THE NEW EMIR (SARAUTA) CHAPTER 1 BY NIMCYLUV

 THE NEW EMIR (SARAUTA) CHAPTER 1 BY NIMCYLUV 

   Anties a kakkaɓe zani banso na saki ba,domin ban shirya hakan yanzu ba,amma naga kamar kun fini damuwa dashi dole nai ƙwanan zaune domin yi maku typing hope zaku amshesa kamar yadda yazu da zafinsa,ni bana da wani warning a kan book ɗin nan,abinda kullum nake faɗa kada kayi karatu danjin daɗinka ko shauƙinka,kayi karatu dan wasu muhimman abubuwa da suke cikin labarin domin zaisa ka amfana da hakan,so

dayawa wasu basu gane hakan sun ɗaukan luv ɗin ciki whatever dai ga THE NEW EMIR nan ya taɓa ko ina kada a fara karatu zai an wanke hannu kuma ansa face mars😂 ok Nimcy taku tana maku sahihiyar ƙauna

_Britol place hotel_

 “for God sake” ya ƙarasa magana cikin muryarsa da bata fita sosai sabida ƙarfin mulki da kuma jinin sarauta dake yawo cikin jikinsa.

Cikin kuka da kuma takaicin rayuwarta Seenat ta kalle shi na wani lkc kafin a hankali ta janye idanunta daga gareshi,sbd sam taba jure kallo cikin idanunsa sosai suke mata kaifi tare da cika mata idanu,Allah yay masa baiwar hallitta ƙyau tsari ga kuma izza irin tasu ta masu sarauta,tabbas idan ta sameshi matsayin miji ta gama jin daɗin rayuwa tayi duk wata ɗiya mace nisa,nisa kuma mai tsayi,idan mafalkinta ya tabba tasa she move “Yes” move ɗin da babu wanda zai tadda  ta,but how can that happen,bai sonta bai son ta raɓesa why ƙaddarar soyayya yaci gaba da haɗasu a wajan da masuyi tunani ba,saukar muryarsa a kanta yasa tayi saurin jan idanunta tare da mannasu a kanshi,kasa control  kanta tayi hakan yasa ta faɗa jikinsa ba tare data san hakan ba,cikin kuka tace.

“zuciyana ciwo Lil Prince,sai yaushe ne zaka barni haka? Sai yaushe zaka amshe ni as ur luv i luv u,soyayyarka ƙaddarata ce dan Allah ka amshi jaririyar zuciyana pls”

Dryar mugunta yay wacce ta fitu da ɗan ƙaramin sauti,Alkabbar jikinsa ya gyara tare da murza daimond ring ɗinsa,numfashi yaja kafin ya cireta jikinsa yace.

“look Haseenatu put ur eyes ball to me, am not stupid ni ba age mate ɗinki bane daza kina yimin rubish,bazan iya sanya ki a zuciyana ba saina amshi virgin ɗinki idan kin amince da hakan fny nima a shirye nake domin kuɗi masu yawa nasa na kama wannan ɗakin,idan baki amince ba saiki shamin lpa”ya ƙare zancen yana jan numfashi mai ƙarfi.

Da mamaki Seenat take kallonsa ace mutumin da mutane suke ganin dararja yana matsayin babba ɗan sarki amma shike lalata al’ummarsa wannan wacce irin rayuwace? Mai yasa a koda yaushe manyan gari sune suke aikata zunubai a ban ƙasa kuma zunubai mafi muni,Tayaya za’a samu ƙwanciyar hankali,Mai kuɗi ya hulaƙanta talaka,masu mulki su wulaƙanta talakawansu,shugabanni su tauye haƙƙin na ƙasa dasu,mazaje su tauye haƙƙin matansu,malamai suci zarafin ɗalibansu,ƴan siyasa su lalata yaran mutane ta hanyar basu manyan drug,ya rabbi wannan wacce kalan lukutan masiface,wannan giremamman abun yafi tunanin dukkan mai tunani,yaushe za’a samu sauyi a gari yaushe ƙasa zata dai²ta a samu nutsuwa,ya rabbil izzatu ka kawo mana mafita,Ina sonshi ina ƙaunarsa ina jin zan iya amincewa da buƙatarsa Ubangiji kada ka kamani da laifin aikata Zina,ina da rauni a zuciya ban iya hqr da abinda raina sa ruhina ke buƙata…’

“Damn it” Lil prince ya faɗa  yana ƙoƙarin ficewa daga cikin ɗakin,Sauri miƙewa Seenat tayi tare da kama hannunsa cikin sanyin murya tace.

“na amince indai zan samu luv and care naka”takai ƙarshen mgnar,Killer smile yay tare da murza hannuta dake cikin nasa yace “good gril” yana faɗin hakan yay sauri haɗe bakinsu waje guda ya suma ya mutsata Haseenatu kam dukkan jikinta rawa yake yayinda zuciyarta ke bada wani sauti mai tafiya da numfashinta,yayinda da take jin wani baƙin ciki yana sauka a cikin zuciyarta,sosai Lil prince ya samu nasarar rabata da kayan jikinta kana ya jefata saman makeken gadon take mamallakin hotel ɗin,babu kunyar cewa shiɗin mutum ne mai ƙima da kuma dajara a idanun mutane ya shiga aikata ta’asarsa son ransa,sosai ya muri jikin Seenat hakan yay masa daɗi,Seenat kam faɗin wahalar data sha ba’a magana,sai da yay wajan1hour sannan ya samu nutsuwa ya zare jikinsa a nata,wani mugun murmushi yay cike da mugunta yace.

_Masarautar Kano_

Gida ne na sarauta wanda ni ban isa na fasalta maku tsarin gidan ba,sai da dukkan wanda ya karanta yay tunanin tsarin gidan,sbd dukkan wani da akace sarauta ya fita daban sa sauran,kuɗi,iko,mulki,izza,da sauran abubuwa najin daɗin rayuwa,gida ne wanda idan baki bai isa yafi adadin kuɗi da aka tsareshi ba,tabbas sarkin wannan masarautar yana ji da kuɗi da iko haɗi da zunzurutun mulki wanda ya gajesa,a tarihi musan cewa babu wani wanda ya isa ya gani ya hau mulkin wannan masarauta indai ba gada yay wajan mahaifi ko kuma kaka ba,alaƙa dai mai ƙarfin gske itake sawa a gaji mulki,shin wannan Sarki gada yay ko kuma taka haye yayi? Wannan sarki mai adalci ne ko kuma azzalumi ne mai cin zarafin al’ummarsa da tauye masu haƙƙinsu kamar yadda Haseenatu ta faɗa? Shin wannan sarki halinsu ɗaya da Lil prince ko kuma aƙwai banbanci?.

Baka ganin komai cikin makeken gidan Sarautar sai barori da kuyangi haɗi da fadawa da kuma maharba haɗi da masu tsaron ƙofa,ko wanne tawaga da nau’in uniform ɗin jikinsu Farin yadi na Kuyangi,Jaa da green na Fahadawa,blue na Barori,yayinda baƙi yake na masu tsaron ƙofa.

Fituwarsa kenan daga  cikin Fada wanda yanzu ne lkcn wutawarsa a gida da kuma kaɗai cewa da iyalinsa,Sanye yake cikin wata duguwar Alƙabba da kuma wanda tsarinsa daman idan yana gida bai fiya zama da babbar Alƙabba ba,shigace sosai ta alfarma mai kaɗan milk da  ash,hannayensa sunji ring ɗin daimond da  glod gefe guda sandar girmansa ce,ta azurfa sai ƙyalli yake,komai na turakarsa an tsara sa ne da azurfa,manyan amintattun Kuyangin sane a gefe suna masa firfita,yayinda Gilishi ke gefensa tana yanka masa Apple da kayan fruit,cikin girmamawa tace.

“Allah yana da ƙwana ya baka tsawon rai,ina ganin   lkcn da za’a zaɓawa Lil prince mata yayi hakan zai ƙara maka girma idanun mutane,kafin kayi murabus na tabbas Prince lkcn ya tara zuri’a kaga dole ya gajeka ko ana so ko ba’a so,balle maganarka tamkar umarni ne a wajan talakawanka sai da baka faɗa ba,ranka shi daɗe a yafan idan nayi kuskure”ta ƙare mgnar tana ƙasa da kanta.

Murmushi yay wanda bai kai ga bayyanar haƙwaransa ba,cikin muryarsa mai amo waccw bata fita saisa gargaɗi a cikinta yace.

Uhm muna gdy Kilishi kunyi tunani mai kyau,amma bamu takurawa Prince coz abinda yakeso shi nakeso uhm farin cikinsa shine namu,amma zamuyi tunani a hakan yaka”

Jinjina kai tayi cike da gamsuwa,ciki ƙaunar mijin nata ta miƙa masa Apple ɗin data yanka,dakatar da ita yay ta hanya girgiza kai alamar bai so,kiɗan sarewa ne ya fara tashi cikin tafkekiyar wayarsa,da hannu yaywa Kilishi nuni datai picking kuma tasa a handfree,kirari aka shigayi masa wanda yake jin daɗinsa har cikin ransa kafin mai kiran yace.

“Kaga sarkin da babu kamarsa sarkin sarakuna faɗe taka cikawa tamu dukkan wanda yay ja dakai shizai ƙwana,Allah ya ƙara girma da ɗaukaka aƙwai matsala fa,idan babu damuwa a yau ina son ganinka a garinmu na Kogi domin bakina bai isa ya furta wani abu gareka ba,amma zuwanka shizai warware mana komai,nida a sanina babu wanda ya tsira a ahalin Yayanka Sarki Sufwan Sufrak dukkansu mun kashesu hatta Yarima Bilyamin bamu barshi ba,amma abinda nagani yau yay matuƙar tsoratani domin nasan allon sihirina bayan gayan ƙarya dasai nace yaymin ƙarya idan nayi laifi aga farceni ya shugabana”

Sosai Mai martaba ya shiga tashin hankali amma sbd tsaurin rai irin nasa baka isa ka fahimci komai a garesa ba,cikin murya da mulki ya gama ratsata yace “On mah way”.

*** ***

“i can’t loving u bby gril” cewar Lil Prince,zuba masa idanu Seenat tayi tana jin zuciyarta na zafi haɗi da turiri zafi baƙin cikin rabata da budurcinta da Lil prince yay,da amince dashi yaci amana kuma ya yaudareta mene makomarta wajan Ubangijinta me zata gayawa Allah idan ya tambayeta laifin data aikata garesa,tasan cewa ba komai mene Ƙaddara ba wani abun ana fakewa da itane alhalin ba ita bane,amma tasan soyayyar data ƙewa Lil prince ƙaddarace tabbas tata ƙaddarar kenan,bata da ikon hana zuciyarta abinda ta tsara,zuciya bata mutum ba,ba ƙashi kuma bata da girma,ba mutum ne ke faɗawa soyayya ba,soyayya ce ke faɗawa mutum kamar  ta faɗa mata,to meye laifinta dan zuciyarta taso shi? Cikin muryar kuka tace “ka cuceni” ganshin kansa ya shafa lkcn harya gama sanya kayansa yace “i know” yawo ta haɗiye mai ɗaci tace “Allah bazai barka ba”ta faɗa lkcn numfashinta ya fara sama,nanma murmushi yay yace “i know,idan kin tashi ga kuɗi nan ƙyayi using dashi idan ƙwai buƙatan ganinki zai kiga ɗan aike”

  Girgiza kai tayi cikin fitar hayyaci yace “nasan sonka shine ajalina dan Allah kaji tausayin jaririyar zuciyata,idan kabarni mutuwa zanyi” ga faɗa ya ɗaga kana yace “wahatever ba kanki farau ba,and pls kada kiyi tunanin ne mana idan bani na nemeki ba that all”yan faɗin hakan ya fice daga cikin ɗakin.

Cikin ƙaraji da fitar hayyaci irina wanda suka samu heart attack lkcn guda ɗinan ta shiga faɗin “la’ilaha ilallahu Muhammadun rasulillahi S.A.W” shine abinda yazu bakinta kafin taja wata shaƙuwa mai ƙafin gske sai kuma numfashinta ya ɗauke cak a nan jini ya shiga fita ta hancinta rest in peace Seenat😭.

Jerryna Heroine Jakadiyan tunan silili a masarautar  Bilhas,My luv Autar manyan shugaban masu iya kirari a masarautar Bilhas, this page dedicated to u my guys thank you once again✋🏼😂.

*ASSALAM MY REAL FANS* 

_Duba da yadda labarina na the new emir yake ƙagagge kuma ƙirƙirarre wanda banyisa dancin zarafin wani ko wataba yasa na sauya sunan masauratar cikin labarin wanda ada na saka masarautar kano ne amman duba da yadda labarin nawa yake ƙagagge yasa na juya sunan masarautar sabida ina son yadda labarin yake ƙagagge to yazama sunan masarautar ma ya zama ƙagaggene yanzu ya koma MASARAUTAR BILHAS dafatan kun fahimceni nagode_ 

Lil Prince na fita ya tarar da best friend ɗinsa wanda suka tasu tun ƙuruciya,Murmushi Yazeed yay kafin yace “barka da fitowa Lil Prince”gyara zaman Alƙyabbarsa yay kana ya dubi Yazeed yace “sai ina” kallon room ɗin da Lil ya fito Yazeed yayi kana ya dubesa yace “friend where is she?”taɓe baki Lil yay kafin ya fara tafiya cikin isa da gadara haɗi izza,wajan 2minutes Lil bai amsa Yazeed ba,dan haka Yazeed ya ƙara nanata masa tambayar cikin girmamawa,a ɗan fusace Lil yace”Fuck you Yazeed”girgiza kai Yazeed yay domin yasan halin abokin nasa cikin ɗan fusata shima yace”you mumu i’m care about ur life ne,coz duk macen dakai mu’amala da ita mutuwa take,koda bata mutu ba muna sawa a kasheta domin shi zaisa ka tsira da mutuncinka,and kasan yana ɗaya daga cikin sharuɗan boka idan har aka samu wata tai rar ba zaka taɓa zama SARKI ba harka ƙare rayuwanka,kuma kasan wannan shine burin mai martaba a duk lokacin da yayi murabus,so nazu ina tambayarka kana min rubish i’m not stupid da zan maka questions mara amfani amma think about that”Yazeed yakai ƙarshen maganar yana kallon Prince.

           Shi Lil Prince abinma dariya ya basa,sai yanzu ya tabbatar aƙwai wanda kome ka zama a rayuwa bazai taɓa yi maka biyayya ba,jibi dai yadda Yazeed ya dage yana faɗin magana son ransa,shuru yay yana auna maganar Yazeed a ransa,dan yasan gsky ya faɗa babu batun ƙarya zuwa yanzu yay amfani da sama da mata goma kuma duk ƙarshensu mutuwa suke,yana da tabbacin Seenat ma yanzu bata raye da wannan yana ɗaya daga cikin ƙarfin ikonsa da kuma girman mulkinsa,suna suwa zuwa compound na hotel ɗin suka shiga cikin wata lafiyayyiyar mota wacce aka rubuta Lil prince 3,side ɗin baya suka shiga shida Yazeed sannan drever yaja suka bar hotel ɗin.

Sama da 1hour ba’a kawo key ɗin room 267 kuma sunga fitar Lil Prince,dan haka wata ma’aikaciyar ɗakin ta nufi cikin room ɗin domin gyarawa,mamakin ganin ƙofar abuɗe tayi tana shiga tayi saurin sakin abin hannunta sbd hango Seenat da tayi jini na zuba ta hanci da bakinta,a kiɗime ta juya zata bar ɗakin domin sanarwa da securities  sai kuma ta tsaya domin bata da ikon faɗin wanda ya aikata hakan ga Seenat,ganin bata da wani mafita wanda ya huce ta taimaki Seenat yasa tayi saurin ɗauko ruwa mai sanyi ta shiga zuba mata,tare da danna ƙirjinta tana shafa tafin hannunta zuwa na ƙafarta,wajan 5minutes Seenat ta saki ajjiyar zuciya tare da sakin kuka mai ciwo,tausayinta ne ya kamata ma’aikaciyar duk da  kasance warta ƙabila amma sosai take da zuciyar imani,cikin harshen nasara tace “what’s wrong with you?”Seenat tsayawa da kuka tayi kafin taja numfashi tace “Ubangiji ka isarmi,Allah ka sakawa ruhina da gangar jikina,Allah ka azabtar dashi da soyayya mai zafi kamar yadda ya azabtar da zuciyarta,Allah ka hanashi jin daɗin rayuwa kamar yadda ya tarwatsa farin cikina,Allah ka hanashi ƙwanciyar hankali kamar yadda zai hana iyayena ƙwanciyar hankali,ya Ubangiji ka tarwatsa wannan Sarautar zalunci ubangiji kada ka basu abinda sukeso,Ya hayyu ya ƙayyumu ka kawo *The New Emir* mai jinƙan talakawansa,Allah ka ɗurama Prince son abinda iƙonsa bai isa ya bashi ba,Ubangiji kaya femin kaji ƙaina kaga fartamin,zuciyana ciwo babu daɗi,Ummina kiya femin inajin kunyarki amma nafi jin kunyar mahaliccina”ta ƙarashe magana tana sakin wani kukan,Hawayena ya shiga zuba cikin idanun Emeka sbd tausayin halin da Seenat ke ciki,da ƙyar ta lallaɓata tayi wanka tare da ɗaura alwalar la’asar,ta gabatar da sallah ta roƙi Ubangiji ya fiya,tana idarwa ta saka hijab ɗinta,ta nufi wata court dake kusa da ita,tana zuwa ta basu labarin abinda ta aikata amma ta cire sunan Lil prince ciki,sanan tace tana son afidda haƙƙin Allah jikinta,sosai tabawa mutane tausayi dan haka aka yanke shawarar za’ai mata bulala tunda matsayin budurwa take,tace ta amince babu ɓata lkc aka shiga yanke mata hukunci tunda aka fara take murmushi tare da kiran Ya Gaffaru,ana gamawa ta faɗi a wajan tare da kiran sunan Allah,ruwa mai sanyi aka kawo mata ta girgiza kai alamar sam bata so,bakin tane ya shiga rawa alamar tana son faɗin wani abun,dan haka suka ƙasa kunne cikin rawar murya ta shiga faɗin “Li..li..li..,” kasa ƙara sawa tayi sbd wani abu da taji ya daki kanta cikin fitar hayyaci ta shiga faɗin kallamar shahada mutanan wajan suna tayata,tana kammalawa rai yay halinsa ya salam😭.

N.S University 

A nan motarsu Lil Prince tai parking bashi da wani abu da zaiyi cikin makarantar abokinsa Yazeed shine lecture  na makarantar yana ɗaukan ɗalibai sama da 100 a fannin seicology, yan zuma ya shigo sbd yana sa lecture 4 zuwa 5,direct office ɗinsa suka huce yana zuwa aka fara shiguwa bada Assignment,ana haka wata ƙyaƙƙyawar yarinya ta shigo tare da faɗin “Sir jiya banzo makaranta ba,so bansan ka bada wani Assignment ba,kuma naji kace shine matsayin exam ɗinka,ina neman afuwa a bani nayi yanzu” taɓe baki yay yace “tunda ga ɗan iska ko? Kina gida kina hutawa sai yanzu ki kaga damar zuwa kice wani na baki Assignment ko?” raurau tayi da idanu tace “No sir i’m telling u the true ne,wlh bana da lafiya kasan sanyi ya busa mu sai a hankali”jin jina kai yay tare da ƙoƙarin ɗauko wata peper gyaran muryar da Lil prince yayi ne yasa ya dakata,haɗe rai Yazeed yay yace “wannan shine year ɗinki na kammala makaranta right?”kaita ɗaga alamar eh “good, zan baki amma idan kinyarda da abinda zan faɗa”cikin murna tace “i agree sir kawai faɗi domin bazan ɓata shekaru masu yawa ba,kuma wannan exam ɗin ya rusamin plan” murmushi yay yace “zaki kasance a bed ɗina a wannan daren,so idan kin amince na yafe Assgnment ɗin zan baki mark mafi yawa cikin nasauran” a kiɗime Meema ta zare idanu cikin faɗuwar gaba tace “what sir saɓon Ubangiji fa?” haɗe rai yay yace “out! ba surutu na nema ba,amma ki tabbatar ƙin amincewarki dai² yake ta lalacewar shekara guda a karatunki is not my business is urs,dan haka the choices is urs” kuka ta fara tare da durƙushewa a wajan tace “dan Allah sir idan kuɗi kakeso zan baka,amma kada ka nemi lalata rayuwata ta abinda nafiso,karatuna shine burina kuma mafalkina,kaji tausayina kaima Ubangiji saiya dafa maka” zaro idanu yay yace “ohh nai maki kala da mayan kuɗi ko,kina son nunawa duniya ke mai kuɗi ce ko?get out from my offoce idiot!” ya ƙare cikin ɗaga murya,da gudu Meema ta fice daga cikin Office ɗin tana kuka,Murnushi Lil prince yay yace “weldone Man aƙwai kaya a wannan makarantar fa,nizan huci gida ina son ganawa da mai martaba yau kafin ya shiga tirakarsa,sallama sukai da juna kana Prince ya shige mota drever yaja da gudu suka fice daga cikin makarantar.

_Masarautar Bilhas_

Cikin sauri mai martaba ya gama shirinsa,cikin shiga ta alfarka ya sanya Alƙyabba mai ruwan ƙwai,tare da murza takalminsa na Fata irin nasu na masu sarauta komai ƙyalli yake jikinsa musamman sandar girmansa ta Azurfa,sai kuma ring ɗin gold da daimond wanda suke sanye a hannunsa na hago da kuma dama,wani ƙaramin Guro ya ɗauka wanda shine shaidar duk wani ɗan gidan sarautar,kuma dashi ake gane cewa kai jinin masarautar ne,kuma jinin BILHAS yara da manya babu wanda baya dashi indai jinin sarautar na yawo a jikinsa,indai ka ɗauke Barori da kuyangu haɗi da sauran hadiman gidan sune kawai basu da ita,yana gama shirin ya dubi Kilishi cikin muryar girma yace “ina Prince inaso muje dashi domin a ƙara yimin aiki a kansa” ya faɗa yana jan numfashi,sadda kanta ƙasa tayi alamar girmamawa tace “Ya mijina kuma sarki sarakuna mai taƙama da ƙarfin mulkinsa ka sani Lil prince kai kawai yake jira ya jima da dawowa” murmushi jin daɗi yay yace “Godiya muke Kilishi” yana gama sanya Guron ya miƙe tare dayin gaba nan Kuyangunsa suka mara masa baya,cikin nutsuwa yake tafiya a flat ɗin nasa  wanda yake da nisa da fada,wani ɓangare ya ƙarasu mai shegen ƙyau wanda akayi shi da zallar azurfa,har yau yana jin baƙin cikin wannan sashin yana ƙarasuwa,wani amintaccen Sarki na ƙarnin daya huce ya tasu fuska babu yabu babu fallasa ya shiga yiwa sarki kirari,kafin yasa Remote ya buɗe tangamemiyar ƙofar flat ɗin,cikin sa’a ta buɗe nan Sarki ya umarci Kuyangunsa dasu jirasa a nan,kana ya shige ciki.

Zaune ya sameta kan wani tattausar ladduma mai ƙyau da tsari hannunta riƙe da casbaha,da sallama ya shiga yana zuwa masu kula da ita suka basu waje,cikin girmamawa yace “barka da huta Mai babban ɗaki ya ƙarfin jikin”ya ƙare yana jefa mata harara.

Hajiya mai babban ɗaki da kasance uwa ga sarkin baya sarki Sufrak Bilhas kenan,yayinda take matsayin kishiga ga Mai martaba Khalid sarki maici a yanzu kenan,Ya rasa mahaifiyarsa tun yana ƙarami shine ya ɗauki baƙi hali da son zuciya ya ɗurama kansa,tun yana shekara 15 da mahaifinsu yay murabus saiya bawa yayensa Sufrak Mulki,shi kuma baƙin cikin hakan yasa yabar garin gaba ɗaya bai dawo ba sai ranar da yayensa yay murabus ya bawa ɗansa Yarima Sudais Sufrak Bilhas,a wannan yanar kuma akayi sunan ɗan Yarima Sudais a kuma wannan ranar sarki Sufrak yabar duniya ta hanyar ciwon ciki,Satin Sudais 6 akan mulki cikin dare aka shiga aka kashesu dashi da matarsa Omehi da kuma ɗansa MALEEK(sorry da za kuji nace Bilyamin am sorry Maleek ne) wannan baƙin cikin yasa Hajia mai babban ɗaki tayi kuka kamar zata rasa rai cikin hukunci Ubangiji kuma a wannan lkcn ta samu makanta ta hanyar rasa ganinta wanda shime ba’asan dalili ba.

Mutum ɗaya ta aminta dashi kuma yasan sirrinta wato Waziri na zamanin sarki Sudais wanda aka nema sama da ƙasa aka rasa,daga ƙarshe aka sami gawarsa saman ruwa,shine ɗansa Kamal ya gaji Mulkinsa amma fa ba waziri ba,ta ɓangaren aminta dashi da Mai babban ɗaki da tayi,wannan kenan a taƙaice.

Murmushi tayi tace “A’a Khalid ne da wannan yammacin?”taɓe baki yay dan yana mamakin yadda wani tym ɗin take fahimtar yanayi,shurun da yayi ne yasa ta cewa “kana mamaki da hukunci ubangiji ko?”ɗan zaro idanu yay tare da saurin faɗin “Kamarya kenan mai babban ɗaki?” nisawa tayi tace “munata ta tunanin sanyi ya huce amma naga antashi da hunturo yau” hamdala yay kana yace “daman na leƙo do baki ne,gashi har yau kinƙi bari a kawo maki mai kula da dake sosai” fuskarta cike da haiba tace “ayya Khalid yau nake tsoro nikam na yafe domin gaba ɗaya rayuwar tawa mene yay saura” jinjina kai yay tare da ƙasa da murya yace” hakane mai babban ɗaki domin ance makashinka yana tare dakai,amma idan kasa Allah a ranka sai kaga komai yay dai²,kullum muna addu’ar Allah ya bamu ikon kula da Al’ummar mu” cikin farin ciki tace “Ameen ya samadu Allah ya kare ya kiyaye”sallama yay mata kana ya bar flat ɗin gaba ɗaya.

Yana zuwa ya ƙwashi amintatunsa na Fada tare da Lil prince aka aka kira pilot  ya ƙarasu da jet domin tafiyan gaggawa sukesu zuwa gobe da safe sazu dawo,ba’a fi 5mins ba jet ya sauka suka shiga jiki cikin,da sauri pilto ya data jet suka ɗaga zuwa garin KOGI.

*** ***

Kogi state

Zaune yake gaban Boka daga shi zai bantee ana ƙwara masa jini a jikinsa tare da faɗin wasu kalmomi marasa ma’ana,sun daɗe cikin hakan faɗin a ɗauko wata ƙwarya,sosai na tsorata gani tsotsotsi cikin ƙwaryar sai mutsi suke,ɗan zare idanu nai ganin mai martaba Khalid ya ɗauki guda ɗaya ya zura jikin bakinsa tare da taunewa,kana ya ɗauki guda ya tura cikin sumar kansa,nan take wani baƙin hayaƙi ya fita cikin farin ciki Boka yace, “komai ya kammala amma sosai na tsorata ganin yadda,wani mutum kebinka kaida Lil prince hannunsa riƙe da wata matashiryar yarinya,koda na matsa bincike cikin madubina sai ya tarwatse hakan yasa ban samu damar ganin fuskar matashin ba,amma ga wani aiki zanma indai har yayi to babu wanda ya isa ya gaji mulki idan ba jininka ba,koya hau saiya mutu”cikin farin ciki mai martaba Khalid yace “mun baka dama” gyara zama Boka yay sannan ya haɗa wani garin magani yace “za’a samu ƙaramar yarinyar mai shekaru 17 zuwa 18 amma ta kasance ƙyaƙƙyawace ajin farko kuma mai tsarin halitta kuma wacce magana bata dameta ba,idan aka samu yarinyar zaka bata kulawa na kimanin sati 2 kana saika ƙwanta da ita,amma kafin jikinka ya shiga nata dole ka cusa mata wannan maganin a ƙasanta.

  *_Kun shirya nima na shirya tsaf idan baku shirya ba ya kamata a kakkaɓe zani a gyara zama,magana ake da ƙarfin mulki,magana ake ta matsalolin makarantun university,magana ake akan kuɗi,magana ake ta abinda ke faruwa a wannan zamanin😟😍ku biyoni domin jin yadda  allura zata tuno garma,duguwar tafiya ce inji AUTAR MANYA,kada a baki labari kada a baka labari,wanda na kewa ba dai² ba yay hqr bayin kaina bane aikine yazu da hakan,dan nasan zan farantawa wasu kuma zan baƙanta ransu buy i don’t care ina tsaya akan ra’ayina banyi dancin zarafin wani ko wata ba,SARAUTA kaifi ɗaya ce👌🏻idan nai gaba bana baya da yardar Lillahi wahidul ƙahhar,afuwa😂idan na fara surutu ban iya tsayawa ne yasin kusan san magana ta masu Sarauta amma Allah ba wasa aƙwai ƙalubale babba🙁😒_*

Shuru Mai martaba Khalid yay,yana auna maganganun boka,shi yanzu a ra’ayinsa baya da wani buri na kasan cewa da ƴar mace balle under age mai ƙarancin shekaru,mai ma zai ɗauka a jikinta for God sake? Shi yanzu bashi da buri daya huce ya ingata rayuwar Lil prince,ya zama mai ƙarfin mulki da isa da gadara haɗi da izza,maganarsa ta zama kamar umarnice wa talakawansa,wannan shine hope ɗinsa  a kan Lil prince,shurun da yayi ne yasa Boka ƙara mai²ta masa abinda yace,cikin gajiyawa da maganar bokan ya ɗaga idanunsa da suka soma jaa sbd yadda tsotsotsar ta fara masa aiki,a gajiye yace “What about Lil prince? Ina tunanin wannan aikin dashi ya dace ba wani ba?”ya faɗa yana karkarwa sbd yadda yaji kansa ya fara juyawa hakan kuma shine alamun nasarar aikin.
Rubuce² Boka yay saman allon tsafinsa kana ya dubi Mai martaba yace “aƙwai matsala babba,bana da ikon yiwa Lil prnce aiki a yanzu saiya gama mallakar ƴan mata guda ashirin kamar yadda yake a tsari,dan aljanin dake shanyen jinin matan shine mai akula da prince kuma bai idda shan jinin ba kamar yadda ya buƙata,babban abuma shine kaine a kan karagar mulki bashi ba,so dole wannan aikin naka ne,amma yana da sharaɗi”ya ƙare maganar yana ɗauko wata gawar mahauniya wacce aka jiƙa jikin jini kana ya cilla cikin wuta.
Jinjina kai Mai martaba yay tare da gyaran murya hakan ya tabbatarwa da Boka Mai martaba Khalid ya amshi ƙudurinsa kamar yadda yake buƙata,saida ya kammala komai na aikin sannan yace “Sharaɗin ba’a faɗarsa, kawai dai ka kiyaye da wannan yarinyar da zaka samo”ya faɗa yana shigewa cikin wani kurmin ɗaki mai duhun gaske,Mai martaba yaywa alama da  hannu akan ya shigo,miƙewa yay tare da  fara tafiya,yana shiga suka rufe ƙofa,wajan 3mins na jiyo surutansu sama² da kuma ihu²😱komai suke aikatawa uhuu,saida suka kammala abinda suke kana suka fito fuskar Mai martaba cike da farin ciki da alama dai aƙwai abinda akai masa wanda shima yake buƙatarsa,cikin nutsuwa ya sanya kayansa ya koma Sarkinsa sak komai na kamala ya fito,idan kaga Sarki Khalid ba zaka taɓa cewa zai aikata wani abu na saɓon Ubangiji ba,bai fiye fitowa a asalin colour ɗinsa ba,yana ɓoye mummunan habit ɗinsa sannan ya bayyana good habit ɗinsa,wannan halin duk cikin iya takune dan haka da wahala ka fahimci yana aikata mummunan abu,sai wanda suke good tym dashi.
N.S Quest Place
Shine Hotel ɗin da suka sauka cikinsa,Hotel ne mai ƙyan gske kuma da tsari sosai manyan masu kuɗi suke sauka cikinsa,room 123 shine na Mai martaba,124 kuma na Lil prince sauran rooms ɗin na amintattun Sarki da suka taho tare,daman alrdy pilto yay tafiyarsa sai gari ya hawaye zai dawo.
Yana zaune a kishin giɗe yana kallon new a B.B.C Lil prince ya turo ƙofar ɗakin hotel ɗin ya shigo,zama kusa da mahaifin nasa yay cikin girmamawa yace “Allah ya ƙara maka yawan rai da ƙwana ya mahaifina,wata buƙata gareni idan an bani damar faɗa?”
Gyara zama Mai martaba yay tare da maida hankalinsa kan Lil prince yana fatan ace ba wata babbar matsala bace take damun yaron nasa,cikin tausassiyar murya Mai martaba yace”Haba magaji matsalanku ai tamu ce,faɗi ina jinka”murmushin  jin daɗi Lil prince yay yace ” Allah ya taimaki Sarki ina buƙatar kuɗi masu yawa sbd nayiwa friend ɗina ƙyautar motar as her birthday gift,Papa wallahi Heroine naji dani sosai kuma naga tana mutuwar son mota Bugatti  shine nakeso nai mata gift da ita”
Girgiza kai Mai martaba yay cike da farin ciki yace “ba wani abu za kaga alert anjima shikenan?”ya tambaya cike da ƙaunar ɗan nasa mafi soyowa cikin ransa da zuciyarsa,dariya Lil prince yay tare da hugging mahaifin nasa yace “Thank you soo much Papa heroine na gdy ƙwarai”bayansa ya ɗan bubbuga yace “it ok,Magaji meye tunaninka ga wannan hotel ɗin?”shuru Prince yay dan baiyi wani tunani ba,”i don’t think anything kawai dai yay ƙyau sunsan aikinsu”nisawa Mai martaba yay yace “ni ina da ra’ayin gina irinsa a garin Bilhas”ɗan waro idanu Lil prince yay tare da faɗin “but ina zaa samu babban fili cikin jama’a haka?”wani shu’umin murmushi Mai martaba yay yace “muke da gari fa,zanwa Governor  magana akan babban filin da wani malami ke buƙata zai gina makarantar ismaliya so gwamma ni na amfana dashi tunda harka ake ta kuɗi”jinjina kai Prince yay yace “amma makarantar fa ya…’✋🏼ɗaga masa hannun da Mai martaba yay ya sashi yin shuru dan haka yay masa Goodnight ya fice a ɗakin shime shirin ƙwanciya yay domin yana buƙatar magana da shugaban sujoji yana buƙatar a bashi mai kula da lafiyarsa data Prince da wannan tunanin ya ƙwanta bacci.
*** ***
Ƙwance take saman makeken italian bed ɗinta sai juyi take tym to tym tana murza ƙaramin ring ɗin hannunta,wanda har yanzu bata san yaya akai ring ɗin yazo hannunta ba,wata ranane ta ƙwanta bacci tai mafalkin wani haɗaɗɗan guy mai ƙyan gaske,saimun kanta tayi ta zuba masa gajiyayyun idanunta masu kaifi,cike da ƙaunarsa ta nufi wajansa kafin ta ƙarasa wani baƙin mutum ya shiga tsakiyarsu tare da nufota tana jaa baya,kafin yakai ga inda take taji wata azaba a ƙaramin yatsanta sai kuma wani haske ya bayyana,wanda yay sanadiyar guduwar mutumin cikin farin ciki ta hangi wanda idanunta ke fatan gani ya ware mata hannayensa alamar tazu garesa da gudu ta isa garesa kafin ta ƙarasa an buga mata wani abu a kanta,cikin firgici ta farka daga nannauyen baccin daya ɗauketa,tun daga wannan ranar taga wannan ring ɗin hannunta wanda kullum cikin sheƙi yake tana sonsa kamar ranta shiyasa bata rabuwa da murzasa.
Yauma tunda ta farka take yawan faɗuwar gaba,lumshe sleepyn eyes ɗinta tayi wanda koda yaushe suke a rufe cikin nauyi da kasalan daya sameta ta ware jajayen laɓɓanta masu kauri tace”ya rabbi what wrog with me,i have a test by 10:30 kuma still ina gida”ta faɗin hakan tana taune cute lips ɗinta mai sheƙi,miƙewa tayi tare da ɗaukan teddy ɗinta ta rungome tana jin wani abu mai kama da kewa na ratsa zuciyarta,cikin zuciyarta tace”i luv you my hrt dream where are you?”ta faɗi lkcn da take tura yatsanta cikin ƙaramin bakinta ta shiga tsotsa kamar yarinyar,ta daɗe zaune kafin ta sunbaci teddy tace “my bby boo”tana faɗin hakan ta miƙe tare da shigewa cikin toilet ɗin dake cikin bedroom ɗinta,sosai toilet ɗin ya tsaru komai anyi masa ado da pech colour kamar yadda fenti bedroom ɗin ɗakin yake pech,a ɗan gurguje ta sakarwa kanta shower tana wanka tana rera waƙar cikin film Sam teri kasam domin shine fovarite movie ɗinta,soyayyar film ɗin ita tafi ƙayatar da ita,bayan ta kammala wanka ta zubawa kanta idanu ta cikin mirrow’n dake manne a toilet ɗin.
Turo baki tayi gaba tare da mamulan lips ɗinta cikin ranta tace “i hate this stupid brest ɗin,banso takura garesa”sosai take ƙyaƙƙyawa fara tas da ita,babu abunda yafi ɗaukan hankali a jikinta kamar fresh skin ɗinta,kana kallonta zaka san ita ɗin ruwa biyu ce,musamman yadda eyes ball ɗinta suke blue kamar wata baturiya,tana  da dugun hanci wanda yay dai² ƙaramin bakinta,ga gashin idanunta zara² wanda suke ƙwance luff,gashin girarta kam kamar zasu haɗe sbd yawansu,baƙi siɗik suke sunyi ƙwance luff,sai gefen fuskarta wanda yake ɗauke da saje kamar namiji,ɗan ya tsuna face tayi hakan ya bawa beauty points ɗinta damar lumawa,cikin sauri ta tattare tulin gashin kanta bayan ta gama busar tashi ta ɗaure waje guda,daga wajan toilet ɗin taji ana faɗin.
“ZARINA! ZARINA!”
Tana ji ta kasa amsawa sbd sam magana bata dameta ba hasalima wahala take bata,saida taji kiran yay yawa sannan tace “I’m here Mom” jin amon muryarta a toilet yasa Mom faɗin “ok be past my luv”tana faɗin hakan ta fice a ɗakin domin ƙarasa shirya break fast.
a ɗan gurguje Zarina ta gama shiryawa cikin duguwar riga ta Abaya mai ɗauke da milk colour haɗi da maroon  ɗin stone,beby lipstic ta shafa saman lips ɗinta kana ta ɗauki school bag ɗinta ta rataya,harta tafi ta dawo ta ɗauki teddy ɗinta ta rungome,sosai ta ƙarewa ɗakin ƙallo kamar me nazari sai kuma ta saki murmushi tace “i will come back soon”tana faɗin hakan ta fice ta nufi babban parlour’nsu.
Tana isa ta rumgome Mom tare da bata kiss a kumatu tace “mrng Mom”shafa kanta Mom tayi tace “mrng too my luv”
“ok bye Mom i luv you”da sauri Mom tace “No! No! Zarina come back u forged ur break fast,da sauri Zarina ta dawo ta sanya yam balls a bakinta kana ta kurɓi coffee taiwa Mom bye tare da rungometa sosai cikin sanyi tace “zanyi kewanki Mamana i luv you”cikin sanyi Mom tace “i luv too my luv Allah yay maki albarka take care” ta faɗi hakan tana yi mata kiss a tsakiyar forehead ɗinta,da sauri Zarina ta fice a parlour’n ta nufi hanyar fita daga cikin gidan,tana zuwan compund na gidan ta shiga cikin WCSV drever yaja suka fice daga gidan.
Sosai dreve’n ke gudu ganin sunyi late yana tsaka da gudu tayar motar tayi faci,tsaki yaja tare da faɗin”kaji tsiyar ƙarfan nasara”Zarina dake bayan mota tana danna syetem ɗinta tace “go and cheak nayi late da yawa bro”jinjina kai yay tare da faɗin “afuwa hajia ƙarama bari na ƙarasa wajan bakanike na ari taya saimun sauya amma wannan iskar cikinta ta sace”murmushi tayi masa tace”no problms amma na fara aiki as lawyer ta kanka zan soma”dariya yay mata yace “aga farceni Hajia ƙarama” leƙa fuskarsa tayi tace “Allah yasa mudace”ɗan waro idanu yay tare da faɗin “Hajia mudace dai aike kin riga da kin dace saidai fatan cikawa da imani,Allah yasa mudace idan mundace mu dafe”ya faɗa yana fita a motar ganin idanta biye masa zai cikata da magana yasa tayi shuru taci gaba da bincikenta a cikin System  ɗinta.
Wajan sama da 10 minutes taja ɗan ƙaramin tsaki tare da ɗaga kanta,murmushi ta saki ganin wasu yara na ƙoƙarin tsallaka titi sun kasa,hakan yasa ta ɗauko teddynta tare da ɗiban chocolate masu yawa,ta buɗe motar ta isa ga yaran,tana ƙarasawa tace “hi friends can i help you?”gaba ɗaya suka haɗa baki wajan faɗin “YES ANTY” hannayensu ta riƙe cikin tsutuwa ta tsallakar dasu makeken titin kana ta raba masu chocolate sannan ta juya ta nufin tsallaka titi,watan baƙar mota ƙirar Ferrari tayi parking gabanta,saurin ja baya tayi tare da sanya yatsanta cikin baki,ana haka ta hangi drever ɗinta,cikin sauri ta fara ɗaga masa hannu tare da buɗe baki zata kira sunansa taji anyi sama da ita tare da nufar mota da ita baki ta buɗe zata saki ihu akai saurin danna mata handkerchief  a baki.
Jikinta ne ya saki bayan sun sanya mata handkerchief a baki wanda yake ɗauke da powder mai gusar da hankali,gaba ɗaya idanun Zarina ya lumshe jikinta saki yaza mana bata san inda hankalinta yake ba,sabida ƙarfin powder da akai using da ita a kan  handkerchief ɗin,cikin motar ya turata tare da shimfiɗeta a side ɗin baya,shi kuma ya koma side ɗin gaba,ɗan juyawa yay tare da zuba masa idanunsa yana kallon yadda ta rungome teddy tare da tura yatsanta cikin baki,murmushin gefen baki yay domin nan take wani abu ya caki zuciyarsa,juyawa ya kalli drever yace “let’s go” da gudu drever yaja motar suka bar kan titin.
Ihu Dreve’n Zarina ya saka domin kan idanunsa suka sanyata mota,tsoran ransa yake shiyasa bai ƙarasa ba,domin babban titi ne mutane basu fiya zama wajan ba,cikin kuka ya faɗa mota tare da janta da gudu ya mara masu baya,yana dreving yana kuka tare da faɗin “Hajai ƙarama ubangiji ya kareki daga sharrin mutannan,Yarinya mai halin manya kenan😭idan na rasaki ina zan samu mai bani na kashewa😂”
Sosai dreve’n Zarina ke gudu tsakiyar makeken titin amma kafin wani abu tuni motar ƴan kidnapped ɗin sunyi masa nisa,haka yayta bulayi babusu babu labarinsu,sabida tsoron abinda zai faɗawa Hajia Sultanerh yasa ya kasa zuwa gida sai gefen titi daya nema ya zauna yaci  gaba da rusar kukansa.
Basu tsaya ko’ina ba sai filitin tashi da saukar jirki dake garin Kogi,suna isa jet ɗinsu na sauka,gaba ɗaya suka shiga ciki babu wasting time pilto ya tada jet suka lula saman gaji mare.
Fargaba gaba ɗaya ya cika Mom ganin lkcn da Zarina ke dawowa harya gota,cikin tsoron data sami kanta ta danna number wayarta,tana ji tana ringing but amma babu picking cikin muryar kuka Mom ta shiga faɗin “why Zarina am so scared  pls come back”da sauri kuma ta danna number wayar drever’n cikin sa’a ya shiga ana picking tace “where is my luv,where is she!?”ta ƙare maganar cikin ɗaga murya tamkar yana gabanta,shuru tayi tana sauraran abinda yake faɗa kafin ta ƙwala ƙara tace “What Zarina missing but how, no you’re lie duk  inda yarinyata take kayi gaggawar dawo mani da ita kai shashan inane mtwss” tana faɗin hakan ta juya a guje ta nufi sashin uwar mijinta a babban parlour tana zuwa ta faɗa jikinta tare da sakin kuka,sosai Mamu ta shiga tashin hankali ganin surukarta cikin wannan halin,a tsorace tace “kee! Lafiyanki mene haka kamar wacce akace Abdallah ya mutu”ta ƙara magana tana kallon Sultanerh.
Ƙara ƙanƙame Mamu Sultanerh tayi cikin kuka ta shiga faɗin “Na shiga uku Mamu innalillahi wa’inna ilaihir raji’un” ta faɗin hakan tana ƙara rushewa da kuka,hakan yasa Mamu ƙara ruɗewa cikin wani sabon tashin hankali tace “Waini zaki maida shasha kizu kina kuka kuma kimin shuru oyya tashi ban waje idan baki faɗin abinda yake faru”girgiza kai Sultanerh tayi kana ta sassauta Kukanta tace “Zarina missing Mamu”ta faɗa cikin wani sabon kukan,da mamaki Mamu ke kallon Sultanerh kafin tace “sorry! I did get u kamarya Zarina missing kamar wata ƴar tsana?”nan Sultanerh ta ƙwashe komai ta faɗawa Mamu har abinda ta cewa Drever’n,Salati Mamu ta fara dayin addu’ar duk dayazu bakinta kana tace “Kin faɗawa Abdallah da kuma brothers ɗinta?”girgiza kai Sultanerh tayi tace “bansan tayaya ne zanyiwa swrth baya ni ba,ina tsori domin nasan soyayyar dakewa Zarina kamar ransa,Sufyan da Taufik bansan sanar dasu sbd kinsan yanayin aikinsu na sojoji da wahala yake gashi wannan karan kona kirasu waya ban samunsu ina tsoro zan jira harsu dawo”shuru gaba ɗaya sukai domin babu wani mai sauran kuzari cikinsu,can Mamu ta nisa tace “ko za’a ɓoyewa kowa banda Abdallah domin shine mahaifinta so kowanne tashin hankali zai shiga dole ya sani,ɗaukan wayana a ɗaki”miƙewa Sultana tayi tare da ɗauko wayan ta dawo babu ɓata lokaci ta dannawa Abdallah kira.
_Masarautar Bilhas_
A hankali ta shiga buɗe manyan idanunta wanda sukai mata nauyin gaske tana mamakin irin baccin daya ɗauketa,bakinta ɗauke da addu’ar tashi daga bacci kana taja idanunta ta ƙare kullesu,teddynta ta rungome sosai tare daci gaba dashan yatsanta ƙamar wacce ake feeding,cikin abinda bai huce 3mins ya farayi mata gizu kamar yadda ya saba yi mata cikin baccinta,amma a wannan karan tana mamakin yadda komai nasa yake bayyana abu ɗayane takeson gani hakan kuma ya kasa faruwa,a duk lokacin dataso ganin fuskarta sai kanta ya fara ciwo tare juya mata,ɗan ya mutsa fuska tayi cikin ranta tace “where are you haiding ne?”ta faɗa tana turo bakinta,sosai yake bata haushin ɓoye fuskarsa da yake mata,cikin nasarar da suka samu Zarina ta manta komai tama manta cewa satota sukai,ta manta Mom,Abbanta,Sufyan,Tufik,abu ɗaya take iya tuna ta kuma fahimta shine “Heart dream”
Turo ƙofar ɗakin da akaine yasa tayi saurin ware idanunta tare da zubawa ƙofar ɗakin idanun,saurin miƙewa tayi tare da zama waje guda ta ƙanƙame jikinta ta zubawa mutumin idanu,murmushi yay mata kana ya ƙarasu cikin ɗakin cikin so da ƙaunar ganinta yace “baby harkin farka?”kasa tankashi tayi domin haka kurum taci ta kasa yarda dashi,cije lips yay kana ya zauna kusanta yace “ohh baby badai harni kika manta ba,so how was ur night beby kin daɗe kina bacci harna gaji zarya”nanma shuru tayi masa ta ƙara ƙanƙame teddynta a jikinta ta shiga mutsa bakinta alamar tana son faɗin wani abu,ganin yadda bakinta ke motsi gashi gaba ɗaya sun jiƙe da saliva  wanda ya ƙara hadda fidda asalin ƙyan lips ɗinta,yasa shi saurin lashe gefen bakinsa yana jin wani iri a ransa,cikin wata muryar yaudara yace “ohhya bebyna say something pls”hawaye ne suka wanke mata fuska cikin siririyar muryarta wacce bata fita sosai tace “who are u?”ɗan ware idanu yay alamar mamaki yace “Ohh bebyna ta manta lover ɗinta whatever dai i’m ur husband to be😱”kallonsa tayi da jiƙaƙƙen hawayenta tace “sure?”
        “yeah” shine amsar daya bata cike da murnar nasarar daya samu,ɗan murmushi tayi wanda ya bayyana haƙorin makkanta cikin muryar nutsuwa tace “Thank God,amma da naji tsoro sai nake ganinka kamar mugu irin kumurcin majinnan”ɗan ɓata fuska yay baice bata komai ba yakai hannu zai riƙe hannunta tayi saurin jaa baya,cije laɓɓansa yay yace “ok bbyna take a shower and za kiga komai kamar a mafalki so ki ɗauki hakan matsayin sabuwar rayuwa zaa kawo maki white clothe ki sanya as from today shine kayanki   daga nan banson wata tambaga kin gane”yana faɗin hakan ya fice a ɗakin.
Baki ta taɓe ita wani tsoransa ta keji haka nan,amma taji daɗi cikin ranta tunda yace shine zai zama mijinta tasan kuma miji never ya cuci matansa,miƙewa tayi tare shige wani ƙofa data gani gefenta ganin toilte ne yasa ta faɗa ta shiga sakarwa kanta shower tana gamawa ta maida kayan jikinta kana ta ɗaura alwala,sosai tai mamakin ganin dare ya ƙarayi cikin sauri ta gabatar da sallah sannan ta zauna zaman lazimi,tana iddar wasu Hadimai mata suka shigo kayan suka ajjiye mata sannan suka ajjiye mata kayan motsa baki danginsu fruit,wata Hadima ce tayi dariya tace “kice mun ƙaro wannan mai kalan aljanun ina aka sameta?” cewar ɗaga daga cikinsu kenan,Zaituna ce tace “kee! Saurara banson rashin ɗa’a meye haɗinki da ita?”Kuyanga Furare ta amshe maganar wajan faɗin “Babu fa,nidai ƴan matan duk abinda zaki ki ɗauke idanunki akan Lil prince domin shiɗin nawa ne ni ɗaya”Zaitunce ta maka mata harara tace “ke prince ya maida kuma iska na wahalan damai kayan kaba banda hauka irina Furera waya gaya maki tsarin mulkin Masarautar Bilhas jinin sarauta na kula baiwa,kima daina mafarkin samum prince domin yay maki nisa sosai”ta ƙare maganar tana kallan Zarina wacce taci gaba da laziminta cikin ranta idanunta rufe ba tare data kallesu ba,amma sosai maganganunsu ke damunta sbd bata sama da hayaniya ba sam.
              Zaitun ce ta ƙarasu wajanta tace “ƙanwata sannunki kinji mune masu alhakin kula dake daga nan zuwa sati biyi ki koma ɓangarenmu baki ɗaya,amma kiyi hqr da rayuwa ki karɓeta a yadda tazu maki,amma mene sunanki?”sai lokacin Zarina ta ware jajayen idanunta da suka sauya kala lokaci guda sbd tsaɓar tension ɗin data shiga,sosai take kallon Zaitun kafin ta ware laɓɓa tace “heart dream”tana faɗin hakan taja idanunta ta rufe ta shiga tauna laɓɓanta,girgiza kai kawai Zaitun tayi tare da faɗin “Allah yasa mudace”hannu tasa ta dafe kanta dake sara mata tayi sosai take son tuna inda taji kalman ta,
             “Allah yasa mudace”amma ta gagara tuna komai,cusa kanta tayi tsakiyan cinyoyinta ta shiga rera kuka kamar ranta zai fita a haka wani sabon bacci ya ɗauketa yatsanta cikin baki.
Washe gari
Fada
Zaune Mai martaba yake kan karagar mulkinsa yana amsar bayanai daga wajan talakawa da kuma abinda ke faruwa a gari,wani dagacin baƙin da suka halarci Fadar wani ya numfasa yace “Allah ya ƙara girma yaja ƙwana muna da ƙorafi bisa babban filin da gwamna yay mana alƙawari bayarwa domin a gina makarantar islamiya yanzu kuma mun samu saƙo akan cewa ya fasa bada wannan babban filin,mu’alummu muna cikin tashin hankali bama da kuɗin saka yaranmu a manyan makarantu kuma muma munaso rayuwan yaranmu su inganta kamar t sauran yaran,wannan filin da za’a bamu jahadine kuma taimakon musulunci za’ai Allah yaja da zamanin sarkin sarakuna mai adalci a duba mana wannan lamarin”yakai ƙarshen maganar idanunsa na fidda ƙwaila.
 
Mai martaba ya jinjina kai tare da bada umarnin rubuta bayanai cikin peper,haka ya dingajin abubuwan da talakawa ke buƙata kana ya sallami kowa,Mai martaba ya kalli Tiraki sannan ya bashi umarnin  yaje ya ƙona peper cikin girmama Tiraki yaje ya aiwatar da abinda Mai martaba ya umarcesa dashi,Ɗan aikena ya shigo da sauri tare da zubewa gaban Mai martaba ya soma kirari kafin yace “Ran sarki ya daɗe baƙwan U.S ya sauka yana airport yanzu haka” cikin farin cikin jin mai tsaronsa yazu ya bada umarnin aje a taho dashi,kana zaman Fada ya watse Mai martaba ya shiga tirakarsa.
Kilishi ta sami Jakadiya tace tana so ayi mata iso wajan Mai martaba,wajan 5 minutes Jakadiya ta dawo tare da zubewa gaban Kilishi tace “Allah ya taimaki uwar ɗakina saidai a tara nan gaba”cikin ɓacin rai Kilishi ta kalli Jakadiya tace “wai wannan wanne irin abune baka da ikon ganin mijinka a lkcn da kaga dama sai wanine zai baka dama?”Jinjina kai Jakadiya tayi tace “sai hqr haka tsarin Sarautar yake dole sai Fulanin Sura  ta bada dama”rai ɓaci Kilishi tace “miƙomin Bakilawan can amma ni bazan iya lukutar masifa ba mata sai shegen iyayi kamar wani tafi”Kirara Jakadiya ta shigayi mata tare da zugata kana ta miƙa mata Bakilawan tayi waje.
A hankali wata babbar mota ƙirar Bugatti  tayi parking tsakiyar masarautar,cikin sauri Drever’n ya fito tare da dawowa side ɗin baya ya buɗe ƙofa kana ya ƙame ƙam kamar wani dogari,wanda yake a zaune a bayan motar a hankali a ajjiye news peper ɗin hannunsa,gajiyayun fitinannun idanunsa yaja ya lumshe tare da taune jajayen laɓɓansa masu taushi,wani zazzafan numfashi ya fesar ta hancinsa kana ya shiga murza ring ɗin hannunta wanda ya kejin soyayyarsa kamar ransa,ƙyaƙƙyawane ajin farko Allah ya bashi murɗaɗɗan jiki kana ganinsa zakasan tabbas shiɗin soldier shi,hannunsa yasa ya shafi sajen fuskarsa kana yay ɗan gyara murya kaɗan wanda ya jawo hankalin drever’n cikin sauri ya amshi news peper ɗin tare da wayoyinsa,cikin isa da taƙama haɗi da izza ya zura da ƙyawawan ƙafafunsa waje  ya ɗauki some minutes kafin ya fito da dukkan jikinsa,Sarki ya tabbata ga ubangijin daya tsara wannan halittar ni kaina na alƙalamina ya kusa faɗuwa,sanyen yake da farar t.shirt mai ƙaramin hannun hakan ya haddasa bayyanar murɗaɗɗiyar arms  ɗinsa,sai dugun wandonsa na kakin sojoji yayinda ya ɗaura rigar uniform ɗinsa a waist ɗinsa,tsaiwarsa ya gyara tare zuba hannayensa cikin aljihun wandonsa,cije lips yay wanda hakan ya zama kamar habit ɗinsa,cikin wata zazzaƙar murya mai daɗi da taushi yace “Masarautar bilhas”
*_sorry yau banyi edited bai idan anga errows sunyi yawa afuwa,

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *