UMM ADIYYAH CHAPTER 83 BY AZIZA IDRIS GOMBE
lattin ofis.”
Harararta ya yi, “Yaya Za ayi ki ce na je ofis
yau?” Hannunta ya riko ya zaunar da ita a
gefensa hade da tashi ya jinginu a jikin allon
gadon. “Yau ne ranar da zan fara
zama da ke, lokacinki ne, ba zan raba shi da
kowa ba kuma. Don haka ki zo ke maa
ki yi zamanki, ko kuma bari na shirya, sai na
fito. Amma ba zuwa wurin aiki ba dai
yau ba kam. Haba ai aka ganni a gun aiki yau,
sai ace ba ki yi sa’ar miji ba.”
Umm Adiyya tana dariya ta ce. “Kowa ya gani
ya sani ai ba na kuma bukatar
mutane su jaddada min komai.”
“Aha, na san dai ba haka kawai na zama ad-
dicted to you ba.” Ya fada yana
shinshinan wani sabon kamshin da ya jiyo a
bayan kunnenta.
“Ka bari,”
“Wannan meye sunansa?”
Lumshe idanu ta yi, “Nafhatul ad-deeb.”
“Hmm! Ina sonshi.”