UNCLE NE CHAPTER 5 BY NIMCYLUV

 UNCLE NE CHAPTER 5 BY NIMCYLUV

Da yamma Lamir ya sauka gidan president Mubarak Yahya cibo,motoci ne sama da goma sukai parking a parking space,ga wasu securities wajan ashirin duk riƙe da guns,kowa ka gani fuska babu walwala,a haka aka  buɗewa President Mubarak Yahya cibo,yana tafe wasu masu tsaronsa suka rufa masa baya,da sassarfa ya shige parlour’n da yake meeting mai muhimmanci wanda ba kowa yasan dashi ba,yana zuwa parlour’n wasu manyan mutane su biyar suka miƙe tsaye alamar

girmamawa,farin ciki fal fuskarsa ya kalli Lamir wanda ya ƙara girma shekarunsa suka jaa,sai dai yana nan fresh bawai ya tsofa bane, zama yyi akan wata lafiyayyiyar kujera a hankali kuma ya ɗauki coffee da aka ajjiyewa ko wannansu ya ɗan kurɓa kaɗan, Lamir ne yace “ur excellency sai naji kira daga sama,naji tsoro sbd tunda  ka turani Istanbul domin kula da Company medicine ɗinka baka taɓa kirana ba,shiyasa wannan kiran ya ɗagamin hankali” Gwamna Faisal Lawan yace “ai Lamir abunda ba muyi tunanin zai faru damu ba shine yake shirin faruwa,babu wanda ya taɓa tsayawa takara shugaban ƙasa tun takarar da Khalil ya tsaya shima kafin zaɓe ya mutu,to yanzu an waye gari wani ɗan ƙaramin alhaki na neman tayar mana da hankali, tabbas idan mukai sanya za’a samu matsala” ya ƙare maganar yana kallon president Mubarak, miƙewa tsaye Lamir yyi ya Fara zagaye parlour’n kafin yace “duk wannan ba shine ba,bamu da matsala dashi idan duk sauran gwamnonin da muke dashi basu mara masa baya ba,kaga da zarar anyi zaɓen cikin gida bamu da wata matsala dashi,idan zaɓe yazo a nan zamu tara talakawan gari da matasa mu raba Musa ƴar shinkafa suger da ƴar dubu biyu haka,matasa kuma zamu basu ofer ta aiki amma ta ƙarya,sannan ƴan bangar siyasarmu zamu haɗasu da manyan drugs wacce zata har gitsa masu brain ɗinsu,kaga a nan zasu rage mana wani aikin ranar zaɓe sukaiwa ƴan kungiyar hamaiya farmaki,hakan zai saka magoya bayan jam’iyyar jin tsoro kowa yaƙi fitowa zaɓe sbd yana jin tsoron kada a kashesa ko a yanke sa, shine kawai” murmushi president yyi domin har yaji wani sanyi a ransa, Faisal Lwan  shima ya mike tsaye yace “matsalar duk ba’a nan take ba,tashin hankalin da muke ciki a yanzu shine dukkan gwamnonin da muke dasu guda 39 sama da 30 suna bayan sabon ɗan takarar shugaban jam’iyyar D.R.P ɗin” cikin tashin hankali Lamir yace “wai waye wannan sabon ɗan takarar da yake wasa da rayuwarsa data danginsa?” ya ƙare maganar yana fesar da numfashi sai a lokacin President yace “his name is Muhammad Jalal Kabeer bobo” da saurin Lamir yace “what!!!?.

da wajan yamma akai parking da wata sabuwar mota black colour, wasu manyan securities ne majiya karfk sama da 20 suka zagaye motar kafin wani babba yazo ya buɗe murfin motar bayan motar, ajjiye jaridar hannunsa yyi ta daily truts kafin ya ɗauki farin glass ɗinsa ya manna a idanunsa,wayarsa dake gefensa tana ringing ya ɗauka tare da katse kiran ya zuro da fararan ƙafafunsa zuwa waje,cikin a zaba securities ɗin suka zagayeshi,yana sanye da wata light blue ɗin shaddar ɗinkin riga da wando da kuma babbar riga sai zabga ƙamshi yake,fuskarsa ta cika da haiba, kwarjini,annori da kuma cikar zati, wayoyin hannunsa aka amsa wani ya ajjiyesu wajansa,cikin nutsuwa ya fara tafiya har zuwa cikin gidan gonar tasa wacce yake jiyo ihun matasa da kuma ambatan sunansa da suke,yana zuwa aka ja masa kujera ya zauna,yana zama ya lumshe idanunsa kafin a hankali ya buɗesu ya sauke akan dubban matasan da suke wajan,wani daga cikin matasan yace “ALLAH ya taimaki Jalal bobo,ya ɗaukaka in sha Allah mulki kamar kayi ka gama ne, maƙiyan ka sai dai suji kunya,alfarmar Annabi da Kur’ani saika zama shugaban ƙasar ibadan saika kawo mana sauyin da muke fatan samu,sai ka kawo mana ƙarshen matsaloli mu,sai ka ingatan makarantun gwamnati,sai ka  tantance mana ingantattun malamai da kuma likitoci,saika magance mana shigo da gurɓatattun magani cikin wannan ƙasar tamu saika magance mana (women trafficking *_Sabon littafi nan da bayan sallah_*) safarar matan da ake zuwa wata ƙasar da niyar aiki kuma sai anje aga ba haka bane,aita lalata mana yaranmu da iyayanmu in sha Allah kai ne garkuwarmu” gaba ɗaya suka haɗa bakin wajan faɗin “Ameen ina sha Allah”

Murmushin sa na gefe wanda yake ƙara masa ƙyau yyi kafin yaja kujerarsa baya kaɗan ya fara kallonsu ɗaya bayan ɗaya yace “Ma sha Allah, Allahamdulillah nagode ƙwarai da soyayyarku kuma ina addu’ar Ubangiji ya bani ikon sauke wannan nauyin da zai hau kaina” ya ƙare maganar yana sauke wani wahalallan numfashi sbd tsayin da maganar tayi masa, Jafar dake gefen sa ne yace.

“Munayi maku barka da zuwa,kuma muna fatan zuwanku ya zame mana alkairi,kuma muna fatan zaku mara mana baya har abada zaku jajirce akan abinda kukeso kada ku juya mana baya,ku zama masu ƙarfin guwwa da kuma tsayawa akan ra’ayinsu,sannan muna buƙatar mutum ɗaya a cikinku wanda zai zame maku jagora wanda kuka amince dashi,sannan munasu ku zaɓi mutane wanda zasu dinga yi mana campaign a social media da kuma muta nan da zasu dinga shiga gidan redio,t.v suna yaɗa manufarmu,dukkan wani taimako daza muyi maku zaku samesa ta hannun mutumin da kuka zaɓa matsayin jagorarku”

da wannan maganar suka gama taron,sannan suka zaɓi shugabansu mai suna Prince Hassan,gaba ɗaya matasan wajan sai murna suke suna ihun daɗi,lokaci guda ƙaunar Jalal bobo ta shiga zuƙatansu, Lamir bayan sun gama nasu meeting suka tsaida maganar da suke ganin za suyi amfani da ita wajan ruguje soyayyar da mutane sukewa Jalal bobo, a main parlour Jafar da Jalal suka samu Abbou da Dasu Mameey zaune sai kuma Lamir wanda yake zaune kusa da Mama an cika masa gabansa da kayan motsa baki, Lamir ne yace “wlcm son,kuma president to be” kallonsa Jalal yyi dan ganin inda maganar tasa ta dusa sai dai babu wata alamar da fuskar Lamir zata nuna baya cikin farin ciki, kansa ya ɗauke yace “wlcm uncle” Lamir yace “thanks sai na kejin abin arziƙi,ai nace zama bai kamani ba shine babu shiri na nemi ticket na dawo domin a fara shirin zaɓe dani” Abbou yace “Lamir amma naga kamar ba jam’iyyar kake ba,domin kowa ya sanka da President Mubarak Yahya cibo,shiyasa nake tunanin abun” murmushi Lamir yyi yace “haba Alhaji Kabeer ai gida yafi waje,tayaya zanyi adawa da jini na,dukkan abinda nake samu wajan President bazai  kai alaƙar jini muhimmanci ba,dan haka muna nan zamu fafata” jinjina kai Abbou yyi cike da farin ciki kafin yace “kai abu yyi daɗi Allah ya taimake mu, Allah ya ƙara zumunci “gaba ɗaya suka amsa da “Ameen” murmushi kawai Lamir yake tare dacin abincin dake bagabansa,Jalal bai ƙara magana ba ya shige cikin part ɗinsa bayan yyi wanka ya sauya kaya zuwa na shan iska ya ƙarasa parlour’n ya ɗauki apple da maltina ya dawo saman sofa ya zauna, system yaja ya fara searching akan women trafficking ɗin da suka faɗa masa ɗazo da kuma drugs ɗin da ake shigowa dasu ba tare da Nafdac ta sani ba.

A can Birnin nufar Papa ne zaune gaban uwa sundu yana kirari tare da ɗura hannunsa a sama yana jujjuyawa tare dayin sama da ƙahon kansa,sai da ya shafe awa guda kafin wani abu ya fito daga hannun uwa sundu ya sauka a nasa hannun,da sauri ya duba hannunsa abinda ya gani ba ƙaramin tayar masa da hankali yyi ba, cikin tashin hankali ya kalli jinin sannan ya kalli uwa sundu yace “Me nai maki uwa sundu mene yasa ba zaki amshi addu’a ta ba? ko laifin jikanyata ya shafan? bana da hannu a gudunta sannan bansan inda take ba kamar yadda na faɗa maki,da nasan inda take nida kaina zan kawo maki ita ki yanke mata hukuncin daya dace da ita,domin ita  kaɗai ce ta fara bijirewa umarnin ki a wannan birnin mai ciki da iko da kuma tsantsar al’ada” ya faɗa cikin harshansa na Jewish, wata ƙara uwa sundu tayi tare da fiddo da hannunta ta fisciko Papa gabanta kafin ta fara magana cikin wata iriyar murya tace “kayi babban kuskure daka bar wannan matar a cikin birninmu,babban kuskuren da kayi na barin jikanyarka data gudu, kuskure uku akai a wannan birnin wanda bazai taɓa gyaruwa ba,na farkon kai da kanka ka aikatasa,babban tashin hankalin dani uwa sundu na shiga yadda naga wani babban al’amari yana shirin tunkaro mu” zufar data yankowa Papa ce yasa yyi saurin miƙewa tsaye yace “yanzu uwa sundu mene mafita? wacce hanya za’a bi a gano inda jikanyata take sannan mu bada auranta ga Jushoa” wata dryar ta ƙarayi kafin tace “tana cikin wani hasken wanda indai ba barinsa tayi ba,baza mu taɓa samun galaba a kanta ba,duk yadda za’ai mu rabata da wannan hasken sai munyi,domin idan muka barta tabbas zata rushe mana wannan daular tsakanin ita ko hasken dole za muyiwa wani turan aljanu domin su shiga jikinsa su wargatsa masa dukkan wani shirinsa,zai kasance wannan aljanun shune zai taimaka mana wajan ganin ta dawo birnin nufar..

bayan Papa da uwa sundu suka gama tattaunawa ya fice da sauri zuwa can fadarsa inda ake zaman jiransa,yana zuwa ya samu dubban mutanan da sukai na sarar karɓar budurcin wacce tayi masu,wasu kuma sukace gsky bata da daɗin mu’amala,bata da ni’ima  sannan tana da raki dan haka zasu jira wata shekarar kafin nan wasu matan sun ƙara tasuwa, Jabir yana zaune ya haɗa kansa da quiwa yana kallon yadda Katarina ke kokawa da Zulfa wacce taƙi zama sai kukan kuraye take tana nunawa Jabir teddy hannunta,bawai yana fahimtar abinda take faɗa bane,amma a tasa fahimtar yana ganin kamar wani abunne ya samu teddyn hannun nata, miƙewa yyi jiki a sanyaye ya ƙarasa inda suke tsaye tare da kallon Katarina yace “matsa gefe muga” kallonsa tayi tace “amma jikin Ummi na ban tsoro kalli abinda take?” hannu yasa ya kama hannun Zulfa da sauri ya janye sbd cizon data sakar masa a hannunsa,wata tsayawa ya daka mata kafin a hankali ya fara tofa mata addu’a yana daga tsaye,idanunta ne suka fara rufewa jikinta ya saki gaba ɗaya sai wani hayaƙi daya fara fita ta hancinsa,ganin tana shirin faɗuwa yyi saurin matsowa ta faɗa jikinsa, rungome ta yyi sosai,yana shafa kanta sai a lokacin wasu hawayen tausayinta suka fara sakko masa daga cikin idanunsa gaba ɗaya jikin nata ya rikice a ƴan kwanakin nan,gashi Papa ya hanashi barin birnin bare yaje wajan malam ya amsar mata maganin.

Jalal na zaune yana operating system turo ƙofar parlour’n sa akai a hankali ya ɗaga idanunsa yaga Mummy ce, murmushi yyi yace “wlcm Mom” shuru tayi kafin tace “me kake yanzu bobo?” ba tare daya kalleta ba yace “ina bincike ne akan wani abu Mom”shuru tayi masa tana kallon sai da yaji shurun yyi yawa yace “ya dai?” numfashi ta sauke tace “Jalilerh babu lfy wajan ƙwana biyu,baka tambayeta ba sannan nima ban gaya maka ba,kuma ita ba fitowa parlour take ba,amma ciwon nata ya tsananta” yana kallon system ɗin yace “to akaita asibiti mana” kafin Mummy tayi magana Nihila ta shigo da gudu tana haki tace “Mummy Ja…Ja.. Jalilerh c…,” bai jira yaji abinda za tace ba ya fice da sauri ya nufi part ɗinsu a hanya sukaci karo da Aryan wanda ya taho da gudu gaba ɗaya sukayi cikin ɗakin..

A ƙwance suka sameta ƙasan carpet kumfa na fita ta cikin bakinta kamar mai dafara,da sauri Aryan ya ƙarasa inda take ƙwance babu numfashin kafin yayi wani yunƙuri Jalal ya sanya duka hannunsa ya ɗauketa cak zuwa jikinsa,ba tare daya kalli kowa ba, ya nufi wani part yana shiga ya buɗe ɗan ma dai-dai cin room ɗin wanda yake tamkar chemist,wani ƙaramin bed na marasa lfy ya ƙwantar da ita,yana gamawa ya nufi waje a baƙin room ɗin ya samu duk ƴan gidan, fuska ya haɗe yace “me kuke a nan to?” kafin kowa yyi magana Aryan yace “yaya kalli fa ko numfashi ba tayi,dan Allah bari na shiga naganta Please” banza yyi masa yyi huce  zuwa part ɗinsa wata box ya ɗauka ya koma part ɗin lokacin sun koma parlour ya rage Nihila ce da Aryan wanda ya sunkuyar da kansa ƙasa kamar mai nazarin wani abun,babu wanda ya kula cikinsu,ya shige cikin room ɗin tare da rufe ƙofar,yana zuwa ya sameta kamar yadda ya ƙwantar da ita, zuwa yyi ya zauna bakin bed ɗin tare da ɗaukan hannunta yana dubawa,bayan ya duba ya miƙe ya fara duba inda zaiga allurar suma, kafin ya ɗauka yaji ta kira sunan da ƙarfi da sauri ya juya ya sameta tsaye tana kokawar kama wani abu ƙarasawa yyi kusanta,a hankali ya sanya hannunsa a saman waist ɗinta ya riƙe ta ƙam a jikin jikinsa,still ba ta daina abinda take ba,da kƴar ya ɗauketa ya nufi inda bed ɗin yake,zama yyi da ita a jikinsa kafin yasa hannu ya tallafo haɓarta, ɗan waro idanu yyi waje kafin ya saka hannu ya ranƙwashi kanta yace “eyee kune ashe” cikin ƙasa da murya yace “Jalery” ƙasa ɗaga idanu tayi ta kallesa,kuma bata bar kokawar da take ba,sai wani ihu take ƙasa-ƙasa  gaba ɗaya ta yaƙoshe masa ƙirjinsa sbd singlet daya saka, ƙara jawota jikinsa yyi ya matse ta a hankali kuma ya saka tafin hannunsa ya a saman goshinta ya fara murzawa, ƙasa ya ƙarayi da bakinsa dai-dai saitin kunanta yyi bisimillah kana ya fara karanta Ayatul-qursiyyo tun tana bige-bigen har jikinta yyi laƙwasar ta fara sauke masa numfashinta a ƙirjinsa,hura mata iskar bakinsa yyi kafin yace “Jalilerh” wannan shine karan farko daya taɓa kiran sunanta,can yaji tace “ba ita bace” waro idanu yyi waje alamar mmki,kafin ya shafa sumar kanta yace “ashe? koma waye ita nake nema ba wani ba” ƙara shigewa jikinsa tayi tace “meye haɗin ka da ita? ka daina wasa da jinnu ɗan yaro” lumshe idanu yyi yace “canta matse maku, maganar meye haɗina da ita ku uban mene haɗinku da ita” ya ƙare maganar yana dungure mata kai” ihu tayi tace “wayyo ka tsokanan idona ka rabu damu muyi aikinmu,ka fita sabgar da babu ruwanka” gyara zama yyi yace “gaba ma idon zan cire,dalla ware nina gaji da ganinka,banza mara tsoran Allah” itama cewa tayi “idan kaga muntafi to mun kammala aikinmu,sannan bamu shiga jikinta danmu cutar da ita ba, muma aikomu akai” ƙara ware manyan idanunsa yyi waje cikin gajiyawa yace “to baku da wajan zama jikinta,domin ita ɗin rayuwa tace,duk wanda ya turoko kuce ni Muhammad Jalal bobo nafi ƙarfin sa” dry tayi tace “koda mun tabi wasu zasu dawo domin baza mu taɓa barinta ba” murya ya gyara ya fara karatu cikin nutsuwa yana tofa mata a kunne,ihu ta kurma har saida ya saka hannu ya toshe mata baki,cikin wata murya tace “to wai kai na taɓa ganin musulmi ya zauna da arne ne?” cije lips yyi yace “to ai yanzu kaga alama ko? to maza jeka kafin na sauya maka ka manni” kaita ɗago a hankali ta kallesa sai kuma ta kwaɓe fuska tace “me mukai maka, shikenan zamu tafi amma ka shirya dawowarmu a ko wanne lokaci” tana faɗin hakan tayi atishawa sau uku sai kuma tayi ƙwance jikinsa luff tana sauke numfashi, ƙara shigar da ita jikinsa yyi sbd zafin da jikinta ya ɗauka,a hankali yaci gaba da shafa sumar kanta yana ƙara tofa mata addu’a.
Uwa sundu ce ke tsaye hannunta sai fidda wani irin haske yake,ta ɗauki wajan 5minutes kafin hasken ya ɗauke,tana a tsaye jushoa ya shigo yana zuwa ya baje gabanta tare da ɗaga hannunsa sama,kansa ta shafa tare da zana masa wani jan abu, dry tayi tace masa “komai yyi dai-dai daga yanzu zuwa ko wanne lokaci zata dawo zuwa birnin nufar,sai dai aƙwai babban lamari wanda nima na kasa ganesa,mun tura mata mutananmu sun zauna a jikinta domin su shiga cikin tunaninta” ƙara zubewa Joshua yyi yana ƙara ɗaga hannunsa sama yana yiwa uwa sundu jinjina” wata ƙarar rawace tayi ƙara alamar an amshi riƙonsa.
Abbou ne zaune a main parlour suna tattaunawa akan zaɓen cikin gida daya rage ƙwana biyu a gudanar dashi, Jalal ne yace “eh Abbou an gama komai kawai lokaci ake jira” Aryan ne ya kalli Abbou yace “Abbou wani taimako na keso wajanka ban sani ba ko zakamin? kallonsa kawai Jalal yyi Abbou kuma yace “haba ƴan uku mai zai hana indai ina da iko a kansa” Aryan yace “Abbou ina son Jalilerh aurenta nake sonyi” gaba ɗaya mutanan ɗakin suka ɗago kansa suna kallansa,banda Jalal wanda yake kallon b.b.c inda ake watsa labarai akan zaɓen da za’ai na cikin gida, Abbou numfasawa yyi yace “Aryan tayaya zan baka auran yarinyar dani kaina bansan wacece ita ba?” kan Aryan a ƙasa yace “Abbou Please, i love her da gaske zan aureta babu ruwana dako wacece ita,tunda dai yaya ne yazo da ita ai shikenan” Mama dake sakkowa tayi saurin faɗin “kulll na ƙara jin wannan maganar mu zaka janyowa jafa’i,yarinyar da take da gayyar aljanu uban me zakai da ita…, ohhh banda yaran zamani wazai kalli idon ubansa yace aure ya keso,mu namu auran sai munje ɗaki muke ganin wanda aka ɗaura mana aure dashi,yana ta rarrayarmu sbd mu zauna dashi,huuuuuh!! zamani ya lalace duniya ina zaki damu” haɗe rai Aryan yyi yace “kee sbd kinƙi auren shine zaki hana wasu? kuma yaushe nace aure na keso da zakimin sharri,idanma shi nakeso meye ruwanki ne kinjini da mata” salati ta rafka tace “uwarka salamutu da ita kake bani ba,shiyasa gsky tayi ƙaranci daga nace kayi aurenka abinka yafi ka zauna Kamar wannan basa mudan shine zakai min sharri,ato ai darajar ɗa namiji sai da mata,itako mace darajarta ɗakin mijinta” ta ƙare maganar tana shirin zama kan kujera taji ta zauna a ƙafar mutum da sauri tayi baya ganin ƙafar mutum,wani ihu tayi sbd arba da Jalilerh da tayi a ƙawance jikinta ya ɗauki rawa ta fara faɗin “wa’innahu sulaimanu” wani murmushin gefen baki Jalal yyi kafin ya ɗauke kansa yaci gaba kallon labaran, Aryan ne ya kalli Abbou yace “Abbou Please” kallon sa Abbou yyi yace “tambayi yayanka” kallon Jalal yyi wanda ya ɗauke kai tamkar ba yaji abinda suke faɗa,cikin Muryar damuwa Aryan yace “Please yaya help ur biogical brother” miƙewa Jalal yyi yace “bana da lokacin wannan shirmen..
Yana faɗin hakan ya shige part ɗinsa,Hibba na zaune ita da Hajja Ayushert ta kalli mahaifiyarta tace “Hajja what should I do,ina son shi? Wannan lokacin kine na samawa gudan jininki farin cikinta,mai yasa baki son abinda na keso,ina da kuɗi ilimi,dukkan abinda na keso ina samu,mene yasa ba zaki tayani samun soyayya ba?mene yasa keda Dad bazaku tayani son abinda nake so ba” ta ƙare maganar cikin rawar Murya, kallon ta Hajja tayi tace “kuɗi na iya siyan komai Hibba,amma ban isa na siya maki soyayya da kuɗi ba,bana da wannan ikon,tayaya ma zan tayaki son abinda ban sani ba?ke kanki baki san wane shi ba” shuru Hibba tayi domin tasan abune mai wahala Hajja ta fahimci abinda da ta keji a cikin zcyarta ba,dawa zatai sharing na damunwata ko besty zata kira ta gaya masa ya rabbi ,ta wulaƙanta kowa akan soyayya taci ZARAFI n mutane da yawa akan soyayya,da ace tasan abinda su keji kenan tabbas da batayi masu haka ba, miƙewa tayi tsaye tare da ɗaukan key ɗin motar ta,ta kalli Hajja wacce hankalinta yake kan labarai sbd maganar da taji wani Prince Hassan nayi akan ɗan takarar shugaban ƙasa tace “Hajja zani school yanzu,aƙwai wanda zanwa lectures zuwa yamma” kai Hajja ta ɗaga mata, a can Haske t.v kuwa Jalal ne zaune gaban ƴan jaridu gaba ɗaya sun saita Camera a kansa wasu kuma sun saita recording domin ɗaukan maganganunsa, ɗaya daga cikin ƴan jaridai ne mai Suna Sahabi yace “Muhammad Jalal bobo muna maka barka da zuwa,a ta ƙaice menene yaja ra’ayinka harka fito takarar shugaban ƙasa?” Hibba dake ƙoƙarin fita tayi saurin juyawa sabida sunan da taji an ambata na Muhammad Jalal bobo..
Da Saurin  ta zauna t tare da lumshe idanunta sbd arba da tayi da kyakkyawar fuskarsa wacce take cike da haiba kwarjini,yana sanye da wani maroon ɗin shadda mai ɗinkin wando da kuma half ɗin riga iya waist ɗinsa,sai Black ɗin hula da farin glass sai juya Fararan ƙwayar idanunsa yake,shuru tayi tana kallon sa kafin taji Hajja tace “ya naga kin zauna?” Kallon sa tayi tace “Hajja shine” tace “shine wa?” Cikin rawar murya tace “Hajja shi na keso shine wanda nake gaya maki” waro idanu tayi tace “what!? Kinsan me kike faɗa kowa,wannan fa shine wanda yake neman kujerar Dad ɗinki are you out of your sense Hibba? Kina da hankali kowa?” Itama Hibba tace “Hajja babu ruwana da harkar siyaysarsu ni shi na keso,shine kwanciyar hankali na” shuru Jalal yyi kafin ya ɗan ja kujerarsa baya tare da shafa sajen fuskarsa yace.
“Bana da buri ko sha’awar yin siyasa,hasali ma bata birgeni,sai dai a lokacin da naje karatu Paris naci karo da abubuwa wanda gwamnati bata taɓa magance sa,a lokacin naso na juya yanayin karatuna sai dai shima harkar lafiyar dana karanta is my hopely..,” shuru yyi sbd zafin da yaji maƙogarankansa nayi kafin ya ɗura da faɗin “Women trafficking,Na fahimci ƙalubalan da mata suke samu,ana amfani da talaucinsu ana lalata masu rayuwa,ana amfani da rauninsu ana ruguza masu farin cikinsu,wanda duk abubuwan dake faruwa da matan babu ƴar ƴan masu kuɗi cikinsu, gaba ɗayansu talakawa ne,shin talaka ba mutum bane? Shin talaka baya da ƴan cin kansa ne?.., ɗan jaridar ne ya katse sa da faɗin “Muhammad Jalal bobo kana mana bayani a cikurkuɗen,bani kaɗai  ba nasan da yawan mutane basu mafahimci mene kake faɗa ba, ko dai zamanka na Paris yasa ka manta harshen ka?” Jafar dake gefen Jalal yyi saurin kallon mutumin kafin ya janye idanunsa,Hibba shuru tayi na kallon yadda yake mutsa bakinsa a hankali,a nan kuma ta fahimci rashin ingantacciyar hausa da babu a bakinsa, murmushin president Mubarak Yahya cibo yyi kafin Lamir dake gefensa yace “bana gaya maka babu abinda ya iya,bari kaji wannan tambayoyin da akai masa bazai amsa ba,sai dai wancan mai siffar magen ya fanshe sa” dry sukai shida Gwamna Faisal Lawan suka tafa, murmushi shima Jalal yyi yace ” Ina nufin safarar mata..
Gaba ɗaya suka ɗaga kai suna kallon sa hadda president Mubarak Yahya cibo, numfashi ya sauke tare dasa hannu yaja ma dai-dai cin gemunsa yace.
“SAFARAR MATA shine abinda nake nufi,ana fakewa da guzuma a harɓi karsana,ana ɗaukan mata a matsayin za’a basu aikin yi ko kuma a sama masu aikatau a wani gidan masu kuɗin,abin mmkin shine yadda ba’a basu aikin yi a ƙasar da suke sai an fiddasu wani ƙasar da ban..,”shuru yyi tare da jan numfashi kafin ya lumshe idanunsa few seconds ya ware a kan camera,da sauri president Mubarak Yahya cibo ya sunkuyar da kansa domin ganin yake kamar shi yake kallo,duk da cewa basu taɓa ganin juna ba, murmushi yyi yace “abinda yake ƙara ban mmki idan an fiddasu wata ƙasar bawai aikin suke ba, a’a ana sai dasu ne ga wasu ɓata gari su kuma za suna pursing ɗin su sunayin abinda ba suyi niya ba,za suna sex dasu da sama da maza 4,ko matarka ta gida ba lallai ta juri hakanba bare ƴan mata wanda basu san matsayin hakan ba, human trafficking yana sanyawa rayuwar mata ta lalace wasu sanadin haka dukkan wani good habit nasu ya lalace,all this ace shugabanni basu san da hakan ba? Babu yadda za’ai ace ana fita da dubban mata wata ƙasar da niyar basu wani aikin ko kuma a kaisu aikatau ace shugabannin mu basu sani ba…,” Shuru yyi kafin yaja wani glass cup tare da ɗaukan bottle water ya ɓalle murfinta ya tsiyaya a cup ɗin tare da kaiwa bakinsa, bayan ya shanye ruwan ya ɗura da faɗin.
“Abu na biyu shine SHAYE-SHAYE”
Da sauri Jalilerh ta ɗago idanunta a hankali ta sauke a saman fuskarsa,kafin ta juya ta kalli Aryan dake kusa da ita,tana juyawa taga ita yake kallo, idanunta ta bayar kan t.v lokacin da taji ya ɗura da faɗin.
“Mun taɓa tunanin mene yasa ƴan siyasa basa saka yaransu a bangar siyasa? Mun taɓa tunanin mene yasa ba’a neman matasa sai lokacin siyasa ?mun taɓa tunanin mene yasa matasa basa da aikin yi a wannan lokacin?” Cije lips yyi tare da sunkuyar da kansa,sama da 20 seconds kafin ya ɗaga idanunsa yace.
“Matasa sune ƙasa,matasa sune iyaye,matasa sune shugabanni,amma yanzu an maida su ƴan shaye-shaye an maida rayuwarsu gurɓatacciya, shugabanni suna amfani da matasa a harkar siyaysarsu,suna haɗasu da manyan DRUGS menene aike faɗawa wata ƙawaya ma?” ya faɗa yana kallon Jafar,da sauri Jafar yace “a rungumi doki” taɓe baki yyi yace “i can’t call this name with my  munths, ƙarfi ƙwayar da yadda take aiki a brain yasa aka bata wannan sunan,wacce duk mutumin ɗaya shata kai tsaye cikin tunaninsa take shigewa ta hargitsa ƙwaƙwalwarsa, hakan zai sanya mutum ya dinga aikata abu ba tare daya san mene yake aikatawa ba,babban zunubin baza su taɓa sallah ba,sai Lokacin da ƙwayar  ta sake su suka daina mayan, kuma ace ASSALATU WAƘATIHA shin su mene nasu hukuncin a nan? Mene za suce idan Ubangiji ya zare ranka a wannan halin? Mene yasa shugabanni basu taɓa cewa matasa su kawo takaddunsu na makaranta domin sama masu aiki ba? Mene yasa basu taɓa bawa matasan da suke sonyi karatu kuma basu da hali damar kai takardunsu domin kaisu wata makarantar domin su samu in gantaccen ilimi..” ƙara ɗago kai yyi kafin ya sauke ajjiyar zcy ya ɗan ja kujerarsa baya kaɗan kafin yace “shima kuna nufin shugabanni basu san hakan ba dai-dai bane?,daku nake matasa da iyayen yara baku taɓa tunani abinda sukewa yaranku ba dai-dai bane rayuwarsu kawai ake ruguza wa..!!!? Ya ƙare maganar cikin tsayawa tare buga mencin dake kusa dashi,calmy yyi kafin ya fara jujjuya kujerar yana ƙarewa mutanan wajan kallo, watch ɗin dake manne a tsintsiyar hannunsa ya kalla wanda ya kasance apple,gani yyi  5:30 saura minti 5, ɗan jaridar ne yace “yallaɓai muna jinka” ware idanunsa yyi waje shi kaɗai yasan suyar da maƙoshinsa yake masa sbd yawan mgnar da yyi,fesar da numfashi yyi ta bakinsa kafin yace.
“FYAƊE zuwa yanzu naga abin ya zama kamar ruwan dare a cikin al’umma,yau kaji an ce anyiwa waccan Fyaɗe gobe kaji an ce ayiwa waccan jibi kuma ba’a san mene za’a ce ba,uhmm an taɓa ɗan kan hukunci akan wanda yyi zina da auransa? An taɓa ɗaukan hukunci akan saurayin daya aikata hakan,daku nake Al’kalai nasan kunsan menene hukuncin wanda ya aikata zina da auransa,haka kuma kunsan hukuncin da akewa saurayin da yyiwa wata fyaɗe ku koma zina, kun taɓa tambayar kanku mene ya saka yawan Fyaɗe yake ƙara yawa a ko wacce rana? To me ina ganin rashin sana’a da matasa basu da ita bare har suyi tunanin yin aure,hakan tasa da zarar namiji hqrinsa ya gaza zaije ya akaita Fyaɗe,nasan da yawan matasa a yanzu suna da burin aure amma rashin…,” Shuru yyi kafin ya juya ya kalli Jafar cikin ƙasa da murya Jafar yace ingantacciya, lumshe idanu yyi yace “rashin in…in..ingantacciyar Sa’a da basu da ita yasa kowa ya ajjiye maganar auran a gefe,da ace wata rana gwamnati zata bawa matasa offer ta aiki nasan babu shakka yawaitar Fyaɗe a cikin al’umma zasu ragu” ɗan jaridar ne yace “Yallaɓai kana nufin gwamnatin yanzu bata ƙoƙari akan wannan abubuwan da kake faɗa?” Kallon ɗan jaridar yyi kafin ya gyara zamansa yace “to aini kome na zama sanadin gwamnati ne,why zance ba tayi? Ina faɗin abinda nake ganin suna faruwa da idanuna wanda kuma dalilin hakan ƙasarmu ba’a ci gaba kenan, gwamnati tayi min komai domin ita ta bani damar abinda na zama a yanzu,bazan manta da karamcin gwamnatin baya ba,shekaru kusan 28 kenan” jinjina kai yyi kafin yace “gsky yallaɓai ban taɓa ganin mutum mai karamci da kuma kammala haɗi da hikimar tsara mgn ba, kayi magana ta hankali kuma babu wanda zai ce ka tsoki wannan gwamnatin,samunka matsayin shugaba a yanzu ba ƙaramin cigaba zai haifar a wannan gari namu na ibadan ba, jinjina ga yallaɓai Muhammad Jalal bobo” kamar haɗin baki da mutanan da suke wajan shirar wanda sukai masa rakiya da kuma al’ummar gari sukace “jinjina ga Muhammad Jalal bobo” Hibba take zaune kusa da mahaifiyarta tace “all the best my love” kallonta hajja Ayushert tayi kafin tace “ki iya takunki a cikin gidanan wlh kika sake mahaifinki yaji ko ya gane wa kikeso kinsan sauran basai na gaya maki ba,da wannan shirar Jalal ya kama hanya tare da mutanan da sukai masa rakiya zuwa wajan.
a parking space Jafar yyi parking motar domin Jalal bai cika son securities su dinga binsa ba,ana gama parking Jafar ya fito ya buɗe masa motar yana fitowa ya kaiwa Jafar duka yace “ɗan iska kamar na sashi,kada ka sake buɗen mota ina da hannu” cikin tsokana Jafar ya sunkuyar da kansa ƙasa yace “am so sorry ur excellence ban ƙarawa” banza yyi masa ya shige ciki a main parlour ya samu kusan duk ƴan gida harda Nusaibat,tana ganinsa ta sunkuyar da kanta ƙasa kafin tace “ina yini yaya” baiko kalli inda take ba ya huce wajan Mama ganin tana sharar hawaye hadda majina, kallonta yyi da alamar tambaya kafin yyi mgn Nihila tayi saurin faɗin “yaya wai mgnar da kayi ta kema kuka fa” wata majinar ta face a bakin zaninta kafin ta kalli bobo tace “Ashe haka kake da zcyar imani da tausayi buba? Nidai kaya feni dan har zcyta ina maka kallon mara mutunci musamman idan kaƙi siyomin wannan abun na zoƙa,ahhh to bazan munafurceka ba tunda ba ubana bane kai,amma dai angona kayi hqr kada na tafi lahira da zunubinka” dry Jafar yyi yana zama a kujerar dake kallon Nihila yace ” Thanks God yau Mama ta yadda zata mutu” waro idanu tayi waje kafin tayi saurin miƙewa tsaye tana karkace ƙwankwaso😂 tace “Tabbas mutuwa sai dai ka gani a kanka,amma wlh ni yanzu na fara zama a duniya”huuu nida nake saka ran yin sabun aure na fice na bar maku gidanku” dry sukai kafin ta ɗura da “ahhh to nidai babu ruwana yuuuu duniyar gaba ɗaya nawa take” tana faɗin hakan ta shige part ɗin ta, Jalal bai tsaya ba yyi hucewarsa part ɗinsa, Jafar zama yyi suka ci gaba da hira dasu mummy da Mameey,yana shiga part ɗin nasa ya fara zare kayan jikinsa bayan ya gama ya saka su a inda yake ajjiye kaya masu datti,kai tsaye bathroom ya nufa ya sakarwa kansa shower sosai yaji daɗin ruwan sbd sanyin dake ratsashi yana sauka akan fresh skin ɗinsa,Lamir ne zaune shida Gwamna Faisal Lawan suna tattaunawa akan yadda zasu lalata zaɓen da za’ai a gobe,gaba ɗaya Jalal ya wargatsa masu plan ɗinsu,tun yana ganin abin wasa har ya gagara fahimtar abinda zai yi, murmushi yyi ya kalli Faisal Lawan yace bani kunanka kaji,da sauri ya miƙa kunna sa wata dryar mugun ta sukai a tare kafin gwamna Faisal Lawan yace “gsky Lamir baka da imani,kuma kasan idan wannan abun yyi yadda muke so kashin Muhammad Jalal ya bushe” tafawa sukai Lamir yace “ahhh niɗin na wasa ne” fitowa yyi cikin shigar sa ta shan iska,daga shi sai wando three gaiter ko singlet babu jikinsa,sai fresh skin ɗinsa wacce take ta sharning,zama yyi kafin ya kunna t.v ya fara kallon labarai har lokacin shirarsa ake watsa,inda akai translation 
ɗinta da harshe kala-kala, wayarsa ya ɗauka yyi dailing number Mummy ringing ɗin farko ta ɗaga tace “my love ya akai?” numfashi ya sauke yace “Mom yunwa,bawa beb ko wannan yarinyar su kawo min part ɗina” murmushi tayi tace “ok” kallon Jalilerh tayi tace “my dear jeki haɗawa Uncle ɗinki abinci” kafin ta tashi Abbou yace “dear zauna abinki Nusaibat jeki kai masa..
Miƙewa Nusaibat tayi zcyarta fal farin ciki, kitchen ta shiga ta ɗauki tray ta haɗa masa dukkan abinda ya dace dashi, bayan ta gama ta nufi part ɗinsa,da idanu kawai Jalilerh da Nihila suka bita, Abbou murmushi kawai yyi kafin ya miƙe ya nufi part ɗinsa,yana zaune yana operating system ɗinsa yaji anyi sallama,jin baƙuwar murya yasa ko ɗaguwa baiyi ba,yace “Wasallam” yana faɗin hakan yaja bakinsa yyi shuru,ƙarasa shiga tayi tare tajan table ta ajjiye masa tray ɗin abincin akai,durƙusawa tayi kafin tace “ina yini yaya?”  banza yyi mata kamar baiji me tace ba,kanta a ƙasa ta ƙara cewa “yaya” da sauri ya juya ya kalleta kafin cikin ɗaga murya yace “out!!…
6/10/21, 1:10 PM – Buhainat: _Duk yadda kaso kayi rubutu perfect ba tare da wani matsala ba hakan ba faruwa,nayi mamakin yadda na kasa gane kuskuren, sannan nai mmkin yadda marubutan da suke karantawa suma suka kasa ganewa,sai wata daban ta gane, a Nigeria muna da state 36 muna da OYO wacce ta kasance state,sannan muna da IBADAN wacce ta kasance Capital a garin OYO, nace *Muhammad Jalal Kabeer bobo* na neman takarar shugaban ƙasa president kenan,bayan idan president ke nema sai dai nace na Nigeria baki ɗaya😂,a nan kuskuren yake *Muhammad Jalal bobo* ta karar governor yake nema a IBADAN ba president ba,so Please gusy babu baya kuskure aimin afuwa, shi RUBUTU kamar rayuwa ce,kamar yadda babu wanda yasan mene zai faru da mutum gobe ko jibi,haka babu wanda yasan mene zai faru next a cikin littafi abinda muka sani labarin daga farko zuwa ƙarshe an riga da an gama tsara shi,rubutune kawai ya rage✍🏻kuma shima in sha Allah babu tsayawa sai lokacin da Al’ƙalamina yaje ƙarshen labarin_Da sauri taja baya sbd tsawar da taji yyi mata, kafin ta kallesa tace “Abbou ne yace na gaisheka fa,me nai maka ne da baka son kulani yaya”ci gaba yyi da latsa system ɗinsa,ganin bashi da niyar kulara yasa taja jikinta zuwa parlour,tana fita ta samu Jalilerh zaune ita kaɗai ta rufe idanunta,zama tayi tace “Jalilerh ke ɗaya ce?” buɗe idanunta tai  kafin ta ɗauke kai tace “eh” murmushi tayi tace “kinga na daɗe ko,yaya ya tsaidani wai muyi Shira”kallonta kawai Jalilerh tayi dan a halin bobo yanzu babu abinda bata sani ba tace “yana da kyau ai” Nihila ce ta sakko tana faɗin “har kin fito?,naje ɗaki ɗauko laptop ɗina zan nunawa Jalilerh wani abune”miƙewa tayi tace “Nima zan huce ne,ashe haka bobo yake da kirki yau kam munsha Shira”waro idanu waje Nihila tayi kafin tace “Allah sarki” sallama tayi masu tabar gidan zcyarta cike da takaicin da kuma haushin abinda bobo yyi mata,tana fita ya ajjiye system ɗin tare da miƙewa tsaye ya nufi bedroom kai tsaye bathroom ya shiga ya ƙarasa gaban sink ya wanke hannunsa,yana fitowa ya zauna gaban table ɗin tare da buɗe wermers ɗin,dambun shinkafa  ya gani wanda yaji albasa da zugala da gyaɗa,sai tashin ƙamshi yake yaji kifi,yana gama zubawa a plat Jalilerh na turo ƙofar parlour’nsa tana shigowa,zama tayi kusa dashi tare da yin shuru ta sunkuyar da kanta ƙasa,spoon ya ɗauka ya ɗibi dambun tare da kaiwa bakinsa, daɗi da kuma garɗin gyaɗar daya ratsa kunansa yasa yyi saurin lumshe idanunsa,tunda ta shigo bai kalleta ba a hankali yaci gaba tacin dambun har yaci rabi, ɗaya wermer ɗin ya buɗe yaga zallar kayan cikin rago wanda akai farfesun yaji daddawa da kayan ƙamshi, spoon yasa sau uku yaci ya rufe wermer ɗin, miƙewa yyi ya nufi ƙaramin fridge ɗinsa ya ɗauki bottle water mai sanyi ya ɓalle murfinta sai da ya shanye tass sannan ya ajjiye emty bottle ɗin a side ɗin fridge,sai a lokacin idanunsa suka sauka akan ta yanzu tana durƙoshe ta cure waje guda jikinta duk rawa yake gargasar dake jikin ta duk sun mimmike,idanunsa ya ɗauke tare ɗaukan remote ya sauya channel zuwa sunna t.v yaci Sa’a ana karatun Kur’ani,yana kaiwa yaje kujerar da yake ya zauna.
Miƙewa tayi da sauri zata fice daga ɗaki shima da sauri ya miƙe ya nufi inda tayi tako ɗaya yyi zuwa biyu ya zafkota,dukkan ƙarfin ta tasa ta hankaɗesa baya yyi yana mai dafe kujerar dake kusa dashi,hakan ya tabbatar masa ba ƙarfin ta bane, ƙara suwa yayi wajan ta da sauri ya samu harta isa parlour,tsaye yyi sbd kokawar da yaga sunayi ita da Aryan gaba ɗaya ta wajigasa,jingine jikinsa yyi da jikin bangon tare na daɗe hannunsa a ƙirjinsa ya zoba masu idanu.
Mama dake rakuɓe a gefen kujerar jikinta duk rawa yake ta kalli Nihila itama da take a tsorace cikin ƙasa da murya tace “wlh kada ki yadda ta ganki,gaba ɗaya aljanun zasu dawo kanki,Nima ina budurwa haka wata tayimin wannan muguntar,sai gani da yada zani,kee abindai babu kyau,ba kiga yanzu na ɓuya ba” 
  Kallon Nihila tayi kafin tai magana taji an ƙwala ihu tare da zubewa ƙasa,ihu Mama tayi itama tare faɗin “wa’innahu sulaimanu wa’innahu bisimillahir rahim” shuru itama Nihila tayi tare toshe bakinta hawaye na zuba ta cikin idanunta, Abbou dake tsaye shima ya kalli Jalal yace “Bobo kana ganin abinda take,tana shan wahala fa,kuma Aryan ya kasa da ita” tagumi Mummy tayi abin na mata mmki Ita dai tunda take ba’a taɓa aljanu a gabanta sai yanzu dan duk ta tsorata tausayin Jalilerh ya cika mata zcy, Aryan ne ya kalli Abbou yace.
 “Abbou zan iya kula da ita kabar yaya ya huta”kallon sa Mameey tayi tace “rufen baki kalli yadda kake haɗa zufa tun ɗazo sai kokawa kuke kace Zaka iya” Mummy tace “no kibarsa mana,ai kinsan ƙarfin aljanu dana mutum ba ɗaya bane” Shidai Jalal na tsaye yana kallon kowa da ido,ana haka Lamir yyi sallama ya shigo, kallon su yyi tare faɗin “lfyanku kowa?” Abbou ne yace “inafa mutanan ɓoye suka fara damun dear a ƙwana biyun nan” kayan hannunsa ya ajjiye saman sofa kafin ya ƙarasa inda take ƙwance yace “ai ba’a barta haka ba, aƙwai wani malami dana sani sai a kaita can” sai a lokacin Jalal ya ɗaga kai ya kalli Lamir kallonsa yyi shima kafin yace “sannu bobo” jinjina kai kawai yyi kafin yasa hannu ya shafi sumar sajensa a hankali kuma ya fara takawa zuwa inda take ƙwancen yana zuwa yasa duk hannayensa ya ɗauke ta cak,kai tsaye part ɗinsa ya nufa,wani numfashi Aryan ya fesar tare dabin Jalal da kallo shi kaɗai yasan abinda ya keji a ransa,yana zuwa parlour’nsa ya shimfiɗeta a saman duguwar sofa kafin ya zauna gefen ta tare ɗagota zuwa jikinsa.
Tafin hannunsa a saman forehead ɗinta ya fara murzawa tare da ɗan bubbugawa,a hankali kuma yakai bakinsa saitin kunanta ya fara hura mata iska,cikin natsuwa kuma ya fara yi mata karatun yana jin yadda take fizga yaƙi sakinta saima ƙara matseta da yyi a jikinsa, sama da 30minutes yana abu ɗaya amma ko tari taƙiyi balle ya saka ran zatai magana,hannunsa dake saman goshinta ya ƙara murzawa tare da dukan goshinta wata ƴar ƙara sukai kana tayi atishawa,lufff tayi a saman ƙirjinsa tana sauke numfashi, shuru yyi shima yana jin yadda jikinta ya ɗauki zafi,tambayar da yake wa kansa dama tana dasu ne,ko kuma yanzu ta samu,idan yanzu ta samu a ina?wanan shi ne tarin tambayoyin da suke zcyarsa amma babu wanda zai tambaya.
Ajjiyar zcy Aryan ya sauke yace “Abbou tunda kaji nace ina sonta ai aurenta nake da niya,wlh ban taɓa ganin macen da tayimin irinta ba, tun lokacin da yaya yazo da ita na fara sonta, Abbou idan kaƙi bani ita wazan nema ya ban ita,kace naje wajan bobo kana ganin ko kulani bai yi ba bare na saka ran zan samu abinda nake so a wajansa” Abbou ne yace “shikenan kaje ka samu soyyarta tukunna” sai lokacin Mummy tace “kada ka damu son zanwa bobo mgn,nasan bazai ƙi ba” miƙewa yyi tare da yin waje yabar gidan gaba ɗaya.
“Amma ya dace a sama mata magani domin naga da ƙarfi suka kamata” Mameey ta faɗa cikin tausaya wa, Lamir ne ya ƙarasa cin abincin dake bakinsa yace “ahhh to ai nayi mgnar hakan babu wanda ya tanka” Mummy tace “ba haka bane yaya, lokacin hankalinmu ne gaba ɗaya baya jikinmu” da sauri Lamir yyi baya tare faɗin suwaye a bayan sofa kuma?” Kafin ai magana Mama fito tana rarraba idanu, kallonta Mameey tayi tace “Mama mene a jikinki kamar ruwa?” Daga bakin ƙofa akace “mene kowa banda fitsari” Abbou ne yace “gidanku Irfan Mama kake gayawa haka” ita dai Mama babu wanda ta kula tayi part ɗinta ruwan fitsari na bin jikinta,daman Nihila tunda aka ɗauke Jalilerh daka wajan tayi nata part ɗin da gudu.
Da sauri Jalilerh ta ƙwace jikinta daga na Jalal wanda bacci ya fara ɗauke sa, miƙewa shima tare dasa hannu ya kamota ganin kamar bata cikin nutsuwarta cikin wata murya tace “Uncle ka fita dani,banson gidan nan, Uncle zasu kamani ga sunan wlh,wayyo Uncle zasu kasheni”saurin rungome ta yyi a jikinta yana bubbuga bayanta tare shafa sumar kanta,
Ƙanƙamesa tayi tare da ƙara faɗin “Uncle ka gudu dani zasu kamani ina tsoransu Please Uncle” bakinsa ya sanya cikin nata sbd bai ƙaunar jin abinda take faɗa,gaba ɗaya idanunsa ya sauya kala zuwa jaaa,jijiyar kansa ta mimmiƙe,a hankali shima jikinsa ya ɗauki rawa sbd sarawar da kansa yyi masa, ƙara rungome ta yyi sbd jin yadda jikinta ya ɗauki rawa gaba ɗaya,bakinsa ya cire daga nata tare dasa hannunsa ya ɗauke ta cak yyi cikin bedroom da ita,yana zuwa ya ƙwantar da ita,shima ya ƙwanta remote ya ɗauka ya ƙaro gudun a.c,gaba ɗaya a tsorace take hakan yasa ta shige cikin jikinsa tana sauke numfashi, lumshe idanu yyi a dai-dai kunanta yace “sleep, nothing happen am with you, Uncle ɗinki na tare dake” ya faɗa yana bata peak a goshinta,kanta ta ɗura saman ƙirjinsa ta ƙanƙamesa,shima rungome ta yayi babu jimawa bacci yayi gaba dasu a tare.
 Washegari tun da safe ya fita sbd a ranar za’a gabatar da zaɓen primary election wato zaɓan cikin gida,wanda yake neman ƴan majalissu su mara masa baya kuma yaji Sa’a a kaso 10 7 zuwa 8 suna bayansa, parking Lamir yyi a compound na gidan yana gama parking ya fito daga cikin motar ya nufi parlour, Mama ya samu sai Jalilerh kallonsu yayi yace “Mama ya naji gidan shuru?” Taɓe baki tayi tace “Salamutu da Jamal sunje kasuwa,Nibala ko niwad ohuuu mata,ta leƙa nan maƙota daga Ni sai wannan mai aljanun” ta faɗa tana nuna masa Jalilerh, murmushi yyi yace “daman nazo ɗauka ta ne zuwa wajan malam”washe baki Mama tayi tace “yawwa irin albarka maza kuje a cire su,nake gaya maka ƙwana nake babu bacci sbd far gaba” ledar hannunsa ya miƙa wa Mama yace “banson mutum gidan susan nine nai mata magani,dan haka kada ki gayawa kowa nazo na tafi da ita,idan zan dawo zan ƙaro maki wani naman” cikin farin ciki Mama ta yagi cinyar kazar takai bakinta tace “jeka abinka daman wake faɗar aikin lada, nina san me zance” murmushi yyi yace “my dear zo muje ita dai Jalilerh kallonsu kawai take dan bata da ikon cewa ba zata bane,kwaɓe fuska tayi tace “Mama ban sanshi ba ai” tsaki Mama taja tace “kamar yadda buba bazai cutar dake ba shima haka,to na taƙaice maki zance ni nayi naƙudarsa na shayar dashi da wannan nonon dake jikina,maza tashi kuje keda za’a taimaka ina ke ina iya yi” jiki na rawa Jalilerh ta miƙe hannunta ya kama yace “muje beauty” har mota ya sata sannan yaja motar ya fice da sauri, Jalal na can amma san hankalinsa yaƙi ɗaya haka nan ya samu kansa da tunanin gida,ganin ba’a fara zaɓan ba ya ɗauki ƙaramar wayarsa wacce amsa kira masu muhimmanci yyi dailing number Abbou, Abbou yana tsaka da driving yaji wayarsa na ƙara ɗauka yyi tare faɗin “fatan lfy  dai bobo?” Daga can Jalal ya saki ajjiyar zcy yace “Abbou kada a bar yarinyar nan ta fita koda ita da wani ne” murmushi Abbou yayi yace “yanzu dai na kusa gida,in sha Allah hakan bazai faro ba, Allah ya taimaka” Jalal najin hakan ya kashe wayar yaci gaba da sauran abinda wasu ƴa Majalissu suke faɗa masa.
Lamir na fita Abbou na shigowa Mama ce zaune a parlour ta tisa ƙatuwar kaza tana ci, kallonta yayi yace “mutan gidan basu dawo bane” taɓe baki tayi tace “sa dawo tunda sunbar baiwa a gida”kallon ta yayi yace “Jalilerh fa” tace “tana can tayi bacci yanzu tabar nan ai” jinjina kai yyi yace “bari na dubata” da sauri Mama ta miƙe tsaye tare faɗin”ohhhh ƙarya zan maka kenan ko Kabeeru?” Yace “a’a ba haka nake nufi ba kiyi hqr”yana faɗin hakan ya shige part ɗinsa.
6/10/21, 1:11 PM – Buhainat: Yana driving yana murmushi jifa-jifa kafin a hankali ya juya kan motar zuwa wani waje na daban,a gaban wani kango yyi parking tare da kashe motar ya fito,tana zaune cikin motar idanunta a kansa ga hawayen da yyi ƙwance a cikin idanunta,murfin side ɗinta ya buɗe t fuska babu yabo babu fallasa ya kama hannunta zuwa cikin kangon,yana shiga tayi saurin yin bayansa sbd mutanan data gani wajan mutum goma,daga can ɓangaren aka fara tafi kafin Hon Faisal Lawan ya fito daga cikin wani ƙaramin ɗaki hannunsa riƙe da wata Camera yace “aiki da kai huce takaici,kayi ƙoƙari kayi komai cikin sauƙin”
Wata dry Lamir yyi kafin yace “duk wanda yaci tuwo damu ai miya yasha,wannan yarinyar ita zata wargatsa masa dukkan wani shirinsa,ita zata sanya baƙin ciki a zcyarsa,ita zata sanya masa hawan jini,ita zatai siya wargatsa ɗan ƙaramin farin cikin da yake dashi, tabbas wannan yarinyar zata zame masa masifa a cikin rayuwarsa,ita zata sanya yyi baƙin jini a idanun jama’ar ibadan da kewayanta” gaba ɗaya wajan suka ɗauki ihu tare da tafa hannu,kallon wani yyi yace “ɗaureta” riga ta riƙe masa jikinta ya ɗauki rawa a tsorace tace “Kaiji wajan Uncle ɗina,mai dani gida” kallonta yayi yace “haba shalele yanzu zaki koma gida wani aiki zakimin baki son ki taimaki ɗan uwan Uncle ɗinki?” Cikin kuka tace “am scared,ina tsoran mutanan” taɓe baki yyi kafin ya juya yace “ba’a bin da za suyi maki yanzu zan dawo”yana faɗin hakan ya fice daga cikin kangon,cikin motarsa ya shige tare zama ya kyakkyata dry kafin yace “Muhammad Jalal bobo ka gama yawo” yana fita wani yazo yaja hannunta tare ɗura ta a saman wata kujera, hannunta ya kama tare da ɗaurewa da wata igiya sai kuka take tana kiran sunan Uncle,sai da suka ɗaure ta ciff hannu ta ƙafa,kafin ya kalli wani yace “ko kawo jinin” da sauri ya miƙo wani jini a cikin wata ƴar ƙaramar roba,wandon jikinta suka saka reza suka yayyaga har saida cinyoyinta suka fito,duk inda jikinta ya bai yana a jikin wandon suka bi wajan suka shafa jinin,kafin su ɗauki jinin suka shafa a gefen bakinta zuwa hancinta,suna gamawa wani ya ɗauko cocaine a cikin wata leda ya nufi hancinta,cikin kuka tace “kubarni Please banson, Uncle where are you” dry mutumin yyi yace “kina son zuwa wajan Uncle?” da sauri ta ɗaga masa kai murmushi yyi yace “good gril duk abinda na faɗa maki ki faɗa,kuma ai Uncle ɗinki yace muyi maki hakan” cikin rashin fahimta tace “Uncle bazai ɗaureni ba,ka sakeni ku gyaleni,ohhhh Jesus”dry yyi yace “daman sai dai kice Jesus ɗin,mutumin dake neman taimako ai sunan Allah zai kira bana bawansa ba” yana faɗin hakan ya danna mata gusar cocaine ɗin a cikin hancinta,saurin runtsa idanunta tayi sbd wata azaba da taji a cikin hancinta kafin a hankali idanunta su fara lumshewa cikin ƙasa da murya ta fara faɗin “Uncle.. Uncle ne..!!” dry yayi yace “kice Uncle ya kawo ki nan,kuma kice Uncle ya cire maki kaya,kice Uncle yyi maki Fyaɗe,kice Uncle ya fasa maki baki” cikin maye da gushe war hankali tace “No!! I can’t say it” da ƙarfi yace “say it, I said say it” ya faɗa cikin ɗaga murya,a hankali ta buɗe idanunta wanda yake zubar da hawaye kafin ta ƙara jaa ta rufe tace “i can’t,my uncle my everything” hudar ya ƙara ɗaukowa ya danna mata cikin hancinta har sai da numfashin ta ya kusa ɗauke wa, kafin ya ƙara shafa wani jinin a jikin hancinta ya hargitsa gashin kanta yace “ohyaaa speak” idanunta ta buɗe wanda ya rini ya koma jaaa tace “Uncle ne..!” tafi mutumin yyi cikin sauri Hon Faisal Lawan ya kunna camerar tare saita ta a jikinta,cikin ƙasa da Murya inda Muryar sa ba zata fito ba yace “what he did to you?” numfashi ta yana fizga tace “Uncle ne ya kawoni zaimin magani…,” Shuru tayi kafin ta ɗura da “ya yagamin kaya da reza ya fasa min baki..,” nan ma shuru tayi kafin tace “he raped me” ta ƙare mgnar tana fasa wani gigitaccen kuka “ya waye” idanunta ta buɗe tarrr akan camerar kafin tace “Muhammad Jalal bobo, I hate him I don’t want to see him in my life ever, he betraying me,he lying to me, seriously I hate him”ta faɗa tana saka wani sabon kukan, cutting camerar Hon Faisal Lawan yyi kafin yyi wani murmushi yace “Jalal bobo ka gama yawo”
Lamir dake cikin mota ganin su Hon Faisal Lawan sun fito suna dry ya fito daga cikin motar tare ƙara sawa inda suke yace “komai yayi?” Dry sukai tare faɗin “harma da abinda bamu sata faɗa ba ta faɗa” jinjina kai yyi yace kuje a nemi wata a tura masa,sannan ya haɗasa a media,a nan kuma gidan t.v da redio zasu ɗauka,ni bari naje nasan yadda zan mata” mota suka shiga tare da barin wajen shi kuma ya shige ciki, ƙwance ya taddata tana shasshekar kuka,da sauri ya ƙarasa inda take ƙwance yana zuwa yasa hannun ta ɗauke ya nufi cikin mota da ita,ruwa mai sanyin gaske ya ɗauka ya shafa mata a fuska tare da saka ruwan a cikin bakinta tasha sosai,kujerar motar yaja bata ta ƙwanta kafin yyiwa motar reverse tare da yi mata key a guje yabar wajan.
Sai kusan 3 aka kammala zaɓen inda Jalal yake da rinjayen mutane kashi 15 a kashi 20 kafin ya faɗi sakamakon ya nufi wajan motarsa wasu manyan securities suka rufa masa gefensa kuma Jafar da Aryan ne,yana zuwa motar aka buɗe masa back side ɗin ya shiga kafin aja motar a rufe, Jafar ɗaya motar ya shiga shida wasu ƴan majalissu Aryan kuma ya shiga motarsa, securities ɗinma motarsu suka shiga,kai tsaye cewa yyi suyi gidan sbd gaba ɗaya baijin da daɗin jikinsa,ga wata faɗuwar dake damunsa,a haka suka isa gida gaba ɗaya sukai parking a parking space na gidan,suna parking motar su Mummy na dawowa,motar aka buɗe masa ya fito suma securities ɗin suka ja gefe a cikin gidan kowa hannunsa riƙe da bindiga,cikin nutsuwa yake tafiya a tare suka jera shida Mameey da Mummy sai tsiya Mummy take masa zai tsofa babu aure Mameey kuma na tare masa Shidai kawai jinsu yake dan sam bai gane abinda suke faɗa masa.
A parlour suka tarar da Mama tana bacci gaban cike da tarin ƙashoshowan kazar,zama sukai gabaki ɗayansu,shi kuma Jalal ya nufi part ɗinsa,yana zuwa ya sakarwa kansa shower bayan ya gama ya fito parlour’nsa sanye da wata milk ɗin jallabiya mara nauyi,wajan fridge yaje ya ɗauki bottle water mai sanyi ya ɓalle murfinta ya sanya cikin bakinsa gana gama shanye wa ya ajjiye robar tare miƙewa akan duguwar sofar tare da lumshe idanunsa kamar mai nazarin wani abun.
Suna zaune a main parlour mai aikinsu Laure ta ajjiye masu ruwa da lemo da kuma cake suna shirya sallamar da suka ji anyi yasa suka kalli bakin ƙofar Nihila ce ita da Nusaibat suka shigo,kallonsu Mummy tayi tace “daman ba ƙya gidan” zama tayi kusa da Jafar tace “Mummy kinsan weekend ne,na gaji da zaman gidan shine naje wajan Nusy sai kuma bacci ya ɗauke ni” Mameey tace “ina Jalilerh” parlour’n ta kalla tace “ai a nan parlour’n na barta ita da Mama” Mama da tayi ƙuri jin an tambayar Jalilerh tayi saurin faɗin “Mahammada Rasulullah Ni zakiyiwa sharri da ƙarya,Bihila ki fita ina bacci za kice kin barin da ita,Haram sam ƙarya kike ki tuba kibi Allah da za’a shanshana bakinki tabbas da anjin yana wari” tana faɗin hakan ta miƙe ta nufi part ɗinta tana shiga Abbou ya fito yace “ai Mama tace tana bedroom tana bacci naso leƙa wa amma sai banyi hakan ba” Mummy ce ta miƙe tace “ok bari na duba ta”tana shiga taga babu kowa a cikin bedroom ɗin dubawa parlour bathroom tayi nan ma babu kowa,da sauri ta fito tana daga saman upstairs tace “Abbou Jalal bata nan fa har bathroom na duba” da sauri Aryan ya miƙe yace bari na duba part ɗin Mameey Nihila ma miƙewa tayi tace bari na leƙa ko taje wajan Laure,nan suka fara dubawa amma babu Jalilerh babu labarin ta,a tare suka fito hadda Abbou daya duba gues parlour,kallon juna sukai kowa da alamun tambaya a cikin ransa,kafin Mummy ta juya da sauri ta nufi part ɗin Mama,tana tsaye a cikin parlour sai tafa hannu take tace “Lamiru ni ya haɗawa tuggu,na shiga uku yau ina zankai hakkin marainiya Allah ya sani da niyar taimako na bashi ita,ahhh to data zauna da wannan mugwayen mutanan a jikinta ba gwamma an cire mata su kota ido ne ta huta..,” sauri shuru tayi sbd buɗe ƙofar da taji anyi Mummy tace “dawa kike magana” tace “to uwata matseni na faɗa” Mummy tace “Ina Jalilerh Abbou Jalal yace kice masa tana ɗaki tana bacci kuma an duba ko ina bata gidan,bayan tare kuke da ita a gidan” kuka Mama tasa tace “ashe kallon mayya kuke min sbd ko mayyaceni tayaya zan cuci marainiyar Allah wacce babu ruwan ta,shikenan dan ina cin arziƙi a gidanku zaku yimin sharri” ta ƙare maganar tana face majina,fita Mummy tayi a ɗakin tana fita Mama tasa key ta rufe ɗakin, ganin ta fito da tashin hankali yasa Aryan saurin faɗi “bari na duba ɗakin yaya” yana faɗin hakan ya nufi part ɗin bobo,yana ƙwance idanunsa a rufe ya ɗura hannunsa a saitin ƙirjinsa dake buga masa yaji an turo ƙofar ɗakin da sauri, baiko mutsa saima ƙara rufe idanunsa yayi Aryan ne yace “yaya Jalilerh bata gida fa” da sauri ya buɗe idanunsa tare miƙewa tsaye yace “what!! Kamarya bata gida” yace “an duba ko ina bata nan Jalilerh missed” bai ƙarasa jin komai ba ya saka bedroom silefers ɗinsa ya nufi parlour yana zuwa yaga kowa a tsaye hadda Mama data ta kuɓe gefe sai raba idanu take kallonsu yyi ciki ɗaga murya yace “Wanne irin abune wannan? Tayaya zakubarta ita da wannan rikitacciyar matar” kuka Mama ta saka tace “daman na sani kallon mahaukaciya kukemin,yau ɗin nan zan barmaku gidanku” cikin ɓacin rai yama manta dawa yake magana yace “kin daɗe baki bar gidanma babu da kika iya gashi nan kin salwantar da yarinyar saiki shirya abinda zaki faɗa a court kuma…,” Ba ƙarasa maganar ba yaji an ɗauke sa da mari da sauri yyi ƙasa da kansa, Nihila dake gefensa tana kuka tayi saurin ƙanƙamesa sbd tsoran da taji,cikin ɓacin rai Mummy tace “uwata kake gayawa wannan maganar,uwar data haifan nazo na haife ka zaka maka court Muhammad” kafin wani yyi magana Jafar yace “what!!?” gaba ɗaya suka kallesa lokacin daya sauke waya ya nufi inda remote yake ya kunna t.v kai tsaye b.b.c ya kaita yana kaiwa yaga an rubuta breaking news tashin hankali kenan da sauri Jalal ya ɗaga kansa jin Muryar ta cikin kunansa tana faɗin “Muhammad Jalal bobo he rped me..³⁶,³⁷

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *