an wani shago ta tsaya tare da yima family’nta d’an siyayyan kayan k’walama. Isarta gida keda wuya.

Mutane biyun data gani tsaye cikin gidansu ne suka mugun razana ta. Ido wuru wuru ta zaro tare da dafe k’irjinta tana me salati a zuci. “Baffah Khaleel?! Ya Farouq?!” Kai tasoma kad’awa danko bata yarda da abinda idanunta suke gane mata ba. Mami dasu Afrah dake tsaye gefe guda suma fuskarsu d’auke yake da damuwa.
“Mami dan Allah kice min basu bane, tell me idanu na wasa suke min.”

“Fannah manyan gari wato har gidan TV ake nuna ki, ‘yan matan nawa fa duk sun girma sosai tunba Fannah surikata ba.” Cewar Ya Khaleel yana wani murmushin mugunta.
“Kai Farouq baka ga matarka bane da baraka mata magana ba? Jeku gaisa mana.” Wani tantirin dariya ne a fuskar Farouq a yayinda ya soma takowa gaban Fannah. Baya tayi take ganin haka “Fannah mata ta ya haka kuma? Mijinki ne fa ni, bekamata kina min haka ba, matso mana mu gaisa.” Sosai Farouq ya sake girma yazama cikakken na miji yanzu kyansa ya sake fitowa, sede iskancin nan nasa daya saba har yanzu yana yi be bari ba.

“No don’t touch me.” Kamar kyaftawan ido Mami tashigo tsakaninsu, “Ya Khaleel meh amfanin haka dan Allah? Nasan kai da d’anka kunfi k’arfin mu dan Allah kuyi hak’uri ku koma inda kuka fito. Fannah bata san Farouq Ya Khaleel kayi wa Allah ka hak’ura da kai da d’anka dan Allah.”
“Maman Aiman kenan, in kinga mun koma Bama toh wallahi da Fannah ne. Wace karuwar ‘yarkun ma wacce ko martaba battada, dan ni da Farouq zamu rufa mata asiri zaku wani tsaya kuna mana tsiya yau shekarunta nawa takasa yin aure, ba d’a na mijin da ze amince ya auri Fannah inba Farouq ba.”

“Baffah Khaleel dan Allah kayi hak’uri ka rufa min asiri banasan sake komawa Bama, banasan Ya Farouq ni na rungumi k’addara zan gama rayuwata duka ba aure dan Allah kar ka aura min Ya Farouq.” Fannah ta fad’i hawaye na gangarowa kan kumatun ta abin tausayi. Tajima bataji tashin hankali kamar na yau ba. Ta riga da ta ajiye past nata a gefe mesa su Baffah Khaleel zasu dawo su hargitsa mata komai??

“In baki son shi to shi yana sanki sakariya kawai, aure tsakaninki dashi kuma farillah ne nan da ‘yan watanni, gomma tun wuri ku fara shiri, karatu ne Farouq yayi. Yanada diploma’nsa dakuma aiki me albashin da ze iya rik’eki. Kinga ko wannan karan ke zakiyi kayan d’akinki tunda kema kinada aiki. Abinda ya kawo mu dama kenan, bayan biki zaki bi mijinki Bama ku fara zama acan, in qaninan ya tashi ku gaishesa. Farouq mu tafi.”

“A’a Baba ni ba yanzu ba semun gaisa da matar tawa tukuna.”
“Karka damu akoi gobe ai, gobe zaka dawo har girki seta maka tunda matar kace, mu tafi.” Nan suka fice. Kuka me k’arfi Fannah ta rushe da. Mami na bata hak’uri haka Afrah da Aiman ma. “Mami ni shikenan Ya Farouq zan aura? Duk inda mukaje se sun tsakuro mu. Mami dan Allah do something wallahi banasan Ya Farouq mugu ne, azzalimi banasan sa Mami.” Ta k’ara shigewa jikin Mami tana kuka me tsuma zuciya.
“Yi shiru Habibti in shaa Allah baraki auri Farouq ba kamar yadda Allah ya k’wato ki kwanakin baya haka ma ze miki yanzu mu dage da addu’a kawai.”

“Ya Fannah kiyi hak’uri zamu tayaki da addu’a” cewar Afrah cike da tausayi. Kuka sosai Fannah takeyi haka yadda taga rana taga dare ta kasa bacci. A ranan kowa hankalinsa tashe yake basu san kuma ina zasu sake zuwa ba, basu san ko in sun bar Maiduguri akoi inda zasuje Fannah tasamu aiki me kyau kamar na nan ba. Baba ya tausaya wa ‘yarsa sosai ba kuma abinda yafi bak’anta masa rai kamar in ya tuna ba abinda ze iyayi ya cheto ‘yarsa daga halaka. Dan auren Farouq halaka ne yaron da besan darajar mace ba ko kad’an, d’an giya d’an iska.
Daga Fannah ta rufe ido seta soma mafarke mafarke ganin ba mahilicci se Allah ta tashi tayi alwala tariga nafilfilu har seda k’arfinta ya k’are sannan tayi zaman istighfaar. Da safe ta tashi tana shirin office sanyi sanyi kamar wacce k’wai ya fashe ma aciki duk Afrah na kallonta takasa koda ce mata uffan dan tausayi. Mami ce tashigo ta tarar da ita tana sa kaya bayan gaisuwa Mami ta tambayeta cike da tausayi “Fannah ba se kinje office ba yau ki huta”

“Mami gomma inje saboda zama anan ba abinda ze haifar min inbanda bak’in ciki jiya Baffah Khaleel yace Ya Farouq ze dawo yau, bana san ganinsa Mami na gwammaci naje office.”
“Toh shikenan Fannah Allah kare kicire damuwa daga ranki kinji? Muna nan muna kan miki addu’a.”
“Nogode Mami ni na tafi.” “Allah kare” both Mami da Afrah suka mata sannan ta fice.

8:01AM daidai ya mata a office na Mr. Fauzi kanta sauk’e a k’asa ta gaishesa, sama sama ya amsa. Jakarta ta bud’o tare da ciro hand kerchief daya bata jiya ta ajiye kan table nasa. “Gashi, nagode.” D’gawa yayi ya sake mik’a mata “na baki keep it.”
“But Sir-” katse ta yayi “I said keep it” yace a hankali. Amsa tayi tare da masa godiya ta mayar cikin jakar ta.
Har yanzu basu had’a ido ba dan kanta a sunkuye yake.

“Ina schedule d’ina na yau?” Ya tambayeta yana danne danne a laptop nasa.
“I’m sorry bansamu na had’a ba excuse me yanzu zanje in had’a maka.”
“Mesa? Me kikeyi tun jiya da baki had’a ba?” Ya tambayeta cike da tsiwa.
“I’m sorry” tace nan ma bata d’aga kai ba sede daga yadda take maganar Anas ya gano wani abu na daminta ya tambayeta meneh kuma girman kansa bare barsa ba. Kallonta ya tsaya yi kusan na minti biyu amman sam bata gwada yunk’urin d’ago kai ba bale ya kalli cikin idanunta ma. “Miss Aleeyu” ya kira sunanta a hankali.
“Yes Sir” ta amsa ba tare da ta d’ago kai ba. “Make me coffee” ya fad’i. A sanyaye ta juya ta nufa wajen machine d’in sede hankalinta ko kad’an baya jikinta tayi nisa tunanin abubuwan da suka faru jiya she actually can’t believe Baffah Khaleel da d’ansa Ya Farouq sun dawo suna san maida ita Bama da bata sake tsammani zata koma wataran ba.

Bayan ta gama had’a jagual-gualenta ta juyo dan ba coffee ba sunan abinda ta had’a. D’an k’usa ne ya kama mata hijabi agarin cirewa tayi b’arin coffeen duka ya zube a k’asa cup d’in kuma ya fashe. Kid’imewa tayi a lokaci guda batasan lokacin da ta tsuguna ba dan tattarawa. “Don’t Miss Aleeyu karki ki tab’a” Anas yayi warning nata da ihu chak ta maida hannunta. “I’m sorry” ta fad’i hawaye na cikowa a idanta. “I’m sorry please” ta sake basa hak’uri.
Toh kuma kukan meh? Ai be tab’a taba, bekuma mata masifa ba kodan d’an ihun dayayi dan kar ta tab’a glass d’inne ya sata kuka? Tasowa yayi daga mazauninsa ya nufo gabanta har yanzu tana tsugune “get up” yace mata. A hankali ta mik’e kanta sunkuye se hawaye takeyi side bag nata ya mik’a hannu yaja a hankali, batace masa komai ba, bud’ewa yayi ya ciro handkerchief daya batan “wipe off your tears” amsa tayi ta na gogewa sede the more tana gogewa the more kukan yake k’aruwa harda me sauti da k’yar ya zaunar da ita.

Besan me ba se kawai yaji ya damu da ita bayasan ganin ta tana kuka. “Miss Aleeyu mesa kike kuka na miki wani abu neh?” ya tambayeta a hankali. Kai ta kad’a masa da nufin a’a tana me cigaba da kukan.
“Toh mesa kike kuka? Sabida glass cup da kika fasa min ne? Don’t worry I have lots more.”
Kukan take har yanzu ba makawa hasali se k’ara volume na kukan nata ma take. “Miss Aleeyu what is it?” Kai kawai take kad’a masa chan ma ta tashi ta ruga office nata a aguje kan table nata ta baje sekuka take shark’af shark’af abin tausayi. Anas nason bin bayanta amman girman kai irin nasa bare barsa ba. “For goodness sake what is wrong with me? Mesa nake damuwa da Fannah? She is not my responsibilily so let her be, duk abinda ke damun ta ita taji wajen.” Mik’ewa yayi tare da zama kan kujerar sa yana me cigaba da abinda yakeyi. Sede inaa mind nasa gabad’aya yana wajen Fannah. What if har yanzu kuka take? Me aka mata ko daga gida ne aka b’ata mata rai? Wayarsa ya d’ago dan kiran Mami se in ya soma shiga se ya katse haka ya kasa kirarta dan tambayen meke damun Fannah. Meeting dayake dashi ma yau shi kad’an sa yaje saboda yasan there will be no point yaje da Fannah tunda haka ta taho yau tana kuka. Shi kad’ansa yaje though shima duk hankalin sa na kan Fannah bayan da meeting d’in ya k’are as usual driver ya wuce dashi hotel dan cin abinci.

Ga abincinsa a gabansa amman yakasa chi, dududu sau nawa suka chi abinci da Fannah amman yaji yau inba ita bare iya chi ba kuma bawai fa baya jin yunwa bane kawai seda ita ze iya chin abincin. Kacallah ya kira kan ya sanar da Fannah driver ze zo d’aukanta yanzu dan bayasan ya kirata da kansa ta raina sa, hakan kuwa akayi bayan 20minutes aka kawo Fannah hotel d’in tana shiga tagansa zaune dan bata masan nan za’a kawo ta ba ce mata kawai akayi Boss na nemanta. Idanunta sun kumbura sunyi ja dan kukan datasha a hankali ta k’arisa gaban table nasa ta tsaya ba tare da tace uffan ba.
“Sit” yace mata hakan ko tayi bada jimawa yasa aka kawo mata abinci sak irin na jiya. Nan ma “eat” yace mata.
“I’m not hungry” ta masa k’arya dan kuwa ko breakfast batayi ba yunwa takeji amman batada appetite na cin abincin saboda damuwar dake kanta kad’ai ya isheta. Spoon biyar yakai yaga ko yunk’urin tab’a abincin ta batayi ba.
“Miss Aleeyu bakiya so ne akawo miki wani daban?”
Kai ta kad’a masa. “Then why are you not eating?”
“Sir I’m sorry bana jin yun-” bata k’are maganar ba cikinta yayi wani irin kuka.
“Yes kinajin yunwa eat.” Nanma kai ta kad’a masa. “Kichi kokuma in baki 500 papers kiyi correcting nasu” ya gwada taorata ko dan haka zata chi. “Okay I’ll do it in muka isa office d’in.” Mamaki sosai amsarta ya basa itan da kullum take had’asa da Allah in ya bata aikin yau ita ke fad’in zatayi kai tsaye? Toh meke damun ta?

“Miss Aleeyu meke faruwa? Meke damunki? Tell me.” Ya tambayeta cikin sanyin murya dan duk yashiga cikin damuwa ganin Fannah a damuwa.”
“Babu Sir thanks for your concern, zan jiraka a waje in ka gama se mutafi in fara correcting papers d’in da wuri saboda in gama on time.”
“Barakiyi correcting komi ba, I don’t mean it kawai kichi abincinki kinji? You are sick har yanzu zama da yunwa won’t help, eat.” A hankali ta d’aga spoon nata ta soma ci sede ba hab-hab kamar yadda ta saba ba. Anas ko da jimawa yagama cin nasa yayi zaman jiranta saba’anin yadda ya saba. Dududu quarter kawai taci tace ta k’oshi. “Are you sure?” Ya tambayeta kai ta gaid’a masa. Bayan ya biya kud’in suka fice.

Shigarsu mota Anas yace da driver “ba office zamu wuce ba gidansu Miss Aleeyu zaka kaimu.” Cike da mamaki ta d’ago kai se yanzu suka had’a ido dashi tun had’uwansu yau. “Gidan mu kuma Sir? Mesa?”
“Saboda inji meke damunki.” Yabata takaicaccen amsa.
“No Sir please don’t ba abinda ke damuna kawai fad’a mukayi da Afrah” tanasa k’arya
“Ban yarda ba” ya bata amsa yana duban agogon sa.
“Sir I’m serious.” Ita tsoronta kar in sunje su had’u da Baffah Khaleel kamar yadda ya saba kiranta da karuwa ko karya ya kirata gaban Anas. “Sir please mu juya na bar wayana a office I need to get it.” ta masa k’arya ko ze canza mind nasa.
Resting kansa yayi jikin kujerar “karki damu zansa Ahmad ya kawo miki.”
“Sir-” hannu ya aza kan lips nasa “shhh! Banasan surutu dayawa.” Ahaka har suka iso gaban gidansu Fannah zuciyarta se bugun d’ari d’ari yake. Driver na parking Fannah ta fito da sauri dan duba ko su Baffah Khaleel suna gida takai da shiga k’ofar gidansu kenan kawai suka ci karo da Ya Farouq kafin tayi wani k’wak’waran motsi ya cafko ta da hannu daidai lokacin Anas yake fitowa daga motan shima, idanunsa basu tsaya ko ina ba se kan hannun Farouq rik’e dana Fannah se k’ok’arin k’wata take amman ta kasa. Wani erin mahaukacin kishi yaji ya bugesa inba wai kashe koma waye mutumin yayi ba yana ganin bare samu sukuni ba.

A fusace ya k’ariso wajen. “Matata me haka dan na kama miki hannu? Ke wai bakiyi missing d’ina bane? Ko d’an shafaki bara ki bari inyi ba?” Cewar Farouq dawani shu’umin murmushi fal a fuskarsa.
“Ya Farouq ka sake min hannu niba matar ka bace let me go” ta fad’i tana hawaye tare da k’ok’arin k’wace hannunta.
“Ka sake mata hannu!” Anas ya fad’a cike da isa. Fannah da Farouq tare suka juya suna kallon Anas. “Waye kuma wannan baturen?” Farouq ya tambaya.
“Mr. Fauzi please ka tafi, don’t involve yourself in here.”
“Kinsan sa kenan” Farouq ya sake tambaya. “Bade shima saurayin ki bane kina kwana dashi, kinsan sana’a sa’a.” Anas be san lokacin daya kai wa Farouq naushi a fuska ba da zobobin azurfa a hannunsa. Take hancin Farouq ya fashe gefen bakinsa yasoma na d’igan jini.

© miemiebee

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 42
BY MIEMIEBEE

          Baki Fannah ta bud’e tare da aza hannunta bibbiyu kai cike da mamaki da tsoro duka. Hannu Farouq yasa tare da tab’a inda yaji moisture a fuskarsa yana dubawa yaga jini ta hanci da bakin sa, “Kai! Ni ka fasawa baki? Dama nasha jin cewa ku turawa bakuda tarbiyya yau zan koya maka.” Hannu ya d’aga da k’arfin da Allah ya bashi shima ze kai wa Mr. Fauzi punch ai karap Anas ya kama hannun nasa tare da murd’awa cike mugunta ta bayansa. K’ara sosai Farouq ya saki dan azaba.

    Fannah duk ta rikice “Mr. Fauzi please ka sake sa ya isa please” ko saurarenta Anas beyi ba k’ara murd’a hannun nasa yayi a bayansa k’ara sosai Farouq ya sake saki dan azaba. “Repeat what you just said.” Anas yace dashi, daga yadda yake magana ma kad’ai za’a san ransa a b’ace yake, na bala’i ma kuwa. Duk zafin da Farouq ya keji be hanasa misbehaving ba. “K’arya nayi dan nace kuna kwana tare karuwarka ce”
     “You really want to die” Anas ya sake shi, kafin Farouq ya sake wani k’wararren motsi Anas ya sake kai masa punch a fuska fiye da yadda yayi d’azu sosai jini yake fita daga baki dakuma hancin Farouq.

     “Mr. Fauzi please ya isa dan Allah” Fannah ta fad’i duk a kid’ime idanta tuni suka cike da hawaye.
    “Kai ko kasan waye ni? Mijinta ne fa ni, aurenta zanyi banza da kai zakazo kana intruding. In ita karuwan kan bata fad’a maka yanzu ai kaji I’m her husband. Ke Fannah dan iskanci ya miki yawa kin kusa aure ma baraki fad’awa ‘yan iskan samarukan kin su hak’ura bako?” Hannu ya mik’a ze jata dan wanke ta da mari. Kamar a kyaftawan ido Anas yajata bayansa kamar ‘yar baby tare da rik’e hannun Farouq, rik’o kawai ya masa amman idan Farouq sanda ya cike da hawaye. D’ayan hannunsa ya d’aga ze sake kaiwa Farouq mumunar punch Fannah ta rik’e hannunsa da nata bibbiyu. Hawaye take sosai “Mr. Fauzi please ya isa kayi hak’uri ya isa please.”

     Hawayen da takeyi ne kawai ya hana Anas kaiwa Farouq punch da ze iya kwantar dashi a asibiti. Kwalan rigar Farouq ya chukumo. “In bakada manners na magana wa kamilallaiyar mace I will teach you some, the next time ka sake kwatanta Fannah da wad’annan munanan suna I assure you zakayi kwanan cell, pathetic fool kawai, idiotic bastard.” Sannan yayi wulli dashi har k’asa Farouq yayi landing, daidai lokacin Ya Khaleel ya yanko kwanan gidansu Fannah shi a dole yazo cin abincin ranan da surikarsa ta dafa masa kamar yadda yace jiya.

     Ai ganin his only son a k’asa ga kuma jini ko ta ina fuskarsa ya falfala da gudu yayi kan Farouq. “Farouq meya same ka? Wani d’an shegiyan ya maka wannan tsiyan, waye shi?”
       “Baba kafin ka kira wani da d’an shegiya make sure ka cire sunan d’anka daga number a list d’in. Nayi warning nasa but I think I have to warn you too, the next time ya sake shiga harkan Fannah bare kwana a garin Maiduguri qalau ba.”

     “Tohh sannu fa, sannu shugaban k’asan Nigeria. Toh kaine d’an shegiyan ba d’ana ba, kai har kanada da right da zaka hana Farouq shiga harkan Fannah ne? Ka tab’a jin inda aka shiga tsakanin mace da miji?”
   Fannah dake tsaye bayan Anas tace, “Baffah Khaleel Ya Farouq ba miji na bane.”
    “Ke karuwa rufa min baki.”
   Ran Anas in yayi dubu be b’aci ba, taku yayi yunk’urin yi zuwa gaban Ya Khaleel dan kai masa had’add’en punch shima, “how dare you call Fannah karuwa!” yace a yayinda Fannah ta rik’e rigansa dan hanasa aiwatar da abinda yayi niyyar yi. “Mr. Fauzi let them be please, ya isa ka tafi wannan problem d’ina na ne bansan na jaka ciki, please go.” Wayarsa ya ciro a fusace bayan an d’aga yace, “Hello send me 10 men, I mean 10 a unguwar Polo…” Nan ya masa kwatance. Baki na b’ari police d’in yace, “yy.yyyes Sir right away!”

    Aiko cikakken minti biyar da gama wayan Anas beyi ba sega motan polisawa guda biyu. Farouq harda rud’ewan ciki Ya Khaleel kuwa sanda ya saki fitsari a wando shi be d’au dagaske baturen yake ze kira polisawa ba, toh waye shi.
     “Take them both, kuje ku rufesu right away” ya fad’a a fusace.
    Farouq da baki ke jini yace, “wallahi kayi k’arya me mukayi da zakace aje a rufe mu?” Can k’asa k’asa Ya Khaleel yace, “kai kayi shiru se yanzu nagane waye wannan mutumin, ba bature bane shine wanda aka nunasa da Fannah ranan a BRTV wallahi babban mutum ne mu basa hak’uri in bahaka ba in aka rufemu me bailing namu se Allah.”

     “Mr. Fauzi ko? Dan Allah kayi hak’uri, wallahi misunderstanding aka samu anan my apologies please karka sa a rufe mu dan Allah. Farouq baraka basa hak’uri bane?”
     “Officer take them away banasan jin komai.”
    Nanne bakin Fannah ya bud’u. “Mr Fauzi please kayi hak’uri karka rufesu dukda cewar basuda kirki ‘yan uwana na ne, Ya Khaleel Baffah na ne Ya Farouq kuma cousin d’ina kayi hak’uri and set them free please.”
    “Miss Aleeyu why? Bakiji munanan sunan da suke kiranki dashi bane?”
    “Naji Sir just please set them free, please.” Ta fad’a idanta na cikowa da hawaye.
    “Officer let them be zaku iya tafiya sorry for the disturbance.”
   “Ba komai Mr. Fauzi muna da godiya”
  “Zuwa anjima zakuji alert thanks.”
    “Mungode sir, mungode sir” a haka suka ja motocinsu suka fice.

    “Miss Aleeyu kinasan in samusu retricting order from the law yadda barasu sake zuwa kusa dake ba? So they won’t disturb you in na bar nan?”
     “Sir thank you but karka damu in shaa Allah ba abinda zasu iya min you can go kadena b’ata lokacinka akaina please, thank you”
    “Call me in wad’annan foolish mutanen suka sake miki wani abu” ya k’are maganan yana ma Ya Khaleel da Farouq kallon banzaye cikin banzaye. Farouq zeyi magana Ya Khaleel ya taka masa k’afa dan haka yayi shiru.
    “Ki shiga ciki.”,Ba musu bale gardama ta shige ciki sanda ya tabbata ta shiga ya dawo da kallonsa kan like father like son yana nuna su da yatsa “kun ji na rantse in kukayi ma Fannah wani abu zaku k’are rayuwanku a jail, assholes.” Yana kaiwa nan yashige motarsa driver ya rufe yajasa suka fice.

      Se yanzu bakin Farouq ya bud’u. “Shege se meh? Wallahi kasani ka tab’o tsuliyar dodo, zancen kakeso.”
    “Kai Farouq ya isa saurayin nan babban mutum ne a garin nan ka rufa mana asiri muyi abinda ya kawo mu mukoma da Fannah Bama cikin kwanciyan hankali.” cewar Ya Khaleel.
    “Wallahi Baba be isa ba ya zubar min da jini ya kwana lafiya Allah kaimu gobe. A ina yake aiki kace?”
    “Wai meka isa kayi masa ne dawani fashasshen bakin ka da hancin ka, se uban kurin baki wai kana zuwa gym ji yadda kabari wancan Fauziya ne ko Fauzi ya maka tatas. Kona fad’a maka inda yake aiki me ka isa ka masa?†
   “Niko nasan me zan masa just tell me ina yake aiki?”
    “A Flames Enterprises shine CEO’n wajen naga sun sa a TV” 
   “Good” Farouq yace tare da ficewa. Babansa na kiransa ko a kwalan rigarsa, Ya Khaleel kuwa shegen tsoro ne dashi sekace farar kura. So yake ya shiga cikin gidansu Fannah amman kuma yana tsoron abinda Mr. Fauzi  ya fad’a masa. Dan haka ya nufa masauk’insu kawai.

    Anas kuwa isar sa gida ya wuce d’akinsa tare da sa lock ba tare da yace da kowa komi ba. Wani irin tausayin Fannah yaji ya kama sa, ba abinda yakeso yanzu kamar yayi protecting Fannah daga wannan shegun Baffan nata da d’ansa. Mesa zasu na kiranta da karuwa? Mesa zasu na kiran yarinya me tarbiyya kamar Fannah da karuwa? To kode ta tab’a yin hakan ne da a baya se Allah yamata shiriya? “No!” ya fad’a a fili no matter what Fannah batayi kalan wanda zata iya aikata abinda uncle nata yake fad’a ba. Ai inhar dagaske karuwan ce da bare so ya aura wa d’ansa ba k’azafi kawai suke mata, ayyah ashe shiyasa taketa kuka a office yau, shiyasa ko abinci ta kasa ci. “I will protect you Fannah no matter what.” Ya fad’a a fili.

   *****

9:23PM
     Fannah da family’nta ne zaune d’akin Baba yanzu tagama basu labarin abinda ya faru d’azu, abinda Mr. Fauzi yama su Ya Khaleel. Kowa wajen yasha mamaki matuk’a.
   “Alhamdulillah! Alhamdulillah! Allah sak’a wa Anas da alhkairi, abinda yama Ya Khaleel daidai ne Allah saka masa da alkhai”  “Ameen” kowa ya amsa wajen.
     “Habibiti amman har duka Anas yama Farouq?” Mami ta tambaya cike da mamaki.
   “Eh Mami, Mami tsoro nakeji wallahi Ya Farouq ze iya cewa ze rama dukan akaina.” Rungumota Mami tayi gam ajikinta tana shafa jelar gashinta da d’ankwalinta be samu ya rufe ba. “In shaa Allah ba abinda ze miki kina da Allah bayan haka kuma ga Anas na tabbata bare bari wannan shegen Farouq d’in ya miki wani abu ba.”

    ***

    10:30PM
“Wai ina wannan hegen yaron yajene?” Cewar Ya Khaleel da kansa for the 100th time yana duban k’ofar one room apartment da suka d’an kama da d’ansa. Chan ya hango shadow’n mutum, torchin hannun sa ya haska, ganin Farouq ke tahowa ya saki hamdala tare da nufan wajensa. “Kai Farouq ina kashiga tun d’azu? Kasan na rasa mahaifiyarka barin iya juran rasaka ba kaima. Kuma dan rashin hankali haka kata yawo a gari da fashasshen baki da hanci?” K’eyarsa ya tand’e “wuce ciki mu goge maka.”

5 minutes later…

    Farouq ne mik’e kan ‘yar katifarsu a yayinda Ya Khaleel ke treating masa ciwon da Anas yaji masa a fuska da dettol. “Ina kaje ina tambayarka tun d’azu kamin shiru.”
    “Kai de Baba Allah kaimu gobe se Mr. Fauzi ne ko Fauziyan nan ya raina wa kansa nan gaba ko kafad’an juna muka buga bare min koda kallon banza ba.”
   “Wai me kake nufi Farouq? Kaga fa ka rufa mana asiri ni na fad’a maka kokuma in anzo tafiya damu in ce mai kai kad’ai ne banda ni, am warning you.” Lebb’an sa yacize irin mazan nan mana aikuwa yacize wajen ciwon.

★★★
Washegari…

      K’arfe 8:10AM ya ma Fannah a office na Mr. Fauzi tun 8:00AM yake jiranta a zatonsa ma ko barata samu zuwa ba se kawai ya ganta, har cikin ransa yaji sanyi sede yau ma fuskarta ba walwala kamar jiya. As usual ta k’ariso gaban table nasa ta gaishe sa kanta a sunkuye. “Good morning Mr. Fauzi.”
     “How are you feeling?” ya tanbayeta a hankali.
   “Alhamdulillah, thank you for yestarday.”
   “Ba komai” yace mata.
    “Sir bansamu nayi making schedule naka jiya ba am sorry.”
  “Is okay” yace mata ba tare da ya nuna damuwa ba. “Mesa baki fad’a min ba?” Ya tambayeta. A hankali ta d’ago kanta idanunsu na had’uwa ta sake sunkuyar da kanta, “I’m sorry” tace sincerely.
    “Baki amsa min tambaya na ba, mesa baki fad’a min abinda wad’ancan biyun suke miki ba. Saisa kikazo jiya kika ta kuka kenan koh? Akansu ne?” Kai ta giad’a a hankali.
   “Mesa baki sanar dani ba?”
  “Sir I thought there will be no point in fad’a maka sesa kawai nayi shiru.”
    “Next time call me up and tell me kinji?” Kai ta giad’a tare da godiya.
   “Sun sake miki wani abu?”
   “A’a.”
     “Dagaske ne zaki auri wancan Farouq d’in?” Ya tambayeta kamar me jin kishin ta. Kai ta giad’a a hankali.
      “Mesa? Kina son shi ne?” Nanma kai ta giad’a.
    “Miss Aleeyu” ya kira sunanta “na’am” ta amsa kan ta a sunkuye. “Look at me.” A hankali ta d’ago kanta tana kallonsa kamar yadda shima yake kallon nata. Ba komi ne tattare da idanunta ba inbanda tsoro. “Do you really love him?” Ya sake tambayar ta cikin sanyin murya.

      Hawaye tajiyo na ciko mata, “no Mr. Fauzi banasan sa, ban tab’a san sa ba, mugu ne, azzalimin da besan daraja ta ba.”
     “Shhh is okay kar kiyi kuka, bakiya sansa baraki aure sa ba kinji?” Har hawayen nata sun soma sauk’owa ya ciro hanky ya mik’a mata amsa tayi ta share hawayen. “Sir how? Baffah Khaleel is powerful ni nasan dole zan auri Ya Farouq.”
  “No baraki aure sa ba I promise, jeki huta Kacallah ze kula da aiki ki yau.”
   “Sir don’t worry zan iya yin aik-” bata k’are maganar ba ya katse ta “banasan musu idanunki sun riga sun nuna baki samu bacci ba jiya so just go before I change my mind.” A hankali ta juya sanda takai bakin k’ofa sannan ta juyo tana kallonsa taga yana tattara files na gabansa “Mr. Fauzi” ta kira sunansa chak ya bar abinda yakeyi tare da d’ago blue eyes nasa yana kallonta. “Yes?” Ya bata amsa.
    “Thank you” tace dashi. D’an murmushi ya saki wanda ya sake bayyano da kyan sa. Giad’a mata kai yayi as an answer sannan ya cigaba da abinda yake a yayinda tafice zuwa office nata ita kuwa.

    Batasan me ba amman kwana biyun nan in _TANA TARE DA_ Mr. Fauzi setaji she is safe kuma setaji ta ba damuwa. Kan cushion nata ta baje a hankali bacci me uban nauyin gaske ya isketa wanda takasa yi jiya da daddare dan yadda damuwa suka mata yawa.

  30 minutes later…

A nitse kuma a hankali Anas ya bud’e office na Fannah. Taku d’ai d’ai yake a hankali har yashigo cikin office d’in zube ya sameta kan 3 seater tana bacci peacefully. Har gabanta ya tako tare da tsugunawa d’an hijabin daya tare mata fuska yasa hannu ya gyara dogayen eyelashes nata yatsaya yana kallo sannan yakoma kan girarta dayake nan kamar na Kajol na india yadda ya had’e me kyan bala’i. Sekuma d’an siririn hancinta dayake nan madaidaici dakuma d’an bakinta dakenan ba k’aramin chanba bakuma babba ba tsakatsakiya.

    Besan dalili ba amman kawai ya tsinci kansa cikin jin dad’i, killer murmushi ne kwance kan kyakkyawar fuskarsa wanda ya lotsar da dimple nasa na gefe d’aya. Jakanta dake saqale a kafad’arta ya zira hannu ya cire a hankali yadda bare tada ita ba, tare da ajiye wa a gefe guda, k’afafunta ya daidaita kan kujerar tare da kunna AC’n a medium ta yadda beyi yawa ba bekuma yi kad’an ba. Ficewa yayi zuwa d’akinsa ya d’au wani arabian bargonsa me uban laushi da pillow yazo ya rufeta dashi tare da aza kanta kan pillow’n    ya juya ze fita kenan Fannah ta kama bakin suit nasa ta baya chak ya tsaya tare da juyowa hannun nata ya raba da kayansa a hankali sannan ya rufo mata k’ofar ya fice zuwa office nasa. Yau yagama had’a model nasa sauran asalin gini yanzu. Already filinsa na nan kawai abinda yarage shine asa drawing d’in into action.

© miemiebee

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 43
BY MIEMIEBEE

Bacci meh rai da lafiya Fannah tayi wanda ta jima ma batayi ba se chan bayan azahar ta tashi. A hankali ta bud’e idanunta jin kanta tayi kan pillow cike da mamaki ta duba harda bargon ma, toh waya shigo ya rufeta? Waya kunna mata AC? Ko kad’an bata kawo Mr. Fauzi arai ba saboda tasan halinsa, toh kode Yusuf ne? Toilet ta nufa ta wanke fuskarta tare da brushing sannan tafito ta ninke bargon tsab ta had’a da pillown sannan ta d’aga tafito dashi a hannunta floor na office nasu Yusuf ta nufa akan table nasa ta tsincesa bayan sun gaisa tace, “gashi nagode, shine akan ka tada ni narufe kaina kayi min wahala haka?”

    Cike da mamaki Yusuf ke kallon Fannah totally speechless. “Nikuma?” ya fad’a a k’arshe. “Ina zan samu bargo da pillow a office Fannah? Kode har yanzu baccin naki be wassake bane?”
     “Yusuf banasan wasa please amshi kayan ka, inkuma so kake kabarmin seka fito fili kace Fannah na baki.”
    Murmushi me sauti ya saki. “Fannah wallahi am serious ni banma san wai kina bacci ba kide zagaya ki tambaya waya sani ko Boss ne dakanshi nema ya rufe ki.”

    “Dariya kakeson bani komeh? Boss ya rufeni ina bacci? Impossible barinje in tambayi Ahmad da Kacallah.”
       “Zaki b’ata lokacin ki ne saboda Boss ya aikesu tun d’azu.” Yi tayi kamar bata jisa ba what if abinda Yusuf ke fad’i gaskia ne? ahaka har tashiga elevator ta hauro sama tana tsaye bakin k’ofar office na Anas amman takasa shiga inkuma ba nashi bane fah? Yace tacika shisshigi da k’yar de tasamu tayi knocking a hankali.

  
     Daidai Anas ya d’au bottle na beer nasa ze sha kenan knock yashigo. Haka kawai yau yaji yana san yad’an bugu saboda ya kwana biyu be sha ba tunda Fannah na bacci bare d’an sha abinsa kuma ba ma haka ba so yake yabar tunanin Fannah, ba abinda ya tsinana wa kansa yau, wai mesa ma yaje ya rufeta d’azu da take bacci? Tausayi ne ya fad’a a fili. I don’t love Fannah I just pity her yayi reminding kansa. “Who is it?” Ya tambaya.

    Chan murya k’asa k’asa a hankali tace, “Fannah ce.” Da sauri ya rufe bottle d’in tare da jawo drawer’n gefensa ya rufe. Turare ya feffesa cikin office d’in dan kashe warin giyan tare da kimtsawa sannan yace, “come in.” Tana shiga yaganta da pillow da bargon, kallonta yake har sanda ta k’ariso gaban table nasa. Shiru tayi tana nazarin taya zata fara masa maganan, shima shirun yayi tare da had’a hannayensa biyu k’ark’ashin hab’ansa yana kallonta kamar hoto. Can ta fara kamar haka;

   “Ermm Mr. Fauzi ban sani ba ko wannan naka ne, na tambaya su Yusuf duk sunce ba nasu bane.”
    Kallonta har yanzu yake da wani murmushin tsiya karara a fuskarsa.  “Wato dan kin maidani dustbin shine zaki kawo min?”
     Kai ta d’ago tana kallonsa “No Sir ba abin da nake nufi ba kenan-” katseta yayi
   “Shine mana, kin tambayi saurayinki Yusuf yace ba nashi bane shine kikace bari ki kawo wa dustbin shikam ze karb’a koba haka ba?”
    “No Sir thats not what I mean, in ajiye maka a ina?”
   “Ba nawa bane” ya bata takaicaccen amsa. Kanta ne ya d’aure. Kamar ya ba nasa ba? Toh na waye? Ita se yanzu ma ta tuna ranan da Mr. Fauzi ya rufeta a d’akinsa ai taga bargon nan akan gadonsa, to mesa zece ba nasa bane?
    “Sir but ranan naga bargon nan a d’akinka.”
    “Aww mak’aryaci kikeson ki kira ni dashi kenan, ince miki ba nawa bane kice nawa ne”
   “No Sir ba abinda nake nufi ba kenan.”
    “Inma tunani kike wai da kike bacci ni naje na rufe ki toh you are mistaking dan ni ko shiga office naki banyi ba.”
    “I’m sorry” tace cike da kunya ita de tasan ranan tabbas taga wannan bargo a d’akin Mr. Fauzi kuma gashi yace ba nashi bane. “Jeki ajiye kidawo am waiting for you.” Bayan minti d’aya Fannah ta dawo “yes Sir.” So yake ya ce mata suje suci abinci amman girman kai ya hanasa. Seya bud’e baki ze fad’a se yayi shiru.

   Ganin baida niyyan magana Fannah tace, “Sir you called me.”
   “Ina sane ai” yabata amsa. “Ko ban tambaya bama nasan kinajin yunwa lets go and eat.” ya fad’a in an I dont care tune.
       Qarya tayi niyyan masa tace tana azumi seta tuna yasan batada tsarki.  “Sir I’m not hungry thanks.”
    “Toh ni inaji lets go” zata sake magana yace, “banasan musu” bayan sa ta nufa bayan ya rufo k’ofar office nasa Fannah ta juya zata nufa public elevator, hijabinta ya rik’o. A tsorace ta juyo tana kallon had’add’un yatunsa daya k’ayata su da zobunan azurfa masu tsada rik’e da hijabinta sannan back to fuskarsa. Beso suka had’a ido ba “mu shiga nawa” yace mata. Kai ta giad’a masa a sanyaye tabi bayansa suka shiga private elevator’nsa ba wanda yace ko uffan ahaka har suka sauk’a driver yayi driving nasu zuwa wani hotel na daban ma yau. Abinci me rai da lafiya Anas ya mata ordering. “Eat” yace mata alokacin daya d’aga spoon nasa, ba musu ba gardama itama ta d’au spoon suka soma ci.

    Ko da yagama cin nasa zaman jirarta yayi data gama ya tambayeta, “a k’ara miki?” Kai ta kad’a masa bayan ya biya suka koma office d’an errands kad’an Fannah tayi wa Mr. Fauzi, lokacin tashinsu nayi ta wuce gidah.
     Shima Anas yana gama abinda yakeyi ya kama hanyan gida, tuk’i yake hankalinsa kwance ya d’ibo bottle na giyansa biyu yau a paint house nasa ze kwana, unguwar shiru yake ba mutane sosai yana cikin tuk’i yaga mota ya fito from nowhere yayi blocking nasa, ikon Allah ya tsaya gani reverse ya gwadayi a take yaga bayan san ma anyi blocking. Toh su waye ne? Kafin yanemi amsa wa tambayan daya ma kansa yaga maza uku sun fito daga motar gaban nasa da angansu anga ‘yan maye ‘yan bayan gari. Murmushi kad’an ya saki dan in ‘yan su uku ne acikin minti biyar ze gama dasu. Kafin ya yi yunk’urin yin wani abu yaji ana knocking jikin window’nsa. Window’n yayi wining “munada problem neh?” Ya tambaye gayen.

      “Dade ka fito tukuna.” cewar gayen. Ba gardama ya fito ya tsaya nanne yaga duka duka mazan guda biyar ne. “Will you guys let me pass or senayi muku abinda bakuwa so?”  Familiar murya ya jiyo daga behind nasa yana cewa;
    “Kokuma mu mu maka abinda baka so ba Mr. Fauzi” yana kai dubansa gun da ya jiyo muryan idanunsa suka sauk’a kan Farouq yawani pake kan driver’s sit cike da isa ya taso tare da takowa gunsu Anas.
    “You’ve had your time the other day now is mine.”
    Wani erin dariyan rainin hankali Anas ya saki harda tafi “you are such a genius Farouq. Wai ka d’au dakai da wannan mashirmatan daka taran zaku iya min wani abu ne?”

   Dariyan bosawa Farouq ya saki “Mr. Fauzi kenan kasani sarkin yawa yafi sarkin k’arfi. Apologise to me, tell me sorry akan abinda kamin jiya and I will let you a save passage.”
   “Ni in ce maka sorry?” Yayi murmushi “never!”
   “ATTACK!!!” Farouq ya fad’i nan maza biyar d’in suka soma nufuwa wajen Anas. Sleeves nasa yayi rolling tare da ciro Rolex agogonsa kafin ace me suka b’arke cikin mumunar fad’an BIYAR akan D’AYA. Farouq na tsaye a gefe yana kallon yadda Anas yake destroying masa mutane, duk se kamar yafi k’arfinsu dukda suma suna k’ok’ari dan har sun fasa masa baki amman yafi cin uwarsu. Tsawa Farouq ya daka musu “wai zakuce shi kad’ai yafi ku duka k’arfi ne?”

    Ai se kamar maganar Farouq k’arfi ya k’ara musu. Sunayi Anas yanayi har suka samu sukaci galaba akansa hanci, baki ba wanda basu fasa masa ba. Hannayensa suka kama ta kowani gefe a lokacinda Farouq ya taso daga inda yake. “Ohhh look at you Mr. Fauzi abin tausayi, ina k’arfin naka yaje? Ina polisawan naka? Kud’in ka ya ceto ka mana.” Fuskar Mr. Fauzi dayake yoyon jini Farouq ya d’ago “tell me meh had’inka da mata ta Fannah?”

    Murmushi Anas yayi dukda azaban dayake ji. “Kaikuma tell me meh had’inka da alak’a na da ita? Mind your damn business.”
     “Bakinka be ruhu ba kenan har yanzu. Rik’e min shi dakyau” yace da mazan nasa. Gagam suka sake damk’e Mr. Fauzi punch me rai da lafiya Farouq ya kai masa wanda seda idanun Anas suka juya. “Nace meh alak’arka da matata?”
   “Fannah is not your wife” ya fad’a a wahalince. “Take note”
     “Har yanzu baka bugu ba.” Naushi yakai ma Anas a ciki wanda sakamakon hakan ya saki k’ara sosai dan azaba.
    “For the last time me had’inka da Fannah?”
    “Kanason kaji me had’ina da Fannah? FANNAH IS MY GIRL, I LOVE HER.”
    Cike da b’acin rai Farouq ya cukumo kolar rigan Anas “me kace? Sake nanata abinda ka fad’a inji”
   “I LOVE FANNAH, KUMA NI ZAN AURETA BA KAI BA, FANNAH TAWA CE!!!”
    “You really want to die.” Naushi lafiyayyu guda uku ya kai wa Anas aciki biyu kuma a fuska. Kaca-kaca suka ma Anas, duk wanda ya kallesa bare so sake sa idanunsa kansa ba duk jikinsa jini.

   “Me alak’ar ka da Fannah? Kace min baka son ta kuma baka santa ba.”
     Da k’yar yake maganan “NEVER!! I LOVE FANNAH, ko kasheni zakayi bare canza komai ba.”
    A fusace Farouq yace, “Baaba” na gefen daman Anas “je cikin trunk na motan can kaciro min sandan chan nakega inba dukan mutuwa na masa ba bare shiga hankalinsa ba. Zakace baka son Fannah ko yaya?” Shiru Anas yamasa bece komai ba se nishin wahalan dayake yi abin tausayi.

     “Farouq ga ‘yan patrol zuwa fa!” Baaba yayi exclaiming da ihun gaske ai kamar kyaftawan ido su Farouq suka lodu a mota suka bar wajen a 360. Anas na kwance helplessly a k’asa. Bayan motan patrol d’in ya k’ariso polisawan suka diddiro ganin mutum a k’asa, plate number’n motar Anas d’ayan ya karanta yaga “Mr. Fauzi.”
    “Guys Mr. Fauzi ne!” da gudu sukayi kansa suka d’ago sa zuwa motar sa tare da miqar dashi a back seat. “Abba lets go, mu kaisa asibiti push the start button.” d’ayan officer’n ya fad’i. A wahalince Anas yace, “no karku kaini asibiti just drive me home, to my paint house.”
   “Sir but you are badly injured.”
    “I know, ku kaini paint house d’ina kawai.”
   “Okay sir ina ne paint house d’in?” Nan Anas ya musu kwatance murya yana d’aukewa. “Sir su wa suka maka haka?” Har ya bud’e baki ze kira sunan Farouq seya tuna in ya fad’a musu definately zasu kama Farouq su rufe sa kuma, in hakan ya faru kuwa Fannah barata ji dad’i ba. “Nima bansan suba” yama officers d’in k’arya “ ‘yan iskan unguwa ne kawai.”

    Daidai gaban paint house nasa suka iso. “You can go now zan k’arasa da kaina nagode.” Cewar Anas idanunsa suna kafewa.
    “Sir amman kace barakaje asibiti ba? Wannan mutane sunji maka ciwo fah.”
   “Don’t worry I can take care of myself.” Bottles na giyansa guda biyu yaciro da k’yar yake iya tafiya dan kalan dukan dayasha wajen Farouq da mutanensa, ahaka har ya samu ya isa ciki ko k’ofan ma yakasa locking. Bayi ya nufa da rarrafe da taimakon sink ya mik’e ya kalli fuskarsa a madubi. Sam beso sake kalla ba dan irin ciwon da suka ji masa. Ruwa ya gwada wanke fuskar nasa dashi. Aiko ruwan na tab’a fuskar ya saki k’ara dan azaba daga k’arshe hak’ura yayi yakoma d’aki tare da rage kayan jikinsa yabar short nicker kawai. Kwalba d’aya ya kwankwad’e tas dan samun bacci, yana shanye wa kuwa bugeggen bacci ya d’ibesa ko sallan maghrib beyi ba bale na isha. Wayoyinsa dake cikin mota kuwa se kiransa su Ummie suke ba iyaka amman bai d’aukawa hankalin kowa ya tashi, ko da sukaje office nasa suka tambaya kuwa, kowa ya shaida Mr. Fauzi yabar building d’in lafiya.

***

    Washegari…
    8:10AM yama Fannah a office sede tata knocking a bakin k’ofar office nasa amman shiru chan ta gwada bud’ewa taji a rufe alaman Mr. Fauzi bezo bama kenan! To meya rik’esa? Shida ko lattin minti d’aya baya yi. Meya faru? Mesa bezo ba? Ko baida lafiya ne? Minti 15 ta k’ara tana jiransa amman ba alamansa. Gashi yanada board meeting by 10:30AM. Ganin ba mahalicci se Allah kawai ta sauk’a k’asa ta samu Kacallah tare da tambayansa ko sunyi waya da Mr. Fauzi.
    “A’a wallahi nima Fannah na kirasa ta duka layinsa baya d’agawa tun jiya na rasa dalili.” Kawai setaji gabanta na fad’i. “Toh nagode” tace masa.
   Wayarta taciro ta kirasa har ya tsinke be d’aga ba. Tashin hankali. To ina yashiga? Amal ta kira ta tambayeta ko Anas na gida cike da tashin hankali Amal tace mata itama tun jiya suke neman Anas bedawo gida ba.

    Napep ta tsara bata tsaya ko inaba se paint house na Anas motarsa tagani fake gaban gidan wani hamdala tasaki har ta ciro wayarta zata kira Amal ta sanar da ita se kuma ta fasa, bari de ta tabbata ko yana ciki tukuna. Door bell ta danna sau uku amman ba response. Tana gwada murd’a hannun taga k’ofar abud’e ba sak’e sak’en da bezo mata ba toh kode barayi ne suka shigo masa? Subhanallah amman ai kuma ga motarsa. Ciki tashiga ta lek’a kitchen ba alaman ko motsin mutum “Mr. Fauzi!” ta kira sunansa shiru d’ayan d’akin ta bud’e taga nan ma bayanan toilet dinma haka, guest toilet ma ta duba bata gansa ba. Daga k’arshe d’ayan d’akin ta bud’e a hankali kwalban giya ta soma cin karo dashi, se fad’i gabanta yake ta d’aga tare da k’arisawa cikin d’akin tana taku a hankali cike da tsoro. “Mr. Fauzi!” Ta kira sunan sa alokacin data gansa kwance kan gado yayi ruf da ciki se bacci yake yi ba ko riga jikinsa se bedsheet daya ja zuwa tsakiyar cikinsa.

    A nitse ta k’arisa gefen gadon tare da ajiye kwalban kan side drawer. “Mr. Fauzi!” Ta sake kiran sunansa shiru be amsa ba. Toh kode mutuwa yayi ne? Sede kuma tajisa yana numfashi. Jijjik’asa ta hau yi har se lokacin daya soma motsawa. “Waye ne?” Ya tambaya cikin bacci.
    “Sir Fannah ce, Fannah Aleeyu.”
   “Fannah? Me kikeyi anan? Ban rufe k’ofan bane?”
   “Eh sir baka rufe ba, you need to get up kanada board meeting by 10:30AM.”
   Cikin bacci yace, “barinje ba kiyi cancelling, tell them barin samu zuwa ba.”
    “Sir but why? Kayi hak’uri ka tashi please.” Bece da ita komai ba ya cigaba da baccinsa. Pillow’n daya rufe fuskar sa dashi ta d’aga. Ido ta zaro tana salati alokacin da taga irin ta’addancin da aka ma Anas a fuska. Meya samesa? Waya masa duka haka?

    “Subhanallahi Mr. Fauzi meya sameka? Omg!” ta tambaya a kid’ime a lokacin da ta tsuguna gabansa.
     Da k’yar ya iya bud’a baki yace, “ki rufe min fuska banasan hasken nan.”
     Ignoring nasa tayi “Mr. Fauzi waya maka haka da fuska? Fad’a kayi da wani neh? Meya sameka?”
     “Bansani ba nima just leave me get out.” Haka kawai yaji baya san Fannah tagansa a bad condition irin na yau, bayasan yasa ta cikin damuwa bayasan taji tausayinsa.

   “No Mr. Fauzi I’m not leaving you like this.” Hannu tasa ta dafe goshinta bata ma san ta ina zata fara ba. Hawaye kawai taji yana gangaro mata kan kumatu dan uban tausayi irin nata. Hannu ta aza ta tab’a gefen idansa daya kumburo dan bugun daya sha. K’ara ya saki wanda yasa ta mayar da hannunta baya da wuri. “Sorry” tace cikin kuka. Idanunsa na sauk’a kanta yaga tana hawaye abinda baya so kenan.
   “Miss Aleeyu leave please, goo.”
    “I can’t leave you like this, Mr. Fauzi asibiti yakamata muje su duba ka.”
  

      “Barinje ba” yabata takaicaccen amsa idanunsa a rufe.
   “Please” ta rok’esa tana hawaye ganin yadda aka masa destroying kyakkyawar fuskarsa da a yanzu mutum bare so ya kalla sau biyu ba.

   *© miemiebee*

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 44
BY MIEMIEBEE

      “Miss Aleeyu barin je ba kema leave I can take care of myself” hannu ya mik’a ze amsa pillow’n se kawai ya saki k’ara dan zafin dayaji a cikinsa saboda blows da Farouq ya riga kai masa. A rikice tace, “meneh Mr. Fauzi?” Kafin ya amsata ya mata k’arya ta kwaye bedsheet d’in daya ruhu dashin, hannu ta aza kan bakinta cike da mamaki “Subhanallahi Mr. Fauzi dan Allah meya sameka? Ina kasamu wannan ciwuka? Kalli cikin ka? Ya Salam!!!” Ta fad’i tana hawaye tana kallon cikin Anas da yayi har wani purple brownish colour dan azaba.

       “Mr. Fauzi meya same ka please?” Ta sake tambaya hankali tashe.
      “Nace miki babu in kinsan kuka zaki tayi anan kuma go, leave, I can take care of myself.”
    Innalillahi! what do I do now ta tambayi kanta barata iya barin Anas haka ba he is badly wounded ga fuska ga ciki meya samesa ko b’arayi ne suka shigo suka masa duka? Amman kuma ai gidan tsaf yake ba abinda aka b’arnata. Toh meneh?
          “Mr. Fauzi please kayi hak’uri mu kaika asibiti kaji? Yi hak’uri.” Ta fad’a still tana hawaye dan tsantsan tausayi. Danko ba wanda zega ta’addancin da aka ma Anas be tausayawa masa ko be zubda hawaye  ba.

             “Nace miki barinje ba kitafi please.” Wayarta ta ciro zata soma dialing number’n Amal dan sanar da ita halin da ake ciki.
    “Me zakiyi?” ya tambayeta.
   “Zan kira Amal ne in sanar da family’nka I’ve found you tun jiya suke neman ka.”

     “No karki kira su hang up.”
  “But Sir-” katse ta yayi ta hanyan daka mata tsawan da seda shi kansa ya masa ciwo “I said hang up!” Kansa ya dafe yana muntsika fuska cike da azaba. Nan ta katse ta matso kusa dashi “Sir kanka ke ciwo?” Niyan shareta yayi da farko sekuma ya giad’a mata kai a k’arshe. Jakarta ta ajiye kan side drawer ta nufa toilet tare da fitowa da bowl cike da warm water data d’iga dettol ciki dakuma towels guda biyu, jakarta ta ture gefe tare da ajiye bowl d’in akai. Kallonta yake “me zakiyi?”
  
    “Sir your face is a mess, zan goge maka ne.”
   “Banaso just leave.”
   “No Sir I’m not leaving mesa kai zaka taimaka min amman ni bakasan na taimaka maka? Saboda bankai inyi offering maka help bane? Saboda ka raina ni banida standard? Saboda ni talaka ce? Is that it Sir?”
   “No Miss Aleeyu that is not my point…” sekuma yayi shiru.
    “Toh kabari in biyaka taimakon dakake min koda na yau ne.” Shiru yayi chan ya giad’a mata kai.
   A ranta tace, Ya Allah kar ka kamani da laifi saboda zan tab’a na mijin da ba muharrami na ba, baida lafiya ne taimako zan masa, astaghfirullah.

   Nan ta tsoma d’ayan towel d’in cikin ruwan d’umin tare da matsewa a hankali ta d’an tab’a gefen bakinsa daya fashe. Towel d’in na tab’a wajen yajiyo zafi sosai hannunta ya kama “Sir nasan zeyi zafi hak’uri zakayi kaji? Sorry” a hankali ya sake hannun nata. Tana sake tab’a wani waje ya saki k’ara “arghhh! Ya isa kibari ze warke da kansa, go home”
    “Mr. Fauzi please mana kabari koda germs d’inne a kashe tunda baraka je asibiti ba. Please”
    Haka a nitse cike da tausayi ta riga bin duk ciwon da ke kan fuskarsa tana gogewa a hankali, sosai Anas ya riga sakin k’aran azaba in towel d’in ya tab’a masa kan ciwon ita kuwa duk lokacin daya yi d’an ihu seta basa hak’uri. Tagama da fuskarsa sauran cikin. D’ayan tsumman ta d’aga ta sa cikin ruwan kamar yadda tayi d’azu bedsheet daya rufe jikinsa dashi tasa hannu ta kwaye zuwa cibiyar sa.
    “Me kuma zakimin?” Ya tambaya yana k’ok’arin jan bedsheet din gam ta rik’e tana me hanasa yin hakan. “Ba abinda zan maka Sir zan d’an matse maka wajen ciwon ne.”
    “Don’t worry ze warke da kansa. Wai ke bakia jin tsoron zama da namiji kad’ai ne under thesame roof?” ya gwada tsorata ta ko zatace ta hak’ura zata tafi.

      “Ina ji amman in da kaine bana ji, I trust you Mr. Fauzi nasan ba abinda zaka min shiyasa. Yi hak’uri in d’an matse maka cikin kaji?” sanda ya k’are mata kallo sannan ya giad’a kai.
    A hankali ta aza hannunta kan cikinsa ta matse towel d’in kai. K’ara ya saki sosai dan azaba tare da rik’o hannunta. “Awwchh! Kibari ya isa ze warke da kansa, arghhh!”
     “Sir hak’uri zakayi sauran kad’an sorry.” Haka tata lalashinsa kamar d’an yaro. Towel tasake canzowa tare da k’aro ruwan zafi kan ruwan dan ya riga ya huce. Bayan ta zauna ta sake tsoma towel d’in ciki, cikin siririyar muryarta tace, “Sir did you get drunk yestarday”  Shiru yayi kamar be jita ba. “Sir?” Ta kirasa. “No” ya mata k’arya danko besan taga kwalban a bakin k’ofa ba.

     “Toh wancan fa kwalban meh?” Ta tambayesa a nitse. Kai ya d’aga yaga kwalban sekuma yaji kunya. “Toh me ruwanki dan nasha? You are not my mother ko ita mahaifiyar tawa bata isa ta hana niba, stay out of my personal li-” be k’arisa fad’in ‘life’ ba yasaki ihu “arghh!” Sanadiyar tab’a masa kan inda ke masa zafi sosai da Fannah tayi. “I’m sorry” tace “sauran kad’an.” Chan ta nisanta, “Mr. Fauzi will you listen to me in na fad’a maka wani abu?” Kamar wanda bare ce komai ba seyace “meh abun?” Sanda ta sake matse towel d’in ta mayar kan cikinsa tana daddanewa kan ciwon a hankali tace, “if I were you, in za’a maidani kai abani kyanka da kud’inka da ilimi da komai da kake dashi I will thank God barin na wasting rayuwa na akan shaye shaye ba. Masu shaye shaye sune wanda basuda aikin yi, wanda basuda ilimi basuda komai se shaye shayen da sukeyin. Amman kaga kai komai Allah ya baka Mr. Fauzi, you are handsome, rich and very intelligent, me kake nema? Don’t you think bakayi adalci wa Allah ba ta hanyar masa godiya da shaye shayen da kakeyi?” A hankali ta d’ago idanunta tana kallonsa shima kallon nata yake da blue eyes nasa sannan ya kawar da kallonsa daga gareta.

       “Kayi shiru Mr. Fauzi, do you think you are fair to Allah? Bayan ya gama baka komai seka gode masa ta hanyar bijire wa dokokinsa na hana kowane muslimi shaye shaye”
     “No I’m not” ya fad’a ransa b’ace, muryarsa cike da weakness. “Ke bakisan mesa na mayar da drinking abinyi ba kidena intruding min cikin personal life. Get up and leave” yace a lokacin daya d’aga hannunta daga kan cikinsa.
       “Yafi ace ka rasa mahaifiyar ka ko mahaifinka kokuma d’aya daga cikinsu ya gudu ya barku? Is that the reason kake shaye shaye?” Kallonta yake totally speechless chan kuma ya tuna ashe ranan ta karanta masa diary, cikin chan tagani. Hannunta ta raba da nasa ta mayar kan cikin nasa.

   Hannun nata ya kuma d’aga daga kan cikinsa “ya isa you can go banasan maganan nan, saboda kin karanta min diary hakan be baki daman fad’a min whats right or wrong ba. I’m still your Boss”
        “I know Mr. Fauzi, you are my Boss. Ammana in saboda mahaifiyar ka kake misleading precious rayuwarka ta hanyar shaye shaye you are destroying your bright future. Hakan na nuna you are weak yana nufin ka barta taci nasara kanka kenan. Show her you are strong ko ba ita you can live your life, ka mance da ita and move on if possible forgive her if not ka mance da ita. You have a very bright future kadena b’atawa ta hanyan shaye shaye kaji Mr. Fauzi?” Shiru yayi bece komai ba as ya wula cikin duniyar tunani yana nazarin duk abinda Fannah ta fad’a masa. Tabbas ba k’arya ko d’aya cikin abinda ta fad’a masa dan kuwa haka Shettima ma kullum ke fad’i masa sede koda Shettima ya masa magana bai san sauraro amman yau da Fannah tamasa maganar seyaji yanasan yayi moving on ya manta da abinda Ummimi ta masa sede bawai ze yarda ko ya aminta da mace bane a rayuwarsa ever again he is already broken.

    “Can you do that Mr. Fauzi for Amal’s sake?” Kai ya kad’a mata da nufin “a’a.”  “For mahaifinka?” Nanma ya girgiza kai. “Ummie?” girgiza kai still yayi. “For Shettima?” Nan ma haka. Cike da kunya tace, “for me?” Jiran masifar sa take setaji yace, “yes” a hankali sounding defeated.
     Idanunta ne suka sake bud’uwa cike da jin dad’i da murna. “Dagaske Sir? Zaka dena shaye shaye and move on?”
    “Yes” ya sake fad’i. Dad’i taji sosai wanda ta kasa b’oyewa. “You promise Sir?” ta tambaya dan sake tabbatawa.
   “I promise” yace. Sede duk maganan nan da suke baya kallonta. “Look at me please Sir” tace cikin murya me dad’in sauraro. Yi yayi kamar be jita ba. “Please” ta rok’esa a hankali ya dawo da blue eyes nasa kanta. “Da gaske baraka sake tab’a giya ba?” Ta tambayesa suna kallon juna. Kai ya giad’a a hankali “I promise.”

    “Mr. Fauzi thank you, thank you so much nakega am the happiest woman on earth yanzu, tun ba yau ba nake addu’ar Allah nuna min rananda zaka dena shaye shaye se gashi Allah ya nuna min yau, thank you so much.” bece me komai ba. Nan da nan ta gama matse masa cikin yadawo clean ba jini ko d’igo d’aya jikinsa sede zafin da yakeji. Tashi tayi zata toilet ta zubar da ruwan Anas ya rik’o hannunta a hankali takai dubanta kan hannun nasa sannan kuma zuwa kan Anas d’in tanasan tace masa ya sake mata hannu amman kuma tana tsoro kar yace ze canza mind nasa batun shaye shayen da yace ya dena.

       Godiya yakeson mata amman girman kansa ya hanasa, seya bud’e baki zeyi magana se wani abu ya tsaida shi. Da k’yar ya iya ya sauk’e girman kan yace;

      “Thank you.” ya fad’i a hankali ko kallonta baiyi. For the first time daya soma mata godiya kenan. Ita kanta abin ya bata mamaki, yau Mr. Fauzi ne yake mata godiya?! “You’re welcome Sir” ta amsa sa a takaice da murna fal a ranta. Hannun nata ya sake ta fice zuwa toilet bayan ta fito ta zauna bakin gadon kamar d’azu “sir kayi sallan Asuba?” K’arya yakeson mata yace ‘eh’ sekuma yaga ba amfani tunda ta riga tasan kad’an daga cikin sirrinsa. Kai ya girgiza mata. Kawai se jikinta ya bata ko isha ma beyi ba.
    “Isha fa?” ta tambayesa a hankali cikin dabara yadda bare fusata ba. Nan ma girgiza kai yayi. “Toh Maghrib da La’asar fah?”
  Can k’asa k’asa yace, “nayi la’asar.”
   “Masha Allah its not too late, barin had’a maka warm water sekayi wanka dan jin dad’in jikinka sekuma kayi yi alwala ka rama sallolin da ake binka koh?” Haka kawai ya tsinta kansa cikin san cika wa Fannah qudiri dakuma burinta.

    Kai ya giad’a mata. Nan ta mik’e cikin minti biyu ta had’a ta dawo. “Sir ina bath towel naka?” Nuni ya mata da hannu wajen ta nufa ta ciro “gashi” ta mik’a masa zan jira ka a parlour tana kaiwa nan ta fice.

    Sanda yayi dagaske sannan ya samu ya miqe daga kan gadon, bayi ya fad’a. Shigansa bayi da minti d’aya Fannah ta dawo ta nemi sallaya ta shimfid’a masa bayan tayi amfani da wayarta ta gano Qibla. Nan ta fice, kitchen nasa ta nufa ta d’anyi dube dube sede bataga abinda zata dafa masa ba. Fridge nasa ta bud’e froze chicken data gani ciki ta ciro takoma kitchen d’in. Soya masa tayi duka incase ko zeci zuwa rana. Flask ta nema ta juye ciki, tare da had’a masa coffee cikin flask sannan taje tayi arranging dining table masa. Daidai lokacin Anas yafito, k’amshin designer turarukan daya feshe kansa dashi tun daga sama har k’asa ne ya bugi hancin Fannah. Kai ta d’ago tana kallonsa. Sanye yake da ¾ wando fari da farar vest wanda ya bala’in masa kyau, ga wani sheqin da jik’ak’k’en gashinsa ke, kumburin fuskarsan ma ya ragu sosai, sede alamun ciwo da yankan dake ta bakinsa da gefen ido. Da sauri ta kawar da kanta kafin yace ta cika kallo dayawa. A hankali yake tafiyar har ya iso kan dining table d’in, zaman ma da k’yar yayi harda d’an k’ara “argh!” Tare da rik’e cikinsa.

     “Does it still hurts?” Ta tambayesa cike da damuwa. Kai ya girgiza mata amman ita tasan zafi yake masa. “I made you breakfast I hope you like it.” Yana kallonta tayi serving nasa kajin tare da juye masa coffeen cikin cup ta tura masa gabansa. “Zan jiraka a parlour, eat please.” Kallon abincin yayi sannan ya kalli Fannah. A hankali ta juya zata fice, hijabinta ya rik’o chak ta tsaya bata juya ba.

    “Lets eat together” yace da ita.
     “Sir naci abinci I’m full nagode.”
    “Please.” Ya fad’i wanda besan lokacin daya fad’a ba shi kansa, meke damunsa? Haka kawai yaji in ba ita bare iya cin abincin ba.
   ‘Please?’ ta nanata a zuciyar ta. Dagaske Mr. Fauzi ne yau yace mata please? Lallai!
   A nitse ta juyo, kujera opposite him ta zauna tana watsa da yatsunta. Plate ya jawo ya juye mata ragowar kazan duka. “Eat” yace da ita. Baki ta bud’e data d’ago kai taga uban kajin daya tara mata gabanta.
     “Sir ina zan kai wannan? Yayi yawa.” Hannu ta mik’a zata ja flask d’in a yayinda ya d’aga daga kan table d’in gabad’aya ba tare da yace komi ba.

    “Sir please ka rage yayi yawa.” Ignoring  nata yayi “lets eat I’m hungry.” Nasa ya soma chi itako har yanzu bata tab’a plate d’in ba ina zata kai wanga kaji?
     “Miss Aleeyu eat.” Miyau ta had’iye a hankali ta d’au cinya d’aya ta soma ci. Zaman makokin ne ya isheta tayi gyaran murya sannan tace, “Sir do you want to talk about it?” Sanda ya nisanta sannan yace, “about?” Ba tare da ya kalle ta ba.
     “Abinda ya sameka.” Kai ya girgiza “No.”
  “Okay…” tace a hankali “but Sir next time ka kiyaye please koma mene neh.”
    “Okay” yace mata kamar d’an yaron da mamansa ke masa fad’a. Haka kawai yaji bayasan fad’awa Fannah gaskian al’amarin yasan definately zatayi blaming kanta zatace duk akanta fad’an ya tashi kuma hakan ne komai a sanadin ta ya faru sede bayasan tayi feeling guilty.

      “Sir?” ta kira sunansa. “Yes” ya amsa yana sipping coffeensa. “Mesa kace kar na kira Amal na sanar da ita I’ve found you?”
   “Saboda banasan susan inada gida anan.” Sam bata fahimce me yake nufi ba, so yake yace bawanda yasan yanada gida?
    “Ke kad’ai na fara kawo wa cikin nan, ko Shettima besan I have a paint house ba.”
  
    Meh Mr. Fauzi yake nufi kenan? Does this mean tanada wani matsayi a zuciyarsa da har ya b’oye wa kowa gidan sa hatta family’naa amman ita ya sanar da ita ya kuma barta tana shiga???

© miemiebee

TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 45
BY MIEMIEBEE

THANK YOU SO MUCH DA ADDU’O’INKU MASU SO DA K’AUNA TA, ALHAMDULILLAH NAJI SAUK’I SOSAI

          Shiru tayi bata ce komi ba as tana nazarin abu a ranta.
      “Say it out” yace yana kallonta. Mamaki ne yacika ta how comes ya gane ta nada magana a ranta.
   “Errm babu” tayi k’arya.
   “Akwai say it.”
   “I was thinking ko za’a zubar da abubuwan da suke cikin fridge d’in kar in-” katse ta yayi “jeki d’iba ki zubar, kiyi flushing duka.” Dad’i sosai taji nan take ta mik’e. “After kin gama cin abincin ki amma.”
    “Sir na k’oshi thank you” bata tsaya jiran me zece ba ta nufa fridge d’in tafito da duka kwalabe guda 15 d’in. “Sir akwai wani bayan wad’annan?” kai ya gyad’a mata.
    “Are you sure Sir?”
    Kai ya girgiza “akwai kwali d’aya k’ark’ashin gado na a d’aki.”
   “Thank you Sir.” Uku-uku ta riga d’iba tana kaiwa toilet tana zubarwa har tagama duka kwalaben kuwa tayi disposing nasu. Bayan ta gama ta d’au first aid box daga toilet tafito dashi zuwa dining space inda ta tsinci Anas zaune yayi zurfi cikin tunani. “Sir?” Ta kirawosa tare da dawo dashi daga duniyar tunanin daya wula. Kallonta kawai yayi ba tare da yace komi ba.

     “I think ciwon fuskan kan zefi healing da wuri in aka rufe” ta fad’i tana ciro wasu transparent bandages guda biyu. B’antare d’aya tayi. “May I?” Ta tambayesa kai ya giad’a mata nan ta manna masa na gefen bakin nasa a hankali sannan na kusa da idansan shima a hankali. “Get well soon” tace dashi a lokacin data rufe first aid box d’in ta mayar toilet, fitowarta ta nufi bakin k’ofa.
   “Miss Aleeyu” ya kira sunanta chak ta tsaya tare da kewayo wa. “Yes Sir.”
    “Ina zakije?”
    “I’m going home, jikin naka da sauk’i ba?”
    Alokaci d’aya kuma se yaji bayasan ta tafi, shi yake korarta d’azu amman yanzu kuma so yake ya cigaba da kasancewa _TARE DA_ ita, bayasan ta tafi wanda shi kansa besan dalili ba.

     “Must you go?” Ya tambayeta.
    A hankali tace, “Sir I have to, bareyi in cigaba da zama anan ba.”
    “Okay” yace blankly. Bata ce dashi komai ba ta fice. So yake ya tsayar da ita yace mata ta zauna dashi baya san ta tafi amman bayasan ta raina sa bayasan ta d’auka da wata manufa, ta zata ko santa yake.

    Isar Fannah gida ke da wuya ta tarar da Farouq tsaye bakin k’ofa da alama ita yake jira. Bugun zuciyarta taji ya k’aru in akwai d’an Adam data tsana a doron k’asa toh Ya Farouq ne.  Bayan ta sallami meh napep d’in ta sunkuyar da kanta tayi kamar bata gansa ba se tafiyarta take a yayinda idanunsa suke biye da ita. Takai da shiga cikin gidansu kenan kawai Farouq ya jawo ta da k’arfin gaske, kafin tayi yunk’urin yin wani abu ya matseta jikinsa gagam shi a dole yana hugging nata. “Ya Farouq me haka? Ka sakeni” se k’ok’arin k’watan kanta take amman ta kasa. Batasan lokacin data fara kuka ba. Se bugin k’irjinsa take amman kamar super glue yak’i sakinta. “Fannah mesa bara ki soni ba? Mesa Fannah? Ke bakisan ina sonki bane? Akan ki kowa ze iya mutuwa, mesa se wancan me idan turawan zaki so? Me yake dashi da banida? Tell me mesa bakiya sona?” ya k’are maganar yana wani erin zakin nishi kamar ze cinye ta tare da shunshuna hijabinta sekace ze cire.

       “Ya Farouq ka sa

    Wajen elevator’nsa ya jata bayan sun shiga tace, “Mr. Fauzi where are you taking me to?” Be amsata ba illa wayansa da ya ciro daga aljihunsa yayi waya wanda ga dukkan alamu da polisawa ne. Bayan ya gama Fannah ta maraice “Mr. Fauzi not again please, kayi hak’uri dan Allah.” Beko saurare ta ba. Bayan da elevator’n ya bud’u yaja hannunta daidai gaban motarsa ya tsaya tare da bud’e k’ofar gaba wa Fannah. “Enter” yace ba tare da ya kalleta ba. Dakewa tayi “barin shiga ba Sir, kabari mana dan Allah duk abinda ka masa yanzu nasan Ya Farouq he will fight back, fad’an ya cigaba kenan kuma.”
     “Get in the damn car!!” ya fad’a a tsawace. Ta tsorta iya tsoro amman kuma tak’i shiga.
   “Miss Aleeyu I said get in, karki bari raina ya b’aci in d’aga ki in saki ciki da kaina.”
   “Sir promise me ba wajen Ya Farouq zamuje ba.” Kai ya giad’a.
    “Promise?” Ta tambayesa. “Yes” ya bata amsa nan ne tashiga bayan ya rufo k’ofar ya zaga ta driver’s side yashiga shima. This is the first time yake driving nasu bibbiyu. Ganin hanyan gidansu yake nufa tace, “Sir you promised kace ba wajen Ya Farouq zamuje ba dan Allah ka juya.” Banza da ita yaui sanda suka isa gidan yayi parking tare da fitowa a fusace ya zaga ya fito da Fannah hannunta rik’e cikin nasa tayi tayi ta k’wace amman ta kasa. Ai kaman an turo Farouq se gashi ya yanko corner’n gidan hankalinsa kwance yana tafiya idanunsa suna sauk’a kan Anas yaga yadda yawani rik’e hannun Fannah. Ita kuwa ganin Farouq ta cigaba da k’ok’arin k’watan hannunta daga na Anas amman ta kasa. “Stop it” yayi warning nata. “Sir please ka sakeni kafin ya k’ariso.” Nan da nan Farouq ya iso gabansu se nishi yake kaman zaki dan wani bak’in kishin daya rufesa.
       Hannun nasu ya sake kalla sannan ya kalli Fannah, kanta ta sunkuyar tare da lab’ewa bayan Anas a hankali tace, “Ya Farouq I can explain this dan Allah kayi hak’uri, Mr. Fauzi please ka sakemin hannu.”
     “Bakaji me tace bane?” Ka sake mata hannu.
    “Banji ba” Anas yace kamar kyaftawan ido ya sake hannun Fannah tare da cikumo kolar rigan Farouq punches guda uku lafiyayyu yakai masa har k’asa Farouq ya sauka se zuban jini fuskarsa yake. Binsa k’asan Anas yayi tare da tsugunawa a kansa da k’afafunsa side-by-side na Farouq. Nan ma be bar kai masa bugin ba. Fannah dake basa hak’uri har bakinta yayi dogo “Mr. Fauzi please ya isa.” Se huci yake yana dukansa ba makawa. Hannun Mr. Fauzi ta gwada rik’ewa ya k’wata abinsa da zafi sauran kad’an ta fad’i k’asa. Ganin an kusan sumar da Farouq Fannah ta ruga a guje tare da hugging Anas ta baya cije da tashin hankali, abinda kad’ai yazo mata kai kenan duk da tasan yin hakan haramun ne, in bahakan tayi ba tana ganin Anas ze iya kashe Farouq da yadda yake ta kai masa bugi. Hannu ya d’aga ze sake kaiwa Farouq punch yaji jikin Fannah a nasa, wani irin electrification ya jiyo a jikinsa tun daga tsakiyar kansa har k’afa, wanda be tab’a ji ba tunda yasan kansa. Hawaye take sosai wanda har kad’an daga ciki ya tab’a rigarsa “Mr. Fauzi please ya isa dan Allah kayi hak’uri in ka cigaba zaka kashe sa ya isa dan Allah, please…” Se kuka.
     Ganin jikinsa ya mutu ta matsa baya tana share hawayenta mik’ewa yayi ya nufa wajenta “is okay kukan ya isa kinji?”
     Numfashi take ja dan yadda tasha kuka “please ya isa Sir karka sake tab’a masa.” Kai ya gyad’a mata “stop crying.” Itama kan ta giad’a masa. Da k’yar Farouq ya mik’e se jiri ke k’ok’arin d’ibansa, fuskar nan nasa ya ninka abinda yasa a kayi wa Anas, kayan sa duk ya b’aci da jini, da k’yar yake maganar a wahale. “Wallahi Mr. Fauzi you won’t get away with this, Fannah tawa ce! Fannah mata tace! Ni zan auri Fannah!”
 
     “No Farouq you are wrong *FANNAH TAWA CE! FANNAH MATA TACE! NI ZAN AURI FANNAH* and not you.” Shi kansa besan sanda yafad’i wannan kalamu ba. Fannah kam mutuwan tsaye tayi. Daidai lokacin motan polisawan suka iso guda biyu. Handcuff aka sawa Farouq a hannu “wallahi Mr. Fauzi kasani you won’t get away with this, duk ranan da na fito se na k’wato Fannah daga gareka, sena kashe ka in ban kashe ka ba sena kashe ta dan in barin samu Fannah ba, bawanda ze same ta.” Kansa aka tusa cikin motar. Daidai lokacin Ya Khaleel ya hallaro shima, ganin d’ansa cikin motan polisawa ya falfala da gudu izuwa wajen.
    “Officer ina zaku kaimin d’a dan Allah ku sako shi kuyi hak’uri. Farouq me kayi?” Nan ya juyo wajen Anas da Fannah. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri kasa su sake min d’a wayyo Allah! Kayi hak’uri dan Allah bare sake ba.”
    “Ka sake had’a ni da Allah believe me kaima zaka bisa cell d’in. Take him away” yace da polisawan.
    “Fannah dan Allah karki bari atafi miki da miji ki rok’i Mr. Fauzi please.” Hawaye sosai Fannah take dan tausayi irin nata setaji duk she is ready to forgive them abubuwan da suka mata. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri.”
   “NO” yace mata a tsawace “take him away, NOW!” A 360 suka bar wajen da Farouq. Kuka Ya Khaleel yake “Allah ze sak’a min wallahi, d’a na be maka komai ba kasa aka tafi dashi simply because kaga baida gata in shaa Allahu zan tara kud’i inyi bailing nasa, kekuma Fannah kisani Farouq shine mijinki ba wannan dayake miki wasa da hankali ba.” Yana kaiwa nan ya fice.
    Kuka me sautin gaske Fannah ta fashe da, “Mr. Fauzi why? Dan Allah ka dawo dashi I beg you please, banasan ka mutu, banasan wani abu ya tab’a ka. Ni nace zan aure sa ka sa a sakar dashi, ka sakar min miji.”
    “*Nine mijinki Miss Aleeyu* and that stays that.”
    Cikin kuka tace, “what are you saying Mr. Fauzi kana cikin right mind naka kuwa taya zakace kaine mijina? Ko baka san ba’a wasa da kalman aure bane? Ni ka sa su sake Farouq kawai dan Allah.”
    “Yes Miss Aleeyu nasan me nake fad’a ni zan aureki ba Farouq ba, you are going to be my wife” hannunta yaja tare da zaunar da ita cikin motar. Shima ya zaga ya zauna.
     Hawaye take sosai “Miss Aleeyu for goodness sake kukan ya isa. I’m going to marry you so as to protect you from Farouq atleast duk rashin kunyarsa inyaga ke matar aure ce ze saurara miki koda Babansa yayi bailing nasa, marry me Miss Aleeyu.”
    Kai take girgizawa continiously No! No! No! This can’t be happening bareyi in auri Boss d’ina koba dan haka bama bareyi in barsa ya aureni ba, BANIDA BUDURCI, BANIDA MARTABA duk ranan da Mr. Fauzi ya gano hakan ze tsaneni fiye da yadda ya tsani mutuwar sa, I can’t marry him saboda barin iya fad’a masa sirri na ba kamar yadda barin bari yagano hakan ba da kansa kuma.
     “No Sir I can’t marry you, I can’t dan Allah kabar wannan magana, ni kawai release Ya Farouq.”
   
   “Yes, yes you will marry me Fannah Aleeyu. In ma tunani kike ko wani abu ze shiga tsakanin mu ki kwantar da hankalinki. CONTRACT MARRIAGE zamuyi.”
   “Contract marriage?” Ta tambayesa cike da rashin fahimta.
   “Yes contract marriage nima some weeks ago Abuu yace se nayi aure, seya aura min wata ‘yar uwarshi Falmata saboda yana ganin I’m still young wataran baran iya managing Enterprise d’ina ba kuma wai ban gama mallakin hankali na ba so yakeson yamin aure, nikuma nace masa barin aureta ba, mukayi deal dashi akan in 6 months time zan nemo mace in kawo masa gida wanda zan aura. Ni koda nan da infinity, k’arshen duniya za’a bani banga macen da zata min ba har inji ina sonta zan aureta ba, I will use you  Miss Aleeyu and fake up a relationshop with you. Ni a rayuwa na banason aure, duk abinda ze had’ani da mace ma hasali banaso ke kad’ai ne…” Ya nisanta “when it comes to you I just don’t feel thesame way. Mu rufa wa junan mu asiri and help each other. Zan aureki for just 6 MONTHS TIME after then semu rabu ince wa Abuu kinci amana na kin tafi kin barni, kince you don’t love me anymore, you see daga lokacin nan bare sake tak’ura na da zancen aure ba zece I’m broken I cannot move on kamar yadda shima har yau yakasa sake aure tunda Ummimi ta tafi ta barsa. Ke kuwa kinga nasan by 6 months time d’innan Farouq halan ya gaji da jira ya koma inda yafito kinga seki cigaba da tafiyar rayuwarki kamar yadda take da. Nikuma I promise you a k’arshen 6 months d’innan bayan munyi ending marriage d’in zan baki 6 million tunda dama contract marriage ne.” Ido sosai Fannah ta zaro 6 million???? Ta fad’i a ranta.
   
        “Kinga inma so kike kubar garin nan da family’nki zuwa wani garin zaku iya, yadda Farouq bare sake tak’ura muku ba. Kuma a kowani k’arshen wata zanna biyanki albashinki na aiki N500,000 sede bawai zakina min aiki bane still, zan sauk’e ki daga zama min PA, bareyi ace mata ta PA ta ba. I’ll get the papers ready gobe, all you have to do is sign them So what do you say?”
     Shiruu tayi dan tunanin ma ta kasa. Taya zatayi agreeing wa qudurin nan? Contract marriage, how? Setayi decieving kowa kenan tasa su yarda eh soyayya sukayi da Mr. Fauzi har ya kai ga aure? Kuma seya b’ata mata image gun iyayensa, yace taci amanar sa? Gaskia baratayi ba amman kuma intayi la’akari itace ma zata fi benefiting. Dubu d’ari biyar sau 6 miliyan uku kenan plus miliyan shida daze bata ta tashi da miliyan tara kenan. Wow! Zata samu takai Babanta har k’asar waje ayi masa aiki takuma tattara family’nta subar Maiduguri su koma ko Kano ko Kaduna inda su Farouq bara su sake saminsu ba. Zata samu ta sa Afrah ma a makaranta. To yanzu ya? Ta yarda kenan?
     “Miss Aleeyu?” Ya tsamota daga cikin duniyar tunanin data wula. “Have you make up your mind?”
    “Sir naji komai amman seka b’ata min image gaban iyayenka ne su d’au mutumiyar banza ce ni?”
    “Yes Miss Aleeyu this is the only way zan kub’uta, the only way Abuu zeji tausayi na bare sake min maganar aure ba har se in ni na masa.” Kai ta gyad’a a hankali “Sir amman baramu na had’a kwanciya bako?”
    Lallai ma yace a ransa, shi d’inda ko wace mace nada burin ganinsa kan gadonta ita tasamu zata tsaya tana masa tsiya.
     “Miss Aleeyu nima ba so nake ba dan yazama dole ne, ofcourse we will share a bed amman ba abinda ze shiga tsakanin mu, in ma gudun abinda kike kenan, kisani banida interest cikin wancan abin ko physical contact ban yarda ba, lokacin da zamu iya tab’a juna shine only if either your family or my family visits saboda kar su gane faking auren mukeyi.”
     “Sir you mean barin sanar da su Mami ba? Ai ya kamatasu su sani-”
     “Bekamata ba” ya katse ta. “Ko Afrah ban yarda ki fad’a mata ba, this is our secret dan the moment kika sanar da mutum d’aya kin mana ruining komai kenan. Don’t tell anyone, clear?”
    Kai ta gyad’a tana nazarin ya zata soma b’ullo wa family’nta da wannan zancen auren Mr. Fauzi. Ai se suce dama tuni soayyaya ke kai ta office nasa ba aiki ba.
     “Good” yace. “So starting today zakiyi faking zama girl friend d’ina saboda kar mutane suyi suspecting relationship namun bana gaskia bane.”
       “Is that necessary Sir? Senayi pretending zama girlfriend naka a idan mutane?”
     “Yes Miss Aleeyu kidena san abu kina kaiwa kasuwa, bakiya san zama girlfriend d’inan ne? Sure kinaso so stop pretending and let urself celebrate.”
    “No ni banaso” ta kare kanta.
   Wani shu’umin murmushi ya saki mata. “In ma saboda Yusuf saurayin kine kike wannan abu gwamma tun wuri ki bari, kije kiyi breaking up dashi dawuri dan baraki b’ata min reputation ba ace kina dating d’ina kuma kina dating me aiki k’ark’ashi na ba.”
     “Sir Yusuf ba saurayi na bane.”
   “Allah sa” yace ba tare da ya nuna danuwa ba. “So ki bud’e kunnwanki da kyau ki jini, akwai rules da zan kafa miki regarding wannan aure;.
   Na farko shine don’t fall for me, saboda fake relationship ne I will show you love and care amman kisani bana tsakani da Allah bane, so in kika yi falling min ba ruwa na ke zaki karya wa kanki zuciya dan ni ba sanki zanyi in return ba.” Dad’in abin ba yau ta soma jin munanan kalamunsa ba so ko damuwa batai ba. “Ka kwantar da hankalinka Sir ni barin tab’a falling maka ba, business is business”
         “Allah sa ki iya ignoring beauty na. Na biyu we will be hanging out tare, duk inda zanje tare zamuna zuwa irin su dinner ko lunch da ake inviting d’ina so as inyi introducing naki wa bussiness colluegues d’ina. Inada business trip nan da 1 month da 2 weeks zuwa Morocco dake zanje.
   Na uku, I will re transform you, you are now my girlfriend ya kamata ki fara sa kayaki masu tsada saboda mu nuna wa public kin kai ince ina sonki.” Wannan wace erin zagi ne? Meyake nufi? Kaya masu arha take sawa kenan ko meh? Baki ta bud’e zata masa gana. Ya dakatar da ita ta hanyan aza hannunsa kan lips nasa “shh! Bangama ba karki katse ni. I know kinasan kice you are not ashamed, if you are not toh ni I am and that stays that. Hope am clear for now, more rules will follow afterwards…”
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
 TANA TARE DA NI… PAGE 47
BY MIEMIEBEE
     “Baki jini bane?” Ya tambayeta tare da d’age gira.
   “Naji Sir” ta amsa a hankali. “Good and one more thing, learn to call me Anas in public. Bareyi kina kiran boyfriend naki sir ko Mr. ba. Am I clear?” Wani banbarak’wai maganganunsa suka sauk’a a kunnenta, ita rabuwan ta data kira sa da asalin sunan sa tun kafin ta fara masa aiki ta riga ta saba da Boss ko Sir ko Mr. Fauzi. “But Sir na riga na saba.” ta fad’a.
    “Seki saba da Anas d’in shima. Yanzu rufo min k’ofar mota.” Ba gardama ta rufe, basu tsaya ko ina ba se babban shopping mall dake Maiduguri bayan yayi parking ya juyo ya kalleta kallonsan take itama amman take ta kau da kanta. “So kinga cikin mutane zamu shiga am now your boyfriend dan haka karki kirani da wani suna banda Anas, clear?” Kai ta giad’a a hankali. “Me zamuyi anan amma?” Ta tanbayesa.
   “What else? To shop for you.” Ta kai da bud’e k’ofarta kenan ya dakatar da ita “wait, I’m your boyfriend ko kin manta ne? Let me.” Hannunta ta mayar tana jiransa bayan minti d’aya k’ofarta ya bud’u. Hannunsa ya mik’o mata a yayinda ta tsaya tana kallansa dan bata san me zata masa ba. “Grab my hand” yace da ita romantically.
    “Sir-” kallo ya watsa mata “I mean Anas kai fa kace ba body contact.”
     “If we are alone ba, yanzu kuma cikin mutane zamu shiga we have to pretend like other lovers do, now grab my hand.”
     “Sir I mean Anas amman haramun ne ba kyau, you are not yet my husba-” bata k’are maganar ba yakama hannunta tare da fito da ita daga motar. Janta ya fara suna tafiya se k’ok’arin k’watan hannunta take takasa, bece mata komai ba sanda suka iso daidai gaban k’ofar ya tsaya ya kalleta. Chak itama ta tsaida damben k’watan hannun ta datake kanta a sunkuye.
     “Fannah” ya kira sunanta abinda be tab’a yi a gabanta ba. “Stop it okay? Behave yourself.” A haka suka shiga cikin mall d’in idanu ne sosai akansu dan ko ba’a tab’a ganin Mr. Fauzi da mace ba segashi yau da PA’rsa. Wani business colleague nasa ne dayazo shopping shima da family’nsa ya gansa.
       “Mr. Fauzi” ya danna masa kira from far behind atare Fannah da Anas suka juya suna kallon inda suka jiyo muryar. Anas na ganinsa yakira sunansa shima “hey Mr. Mahmoud!” bayan Mr. Mahmoud sun k’ariso da matarsa sukayi hand shake sannan akayi gaisuwa. “This is Miss Aleeyu your PA ko?” Mr. Mahmoud ya tambaya.
     “Yes this is Fanna”  ya sake rik’o hannunta gam da nasa yana mirzawa a hankali, electric sparks Fannah tajiyo cikin jikinta. “My girlfriend.”
    “Your girlfriend?” Mr. Mahmoud ya nanata abinda Anas ya fad’i cike da mamaki a iya saninsa de Anas baida time na girlfriends.
   “Yes!” Anas ya jaddada masa, “she is no more my PA right BABE? ” Ya juyo yana kallon Fannah. Rasa na cewa tayi chan k’asa k’asa cike da kunya tace, “yy..yyess” ta nisanta “honey ” Wani shu’umin murmushi Anas ya saki. “So Mr. And Mrs. Mahmoud semun sake had’uwa girlfriend ita tanada gajan hak’uri kar mu b’ata mata lokaci se anjima.”
    “Ayi shopping lafiya Mr. And Mrs Fauzi.” A haka sukayi sallama, hannunta rik’e cikin nasa suka nufa wajen inner wears. Me kuma zamuyi anan? ta tambayi kanta a zuci. Me kula kayan wajen tana ganin Mr. Fauzi ta soma washe hak’wara “Mr. Fauzi you’re welcome have a sit please.”
   “No thanks” yace mata tare da k’arisowa gabanta da hannun Fannah cikin nasa. “Dubata wani size ne ze mata.” Baki wangalau Fannah ta bud’e cike da mamaki da kunya gabad’ai wai mesa Mr. Fauzi baida kunya ne? Hijabinta ta hura sede its too late matar ta riga tayi figuring out komai. “Lets say maxi B cup.”  “Okay thanks” yace da ita tare da jan hannun Fannah suka shige ciki, wajen bra zalla ya kaita bi yake yana duba tags na jikin bras d’in har ya kai kan tag B hannunsa ya raba da nata tare da d’iban bras d’in ba iyaka ya jibge mata ajiki, da sauri ta tare a hijabinta.
    “Sir I mean Anas meh haka? Its embarrasing dan Allah ka bari.”
     “What so embarrasing Fannah? You are my girlfriend me aciki dan na saya miki inner wears?” Wani sabon row ya kwasa ya sake zuba mata cikin hijabinta. Janta yayi zuwa side na panties yana duddubawa chan ya d’aga guda d’aya yana duddubawa a sama “Mr. Fauzi I mean Anas dan Allah kabari kar a ganka.” Banza yayi da ita tare da ajiyewa, wani daban ya sake d’agawa shima da be masa ba ya sake d’ago wani.
     “Saboda Allah Mr. Fauzi kabari.”
    “I won’t stop se kin fad’a min size naki.”
    “NOO!!” ta fad’a da ihu.
   “Then fine haka zan cigana da nema har sena samu.” Haka yatayi har wucewa ake ana nuna su. Ganin ba mahalicci se Allah ta rufe ido kawai “Sir size na hannun kan ne.” Juyowa yayi kalle ta dawani shu’umin murmushi a fuskarsa. “Good” ya ce da ita kalan size d’in ya riga d’iba har rows uku ganin kayakin sun soma mata yawa ya buk’aci akawo masu trolley dam ya cika d’aya da inner wears zalla sekace kayan lefe ze had’a. “Anas ya isa please ina zan kai wad’annan kayaki?”
   “Basu miki bane akawo wasu desingers d’in daban?”
  “NOOO MR. FAUZI!!!” Ta masa ihu, trolley’n yaja tare da rik’e hannunta wajen biya suka nufa ya ajiye tare da jawo wani trolley’n daban. Siyayya na fitan hankali yayi wa Fannah tun tana yabari har tagaji, shi kansa be bari taji total amout d’in ba. Har gaban gida ya kaita yasa yara suka shiga da kayakin ciki. “So are you telling Mami ko in shiga in fad’a mata da kaina?”
    “Zan fad’a mata da kaina.”
   “Yaushe yanzu?”
    “A’a se in bikin ya kusa.”
   “Kina nufin har se na gama gina gidan tukunnah?”
   “Yes Sir.”
   “Lallai kam!” yayi exclaiming. K’ofarsa ya bud’e yafita tare da bud’o nata. Hannunta yaja ya fito da ita sannan yasoma janta zuwa cikin gidansu. “Mr. Fauzi dan Allah kar ka shiga zan fad’a mata da kaina.”
    “When gobe jibi? I don’t have that time.” Already su Mami suna tsaye jikin kayakin duk mamaki ne d’auke karara a fuskarsu da Afrah harda Aiman. “Laaaa Mami kiga harda bressier” cewar Aiman. D’aya taciro “kuma wallahi daidai dana ya Fannah ne ko Ya Afrah.” Daidai lokacin su Anas suka iso tsakar gidan bra d’in Mami ta amsa tare da b’oye wa a bayanta ganin Mr. Fauzi.
      “Sannu dazuwa” ta musu duka. Bayan an shimfid’a musu tabarma suka zazzauna, sede Anas yak’i sakin hijabin Fannah dan dolenta ta zauna kusa dashi. Mamaki ne yacika Mami, Afrah kam gani take kamar a mafarki. Gyaran murya Anas yayi;
    “Ermmm Mami you must be wondering me ya kawo ni nan as well as kayakin chan ko? Well Fannah and I have been wanting to tell you amman Allah be bamu iko ba.” Ya juya ya kalli Fannah tare da mata wani killer smile dataji zuciyarta na k’ok’arin fashewa dak’yar ta iya ta mayar masa da murmushin itama. “We two… We two…” Sekuma yakasa k’arisawa nanne Mami tagano bakin zaren.
   “Ya Anas soyayya kuke da Ya Fannah?” Aiman ta tambaya, bakinta Mami ta buge “tashi kishiga ciki.”
   “Mami nayi shiru.”
   “Tashi nace!” Mami ta bud’e mata ido, a sanyaye ta tashi tashiga d’akin Baba.
    “Toh Anas shine har se kai da kanka zakazo ka fad’a min? Ke Fannah meya hanaki fad’a min iyyeh?”
    Kame kame ta soma “erm.. Erm…” Anas ne ya karb’eta “Mami ni na hanata saboda nayi laifi nafara soayyaya da ‘yarku ban tambayi izini wajen ki ko Baba ba, I’m sorry please.”
      “Bakomai Anas nasan bada gangan kayi hakan ba, toh inde blessing d’ina kuka zo nema ni kam na baku, Allah sanya alheri, naji muku dad’i sosai.”
    “Mungode Mami” cewar Anas a kunyace. “Yau ma Baba yana bacci ne inasan mu gaisa.” ya tambaya cike da girmamawa.
   “A’a idansa biyu barin masa magana” nan ta fice. “Congratulations to you two” cewar Afrah. Kallo Fannah ta watsa mata a yayinda Anas yace, “thank you sistaaa.”
   “Toh Ya Anas, Fannah kad’ai aka sani aka ma siyayya mufa?”
    “Ke Afrah bakida hankali ne?” Cewar Fannah tana zaro mata ido.
   “Toh ke me ruwanki?” Anas ya katse ta “don’t worry Afrah” hannu yasa cikin aljihunsa yaciro bundle na d’ari tare da mik’a mata. “Gashi gobe keda Aiman kuje kuyi shopping kinji? In ya kasa muku ki karb’i number na wajen Fannah ki kirani se in k’ara muku kinji?”
      “Yeyy! Ya Anas mungode.” Daidai da fitowar Mami kenan “bismillah Anas kashigo” a hankali ya saki hijabin Fannah tare da mik’ewa ya nufa d’akin. “Ya Fannah ya akayi Ya Anas yasan size naki naga harda bressier ya sayamiki.”
       “Afrah wallahi in baki rufa min baki ba sena cicci miki.”
   “Uuuhhh! Kode harda panties ne? Soyayya dad’i” hannu Fannah ta d’aga zata bugeta take ta gudu d’akinsu wane ta cinye kud’in.
   Bada dad’ewa ba Anas ya fito murmushin dake d’auke a fuskarsa kad’ai amsa ne game da tambayan ya had’uwansa da Baba ya tafi, it was a success. Mami ce ta rakosa waje “toh Anas kaide kullum seka mana wahala mungode Allah saka da alheri ya k’ara bud’i.”  “Ameen Mami ni zan wuce.”
  “Toh masha Allah Fannah baraki raka Anas nakin bane?” Mami ta tambayeta tana mata murmushin tsiya.
   Kamar tace barin raka sa ba sekuma ta fasa tace “zan raka sa Mami.” “Yawwa toh mungode ko Anas a gaida gida.” A sanyaye ta mik’e ta bi bayansa bayan sun fito gaban gidansu yace da ita “toh Mrs. Fauzi thank you koma ciki.”
    “Niba Mrs Fauzi bace tunda ba’ayi auren ba tukuna.”
  “Ohonki nide adena so ana kaiwa kasuwa. Cikin jakar inner wears d’in akoi kud’in d’inki ciki also akwai wani paper da phone number rubuce ajiki, number’n tailor’n Amal ne naga yana k’ok’rin d’inki seki kirasa kuyi magana, okay?” Can k’asa k’asa tace “okay nagode” tare da ficewa.
       Tana dawowa taga su Afrah kan kayan se bud’e bud’e sukeyi. Sanda ta ganta sannan ta soma maganar; “ai dama Mami na fad’a miki akoi b’oyayyen al’amari tsakanin Ya Fannah da Ya Anas bakiga kullum tana zuwa office ba.” Yi tayi kamar bata jita ba takai da shiga d’akinsu kenan Mami ta kira sunanta “Fannah! tsaya” chak ta tsaya. Mami ce ta k’ariso wajen ta “mu shiga daga ciki.” Bayan sun shiga suka zauna kan gado Mami tasa hannunta cikin na Fannah.
   “Fannah shin kin sanar da Anas labarinki kuwa? Banasan ku gina relationship kan k’arya ki fad’a masa komai akanki please dukda da k’yar ne agane wani d’a na miji ya tab’a shiganki amman yakamata ki sanar dashi, k’arya ba abar yi bace.”
 
     Rasa na fad’i tayi.
     “Fannah Habibti kinyi shiru ko baki fad’a masa bane?”
  Qarya ta mata; “ko kad’an Mami,  karki damu na sanar dashi komai ahakan kuma yace yana sona ze aureni, ya kuma buk’ace ni da kar in sake kawo masa zancen koda wasa same goes to you to please Mami, maganan ya wuce kar mu sake d’agowa.”
    “Toh Alhamdulillah na matuk’ar jin dad’i wallahi, mahak’urci mawadaci kinga amfanin hak’uri kenan. Yanzu koda Ya Khaleel ya dawo se mu fad’a masa kinada mijin da zaki aura.”
    “Mami Baffah Khaleel ma bare sake dawowa ba sabida a yanzu haka Ya Farouq yana cell…” nan ta labarta wa Mami komai. Ba abinda Mami ke inbanda sunbud’a wa Anas albarka.
**
    Shima Anas d’in daga gidansu Fannah gida ya zarce cinye sa ne kawai su Ummie basuyi ba dan murnan ganinsa da sukayi. Abuu, Shettima kowa yaji dad’in ganinsa. Bayan sun gama cin abinci ya dawo d’akinsa ya jinguna jikin gado, besan dalili ba kawai ya tsinci kansa cikin nishad’i da jin dad’i musamman inya tuna reaction na Fannah data fad’a masa size na panties nata. Knock ne yazo daga k’ofar sa. “Come” yace.
    Shettima ne yashigo ya nemi waje ya zauna kusa dashi. “So Ya Anas ina kashiga kwana biyu ka kusan sama Ummie hawan jini Amal kuma ciwon hauka?”
    “Nowhere maza just that I needed space to think.”
    “Sure?” Ya tamabayesa yana wani murmushin tsiya.
    “Yau kuma dawani surutun ka taho?” Ya tambayesa.
  Well d’azu aka kirani w“ai an ganga a mall kai da Fannah kuna shopping.”
    “Mutane da gulma!” abinda yace kenan.
    “Aww dagaske ne kenan?”
    “Nima ban sani ba” ya amsa sa a takaice. “Tashi ka fita ma please don’t ruin my day. Nifa na fad’a maka ba san Fannah nake ba I’m just using her and thats all.”
    “Toh in tayi tsami mua ji nide a dage ko weekend ne a kawo mana ita muyi spedning.” Pillow Anas ya d’aga ya wulla masa wanda Shettima yasamu yayi dodging ya fice a guje yana dariya. Shikansa Anas dariyan yake.
***
 
    Da tunanin Fannah wanda keson zama masa jiki yayi bacci. Sede mafarkin Ummimi daya kwan biyu beyi ba yayi yau. A firgice ya tashi yana gumi yana nishi, k’ark’ashin gadonsa inda yake adana bottle d’aya zuwa biyu saboda situations like this in yayi mafarki yasha ya d’au d’aya ya bud’e. Har ya kai baki sekuma ya kasa sha yayi promsing Fannah bare sake sha ba, rufewa yayi. Wata zuciyar tace masa toh ai ko kasha barata sani ba tunda ba ganinka take ba. Nan ya bud’e ya sake kai baki nan ma yakasa sha. “Oh God! NO!!!” Toilet ya nufa ya juye a bathroom yayi flushing haka yayi da d’ayan ma, sannan ya koma ya kwanta. Ina fa, bacci ya gagara, mafarkin Ummimi se hunting nasa yake.
   Wayarsa ya d’ago daga kan side drawer yaga k’arfe 1:20AM. Miyarwa yayi ya sake kwanciya daga ya rufe ido se mafarkin Ummimi ya dawo daga inda ya tsaya. Yayi hakan sau uku kawai ya hak’ura da baccin inda giyansa na nan da yana sha nan da ‘yan mintuna zeyi everlasting bacci, duk laifin Fannah ne ita tasa sa yayi making promise kan bare sake shaye shaye ba, yanzu haka ita tana bacci shi yana nan yana wahala sede ayi  2-0. Wayarsa ya sake d’agowa yaga 1:40AM kan lambarta yakai ya danna mata kira.
    **
   Fannah na cikin baccinta me dad’in bala’i tajiyo ringing na wayarta ita tama rasa meya hanata sawa a silent har yagama ringing bata d’aga ba se a karo na biyu. Cikin bacci ta d’aga “hello” dan ko duba wake kira batai ba.
    “Miss Aleeyu” ya kira sunanta ai take ta nemi baccin nata ta rasa.
   “Mr. Fauzi”,takira sunan sa cike da mamaki. “Me ya faru da daren nan?” Torchi ta haska taga k’arfe d’aya ne.
   “I can’t sleep” yace da ita sincerely.
   “Toh Mr. Fauzi nikuma me zan maka?”
     “Nima bansani ba all I know is that is your fault.” Hamma ta saki tare da zaro idanu “nikuma Sir? Mena maka?”
   “You made me promised to you that barin sake shan wani abu ba, I’m badly in need of that now kuma na kasa sha, because I can’t break my promise to you!” ya fad’a ad’an tsawace.
 
        “Is okay calm down Mr. Fauzi, calm down okay? Karka sha please, zaka iya tashi zuwa kitchen?” ta tambayesa a hankali cikin murya me sanyi.
  “Yes” yace mata.
   “Good you are going to make your coffee, trust me in kasha you’ll go back to sleep peacefully but please kar ka sha wancan abun you promised, kaji Mr. Fauzi?”
   “Naji” yace tare da mik’ewa zuwa kitchen d’in. Haka tana fad’a masa directions d’in yana bi har ya had’a sede koda ya tab’a be kai nata dad’i ba.
  “It didn’t work Miss Aleeyu, ni barinsha ba.”
    “Yi hak’uri kasha, first thing gobe I’ll come to your office in had’a maka kaji? Yi hak’uri kasha wannan d’in  please will you do that for me?” Shiru yayi bece komai ba “please” ta rok’esa.
   “Okay” ya fad’a can k’asa k’asa.
    “Sleep good okay? Gobe da safe zan zo in had’a maka coffeen kaji?”
     “Naji” yace karap ta katse wayar. Da k’yar ya iya shanye rabin coffeen. Kasancewar ba Fannah ce ta had’a masa ba, sam ya kasa bacci amman dan yadda muryarta ke yawo masa a kai besan lokacin daya koma bacci ba.
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 48
BY MIEMIEBEE
     _5:00AM_
  Shettima ne ke knocking bakin k’ofan d’akin Anas, bacci Anas yake sosai wanda ya jima beyi erinsa ba ko jin knocking d’in baiyi. “Bam bam bam! Ya Anas katashi Asubah yayi.”
   Cikin gigin bacci yace, “naji seka b’alla k’ofan neh?”
    “Ya Anas bazaka masallaci bane?” Shi se yanzu ma ya tuna ana zuwa masallaci bayan na juma’ah.
   “Barinje ba zanyi a gida.” Dama amsan da Shettima ke jira kenan, Ya Anas baisan zuwa masjid inbanda na juma’ah daya zamo masa dole sekuma in Abuu ya tilasta masa. A sanyaye ya juya Abuu dake tsaye a parlour yana jiransu ya tambaya, “ya ina wan naka?”
    Qarya Shettima ya masa, “wai kansa ke ciwo zeyi a gidah.”
   “Toh Allah sawaqa.” Da “Ameen” da Shettima ya amsa sa suka fice. Se 5:15AM Anas ya tashi yayi sallah bacci ya koma se 7:00AM ya tashi ya soma shirin office yau kawai yaji yanasan sa jampah kasancewar yau Juma’ah. B’angaren da yake adana jampopin nasa ya bud’o suna nan turum ba adadi, dubawa yake chan yaciro wani sky blue half jampa yasa, se inche tunda nasan Mr. Fauzi be tab’a yin kyau kamar na yau ba, ba k’aramin amsar kayan yayi ba, cufflinks nasa masu tsada yasa. Fefes yafita bayan yagama feshe kusan rabin designer turarukan sa, jakar laptop nasa ya saqalo daidai yafito yaga Abuu zaune kan dining yana shan coffee. Cike da girmamawa yagaishe da Abuu tare da nufan dining space d’in shima dan had’a tea.
     “Ya jikin naka?” Ya tambayesa.
  Jiki kuma? ya tambayi kansa kode qaryan da Shetitima yayi dan rufa masa airi batun zuwa masjid d’azu kenan? “Da sauk’i.” ya amsa.
       Good, Anas I hope kana tsokaci da lokacinka, yau sati d’aya ya tafi cikin 6 months dana baka, kasani ko minti d’aya barin k’ara maka akai ba.” Ko uffan Anas bece masa ba, amman take blue eyes nasa suka k’ada ransa ya b’aci, se faman had’a tea’n sa yake.
   “Anas dakai nake magana.”
   “Naji” yace tare da ajiye flask d’in, tean ma ya fasa had’awa ya gommaci ya tafi da yunwa. Ficewa kawai yayi ransa na tafasa. Yawonsa ya fice se to 8 ya isa office ko amsa gaisuwan da ake masan ma beyi. Ganinsa cikin jamfa duk ya basu mamaki se kallon sa suke.
     “Sir you are looking awesome” cewar Mubarak. Wani kallo Anas ya watsa masa. “You are fired!” Ya daka masa tsawa. “Sir I’m sorry dan Allah kar kayi firing d’ina.” Bello dake gefensa ya basa tausayi. “Sir he is sorry please, consider this.”
    “Kaima kanada bakin magana kenan? Follow him you both are fired kuje ku samu Adam.” Nan ya nufa wajen elevator’n sa ko ya akayi yaga d’an wani stain kan floor d’in oho. “Wa yayi mopping floor d’innan yau?” Baki na b’ari Abdul Hamid dake gefensa yace, “Boss Yakurah ce.”
    “Jeka sameta and tell her she is fired inform Adam yayi replacing nata now, am I clear?”
   Baki na b’ari yace, “yy..yyes sir” nan Anas ya haura zuwa office nasa se huci yake shikad’ansa gawani uban yunwan dayakeji dan rabuwansa da abinci tun jiya da rana.
     *****
      “Ya Fannah kisa wannan d’in mana wallahi yayi kyau kuma ai Ya Anas zeji dad’i idan ya ganki dashi tunda shi ya siya miki.” Cewar Afrah tana mik’a mata wata electric blue gyale.
    “Banaso! Ha’an! Barin sa,ba kema kinsan ba burgeni gyalen nan yake ba, hijabi na mutunci na.”
     “Haba mana Ya Fannah ace saurayinki ya siya miki abu kik’i sawa? Gaskia ba haka ake soyayya ba.”
    Kuma fa haka ne, Fannah ta fad’i a ranta, inhar ta cigaba da behaving bata damu da Mr. Fauzi ba definately Afrah da gane ganenta zata gano bakin zaren wataran. Kai amman kuma bata so, bata son sa gyalen.
      “Barin sa ba ki miyar” ta bata amsa tana k’ok’arin ciro hijabinta daga cikin drawernsu, daidai lokacin Mami tashigo. “Ya Fannah amshi kisa mana.” Cewar Afrah.
   “Meke faruwa ne?” Mami ta tambaya tana k’arisowa cikin d’akin.
  Kafin Afrah tayi magana Fannah ta tareta “ermm babu komai Mami dama Afrah na tambaya ko gyalen hannuntan ya tafi da kaya na.”
   “Eh sosai ma ya tafi, yau kuma gyale za’a sa neh?”
    A kunyace tace, “eh mana Mami ko kin manta Anas ne ya kawo min.”
    “Toh yayi kyau Allah kiyaye hanya.”
   “Ameen Mami.” Gyalen ta amsa gun Afrah dake mata murmushin tsiya yafawa tayi harda rufe kai dashi. “Haba Baaba, meh haka sekace goggo? Ai tsofi aka sani da yafa gyale haka kawo kiga.” Nan Afrah ta tsara mata gyalen sosai tayi kyau.
    “Meh haka?” cewar Fannah tana kallon kanta jikin madubi. “Sekace neman miji zani? Batsan yayi yawa mana Afrah.”
  “Wallahi beyi ba Ya Fannah, dan Allah karki b’ata kibari a hakan.” Da k’yar Fannah ta yarda ta fice, tafi minti biyu tsaye bakin k’ofar Enterprise d’in amman takasa shiga se kunya takeji. Da k’yar ta iya ta shiga Yusuf ta soma tararwa da sauri ya nufi kanta “Fannah barka da kika zo! Dan Allah kije ki ba Boss hak’uri wallahi da safen nan yayi firing mutane uku.”
   
    “Mutane uku?” Fannah ta zaro ido. “Dalili?”
    Nan ya labarta mata komai… “kinsan haka yake in ransa a b’ace, please talk to him.”
   “Karka damu I’ll try.” Nan ta haura sama, jan bakin da Afrah tasa ta sawan dolen ta sa hannu tana gogewa sede koda ta ciro madubi ta duba taga yana nan kan yanzu ta shafa saboda 24hours ne. Tsuka taja, a hankali tayi knocking bakin k’ofar san. “Enter” yace. A hankali ta waina k’ofar ta shiga alokacin ko juyawa yaga waye ne beyi ba as ya zage se masifa yake kan wayan da yakeyi. Kallonsa Fannah ta tsaya yi dan yadda jampan jikinsan ya mugun amsar sa bata tab’a ganinsa da jamfa ba kuma setaga kamar jampan ma yafi amsar body figure’nsa. A’a to kodan bata tab’a ganinsa dashi bane? Wow! amman gaskia yayi kyau kasa kallonsa tayi musamman yadda gashin kansa ke sheqi.
       “Fire them dukansu ukun, fire them and replace them with better ones, am I clear?” Ding! Ya katse wayar. Nan ne ya juyo dan ganin ko waya shigo. A hankali blue eyes nasa suka sauk’a kan Fannah kallonta ya tsaya yi dan wani kyan da tayi, daga kan d’aurinta, yadda ta yafa gyalen, lace d’in jikintan, d’inkin da komai ya masa kyau. Fuskarta kuwa ba inda yakaisa yin kyau, dark red jambakin da tasa ba k’aramin haska skin nata yayi ba. Kallonta yake itama tana kallonsa duk suna admiring kyan junansu sekuma gashi kamar sun had’a baki duk suka sa blue kaya sede nashi light nata dark.
      Haushin da Abuu ya tusa masa ya nema ya rasa daga ganin Fannah. Ita ta fara kau da kai sannan shima ya kawar. A hakali ta tako izuwa gaban table nasa “good morning Mr. Fauzi.” Ta gaishesa beko amsa ba, kallonta kawai yake kai ta d’ago a hankali tana kallonsa taga shima ita yake kallo kuma koda suka had’a ido beji kunya ya kawar da idanunsa daga gareta ba. Ganin kallon bana k’arewa bane tace, “ermmm let me make you coffee sir./ Be ce mata komai ba ta juya.
    2 minutes later ta gama had’awa ta kawo masa tare da ajiye wa agabansa. Ganin baida niyan sha tace, “please take it sir” magana take masa a hankali dan abinda Yusuf yace mata kan ran Boss a b’ace yake yau. Sip d’aya ya kai baki tana tsaye a kansa. “Sir” takira sunansa cikin siririyar muryarta. Be amsa ba illa dawo da kallonsa dayayi a gareta.
   “Ermmm nace can you do me a favour?” Shiru yayi chan yace, “what is it?”
    “Sir please kadawo da wad’anda kayi firing… Please.”
    “No barin dawo dasu ba, bana son shisshigi, just make me coffee and leave ga chan flask d’in achan” ya nuna mata da yatsa.
   “Please fa nace, do this for me please, will you?”
   “No Miss Aleeyu, they are useless workers sesa nayi firing nasu.”
  “Sir saboda ance maka kayi kyau? Is it a crime? Yanzu nima in nace maka kayi kyau sekayi firing d’ina?” Ta tambayesa, shiru yayi bece komai ba.
  “Toh Mr. Fauzi kayi kyau yau, kayi kyau sosai. Is that it? Fire me toh.”
    “No Miss Aleeyu stop it! I can’t fire you, I just can’t.”
   “Why Mr. Fauzi? kamar yadda suke mutane nima haka nake, abinda zaka musu shi zaka min, be fair please.”
   “No Miss Aleeyu, you are diffrerent, kidena had’a kanki dasu. Kina min abubuwa da dama dayaci ache nayi firing naki amman I can’t.”
     “Toh kayi hak’uri ka dawo dasu please kaji Mr. Fauzi? Yi hak’uri this job is their only source of income yi hak’uri zasu kiyaye nan gaba.” Shiru yayi bece komai ba kuma bayida niyyan magana.
   “Mr. Fauzi must I beg on my knees zaka dawo musu da aikinsu? I’ll do it.”
    “No don’t! Zan dawo musu da aikinsu, don’t kneel.” Yayi warning nata dad’i taji sosai. “Sir are you serious?”
    “Yes kije kice Adam ya dawo dasu.”
   Cike da jin dad’i tace, “thank you sir, thank you” nan ta fice taje ta sanar da Adam godiya duka suka riga mata kamar su cinye ta. Bada jimawa ba ta dawo office na Anas. Coffee ta had’a masa cikin flask sede duk sanda ta d’aga kai ta kallesa shima ita yake kallo, har ya soma sata feeling uncomfortable. Gyalen nata tayi yunk’urun d’agawa zuwa kanta.
     “Stop, kibarshi haka” yace da ita. Yi tayi kamar bata jisa ba, se k’ok’arin d’agawa take. “Miss Aleeyu as your Boss and boyfriend I said stop it, okay?” Ya fad’a a tsawace nan ta bari wayarta dake side bag nata ne ya soma ringing nan ta ciro ganin Yusuf ke kira ta d’aga a takaice. “Hello?” On the other side yace;
  “Our life saviour!”
Murmushi ta saki wanda yasake fidda kyanta. “Kai dan Allah, ba komai don’t worry.”
    “Dama kira nayi  dan na sake miki godiya and to offer you a lunch saboda in sake nuna miki godiyata.”
    “Haba Yusuf is it necessary?” Duk wannan waya da takeyi Mr. Fauzi na zaune yana kallonta wani kishi yaji wanda be tab’a feeling ba ya tokaresa jin ta ambato sunan Yusuf wato dashi ma take wannan murmushi sekace an mata albishir d’in shiga aljannah, lallai Yusuf you wanna die ya fad’i a ransa.
     “Awwn! Lunch zaka siya min?… Aww tare zamuje muci?… Are you sure?… Toh nagode zan sauk’o yanzu… Thank you.” Nan ta katse wayar. “Mr. Fauzi zan tafi dama had’a maka coffee kace inzo yi nayi zan tafi, se anjima.”
   Bece mata komai ba as tunanin wani aiki ze bata tayi dan hanata fita da yake. Chan ya duba gaban table nasa yaga wasu mails da Kacallah ya kawo masa jiya wanda za’ayi reprinting nasu. Har takai bakin k’ofa ya kira sunanta “Miss Aleeyu!” Chak ta tsaya tare da juyowa. “Yes Sir?”
   “Come” yace da ita ba musu ta k’ariso. Pen da plane sheets guda goma ya irga ya mik’a mata tare da had’a mata da mails guda goman. “Gashi min copying wad’annan da neat handwriting don’t make any mistakes.” Kallon papers d’in ta tsaya yi sannan takoma kan Anas. “Mr. Fauzi kai kace fa am nomore your PA kuma yanzu kana bani aiki?”
 
   “Yes Miss Aleeyu, na canza mind d’ina ne yanzu in aiki ya taso zan iya saki tunda mu bibbiyu ne kawai, kiyi sauri I need them ASAP.”
    “Ayyah Mr. Fauzi kaifa kace ba aiki yanzu kuma…” Katse ta yayi “hurry Miss Aleeyu yau Juma’ah ne zanje masjid.”
   “Toh Mr. Fauzi ayi printing nasu mana ba sena rubuce su ba.”
   “Yes Miss Aleeyu rubuce su nakeson kiyi hurry up go and sit acan.” Zata sake magana yace, “now!” A d’an tsawace. Batada wani option haka taje ta zauna tafara copying tana rubutawa. Kallonta yake. Daidan ki kenan se muga ya ke da Yusuf d’in zaku fita lunch. Yace a zuci. Huh! Nima yunwa nakeji bari ta gama muje muci breakfast/lunch tare daga chan sena wuce masjid.
kuyi hak’uri abinda yasamu kenan yau
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 49
BY MIEMIEBEE
Kallonta yake kamar TV a yayinda take sauri sauri tayi tagama dan zuwa samin Yusuf. Guda 4 tayi cikin goma amman wani zogi hannunta ke mata saboda tsawon mails d’in, idanunta ta d’ago tareda maraice fuska koze d’an ji k’anta. Sosai shima yaji ta basa tausayi amman kuma ya ya iya? In yace tabari definately zata je ta samu Yusuf abinda baiso kenan, shikuma bayasan raini bayasan tasan kishinta yake ta d’au ko sonta yake (ni Miemie nace toh da ba sontan kake ba?) Yanason ce mata barata fita da Yusuf ba amman bayasan ta d’auka da wani manufa ta d’au ko santa yake kanta ya soma girma. Kansa ya kawar daga gareta kawai dan kar tausayinta ya kama sa tare da concerntrating akan laptop nasa.
    Bayan tasamu tayi guda takwas ta d’ago kai “Mr. Fauzi please kayi hak’uri nagaji.” Banza da ita yayi. “Mr. Fauzi please” nanma bece da ita komi ba dan yasan muddin bakinsa ya bud’u zece ta ajiye shikenan, abinda baiya so kenan. Wayarta ne ya soma ringing tana kai dubanta taga Yusuf ke kira bayan ta d’aga tace, “Yusuf I’m sorry wallahi aiki ne yad’an rik’eni amman I’m almost done yanzu zan sauk’o.” Nan ta katse.
 
       Anas dake sauraronta yace a ransa yanzu zaki sauk’o ba? We shall see. Bayan 10 minutes tagama, wani hamdala ta saki se murza yatsunta take dan azaba. “Sir gashi na gama” ta sanardashi alokacin da take tsaye gaban table nasa. Amsa yayi yana dubawa one-by-one komai yayi sede bayasan ya barta ta tafi, taya zataje tayi having lunch da Yusuf bayan gashinan, bayan tasan tare suke ci always, Isn’t he her boyfriend? Ai koda relationship nasun na k’arya ne still be kamata ba. Besan meh ba amman yanzu bayasan ganin Fannah da wani d’a na miji in ba shiba.
    “Sir can I go now?”
    “Wait” yace, tare da zaro d’aya daga cikin papers d’in “seda nace miki be careful banason cancelation kalli nan. D’au new plane sheet ki sake copying.” Kamar wacce zatayi kuka tace, “ayyaahh manaaaa Sir mana, letter ‘f’ nefa kawai nayi canceling its not looking rough ai.”
      “Ma ke kenan, to me it is morethan rough…” Yacigaba da duban sauran nan ya tsakula wasu guda ukun da tad’anyi light mistakes, in aka had’a dana farkon hud’u kenan. “Recopy them all duk kinyi omiting mistakes”
   Baki ta sake, “Mr. Fauzi wallahi barin iya ba dan Allah karka min haka.”
   “Miss Aleeyu what is wrong with you? I am paying you bawai aiki kike min kyauta ba d’auka kije ki zauna ki gama yanzu.” Ya fad’i authoritatively tare da kawar da kallonsa daga gareta. Harara mai rai da lafiya ta watsa masa ganin bai ganinta sannan ta tattara ta koma ta zauna. Yusuf takira ta basa hak’uri kan fitarsu bareyi ba seko next week saboda tasan ba yanzu zata gama ba, hannunta yayi tsami layi d’aya ta rubuta seta tsaya taja yatsunta.
     “Ba komai” yace “Allah kaimu” tare da katsewa.
   Dad’i sosai Anas yaji dayaji tace ta hak’ura. Kallonta yake tayi ta tsaya tayi ta tsaya tana gama guda d’aya tausayinta ya kama sa, tasowa yayi daga kujeran sa ya nufo gabanta, ita a zatonta ko yaga mistake na ‘a’ da ‘e’ da tayi ne yazo mata masifa. A maraice tace, “Sir dan Allah kayi hak’uri don’t make me recopy it please, wallahi guda d’aya ne kuma bara’a gane ba” ta k’are maganar kamar wacce zatayi kuka. Tsugunawa yayi a gabanta, ido wuru-wuru ta zaro meyake shirin yi? Kafin ta kawo wani abu a ranta ya ja hannunta a hankali, bugun zuciyarta taji ya k’aru, a hankali take k’ok’arin k’watan hannun nata gudun karya k’ara mata wasu papers d’in. Biron ya amsa ya ajiye tare da bud’o tafin hannunta me uban laushi yana mata tausa a hankali daga kan yatsunta har zuwa wrist nata.
      Har wani sanyi sanyi takeji saboda yadda hannun yayi tsami yana mata ciwo amman kuma be kamata  tabar masa hannunta yana tab’awa harda mata tausa ba. “Ermmm Mr. Fauzi” ta fad’i tana k’ok’arin karb’e hannun nata, sarai yagane tanason k’watan hannunta ne amman be kula ta ba, hasali yi ma yayi kamar be san tanayi ba, sanda ya tabbata ya mata tausan da yaci ace hannun ya bar zafi ya bari. Mik’ewa yayi ya koma ya zauna ba tare da yace da ita komi ba, dukda kuwa so yake ya bata hak’uri amman inaaa girman kai!
 
    Bayan ya zauna ta d’aga biron daga inda ya ajiye da nufin cigaba da rubutun tunda ba cewa yayi ta bari ba. Bece komi ba har yanzu se da yaga zata fara rubutun. “Keep the pen, stop it, don’t write.” Ya bata wannan commands. Kallonsa take  fuskarta d’auke da kan mamaki. “Sir bangama bafa-”
   “I know” ya katse ta, “just kibari don’t write again.” Dad’i sosai taji yanzu seta samu tafita da Yusuf ma tunda Boss yace tabari. Arranging papers d’in tayi ta kai ta ajiye masa kan table sannan ta koma ta d’au jakarta ta saqala, duk kallonta yake bece komai ba seda ta kai bakin k’ofa ya daka mata kira “Miss Aleeyu!” Har tsakiyar kanta tajiwo muryarsa. Juyowa tayi tana b’ari dan firgitan da tayi. Toh me tayi kuma yanzu? Da hannu yayi gesturing nata kan tazo. Taku take k’afa na rawa har takai gaban table nasa.
   “Who asked you to leave?” Ya tambayeta yana kallon cikin idanunta. Da sauri ta kawar da kallonta elsewhere ba tare da tace komai ba. “Am talking to you!” ya fad’a ad’an tsawace duk ransa yabi ya b’aci har yanzu be yarda Yusuf nada gut daze ce zekai Fannah cin abinci ba, yaushe ma yagama ciyar da kansa kuma awani local restaurant zekaita ko hotel ma bare iya kama musu ba to talk more of ya musu reserving.
     I’ina tasoma “ermm.. Si.. Sis.. Sir naji kace in ajiye in bari kuma aikin daka sani kenan.”
   “Amman nace ki tafi?” Kai ta girgiza a hankali. “Good kinga book shelve d’in can?” Kai ta giad’a tana kallon shelve d’in. “Jeki min arranging nasu.”
      Kallon shelve d’in ta tsaya yi nakusan ‘yan mintuna sannan back to Mr. Fauzi. Itade bata ga abin gyara cikin shelve d’in ba ga books nan duk anyi arranging nasu tsatsaf. “Bakiji me nace bane?” Ya tambayeta.
   “Naji Sir amman kuma naga ba abin gyara ciki, shelve d’in is well arranged.”
    “Toh ni banasan arrangement d’in na hannun dama a k’asa nakeson su koma hannun hagu a sama. Na tsakiya ki dawo dasu second to the last row, second row ki raba into two a 4th raw…” Haka ya ringa juye-juye. Kallonsa take kamar tayi kuka, ita ba abinda taji ma inbanda na hanun dama a k’asa su koma hannun hagu a sama.
  “Well baraki fara bane?”
   “Zan fara” ta amsa sa a takaice murya k’asa k’asa. Jakarta ta ajiye ta nufa wajen book shelve d’in. A hankali ta fiddo da na saman tayi replacing nasu dana k’asan kamar yadda ya buk’ata, a yayinda shikuma ya katse duk wani abinda yakeyi yana kallonta ko kyafta ido baiyi.
   Itade Fannah arranging take yadda taga dama, chan ta tsaya admiring wani latest english novel data jima tana nema bata samu ba. «Half Bad by Sally Green» kusan na minti biyu tana kallon littafin sannan ta had’a da sauran ta cigaba. A takaice de seda ta kusan awa tagama had’a uban book shelve na Anas dake nan kamar library. Daidai lokacin k’arfe 11:30AM kenan. Tagaji iya gajiya.
     “Sir na gama” tace all exhausted, ga wani uban yunwan daya keto mata lokaci guda. Bece da ita komai ba illa d’akinsa da ya nufa bayan like 5 minutes ya fito se k’amshin turare yake, gashin kansa ma ya sake gyarawa, kallonsa Fannah ta tsaya yi. “My girlfriend” yace da ita yana kallonta dawani killer smile tattare da fuskarsa shikansa yasan yayi kyau yau. Zuciyarta taji ya tsallaka bugu uku lokaci guda, kai ta d’ago a rikice tana kallonsa da ita yake koko a’a. “Me?” Ta tambayesa tana nuna kanta.
    “Yes you, you are my girlfriend ko kin manta ne?” Lallai ma! Kallansa take cike da mamaki yanzu yagama azabar tar da ita yawani zo yana shegen murmushinsa yana kiranta girlfriend nasa. “I’m hungry muje muci abinci nasan kema you must be hungry.” Yunwan takeji amman ta dake “no I’m not ni barinje ba kawai ka sallameni in koma gida.”
    “No ba gidan da zakije, we are going to eat, oya stand up na baki 5 minutes kije ki kimtsa a office naki.” Yi tayi kamar bata ji saba.
    “Miss Aleeyu! Don’t try my patience.” Ganin bai kallonta ta galla masa harara kan zata cire idanta sannan ta mik’e tare da jan jakarta ta fice zuwa office nata wajen book shelve d’in ya nufa yad’anyi dube-dubensa. Exactly after 5 minutes d’in yafito daga office nasan itama a daidai lokacin ta fito.
     Light makeup nata ta gyara ta hanyan k’ara powder da zalla datayi sekuma d’aurinta data sake gyarashi. Gyalen nanan yadda yake d’azu ta yafasa kamar yadda Afrah tamata d’azu. Kallonta yake wane ze had’iyeta. A hankali cikin k’asaita ya tako gabanta gam ta rufe idanta tana jiran ya fara suburbud’a mata surutu setaji ya kama hannunta take ta bud’e idan so take tace masa ya sake mata hannu sekuma ta tuna there will be no point doing so dan ba jin maganarta zeyi ba. Wajen elevator’nsa suka nufa bayan daya bud’u tace, “Sir semun nunawa duka ‘yan office naka muna dating ne? Kabari in mun fita anan amnan yanzu ka sakemin hannu please.” Ko tanka ta beyi ba illa janta waje da yayi suka soma tafiya.
      Take floor d’in yakama da surutu da gulma kowa se tofa albarkacin bakinsa yake k’us-k’us dan sun san halin Boss yanzu seya buga fire! Kunya ne ya rufe Fannah kamar ta nitse k’asa yanzu shikenan zasuce daman abinda ita da Mr. Fauzi keyi kenan kullum a office nasa, soyayya. Da idansu ya had’u da receptionist kuwa harara ta watsa mata dan ta jima da fad’awa tarkon san Mr. Fauzi koda ta fad’a masa kuwa tatas ya mata ya k’yamace ta. Ignoring nata kawai Fannah tayi, Yusuf dake shigowa yanzu ne yagansu tare da Mr. Fauzi amman ko kad’an idanunsa be kai kan hannun su ba.
   “Fannah!” Ya danna mata kira a yayinda ya gama k’arisowa kusa dasu. “About the lunch I think zamu-” be k’are maganar ba idansa ya sauk’a kan hannun ta dana Boss. Ido wuru-wuru ya zaro sekace a mafarki! Me had’in Fannah da Boss to kodai soyayya sukeyi? Fannah da hanaklinta zatayi soayayya da me shaye shaye?
   “Oh I’m sorry bansani bane daban gayyaceki lunch d’inba” ya fad’a tare da juyawa. Fannah ji take kamar ta nitse k’asa. “Yusuf” Mr. Fauzi ya kira sunan sa chak ya tsaya tare da kewayo wa. “ SWEETHEART baki sanar dashi bane dama? Why?” Shiru tayi bata amsa saba. “Tell him now to clear all doubts.” Nan ma bata tanka saba.
    Hannunta dake cikin nasa ya matse yadda ze d’an mata zafi.
    “Na zata na fad’a masa, Yusuf I’m sorry.”
    “Sorry for what? Don’t apologise HONEY fad’a mashi yanzu.” Shiru tayi duk takaici yabi ya cikata.
   “ QUEEN,ko yunwan ne bakiya son magana? I’m sorry yanzu zamuje muci abincin just tell him kinji HONEY BOO? ” Wai meke damun Mr. Fauzi ne ta tambayi kanta so yake yayi ruining friendship nata da Yusuf ne ko me? In yacigaba da abinda yakeyi ai se Yusuf ya d’au k’arya ta masa d’azu batun aikin dayace ya mata yawa, se yace ko k’arya ta masa daman fita zatayi da Mr. Fauzi take b’oye masa.
 
       Ido kawai ta rufe tace, “Yusuf I’m sorry ban fad’a maka ba, Anas is now my boyfriend excuse us please zamuje muchi abinci.” Mamaki ne sosai ya ratsa Yusuf lallai ma Fannah tacika ‘yar halak.
  “I’m sorry for delaying you, by the way congratulations” a sanyaye ya juya yayi tafiyarsa, binsa da kallo Fannah tayi, ji take kamar tayi kuka, mesa Mr. Fauzi ze mata haka? Bata sake ce masa komai ba har suka isa hotel d’in shi da kansa ya bud’e mata k’ofa se dad’i yakeji saboda yasan definately yanzu Yusuf da yake zaton saurayinta ne ze rabu da ita tunda ya gansu tare.
 
     Abinci kala d’aya ya musu ordering kafin abicin ya iso ba abinda Anas yake inbanda kallon Fannah shi inama haka zata namasa shiri kullum. Duk lokacin data d’aga kai setaga ita yake kallo. Da k’yar kalamun dayakeson kiranta dasu tun d’azu da safe suka fito yanzu, “you are looking beautiful today.” Kai ta d’ago tana kallonsa da mamaki karara a fuskarta. Wayace mata tayi kyau? Mr. Fauzi? Kode k’arya kunnuwanta suke mata. “Eh sir?” Ta tambayesa.
    “Not Sir, Anas” yayi warning nata.
   “Anas me kace?”
   “Nace kinyi kyau yau.” Ido wuru-wuru ta zaro yau wata rana Mr. Fauzi ya yabata, sede bata san meh ba seta tsinci kanta cikin jin dad’i, toh se meh dan yace tayi kyau? Se komai ya faru k’wak’walwarta ta bata amsa. Murmushin jin dad’in datayi k’ok’arin kawar dashi ne ya kub’uta mata, kallon ta Anas yake dad’i yaji yasata murmushi. “Thank you” tace a hankali cikin jin dad’i, take ta nemi bak’in cikin daya tusa mata ta rasa. “You too kayi kyau.”
   “I know already ba sekin fad’a min ba, I always look good.”
   Toohhhh! Ta d’ago kai tana kallonsa yaga shima ita yake kallo, shegen girman kai tace a zuciyarta wai I always look good irin yasan shi kyakkyawan nan ne, Allah raba mutum da erin wanga hali.
   
    “My girlfriend nasan ban isa in hanaki kallo na ba amman kallon yayi yawa unless you wanna eat me up.”
   Wai lallai ma tace a ranta wato shi ya zage yana kallona in ni nad’an kallesa yace wani na cika kallo.
    “But Sir naga nima ai kallo na kake, kuma tun d’azu tunda nashigo office naka yau.”
   “Toh ai dan na kalleki doesn’t mean anything, ni kawai kallon ki nake saboda kin d’an yi kyau yau kuma ni bada wata manufa nake kallonki ba amman kinga ke kullum cikin kallona kike, day and night kuma da wata manufa kike kallo na. I can see it in your eyes, kallon soyayya kike min nikuma nayi warning naki don’t fall for me.”
Bakin Fannah seda ya kusa fad’i a k’asa dan yadda ta sakosa. “Nide ba kallon soyayya nake maka ba.” Ta fad’a tare da kare kanta.
   “Ohonki nide na fad’a miki SWEETHEART don’t fall for me.” Dadai lokacin abincinsu ya iso. Waiter’n ranan ne ya kawo musu wanda ta tambayesa nawa ne kud’in plate. “Wow Miss Aleeyu you are looking amazing.”,Murmushin daya k’ayata ta tasaki “thank you.” Wani kallo Anas ya watsa wa waiter’n take yaji wani bak’in kishi ya tokaresa ji yake kamar ya tashi ya shaqure sa ai shi yakamata ya yaba kyan da tayi ba wani daban ba, kuma yayi.
 
  “Can I have your number?” ya tambayeta, “zanso zama abokin ki.”
   “K’ato dakai?” Anas ya tambaya a fusace, “toh barata bayar ba. Ko kunya ma bakaji ma mschww! Boss naka zan kira yayi firing naka next time baraka sake cewa kanasan wata da abokanta ba, stupid kawai.”
    “Mr. Fauzi I’m so sorry dan Allah naga PA’rka ce am sorry please.”
    “She is not my PA she is my girlfriend.”
   “Omg! Mr. Fauzi please forgive me wallahi bansani ba.”
   “Damuwanka, Boss naka zan kira abincin ma mun fasa ci.” Wallet nasa yaciro ya irga kud’in ya wurga masa.
   “Fannah lets go” ya fad’i a fusace. Dakewa tayi, “Anas” ta kira sunansa cikin wani irin salon muryan da bata tab’a amfani dashi ba. “Calm down kaji? Calm down please.”
    A hankali yaji hankalinsa na kwantawa. “Calm down please” ta sake fad’i. Idanunsa da suka kad’a taga sun soma dawowa asalin farin kalansu.
*© miemiebeee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 50
BY MIEMIEBEE
Kamar wanda bareyi magana ba yace, “naji tashi mu tafi.”
    “Promise me baraka kira boss nasa ayi firing nashi ba.”
   “Thats none of your business, he deserves to be fired.”
    “Please Anas for me, please karka kira Boss nasa kaji Anas? Please.”
    “Fannah no!” Ya fad’a ad’an tsawace.
         Fuska ta maraice, “Shikenan tunda d’an wannan ma baraka iya min ba” jakarta ta tattara ta mik’e da niyyan tafiya gyalenta ya rik’o. Da k’yar bakinsa ya iya furta “no don’t go, barin kira Boss nasan ba, just don’t go.” Dad’i taji sosai da murmushi ta juyo tana kallonsa “thank you, so ka hak’ura muci abincin anan?”
 
    “No not here, lets go somwhere” be jira tace wani abu ba yakama hannunta suka fice, gidan baya suka shiga dukansu a yayinda driver ya kunna mota. Ita yanzu Fannah damuwarta d’aya ne yadda zata masa wa’azi yadena rik’e mata hannu, tana son tabisa a hankali ne kar ta had’a masa komai lokaci d’aya shiryuwan ma yace yafasa akoma gidan jiya. Gaban wani makeken hotel driver’n ya tsaya bayan ya bud’e musu k’ofa Anas yafito sannan ita, ciki suka shiga hannunta rik’e cikin nasa sede yau da mutane cikin hotel d’in zaune suna cin abinci ana ganinsu aka soma gulma k’us-k’us. Magana take iya yadda Anas ne ze jiyota.
      “Anas kad’an sake min hannu kaga duk maganan mu suke kaji please.” Banza yayi da ita ya nufa wajen receptionist. “I want to reserve this place now.”
    “Okay sir bara a sake karb’an customer ba, but bari na cikin su gama please.”
   “Kasan ko waye ni? I said reserve it now ka koresu duka I will pay you double of the money.”
   Ido ya zaro sosai jin double, “okay sir, bari amusu magana.” Haka mutanen suna ji suna gani aka kaisu wani d’an waje suka k’are cin abincin chan, aka barwa Fannah da Anas kad’ai makeken wajen. Kujeran tsakiya suka zauna ya musu ordering abincin, bayan minti uku abincin nasu ya iso spoon nasa ya d’aga ya soma ci, yayi spoons biyar yaga ko tab’a nata batayi ba.
     “Fannah why are you not eating? Acanzo miki ne?” Kai ta girgiza “Anas dole in zakaci abinci sekayi reserving ne?”
   “Yes wani abu ne?” ya tambayeta yana cin abincin sa.
    “No-” kafin ta k’ara fad’in wani abu yace, “banasan surutu while eating just keep quiet and eat okay?” Kai ta giad’a masa ta soma ci a hankali, kamar kullum yagama yayi zaman jirarta, wayarsa dake ringing ya d’aga “okay then” yace tare da katsewa. Bayan tagama ci ya biya suka fice gidan gaba ya bud’e mata cike da mamaki tace, “Anas ina driver’n yaje?”
     “He went somewhere, I’ll be the one to drive, enter.”
    “Sir zan tafi da kaina” haka kawai taji batason tana shiga mota dashi kad’ai.
    “Miss Aleeyu kina b’ata min lokaci zanje masjid get in.” Zata sake magana yace, “now” a tsawace.
        Ta tsorata amman ta dake “sir ni zan tafi da kaina.”
       “I’m your boyfriend ko kin manta? Kishiga ko in d’aga ki in saki ciki da kaina.” Miyau ta had’iye tashiga a hankali danko tasan Anas baida kunya tsab ze d’agata. Nan ya rufo k’ofar, not long enough yatada motar, agogon hannunsa ya duba yaga 15 mins to 12:55PM lokacin sallan juma’ah. “Fannah” ya kira sunanta, nan tabar kallon windown da takeyi ta juyo dad’i sosai yake mata yadda Anas ke kiran sunanta ‘Fannah’ cikin daddad’an muryarsa, har setaji ta sake k’aunar sunan nata inama dashi yake kirarta kullum. “Yes” ta amsa sa.
     “Can you wait in idar da sallan juma’ah se in kaiki gidah?” Kai ta giad’a masa daga nan be sake cewa komai ba a inda manyan mutane suke parking motocinsu yayi parking nasa a space da aka tanada masa, a kunne yabar motar dan AC’n daya kunna mata. “I’ll be right back.”
  “Okay” tace masa tana kallonsa har ya b’ace cikin mutane, shiru ta zauna tana d’an kalle kallenta chan bacci ya d’auketa wanda batasan yaushe ba. Bayan 25 ninutes Anas ya dawo yana bud’e motar yaga Fannah na bacci da wuyanta karkace gefe d’aya, gyalenta kuwa rabinsa ba’a jikinta yake ba hakan yabawa Anas daman k’are wa k’irjinta kallo, yayi kusan minti d’aya yana kallonta sannan take ya kawar da kansa yana girgizawa “no this is not approppriate.” Zagayowa yayi ta side nata ya kwantar mata da kujeran yadda zatafi jin dad’i tare da gyara mata kanta agarin haka d’ankwalinta ya kunce. “Oh no!” Anas ya fad’i k’asa k’asa. Allah yaso ribbon natan be kunce ba, yanayin gashin dake kwance kan goshinta da sajenta ya tsaya yana kallo, besan sanda ya d’aga hannunsa ya shafa kan sajen fuskartan ba, ganin ta d’an motsa yaja hannun nasa baya da sauri gudun kar ya farkar da ita. Mayafinta yaja a hankali ya rufe mata k’irjinta dashi, kanta kuwa d’ankwalin ta ya bud’a ya d’an rufe mata gashinta sama-sama sannan ya rufo k’ofar yadda bareyi k’ara ba.
   
      Side nasa ya nufa ya shiga ya zauna sede sam ya kasa kunna motan a gudunsa kar ya fara driving kuma ta tashi in suka d’an hau kan bomb. Zama yayi tare da ciro wayarsa yana chatting yana zaman jiran tashin Fannah. Bacci sosai takeyi chan ya juyo yana kallonta, kallo na sosai, cameran wayarsa yashiga yayi positioning sannan ya d’auketa picture d’aya, ganin tayi kyau ya k’ara mata d’aya kasa hak’ura yayi seda ya mata pictures kusan hams
Nishi take sosai tana hak’i a yayinda zuciyarta ke bugawa d’ari bisa d’ari, ko damuwa ta kewayo dan ganin ya cikin gidansu Anas yake bataiba, abinda tasani kawai gidan nada kyau, bayan ta tabbata dawakan sun wuce tagwada bud’e k’ofar daidai lokacin Shettima ke dawowa daga yawonsa shima a tare suka tura k’ofar sede ya rigata. Suna had’a ido ya sakar mata da murmushi, murmushin ta mayar masa sede daga yadda take abu yagano tana cikin hanzari.
   
    “Fannah!”
    “Na’am Shettima.” Ta amsa.
    “Yau kece a gidan namu?” Ya tambaya yana mata murmushi.
   “A’a dawakai suka biyo ni, ina jiran Anas ne barin wuce please.” Ta fad’a cikin hanzari duk hankalinta ba’a kwance ba.
    “Fannah lafiya?” ya tambaya tare da sake blocking nata.
   “Shettima please ka matsa min in fice, kar Anas yaganni anan.”
    “Ya Anas? Shi yace karki shigo ne?” Shiru ta masa bata amsa ba hakan ya tabbatar masa da ‘eh’ ne amsar. “Karki kula sa haka yake shigo please kinji? Amal tayi missing naki.”
   “A’a Shettima, wataran zan dawo amman yanzu ka matsa min in fice please.” ta fad’a tana duba bayanta gudun kar Mr. Fauzi yaganta.
    “Haba mana Fannah yanzu baraki shigo ba? Yi hak’uri, Ummie naciki kinga seku gaisa kinji ko bahaka ba?” Kai ta girgiza masa tana tuna irin warning da Mr. Fauzi ya mata. “A’a I promise next time amman yanzu wallahi nashiga Anas ze sab’a min.”
    “Trust me ba abinda ze miki shi Ya Anas haka yake, sharesa please kishigo.” Nan ma kai ta kad’a “please mana Fannah sena had’aki da Allah ne? Kishigo please.”
    “Shettima wallahi Anas yace kar in shiga, kabari next time.” Kafad’a ya buga “ai wallahi sekin shiga Fannah, mubar musu kawai kinji? Bismillah.”
   “Shettima please…” Kai ya girgiza mata ganin ba mahalicci se Allah tace, “Shettima inyamin masifa fah? Seda yace min kar inshiga fa.”
    “Ai sharesa zakiyi, haka yake mushiga please.” A sanyaye tabi bayansa duk tsoro yabi ya ratsa ta tunanin wani erin masifa zata sha wurin Mr. Fauzi kawai take, sun kusa da bakin k’ofar ganin Shettima bai ganinta taja da baya zata gudu aiko tuni yaganta ta jikin mirron window karap ya cafko abayanta. “Fannah aini ba’a min wayo, mushiga kawai.”
    “Shettima kayi hak’uri please kabarni in tafi.”
   “Mushiga kawai Fannarmu.” Haka suka shiga cikin katafaren parlour’n su, dake d’auke da kayan tafiyar da imanin mutum a kowani second. Zaune ta iske Anas da Ummie kan kujera. Bayansa ta hango saboda kallon direction na Ummie dayake. A lokacin da idanunsu ya had’u da Ummie kuwa tayi saurin sunkuyar da kanta.
   “Shettima!” Ummie ta kira sunansa cike da mamaki ganinsa da budurwa. “Yau kuma budurwarka ka kataho mana da ita gida?” Jin an ambaci budurwa Anas ya juyo dan ganin wannan budurwar Shettiman yayi dariya.
    Ai zubewa ne kawai idanunsa basuyi ba a k’asa dan yadda ya warwarosu ganin FANNAH a parlour’nsu. Inba wai ya manta bane he made it clear to her karta kuskura tashigo. K’in d’ago kanta tayi su had’a ido tinda taji alamun blue eyes nasa a kanta. Yafi minti d’aya yana kallonta totally speechless bema san me zece mata ba dan yadda tabasa mamaki.
    “A’a Ummie ai wannan tafi k’arfina zubin billonaires ne da ita” cewar Shettima har yanzu Anas bebar kallon Fannah ba launin fuskarsa take ya koma ja dan b’acin rai ko sauraron Shettima ma beyi ba. “Dade Ya Anas kika tambaya bare rasa amsar da kike nema ba.”  Se yanzu hankalinsa yadawo, kallon Shettima yake tare da watsa masa wani irin wawan kallo.
     “Kai Shettima deh!” Cewar Ummie cike da zumud’i. “Fannah ga Ummie, Ummie ga Fannah.” Shettima yayi introducing nasu wa juna. Har k’asa Fannah ta tsuguna ta gaishe da Ummie cike da girmamawa, itama Ummien cike da fara’a ta amsa ta. “Taso ‘yata taso dan Allah” kafin ace meh Ummie taje ta r’iko Fannah tare da k’ariso da ita kan kujeran da suke zaune da Anas, a yayinda ta zauna kan hannun kujerar irakuma se kallon Fannah take kamar ta cinye ta, Fannah kuwa fitsari ne ya matse lokaci d’aya dan har yanzu Anas bebar kallonta ba.
    “Shettima kace wannan kyakkyawar ba budurwarka bace?”
   “A’a Ummie, Ya Anas kama Ummie explaining mana.”
 
    Kallonsa yadawo gare da Shettima, “wallahi inbaka min shiru anan ba zan maka duka.”
    “Kai Ya Anas a gabantan ma bara muyi koda shirin k’arya ba? Ai ganga ake bugi ba mutum ba. Zaka fad’awa Ummie wace ita ne ko in fad’a mata.” Takalmin k’afarsa yayi yunk’urin cirewa, Shettima na ganin haka ya lab’e bayan labule. “Fannah koh?” Ummie ta tambaya a nitse.
   “Eh Ummie” ta amsa ta cikin siriryar muryarta.
   “Toh Masha Allah ke da wa kuka shigo?” A hankali ta d’aga kai ta kalli Anas da ba abinda yake in banda hararan dayake watsa mata, miyau ta had’iye takasa amsa tambayar Ummie duk tsoro ya cika ta.
    “Ita da Ya Anas ne” cewar Shettima dake lab’e bayan labule. “Wai Ummie ke baki gane bane? Budurwar Ya Anas ce fah.” Ido gam Fannah ta matse tana niran sauk’an duka.
    “Budurwarsa fa kace Shettima? Alhamdulillah!” Rungumo Fannah tayi, se mammatse ta take a jikinta. Anas ji yake kamar ya k’urma ihu dan takaici da bak’in ciki.
     “Ashe Allah ze nuna min ranan da Babana ze kawo min mace gida, kai alhamdulillah. Fannah tunba yau ba nake jirar wannan rana, ranarvda zamu had’u. Allah miki albarka, kai nagode. Kinga sekina hak’uri da Baban nawa sabo-” bata k’are maganar ba Anas ya katse ta.
    “Wai me haka Ummie? Nifa ba budurwa ta bace, tsiyar Shettima ne kawai, ke tashi mu tafi.” Yace da Fannah alokacin daya dawo da kallonsa gareta yana galla mata wani erin harara.
   “Baba na meyayi zafi? Ai wannan ba abar b’oyewa bace iyyeh? Ko rowarta kake mana ne?” Shafo fuskar Fannah tayi “ ‘yata karki jisa kinji? Yi zaman ki.”
Cike da kunya da tsoro tace, “uhm Ummie ba buduwarsa ce ni ba, wasa Shettima ke miki.”
    Da murmushi sosai a fuakarta tace  “ni nagane ‘yata, Allah barmin ku tare. Barin kawo miki koda ruwa kinji?”
 
   “Wai Ummie meh haka ne? Kekuma tashi mutafi.” Anas ya fad’i a fusace.
   “Ba inda zataje, Shettima duba ko Abuu na gida ka masa magana.”
   “A’a Ummie karki damu please-” Fannah bata k’are maganar ba Ummie ta katse ta “ ‘yata karkiji komai kinji? Feel free, feel at home. Jeka duba Abuu Shettima.” Nan ta fice kitchen a yayinda Shettima yaje duban ko Abuu na gida shima, yarage daga Fannah se Anas. Hannunta ya kama tare da murd’awa cike da mugunta. K’ara ta saki “arghh! Mr. Fauzi please ka sake min hannu da zafi.” take hawaye ya soma cikowa a idanta.
    “Da zafi? Me nace miki amma, didn’t I tell you kar ki shigo? Mesa bakiya jin magana ne?” Azaban ne yamata k’ak’a har hawayen suka soma tsiyaya dan yadda ya murd’a hannun nata. Daidai nan Ummie tafito da tray cike da snacks da drinks akai. “Ya meke faruwa?” ta tambaya alokacin datake k’arisowa cikin parlour’n. Hannun Fannah ya sake da wuri gudun kar Ummie tayi suspecting wani abu amman ina ta riga ta hango hawayen dake mak’ale cikin idanun Fannah.
   
    “Ya Salam Mama na meya sameki?”
    “Bakomai Ummie abu ne yashiga mata ido.” Anas ya amsa tun kafin Fannah da aka tambaya tayi magana. “Sorry dear ya fita? Muga.” Kamar dagaske yawani sa hannu yana duban idanta harda hura mata iska.
    Hawayen ta had’iye “shikenan yafita” tare da kawar da kanta ba tare da ta kallesa ba. Serving nasu drinks d’in tayi. “Bismillah uwata” Ummie tace da Fannah. “Babana fad’amin mana toh ina kuka had’u da Fannah?”
     “Ummie please me haka ne? Fannah tashi mutafi.”
    “Yanzu Anas itanma se an mana rowanta?”
  K’arya ya mata, “Ummie we need to go ne, zan kawo ta some other day.”
    Dad’i sosai taji “ka yarda budurwarka ce kenan.” Ta fad’i dawani shu’umin murmushi tattare a fuskarta.
   
     Shiru yayi kamar be jitaba. “Anas fad’a min mana.”
    “Eh Ummie shikenan kinji? She is my girlfriend. Tashi mutafi Fannah.” Daidai lokacin Shettima ya dawo “Ummie Abuu fa bai gida kuma ga motarsa a pake.” Wani sanyi Anas yaji a ransa bashi kad’ai ba hatta Fannah dagajin Abuu bai gidah. Mik’ewa yayi itama haka, ko jiran tama Ummie se anjima beyi ba yasoma janta, itade Ummie cike da mamaki take kallon Anas budurwarsan ma bare saurara mata ba.
     Bayan sun shiga mota ya soma suburbud’a mata masifa wane an turoshi. “Wai ke mesa bakiya jin magana ne iyyeh? Didn’t I tell you karki kuskura ki shiga? You are not my girlfriend you are just a fake one banasan family na su ganki, kin huta ai yanzu da Ummie taganki mschww! Mutum ace mishi don’t amman seyayi.”
    Hawaye take sosai “Sir kad’au wai dagangan na shiga gidanku ne? Doki ne ya biyoni ta fad’i” cikin kuka tana share hawayenta.
    “I still don’t care!” Ya fad’a a tsawace. “Acikin motan me ze miki? Msschw! Kin d’au wasa nake ba, you’ll be suprised 1000 paper zan baki kiyi correcting.” Kukanta ne ya tsananta kamar ‘yar yarinya ta tsaya tana kuka harda me sauti tsuka yaja ya soma driving ganin kukan nata bana tsayawa bane ga kuma kukan ya soma damunsa ya tsaya gefe guda akan titi. Ko d’ago kai ma batai ba se kukanta da takeyi kanta cuse cikin cinyarta.
     “Toh kukan ya isa” ya fad’i a hankali. Banza tayi dashi ta cigaba.
     ‘Sorry’ yakeson fad’a mata amman bare iya ba, “ya isa I shouldn’t have shout at you kinji? Stop crying” namma bata bar kukan ba. “Okay barakiyi correcting 1000 papers d’inba, I take that back, bar kukan.” Bata d’ago kai ba har a yanzun sede ta d’an rage kukan nata. “Bafa dan wai inaso bane na shiga gidan naku, doki har biyu ne suka biyoni ni nikuma inajin tsoro, dana shiga na had’u da Shettima, shine yayi insisting sena shiga.” Ta sanar dashi cikin sautin kuka.
     Sekuma yaji wani iri amman ai still da ta shiga koda gidan neighbours ne. “Toh d’ago fuskarki, kukan ya isa na fad’a miki banasan jin kukanki.” Tana d’ago kai ya mik’a mata hand kerchief nasa, amsa tayi ta share hawayenta a yayinda yayi zaman kallonta, kukanta na d’aya daga cikin abubuwan da yake burgesa a gareta, abu kad’an setayi kuka. Ice cream shop ya wuce da ita bata ce dashi komai ba. Bayan yayi parking yafito ya bud’e mata nata tare da rik’o mata hannu mutane kad’an suka samu ciki.
   Kap flavours dayasani na ice cream seda ya siye mata amman kuma bece mata nata bane haka suka dawo cikin motar, zaman makoki suka tayi har seda ya kawo ta gaban gidansu, a nitse ta bud’e k’ofar ko se anjiman ma batayi niyyan fad’a masa ba “girlfriend” ya kirata, banza tayi dashi da sauri ya cafko abayanta kafin ta rufo k’ofar. “Your ice cream take it.”
  “Banaso” tace tana turo bakinta, har yanzu haushi yake bata jibi yadda ya riga mata masifa.
    “Girlfriend take it kinji?” Hak’urin nan de dayakeson bata ne ya kasa. Ganin battada niyan d’aukawa yace, “okay barin sake miki masifa ba, kema obey all my rules yanzu d’auka kinji?”
    Wato shi be iya bama mutum hak’uri bako? Tace a ranta. “Ni ka sakemin abaya in tafi.”
     “Fannah” yakira sunanta yadda takeso “take it kinji? Barin k’ara ba.” Kallonsa tayi na ‘yan seconds sannan ta ciro ledan tayi tafiyarta ko godiya babu.
★★★★★
    “Ummie dan Allah Ya Fannah tazo?” Amal ta tambaya.
   “Eh kai!” Ummie ta amsata se dad’i takeji Anas yakawo budurwarsa gida. “Yace ze sake kawo mana ita karki damu.”
   “O’o ni barin yarda ba. Ni zanyi inviting nata birthday party na.” Daidai lokacin Anas yake sa kai cikin parlour’n da alama yajiyo abinda Amal tace just now.
    “Wa zakiyi inviting a birthday nakin?”
   “Ya Fannah mana Ya Anas shine ko ka fad’a min zaka kawota, amman ka iya cemin kar in fad’awa kowa picture’nta dake wayarka.”
   “Rangem! Ya zama fashashhen k’wai” cewar Shettima yana daka tsalle. “Ashe abin kenan, wayyo! Ya Anas ka nunwa Ummie mana taga hoton surikar tata.” Dafe baki Amal tayi batasan lokacin data fad’a ba. “Ya Anas I’m sorry wallahi bansan ya akayi na fad’a ba.”
   Wani irin kunya ne ya ratse Anas dayakeji kamar ya tone k’asa ya shiga ai yanzu shikenan sekowa ya zata eh son Fannah yake, bece da Amal komai ba illa k’arisowa cikin parlour’n da yayi a gaban Ummie ya tsuguna.
    “Ummie please kar kowa ya fad’awa Abuu yau wata ta shigo gidan nan.” Cike da mamaki Ummie ke kallonsa “toh Babana ai abu ne me kyau kuma shima dad’i zeji.”
     “A’a Ummie ni kawai kar kowa ya fad’a masa kaji Shettima?”
   “Senayi tunani tukun” yabasa amsa yana kallon yatsunsa dan tsiya.
   “Zan baka kud’i wallahi yanzu ma kaje ka d’auka bundle na d’ari biyu ni kawai kar ka fad’a masa.” Shettima lashe money najin haka yace “karka damu Ya Anas your secret is safe with me” take yayi d’akin Anas. Instead ya d’au na d’ari biyun seya zari na d’ari biyar dan kud’in suna nan ne ba adadi. Bayan yafito Anas yace, “muga nawa ka d’auka.”
    “Ji Ya Anas de baka yarda dani bane?” Wayarsa yaciro kamar ana kiransa. “Lecturan?” Yayi pretending yana kan waya. “Toh gani zuwa.” Aiko sauraran Anas beyi ba yafice shopping, yau za’ayi renewing wardrobe.
**
     “Ya Anas amman please ka amince inyi inviting nata birthday na ran monday, please Ya Anas.”
   “Eh mana Babana kabarta tazo kaji?” Ummie tasa baki.
   “A’a Ummie nikam kunga matsalar dayasa banso shigowar yarinyan nan ba kenan.”
   “Toh meh aciki? Ai wallahi ko ka yarda ko in fad’awa Abuu yaso nan da wata ma ayi bikinn mu huta, in tanada k’anne ma duk su taho tare.”
   “A’a please na yarda zan fad’a mata ni kawai karku fad’awa Abuu. Ita kad’aice batada k’anne.”
  “Ya Anas amman fa akoi wata Aiman da muka tab’a gaisawa da ita.” Kunya yaji an kamasa yana k’arya. Wani kallo Ummie take masa ina irin angano kan nan.
  “Toh meh? Ai ba k’arya nayi ba na mance ne.” Nan ya tashi yashiga d’akinsa se huci yake shi ya tsani abunsa haka. Yanzu what if Abuu ya had’u da Fannah kuma fah? Mschww! Wayarsa ya zaro daga pocket nasa ya danna mata kira alokacin kuwa ita dasu Aiman da Afrah duka suna zaune suna shan ice cream nasu. Ganin shi ke kira tak’i d’agawa halan wani masifan yakeson mata. Seda yakusan tsinkewa ta d’aga “hello” tace a hankali, Afrah kam ko kyafta ido battayi dan gulma ganin haka Fannah ta bar musu d’akin.
    “Kin iya shiga gidanmu ba? Ai gashi yanzu Amal tace sekinzo birthday’n ta ranan monday mutum ace masa don’t amman se yayi.”
   “Birthday’n Amal? Toh Sir kace musu zanyi tafiya mana ai ba lalle ne senaje ba tunda baka so.”
    “You should have thought about that ai kafin kika shiga, daman abinda kikeso kenan kisamu kina shigan affairs na family na.”
   “Ni ba abinda nakeso ba kenan kuma barinje ba, shikenan?”
   “Miss Aleeyu don’t dare me, Monday by 4:00PM driver zezo ya d’aukeku dasu Afrah duka inform them, ni na fad’a miki” karap ya katse. Harara ta watsa wa wayar wane shine Anas d’in. Bayan takoma ciki tabasu Afrah labari ai ice cream da ba’a gama sha ba kenan dan dad’i. Kayan wardrobe nata ta zazzage duka ana neman kayan zuwa party ganin ba wanda ya gameta ta yafo mayafinta suka fice shopping da Aiman.
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 52
BY MIEMIEBEE
English wears had’ad’d’u na ‘yan gayu maras tsireci ta siya wa kanta sannan wani had’ad’de wa Aiman itama bata damu da Fannah ba saboda tasan bara’a rasa d’aya cikin kayakin da Anas ya siya mata ba.
    2 days later…
   _Monday 3:30PM_
     Kaya ne wargaje cikin d’akinsu Fannah, su Afrah ana shirin zuwa party. Ba hassada tayi kyau, kayan ya mata kyau makeup nata yayi kyau, kamar yadda ta tsara kanta haka ta tsara Aiman ma dukansu biyu sunyi kyau banda Fannah dake zaune kan gado tana buga candy crush da towel d’aure a k’irjinta.
   “Wai Ya Fannah bara kije bane? Dubi time fa! Ga kayanki nan tun d’azu na cire miki kink’i sawa.” Cewar Afrah
     “Barin jeba in kun had’u kice masa banida lafiya.” Daidai da shigowar Mami kenan “waye ne baida lafiyan?”
    “Mami wallahi gatanan tak’i tashi ta shirya.”
  “Mami wallahi k’arya take, yanzu fitowa na daga wanka ko Aiman? Ina kayan nawa insa. Wane ni ace birthday na in-law na barinje ba.† Kallonta Afrah ke cike da mamaki. Kayan ta jawo ta zira wata maroon doguwar riga ne har k’asa me hannun vest da kwalya sosai a jikinsa ta saman, bayan tasa shi ta d’auko wata had’ad’d’iyar ash-ash jacket me siririyar dogon hannu dake shek’i ga kwalyan stones daya sha, yana nan da tsayi shima har kusan k’asa amman be gama kaiwa ba, ta d’aura akai. A bud’e yake saboda ya bayyano da kwalyan dake d’auke da doguwar rigar dake cikin. Afrah ce tamata makeup d’in basu d’au lokaci ba saboda ba wai gira za’a zana mata ba. Maroon gyale tayi rolling dashi seda ash jaka da takalmi data sa. Feffeshewa sukayi da turare 4:00PM on the dot driver’n yamata waya kan gashi nan.
   Allah kare Mami ta musu suka fice. Daidai gaban gidansu Anas ya tsaya bayan an bud’e gate ya shiga dasu. An k’ayata filin tsakar gidan da had’ad’d’en decoration na red and white, tsayuwa dan kwatanta kyan wajen ma b’ata lokaci ne. Bayan sun fiffito daga motar suka tsaya chak Afrah da Aiman kam se k’are wa gidan nasu Anas kallo suke bada jimawa ba gate ya bud’u motan Shettima ya  bayyana. Yana ganin Fannah yaji wani dad’i ko lura dasu Afrah beyi ba seda ya fito suka gaisa da Fannah sannan idanunsa suka sauk’a kan Afrah (fire) kasa dena kallonta yayi dan had’ewar data masa, ashe ba Ya Anas kad’ai keda rabo ba harda nima ya fad’a a ransa.
    “Ina wuni?” ta gaishe sa.
   “Lafiya sannu ko? Fannah kuna kama ko sister kice?”
   “Eh sunanta Afrah wancan kuma Aiman.”
   “Wow pretty ladies sede ma Afrah duk tafi ku kyau.”
    “Noi! Wani kyau tafimu? Kwalya de ta fimu, nida Aiman duk munfita kyau.”
   “A ganinki kenan nide Afrah tafi min kyau.” Afrah kam se blushing take, wani me kama da Blue eyes yace mata tanada kyau.
       “Fannah kushiga daga ciki su Ummie suna parlour you all are welcome.† Duk wannan magana dayake yakasa d’aga idanunsa daga kan Afrah.
   “Tam, taho muje Aiman, Afrah lets go.”
    “A’a ni dakaina zan kai Afrah koban fad’a miki tafi ku kyau duka bane.” A hankali ta d’ago idanunta da suka sha tozali da liner ta azasu kan Shettima dake d’auke da murmushin dayake k’ara masa kyau, murmushin ta mayar masa, “lets go ko? My lady.,By the way I’m Shettima, k’anin Ya Anas amman fa karki d’au wani babban bro na ne, dududu shekara d’aya da rabi yabani.”
   Murmushi sosai Afrah ke harda ‘yan hakwara a waje.
    “Nima ai, 1½ years ne kawai tsakani na da Ya Fannah.”
   “Owww really? Zo mud’an fita kafin programme d’in ya fara.” Motarsa ya bud’e mata tashiga se rawan jiki yake yasamu ‘yar kyakkyawa. A ice cream shop ya tsaya suka sauk’a, kud’in Ya Anas zeyi amfani.
      Bayan an kawo musu ice cream d’in suka soma sha a hankali. Cikin d’an k’ank’anin lokaci suka saba sosai, dake halayensu na neman tsokana da neman zance duk d’aya ne, labarin abubuwan da suke ma yayunsu suka rigayi, bayan sun gama chan suka tab’o b’angaren karatu Shettima harda zuzutawa wai yana d’an business. Afrah ta jima tana nan perfect boyfriend segashi tasamu kyakkyawa k’anin billonaire. Ba b’ata lokaci Shettima ya fad’a mata santa yake, tunda idanunsa suka sauk’a kan kyakkyawar fuskarta yaji yana sonta. Aiko itama ma hakan ne, take sukayi exchanging I love you da I love you too. Bayan sun k’are shan ice cream d’in yakaita shopping duk acikin kud’in daya sata gun Anas ranan.
    Afrah kam dad’i kasheni.
     ****
   Fannah kuwa tun shigarsu gidan bata had’u da Anas ba taji Ummie na cewa baya gida ma, Abuu kuwa yayi tafiya, hamdala ta saki. Birthday girl ansha kyau sosai tana ganin Aiman taji tana san miyar da ita little sister tunda ita batada. Bada dad’ewa ba programme ya fara har a yanzu su Shettima masu soyayya basu dawo ba. Bada dad’ewa ba gate ya bud’u had’ad’d’iyar benz na Anas ya shigo. Bayan yayi parking yafito ko kallon direction na mutanen baiyi wajen Amal nasa ya nufa yayi wishing nata happy birthday tare da ajiye mata present nata na iphone 6+. Direct parlour ya nufa bayan yasha ruwa ya ciro wayarsa ya kira Fannah yaji ko sunzo. Tana zaune abinta taga call na Anas. Me kuma zece mata yanzu? Da k’yar ta d’aga “hello?”
  “Kunzo?” Ya tambayeta a takaice
“Eh.” ta amsa sa.
   “Ina kike? Kizo parlour yanzu ina jiranki” karap ya katse. Inje kamin me ta tambayi kanta kamar wacce barata ba, sekuma ta mik’e taje zaune kan dining chair ta samesa ya aza k’afafunsa kan table d’in yana kad’awa da wayarsa rik’e hannunsa. Sosai shirin dayayi ya masa kyau kodan bata tab’a ganinsa da erin shirin bane?
   Shima kallon nata yake, gani yake kamar bata tab’a kyau erin na yau ba, kodan be tab’a ganinta cikin english wears bane? Kasa dena kallonta yayi, da k’yar ya iya cemata “zoki zauna” tare da ja mata kujeran gefensa.
    A sanyaye tanufa wajen sede bata zaunan ba gudun kar Ummie tazo ta kamasu bibbiyu.
     “Mr. Fauzi you called for me, wani abu ne? Kaga I need to get back.”
   “Sit toh.”,Yi tayi kamar bata ji saba. Hannunta ya rik’o “sit first.” Dan kawai ya sake mata hannu ne ta zauna. Bayam daya k’are mata kallo kusan na mintuna biyu yace, “kinyi kyau.” ‘Yar murmushi ta saki, “thank you.” Dad’inta kenan da Anas duk sanda tayi kyau ze fad’a mata. Cameran wayarsa ya shiga yayi muting, yasoma d’aukanta hoto seyi yake kamar amfani da wayar yake.
    “About business trip da zanje Morocco ne, nafasa zuwa dake tunda you are now my girlfriend, zamuje da Kacallah.” Dad’i sosai taji.
   “Okay Sir.”
   “Call me Anas.”
   “Okay Anas shikenan zan iya tafiya?” Besan meh ba seyaji bayason ta tafi yafison ya kasance tare da ita always.
   “Jibi ne tafiyan nayi rescheduling.”
   Nanma “okay” tace. So barata ce masa ko safe trip ko Allah kare ba wato.
    “What kind of an I don’t care girlfriend are you? I’ll be travelling ko d’an safe trip babu.”
   “Toh Sir nag-”,sekuma tayi shiru ganin battada abin cewa “I’m sorry, safe trip Allah ya kare ya dawo dakai lafiya.” Chan k’asa k’asa yace, “ameen seda na tambaya.” Ita Fannah bata aza abin boyfriend girlfriend nasun a ka ba saboda batasan ta sake bud’e zuciyarta ma wani na miji because a k’arshen ita zata wahala danko duk na mijin daya gano some day batada budurci ze guje ta, abinda bataso kenan, maganin bari kar ma a soma.
   “Zan tafi.”,Tace a hankali.
  “No I want you to stay Fannah don’t go.” Har a yanzu bebar d’aukanta hoton dayake tayi ba haka yak’i  barinta ta tafi, kuma bawai hira yake janta dashi ba kallonta kawai yake yana d’aukanta hoto. Da kallon ya isheta tace, “Sir kaifa kace adena kallo dayawa.”
    “Yes amman ni ai am your boyfriend me aciki dan na kalleki? You also enjoy it when ever I’m starring at you so kidena pretending.”
    “Nima ai am your girlfriend amman dana kalleka sekace bakasan kallo, kayi adalci kenan?”
        “Miss Aleeyu kallon soyayya kikemin nikuma banaso, ni kawai kallonki nake saboda kinyi kyau.”
   
        “Toh nima ai saboda kayi kyau nake kallonka.”
         “Ni ai kullum inayin kyau, am handsome kekuma time-to-time kikeyin kyau.” Ganin inta sake magana ze iya zaginta tayi shiru kawai bata sake cewa komai ba k’arfe 5:30PM nayi ta mik’e “Sir zamu tafi kar Maghrib ya mana anan.” Hannun ta ya rik’o “I will take you guys home.”
     “No please karka damu we can go on our own.”
    “Fannah I’m your boyfriend I insist.”
    “Toh Mr. Fauzi kasakemin hannu please.”
   “No Fannah, I enjoy holding your hand, allow me.”
   “Sir ba kyau ne.” Kafin yace wani abu ta b’arke masa da kuka, shark’af shark’af besan lokacin da ya ciro hanky ya soma share mata hawayen nata ba. “Fannah why are you crying? Na miki wani abu ne? Kodan danace time-to-time kikeyin kyau? I don’t mean it kinji? You are beautiful, always looking gorgeous saisa nake kallonki kullum. Bar kukan kinji?”  Har yanzun be sake mata hannun ba duk yabi ya kid’ime ganin yadda take kuka. Baya san ganin ta tana kuka bayyaso ko kad’an.
      “Niba wancan ba” ta ce tana kukan still.
Sosai taji dad’i daya yaba kyanta haka. “Toh meneh Fannah? Stop crying please”
      “Anas ba kyau, akace da namiji ya tab’a jikin macen daba muharramarsa ba gomma yatab’a garwashi, azabansa kuwa yafi ad’au k’usa a buga masa a kai har se ya nitse. Anas banason amaka wannan azaba, banaso please kadena rik’e min hannu gomma ace ma muna da aure ne kake rik’emin hannun I wouldn’t mind amman a yanzu haka haramun ne, kadena kaji? Banason amaka wannan azaba, please.” ta k’are maganar tana hawaye. Shiru yayi chan yace a hankali “shine dalilin da kike kuka?”
   Kai ta giad’a masa a hankali har yanzu bata bar kukan ba. Hannunta ya sake a hankali “toh ya isa daga yau barin sake rik’e miki hannu ba kinji? Stop crying.” Da murmushi a fuskarta ta d’ago kai tana kallonsa “promise?”
   Kai ya giad’a mata.
    “Bani kad’ai ba kowace mace baraka sake rik’e mata hannu ba?”
    Nanma kai ya giad’a, “what of Amal? Har itama?” Ya tambayeta.
    “Amal muharramar kace zaka iya rik’e mata hannu da ita da Ummie amman banda matan waje.”
   “Okay…” ya fad’a yana giad’a kai. “Cry nomore kinji? Barin k’ara ba”
    Tana murmushi ta giad’a masa kai “I won’t ever. Thank you Anas lets go?”
  “Yes lets go.” Yayi assuring nata, da a dana ne hannunta cikin nasa zasu fice amman banda yanzu. Side-by-side kawai suke tafiyar. Bayan sunfito suka sami Afrah da Shettima zaune kan wata doguwar kujera sun baje se hira suke suna dariya kamar wanda suka jima da sanin junansu.
      “A ina suka saba?” Anas da Fannah suka tambayi juna a tare.
   “Nima bansani ba” suka sake amsar junansu a tare. Murmushi kad’an suka saki. “Shettima fa baida matsala ina shi ina Afrah?” ya tambaya cike da mamaki.
   “No let them be please karka mishi magana.” Cewar Fannah cikin salon da dazaran tama Anas magana dashi yake amincewa da k’udurinta.
  “Fannah amman kina ganin is okay?”
   “Yes don’t bother, lets go.” Bayan ta ajiye wa Amal birthday present nata taja hannun Aiman, ai atapir Amal tace se Aiman ta kwana mata, ita a dole tasamu sister. Da k’yar ta amince tabar Aiman ta tafi bayan ta kwashe mata kusan rabin birthday present nata tabata.
    “Toh Afrah seki tashi ai mutafi ko? Soyayyar ya isa.” cewar Fannah. Murmushin jin dad’i Shettima ya saki a yayinda kunya ya ratsa Afrah musamman ma dataga Ya Anas gefen Ya Fannah yana kallonsu.
 
    “A’a kuje ni zan kaita.” Cewar Shettima. Anas zeyi magana Fannah ta dakatar dashi “lets go ze kawo ta yace.” Badan Anas naso ba yabi Fannah suka fice.
kuyi min uzuri please da rashin posting da nakeyi kwana biyu, somethings came up
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 54
BY MIEMIEBEE
Ba Afrah ce ta dawo gidah ba se bayan Maghrib, hankalin Mami duk yabi ya tashi dukda kuwa Fannah ta tabbatar mata cewar Afrah is safe with Shettima k’anin Anas.
   
      “Shettima thank you for today.” Cewar Afrah alokacin da take k’ok’arin bud’e murfin motan. “No let me babe” nan ya zagayo ya bud’e mata tare da ciro shopping bags guda biyu daya cika mata da kayaki. “Will call you as soon as na isa gidah, I love you My Afrah.” Tana murmushin jin dad’i tace, “I love you too My Shettima” ahaka suka rabu.
     Taku take a hankali gudun kar a jiyota aiko tana shiga suka had’u da Aiman kafin tace meh Aiman ta sa ihu “Mami ga Ya Afrah ta dawo.” A 360 Mami da Fannah suka fito. “Ke Afrah zo nan” cewar Mami kai a sunkuye ta k’ariso kafin Mami ta fara mata masifa ta kare kanta ta hanyar yin k’arya “Mami wallahi motarsace ta samu matsala seda muka kira me giara.”
    “Uhn uhn fa Afrah kiyi a hankali daga had’uwan ki da yaro seku zarce da soyayya?”
   “La ilahi! Mami abakin wa kikaji wannan zance?”
   “Ni na fad’a mata ai ba k’arya bane” cewar Aiman. “Mami wallahi har zama sukayi gu d’aya.”
     “Ai Aiman barta-”
    “Mami yi hak’uri ya isa zan mata magana” Fannah ta katse ta a hankali cikin dabara. “Afrah mushiga daga ciki.” Amsar d’ayar ledan hannun nata tayi sukayi d’akinsu. Bayan sun baje kan gado Fannah ta soma mata magana; “Afrah ni bawai hanaki zanba amman ki bi komi a hankali kinji? Na miji na miji ne.”
    “Ya Fannah wai nikan hassada akemin neh? Me aciki keda Ya Anas nida Shettima darling kin-” bata k’are maganar ba wayarta ya soma ruri tana kai dubanta taga Shettima ne datayi saving da ‘hot baby.’ Karap ta d’aga. “Hello baby” tace a nitse cikin wata salon da Fannah bata tab’a saninta dashi ba. Baki ta bud’e cike da mamaki tana kallonta haka har Afrah tagama wayar ta katse Fannah bata bar kallonta ba.
      “Har haka soyayyar taku tayi nisa?”
      “Hummn!” Taja numfashi, “Ya Fannah kenan, guguwar son Shettima ne ya kamani, wallahi ya had’un had’ewa duk abinda nake nema jikin d’a na miji yaja dashi. Daman ni dream d’ina na auri kyakkyawa sega Shettima nan Allah ya kawo min.”
   “Awww! Har tunanin auransa kike?” Cewar Fannah baki wangalau.
    “Humm! aini barni kurum har yaran da muka haifa ma na hango, barni in duba kayakin da ya sissiyo min ma tukun.”
    ★★★★★
       “Ya Anas in shigo?” Cewar Shettima dake tsaye bakin k’ofar Anas.
     “Shigo” ya basa amsa. A nitse ya bud’e k’ofar ba kamar yadda ya saba ba, ‘yar vest na Anas dake k’asa ya d’aga “Ya Anas in sa maka wannan cikin laundry basket?”
   Kallonsa Anas yake yau wata rana. “Eh sa” yabasa amsa. Bayan yasa yadawo ya zauna kusa dashi. “Ya Anas dan Allah alfarma nike nema.”
   “Name fah?” Cewar Anas yana duban laptop nasa.
    “Ya Anas bundle na d’ari biyar zaka bani please.” Ajiye laptop d’in yayi gefe guda cike da mamaki, “Shettima yaushe ne na baka na 200 da zakace in baka na 500 yanzu? Me kake da kud’in. Awww! Kaima kasan kayi girlfriend ko? LOL ba abinda zan baka, go and work for it, earn it!”
      “Ya Anas mana please, wallahi na mayar da hanakalina wajen karatu yanzu ka taimaka please.”
    “Amman Shettima kai kanada hankali mah kuwa? Ina zaka kai Afrah?”
    “Ni Ya Anas banche ka zageni ba, kud’i kawai zaka ban.”
   “Aww kawai ne? Sekayi kashinsa ai tunda kawai ne.”
    “A’a Ya Anas please yi hak’uri.”
   “Naji banasan surutu ina ganinka bud’e safe d’in d’au d’aya kabani waje.” Tsalle ya daka yana masa godiya sannan ya zaro d’aya daya lek’a yaga Anas bai kallonsa ya k’ara d’aya tare da b’oyewa cikin kayansa.
     “Uhm Ya Anas dama nace batun mota ta wallahi ta tsufa tasoma shan mai ko za’a d’an canza min.”
   Maganar da yayi kad’ai yasa Anas shak’ewa harda tari. Dududu shekarar motar nawa ne? Da k’yar inya kai d’aya shine Shettima ke wannan zance.
     “Ai da fili kafito kawai kace min kayi budurwa kaima kanasan ka fara hawa babban mota irin nawa.”
   “A’a wallahi Ya Anas ni ko E350 ka siya min walillahil hamdh Allah zan karb’a, kaji Ya Anas.”
  “Hehehe! su Shettima an girma har ansan ayi budurwa.”
   “Ya Anas mana…”
“Naji in naga kayi hankali zan canza maka motar, inko a’a zaka cigaba da zama da C 230 d’inka.”
    “Thank you so much Ya Anas, nagode, Allah bar mana kai ya k’ara dank’on soyayya tsakanin ka da Fannah.” Bejira jin meh Anas zece ba yafice. Murmushi ya saki jin an ambato sunan Fannah, shi yau through out ma besha coffeen ta ba, yayi missing inshi kuwa sosai, wayarsa ya lalimo ya danna mata kira bada dad’ewa ba ta d’aga “hello Anas.”
    “Fannah” yakira sunanta.
   “Na’am” ta amsa.
   “Yau bansha coffee ba.”
    “Yi hak’uri gobe zanzo in had’a maka.”
   “Har gobe?” ya tambayeta cikin wani irin salo cike da damuwa.
     “Toh Anas ai bareyi infito yanzu ba yayi dare, goben kaji?” Shiru yayi bece komai ba. “Kaji Anas?”
   “Naji” yace chan k’asa k’asa.
   “Yawwa goodnight” sannan ta katse. Ji yake kamar ya sake kiranta bai gajiya da jin muryarta amman kuma bayyasan ta raina sa ta d’au ko sonta yake. Bayan ya idar da isha yayi forcing kansa yayi bacci da k’yar danko yunwa yakeji kamar hauka.
     Washegari ya tashi as usual ya soma shirin office yashiga wanka kafin yafito yaga an share masa d’aki anyi mopping an gyara gado, toh waye ne? Yaushe Amal ta share nata d’akin bale ta share masa nasa, ganin baida amsar wannan tambaya kawai yayi shirinsa yana fitowa yaga shock of his life, Shettima har yagama tsara masa breakfast da alama sharan d’akin ma shi yayi.
   “Shettima?” Anas ya kira sunansa still not believing abinda idanunsa suke gane masa.
   “Na’am Ya Anas good morning bismillah ga breakfast nan na had’a maka.” A hankali ya tako ya zauna kan kujerar Shettima ya zuba masa chips da scarmbled egg daya masa, sannan ya had’a masa tea.
 
      “Tsaya aljanu ne suka shige ka komeh?” Anas ya tambaya.
   “Aljanu kuma Ya Anas? Dan na had’awa wa Yaya na guda breakfast se ace aljanu sun kamani?”
    “Toh d’akina fah? Kai ka share?”
   “Eh Ya Anas bismillah ci kar kayi latti.” A zuci Anas yace ahhh lalle Shettima nasan in canza masa mota LOL gaba ta kaini, nasamu new man servant. Koda yagama breakfast d’in Shettima ne yakai masa jaka mota.
   Tuk’i yake hankalinsa kwance Baana ya danna masa kira cike da jin dad’i ya d’aga.
    “Maza ne!!” Yace yana murmushin jin dad’i.
    “Blue eyes nashigo gari fah jiya.”
  “Ohh haba! Shine baka fad’amin ba?”
   “Wallahi tafiyan dare ne, zanzo office naka yau.”
   “Toh sekazo, Kashim fah?”
    “Wancan? Ai yana chan a Bama ya washi tafiya.”
    “Kace be canza ba kenan, anyhow ina jiranka.” Ding! Ya katse wayar. Kamar kullum aka bisa da gaisuwa har zuwa office nasa, bada dad’ewa ba Kacallah yashigo da complain, na barin gidan man engine da akayi a dalilin haka ya b’aci se an kira me gyara. Bayan da ya gama karantawa yace, “fire him, ka kori me aikin ai ganganci ne yasa sa mancewa be rufe gidan man ba, ka kuma yi replacing nasa with someone better, clear?”
  “Yyy… Yes Sir.”
   8:30AM yama Fannah a building, kamar jirarta Sule me kula da engine yake, yana ganinta ya nufo ta dan yaji intama Boss magana yana saurarenta. Bayan ya gaisheta yake bata labarin abinda ya faru, “wallahi Hajiya waya aka min mata ta tana labour kuma ba motan da ze kaita sesa duk na rikice na mance ban rufe gidan man ba, dan Allah kima Boss magana ya dawo min da aiki na, in na rasa aikin nan bansan dameh zan ciyar da matata da d’an mu data haifa ba.”
   Tausayin sule ne gabad’ai ya ratsa ta. “Don’t worry kaji? Zan masa magana in shaa Allah ze dawo maka da aikinka.”
   “Godiya nake Hajiya, Allah saka miki da alkhairi.”  “Ameen” tace sannan ta fice. Bayan tayi knocking yace, “enter” a nitse ta bud’e k’ofar ta shiga tun daga chan yake kallonta, wata skyblue silky doguwar riga ne a jikinta me dogon hannu, seda kuma red gyale d’an siriri data yafa ta nannad’e a wuyarta. Jaka da takalminta kuwa fari ne. Kallonta yake har yanzu, yafisan ganinta ba hijabi tafi kyau, bayan ta k’ariso gaban table nasa ta gaishesa ba takan gaisuwar yake ba ko amsawa beyi ba “kinyi kyau” yace mata. Tana murmushin jin dad’i tace, “thank you” tare da juyawa nan da nan ta had’a masa coffee, ko ina taje idanunsa na kanta, bayan ta had’a ta kawo masa ta ajiye a gabansa.
     Ba tare da b’ata lokaci ba ya soma sha tana tsaye a gefensa seda taga ya ajiye cup d’in tace, “Sir.” Kai ya girgiza mata “Anas.” Ya gyarata.
   “Okay Anas nace ba batun firing Sule da kayi ne dama.”
   “What about him?” Ya tambaya yana kallonta. “Yabar min gidan mai a bud’e yayi destroying engine d’in sena kira me gyara fa yanzu, he is not paying attention to his work.”
   “Ayyah Anas ba haka bane, matarsa ce tashiga labour shine aka kirasa hankalinsa ya matuk’ar tashi. Dalilin dayasa ya mance kenan.”
    “Wancan kuma damuwansa, he is fired and that stays that.”
    “Anas ka dawo masa da aikinsa please, kaji? For me please.” Shiru yayi be ce komai ba. “Please kaji?” Nanma shiru. Kukan da baya bata wahalan yi ta soma take hankalinsa ya tashi. “Toh kukan me kuma?”
    Cikin kukan tace, “ka dawo masa da aikinsa please.”
   “Fannah NO!” Wani sabon kukan ta k’irk’iro harda me sauti. “Fannah for goodness sake me haka kitayin kuka? In na dawo masa da aikin zaki bari?” Kai ta giad’a “okay, okay naji stop crying.”
    “Se ka kira Adam kace adawo dashi zan dena.” Take yakira Adam, “bring back Sule aikinsa.” Ya katse. “Shikenan zaki bar kukan?”
   “Eh” tace tare da share hawayenta. “Thank you Anas.” Wajen coffee machine ta nufa dan had’a masa cikin flask. Knock ne yazo daga bakin k’ofa “come in” Anas yace. K’ofar na bud’uwa sega Baana bayan ya k’ariso sukayi manshake se hirar su suke irin tasu ta maza nan da nan Fannah tagama d’ura masa coffeen cikin flask, ko d’aga kai taga wayene batai ba. “Sir nagama zan tafi” kafin ya amsata ta fice.
   “Woooww!” Baana yayi exclaiming.
   “Maza wannan me zubin india fah?”
    “Kai de halinka na son mata na nan har yanzu ko?”
   “Me za’a fasa? Gaskia tamin inaso.”
  “Kanaso?” Anas ya tambaya tare da d’age gira. Kai Baana ya giad’a masa yana assuring nasa. “Lallai kam tun wuri ma gomma ka hak’ura wannan tafi k’arfin ka.”
 
    “Ban tsammanin akoi macen da zata fi k’arfi na yanzu, sufa mata kud’i kawai suke bi wallahi yau da za’ace biri goggo yazama billonaire mata zasu bisa su auresa, so ya za’ayi ne in samu lambarta?”
    “You are wrong Baana, kaga wannan duniya da abinda ke cikinta be dameta ba, your money will never impress her, she is different from all other women, saboda haka ka fita daga harkanta.”
   “Kode kaima kana ciki ne?”
    “Ai itace matar da zan aura.”
   “Aure Anas!” Ya tambaya yana zaro ido. “Yaushe a gari?”
“Nide na fad’a maka kafita kabar harkan Fannah wallahi dan akanta se mu b’ata.”
   “Allahu Akbar! Maza kaine kuwa? What changed you haka?”
   “Fannah, she is the one who changed me.”
★★★★★
     *MOROCCO, 2:15PM*
  Cikin _Royal Mansour Marrakech Hotel._
   
    Kwance Anas yke bisa kaftareren California bed ya d’aga pillow tare da jingina ajiki, da isarsu Morocco shida Kacallah awa biyu kenan yanzu. Jiran sim card daya aiki Kacallah siyo masa yake, through out yau be sha coffeen Fannah ba, besata a ido ba, bekuma ji muryarta ba, seji yake kamar ya rasa wani sassa a jikinsa Kafin subar Nigeria yaso kiranta amman girman kai ya hanasa sekuma yanzu yake regreting. Bada d’adewa ba Kacallah ya kawo masa yana sa sim d’in ko gida be kira ba ya zuba number’n Fannah.
**
    Tana kishingid’e a kan gado ita d’ayanta tana buga game a wayarta ya soma ruri ganin international number yasa bata d’aga da wuri ba. A hankali ta sa a kunne “hello.”
   “Fannah” ya kira sunanta.
  “Na’am Anas, ina wuni?”
   “Lafiya” ya amsa blankly.
   “Uhm har kun isa ne?”
   “Eh you didn’t even mind calling me.”
   “I’m sorry, so yaushe zaka dawo?”
   “Are you missing me already?” Ya tambaya yana jin dad’i.
    “Yes I am missing you, I’m missing your your girman kai da masifa.”
   “Ai nabar yin masifa yanzu.”
   “Anya kuwa?” Ta tambaya tana murmushi.
     “Yes, nikuma I’m missing your coffee, your crying and face.” Dad’i sosai taji ya ratsa ta, wannan na d’aya daga cikin abubuwan da takeson Anas, he is very sincere komin ya gaskia take yana fad’i unlike ita, itama tayi missing kyakkyawar fuskarsa sabida rabuwansu da juna tin ran tuesday yau thursday amman ta b’oye masa.
   “To be sincere I miss your face you too.”
    “I know you would, dole zakiyi missing handsome face d’ina ga kuma unguwan ku ba kyawawa ko?”
     “Mr. Fauzi kaga irin halinkan ba, sesa banasan fad’a maka abu kacika feeling dayawa, I have to go Mami na kira na.” Karap ta katse tana murmushi, bawani Mamin dake kirarta bata san me zata ce masa bane kawai, duk lokacin da take waya dashi setanajin wani iri.
      Shigowar Afrah d’akin kenan ansha gayu kamar ba gobe, “Afrah ina zuwa haka?”
    “Wallahi hot baby na ne yazo, yana jira na ma yanzu haka. Madubi nazo kalla in fice” aiko tana ganin kanta ta fice. Tsaye tasame Shettima yayi crossing arms da legs jikin motarsa sanye yake da wata farar half jampa.
  “My queen kinyi kyau” yace da ita alokacin data gama k’arisowa kusa dashi.
  “You too my king.” Hira suka sha kamar ba gobe se kusan Maghrib yace ze tafi  bundle na d’ari biyar ya tsakulo a aljihunsa ya bata. Ido tazaro “hot baby duka wannan?”
   “Eh nakine sweetie, jiya mun samu profit sosai a business namu shine nima nace barin kawo miki rabon ki.”
   “Thank you hot baby” ta amsa. Bayan ta dawo ciki ta wula kan gado ta sami Fannah. “Ya Fannah you won’t believe this.” Bandir na d’ari biyar d’in ta ciro ta miqa mata.
   “Ke ina kika samo wannan?”
  “Hot baby na yabani.”
  “Shettiman? Aina yasamu? Yana aiki ne?”
    “Yana business mana.”
   “Business? Toh aini bansani ba. Ke Afrah bafa haka ake soyayya ba, ai kika cigaba da amsar kud’i dayawa haka gunsa seki talautar dashi.”
  “Toh ai bani yayi ba rok’a nayi ba. Wayyo! A gobe zanje in siyo Iphone nima.”
**
   Chan dare misalin k’arfe goma sha d’ayan dare a Morocco ko bacci Anas yakasa se juye-juye yake, ga gajiya amman yakasa baccin ba abinda yake inbanda tunanin Fannah. “Oh God! What is wrong with me? Why can’t I think of anyone se Fannah? Why?” Pillow ya d’au ya rufe fuskarsa dashi ko ze d’an rage tunaninta, ai se worse ma yake. Wayarsa ya d’ago daga kan bed side drawer ya kirata. Tana cikin baccinta tajiyo ringing na wayarta kamar wacce zatayi kuka ta d’aga ko duba wanda ke kira batai ba.
  “Fannah” ya kira sunanta. Jin muryarsa ta tashi ta zauna.
   “Mr. Fauzi what is it?” Ta tambaya cikin bacci.
  “What are you doing?”
   “Bacci mana” ta amsa sa a takaice rai ad’an b’ace.
    “Okay shikenan” ya fad’a kamar d’an yaron da aka mai rowan sweet ya katse wayar. Wayar ta ajiye ta koma bacci sede kuma daga yadda Anas ya mata maganar kamar bacci ya kasa, sekuma taji tausayinsa yaje chan besan kowa ba wayar nata taja ta kirasa yana gani yak’i d’agawa.
   “Toh ko har yayi bacci ne? Barin sake gwadawa inga.” A karo na biyu ne ya d’aga “Anas” ta kira sunansa a hankali, jin shiru tace. “Anas are you there?”
    “Yes” yace chan k’asa k’asa.
“Ka kasa bacci ne?”
   Nama “yes” yace. Shiru tayi tana nazarin me zata ce masa chan tace, “uhm if you need someone to talk to I’m here for you.”
    “Just go, jeki kwanta.”
   “Anas kaifa?”
   “I can’t sleep” yanason yace mata saboda yana missing nata ne ya kasa bacci amman kuma yak’i.
    “I can’t either.” Ta fad’a.
   “Why? Ba bacci kikeyi ba yanzu?”
  “Not anymore, you can’t sleep I’ll stay awake with you.” Dad’i yaji sosai.
   “Are you sure?”
   “Yes” ta fad’a tana giad’a kai.
   “Thank you.”
   “So yaushe zaka dawo?”
   “Maybe in 3-4 days time.”
  “Okay Allah kaimu.”
  “Ameen, so ya Afrah da Shettima?”
  “D’azu ma yazo wajenta, wai dama Shettima na business?”
   “Business kuma wani erin business kenan?” Anas ya tamabaya cike da rashin fahimta.
    “Nima I don’t know haka yace mata wai yana business harda kawo mata bundle na N500 dayazo.”
    “Are you serious?? Lallai ma Shettima, abinda zeyi da kud’in kenan dama. LOL”
   “Kamar ya Anas?”
     Nan ya labarta mata yadda Shettima yasamu kud’in. Dariya sosai dukansu suka b’arke da. Haka sukata hira kamar ba gobe sekace ba Mr. Fauzi ba, sun fi awa suna waya har bacci ya sace Fannah.
Jin shiru ya kira sunanta, shiru bata amsa ba “kinyi bacci ne?” Nanma shiru. “Goodnight” ya fad’a ahankali, k’in kashe wayar yayi yana d’an jin nishin Fannah da haka shima ya samu yayi bacci wayar mak’ale a kunnesa.
 
   *©miemiebee*
TANA TARE DA NI… PAGE 54
BY MIEMIEBEE
    Se Asuba da Fannah ta tashi Sallah ta tuna ashe waya take da Mr. Fauzi bacci yayi gaba da ita. Wayarta dake kwance a gefenta ta d’aga to her suprise taga Anas be kashe wayar ba. “OMG! Whattt!!!” Ta fad’a cike da mamaki, yanzu Mr. Fauzi be kashe wayar ba tun tun tuni? Har zata kashe seta tuna kuma what if be tashi yayi Sallah bafah? Daman ba ma’abocin Sallah akan lokaci bane. “Anas” takira sunansa ta wayar softly. Bacci sosai Anas yake wayar na ajiye kan pillownsa.
     “Anas!” Tasake kira da d’an k’arfi nan ma shiru. “Mr. Fauzi!!” Ta kira da ihu kwanciyansa ya gyara kodaya bud’e ido seya rasa daga ina ake kirar sunansa ko kad’an hankalinsa bekai kan wayar dake kan pillon sa bane.”
    “Mr. Fauzi wake up, wake up kaji? Fannah ce.” Se a yanzu yakai dubansa kan wayarsan yaga Fannah ke magana ba b’ata lokaci ya kai kunne cikin gigin bacci “Fannah” ya kira sunanta.
  “Huh!” Ta saki numfashi. “Good morning.”
   “Morning? Har safiya tayi neh?”
   “Yes Anas and bakayi Sallah ba.” Ze mata k’arya yace yayi sekuma ya fasa instead yace “lokaci beyi ba anan.”
    “Aww haba? Ta fad’i cike da gatsine “dad’in abin lokacin Morocco da Nigeria d’aya suke tafiya nan kuma lokaci yayi kaga chan ma haka kenan.” Kunya yaji sosai Fannah ta kamasa yana k’arya.
    “Toh aini bansani ba.”
   “But now you do tashi kayi Sallah toh.”
   “I’ll bari in 6 yayi I need to sleep a little more.”
   “Anas har 6? Ana sallah 5:10-5:20 kace kai sai 6? Ba kyau jingina Sallah fa. Yi hak’uri ka tashi kaga nima banyi ba semuyi tare kaji Anas?”
   “No se 6 I’m hanging up.”
    “No boyfriend karka katse please, katashi muyi Sallah kaji? Yi hak’uri kaga inka idar se ka koma bacci…” Da k’yar ta samu tayi convincing nasa ya yarda
   ****
   12:30PM su Anas suka k’are first meeting daya kawosu Morocco, da k’yar ya iya yayi breakfast da safe dan yadda yake missing coffeen Fannah. Zaune yake da laptop nasa a gabansa yana ‘yan aiki alokacin da wayarsa ya soma ruri. “Hello” yace bayan ya d’aga “dama nace meetings d’innan bara a iya rescheduling muyi duka a gobe ba? Nagaji da zaman nan, I wanna go back home.”
    Ta wayan akace, “but Sir you just arrived yestarday, nan da 3 days duk komai ze k’are, ka k’ara hak’uri please.”
   “NO!” Ya fad’a a tsawace “hak’uri na ya k’are ni nagaji ko kayi rescheduling a k’are komai a gobe kokuma kuyi meeting naku ba ANAS IBRAHIM FAUZI.”
  “Sir please calm down, naga bawai family kake dashi achan Nigeria ba why in such a haste?”
   “Yes banida family amman inada girlfriend and I’m missing her ni na fad’a maka do what is need to be done.” Karap ya katse wayar. Laptop d’in ya rufe a fusace tare da jingina jikin couch dayake zaune akai. Duk yadda yayi denying he can’t he is missing Fannah, baya missing Amal kamar yadda yake missing Fannah. Number’n ta ya kira.
     Alokacin Fannah na zaune dasu Baba a d’akinsa se hira sukeyi tana ganin number’nsa da tayi saving da Anas ta saci jiki ta nufa d’akinsu bayan ta baje kan gado tayi picking “hello Anas.” muryarta kawai ya jiyo se kawai yaji duk wani b’acin ransa ya gushe.
  “Fannah I’m missing you.” Yace tsakani da Allah ba kunya ba tsoro ba komai, he needs to tell her saboda the more yana keeping secret d’in wa kansa the more yake missing nata a kowani second.
    Gatsau tajiyo abinda ya fad’a matan, kamar ya he is missing her? Ai coffeen ta yake missing a kullum ba ita ba, ta b’angare guda kuwa wani irin feeling da bata tab’a feeling ba taji ya ratsa ta.
   “Fannah are you there?” ya tambaya jin tayi shiru. Nanne ta dawo daga duniyar tunanin data wula.
   “Uhm… Ermm. Yes Sir.”
    “Stop calling me Sir.”
   “I’m sorry Anas ban-” katse ta yayi.
   “Fannah I miss you, I want to come back, I miss everything about you.” Wai meke damun Mr. Fauzi ne? Ta tambayi kanta. Rasa na cewa tayi chan tace, “Anas calm down kaji? Nan da 3 days zaka k’are komai kaga seka dawo, dama zama mutum kad’ai ba dad’i hak’uri zakayi kaji?”
   “But I miss you.”
    “I miss you too Anas hak’uri zakayi kaji boyfriend?” Shiru yayi be amsa ba, “boyfriend?”
   “Yes” ya amsa chan k’asa-k’asa.
    “Kayi hak’uri kaji? What are you doung now?”
    “Nothing, jus sitting alone.”
  “Call up Amal nasan she will have alot to tell you, kaji?”
     “But I don’t want to, ni dake nakeson nayi magana.”
   “Toh nikuma ai bansan me zance maka ba.”
    “Tell me anything.”
   “Anything like?”
   “Your boyfriend.” Shi kansa besan lokacin daya fad’a hakan ba, kawai seyaji yanason yasan ko Fannah nada wani saurayin.
    “Ni banida boyfriend.”
  “Yusuf fah?”
    “Anas Yusuf ba boyfriend d’ina bane kawai good friend ne thats all.”
    “Okay who is your boyfrined yanzu?”
   “Banida boyfriend.” Ta mayar masa da amsar d’azu.
     “What of before?” Ahmad nata ne ya fad’o mata arai, masoyinta na hak’ik’a da aka rabasu na k’arfi da yaji, incident daya faru da ita a Bama na yadda wani azzalimi yayi raping nata ne kawai ya soma dawo mata batasan lokacin da ta fashe da kuka cikin wayar ba.
      A rikice yace, “Omg Fannah why are you crying? Saboda question dana miki neh? I take it back bar kukan kinji?” Hannu tasa ta share hawayenta cikin kuka tace, “no ba kai bane, I’m sorry.”
    “Ex boyfriend nakin ne?”
    Kamar tana gabansa ta girgiza kai. “Shine?” Ya sake tambaya hankali a tashe. “Ba shi bane.”
    “Do you want to talk about it?”
   “No it makes me cry.”
   “Shhh! Is okay bar kukan kinji? We will talk later.” Nan ya katse wayar duk hankalinsa yabi ya tashi, meh yasa Fannah kuka? Meh saurayin nata ya mata da dazaran anyi maganansa take kuka?
    Through out ranan Anas be kira Fannah ba aganinsa karya tak’ura mata, itako har ta saba d’an kwana biyu da suke yin waya, dabe sake kirarta ba setaji wani eri, ita kanta bata san wani erin feeling take ma Anas ba. Tana enjoying every single second da take spending da Anas hakan kuwa na nufin sonsa take kenan. Amman sede tana tsoro, tsoron ta fad’a tarkon son sa wataran gaskia ya bayyana ya guje ta, abinda barata iya jurewa ba kenan sesa take yayyafa wa zuciyarta ruwan sanyi da son Anas.
   ★★★★★
1 day later…  
    Kamar yadda Anas ya buk’ata a washegarin akayi rescheduling masa duka meetings d’in, a ranan yayi attending duka kansa kamar ze fashe gashi rabuwar sa da waya da Fannah tunda da ta fashe masa da kuka a waya shekaran jiya. Yana son kirarta amman bayasan tak’ura mata kuma he is damn missing her.
    Itama Fannah ta b’angarenta haka ne, so take ta kirasa amman kuma tana tsoro kar ya gwale ta yace mata waya rok’eta.
    10:20PM
   Kasa hak’ura tayi ta kira sa, dan hankalinta ya matuk’an tashi seji take kamar ba lafiya ba. Har call d’in ta tsinke Anas be d’aga ba, yana gani amman yak’i picking se a karo na biyu nan ma bece komai ba ita ta soma magana. “Anas.”
    “Yes Fannah.”
    “How are you?”
   Be amsa ba ya tambayeta “how are you too?”
    “Alhamdulillah, just called to check on you, se anjima.”
    “Wait Fannah, I miss you.”
     “I miss you too.” ta fad’a sincerely kamar yadda shima yayi. Hira kad’an suka tab’a sam be fad’a mata gobe ze dawo ba he wants to suprise her.
 
    Washegari da misalin k’arfe 2:00PM jirginsu Anas ya sauk’o a International Airport dake Abuja daga chan yashiga na Maiduguri direct. 2:30PM yamasa agarin Maidugiri, already Shettima da Amal suna jiransa. D’an tafiyan kwana uku yayi amman Amal seji take kamar shekara tayi bataga Ya Anas nata ba, haka kowa ma agidan. Abinci suka gama chi ya shiga d’akinsa dan watsa ruwa, tsatsaf ya sami ko ina har cikin wardrobe nasa yaga an gyara masa, murmushi kawai yayi danko yasan wa yayi hakan, Shettima ne. Bayan yafito yasa baqar ¾ wando da baqar plane T-shirt. Key’n motar sa ya d’auka ya fice.
     Fitowarsa parlour kenan, “Babana daga dawowa se fita kuma?” Cewar Ummie tana taya Amal tsifa.
   “Eh Ummie aiki just came up a office.”
   “Toh Allah kare.” Nan ya fice be zarce ko ina ba se gidansu Fannah. Almajiri ya tura ya mata sallama bada jimawa ba tafito sanye dawani light purple hijabi me hannu kodan ya jima be sata a ido bane seyaga ta k’ara masa kyau dukda ba makeup bane a fuskarta.
   He can’t explain how he missed her, rashin ganinta ya kasance wani babban rashi tattare dashi wanda bare iya bayaninsa ba.
Mamaki sosai tasha ganin Anas, har ma kamar bata yarda ba ko decieving nata idanunta suke ne? Ai ko ajiya da sukayi waya bece mata zezo ba.
      “Senayi magana kice ba kallon soyayya kike minba.” Magnarsa ne ya sake tabbatar mata da eh Anas ne a gabanta a hankali ta tako zuwa gabansa. “Anas! Yaushe kadawo?”
    “Some few hours back.”
  “Welcome back” murfin motar ya bud’e mata “get in I have something to show you” ba gardama tashiga bayan daya zaga ya shiga shima ya ciro wasu files ya mik’a mata bayan data amsa taga heading d’in *CONTRACT MARRIAGE AGREEMENT* rubuce da babban bak’i. A hankali tabi ta soma karanta rules d’in.
    Duka sun mata sede na had’a gadon ne battaso dukda kuwa yasa a k’asa ba abinda ze shiga tsakaninsu amman still tana tsoro, bata son Anas yasan ba virgin ce ita ba. Pen ya mik’a mata “sign them.” Ba gardama tabi su one by one tayi signing bayan da tagama ya amshe “very good I hope my rules are clear? Don’t fall for me, don’t get jealous in kinganni da wata mace.”
      “Ka kwantar da hankalinka nima dan banida wani option ne yazama min dole in yarda da wannan aure if not ba abinda ze had’a mu kwanciya gu d’aya da kai”
   “Allah sa” yace a lokacin da yake miyar da files d’in cikin envelope daya cirosu. “So auren will take place in a month time, you have 4 weeks to prepare.”
    “Wata d’aya?!” ta dafe k’irji tare da zaro ido in disbelief.
   “Yes wata d’aya Miss Aleeyu.”
   “But Sir wata d’aya yayi kusa ina laifi biyu ko uku?”
    “Huh! Look at you nid’in ance miki dan inaso ne? So nake ayi auren muyi mu rabu in huta dake in huta da Abuu. So don’t think othwrwise ki d’auka ko dan inason ganin ki ne always na matso da bikin.”
    Itade har yau barata iya fad’in ga halin Mr. Fauzi ba, in baya kusa da ita ya riga ce mata yayi missing nata ayau suka had’u kuma yasoma gasa mata bak’ar magana.
    “Anas to gidan da kake ginawan fa? Ai ba’a gama ba kaga ba yadda za’ayi ayi bikin nan in a month time.”
     “Nasani saisa zamu zauna a hotel for the meantime, nanda 2 months za’a gama ginin semu tare.” Ita har yanzu hankalinta be d’au wata d’ayan nan ba, haka kawai tasoma jin tsoro.
      “Anas ai bamu keda ikon sa wa bikin date ba, iyayenmu ne ko ba haka ba?”
    “I have money Miss Aleeyu inma a gobe nakeson ayi bikin za’ayi inada komai under control. Bana buk’atar ki saya wani abu, komai ni zanyi just ki sanar da Mami maybe gobe ko jibi Abuu zasu so kinji?” Kamar wacce barata motsa ba ta gyad’a kai.
    “Can I go now?”
   “Yes you can, nima nagaji da ganinki cikin motar.” Bata bar bak’ar kalamunsa suka tab’a taba ta fice. “Fannah I’m sorry for hurting you banasan kigane ko ina sonki ne saboda nima har yau bansan wani erin feeling nake miki ba, a farko nace tausayi ne sekuma naga bakida abinda za’a tausaya miki ayanzu amman kuma har a yau I care about you, I’m afraid I love you amman barin bar wannan love yayi ruining d’ina ba, I will do whatever it takes in kashe ‘yar soyayyar because I’m Anas Ibrahim Fauzi its not in me to fall in love.”
    **
     “Anas, Ummie tace kanason magana dani.” Cewar Abuu dake k’arisowa cikin parlour’n da daga Ummie se Anas ke zaune ciki.
     “Eh Abuu.” Bayan Abuu ya zauna Anas yayi gyaran murya, “Abuu batun matan aurer da kace in nema ne nakeson sanar dakai na samu, ina sonta kuma zan aureta.”
   “Alhamdulillah! Alhamdulillah! Sede wace yarinyan? ‘yar wace gida ce?”
  “Ba ‘yar kowa bace Abuu, Fannah PA ta ce, tanada diploma a Business Admin am very sure she’ll bring a great contribution to my Enterprise bayan ta zamo mata ta saboda ko a yanzu with her beside me nayi achievibg abubuwa da dama.” Kai Abuu ke gyad’awa nufin he is convinced, ya yarda.
    “Toh Masha Allah Anas a gaskia ina me matuk’ar farin ciki da Allah yabani d’a me hankali kamar ka, Allah saka maka da alkhairi Babana. Ita kuma Fannah ko?” Kai Anas ya giad’a Abuu yacigaba “zanso kamin kwatancen gidansu sabida inje inji kuma ingani ko d’iya ce me tarbiyya.”
   “Ba matsala Abuu first thing gobe zan kaika har gaban mahaifinta.”
   “Toh toh masha Allah sannu ko Babana?”
    “Yawwa Abuu one last thing please.”
“Mene ne Baban tell me.”
   “Abuu inda hali banasan bikin auren ya wuce nan da wata d’aya, inason Fannah Abuu I can’t wait har zuwa nanda wani dogon lokaci bata kasance mata taba, if possible nan da one month ayi komi ya k’are.”
    “Wannan ai ba matsala bace Babana kaida kake da kud’i a hannu. Addu’armu de kawai Allah sa muji sheda mekyau a gareta goben, yaso ko a jibi a muku aure in iyayenta suka amince.”
   “In shaa Allah ma zasu amince Abuu nide kawai kar ya wuce nan da wata d’aya.”
   “Allah kaimun toh.” Nan duk suka amsa da “Ameen” sannan Anas yayi d’akinsa. A hankali ya bud’e k’ofar kamar ko yasan Shettima na ciki.
     “Aww ashe kaine b’arawon. Oya miyar! Miyar nace!”
   Shettima dake zaro bundle na d’ari bibbiyu daga safe na Anas ya tsule besan lokacin da ya zubar da kud’in daya kwasan duka a k’asa ba.
     “Wayyo! Ya Anas ka tsoratani wallahi.”
   “Naji miyar b’arawo kawai. Ashe kaine, tun dawowa na naga kud’in safe d’innan ya ragu ashe kaine b’arawon ka gama min sata kaje ka samu Afrah kace mata kana business koh? Toh k’aryanka ya k’are yau.”
    “Ya Anas fa basata nake maka ba, arranging kud’ad’d’den nake.”
  “Ka rantse” Anas ya katse sa shiru Shettima yayi yakasa rantsuwar. “Oya ina ganinka one by one mayar min da kud’i na.”
   “Ya Anas mana dan Allah ko guda biyu ne kabani please wallahi na mata alk’warari kaji dan Allah.”
    “Seka karya, nide miyar min kud’ina dan tsiya duk wanda ka riga d’iba basu isheka ba? Mayar min ka fice kuma.” Kamar wanda zeyi kuka yasoma miyarwa ganin idan Anas bai kansa ya zira d’aya cikin aljihu ai kuwa Anas ya gansa ta gefen ido. “Miyar fa na riga na ganka b’arawo kawai, kai barakayi karatu ba se soyayya da sata ka iya.”
     “Ya Anas d’aya fa dan Allah” ya maraice fuska.
  “D’auka ka bani waje.”
   “Yeyy! Nagode sosai Allah bar mana kai.”
   Washehari da misalin k’arfe 11:00AM Anas yasa Abuu dawasu uncles nasa guda uku cikin mota se unguwar su Fannah kafin su shiga gidansu Fannah seda sukayi tambaya gidan mak’ota kusan biyar kan halayen Fannah sede kowa shaida me kyau yake bata yana yaba hankalinta kuma. Dad’i sosai Abuu yaji daga nan suka shiga gidansu Fannah banda Anas. Maganar awa d’aya da mintuna aka sukayi aka yanke hukuncin date na bikin Anas da Fannah a wata d’ayan da Anas ya buk’ata, Abuu ya d’au nauyin yin komai, ko tsinke be yarda Fannah ta kai gidan mijinta ba saboda yadda ya karanchi basuda arziki. Shopping da Anas ya musu Abuu yasa almajirai suka shigo dasu. Inbanda godiya ba abinda Baba da Mami keyi. Afrah kam bakin nan har kunne Fannah zatayi aure, zata auri Nigerian’s youngest billonaire tasan dole suhau gidan TV suma.
   Fannah de ta rasa me ke mata dad’i, wani tsoron Anas da bata tab’a ji ba ta soma ji yanzu. Taya zata auri Boss nata? Taya zasu kwanta gado d’aya da Anas su zau
Wani irin tausayin daya jima be mata irinsa ba ya soma jimata yau, azabarcaccen kuka take na hak’ik’a daga ya gwada tab’a koda hannunta ne sekuma ta tsala ihu tana had’asa da Allah. Toh wannan wace erin mafarki ne? Ya tambayi kansa. Kasancewar akoi d’an haske d’akin be damu ya kunna wuta ba, wajen dispenser ya nufa ya tsiyayo mata ruwa a cup cike da tashin hankali. “Fannah gashi sha kinji?” Ko kallonsa batai ba se b’ari da take tana hawaye, “Fannah mafarki ne bawani mutumi anan kinji? Sha ruwan ki koma bacci.” Hannunsa daya aza kan bayan ta taja jikin nata baya da wuri. “Dan Allah kayi hak’uri Mami please kizo wallahi gashi nan.” Cup d’in ya ajiye bisa side drawer tare da finciko ta da hannu seda ta fad’a a jikinsa, gagam ya matse ta a jikinsa me k’amshin bala’i dakuma d’umi, ta hanyan hugging nata. Ihu ta saki sosai tana b’ari a yayinda kukanta ya tsananta sekuma had’a sa da Allah da take tana k’ok’arin k’watan kanta amman sam ta kasa. “Dan Allah kayi hak’uri ka sakeni, kar ka k’ara dan Allah…”
“Shhh! Fannah is okay, stop crying kinji? Bawani mutum anan Anas ne kawai, stop fighting it keep calm, I’m here for you bar kuka kinji?” Anas ya sanar da ita cikin wani irin salon da be tab’a using ba, hab’ansa na akan kanta. A hankali ta dena fad’an da takeyi na k’watan kantan sede kukan da take har yanzu bata bari ba.
“Is okay kinji? Mafarki ne, I’m here, bar kukan.” Hijabin ta daya jik’e jak’af da gumi yayi yunk’urin cire mata wata ihun tasake tsalawa.
“Fannah ba abinda zan miki you are sweating, duk kin jik’e tsaya in cire miki hijabin kinji?”
“No banaso dan Allah kayi hak’uri, karka k’ara.”
“Ba abinda zan k’ara kawai cire miki zanyi, you’re sweating.” Sam tak’i yarda yacire mata shiko ya dage seya cire saboda irin zufan datake ta had’awa duk wuyan hijabin nata ya jik’e. Da k’ak’ani k’ak’a yasamu ya cire mata hijabin tana manne a jikinsa har yanzu. Sunyi kusan minti goma a haka se daddad’un kalamu yake fad’a mata yana shafa bayanta a hankali, hankalinta yana kwanciya, nan ne tasamu tabar kukan sede numfashinta be dawo saiti ba har yanzu. Bacci sosai Anas yakeji, “Fannah” ya kira sunanta a nitse. Cike da tsoro ta amsa kanta manne a k’irjinsa. “Uhmm” tace.
“Ba wani mutumi mafarki ne ba?” Ya tambayeta.
Kai ta giad’a a hankali.
“Good toh lets go back to sleep, nasan kema kinajin bacci.” Hannunsa daya zagaya a bayanta ya zaro wani tsoro taji ya sake ratsa ta atake batasan lokacin da ta zagaya hannayenta bibbiyu a jikinsa ba gagam ta matsesa not letting go. Wani erin sparks Anas yajiyo within him.
“Dan Allah kar ka tafi wallahi mutumin ze dawo.”
“Fannah I’m here bare dawo ba, ba tafiya zan ba kinga ina chan, ba mutumin da zezo kinji?”
Kai ta girgiza “please kar ka tafi wallahi zezo.”
“Fannah we need to sleep, bacci nakeji.”
“Anas please…” Ta rok’esa cikin sautin kuka.
“Okay okay naji barin tafi ba amman lets sleep kinji? Barin d’auko pillow na se mu kwanta.” Nanma kai ta girgiza da k’yar ta sakesa ya d’auko pillow ahakan ma binsa take hannunta nannad’e cikin nasa. Bayan ya ajiye pillow’nsa kan gadon yace, “oya hau ki kwanta.”
“Ina jin tsoro.”
“Fannah I’m here.” Ture pillows datayi katanga dasu a jiya yayi a k’asa sannan ya kwanta tana tsaye a kansa se b’ari take. Hannunsa ya bud’e mata “come here.” Ba musu bale gardama ta haura kan gadon itama, hannunta yaja a hankali ta fad’a kan k’irjinsa, kanta ta daidata ta kwanta comfortably a jikinsa, da rabin jikinta akan nasa se b’arin take har yanzu. A nitse ya zagaya hannunsa a bayanta yana shafawa a hankali.
“Yi bacci kinji ba mutumin daze zo.” Kai ta gyad’a a hankali tare da yab’a hannunta kan cikinsa ta zagayesa gagam. Ganin bata bar had’a gumi ba har yanzu ya d’an k’ara k’arfin AC’n. A hankali bacci me uban nauyi yayi gaba da Fannah, jin nauyinta a jikinsa ya k’aru ya tabbata tayi bacci. Cike da dabara ya gwada mai da ita wajen kwanciyarta sede anytime ya gwada motsi seta sake matsesa a jikinta. Sau biyu ya gwada janta daga jikinsa amman tak’i sakesa agarin haka ya since mata ribbon. Uban gashinta ya bayyano kamar wadda zeyi kuka ya gwada packing mata gashin amman ya kasa gashi anytime ya gwada janta daga jikinsa seta sake matsesa.
Ahaka shima wahalellen bacci yayi gaba dashi da gashin Fannah duk yabi ya cika masa fuska.
Asuban fari Fannah ta tashi a hankali ta soma bud’e idanunta har ta bud’e duka ganinta tayi kwance jikin na miji da hannunta zagaye kan cikinsa ihu tayi niyan sakarwa sewani abu ya dakatar da ita. Hannun nata taja daga kan cikinsa da wuri tana d’ago kanta taga Anas ne, meh hakan? Meya kawosa kan gadon? Me takeyi a jikinsa? Bata gama nemo amsoshin tambayoyin nan ba ta tab’a jikinta taji ba hijabinta me zata gani? Gashinta baje a fuskarta da jikinta gabad’aya. Ihun da tayi niyan yi d’azu ta bud’e baki zatayi yanzu, chak tunanin mafarkin da tayi ya fad’o mata akai ya dakatar da ita.
Se a yanzu take tuna duk wani abinda ya faru a daren. Kunya taji sosai inta tuna Anas ya ganta da ‘yar kayan dake jikinta dakuma yadda ta riga matsesa a jikinta jiya. Ribbon nata ta lalimo a garin haka ta farkar da Anas tun idanun nasa suna kafewa har ya bud’e su gabad’aya. Idanunsu na had’uwa tayi saurin kawar da kanta bedsheet ta soma ja tana kare k’irjinta. K’aramar tsuka yaja tare da juya mata baya dan cigaba da baccinsa. Ribbon natan take k’ok’arin miyarwa amman takasa batada ma k’arfin kamawa batasan lokacin da tasaki wani wahalallen k’ara ba take Anas ya juyo yakusan minti yana kallonta tayi nan tayi chan amman takasa kama gashin ya tashi ya zauna. Hannu ya mik’a mata da nufin bani. Itako sam bata gane meyake nufi ba. Hannu kawai yasa ya amshi ribbon d’in daga hannunta cike da tsoro ta gwada matsawa baya ayayinda yajawota ta fad’a jikinsa. Uban gashin nata ya soma packing nasu gu d’aya a yayinda take k’ok’arin fisgo jikinta. “Stop it Fannah” yayi warning nata. Ba tare da b’ata lokaci ba ya kama mata gashin a daidai tsakiyar kanta yabar jelan na yawo. Bayan ta d’ago daga jikinsa ta tuttusa jelar ta nannad’e waje d’aya. “Thank you” ta fad’a masa kanta sunkuye.
Bece mata komai ba illa observing nata da yake, nan ya gane hijabinta take nema hannu ya mik’a ya d’ago a k’asa tare da mik’a mata. Hannu tasa ta amsa da wuri ta miyar jikinta sannan ta mik’e tashiga bayi, bayan tafito tayi kan Anas taga har ya koma bacci.
“Anas” takira sunansa a hankali. Idanunsa kawai ya bud’e be amsa taba.
“Asuba tayi ka tashi kayi muyi Sallah.” Bayan daya gama sauraronta seya sake rufe idanun nasa ba tare da ya amsata ba. “Anas kaji?” Ta fad’i.
“Naaji!” Ya fad’a a d’an fusace. Mik’ewa yayi daga kan gadon daga shi se nickers nasa, k’are wa jikinsa kallo tayi nan ‘yan seconds sannan tayi saurin kawar da kanta. Ko ta kanta beyi ba ya nufa bathroom kafin yafito ta shimfid’a musu dadduma tana zaman jirar fitowarsa.
Bayan ya fito ya zaro wata milk jallabiyansa sabo pil ya zira sannan ya nufa inda tayi musu shimfid’an, ganin ze fara sallan ba ita takira sunansa. “Anas.”
“Meh?” Ya amsata a fusace.
“Ba tare zamuyi sallan ba?”
“Kowa yayi nasa” ya amsa ta a takaice.
“Anas but Sallar jam’i yafi lada.”
“Da a gida keda su wa kikeyi?”
“Dasu Afrah.”
“Naji lets pray then.”
“Uhm amman se munyi Rakatainul~fajir ba?” Ta sanar dashi kanta a sunkuye.
Raka… Rakatainul~fajir? ya nanata a zuciyarsa. “Me kuma rakatainul~fajir?” Ya tambayeta a fili.
“Raka’a biyun da akeyi gabanin k’etowar al~fijr.”
“Ohhh! Fannah!” Ya fad’a rai ad’an bace tare da sa hannu cikin gashinsa yana hargitsawa. “Ke komai ne sekin had’a masa concussion? Sallan Asuba ma se anyi rakatainul~fajir ne ko meh?”
“Anas hadisi ne fa ingancecce, yin nafilar yafi duniya da kanta dakuma duk wani abinda ke cikinta”
“Toh naji raka’a nawa ne?”
“Biyu ne kacal, a first raka’ah suratul~kafirun na biyu kuma ikhlas.” Kai kawai ya giad’a mata yajasu. Ita Fannah bata zata ma Anas ya iya Sallah kamar yadda yajasu ba, ta d’au ko sallan ma seta koya masa. Bayan sun sallamesa yajasu Sallar Asuban, duk wani k’aidojin karatu taji yana karewa, duk wani hukunce hukunce yana biya, a takaice sautin k’ira’ar sa ya burgeta ba kad’an ba saboda yadda yake da zak’in murya, sosai yayi impressing nata ashede ba jahili ta aura ba.
Bayan sun sallame ya mik’e ze koma ya kwanta.
“Anas” ta dakatar dashi da wuri.
“What now Fannah? I want to sleep please.”
“Babu kawai so nake na fad’a maka qira’arka tamin dad’i.”
“Naji” yace sama sama yana k’ok’arin cire jallabiyar. Chan k’asa k’asa tace, “aini ban zata ka iya karatu bama.” Sekuwa yaji ta.
“Kafiri ne ni ai dole kice baki zata na iya karatu ba. Toh in baki sani ba barin sanar dake yau cikin izu sittin na Qur’ani nayi talatin da biyu, kin gane? Ba jahili ne niba.”
Mamaki sosai tajiyo, 32? Ta nanata a ranta. Amman shine bai aiki da ilimin Qur’anin nasa? Kuma besan hukunce hukunce ba a addinin muslinci.
“Anas amman shine baka aiki da ilimin naka?”
“Me ruwanki? My life is not your business, kuma ai ba ce miki nayi islamiyya nayi attending ba hadda ne, zallan Qur’ani da tajweed kawai akeyi sesa kiga ga bansan sauran religious stuffs d’innan ba time daya kamata nashiga islamiya nak’i ban shiga ba.” Sekuma yayi shiru “why am I even explaining these to you? Kin ga dama kice ban san komai ba game da addini keda kika sani sekita bragging dashi be damen ba kuma bare damen ba, allow me to sleep now, will you?”
“Anas I’m sorry ba abinda nake nufi ba kenan also in aka idar da Sallan Asuba dama kowani Sallan ba direct akeson mutum ya tashi ba. Akwai morning azkar da akeyi wanda yake da falala sosai shima.”
“Ohhhh!” Ya sa hannu cikin gashinsa a fusace yana hargitsawa. “Fannah please, please nace nan ba islamiyya bane kince inyi rakatainul~fajr nayi be isheki ba yanzu kuma azkhar kikeson sani yi? for goodness sake jiya bansamu nayi bacci ba, wannan mafarkin da kikayi duk ya bi ya tadda min hankali, haka kika hana ni bacci yanzu kuma dayakamata in kwanta shina kice barin yi ba?” Ya tambayeta a tsawace. Bata san lokacinda ta soma hawaye ba.
“I’m sorry, Allah baka hak’uri.” Ta fad’a tana tare hawayenta. Kallonta yayi na ‘yan seconds tare da kawar dakansa, nan yacire jallabiyan ya haura kan gado. Sautin kukan tane ya hanasa sukuni, ya d’au pillow ya rufe kunnuwasa amman still yakasa bacci gashi kuma ita tak’i yin shiru besan ina ze kaita ba. Mutum da an masa magana se kuka sekace ‘yar yarinya. Ganin ba ubangiji se Allah ya taso daga kan gadon tare da zura jallabiyar sa, gabanta ya tako ahankali ya zauna tana azhkar nata da hisnul muslim nata ahannu tana kuka a hankali ko d’aga kai ta kallesa batai ba. Zama yayi a gefenta yana fuskantar ta.
Littafin ya k’wace nan ne ta d’ago idanunta da suka soma canza launi. ‘I’m sorry’ yakeson fad’a mata but he can’t saboda girman kai instead yace, “they came out wrong, I don’t mean any of those words, kinji? Stop crying.” Yi tayi kamar bata ji sa ba “kabani littafi na” tace ba tare da ta d’aga ido ta kallesa ba. Shi mesa baya cewa sorry? Ita abu kad’an tayi masa zata ce sorry amman shi sede yace they came out wrong.
“I said they came out wrong, ba haka naso su fito ba ko bakiji ba?”
“Naji kabani littafi na toh.”
“No zanyi Azkhar d’in.” Batasan lokacin da fuskarta ta sake ba, “zakayi?” ta tambayesa cike da jin dad’i.
“Yes zanyi, show me the page.” Nan ya mi’ka mata bayan ta bud’e masa daga farin ta nunnuna masa. Kai ya gyad’a tare da amsa ya somayi. Kallonsa ta tsaya yi, ba k’aramin dad’i taji ba, a rayuwa batada burin da yafi ta shiryar da Anas, kuma alhamdulillah a hankali yana shiryuwan. Ya d’anyi nisa seya dakata tare da d’ago kansa nanne ya kama Fannah na kallonsa. ‘yar murmushi ya saki. “Kefa bara kiyi ba? Gashi gama seki bani, I’ll wait for you.”
“No karka damu na iya a ka zanyi just use it.” Kai ya giad’a mata tare da mayar da hankalinsa kan littafin. Koda ta gama nata bata tashi ba seda ta jira ya gama shima sannan suka tashi atare. Jallabiyar yakuma cirewa ya haura kan gadon. So take tace masa ya koma wajen sa na jiya sede kuma ta tuna batada iko. D’ayan b’angaren ta nufa ta d’an ajiye pillows uku a tsakaninsu sa’annan ta kwanta itama daga chan nesa nesa.
A hankali ya juyo yaga tana fuskantar d’ayan gefen ga kuma jera pillows d’in data sake a tsakaninsu. Kai kawai ya kad’a. “Da hijabin zaki kwanta?” Ya tambayeta.
“Eh” ta basa amsa.
“Yayi kyau.” Ahaka duk suka koma bacci ba su suka tashi ba se chan k’arfe 11:30AM nanma Anas ne ya tashi, idanunsa basu sauk’a a ko ina ba se akan kyakkyawar fuskar Fannah, tad’an gangaro kad’an zuwa wajen data yi katanga tsakaninsun. Wayarsa ya d’ago ya soma d’aukanta hoto yayi kusan guda ishirin yaga ta motsa k’afa da wuri wuri ya miyar ya cigaba da kallon ta. A lokaci d’aya kawai ta bud’e ido se karo taci dana Anas a kanta kunya yaji sosai a lokacin da ta tare fuskar tata da hijabi. Se k’arya ya mata wai; “ace warki kallon ki nake ne? Wannan uban minsharin da kiken ne ya tadani in the first place.”
Fuskarta cikin hijabin tace, “ni bana minshari.”
“Nikuma ba k’arya nake ba” yana kaiwa nan ya mik’e, towel da jakar wankansa ya ciro ya nufa toilet. Se ayanzu ta fiddo fuskar ta. Wajen akwatinta ta nufa ta ciro jakar wankanta da towel nata itama, takaici tajiyo data ga ‘yar tsawon towel d’in, ko gama kai tsakiyar cinyarta beyi ba, se yanzu ma take dana sanin d’auko towel nata na gida wanda yakai kusan guiwarta.
Wayarta ta ciro takira gida suka gaisa da kowa da kowa se tsiya Afrah kemata amarya ansha amarchi, ya first night. Tsuka taja tare da kaste wayar. Bada dad’ewa ba Anas yafito tunda Fannah ta kafa idanunta akansa ta kasa d’aga wa. Ya d’aura towel d’in daidai iya V line na k’asansa, packs nasa da suke nan ‘yan daidai suka sake bayyana. Wani k’aramin towel ne kuma rataye a wuyarsa wanda da d’ayan jelar yake goge gashin kansa daya jik’e jak’af yana sheqi. Wani haske skin nasa ya k’ara da d’igo d’igon ruwa kwance akai. Gashin jikinsa duk sun kwanta luf-luf, da fuskarsa ya bayyana kuwa, ruwa ke d’iga daga tip na hancinsa. “Kallon ya isa.” Yace da ita wani irin kunya taji kamar ta nitse k’asa wato tun d’azu ya karanchi kallonsa take kenan. Ya Salam!! Tace a ranta.
“I get it I’m your husband you can stare at me amman banda irin kallon nan yayi yawa.” Fuskarta kawai ta rufe da hijabinta ta bi ta gefensa ta shiga bathroom d’in. Nan da nan ya shirya cikin sirinsa na safiya akullum ¾ wando da vest, gashin kansa yayi styling mekyau ya feffeshe da designer turarukansa tare da sa Bouzet agogonsa ya dake kan gado yana ‘yan latse latse a laptop nasa.
“Ya Salam!” Fannah tasaki k’ara a cikin bayin kasancewar hijabinta daya fad’a tsundum cikin bathtub, kafin tace zata cire yariga yasha ruwa ya jik’e liqis. Kuka ne kawai batayi ba yanzu ya zatayi tafita da wannan gajeren towel dake jikin tan? Matsewa tatayi amman ina its not at all helping, tasa a haka kuma tana tsoron pneumonia nata karya tashi dan ba wai magani tasha ya mutu ba gabad’aya. Ganin ba ubangiji se Allah ta shanya hijabin a bayin, d’ayan k’aramin towel d’in ta d’aura a gashinta data wanke. Ta iso bakin k’ofar ta sake kallon jikinta kai bara ta iya fita haka ba gaban Anas, tsirecin yayi yawa ta baya kam ma inta tsuguna za’a iya ganinta. “Anas” ta kira sunansa daga cikin bayin ta yadda ze iya ji inhar yana cikin d’akin.
Juyowa yayi yana kallon k’ofar. Me kuma takeso yanzu? Ya tambayi kansa. K’in amsawa yayi.
“Anas are you there?” Nanma shiru yayi. Hamdala ta saki a ranta shikenan bayya ma d’akin barinyi sauri inje in zaro wani hijabin insa kafin ya dawo.
Karap ta bud’e k’ofar tare da rufewa tana juyowa kawai taga Anas mik’e kan gado, mutuwar tsaye tayi a wajen…
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 57
BY MIEMIEBEE
Kallonta Anas yake wane ze had’iyeta, ko kyafta ido ya kasa, numfashinsa ma gabad’ai yankewa yayi, in ya d’auka daga k’afafunta seya kai kanta ya tsaya sannan ya sake d’aukowa daga k’afafun nata. Yasha kallon mata kan bikini(pant da bra) amman ba wacce ta tab’a birkita masa lisafi kamar Fannah, she is just different in her own ways. Itako kasa koda motsi tayi she still can’t believe Anas ya ganta da towel. Idanunsu na had’uwa ta yi saurin sunkuyar da kanta a yayinda Anas ya soma faking tarin tsiya shi a dole wai ya shak’e ganin ta ba kaya disgusts him. Alokaci guda kuwa hankalinta ya dawo jikinta k’ofar ta soma jijjigawa ta baya tana k’ok’arin bud’ewa amman ta kasa dan yadda ta rikice.
Idanunsa da ya kawar ya sake maido su kan ta a lokacin da take k’ok’arin bud’e k’ofar da sauri ta juya masa bayanta, data murd’a handle na k’ofar da k’arfi kuwa se ya bud’u. Kansa ya girgiza dan kawar da image na Fannah da towel daga k’wak’walwarsa.
Wani takaici taji ya rufeta data sake kallon jikinta. K’ofar ta sake bud’ewa kad’an ta lek’a, k’afafunsa ta hango yana nan kan gadon har yanzu. Tunanin ya zata d’auko hijabinta take ganin batada wata mafitan dayafi ta kira Anas ta rok’esa kawai ta rufe ido ta kira san. “Ermm Anas.” Yana jinta yayi shiru har yanzu se yawo hotunan ta da towel yake masa akai.
“Anas please nasan kana jina.”
“Meh?” Ya tambaya a fusace.
“Please hijabi na zaka ciro min cikin medium size akwati na maroon d’in.”
Idanunsa ya miyar kan maroon akwatin nata sannan yace, “barin iya ba.”
“Anas dan Allah kayi hak’uri please.”
“Kifito ki d’auka da kanki.”
“Anas banida kaya a jikina shiyasa please kayi hak’uri.”
“Toh aini ba kallonki zanba.”
“Nasani kawai ka taimaka please.” Kamar wanda bare tashi ba ya mik’e akwatin nata yaja ya bud’e to his suprise yaga na inner wears nata ne, ba komai banda bras da panties ciki. Daidai nan Fannah ta tuna ashe inner wears nata ke ciki, a red d’inne hijabanta ke ciki.
“Anas hold on please kar ka bud’e bashi bane.” Inaaa aikin gama ya riga ya gama. Ko sauraranta beyi ba seda ya k’are wa inner wears natan kallo sannan yace, “nafasa kifito ki d’auka da kanki.”
“Anas I’m sorry dan Allah cikin jan ne yana nan a gefe, please kaji?” Banza da ita yayi se chan daya ga dama ya bud’o jan ya ciro mata d’aya daga cikin hijaban nata. “Fito ki amsa gashi.”
“Anas na d’au zaka kawo min ne fah.”
“Cemin kikayi in ciro miki ba inkai miki ba, so kizo ki karb’a.”
“Hausan nawa ne baka gane ba, ka mik’o min please.” Seda ya gama wasting mata lokaci sannan ya nufa wajen bathroom d’in tare da mik’a mata be jira ta gama karb’ewa ba ya sake k’iris ya rage ya fad’i a k’asa. “Thank you” tace masa a yayinda yayi banza da ita bayan tasa hijabin tafito kanta a sunkuye, akwatin inner wears natan taga a bud’e ga bressiers nata duk a k’asa duk Anas yayi watsi dasu. Shima kallon bressiers natan yake atare suka d’ago ido suna kallon juna cike da kunya ta kawar da kanta, a kunyace ta tsuguna tasoma tattara abinta duk inda ta nufa Anas na binta da kallo. Se guna guni take “kawai da ancewa mutum ya taimako da hijabi seya hargitsa wa mutum kaya.”
“An hargitsan nan gaba seki na shiga da hijabinki in bakison ana ganin jikinki.” Shiru tayi batace masa komai ba, bayan ta gama had’a kayakin nata ta rufe, man shafawanta ta ciro tunanin ya zata shafa take chan ta juya taga Anas na kallonta mik’ewa tayi da nufin shiga bathroom ta yafe zataje ta shafa man acan. K’aramar tsuka yaja, “dawo ki shafa manki, I’m not interested in looking at your body.” Yana kaiwa nan ya tattara wayoyinsa ya fice ko ina zeje se Allah.
“Tafi nono fari” tace chan k’asa k’asa yadda bare jita ba. Bayansa tabi ta sa lock a k’ofar, nan ta cire hijabin nata cikin kwanciyan hankali ta shafa manta ta bud’o akwatin kayakinta takaici ne ya rufeta kap ba atamfa english wears ne zalla ciki. “Afrah wallahi zan sab’a miki, seda nace miki karkisa min english wears ciki. Mschww!”
Haka ba yadda ta iya ta ciro wani red highwaist skirt da white blouse had’ad’d’e ta ajiye a gefe, bayan tasa inner wears nata ta jawo skirt d’in bata gama sawa ba Anas ya murd’a hannunn k’ofar, jin a rufe ya fusata. “Fannah me na rufe ni a waje? Daga baki privacy seki kama kiyi locking d’akin?”
“Toh ai na d’au ko fita zakayi.”
“Toh ba fitan nayi ba, open the door.”
“Barin sa kaya.”
“Wai me zan kalla a jikinki? Open it.” A ranta tace ai wallahi sena gama sa kayan zan bud’e hakan kuwa tayi ignoring nasa seda ta gama sa kayan nata ta bud’e masa. Masifeta yayi niyan yi amman ganin yadda kayan jikinta ya mugun mata kyai seya fasa, yaji bayason sata kuka. Matsa masa tayi ya wuce ba tare da yace mata komai ba. Wajen kayakinta ta nufa ta since towel dake kantan a hankali take taje kanta har tagama da k’yar anzo wajen tayi tayi ta kama ta kasa koda ta kama se ya sake fita. Kamar wacce zatayi kuka ta juyo tana kallon Anas, kallon nata yake shima ganin ta juyo yayi saurin maida kallonsa kan wayarsa.
A hankali ta tako zuwa gabansa ta tsaya “Anas help me pack my hair please.” Banza yayi da ita “kaji Anas please?” Nanne ya d’ago blue eyes nasa yana kallonta, irin kallon data tsana kenan, kanta ta sunkuyar chan ta d’ago ta ga still kallonta Anas yake ko kunya ya kawar da kansa ma be ba. “Anas kabar kallo na haka mana, in ni ke kallonka seka ce na fiye kallo dayawa, nima banason kallon ya isa please ka kama min. Kaji?” Nanma bece mata komai ba. Ganin baida niyyan kama mata ta juya zata tafi hannunta yajawo seda ta fad’o jikinsa nauyinta kan cinyarsa, hannunta ta zagaya a wuyansa dan balancing kanta. K’ara ta saki take ya aza hannunsa kan lips nata “shhh!” Shirun tayi kum. Kallon cikin idanun juna suke na kusan minti biyu sannan ta d’aga kanta daga jikinsa, murmushi ya saki ta gefe d’aya saboda yasan yadda d’an wannan abu yayi affecting Fannah. Hannunta ya rik’i kafin ta fice, “tsaya mana ko bakiya so in kama miki gashin ne?”
“Banaso I’ll manage sakemin hannu Mr. Fauzi.” K’in sake mata hannun yayi, wayansa ya ajiye tare da mik’ewa. Hannunta me ribbon d’in ya kama shima tare da zare ribbon d’in. Fannah kad’ai tasan irin shock da takeji, akoda yaushe Anas ya tab’a ta wani erin electrification takeji a ajikinta wanda battaso. A hankali ya sake duka hannun nata ya soma packing gashin natan, a hankali har ya kama waje guda. Hannunta tasa zata tattare jelar a yayinda ya kama hannun nata “kibarshi haka kinfi kyau.”
“But An-“
“Lets not argue haka yafi kyau, karki tab’a kinji?”
Kai kawai ta gyad’a masa tareda k’watan hannunta a hankali, binta da kallo yake har ta nufa wajen kujera ta zauna jin idanunsa akanta tak’i d’aga kanta. Chan da zaman shirun ya isheta tace, “Anas ba breakfast ne?”
“Jiya danace kici abinci me kika cemin? you are not hungry koba haka ba? Ba bareakfast ’cause bana jin yunwa ni se lunch.” Fuska ta maraice “Anas yunwa nakeji.”
“Kijira zuwa anjima se muci lunch.” Bata sake ce masa komai ba ta mik’e kan 3 seater’n tare da juya masa baya. Yunwa sosai takeji har wani kuka cikinta yakeyi. Knocking akayi bisa k’ofar nasu nan ya mik’e abincinsu aka kawo musu bayan ya amsa ya ajiye kan table d’in har ayanzu Fannah batasan meke faruwa ba. Plate natan ya b’oye k’ark’ashin gado. Yana bud’e nasan k’amshin sardine sauce da chips d’in ya cika d’akin, Fannah bata san lokacin da ta juyo tana kallon sa ba, har d’igan miyau takeyi gawani kukan da cikinta keyi. Seda ya tabbata tana ganinsa yakai spoon d’aya baki se exxagerating dad’in abincin yake.
“Anas ni banda ni ne? Ina nawa?”
“Babu” yabata takaicaccen amsa.
“Kamar ya babu?”
“Jiya danace kici abinci ba k’in ci kikayi ba?”
“Anas ba ya wuce ba? Nan gaba barin sake ba, please ina plate d’ina?”
“You promise? Nan gaba nace kici abinci zakici?” Kai ta gyad’a a hankali. “Good” hannu yasa k’ark’ashin gadon yaciro mata plate natan. “Come over lets eat.” Ba musu ta tashi taje ta samesa bayan ya mik’a mata plate natan ta zauna gefe dashi ahaka suka samu sukayi breakfast nasu.
Kallonta yake yadda take ta cin abincin ba makawa gaskia yunwa yacita da yawa, bayan da ta gama ya tambayeta “a k’ara miki?” Kai ta gyad’a a hankali plate nasa ya mik’a mata. “Kaifa ka k’oshi?” Kai ya gyad’a mata nan da nan ta d’ura nasan cikinta se ayanzu ta jita dam. Lokacin Sallah ya riga yayi nan ta fad’a bayi tayi alwala shima haka sannan ya jasu Sallah bayan da suka idar ya sake feshe jikinsa da turare binsa kawai take da kallo seda yazo fita takira sunansa ganin baida niyyan fad’a mata inda zasa.
“Anas.” Chak ya tsaya “wani abu ne?” Ya tambayeta bayan ya bud’e k’ofar. “Nace ina zakaje?”
“Toh wifey kishi ne ya motsa?”
“Nifa ba kishin ka nake ba.”
“Toh why asking? Ka
I thought ko zaka sauk’eni a gida ne.
Kin tab’a ganin inda amarya ta fita?
Anas zaman nan d’in ba dad’i.
Wani murmushin tsiya ya saki, just say it you are gonna miss me, karki damu I won’t take long yanzu zan dawo. Bejira jin me zatace ba ya rufe k’ofar. ‘Yar tsukar ta taja tare da hayewa kan gadon, game na candy crush ta hau yi batans seda bacci yayi gaba da ita ba.
40 minutes later…
A nitsr ya bud’e k’ofar kamar ko yasan tana bacci. Ledar chocolates da ice cream daya siyo musu ya bud’e fridge yasa ciki sannan ya nufa kan gadon inda take kwance bayan ya zauna gefenta ya zura mata ido. wayarta dake kwance a gefenta ya zaro yayi quitting game d’in. Hannu yasa a fuskarta a hankali ta yadda bare farkar da ita ba, gashin dake kwance kai ya d’ad’d’aga sannan ya jawo bargo ya rufeta.
**
Seda La’asar ya tada ta suka idar da Sallah tare da musu ordering abinci, suna cikun ci aka yi knocking get it yache mata ba musu ta mik’e ta bud’e kad’an daga photo album na bikinsu ne. Bayan ta amsa ta masa godiya. Mugani Anas yace.
Nima ingani mana.
I’m your husband yiu follow my instructions so bani. Kallo ta galla masa awww ni kike harara?
Bafa harararka nake ba. Nan ta mik’a masa. Na english dinner’n su ya bud’e wow! Tace cike sa jin dad’i ganin yadda tayi kyau a hoton.
Wow me or you?
Ni mana, ni ba kai nake kallo ba.
Da banga idanunki kan fuska na bane seki fad’a min maganan banza.
Nide ba kai nake kalla ba. Ignoring nata yayi suka cigaba da kallon pictures d’in se anzo page dayaga tayi kyau se ya wani wuce da wuri wuri in akazo inda yayi kyau kamar ba gobe kuma seya tsaya yana admiring kansa. K’ananun tsuka take ja.
Toh Anas a wuce page d’innan mana munfi minti uku fa muna kallo.
In kun gaji seki tashi, thank god I’m handsome and admit it you enjoy looking at my handsome face.
Nide I don’t enjoy. D’ayan page d’in ya juya ganin tayi kyau yayi sauri ya juya Anas ka tsaya mana muga nan d’in.
Keda wa? Page d’in beyi kyau ba bara’a kalla ba. Bata sake ce masa komai ba ya juya next page d’in. Babban hotonsa da Fannah ne kad’ai a page d’in wanda tabar wani duk abinda takeyi tana kallonsa zallah. Munya taji sosai ita kanta bata san ya akayi hakan ta faru ba. Hannu tasa ta rufe. Me haka? D’aga hannun mana.
A’a Anas dan Allah ka juya.
Nak’i ni nace ki tsaya kallo na awajen d’aga hannun. Kinga I can’t touch you saboda a contract namu ba body contact, d’aga hannun ki.
Tana d’agawa ta bar wajen. Dariya yakeson yi amman bayason ta raina sa. Tana kallonsa ya d’au hoton a wayarsa.
***
Bayan sun idar da Sallan Isha sukaci abinci bayi Fannah ta fad’a ta watsa ruwa a cikinsa ta canza kaya tana fitowa kamar jiya ta jera pillows tsakaninsu. Kallonta kawai yayi tare da kad’a kai bayan data kwanta yaje ya watsa ruwan shima. Pillow d’aya ya zaro ya koma kan cushion daya kwanta jiya ya mik’e kai bada jimawa ba shima yayi bacci. Kamar jiya yau ma ta farka da ihu nan shima Anas ya tashi. Kukan da takeyi yau kamar ma yafi na jiya. Kamar jiya haka ya samu yayi calming nata da k’yar tabar kukan sede b’arin da take har yanzu.
Toh sakeni zan koma in kwanta.
A’a dan Allah Anas karka tafi wallahi mutumin ze dawo.
Bare dawo ba, sakeni toh. Gangamesa ta sake tana girgiza kai.
Haka kikeson mu raya daren a zaune?
A’a nide kawai karka tafi dan Allah ta rok’esa cikin sautin kuka. Ka kwanta anan.
A’a achan zan kwanta ba kece sarkin yin katanga da pillow ba? Kwanta abinki zan kwana achan nima.
A’a zan cire dan Allah karka tafi Anas.
Nifa barin kwana nan ba sekin cire pillows d’in da kanki.
Naji zan cire hannunsa ta kama gudun kar ya gudu tayi watsi da pillows d’in. Nacire dan Allah don’t leave me, inma zaka barni ka kira Mami tazo.
Naji I won’t leave you barin d’auko pillow na.
A’a ga nawa dan Allah kar ka tafi. Murmushi ya saki. Toh matsa ciki ba musu ta matsa kan pillon nata ya kwanta. Azaune zakiyi baccin ne?
Kai ta girgiza. Kicire hijabin waj bakiya jin zufan da kikeyi ne?
Nanma kai ta girgiza fine zan koma kan kushion na kwanta.
Anas dan Allah karka tafi har yanzu bata bar b’arin da take ba. Toh kicire you are sweating. A hanakli ta yaye hijabin ta shiga kare k’irjinta. Kansa ya kawar daga gareta sdki kwanta. Pillow d’aya taja ta matso dashi kusa da nasa duk tsoro yabi ya ratsa ta. Bayan minti biyar Anas ya juya aga har yaznu batai nacci ba se b’ari take tana had’a gumi sekuma ta basa tausayi. Kin kasa bacci neh? Ya tamnayeta.
Kai ta gyad’a a hankali. I’m here kinji? Ba mutumin daze zo, ina zuwa. Hannunsa ta rik’o Anas ina zakaje?
Bathroom ya amsata.
Dan Allah kar ka tafi please.
Fannah I want to use the bathroom ba tafiya zan yi ba, kibani just a minute. Ai sam tak’i sake hannun nasa. Haka har bakin bathroom d’in tabi sa tana jiransa se waiwaye take kar mutumin yazo. Anas kayi sauri dan Allah kaji? Se buga k’ofar takeyi sam tak’i barinsa yagama biyan buk’antansa. Yana fitowa ta kama hannunsa ahaka suka isa kan gadon suka kwanta. Ta sake masa hannu ma tak’i.
Ahaka har tayi bacci, hannun nasa ya gwada cirewa daga nata amman gam ta matse cikin nata bibbiyu…
© miemiebee
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 58
BY MIEMIEBEE
Cikin baccin tace, “Anas dan Allah kar ka tafi please.” Alokaci guda kuma yaji wani irin tausayinta ya kamasa, bacci take amman idanunta basu bar zuban hawaye ba. D’ayan hannunsa yasa ya share mata hawayer. “Bar kuka kinji? I’m here.” Hannunsa ya raba da nata na k’arfi ganin yadda ta kama nasa gagam. Firgit ta tashi tana hawaye “Anas please don’t go.”
   “Ba tafiya zanyi ba Fannah” ya sanar da ita a lokacin dayake k’ok’arin kwantar da ita kan k’irjinsa. Bayan ya kwantar da itan ya soma shafa bayanta yana kwantar mata da hankali.
   “I’m here ba tafiya zanyi ba kinji?” Kai ta gyad’a cikin tsoro. Chan yaji nauyinta ya dad’u a kansa, beyi yunk’urin d’agata ba, barinta yayi ta cigaba da baccin gudun kar ya tayarda ita.
    Tunanin me yake sata mafarki haka yake. Waye mutumin? Mesa take kuka? Me ya tab’a mata? Me kuma take tsoron ze sake yi mata? Mesa kullum take irin mafarkin? For how long take erin wannan mafarkin dayake mugun tsorata ta haka? Me wannan mutumi ya mata? Har bacci yayi gaba dashi besamu amsoshi ga wad’annan tambayoyi ba.
    Asubar fari Fannah ta tashi a hankali ta bud’e idanunta, hannunta taja daga kan cikin Anas a hankali. Ta rasa meke sata mafarkin mutumin kullum kwana biyu, a da ne da abin yafaru take mafarkin kullum but as days passed by tadena yi kullum setayi kwana uku ma wani sa’in batayi ba amman tunda tayi aure takeyi kullum yanzu, kuma na yanzu yafi nada kayan ban tsoro. Me dalili? Bata kawo wani tunani a ranta ba ta miqe tayi alwala har a yanzu tsoro takeji mafarkin jiya yafi kowanne abin tsoro bayan tafito ta yi musu shimfid’a sannan ta tada Anas.
    Sun idar da Sallansu sunyi Azkhar suka koma kan gado. Pillow’nta ta matsar baya daga nasa tare da duk’unk’unewa cikin hijabinta tana kallon d’ayan side d’in. Anas ya karanchi hakan, yagano har yanzu tsoro takeji ga rashin maganar da takeyi yau kamar ba ita ba. Tausayinta yasake ji ya kama sa making him so anxious jin labarin mafarkin nata.
 
      “Fannah” ya kira sunanta cikin wani irin salo.
    “Na’am” ta amsa ba tare da ta juyo ba.
    “Are you still scared?”
   Kai ta girgiza masa tana matse ‘yar k’wallarta batadamu ko yana kallonta ko a’a ba.
   “I’m here for you kinji? Kibarjin tsoro ba mutumin da ze zo.” Yayi assuring nata. Kai ta gyad’a.
   “For how many months now kike mafarkin?” Bata masa k’arya ba tace, “7 years now.”
   7 years? Ya nanata a ransa, Allah sarki poor Fannah. “Turn and look at me.” Ya buk’ace ta. Ba gardama ta juyo hawayen da take ta k’ok’arin matsewa ne suka soma gangara. Hannunsa ya bud’a mata “come.” Matsowa tayi kusa dashi cije da tsoro, kanta ya aza a kan k’irjinsa. “Everything is going to be alright kinji? Stop crying.” Hannu yasa ya share mata hawayen. “Do you want to talk about the dream?” Kai kawai ta girgiza masa.
  “Even now that I’m your husband?” Ya tambaya cikin wani irin demanding salo. Kuka ta fashe da, “Anas nima bansani ba anytime na kwanta kawai se inji wai wani mutumi yazo yana bina ze gudu dani.” Ta masa k’arya dan battason sanar dashi sirrinta.
   “Shhhh! Is okay bar kukan, lets sleep.” Hannunta ta zagaya akan cikinsa ayayinda yake ta shafa bayanta har tayi bacci.
  **
    Da misalin k’arfe 10:00AM Fannah na zaune shiru kan cushion, game data saba yin ma tak’iyi yau. Yanzu suka gama breakfast da Anas. Observing nata yake tun da suka tashi haka take ta acting strange, ya rasa me ze mata koda ya mata magana amsarta befin ‘eh’ ko ‘a’a’. “Fannah” ya kira sunanta a nitse. “Na’am” ta d’ago kai tana kallonsa. “Kinason kifita yau?” Kai ta girgiza masa da nufin a’a sekace ba ita ba..
     “In kaiki wajen Mami?” Batasan lokacin da ta saki murmushi ba “eh” ta basa amsa cike da jin dad’i. “Lets go then.” Dama abaya ne a jikinta, gyalenta ta d’auka tayi rolling tare da feffeshe jikinta da ture haka shima Anas d’in.
   
    Hannunta rik’e cikin nasa suka fice motan ma shiya bud’e mata da kansa ya rufe bayan ta shiga. Zaman tsit suke cikin motar chan da shirun ya masa yawa yace, “mesa bakisha ice cream naki ba? Bakiya son flavour’n ne?”
    “Inaso.”
   “Mesa bakisha ba toh?”
   “In muka dawo zansha in shaa Allah” ta amsa sa a takaice. Shiru ne ya sake ratsa su chan yace, “I miss your coffee” sincerely. Kuma hakan ne rabuwansa da coffeen ta he can’t even remember.
    “Muje office naka ko painthouse in had’a maka.” tace. Duk wannan magana da suke bata juyo ta kallesa ba shiko fuskarta yakeson kalla dan tayi kyau sosai, maroon jan bakin data sa ya mugun amsarta dukda kuwa fuskarta yad’an kumbura dan kukan data sha jiya dakuma yau da safe.
 
    “Fannah look at me.” Ya buk’ace ta ba musu ta juyo. Murmushi ya saki mata daga heart nasa, “kinyi kyau.” Murmushin ta mayar masa “thanks and you too.”
    “Nikam ai kullum ina yin kyau” ya gwada janta da surutu.
   “Yes Anas, kullum kanayin kyau.” ta fad’a tare da miyar da kallonta gare da windon. Daga yadda take maganar ya karanchi batason surutu. Be sake tuhumarta ba dan bayyason tak’ura mata, abinda ke damunta kad’ai ma ya isheta. Enterprise nasa suka nufa ya bud’e mata k’ofar dan neman magana ba rik’e hannunta yayi ba wannan karan. Hannun nasa ya zagaya a waist nata tsam ya matso ta jikinsa suna shaqan k’amshin turaren juna. Ko uffan batace masa ba, duk abinda zeyi yayi atleast sunada aure yanzu ba zunubi. Tun shigarsu cikin Enterprise d’in ake ta congratulating nasu. Bayan sun shiga office nasa ya zauna kan couch a yayinda ta ke had’a masa coffeen ba abinda yake banda binta da kallo, flask dam ta cika masa tare da sa masa cup ta kawo masa. Hannunta yaja ta zauna gefensa.
     “Thank you” yace da ita. Murmushi tamayar masa as a reply. Bayan ya kurb’e rabi yayi pausing. “Kefa zakisha?” Kai ta girgiza masa. “Why?” ya tambaya.
    “Toh ka tab’a min tayi neh?” Ta amsa tambayarsa da tambaya, abinda ya tsana kenan.
    “Da biyu kikayi hakan koh?”
  “Meneh?” Ta juyo tana kallonsa.
   “Again! Aswering my question with another question.”
   “I’m sorry Mr. Fauzi na manta rules naka ne.” Cup nasan ya mik’a mata da ragowar coffeen ciki. “Shanye lets go.”
     “Se wanda kasha zaka bani?”
  “Admit it Fannah kidena so kina kaiwa kasuwa, tunba yau ba kike kallona in ina shan coffee kinason sha daga cup d’ina. Na baki yau so kisha.”
   “Oh please Mr. Fauzi girman kanka yayi yawa wallahi, I pity duk wata macen dazata aureka.”
  “Kema haka I pity duk wani mijin da ze aureki, kisha lets go.”
   “Ni barin sha ba” ta fad’a stubbornly.
   “Okay shikenan tashi mukoma hotel namu toh, da rabon bakison ganin Mami.”
    “Haba! mana Anas me had’in shan coffee na da kaini gida gun Mami kuma?”
    “Nima bansani ba all I know is that sekinsha zan kaiki.” Harara ta watsa masa aiko yaganta.
    “Ni kike harara ko me ake kiran abun?”
    “A’a nifa ba harararka nake ba abu nagani agashin ka” ta masa qarya, nan tasa hannu cikin gashin nasa seyi take kamar tana cire abu. Chan taciro hannun nata. “Ina abun?” Ya tambayeta.
  “Na yasar.” Yasan sarai k’arya take kawai ya mata murmushi. Coffeen ta kurb’e tas ashe de da dad’i. Zata iya irga so nawa take shan coffeen befi sau uku ba dana yau kenan, gaskia she have been missing. Harshe taciro ta lashe lips nata. Kallonta yake in a cute manner.
   “Zaki k’ar” Sarai yasanta da ci zatace eh aikuwa ta gyad’a kai.
   “Toh baraki k’ara ba ai nawa ne tashi mutafi.”
   “Toh Anas I will make another one.”
   “Zaki b’ata min lokaci mutafi.”
   “Anas please.”
  “Fannah please lets go.” Haka Anas ya hanata shan coffeen. Ahmad yasa ya sauk’o masa da coffee machine da flask nasa ta yadda zata na had’a masa coffee always.
    Bayan isarsu gidansu Fannah ta ruga a guje tashiga da Mami ta soma cin karo hugging nata tayi har tana hanata nishi. Bayan sun zazzauna Mami ta kawo musu d’anwake me rai da lafiya yasha had’i kam. Bajewa Fannah tayi taci kamar ba gobe sekace wacce batayi breakfast ba kallonta kawai Anas yake ko tab’a nasa beyi ba saboda he is not a fan of d’an wake be iya ci ba, inma zeci sede ya tsotse zak’in kawai.
    “Baba na ya baka cin naka?” Mami ta tambayesa.
    “Bakomai Mami kawai ban iya chi bane, I’m sorry.”
   “Su Mr. Fauzi ajebo, gaba takaini” Fannah tace chan k’asa k’asa yadda Anas kad’ai dake kusa da ita ya jiyota. Ignoring nata kawai yayi. Plate nasan taja ta soma chi bayan data k’are nata.
   Afrah da Mami kam baki suka bud’e suna kallon ikon Allah. Cike da kunya Mami tace, “haba Fannah taya zaki d’au nasa kuma.”
   “Mami bakiji me yace bane? Cewa yayi baya ci, ajebo ne shi.” Cike da mamaki Mami ta bud’e baki zata masifeta. Da wuri Anas ya katse ta, “A’a Mami barta please, chi abin ki kinji?” Taci morethan half of plate nasa sannan tajita dam.
    “Mu tafi koh?” Ya tambayeta. “Mami zamu koma inason mu gaida su Ummie ma.” Kafin Mami tayi magana Fannah ta rigata. “Tafiya kuma Anas? Na d’au fa zaka ajiye ni ne kayi tafiyarka se anjima kadawo ka d’aukeni.”
   A ransa yace dake driver’n kine niba?
 
    A fili yace, “Fannah sweetheart kinsan zamuje mu gaishe dasu Ummie fah, ba time.” Ganin zasu fara muse-musen ma’aurta Mami tayi excusing kanta tare da jawo Afrah ma suka basu space.  
  Ganin haka yace, “Driver’n kine ni ai da zaki sani jeka ka dawo, tashi mutafi, aikinga su Mamin.”
   Fuska ta maraice “ayyah amman banga Baba ba fa yana bacci. Yi hak’uri please kabarni in wuni anan wallahi chan ba dad’i.”
    “Ohonki tashi mutafi, ina ni kike cema ajebo kina zagina, stand up lets go.”
   “A’a I take that back dan Allah kayi hak’uri.”
   “Nak’i tashi mu tafi.”
   “Anas please” ta shakwab’e fuska tana murza ido. Yasan sarai zata iya fashe masa da kuka anan. Nanne mami ta fito daga d’akin. Ganin ta cika hawaye a idanunta yasa hannu tare da rik’o fuskar natan, “muga yafita?” Iska ya hura mata a idon “sannu ko?” Kai ta gyad’  “eh ya fita.” Chan k’asa k’asa tace, “ka yarda?” Harara ya galla mata tare da gyaran murya.
    “Uhm Mami zan tafi , zan bar Fannah anan I’ll be back in d’auketa.”
   “Toh toh yayi kyau sannu ko Baba na?” Dad’i sosai Fannah taji sebinsa da kallo take har yasa takalmansa. “Adawo lafiya baby.” Juyowa yayi tare da sakar da best smile nasa. “Thank you” sannan ya fice.
   “Soyayya ruwan zuma…” Cewar Afrah tana gyad’a kai. “Su wani baby kuka samu sara?” Banza da ita Fannah tayi seda Mami takoma d’aki bakin Fannah ya bud’u. “Amman ke mena cemiki? Bance karki samin english wears cikin akwatunan da zan tafi dasu ba?”
   “Toh meh? Ai naga da english wears ake amarchi” nan ta kewaya taga ba Mami “Ya Fannah ya first night d’in? Kinyi kuka?”
   “K’asaran ki maras kunya kawai nima bansani ba.”
   “Heheh!” ta sheqe da dariya, “Toh Allah kawo zuriah d’ayyiba yasa du sharpshooters ne” nan iphone nata yayi k’ara alaman shigowar message. Tana bud’ewa taga airtime ne na dubu biyu hot baby nata yamata sending. Bayan tayi replying nasa tace a fili “Allah bar min kai yau akwai flexing a instagram da kallon stories a snapchat.”
      Har yanzu Fannah ta kasa rufe baki a iya sanin ta de Iphone 5s ce wayar Afrah how comes take rik’e 6s plus yanzu?
    “Ke ina kika samu wannan k’aton wayar? Waya baki?”
    “Wanne wai?” ta tambaya cike da tsiya. “Awww Iphone d’ina? Hot baby ya siya min wallahi, yayi kyau ko?”
   “Hot baby wa kenan?” ta kuma tambaya cike da rashin fahimta.
   “Wa kuwa inba Shettima darling ba, business nasa se bunk’asa yake wallahi.”
   Dariya sosai Fannah ta sheqe da dan tasan ina yake samun kud’in daya ke kashe mata. “Shi business d’in kenan?”
  “Eh mana abin hassada ne kuma?”
  “A’a babyn Shettima Allah barku tare ni taho ki tayani in shirya atamfofina gu d’aya dasu zan koma.” Afrah ta bud’e baki zata kuma wani zancen Fannah ta katse ta “a’a banason bayani muje.” Suna hira suna shirya kayakin har suka gama.
11:30AM
    Daidai nan Anas ya dawo d’aukanta beso sake shiga ba se kawai ya kira ta ta waya alokacin wayar tata na d’akinsu itako tana d’akin Baba se hira suke bazawa kamar ance ta mik’e tace bari taje d’aki. Tana shiga taji rurin wayarta nan ta d’aga tare da duban waye. ‘Anas’ taga tubuce kai. K’in picking tayi dan battason sake komawa hotel nasun nan its so boring. Se a karo na biyu ta d’aga nanma seda ya kusa tsinkewa.
    “Kifito I’m waiting for you.”
   “Anas mana please, bamu had’u da Aiman bafa, tana school se 1:00AM zata dawo kaji? In jira?”
   “Banji ba kuma baraki jira ba, Fannah kifito don’t let me repeat myself.” Karap ya katse wayar, tsuka taja. Aiko ya fad’a kunnen Mami. “Keda waye ne?”
  “Erm.. Ermm…” kafin ta had’o k’arya Mami tace, “keda Anas ko? Fannah tun ba’ayi nisa ba kin soma masa rashin kunya, iyyeh? Me dalili?”
   “Mami waifa har ya dawo infito mu tafi.” ta fad’a tana turo baki.
   “Toh se meh? Out!” ta nuna mata k’ofa. Dake kafad’a tayi. “Fannah zan sab’a miki fa!” Haka kamar wacce zatayi kuka taja akwatinta ta fice ko sauraron Afrah batai ba. Bayan fitarta ta bud’e gidan baya tasa akwatin yana kallonta bece komai ba. Tana shiga ya kunna motar ba wanda yace ma wani ko uffan. Bayan isarsu gida suka gaggaisa, Ummie kamar ta cinye Fannah. Besamu ya had’u da Amal ba dake tana school haka Shettima ma.
     “Kuyi sauri ku gama gaisawan ku zan d’au abu cikin d’akina ne yanzu mukoma.”
     “Kai Babana daman ba yini kuka zo mana ba?”
   “Yini? A’a fa Ummie gaisuwan minti biyar ne kacal.” Yana kaiwa nan yashige d’akinsa. “Oh! Fannah kinga halin mijin naki ko? Yafiye rowa dayawa.” Murmushi cike da kunya ta saki tana kare fuskarta.
     Bayan shigan Anas d’akinsa ya nufa wajen safe dan ciro kud’ad’ensa wanda ze buk’ata to his suprise yaga  an kwashe kusan rabin kud’ad’en. Dubawa dakyau ya kuma yi yaga eh fa kud’in nasa ne babu to waye ya masa wannan d’anyen aiki? Rufewa yayi tare da dawo wa cikin parlon “Ummie” ya kira sunanta.
    “Kin d’au abu cikin d’akina?”
   “Kamar ya abu kuma Anas?”
   “I mean my money morethan half of it are gone.”
   “Wai! Wai! Ka duba dakyau kuwa?”
   “Eh jeki duba kiga” nan ta mik’e ta nufa d’akin nasa. Ganin haka Fannah ta b’arke da dariya har rufe bakinta take, ashe nan ne business na Shettima yake bunk’asa tunda Anas bai gida. Kallon ta Anas yake ya rasa dalilin dariyar tata. Ummie tagama dube dubenta ba kud’ad’en, ko kad’an Anas be kawo aransa Shettima neba.
***
    “Bari in yaran suka dawo zan tambayesu halan sunkai wani wajen daban.” Cewar Ummie dake tsaye bakin k’ofa ayayinda Anas ke k’ok’arin kunna mota. “Okay in Abuu ya dawo ki gaishe min shi.”
   “Toh, amaryar mu semun shigo ko? Mungode.”
  “Yawwa Ummie se anjima” Fannah ta amsata. Acikin motan ne Anas ya juyo yana kallon Fannah. “Dariyan me kuke d’azu?”
   “Da yaushe?” Ta tambaya pretending as if bata gano inda ya dosa ba.
   “Fannah banaso answer me.”
   “Babu kawai daga yin dariya yazama matsala.”
    “Bari zakiyi mafarki ma ai yau zamuga waze zauna dake, infact seperate d’aki ma zan kama.” Jin haka tace, “a’a zan fad’a maka.”
  “Good ina jinki.”
   “All I know is business na Shettima ya bunk’asa.”
  “Kamar ya kenan?” ya katse ta.
   “Oho nifa kar azo ace ina had’a munafirci.”
   “Just tell me.”
  “Promise barakayi reacting akai ba?”
  “I promise.”
   “Nide naga Afrah da 6s plus kuma tace Shettima ya siya mata.”
   “6s plus?” Ya tambaya tare da juyowa yana kallon ta cike da mamaki.
   “Anas kalli gabanka please kar ka bugamu ko mu fad’a rami.”
   “Wato da kud’i na aka sai wa Afrah 6s plus d’in koh? Da kud’in mijinki shine kike dariya. Da kyau zamu had’u dashi.”
     “Toh me zanyi? Shida kud’in yayansa. Plus a’a Mr. Fauzi kaga you promised you won’t react.”
   “So kike inyi shiru in zuba masa ido? Ya kwashe morethan half of kud’in dake cikin safe d’ina fa.”
  “Hak’uri zakayi he is in love kuma dan baida aikinyi ne, let them be please, kaji Mr. Fauzi.”
   “You really wants to annoy me ko Miss Aleeyu?”
   “A’a Anas toh, nide kar ka masa magana.” Chan k’asa k’asa yace, “barin masa magana ba kamar yadda barin canza masa motar sa ba kuwa”
   “Yafi amman dekam karka masa magana.” tache.
TANA TARE DA NI…
TANA TARE DA NI… PAGE 58
BY MIEMIEBEE
Cikin baccin tace, “Anas dan Allah kar ka tafi please.” Alokaci guda kuma yaji wani irin tausayinta ya kamasa, bacci take amman idanunta basu bar zuban hawaye ba. D’ayan hannunsa yasa ya share mata hawayer. “Bar kuka kinji? I’m here.” Hannunsa ya raba da nata na k’arfi ganin yadda ta kama nasa gagam. Firgit ta tashi tana hawaye “Anas please don’t go.”
   “Ba tafiya zanyi ba Fannah” ya sanar da ita a lokacin dayake k’ok’arin kwantar da ita kan k’irjinsa. Bayan ya kwantar da itan ya soma shafa bayanta yana kwantar mata da hankali.
   “I’m here ba tafiya zanyi ba kinji?” Kai ta gyad’a cikin tsoro. Chan yaji nauyinta ya dad’u a kansa, beyi yunk’urin d’agata ba, barinta yayi ta cigaba da baccin gudun kar ya tayarda ita.
    Tunanin me yake sata mafarki haka yake. Waye mutumin? Mesa take kuka? Me ya tab’a mata? Me kuma take tsoron ze sake yi mata? Mesa kullum take irin mafarkin? For how long take erin wannan mafarkin dayake mugun tsorata ta haka? Me wannan mutumi ya mata? Har bacci yayi gaba dashi besamu amsoshi ga wad’annan tambayoyi ba.
    Asubar fari Fannah ta tashi a hankali ta bud’e idanunta, hannunta taja daga kan cikin Anas a hankali. Ta rasa meke sata mafarkin mutumin kullum kwana biyu, a da ne da abin yafaru take mafarkin kullum but as days passed by tadena yi kullum setayi kwana uku ma wani sa’in batayi ba amman tunda tayi aure takeyi kullum yanzu, kuma na yanzu yafi nada kayan ban tsoro. Me dalili? Bata kawo wani tunani a ranta ba ta miqe tayi alwala har a yanzu tsoro takeji mafarkin jiya yafi kowanne abin tsoro bayan tafito ta yi musu shimfid’a sannan ta tada Anas.
    Sun idar da Sallansu sunyi Azkhar suka koma kan gado. Pillow’nta ta matsar baya daga nasa tare da duk’unk’unewa cikin hijabinta tana kallon d’ayan side d’in. Anas ya karanchi hakan, yagano har yanzu tsoro takeji ga rashin maganar da takeyi yau kamar ba ita ba. Tausayinta yasake ji ya kama sa making him so anxious jin labarin mafarkin nata.
 
      “Fannah” ya kira sunanta cikin wani irin salo.
    “Na’am” ta amsa ba tare da ta juyo ba.
    “Are you still scared?”
   Kai ta girgiza masa tana matse ‘yar k’wallarta batadamu ko yana kallonta ko a’a ba.
   “I’m here for you kinji? Kibarjin tsoro ba mutumin da ze zo.” Yayi assuring nata. Kai ta gyad’a.
   “For how many months now kike mafarkin?” Bata masa k’arya ba tace, “7 years now.”
   7 years? Ya nanata a ransa, Allah sarki poor Fannah. “Turn and look at me.” Ya buk’ace ta. Ba gardama ta juyo hawayen da take ta k’ok’arin matsewa ne suka soma gangara. Hannunsa ya bud’a mata “come.” Matsowa tayi kusa dashi cije da tsoro, kanta ya aza a kan k’irjinsa. “Everything is going to be alright kinji? Stop crying.” Hannu yasa ya share mata hawayen. “Do you want to talk about the dream?” Kai kawai ta girgiza masa.
  “Even now that I’m your husband?” Ya tambaya cikin wani irin demanding salo. Kuka ta fashe da, “Anas nima bansani ba anytime na kwanta kawai se inji wai wani mutumi yazo yana bina ze gudu dani.” Ta masa k’arya dan battason sanar dashi sirrinta.
   “Shhhh! Is okay bar kukan, lets sleep.” Hannunta ta zagaya akan cikinsa ayayinda yake ta shafa bayanta har tayi bacci.
  **
    Da misalin k’arfe 10:00AM Fannah na zaune shiru kan cushion, game data saba yin ma tak’iyi yau. Yanzu suka gama breakfast da Anas. Observing nata yake tun da suka tashi haka take ta acting strange, ya rasa me ze mata koda ya mata magana amsarta befin ‘eh’ ko ‘a’a’. “Fannah” ya kira sunanta a nitse. “Na’am” ta d’ago kai tana kallonsa. “Kinason kifita yau?” Kai ta girgiza masa da nufin a’a sekace ba ita ba..
     “In kaiki wajen Mami?” Batasan lokacin da ta saki murmushi ba “eh” ta basa amsa cike da jin dad’i. “Lets go then.” Dama abaya ne a jikinta, gyalenta ta d’auka tayi rolling tare da feffeshe jikinta da ture haka shima Anas d’in.
   
    Hannunta rik’e cikin nasa suka fice motan ma shiya bud’e mata da kansa ya rufe bayan ta shiga. Zaman tsit suke cikin motar chan da shirun ya masa yawa yace, “mesa bakisha ice cream naki ba? Bakiya son flavour’n ne?”
    “Inaso.”
   “Mesa bakisha ba toh?”
   “In muka dawo zansha in shaa Allah” ta amsa sa a takaice. Shiru ne ya sake ratsa su chan yace, “I miss your coffee” sincerely. Kuma hakan ne rabuwansa da coffeen ta he can’t even remember.
    “Muje office naka ko painthouse in had’a maka.” tace. Duk wannan magana da suke bata juyo ta kallesa ba shiko fuskarta yakeson kalla dan tayi kyau sosai, maroon jan bakin data sa ya mugun amsarta dukda kuwa fuskarta yad’an kumbura dan kukan data sha jiya dakuma yau da safe.
 
    “Fannah look at me.” Ya buk’ace ta ba musu ta juyo. Murmushi ya saki mata daga heart nasa, “kinyi kyau.” Murmushin ta mayar masa “thanks and you too.”
    “Nikam ai kullum ina yin kyau” ya gwada janta da surutu.
   “Yes Anas, kullum kanayin kyau.” ta fad’a tare da miyar da kallonta gare da windon. Daga yadda take maganar ya karanchi batason surutu. Be sake tuhumarta ba dan bayyason tak’ura mata, abinda ke damunta kad’ai ma ya isheta. Enterprise nasa suka nufa ya bud’e mata k’ofar dan neman magana ba rik’e hannunta yayi ba wannan karan. Hannun nasa ya zagaya a waist nata tsam ya matso ta jikinsa suna shaqan k’amshin turaren juna. Ko uffan batace masa ba, duk abinda zeyi yayi atleast sunada aure yanzu ba zunubi. Tun shigarsu cikin Enterprise d’in ake ta congratulating nasu. Bayan sun shiga office nasa ya zauna kan couch a yayinda ta ke had’a masa coffeen ba abinda yake banda binta da kallo, flask dam ta cika masa tare da sa masa cup ta kawo masa. Hannunta yaja ta zauna gefensa.
     “Thank you” yace da ita. Murmushi tamayar masa as a reply. Bayan ya kurb’e rabi yayi pausing. “Kefa zakisha?” Kai ta girgiza masa. “Why?” ya tambaya.
    “Toh ka tab’a min tayi neh?” Ta amsa tambayarsa da tambaya, abinda ya tsana kenan.
    “Da biyu kikayi hakan koh?”
  “Meneh?” Ta juyo tana kallonsa.
   “Again! Aswering my question with another question.”
   “I’m sorry Mr. Fauzi na manta rules naka ne.” Cup nasan ya mik’a mata da ragowar coffeen ciki. “Shanye lets go.”
     “Se wanda kasha zaka bani?”
  “Admit it Fannah kidena so kina kaiwa kasuwa, tunba yau ba kike kallona in ina shan coffee kinason sha daga cup d’ina. Na baki yau so kisha.”
   “Oh please Mr. Fauzi girman kanka yayi yawa wallahi, I pity duk wata macen dazata aureka.”
  “Kema haka I pity duk wani mijin da ze aureki, kisha lets go.”
   “Ni barin sha ba” ta fad’a stubbornly.
   “Okay shikenan tashi mukoma hotel namu toh, da rabon bakison ganin Mami.”
    “Haba! mana Anas me had’in shan coffee na da kaini gida gun Mami kuma?”
    “Nima bansani ba all I know is that sekinsha zan kaiki.” Harara ta watsa masa aiko yaganta.
    “Ni kike harara ko me ake kiran abun?”
    “A’a nifa ba harararka nake ba abu nagani agashin ka” ta masa qarya, nan tasa hannu cikin gashin nasa seyi take kamar tana cire abu. Chan taciro hannun nata. “Ina abun?” Ya tambayeta.
  “Na yasar.” Yasan sarai k’arya take kawai ya mata murmushi. Coffeen ta kurb’e tas ashe de da dad’i. Zata iya irga so nawa take shan coffeen befi sau uku ba dana yau kenan, gaskia she have been missing. Harshe taciro ta lashe lips nata. Kallonta yake in a cute manner.
   “Zaki k’ar” Sarai yasanta da ci zatace eh aikuwa ta gyad’a kai.
   “Toh baraki k’ara ba ai nawa ne tashi mutafi.”
   “Toh Anas I will make another one.”
   “Zaki b’ata min lokaci mutafi.”
   “Anas please.”
  “Fannah please lets go.” Haka Anas ya hanata shan coffeen. Ahmad yasa ya sauk’o masa da coffee machine da flask nasa ta yadda zata na had’a masa coffee always.
    Bayan isarsu gidansu Fannah ta ruga a guje tashiga da Mami ta soma cin karo hugging nata tayi har tana hanata nishi. Bayan sun zazzauna Mami ta kawo musu d’anwake me rai da lafiya yasha had’i kam. Bajewa Fannah tayi taci kamar ba gobe sekace wacce batayi breakfast ba kallonta kawai Anas yake ko tab’a nasa beyi ba saboda he is not a fan of d’an wake be iya ci ba, inma zeci sede ya tsotse zak’in kawai.
    “Baba na ya baka cin naka?” Mami ta tambayesa.
    “Bakomai Mami kawai ban iya chi bane, I’m sorry.”
   “Su Mr. Fauzi ajebo, gaba takaini” Fannah tace chan k’asa k’asa yadda Anas kad’ai dake kusa da ita ya jiyota. Ignoring nata kawai yayi. Plate nasan taja ta soma chi bayan data k’are nata.
   Afrah da Mami kam baki suka bud’e suna kallon ikon Allah. Cike da kunya Mami tace, “haba Fannah taya zaki d’au nasa kuma.”
   “Mami bakiji me yace bane? Cewa yayi baya ci, ajebo ne shi.” Cike da mamaki Mami ta bud’e baki zata masifeta. Da wuri Anas ya katse ta, “A’a Mami barta please, chi abin ki kinji?” Taci morethan half of plate nasa sannan tajita dam.
    “Mu tafi koh?” Ya tambayeta. “Mami zamu koma inason mu gaida su Ummie ma.” Kafin Mami tayi magana Fannah ta rigata. “Tafiya kuma Anas? Na d’au fa zaka ajiye ni ne kayi tafiyarka se anjima kadawo ka d’aukeni.”
   A ransa yace dake driver’n kine niba?
 
    A fili yace, “Fannah sweetheart kinsan zamuje mu gaishe dasu Ummie fah, ba time.” Ganin zasu fara muse-musen ma’aurta Mami tayi excusing kanta tare da jawo Afrah ma suka basu space.  
  Ganin haka yace, “Driver’n kine ni ai da zaki sani jeka ka dawo, tashi mutafi, aikinga su Mamin.”
   Fuska ta maraice “ayyah amman banga Baba ba fa yana bacci. Yi hak’uri please kabarni in wuni anan wallahi chan ba dad’i.”
    “Ohonki tashi mutafi, ina ni kike cema ajebo kina zagina, stand up lets go.”
   “A’a I take that back dan Allah kayi hak’uri.”
   “Nak’i tashi mu tafi.”
   “Anas please” ta shakwab’e fuska tana murza ido. Yasan sarai zata iya fashe masa da kuka anan. Nanne mami ta fito daga d’akin. Ganin ta cika hawaye a idanunta yasa hannu tare da rik’o fuskar natan, “muga yafita?” Iska ya hura mata a idon “sannu ko?” Kai ta gyad’  “eh ya fita.” Chan k’asa k’asa tace, “ka yarda?” Harara ya galla mata tare da gyaran murya.
    “Uhm Mami zan tafi , zan bar Fannah anan I’ll be back in d’auketa.”
   “Toh toh yayi kyau sannu ko Baba na?” Dad’i sosai Fannah taji sebinsa da kallo take har yasa takalmansa. “Adawo lafiya baby.” Juyowa yayi tare da sakar da best smile nasa. “Thank you” sannan ya fice.
   “Soyayya ruwan zuma…” Cewar Afrah tana gyad’a kai. “Su wani baby kuka samu sara?” Banza da ita Fannah tayi seda Mami takoma d’aki bakin Fannah ya bud’u. “Amman ke mena cemiki? Bance karki samin english wears cikin akwatunan da zan tafi dasu ba?”
   “Toh meh? Ai naga da english wears ake amarchi” nan ta kewaya taga ba Mami “Ya Fannah ya first night d’in? Kinyi kuka?”
   “K’asaran ki maras kunya kawai nima bansani ba.”
   “Heheh!” ta sheqe da dariya, “Toh Allah kawo zuriah d’ayyiba yasa du sharpshooters ne” nan iphone nata yayi k’ara alaman shigowar message. Tana bud’ewa taga airtime ne na dubu biyu hot baby nata yamata sending. Bayan tayi replying nasa tace a fili “Allah bar min kai yau akwai flexing a instagram da kallon stories a snapchat.”
      Har yanzu Fannah ta kasa rufe baki a iya sanin ta de Iphone 5s ce wayar Afrah how comes take rik’e 6s plus yanzu?
    “Ke ina kika samu wannan k’aton wayar? Waya baki?”
    “Wanne wai?” ta tambaya cike da tsiya. “Awww Iphone d’ina? Hot baby ya siya min wallahi, yayi kyau ko?”
   “Hot baby wa kenan?” ta kuma tambaya cike da rashin fahimta.
   “Wa kuwa inba Shettima darling ba, business nasa se bunk’asa yake wallahi.”
   Dariya sosai Fannah ta sheqe da dan tasan ina yake samun kud’in daya ke kashe mata. “Shi business d’in kenan?”
  “Eh mana abin hassada ne kuma?”
  “A’a babyn Shettima Allah barku tare ni taho ki tayani in shirya atamfofina gu d’aya dasu zan koma.” Afrah ta bud’e baki zata kuma wani zancen Fannah ta katse ta “a’a banason bayani muje.” Suna hira suna shirya kayakin har suka gama.
11:30AM
    Daidai nan Anas ya dawo d’aukanta beso sake shiga ba se kawai ya kira ta ta waya alokacin wayar tata na d’akinsu itako tana d’akin Baba se hira suke bazawa kamar ance ta mik’e tace bari taje d’aki. Tana shiga taji rurin wayarta nan ta d’aga tare da duban waye. ‘Anas’ taga tubuce kai. K’in picking tayi dan battason sake komawa hotel nasun nan its so boring. Se a karo na biyu ta d’aga nanma seda ya kusa tsinkewa.
    “Kifito I’m waiting for you.”
   “Anas mana please, bamu had’u da Aiman bafa, tana school se 1:00AM zata dawo kaji? In jira?”
   “Banji ba kuma baraki jira ba, Fannah kifito don’t let me repeat myself.” Karap ya katse wayar, tsuka taja. Aiko ya fad’a kunnen Mami. “Keda waye ne?”
  “Erm.. Ermm…” kafin ta had’o k’arya Mami tace, “keda Anas ko? Fannah tun ba’ayi nisa ba kin soma masa rashin kunya, iyyeh? Me dalili?”
   “Mami waifa har ya dawo infito mu tafi.” ta fad’a tana turo baki.
   “Toh se meh? Out!” ta nuna mata k’ofa. Dake kafad’a tayi. “Fannah zan sab’a miki fa!” Haka kamar wacce zatayi kuka taja akwatinta ta fice ko sauraron Afrah batai ba. Bayan fitarta ta bud’e gidan baya tasa akwatin yana kallonta bece komai ba. Tana shiga ya kunna motar ba wanda yace ma wani ko uffan. Bayan isarsu gida suka gaggaisa, Ummie kamar ta cinye Fannah. Besamu ya had’u da Amal ba dake tana school haka Shettima ma.
     “Kuyi sauri ku gama gaisawan ku zan d’au abu cikin d’akina ne yanzu mukoma.”
     “Kai Babana daman ba yini kuka zo mana ba?”
   “Yini? A’a fa Ummie gaisuwan minti biyar ne kacal.” Yana kaiwa nan yashige d’akinsa. “Oh! Fannah kinga halin mijin naki ko? Yafiye rowa dayawa.” Murmushi cike da kunya ta saki tana kare fuskarta.
     Bayan shigan Anas d’akinsa ya nufa wajen safe dan ciro kud’ad’ensa wanda ze buk’ata to his suprise yaga  an kwashe kusan rabin kud’ad’en. Dubawa dakyau ya kuma yi yaga eh fa kud’in nasa ne babu to waye ya masa wannan d’anyen aiki? Rufewa yayi tare da dawo wa cikin parlon “Ummie” ya kira sunanta.
    “Kin d’au abu cikin d’akina?”
   “Kamar ya abu kuma Anas?”
   “I mean my money morethan half of it are gone.”
   “Wai! Wai! Ka duba dakyau kuwa?”
   “Eh jeki duba kiga” nan ta mik’e ta nufa d’akin nasa. Ganin haka Fannah ta b’arke da dariya har rufe bakinta take, ashe nan ne business na Shettima yake bunk’asa tunda Anas bai gida. Kallon ta Anas yake ya rasa dalilin dariyar tata. Ummie tagama dube dubenta ba kud’ad’en, ko kad’an Anas be kawo aransa Shettima neba.
***
    “Bari in yaran suka dawo zan tambayesu halan sunkai wani wajen daban.” Cewar Ummie dake tsaye bakin k’ofa ayayinda Anas ke k’ok’arin kunna mota. “Okay in Abuu ya dawo ki gaishe min shi.”
   “Toh, amaryar mu semun shigo ko? Mungode.”
  “Yawwa Ummie se anjima” Fannah ta amsata. Acikin motan ne Anas ya juyo yana kallon Fannah. “Dariyan me kuke d’azu?”
   “Da yaushe?” Ta tambaya
     Kasa koda amsashi tayi wani kunya taji ya rufeta, she can’t believe abinda ta aikata sede kuma chan cikin zuciyarta tana miradi da abinda tayi atleast tayi proving masa tana sonsa bare sake kokwanton san da take masa ba. Hannunsa ta sauk’e daga hab’arta tare da juyawa kafin ta soma tafiya yasa hannu a kunkuminta ya juyo da ita tare da matse jikinta a nasa. “Flower look at me” har a yanzu tak’i d’ago kai su had’a ido. “Flower baraki kalleni ba?” Kai ta kad’a masa. “Then look at me” kai ta sake kad’a masa kunya bare barta ta kallesa ba.
     “You love me right?” Ya tambayeta. Kai ta gyad’a masa. “I want to hear it again Flower.” Hannunta ta zagaye a bayansa tayi hugging nasa “I love you Anas, I love you so very much My Lion” shima a hankali ya zagaye hannayensa a bayanta pulling her closer to him. Gashinta yayi kissing “I love you so much more Flower.” sosai yaji dad’in sunan data kirasa dashi •°LION°• it means everything to him.
       Sun d’au tsawon lokaci suna atsaye sannan a hankali ya raba jikinsa da nata tare da jawo hannunta suka zauna kan kujera. Hannyensu ya had’a duka waje d’aya cikin sanyin murya a hankali yace, “Flower fad’amin mesa kikayi shunning d’ina jiya? Nasan kina da qwararren dalili koh?” Kai ta gyad’a “then tell me kinji? Karki b’oye min tell your husband” Innocent eyes nata data k’ayatasu da kajol ta d’ago a hankali ta azasu akansa.
      “I’m afraid Anas tsoro nakeji” ta sanar dashi cikin cracky voice.
     “Tsoron meh Flower? Kin d’au zan miki wani abu neh?” nan ma kai ta gyad’a. “Don’t be kinji? Ba abinda zan miki seda yardan ki I will never do anything to you ki saki jikinki dani kinji?”
        Batasan lokacinda hawaye yasoma ciko mata a ido ba cikin sautin kuka tace, “for how long Anas? For how zaka ta zama haka? For how long zanta toye maka hak’k’in ka?”
     
     “For as how long it takes Fannah ni ban damu ba I love you so kema kibar damuwa kinji?” Kai ta kad’a “Anas dole in damu saboda na miji ne kai dole wataran sha’awah ze taso maka and saboda bakason kayi forcing d’ina seka hak’ura ka tauye wa kanka hak’k’i saboda matarka batason baka hak’k’inka? In hakan ya faru kasan me mala’ikum Rahma zasu min? Anas tsine min zasuyi, zasu tsine min…” ta fashe da wani irin matsanancin kuka. Duk tabi tasa Anas rikicewa a rayuwa ba abinda ke tada masa hankali kamar kukan flowersa. Matso ta yayi ajikinsa yana bubbuga bayanta “Flower kibar kukan nan please I can’t take it please kibari kidena.” Pecking gashinta yayi “stop crying kinji? Ba tsinuwan da za’a miki in shaa Allah ni nayi deciding I won’t touch you se in rananda kika yarda so kibar kukan kinji?” Kai ta gyad’a masa a hankali tasoma shanye kukan nata.
     Seda ya tabbata tayi shiru ya d’ago ta daga jikinsa yana kallonta “Flower but what are you so afraid of? Mesa kike tsoro haka? Saboda kin ganni kind of large?” Ya tambaya tare da d’age gira. Murmushi kad’an ta saki tana kad’a kai danko yabata dariya shi ya d’au wai tsoronsa take amman ko kad’an. “Tsoro na kikeji flower?” Kai ta girgiza masa “mesa zanji tsoron ka Cherie Pie?”
     “I don’t know kodan kinga inada builded body kinga muscles all over my hand kike tsoro I might destroy you on bed kekuma gaki ‘yar k’arama” Dariya sosai ta tsaya tanayi harda rik’e cikinta. “Anas I’m not small kadena cemin small.”
      “Yes you are Baby and thats why kike tsoro.”
      “Ko kad’an ba haka bane Doodle bug matsalar ba daga gareka bane…” Sekuma tayi shiru take mood nata ya canza.
    Hannunta ya rik’o “ba daga ni ba Flower? Bani kike tsoro ba?” Kai ta gyad’a masa “toh daga waye ne Flower?” Take idanunta suka ciko da hawaye “Anas daga ni ne, matsalar daga ni ne…” Sekuma ta fashe da kuka. Hankalin Anas in yayi dubu be tashi ba kamar ya daga ita? Me take nufi? Mesa take kuka haka? Is she lacking something as a woman? Subhanallah!
     Kwanto da ita yayi a kan k’irjinsa yana fad’a mata dad’ad’d’un kalamu masu kwantar da hankali. Duk yabi ya k’osa yaji dalilin dayasa take tsoron had’a kwanciya dashi. Seda ya tabbata tayi shiru ya d’ago ta tare da rik’o fuskarta da hannayensa bibbiyu.
      “You don’t have to be afraid anymore, Flower ko a yaya kike I love you koda you are lacking something as a woman I still love you ahakan ina sonki nake tsakani da Allah badan wani abinda kike dashi ba.” Idanunta taji suna sake cikowa da hawaye “Anas koda… Koda…” sekuma ta sake fashewa da kuka. Haka ya sake rungumota seda tayi kukan me isarta sannan ta taso da kanta, hannunsa ta rik’e cikin nata tana kallon cikin idanunsa da kumburarrun idanunta da sukayi ja “Anas I’m insecure of your love gani nake kamar I’ll lose you, gani nake kamar in na fad’a maka sirrina zaka gujeni ka nisanta daga gareni ka kuma tsane ni, abinda baran iya jurewa ba kenan, I don’t want to lose you My Lion.”
      “Flower I will never hate you kibar fad’an haka, I will never leave your side koda kuwa wannan sirrin kin is as worse as kisan kai God forbid I will never leave you Fannah. I love you for the sake of Allah and nothing more ki d’au wannan sirrinkin k’addara ne a rayuwar aurenmu kinji? And stop saying zakiyi losing d’ina kinji na rantse I will never leave you, never.” D’an sanyi taji a ranta duk da cewa kuwa bata gamsu ba acewarta Anas na fad’in hakan ne dan besan ba cikakkiyar budurwa ce ita ba.
      “So can you tell me? Zaki iya fad’amin dalilin dayasa kike tsoron wani abu ya shiga tsakani na dake? trust me koda mene barin tab’a barinki ba Flower _INA TARE DA KE”_ kai ta gyad’a masa tsili-tsilin hawaye na gangarowa kan kumatunta wanda yasa hannu ya share. “Anas kayi hak’uri dan Allah kasani bawai nayi hakan bane dan cin amanarka, I just can’t bring myself to tell you I’m.. I’m not complete as your woman I’m lacking something. Anas banida… Banida…” sekuma kuka yafi k’arfinta.
     
     Zuciyarsa yaji ya buga tsoro shi kansa ya somaji. “Shhhh is okay” yayi hugging nata “ya isa you can’t talk right now ya isa kinji? Mubar maganan” sosai hankalinsa ya tashi shima yarasa meke masa dad’i me Fannarsa ta rasa? Mesa da zaran ta tuna abin take kuka? Ko kad’an be kawo a ransa wai ko nufi take batada budurci ba saboda yasan hankalinta ya yaba da tarbiyyan ta yasani barata tab’a siyar da budurcinta ma kowani k’ato ba. Seda ya tabbata tayi shiru yace da ita “tashi muje d’aki ki kwanta kinji?”
     “Anas I’m sorry trust me I really want to tell you, wallahi inason sanar dakai I can’t-” katse ta yayi “I trust you My Flower shikenan don’t bother kinji? Mubar maganan I trust you ko baki fad’a min yau ba you will some other day ko ba haka ba?” Kai ta gyad’a. “Shikenan tashi muje d’aki.” Tana manne ajikinsa suka k’arisa d’aki ya kwantar da ita ajikinsa har a yanzu nishinta be dawo normal ba yana bubbuga bayanta har tasamu tayi bacci.
     “Flower” yakira sunanta. Jin shiru yad’an lek’a fuskarta yaga tayi bacci. Hannunsu ya had’a “Fannah I love you kinji? Banga abinda zesa in barki ba no matter what *INA TARE DA KE* forever” ahaka shima yasamu ya kwanta da tunanin Fannah a ransa.
   *****
        Seda Maghrib Fannah ta tashi a hankali ta raba jikinta da nasa ta fad’a toilet bayan tagama duk abinda zatayi tafito tayi kan Anas cikin wani irin romantic salo ta tayar dashi daga bacci yayi alwala shima yajasu Sallah. Bayan sun idar suka ci dinner, kallo kad’an suka tab’a suna hira suna tambayan junansu questions about likes and dislikes nasu dakuma age da sauran abubuwa da dama. Sosai shekarun Anas ya bata mamaki ashede mijin nata yaro ne ko 25 be cika ba gashi kuma ajebo abubuwa dayawa bayya chi. Haka suka tayi har zuwa 10:00PM sannan suka koma d’aki shi da kansa yaciro mata rigar baccin dayakeso tasa.
      “Babe wannan?” ta tambaya tana zaro idanu waje “Ai wannan ba marabansa da babu jibi fah.” ta d’aga shimen sama.
     “Flower shi nakeso.” Wani daban taciro “zansa wannan.”
    “A’a flowor ni wancan nakeso” zata sake magana yace, “zanyi fushi in baki sa ba” da sauri ta katse sa, “a’a karkayi zansa.” murmushi ya saki yana binta da kallo ta shige d’akinta ta koma tasa tare da k’are wa kanta kallo jikin mirror. Kai ta kad’a no gaskia yayi tsireci dayawa wata zuciyar ce tace mata toh ai mijin ki ne bawani gardi ba. Sam ta kasa fita da kayan hijabi ta b’urma akai tana kai k’ofan d’akinsa ta tsaya daga bakin k’ofar a nitse ta bud’e k’ofan kad’an nan ya maido da kallonsa wajen. “Come in Baby” ya buk’ace ta. Ido ta rufe ta cire hijabin da k’yar ta iya shiga cikin d’akin kanta a k’asa se murza hannayenta take duk kunya yabi ya cinyeta kallonta ya tsaya yi wane yau ya soma sata a ido ji yake kamar ya had’iyeta ko kyafta ido ya kasa why is she so damn beautiful? Abinda yake ta nanatawa a ransa kenan. Da kallon ya isheta seta fara k’ok’arin miyar da hijabin nata kamar a kyaftawan ido ya k’ariso gabanta tare da k’wace hijabin.
      “Anas kabani please.” Murmushi ya saki me k’ara masa kyau. “Flower you are damn beautiful” hannu yasa ya zagaye a kunkuminta ya matso da ita kusa dashi. “Kiss me” ya buk’ace ta. Yi tayi kamar bata jisa ba. “Flower I said kiss me.” Kai ta d’ago ta k’are masa kallo sannan tayi d’agel ta yi pecking nasa a kumatu. “There bani hijabi na toh.”
      “Are you kidding me? Kiss me like you did d’azu.”
     “Barin iya ba” ta fad’a stubbornly.
    “Nima barin bada hijabin ba.”
    “Anas please kabani.”
    “Kiss me first.”
    “Okay naji sakeni toh.” Kafad’a ya buga mata. “Ka sakeni toh I will kiss you.”
    “Are you sure?”
   “Yes My Lion.” Ba musu ya saketa hannunta ta zagaye a wuyansa sannan ta k’are wa light red lips nasa kallo seda ta tabbata ya shagalta yana jiran tayi kissing nasa tasa hannu ta fisge hijabin ta ta haye kan gado a 360 tana mai dariya. Murmushi ya saki ya juyo yana kallonta se faman dariya take masa. “Kin min wayo koh?” Abinda yace da ita kenan. Dawowa yayi ya haye gadon shima tare da k’wace hijabin hannun nata jawota yayi ya haye kanta se faman chakulkuli yake mata itako se dariya take harda hawaye tana basa hak’uri ya dena sam yak’i chan zuwa shad’aya suka kwanta a gajiye dan wasan da suka tayi sukayi bacci.
    7:42AM
        Yanzu su Fannah suke gama breakfast. Yau breakfast d’inma a plate d’aya suka yi har suka gama tana zaune a kan cinyarsa, tabashi ya bata ahaka har suka gama karyawan. Tayasa tayi ya gama shiri sannan ta rakosa har bakin k’ofa ta miqa masa lunch pack nasa.
     “My Handsome” ta kirasa.
    “Yes Flower.” murmushi ta saki masa;
    “Yau in ka dawo I’ll reveal my secret for you. Kai mijina ne be kamata ace ina b’oye maka wani sirri na ba zan fad’a maka komai”
    “Are you sure Babe?” ya tambayeta.
   “Yes I am, na yarda da kai dakace baraka barni ba koda kaji wannan sirrin nawa so zan fad’a maka My Husband Baby.”
    Taku d’aya ya k’ara ya rufe gab dake tsakaninsu. “I will never leave you Flower I love you” yayi pecking nata a goshi. “I love you too My Lion take care of yourself for me kaji?”
     “I will Baby.”
    “Me kakeso in dafa maka yau?” Ta tambayesa tana gyara masa necktie nasa daya d’an gauce.
    “Anything yummy” ya kashe mata ido.
    “Okay toh I will cook your favorite”
     “Kina nufin pounded yam da Eghusi soup?”
    “Yes Baby off you go I love you.” Kai ya girgiza mata cike da rashin fahimta ta tambayesa “why?”
    “You don’t love me” yace da ita.
    “Ofcourse I do My King I love you kadena fad’in haka zuciya na bare iya d’aukawa ba.” Hannu yasa ya taro fuskarta.
     “Flower bakiya sona, in har kina sona be kamata ace zan fita office baraki bani ko d’an goodluck kiss ba.”
    Murmushi kad’an ta saki “dalilin dayasa kace bana sonka kenan Baby?” Kai ya gyad’a. ‘Yar murmushi ta saki “wannan bare kawo fad’a ba My Lion.” D’agel d’in k’afa tayi tare da zagaye hannayenta biyu a wuyansa sannan tayi kissing nasa passionately ba kamar jiya da tanayi zuciyarta na bugawa ba, kissing nasa take fiye da yadda tayi jiya duk sun zurfafa cikin abinda sukeyi daga bisani tayi pulling out. Kallon idanun juna suke suna murmushi peck ta manna masa a duka kumatunsa one-by-one sannan tip na hancinsa tayi tayi ta masa a goshi amman takasa dukda d’agel d’in k’afa da tayi. Daya gano haka seya sa hannu ya d’aga ta sama nan ta manna masa peck a goshin sannan ya sauk’e ta.
     “Here are goodluck kisses seka dawo koh? I love you.” Hugging nata yayi “I love you too Flower” daga nan sukayi ba-bye wa juna ya fice. Kan kujera ta fad’a se blushing take tana fad’in “love is the sweetest thing” a ranta “His lips are sweeter than everything and his eyes? OMG!” throw pillow taja ta rufe fuskarta dashi. Shima Anas yana tuk’i amman hankalinsa na akan irin kiss da sukayi sharing da Fannah, “your lips are probably the most sweetest thing I’ve ever tasted Fannah.”
   _3:25PM_
      Fannah tagama duk wani aikin da zatayi, abinci na nan ready ajiye kan dining wanka ta sakeyi tasa wata black lace me torches na pink wanda ya bala’in tafiya da surar jikinta. D’aurin network ta kashe me kyau ta tsara kwalya sannan ta feffeshe jikinta da turare masu k’amshin bala’i. D’akinsa ta shiga ta bud’e wardrobe nasa haka kawai taji bari ta gyara masa dukda kuwa a gyare yake neman abinyi kawai take.
      Drawer’n under wears nasa ta bud’e ta zazzagosu acikin haka diary nasa data soma karantawa da jimawa ya fad’o. A nitse ta d’aga ta miyar ta soma ninke masa boxers da shorts nasa kap ta gama se fad’a mata zuciyarta ke ta bud’e diary’n ta karanta ai matarsa ce ita abinda zata sanar dashi sirrinta itama yau toh se meh dan ta karanta nasa? Hannu tasa wane ana ganinta ta zaro diary’n kwad’o tagani datse a jiki nan tashiga neman key’n cikin inda yake adana cufflinks nasa tasamu ta bud’e. Flipping first 3 pages d’in tayi saboda ta tab’a karantawa. A page 4 d’in taga heading an rubuta da manyan bak’i
 
    THE UNFORGETABLE INCIDENT (THE GIRL)
     Wani irin kishi taji ya gulleta wani girl yake nufi? Dama Anas nada wata bayan ita? So she is not his first love as yadda ya fad’a mata jiya? Bata hankara ba taji hawaye na cikowa a idanunta (Toh fa Fannah uwar kishi) tsuka taja tare da juya pegin ita a dole kishi barata karanta ba. Kujera tanema ta zauna ta soma karanta rayuwarsa na London tana murmusawa tana jin wani sabon sonsa me d’anko yana sake k’aruwa a birnin zuciyarta da zaran taga wajen daya rubuta yasha barasa sekuma ta had’e fuska.
      Dogon tsuka taja sanadiyar ganin mafarke-mafarken yarinyar datake da tabbacin itace wanda yake nufi a page 4 na littafin. Wato ma itace yarinyan dayake mafarkinta time to time yana ce min *_TANA TARE DA SHI?_* Koh”
       “Wallahi Allah kawo ka Anas gaskiya barin yarda ba, waima wace wannan yarinyan?” Duk wannan magana da take a fili take yinsu. Page 4 d’in ta koma ta bud’e tasoma karantawa kamar haka…;
     *© MIEMIEBEE*
TANA TARE DA NI… PAGE 69
BY MIEMIEBEE
Saturday evening Bama, Maiduguri Borno.
 
     Dakata karatun tayi mamaki shimfid’e karara a fuskarta “dama Anas yayi zaman Bama? Wow! Tsaya tukuna ko achan na tab’a ganinsa? Yes definately shiyasa rananda muka sake had’uwa dashi anan Maiduguri naji natab’a ganinsa somewhere ashe a Bama ne. Wow!” Murmushi ta saki ta cigaba da karantawa.
     
    _It pains me writing this, I can’t forgive myself for what I did to this 15 years old girl. I’m so so sorry, I was drunk I didn’t know what I was doing. I blamed everything on her nayi blaming nata akan laifin da ba ita ta aikata ba I’m so sorry I hope we meet in the future saboda in nemi gafararki. Tun rananda abun ya faru na rasa sukuni a rayuwa, I’ve been living a life of guilt. Kullum cikin mafarkin ta nake I don’t know ko tana raye ko ta mutu saboda sautin kukan ta da suke min yawo akai har a yau. Bansan wani erin k’uncin rayuwa na tusa ta ciki ba, believe me wallahi I had no intention of doing so to your precious life. I was densed, stupid and young lokacin my past kept on hunting me sanadin abinda Ummimi tamin my own MOTHER._
     _Da yammacin ranar Asabar, 23rd March 2012_
       Dakata karatun tayi “Innalillahi wa inna ilaihi raj’un!” ta furta cike da rashin yarda tana kad’a kai take idanunta suka cike da hawaye rawa jikinta  ke sosai yana bata wai itace wannan yarinyan da Anas yake nufi itace wacce _TAKE TARE DA SHI_ a kullum “Ya Allah karka tabbatar min da abinda nake zato 23rd March shine ranar da aka k’wace min budurcina aka rabani da martabana na k’arfi da yaji.” Hawayenta ne ya d’iga kan page d’in a yayinda tayi k’arfin hali ta cigaba da karantawa.
 
       _I wrecked a 15 years old girl, nayi raping ‘yar yarinyar da bansan wace ita ba, bansan ya take ba bansan kotana raye kota mutu ba yanzu. Her words are forever stocked in my head._
   
   _“Dan girman Allah bawan Allah kayi hak’uri I beg of you please. Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri I’m just 15 ba abinda zan iya baka have mercy on me please dan Allah.”_
       
        Rufe littafin tayi cike da tashin hankali a yayinda hawaye ke ambaliya a fuskarta kanta yana wani irin juyi ga kuma wani jirin da ta soma ji yana neman d’ibanta tabbas bara tab’a mancewa da wad’annan kalamu ba. Kalamun data ta nanata wa mutumin dayayi raping nata haka tata rok’ansa amman haka ba imani ba tsorom Allah ya danne ta yayi raping nata. Kasa rik’eta k’afafunta sukayi ta sauk’a k’asa se “Innalillahi wa inna ilaihi raj’un” take ta nanatawa. Wani irin k’ara ta saki “Wayyo Allah! Anas… Anas ne mutumin, I married the man who raped me, I fell in love with the man who raped me, mutumin danata had’asa da Allah karya k’wace min budurcina amman yak’i koda tausaya min haka ya danne ni ya amshe min martaba. I married the man who made my life miserable, mutumin daya juya min rayuwa ya raba dani da first love d’ina AHAMD bawan Allan da yasoni tsakani da Allah, na auri mutumin da yayi sandanin rashin lafiyan mahaifina, mutumin daya jefa min rayuwa cikin k’unci da bak’in cikin rayuwa, mutumin daya sani cikin tsoro kowani dare sena tashi ina kuka ina mafarki ze dawo ya sake azabar dani kamar yadda yayi a baya. Innalillahi wa inna-” bata k’are salatin ba wani erin masifaffen kuka cike da azaba ya rufe ta, ihu take sosai wasu irin zafaffun hawaye suna ambaliya a fuskarta se juyi take kan rug d’in (k’aramin carpet) ji take kamar ranta ze fita, wannan wace erin rayuwa ce?
   
      “No this can’t be Ya Allah kasa mafarki ne wayyooo!! this can’t be happening mesa ban tab’a gane shine wanda yayi raping d’ina ba? Am I that stupid da har na fad’a soyayya da mugun mutumin daya cuceni har abada? Taya tun rananda naga wancan babban ciwon dake hannunsa na kasa gane a ina na tab’a gani? Taya nakasa recognising blue eyes nasa Why am I stupid?” Kai take kad’awa a yayinda kukan ta ya tsananta har wani sama sama nishinta yake tafi minti talatin tana kuka kamar wacce ta zare, idanunta sunfi jan kala shiga rabuwanta da tashin hankali irin wannan tun lokacin da abin ya faru. A sannu a sannu ta rarrafa wajen drawer’n ta miyar masa da littafin ciki har ayanzu kuka take ba makawa da k’yar ta ja kanta d’akinta tasa key ta rufe sannan ta baje kan gado, d’aurin kan nata ta sinche tasake k’urma wani irin balad’ad’d’en ihu tana jan bedsheet na kan gadon tana duk’unk’unewa a hannunta. “Anas mesa zaka min haka? Mena maka? Mesa seni? I thought I could trust you Anas why does it have to be this way? Wayyo Allah wayyo kaina.” ta rik’o kanta dan wani erin ciwon fitan hankalin da yake mata. “I married a monster. Ya Allah tanan ka kamani akan qaryan danayi ma iyaye na nasasu suka amince auren soyayya mukayi da Anas? Ya Allah na tuba kayafemin badan hali na. This is a dream ba reality bane it can’t be it just can’t be.”
 
      Kuka Fannah ke kamar zata cire ranta har cewa take a ranta ina ma Allah ya d’auki ranta kawai ta huta dukda tasan yin hakan haramun ne, amma kuma da living irin wannan rayuwa gara mutuwa, bayi ma Allah shisshigi ba amman mesa rayuwarta take haka? Daidai lokacin data sama wa zuciyarta sukuni ta fara son Anas hakan ze faru why? Why? Kuka ta cigaba da yi ciwo kanta yake mata kamar ze tsage amman still tak’i barin kukan tun hawaye na zuba har hawayen nata ma yayi seizing, shima muryan nata ya d’auke dan irin ihun data riga yi amma haka tacigaba da kukan ba sauti saboda rashin tausayawa kanta. Wannan wace erin jarabawa ce? Ka auri mutumin da yayi raping naka ba nan kad’ai ba har ka soma son meshi. Wace erin k’addara ce haka?
        “Zama na a gidan nan ya k’are barin iya cigaba da rayuwa da mutumin daya rabani da farin cikin rayuwa naba, barin iya cigaba da rayuwa da kai ba Anas.” Murmushin takaici ta saki “mesa ma nake son sanar dakai sirrina bayan kafi kowa sani? Bayan kafini ni karan kaina sanin wannan sirrin, nayi sakaci da sallolin dare da addu’o’i na shiyaza har na aureka ban gane kaba. Anas abinda kamin is UNFORGIVABLE ka dawo ka sallameni kawai inkuma barakayi ba in tattara kayakina inbar maka gidanka I can’t continue living you with Allah kad’ai yasan abinda zaka iya min nan gaba.”
   
4:21PM
   
    Daidai nan Anas yake dawowa daga office cikin jin dad’i ya miyar da k’ofar ya rufe, he can’t wait ya sa Flowersa a ido. Flasks yaga suna masa sallama kan dining table wanda kobe bud’e ba yasan favorite nasa ne ciki ba abinda yakeyi aransa banda sawa Fannah albarka besan ya rayuwarsa zata kasance ba Flowersa ba. Kitchen yauma yasoma lek’awa beganta ba daga chan yayi d’akinsa. Murmushi ya saki danko yanada tabbacin a d’akinta take. Bayan ya rage kayan jikinsa ya nufa d’akinta sede tun daga nesa yakeji kamar sautin kukan mutum… Kukan mace… Kukan Fannah OMG! “Flower” a rikice ya kira sunanta ya k’arisa k’ofar d’akin ya gwada bud’ewa suprisingly yaga a rufe da lock. Tana jin k’ara ta miyar da kallonta kan k’ofan.
      “Fannah! Fannah! Open up please mesa kike kuka? Dan Allah stop it kitaso ki bud’e min k’ofan please.” Kukan nata ne ya tsananta daga jin muryarsa. “OMG! Fannah whats wrong? Why are you crying dan Allah ki bud’e” yayi stating cike da tashin hankali bare iya jure kukan flowersa ba meya sameta? Meyasa take irin wannan matsanancin kukan? Bubbuga k’ofan yake da k’arfin da Allah yabasa amman yakasa b’alla gun lock d’in dake security door ne.
        Tana tsugune a k’asa se kuka take sha kamar ba gobe.
     “Dang it!” Ya buga k’ofar a fusace se a yanzu ya tuna da akoi spare key a 360 ya wuce d’akinsa yaje ya binciko ya ciro da sauri ya dawo yasa ya bud’e k’ofar. Da gudu ya nufi k’asa inda ya ganta ko d’ago kai ta kalle sa batai ba tsugunawan yayi shima a gabanta cike da tashin hankali da tsantsan tausayi. “Flower” ya kira sunanta cikin sanyin murya cike da tausayi. “Flower dan Allah kibar kukan nan please ya isa dan Allah” ya sanar da ita muryarsa har shaking yake dan tausayi. Ko d’ago kai ta kallesa batai ba se kuka take ba makawa hannu yasa ya dafe kafad’arta hannunsa na tab’a ta ta d’ago kai a firgice ta matsa baya sekace taga aljani. Beso sake ganin fuskarta ba dan yadda ya kumbura gakuma wani irin mahaukacin jan da idanunta sukayi besan seda idanwansa shima suka cike da hawaye ba.
 
     “Fannah why are you crying like this? Meya sameki?” Hannunta ya gwada rik’ewa a firgice taja baya tana matsawa baya daga garesa ganin haka yace, “Fannah Anas ne ba mutumin ba, kinji?” gabad’aya yagama zato ko mafarkin mutumin data sabayi ne tayi take irin wannan wahalallen kukan. Kai kawai take girgiza masa. “Its me Anas your husband bawani ba come kinji?” kai ta kad’a masa  ike da tsoro daga gawani irin kallon da take masa. A guje ta ruga bayi tasa key ta rufe a gujen shima yabi bayanta cike da tashin hankali. “Fannah meya faru dan Allah?” Jikinsa ne ya soma basa ba mafarki tayi ba to mene neh? Ko rasuwa akayi mata? Amman ai in rasuwa ne da shima za’a kirasa a sanar dashi.
      “Fannah I beg of you dan Allah kibud’e please.” Sautin kukanta ta tsananta tana tsugune k’asan bayin se kuka take kamar zata cire ranta. K’ofar yake ta bugawa ba yadda beyi ba dan b’allawa amman ya kasa besan lokacin da hawaye tsili-tsili suka soma gangaro masa kan kumatu ba. Da kukan Fannah ya gommaci yarasa duk wani abinda ya mallaka a duniya.
      Daga k’arshe ma kasa rik’esa k’afafunsa sukayi sauk’a yayi har k’asa hannun sa dafe jikin k’ofar “Fannah koda baraki bud’e k’ofan ba please kibar kukan dan Allah kibari I can’t take it please I beg you.”
     Har ayanzu batajin zata iya dena kukan ba. “Fannah dan Allah fa nace kibar kukan please ya isa haka nasan kinada qwararran dalilin dayasa kike haka becuase I trust you Fannah and I love you please come out kinji? Barin bar nan ba sena gankin Flower” ba irin rok’ar duniyan da be mata ba amman sam tak’i bud’e k’ofar. Ga wani irin masifaffen yunwan dake cinta rabuwanta da abinci tun breakfast gara shi Anas d’in yachi lunch a office. Har Maghrib suna nan ahaka ganin lokacin Sallah ya shiga yayi k’arfin hali yace, “Fannah kifito kiyi Sallah kinji? Nasan koda zan had’a sama da k’asa bara ki bari in ja muba so kifito kiyi naki nima zanje inyi nawa, I love you.” Yana kaiwa nan ya fice seda ta jiyo k’aran rufe k’ofa sannan ta dage ta yi alwala har wani dashi dashi take gani dan ciwon kai dakuma tsantsan yunwa. Cike da tsoro ta bud’o k’ofan bayin kad’an ganin baya cikin d’akin ta d’an taka da wuri ta zaro spare key ta bayan k’ofar ta sake locking abinta yadda bare iya shigowa ba again.
       Yin Sallan kawai take badan tasan me take karantowa ciki ba dan tashin hankali ko raka’a uku tayi ko had’u tayi bata sani ba se Allah shima Anas ta b’angaren sa haka ne. Yana sallamewa ya d’ibi hanyansa back to d’akinta nanma yaga ta kuma rufewa gashi ta zare spare key d’in. Kai gaskia ba lafiya ba what is wrong with Fannah? why is she acting thsi way? Ko an mata wani abu ne? The real question is ko nine na mata wani abu bisa rashin sani. Tsayawa yayi yana nazarin abubuwa sam bai tunanin da akoi aami abinda ya mata wanda za’a ce shi yayi hurting feelings nata haka. Barin maganar zucin yayi a haka “Fannah nasan kina jina I don’t know what got into you sabida ban tab’a ganin ki a yanayi irin na yau ba ko abinci kink’i chi tun d’azu nake miki magana amman kink’i tankani I can’t take it anymore. Please in wani abun na miki wanda yayi hurting naki haka I’m sorry kiyi hak’uri dan Allah ki sanar dani na zauna nayi tunanin duniyan nan amman na kasa tuna koda abu d’ayan dana miki da zesa ki shareni haka yau har ki rufe kanki a d’aki. I’m sorry I’m truely sorry ko abinchi ne kifito kichi not for my sake but for your health’s, I love you.” Ya sanar da ita cikin cracky voice yana kaiwa nan ya wuce d’akinsa ko maybe intaji alamun ba motsinsa zata fito.
      Kalamunsa masu narkar mata da zuciya taji bata k’aunar sake sauraronsu ko k’arfin kuka batada. 20 minutes later bayan ta tabbata baya bakin k’ofar ta mik’e tana dafe dafe har ta isa bakin k’ofar ta bud’e a hankali, leqawa tayi da kyau bata ganshi ba sannan ta sa kai tajeta dining area ta d’ibo abinci kad’an kan plate ga yunwa har yunwa amman ba tajin zata iya chin abincin ma. Ruwa ta cido daga fridge d’in takama hanyan komawa d’akinta gabanta ne yayi mumunan fad’i ganin Anas da tayi tsaye jikin k’ofar d’akinta, data kallesa seta gano yayi kuka shima. Toh kukan meh kuma zeyi bayan abinda ya mata shekaru had’u koma tace biyar da suka wuce. Kai ta soma kad’awa take hawayen ta da sukayi seizing suka soma sauk’owa. A hankali take ja da baya baya wane taga aljani.
       “Fannah please why are you doing this?” Ya tambayeta cikin wani irin salo. “Mesa Flower? Meya faru? In ni na miki wani abun I’m sorry dan Allah ki sanar dani mistake nawan se in gyara kefa kike cemin a baya silence is never the solution to a problem amman kuma kikeyi yau please talk to me.” Kai still take kad’a masa ga wani irin b’arin data soma yi hawaye se ambaliya suke kan kumatunta. Taku ya soma yana nufanta.
      Takasa furta koda ‘A’ se baya baya take har ta isa jikin bango bebar binta ba alokacin da ya rage saura befi taku uku tsakaninsu ba nishinta ya soya tsabagen b’arin da hannunta suke batasan lokacin da ta sake plate da gorar ruwan a k’asa ba. “Tata tas!!” kukeji k’aran fashewar glass.
© MIEMIEBEE

tana-tare-dani.jpg TANA TARE DA NI… PAGE 70 BY MIEMIEBEE Miyan kap jikinta ya zube shima Anas yad’an tab’a sa kad’an. Irin rikicewa da b’arin da Fannah keyi ko gamo mutum yayi da aljan bareyi irinsa ba take ta tsuguna tasoma tattarawa abinda Anas ya tsana kenan ya washi yaganta tana picking broken glasses da hannu. Kafin yace tabari ko ya d’aga ta aikin gama ya riga ya gama kyat! Ta yanke a yatsanta k’ara sosai ta saki kamar a kyaftawan ido ya k’ariso gabanta hannayensa na sauk’a akan jikinta ta tsala wani irin rikicaccen ihun da shi kansa seda ya firgita. “Fannah please what is wrong with you? Anas nefa ba wani ba, its Anas your husband mesa kike haka da zaran na tab’aki ki rikice? Muga hannun” da zaran ya matso ze tab’a ta seta sa ihu ko magana takasa masa duk tabi ta tsure ta gefensa tabi da gudu da sauri ya cafko ta da hannu ya dawo da ita baya. “Fannah what is your problem why are you acting like this? Mena miki kike gudu na kamar kinga mala’ikan d’aukan rai, what is it tell me?!” Ya k’are maganar cikin sautin tsawa saboda he can’t take it anymore taya matarsa zata na gudunsa haka. Hannun nata take ta k’ok’irin fisga amman takasa hawaye kam sekace lalacaccen famfo. Bright blue eyes nasa da suka zamanto dull and weak dan tsantsan tashin hankali ya d’agosu a maraice yana kallonta se k’ok’arin karb’an hannunta take amman takasa. “Fannah mena miki? Ki fad’a min please, OMG!” Yayi exclaiming alokacin dayaga yadda jinin jikinta ke zuba a k’asa. Hannunta yasoma ja zuwa d’akinsa. Sam tak’i bud’e baki ta masa magana se hawayen da takeyi ganin sunkusan kai ga d’akinsa ta ja hannunta da k’arfin da Allah yabata seda ta fisge daga rik’onsa. “Fannah please don’t go…” bata ko sauraresa ba ta ruga d’akinta a guje tare da sa lock. Har k’asa ya sauk’a wasu irin zafaffun hawaye na maza suna sauk’owa tsili-tsili a fuskarsa. “Why Fannah? Mena miki? Your silence is killing me why are you punishing me like this?” Itama Fannar ba abinda take banda kuka, wanke ciwon nata tayi se kuka take ga wani irin yunwan dake azabartar da ita batajin zata iya kwana inbatasa wani abu acikinta ba. Rarrafawa tayi zuwa fridge na d’akin hamdala ta saki ganin da akoi cookies da drinks uku ciki. Ledar cookies d’in ta ciro ba makawa ta soma kaiwa cikinta seda taci fiye da rabi sannan ta kora da fanta nan ne tad’anji dama-dama. K’aran shigowar sak’o taji a wayarta kamar wacce barata duba ba sekuma ta miqe ta bud’e taga saqo ne daga Anas ta karanta kamar haka; Fannah please in wani abun na miki ki sanar dani stop punishing me like this zuciyana bare iya d’auka ba please Flower I’m missing your smile, body, and fragrance already open the door for me please. I love you #crying Wani sabon kukan ta fashe da har k’asa ta sauk’a tana birgima a kan rug na d’akin. Anas dake bakin k’ofar ji yake kamar ya b’alla k’ofar yashiga if only he could. “Fannah please stop crying kinji dan Allah kibari… Kidena please stop it” yayi stating cikin sautin kuka. Zama yayi bakin k’ofar yana hawaye tana kuka. Isha nayi ya rok’eta da ta tashi tayi Sallah ba gardama ta d’au hijabin ta tayi Sallan kamar yadda shima yayi a parlour bayan yagama shafa’i da wutr nasa ya dawo. “Fannah kifito kichi abinci kinji? I get it bakison sake sani a ido, zan koma d’aki sekin gama infito kinji? I love you.” Yana kaiwa nan ya juya a sanyaye kamar wanda k’wai ya fashe mai a ciki ya nufa d’akinsa bayan minti ishirin ta bud’o d’akinta a hankali, parlour ta nufa dan tattara wajen da plate ya fashe mata d’azu to her suprise taga wajen tsaf ko alaman miya babu tsaf Anas ya share yayi mopping. Dining area ta nufa ta d’iba abincin kad’an se sauri take kar ya fito su had’u gefen flask d’in taga wani paper hannunta na b’ari ta d’aga ta karanta. Flower please wear the plaster and cover your wound please kinji? I’m sorry. Wani sabon kukan taji yana k’ok’arin rufeta ga plaster’n tana gani amman batajin zata iya d’agawa, miyar da paper’n tayi ta ruga d’akinta a guje ta baje kan gado, ta cigaba da kukan daga inda ta tsaya. Bayan shiganta da kamar minti uku Anas yafito daga d’akinsa wajen daya ajiye mata paper’n ya nufa disappointedly yaga bata d’aga plaster’n ba to ko bata fito bane? Flask d’in ya bud’e yaga da alaman ta d’iba abincin mesa bata d’au plaster’n toh? “Fannah haka kika tsaneni yanzu? Bakiya son koda help d’ina?” Ya k’are maganar da hawaye na gangarowa daga kumatunsa guda. Hannu yasa ya share ya koma bakin k’ofar d’akin ta ya zauna yana sauraron sautin kukanta yana hawaye shima har bakin sa yayi dogo da ce mata tayi shiru amman tak’i. K’arfe 9:00PM na bugawa ya mik’e “Fannah anan zaki kwana?” Ya tambayeta tana jinsa amman tak’i amsawa dan batada burin sake masa magana a rayuwarta again. “Fannah kifito muje mu kwanta kinji? I can’t sleep without you by myside please kifito.” Sautin kukanta yaji ya k’aru. “Flower kibar kukan nan please…” ba irin rok’ar duniyan da be mata ba amman tak’i bud’e k’ofar ta kuma k’i barin kukan, ga wani uban ciwon kan da ke cinta. D’akinsa ya koma ya d’ago pillonsa da bargo ya dawo bakin k’ofar d’akinta ya shimfid’a ya kwanta kai be damu da uban sauron Maiduguri ba all he knows is that he don’t want to leave his flower alone. “Fannah goodnight, I love you so much.” Alokacin da yayi maganan tana kwance kan gado ta d’au tafiya yayi wani irin tsoro taji ya ratsa ta ko kashe wutan d’akin ta kasa, duk’unk’une kanta tayi cikin bargo se b’ari take cike da tsoro. Tafi awa d’ai tana neman bacci sannan a wahale yazo mata. Anas kam sam ya kasa bacci he is missing her in his hands se juyi yake amman ya kasa bacci bare iya kwatanta how he is missing her legs wrapped around his body ba. *** 2:34AM Firgit Fannah ta farka dan wani erin masifaffen mafarkin datayi. “Anas!” ta kira sunansa da ihu take ya jiyota dake daman baccin nasa beyi nisa ba. “Fannah” ya kira sunanta tare da mik’ewa. “Fannah I’m here kinji?” Kuka take sosai cike da tsoro duk ta duk’unk’une kanta da bargonta ta cusa kanta cikin cinyoyinta se kuka me sauti take. “Anas” ta sake kiran sunansa. “Yes Fannah I’m here please stop crying bud’e min kinji please I beg you…” Har a yanzu bata bar kukan ba. Zaman gadon ne ya gagareta ta tako zuwa bakin k’ofar ta tsaya adaidai lokacin yake kiran sunanta again “Fannah.” Kuka ta fashe da, yana jin muryarta kusa dashi hankalinsa ya sake tashi. “Fannah, Fannah ki bud’e min kinji? Let me in please.” Kuka take sosai ta inda yakejin sautin kukan nata ya matso tare da had’a kansa da wajen “Fannah I’m here please kibar kukan.” K’asa ta sulale kamar yana ganinta shima ya sauk’a. Hannunta ta aza jikin k’ofar tare da dafe kanta jikin k’ofar tana me cigaba da kukan. Daidai inda hannunta yake ya aza nasa shima “Flower I’m here you are not alone I’m here with you kibar kukan kinji?” A hankali taji tsoronta na gushewa da dad’ad’d’un kalamun Anas awajen bacci ya d’auketa tun Anas najin k’arfin nishinta har yazo yaji shiru hakan ya tabbatar masa tayi bacci anan ne shima yasamu ya d’an kwanta although sauro sunk’i barinsa saura na masa waqa a kunne saura suna cizon sa farin fatarsa duk yayi pink amman haka ya hak’ura dan baison barin Fannah ita kad’ai ahaka har Asuba tayi bayan ya idar da nasa ya gama addu’o’insa ya dawo ya soma kirar sunanta a hankali cikin baccin tasoma jin sunanta. “Fannah ki tashi kiyi Sallah kinji? Asuba yayi. Fannah tashi kinji?” A kasalance ta mik’e ta nufa bayi ta d’auro alwala tayi Sallah sannan ta koma kan gado ta kwanta har a yanzu Anas ya kasa bacci. Ko kad’an baijin ma ze iya zuwa office yau, bare iya barin Fannarsa awannan hali ba. Se anan ne yasamu yayi bacci shima 9:45AM ya tashi har anan Fannah na bacci tattara bargon nasa yayi ya wuce d’akinsa yayi wanka sannan yayi shirinsa na kullum fridge ya dosa ya ciro irin sliced potatoes d’innan da ake packaging ya musu frying da omalet ya had’a musu breakfast. Cikin awa d’aya dining table is set agogon hannunsa ya duba yaga 11:02AM knocking yaje yayi a k’ofar d’akinta alokacin da take fitowa daga wanka kenan. “Fannah kin tashi? If yes good morning kifito ki karya kinji? I love you” yana kaiwa nan ya koma dining ya soma zaman jirarta. Kukan dake son k’eto mata ta shanye simple doguwar riga tasa bak’i me silky jiki. Babban akwatinta ta ciro ta soma tattara kayakinta wanda zatayi amfani dasu ciki. Dam ta cika da essential stuffs nata ba mantuwan da tayi tana gama had’a akwatin ta ja ta rufe sannan ta zira hijabinta dogo har k’asa ta d’au wayarta sannan ta soma ja, a hankali ta bud’e k’ofar ta fito tafiya take kanta a sunkuye da jakarta tana ja daidai ta iso parlour ta bayyana a idon Anas. Kasa believing abinda idanunsa suke gane masa yayi. What is he seeing? Ina Fannah zataje da wannan babban akwati? Ganin se dosan bakin k’ofa take ya k’urma mata kira “FANNAH PLEASE STOP!” A guje ya nufa inda take, k’ara saurin tafiyar ta take gabanta yasha da wuri idanunsa take suka kad’a sukayi ja. B’ari bakinsa yake kalamunsa suna stammering “Fa.. Fan.. Fannah meh wannan? Ina za kije? Meke faruwa Fannah? Tafiya zakiyi ki barni? Mena miki Fannah? Dan Allah karki tafi in wani abin na miki tell me I’m sorry for everything that I’ve done I’m sorry please karki tafi.” Ya k’are maganar cikin sautin kuka. Zuciyarta taji ya karye, batasan seda hawaye suka soma ambaliya a fuskarta ba sam ta kasa dena kukan musamman ma dataga alaman cizon sauro all over his face and hands nufin a waje ya kwana yana gadinta jiya. “ Fannah please karki tafi mena miki da zaki tafi? Kiyi hak’uri dan Allah.” Hannunta yayi yunk’urin rik’ewa baya taja da wuri taja akwatin nata tabi ta gefensa da wuri ya rik’o hijabinta. Abin da be tab’a faruwa ba ya faru yau. Mr. Fauzi ya sauk’e girman kai da duk wani feeling daya keyi ya sauk’a har k’asa akan knees nasa duka biyu. Hawaye yake sosai “Fannah please don’t go dan Allah karki tafi. In wani abun na miki please let me know.” A nitse ta juyo ganinsa akan guiwowinsa ba k’aramin mamaki ya bata ba. Idanunsa a raunane ya d’agosu yana kallonta duk setaji wani iri tasa mijinta kneeling tace masa ya tashi kuma batason sake masa magana ganin yadda yake kuka itama ta k’ara k’arfin nata kukan. Juya masa baya kawai tayi batason ganin hawayensa kamar yadda shima baison ganin nata. “Fannah turn and look at me please mesa zaki tafi? Mena miki? Kinsan barin iya rayuwa ba ke ba please karki tafi Fannah in wani laifin na miki ki sanar dani dan Allah.” Juyowa tayi cikin sautin kuka ta soma magana har wani sama sama nishinta yake. “Anas are you serious? Bakasan me kamin ba? Kana nufin har a yau baka gane ni ba? Kana nufin baka san yarinyan dake _TARE DA KAI_ ba har a yau?” Cike da rashin fahimta ya taso “Fannah what are you talking about? Wace yarinya kike nufi?” Hannu tasa ta share hawayenta kamar yadda yayi shima. “Anas kaine mutumin, kai nake mafarki kullum zaka dawo ka sake azabartar dani kamar yadda kayi 5 years back. Anas don’t you get it? I’m the girl, nice yarinyan… Ni kayi raping 5 years bacm. Nice yarinya from the incident a Bama na yammacin Asabar 23rd of March…” Sekuma ta fashe da wani irin masifaffen kuka. K’wak’walwarsa kasa d’aukan abinda ke faruwa yayi. Se kai yake kad’awa yana salati a ransa da k’yar bakinsa ya bud’u cike da tashin hankali da rashin yarda yace “no you are not Fannah, you are not the girl inda kece da nayi noticing naki bake bace Fannah baki gane bane taya ma kika sani? I never told you.” “It doesn’t matter ‘cause I read your diary Anas ni kayi raping. Anas nice yarinyan da ka raba ta da budurcinta, ka cuceni Anas saboda kai nida family na muka bar Bama muka bar ‘yan uwanmu, saboda karya me bin maza da ‘yan unguwa ke kirana dashi muka bar Bama a sanadin abinda kamin, saboda abinda kamin Anas ka rabani da first love d’ina AHMAD wanda yasoni tsakani da Allah, saboda kai na rasa gatana, sabida kai Ya Farouq da Baffah Khaleel suka samu baki suke zagina suna kirana karuwa saboda abinda kamin kasa Baba ya kamu da ciwon zuciya Anas you are the source of my sorrow and fear. Mena maka Anas? Mena tab’a maka daka gommaci ka k’untata min? A rayuwa ba abinda naso kamar in gyara maka rayuwarka and I did mesa ni baka min haka ba? Mesa ka shafawa rayuwata bak’in fenti Anas? Barin iya zama dakai ba, barin iya cigaba da zama da mutumin daya cuceni kamar yadda kayi ba. Ka sallameni in tafi gida ka sallameni inkoma gun Mami na dan Allah karka hanani takarda na. Anas I’ve loved you but not anymore, I thought I could trust you why is the handsome Anas I know turning into a monster? Ka sallameni dan Allah…” © MIEMIEBEE

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *