WA NAKE SO CHAPTER 15

 WA NAKE SO CHAPTER 15

Www.bankinhausanovels.com.ng 

Zaune take a office din nata tana duba wani littafi dake gaban ta bayan tayi round ta dawo. Wayar tace ta dau kara tana dubawa taga sabuwar number. Dauka tayi tayi sallama. Amsawa akai sannan akace

“Doctor An tashi lafiya ya kike ya aiki?”+

“Alhamdulillah amman ban gane waye ba?”

“Jannah ce!”

“Oh Jannah ya kike ya gida ina Noor?”

“Gata!”

Ta amshi wayar tace

“Ina kwana ya aiki?”

“Alhamdulillah ya gida da Hajiya?”

“Tana lafiya!”

“To agaishe ta!”

“Zata ji.”

“Aha nagode!”

Jannah ta amshi wayar tace

“Doctor ranar friday zan shigo muje radio station tare.”

“To shikenan sai kinzo!”

“Yauwah nagode ki gaida Momy.”

“Zataji sai anjima!”

Ta fada tana kashe wayar. Ido ta lumshe tana murmushi take ta tuna zuwan su gidan. Kenan su Noor yayan wannan mutumin ne Uncle wa ma taji suna cewa? Ohoo ta manta.

4:00pm

Aka shigo office din ta da sallama. Dagowa tayi tana amsa sallamar Aslam ne ya fara shigowa ya kura mata ido,  kai ta dauke tana kallon system din gaban ta.

Dagowa tayi suka kara hada ido. Kai ta dauke ya saki murmushi ya harde hannu yana kallom ta. Aiki ta cigaba dayi bata yadda ta dago ba.

“Assalamu alaikum!”

Jiddah tayi sallama

“Wa’alaikun salam!”

Suka amsa. Jiddah tace

“Ya ka tsaya anan!”

Fateema ya nuna mata yace

“She didn’t welcome me!”

Kallon Fateema tayi. Fateema tayi murnushi tace

“Bismillah!”

Murmushi Jiddah tayi tace

“Thank you!”

Ta kama hannun sa suka karasa ciki. Zama tayi shima ya zauna.

“Ina yini Doctor?”

“Lafiya Alhamdulillah ya gida?”

“Alhamdulillah!”

Ta mika mata files din hannun ta tace

“Na shiga na amso result din ne.”

Amsa Fateema tayi ta zare envelope din sannan ta bude tana karata abinda ke a ciki. Idon ta akan takardar tana dubawa wanda Aslam ya tattara gaba daya hankalin sa ya maida kan fuskar ta yana kallon ta yana sakin murmushi. Itama Jiddah kallon ta take. Can ta dago tana kallon Aslam da ya kurawa Fateema ido. Zungurin sa tayi da hannu ya juyo a hankali ya kalle ta ya dage mata gira alamar

“Ya dai!”

Murmushi tayi tace

“Matar aure ce dai!”

“Waya fada miki?”

Fuska ta bata tace

“What did you mean to?”

Murmushi yayi yace

“Antyn kishi!”

Murmushi tayi tace

“Kar nayi kishin abinda nake so ne?”

“No kiyi!”

Tai murmushi. Fateema ta ajiye na Aslam ta dauki dayan na jiddah ta duba shima sannan ta ajiye tace

“To from dis result it shows that both of you are fine. Zaku iya haihuwa lokaci ne kawai bai zo ba.”

Ajiyar zuciya suka sauke. Fateema tace

“Sai dai kila matsalar wata kila daga baya ne abinda kika yi ne! Kisan planning yana da matsala wani lokacin allura tana sa jinkiri akan daukar samun ciki. Yanzu dai abinda zan ce baki da matsala tinda aladar ki ta saitu to ba matsala domin allura na bada matsala wani ta dauke miki zubar jini wani ta birkita miki wanda kila daga nan a samu matsala dan haka muke cewa aje cibiyar kiwon lafiya dan auna jinin ki aga wane tsari za’a a saka ki. Matsalar kuma ke kinga baki shiga dakin ki ba ace baki tabbatar ma kiina haihuwar ba amman kinje kin fara planning dan haka yana dakya ana wayar da kai akan wannan matsalar in har planning kake so kaje cibiyoyin kiwon lafiya dan a gane wanne ya dace. Yanzu ba abinda zance sai dai nace Allah ya kawo zuri’a mai albarka ya kawo haihuwa nan kusa Amin. Fatan alheri gareku!”

STORY CONTINUES BELOW

“Nagode Doctor kuma na dauki shawarar ki da izinin Allah za a kiyaye kuma nima zan na fadakar wa masu hali irin nawa Allah yasa su kiyaye kuma su gane nagode doctor allah ya baki kema zuri’a masu albarka Allah biya miki bukatun ki.”

“Amin Amin amman da an samu juna biyu nan zaki zo ina miki awo ko?”

“Insha Allahu doctor gunki zanzo har haihuwa ta.”

“To Allah kawo masu albarka.”

“Amin.”

“Mungode Doctor Allah saka.”

Aslam ya fada. Bata kalle shi ba tace

“Amin nagode ai ba komai.”

“Muje ko?”

Jiddah ta fada tana tabo Aslam dake kallon Fateema.

“Ok!”

Ya fada ya kasa tashi. Ita kuwa har ta mike ta kalli Fateema tace

“ko zaki ban number ki?”

“Ba matsala!”

Ta nika mata waya ta saka number ta Amsa tayi tace

“Sunan fa?”

“Fateema!”

“Ok Dr Fateema kenan!

Murnushi Fateema tayi. Jiddah ta kalli Aslam dake zaune tace

” muje ko?”

Tayi gaba. Wayar ta ce ta dau kara tana dubawa taga Khady ce dan haka ta fita da sauri dan ta dauki wayar. Mikewa Aslam yayi yace

“Doctor wa ya sani ko ta gun ji zamu fara samun ya’yan?”

“Kamar yaya?”

“In kin zama matata!”

“What?”

“Yea Doctor ban taba jin abinda nake ji akan ki ba doctor ki taimaka ki agaji rayuwa ta na fada miki am in pain of your love please ki bani maganin ciwo ba.”

“But na fada maka kaje ka nemi wasu likitocin su baka shawara dan abinda ka saka a zuciyar ka yana da illah gwara kaje ka nemi shawara yadda zaka fitar da abin kasa dangana.”

Ta fada tana dannan system din ta.

*

**

***

****

*****

******

*******

Sunfi awa nawa a dakin amman basu fito ba. Su Yaa Abubakar kuwa banda addu’a ba abinda suke dan sun leka sun gane meke faruwa dan haka jikin su yai matukar sanyi.

Mama ce ta shigo ta shimfidda sallaya ta hau ta fara sallah kara’a biyu tayi amman sai da ta dauki awa daya akai dan addu’a kawai take Allah ya tashi kafadun Aliyu. Allah maji rokan bayin sa bayan sun dauki wajen awa biyu akan sa ba alamun numfashi ko wani alamu na yana da rai sai kawai ji sukai ya sauke wata ajiyar zuciya take kuma ya fara tari wanda nan jini ya dinga fitowa daga bakin sa.

Cikin azama sukai kansa suka hau bashi taimakon gaggawa dan oxygen ma suka saka masa saboda yadda numfashin sa ke son daukewa. Yaa Abubakar duk abunda ake akan idon sa.

“Allahu Akbar! Alhamdulillah!”

Ya fadi yana rufe fuskar sa da hannun sa. Da sauri su Yaya Usman sukayo wajen suna leken dakin. Computer dake gefen gadon suka kalla sukaga yadda numfashin sa ke harbawa duk da ba sosai yake fita ba sai yayi layi sai kuma ya nuna alamar mutumin yana da rai. Sai da suka dauki wajen awa biyar akan Aliyu kan suyi masa allurar bacci sannan suka kara saka masa ruwa suka fito aka bar wasu biyu a dakin.

Yaa Abubakar da Usman ne suka bi bayan su. Office suka shiga suka zauna. Sannan Dr ya zauna ya dauko folder Aliyu wacce take da uban takardu a ciki. Budewa yayi yana nazartar ta sannan ya dago yace

“Jikin sa da sauki Alhamdulillah. Dazu numfashin sa ne ya dauke gaba daya to cikin ikon Allah dai yanzu ya dawo har ya dai dai ta da taimakon oxygen.

A binciken da mukayi jiya da muka saka shi a computer mun gane yana fama da matsalar ta damuwa. Wanda ya haifar masa da ciwon zuciya.

Sakamakon wani karamin bincike da muka gabatar na kungiyar masana ciwace-ciwacen zuciya na Tarayyar Turai ya nuna cewa masu fama da wani bacin rai suna iya mutuwa a cikin shekara guda.

Koda yake dalilai da dama suna iya haddasa ciwon tare da kara zafafa shi, masu binciken sun ce yana da muhimmanci a yi kokarin yaye ma majiyyata ciwon bakin ciken dake damun su. Ba zan ce ga abinda yake damun sa ba amman a gaskiya ya saka wani abu a ransa ne wanda ya haifar masa da ciwon zuciya. The worse part of it ma kaga ya fara aman jini ba anan abun yake ba ina tsoro kar ya kai stage din da zuciyar tasa zatai rauni ko jijiyoyin zuciya suka yi rauni ko kuma suka yi tsauri, abinda zai hana su harba jini ga sauran sassan jiki. Shi zai iya haifar masa da bugawar zuciyar tasa gaba daya.

A yayinda haka ta kasance, masu fama da ciwon kan yi laushi, wannan kuma zai iya kai su ga mutuwa.”

STORY CONTINUES BELOW

Ya dafe kai yace

“Yanzu dai ina son na gano menene asalin ya haifar masa da ciwon ta nanne zan gane akan treatment din zan daura shi.”

Kallon Juna sukai sannan Yaa Abubakar yace

“Zamuyi iya yin mu, mu gano hakan insha Allahu. Sai dai Aliyu zurfin ciki ne dashi sam ba a gane meke damun sa.”

Kai Dr ya jinjina sannan yace

“Sam baya son cin abinci dan haka ulcer ta shige shi dole yanzu ana samar masa wani abu da zai na ci. Ciwon ulcer babban ciwo ne wanda zai haifar masa da ciwon kai har da zazzabi da ciwon baya kunga matsalar zata hade masa biyu matsalar zuciya ga wannan kuma.”

“Insha Allahu Doctor za a kiyaye!”

“Muma zamu iya bakin kokarin mu wajen ganin komai ya dai daita. Insha Allahu.”

Mikewa sukai suka bashi hannu sannan suka fita. Suna shiga suka tadda kowa na cikin dakin da Aliyu yake.

Zama sukai a falon dakin Yaa Abubakar ya Kalli Yaa Usman ya ja nunfashi yace

“Yanzu ya zamuyi?”

“Kada mu fadawa Abbah da Mamah!”

“Menene ba za a fada mana ba Abubakar?”

Abbah ya fada yana fitowa daga dakin. Shigowa dakin yayi ya zauna ya kalli Abubakar yace

“Me yake damun dan uwan naku?”

“Abbah Ulcer ce daman sai….”

“Sai ciwon zuciya ko?”

Dagowa sukai suka kalli abbah. Abubakar yai kasa da kai. Usman yace

“A ina ka sani Abbah?”

Murmushi Abbah yayi yace

“Acan sun fadamin shiyasa na ce mu fito dashi waje. Dazu Mamahn ku tace daga tari sai jini fa.”

Kai suka gyada suka ce

“Eh Abbah haka ne.”

Shiru Abbah yayi yace

“Me suka ce?”

Nan Yaa Abubakar yai masa bayanin komai. Kai ya gyada yace

“To Allah yasa kaffara!”

“Amin Abbah!”

Mikewa sukai suka shiga dakin Mamah suka gani gaban gadon tana ta tofa masa addu’a idon ta jajir. Dafata Abubakar yayi yace

“Mamah kiyi hakuri zai ji sauki da yaddar Allahu!”

“Allah ya yadda!”

“Amin!”

Ya fada yana kamata ya zaunar yace

“Kina rage damuwar nan Mamah!”

Kai kawai ta gyada. Wayar Aliyu ce tayi kara dake hannun Maryama wannan yasa ta mike ta fita dan dauka. Faisal ne ta dauka tace

“Hello!”

“Maryama kuna wane asibiti ne ki turon address din na sauka.”

“Alright!”

Ta fada ta kashe wayar ta tura masa sannan ta koma daki ta kalli Abbah tace

“Abokin Yaa Aliyu ne Faisal zai zo!”

“Ok Allah kawo shi.”

Wayar hannun Maryama ce ta kara daukar kara ta duba taga an saka Pres Ahmad. Mikawa Abbah tayo tace

“Abbah kamar President ke kira.”

Amsa yayi yai sallama. Shugaban kasa ya amsa yana fadin

“Aliyu kwana biyu najika shiru Allah yasa lafiya.”

“Ba shi bane Alhaji Kabir ne!”

“Ah ranka ya dade ashe kai ne ya kake ya gidan?”

“Alhamduliah ya jama’a ya iyalai!”

“Alhamdulillah!”

“Madallah!”

“Ina Aliyun ne kwana biyu ba muyi waya ba ko na kira a kashe fa.”

“Ikon Allah ai ka ganmu nan bama kasar ma Aliyu ba lafiya shekaran jiya muka bar kasar.”

“Subhnallah amman ba labari meyasa bai fada min ba.”

“Abin ne yazo a korarren lokaci kuma duk ba nutsuwa.”

“Ya jikin nasa?”

“Alhamduillah!”

“Kuna wacce kasar?”

“Egypt!”

“To insha Allahu ina hanya ai Aliyu danane Allah yabashi lafiya zan turo da kudin kula dashi.”

“Haba Alhaji Ahmad ka barshi!”

“Nima fa ‘da nane!”

“To shikenan godiya muke!”

Ya kashe wayar. Maryama Abbah ya kira yace

“Ina Faisal yace yana ina?”

“Nima ban sani ba.”

Umar Abbah ya mikawa wayar yace

“Kaje ka dauko sa ka kai shi gida ya huta yaci abinci sai ku taho.”

Amsar wayar yayi ya fara kiran sa yace gashi nan sannan ya fita.

*

*

*

Aisha na exam hall suna final papper amman duk hankalin baya jikin ta yana can ga Aliyu. Ji tayi wani tari ya zo mata nan ta dingayi tana rike da zuciyar ya. Ta jima tana tarin sannan ya tsagaita. Karasawa tayi ta fito daga exam hall sai dai tana fitowa taji jikin ta na rawa kafafun ta suka kasa daukar ta durkushewa tayi a nan ta fashe da kuka.

Da sauri kawayen ta suka karaso suna fadin

“Lafiya Aisha?”

Kai ta hau girgiza musu tana fadin

“Na kasa tashi jikina duk rawa yake.”

Ai kuwa jikin ta rawa yake kar kar kamar me zazzabi. Daya a ciki tace

“To bari mu samo napep!”

Sa sauri ta fita ta samo suka dagata suka fita suka saka ta a napep din.

A kofar gida suka tadda Yaa Muhammad ya fito da katuwar leda zai fita yana ganin su ya karaso yana fadin

“Lafoya?”

Kuka Aisha ta saki ya karasa ya dauke ta sukai cikin gida. Bayan sa suka bi da jakar ta suka dauki ledar da ya jefar.

A tsakar gida ya ajiye ta ta dunkule waje daya jikin ta na ta karkarwa tana kuka. Umma ce ta fito tace

” lafiya?”

“Yanzu zan fita na ganta an dawo da ita daga makaranta.”

“To ikon Allah”

Kawayen ta ne suka shigo Umma tace

“Me ya same ta?”

“Tana fitowa daga exam hall ta zibe wai ta kasa tafiya jikin ta kuma sai rawa yake.”

“Inna lillahi wainna illahir rajiun”

Ta durkusa tace

“Aisha!”

Dagowa Taui ta fada jikin Ummah tana fadin

“Ummah tsoro nake ji zuciya ta sai bugawa take Ummahh!”

Sai ta fashe da kuka. Dagota Umma tayi tana fadin

“Kina addu’a Aisha. Muhammad ka kira Baban ku yazo kaji.”

Fita yayi suma sukai musu sallama suka tafi. Daki ta kamata ta shiga da ita zata fito ta rike mata hannu tace

“Ummah kada ki fita ki barni.”

“Ruwa zan debo nai miki tofi Aisha.”

Sakin ta tayi. Ta hade kai da gwiwa tana kuka hadi da dafe zuciyar ta dake buga mata da karfi.

“What is happening to me? Ko dai Yaa AK ne?”

Tana fadar haka ta kuma fashewa da kuka.

“Yaa Allah protect Yaa AK Get well soon Yaa AK Allah ka bashi lafiya.”

Ta fada tana dafe kirjin ta dan ji take kamar zuciyar ta zata fito. Ido ta runtse Umma ta dawo tai tofi ta bata ta sha sannan ta koma ta kwanta. Adsd’a ta dinga mata tana tofa mata.

Baba da Yaa Muhammad ne suka shigo Baba ya tsaya kanta yace

“Ya kike ji uwa ta?”

“Ni kawai zuciya ta ke bugawa dazu ne na kasa tafiya jikina yana ta rawa.”

“Ko asibiti zamuje?”

“A’ah Baba ya daina yanzu kawai zuciya ta ke bugawa.”

“To sannu Uwa ta.”

Ya kalli Muhammad yace

“Debon ruwa a kofi.”

Ya fita ya kawo masa. Amsa yayi yai tofi ya bata ta amsa ta sha yace ta shafa a jikin ta. Shafawa tayi sannan ya juya ya fita.

Ummah ma fita tayi Yaa Muhammad ya zauna a gefen katifar ta yace

“Sannu Aisha!”

Kai ta gyada ta lumshe ido kawai.

Mikewa yayi ya fita ta bude ido ta bishi da kallo hawaye ne ya zubo mata ta girgiza kai ta lumshe idon ta.

Sai yamma suka shiga asibitin Umar da Faisal da Farouk dakin da aka kwantar da Aliyu suka shiga yana ta bacci tin da sukai masa allura bai farka ba su Abbah Faisal ya gaisar yai musu ya mai jiki sannan ya karasa yana kallon abokin nasa. Haka suka zauna har dare sannan suka tafi suka barshi da kyar Mamah ta tafi sai da mai martaba ya lallabata suka bar kuma Yaa Abubakar a wajen sa.
Suna fita Faisal yace zai wuce hotel din da ya sauka Abbah yace a’ah ai akwai wajen kwanan sa dole ya hakura suka tafi gidan.
*
10:00am
Lokacin suka shirya suka tafi asibitin. Faisal yace zai biya wani waje zai karaso. Suna shiga suka tadda Aliyu zaune Yaa Abubakar na bashi abu a cup. Da sauri Mamah ta karasa tana murmushi tace
“Ka tashi Baba na?”
Murnushi ya sakar mata ya gyada mata kai. Tace
“Sannu Baba na!”
Hannu ya daga ta karaso ta kama hannun nasa tana fadin
“Sannu Babana Allah kara sauki.”
Abbah ya karaso yace
“Sannu Aliyu ya jikin?”
A hankali kamar mai counting worda yace
“Da sauki!”
“Allah kara sauki!”
Ya gyada masa kai. Maryama ta karaso ta kama hannun sa tace
“Sannu Yaya Allah baka lafiya.”
Murmushi yai mata kawai. Hajara dake can baya ya hango ya kalle ta ya mika mata hannu a hankali ta karaso ya kama hannun ta kan ta a kasa tace
“Sannu ya jikin?”
“Da sauki!”
Ya fada yana dafe kirjin sa.
“Kirjin ne?”
Yaa Abubakar ya fada. Kai ya girgiza kawai. Yaa Usman ne ya shigo shi da Umar da Farouk suna ganin sa a zaune suka saki murmushi. Gunsa sukayo kowa ya rumgume shi yana masa sannu. Kai kawai yake gyada musu.
Cikin kwana biyu da zuwan sa ya rame har yafi  da yana goda nigeria. Kowa yana zauna ana dan taba hira Aliyu ya kalli N
Maryama dake zaune a can gefe tai shiru hannu yasa ya yafito ta. Mikewa tayi ta karaso ta zauna a gefen gadon
“Ina Aysher?”
Murmushi ta saki ta kama hannun sa tace
“Yaya tana nan zuwa ai na fada maka!”
“Da gaske?”
Kai ta gyada ya rike hannun ta ya jinginar da kan sa yana murmushi.
1:00pm su Mamah suna falo suna sallah Maryama ce kadai zaune a dakin bayan ta idar da sallah ta dawo ta zauna a gefen sa. Su Abbah duk suna masallaci. Faisal ne ya shigo Ya durkusa ya gaida Mamah ta amsa tace
“Ka shiga yana ciki!”
Mikewa yayi ya shiga. Yana bude kofar suka dago suna kallon sa. Mamaki sosai kwance a fuskar Aliyu. Shiga yayi yace
“Abokina kana mamaki ne to tin jiya nake garin nan da nazo kana ta bacci!”
Maryama,  Aliyu ya kalla ta gyada masa kai. Murmushi ya saki ya mika masa hannu karasowa yayi ya kama hannun ya zauna akan kujerar gaban gadon yace
“Ashe baka da lafiya Aliyu amman shine baka fada min ba.”
Murmushi kawai Aliyu yayi. Mikewa Maryama tayi ta fita. Faisal yace
“Ya jikin to?”
Ido ya lumshe sannan ya bude a hankali yace
“Da sauki!”
“Sannu friend since when wai?”
STORY CONTINUES BELOW
“Tin ranar da mukai last magana.”
“Me yake damun ka ne?”
Kafada ya daga ya lumshe ido. Faisal ya dafa Aliyu yace
“Aliyu ya batun Aisha?”
Da sauri ya bude idon sa take kwalla ta taru a idon yace
“Faisal ina son Aysher amman nasan ba zan samu Aysher ba na hakura da Aysher amman nasan son Aysher shine ajali na.”
Ya dafe zuciyar sa yace
“Ina son Aysher Faisal please amson wayata wajen Maryama ka kira min ita. Maryama tace zata zo amman yau kwanan mu uku bata zo ba naso jiya na kira ta na mata murna gama jarabawar ta amso min please.”
Mikewa Faisal yayi ya fita. Maryama ya kalla yace
“Ina wayar Aliyu!”
Jaka ta bude ta dauko ta bashi. Amsa yayi ya juya ya koma.
Wayar ya amsa ya fara dailing number ta.
*
*
*
Tin daga ranar da suka gama jarabawa abun nan ya faru sai kuma ciwon kai da zazzabi da kakalleta zaka san tana da damuwa dan cikin kwana daya tayi wata irin rama kamar wacce tai wata tana jinya.
Kwance take cikin bargo ta saka suratul bakara tana bin karatun ji tayi karatun ya tsaya wayar ta fara vibration da ba zata duba ba sai kuma ta janyo wayar a zabure ta mike zaune ganin sunan Yaa AK akan screem din wayar. da sauri ta dannan receive ta kai kunnen ta.
“Assalamu Alaikum Yaa AK kai ne? Yaa AK ya jikin kaji sauki ya kake ji yanzu?”
Yadda yaji muryar ta sai da ya lumshe ido hadi da sakin wani murmusni. Muryar ta ce ta cigaba da ratsa dukkan wata gaba ta jikin sa.
“Wa’alaikum salam Aysher cool down!
Ya fada a hankali. Murnar ta ce ta koma ciki ta fashe da kuka tace
“Yaa AK jikin ne?”
“No Aysher naji sauki!”
“Baka ji sauki ba Yaa AK kaji muryar ka kuwa na shiga uku Yaa AK ka fada min ya jikin?”
Ta fada tana sakin kuka.
“Ya salam Aysher please ki kwantar da hankalin kk…”
“Uhmm ba zan iyaba tinda ka tafi na kasa kwantar da hankali na na kasa samun nutsuwa Yaa AK ka fada min ya kake ji ya jikin naka dan Allah!”
Zai magana tari ya tayar masa wayar ya dauke yai tarin sannan ya maida wayar yace
“Hello kina jina?”
“Ina ji Yaa AK tell me how did you feel!”
“Alhamdulillah!”
Hawaye ne suka zubo mata tace
“Yaa AK ina son na ganka ina son naga ya jikin ka yake ina ji a jikina kana kwance sosai Yaa AK dan Allah ka fada min zuciya ta ta samu sauki Wallahi na kasa samun nustuwa tin tafiyar ka kowanne motsi na tunanin ka nake yaya kake Yaa AK ya kake ya jikin kana zazzabin ka daina tarin da jini jikin ka ya daina jin zafi a zuciyar ka?”
Ta fada tana fashewa da kuka.
“Aysher!”
Ya kira sunan ta wanda yasa ta dago da sauri dan har cikin zuciyar ta taji sunan.
“Aysher i love u,  ina sonki da kaunar ki!”
Ido ta runtse da karfi.
“Aysher son ki ya min illah wanda rashin ki zai yi sanadiyar rasa rayuwata. Na fada zan kuma fada ba zan miki dole ki soni ko ki amshi ni ki aura ba amman ki sani ni na yadda in mutu ke ki rayu in har zaki samu farin ciki a rayuwar ki.
Hakika kin canjan rayuwa ta Aysher wanda in har zan bada labarin rayuwata dole ki shiga ciki a san dake domin a rayuwa ta kin ban farin ciki kin sauyan rayuwa ke ce kadai macen da ta sauyan tunani dan haka dole sunan ki zan kira fari domin kina da alheri,  kyawun halin kine jari ga nutsuwa dakyan tsari auren ki shi nayi buri wanda nake ganin ba zan samu ba.
Ban taba kallon mace sau biyu ba Aysher sai akan ki ko matata sai da a aure ta da dadewa na ke kallon ta. Ban taba sunkuyar da kai na ga wata mace ba amman na sunkuyar akan ki Aysher,  hankali na bai taba tafiya gun wata mace ba sai ke. Ke kika ja hankali na har na baki zuciya ta gaba daya.”
Zuciya ya dafe yace
“Ke kyakyawa ce wacce a guna kin wuce min kowa domin in har dake a waje ko na same ki ba wanda zan so ko da na mutu da son ki zan mutu a cikin zuciya ta. So da kaunar ki sun shiga zuciya ta kin mallaken komai domin zuciya ta taki ce gaba daya.”
STORY CONTINUES BELOW
Murmushi ya saki mai ciwo ya gyara zaman sa yana cije bakin sa dan yadda yake jin radadi a zuciyar sa sannan ya kara sakin wani murmushin yace
“A lokata da dama kin ban farin ciki ko ina bakin ciki kina sani in dara. Kin ban farin ciki wanda yake kawar min da damuwa ta ko ina da bacin rai nazo wajen ki zan samu nutsuwa da farin ciki dan haka bazan taba mantawa ba dole Aysher naso farin cikin ki dole na fifita farin ciki ki akan nawa koda zan sadaukar da farin cikina. Aysher abu daya zan roka a wajen ki.”
Yai shiru yana son yaji respond din ta sai yaji tayi shiru yace
“Aysher!”
Sheshekar kukan ta yaji yace
“Dan Allah kibar kukan nan ban kira dan na saka ki kuka ba Aysher na kira ne dan nai miki bankwana dan haka ki tsaya kiji abinda zan roka a gun ki.”
Yana fadar haka komai ya tsaya mata har kukan da take tai shiru. Can kuma Tace
“Wane irin bankwana Yaa AK ina zaka tafi ka barni?”
Murmushi yayi yace
“Mutuwa zanyi Aysher!”
Bakin ta ta danne dan kuka ne ya taho mata. Yace
“Aysher ko na mutu kada ki manta dani kina sani a addu’a ban haifa ba kinga ki daure ki rike wannan kina sani addu’a da ya’yan da zaki haifa suma suna min addu’a dan Allah. Batun karatun ki zanyi magana dasu Yaa Abubakar insha Alahu sai kince kin gaji da karatu sannan zasu barki nagode da bani farin cikin da kikai. Nagode da bani shawarwarin da kikai nagode da komai da kikai min Aysher ba zan taba daina son ki ba.”
“Yaa AK ka daina fadar haka bazaka mutu ba baza ka mutu ba,  ba yanzu zaka mutu ba. Baza ka mutu ka barni ba.”
“Uhmm Aysher kenan ai mutuwa bata sanar da lokacin ta amman ni a jiki na ina jin na kusan tafiya na barki ki yafen in nai miki wani abu!”
“Ba kai min komai ba Yaa AK kuma ba zaka mutu ba ba yanzu zaka mutu ba sai kaga ya’yan ka har da jikoki kai harma da tattaba kunne!”
Murmushi ya saki yace
“Ko?”
“Insha Allahu!”
Yai shiru tace
“Yaa AK!”
“Na’am Aysher!”
Shiru tayi kuma yace
“In kara neman wata alfarma a gunki?”
“Uhm!”
“Aysher dan Allah kice kina sona!”
“Yaa AK ina sonka ba rashin son kane yasa naki amsar auren ka ba sai ba zan iya cewa ba zan auri Yaa Muhammad ba amman ina son ka Yaa AK ka daina zaton bana son ka ina son ka.”
Murmushi yayi yace
“Nagode Aysher!”
Sai kuma ya fara tari da karfi da sauri Faisal ya amshi wayar hannun sa jini ne ya fara fita ta bakin sa ya goge masa yace
“Sannu Aliyu har da jini wai me yake damun ka ne wannan sign ne na ciwon zuciya fa.”
Murmushi Aliyu yayi yace
“To dan na kamu da ciwon zuciya shine me Faisal kada ka manta fa soyayya ke wahalar dani. Ada bansan menene so ba ban yadda da shi ba amman daga haduwa ta da ita so yai min mugun kamu.
Faisal Zuciya sirrin mai shi take koka kasa kunnuwa ba zakaji komai ba. Ni kadai nasan me nake ji a cikin ta.
Shi kuma so tamkar iska yake ko ka tara hannu bazaka tabo komai ba.
Ni da Aysher hadin Allah ne kuma soyayyar mu zata kafa tarihi domin zan sadaukar da rai na da farin ciki na domin samuwar nata.
Faisal ban taba jin haushin Aysher ba domin Aysher ta nuna min tana da amana wanda kowa zai fatan samun mace kamar ta. Inama ace nine wannan Yaa Muhammad din. A gaskiya yayi dacen kanwa yayi dacen mai son sa.
Aysher tamkar raina ce in har na rasa ta to tabbas mutuwa zanyi in kaga na rayu to ka sani Aysher ce ta zama tawa. In har ba Aysher to ba zan numfashi ba.
Yanzu nasan menene so. Na yadda da aka ce ruwan zuma soyayya kasha ka bai masoyin ka. Aysher ta sha ta ban ragowar wanda Yayan ta ya bata wanda nasha naji dadin sa kuma bani jin kishirwa akan son ta. Ni da Aysher hadin Allah ne jini mune kawai ya hadu wanda Alah shi ya hada mu.
Hakika nasan akwai shakuwa mai karfi tsakani na da Aysher wanda ko bayan raina ita kan ta zatai rashina kuma wannan zai saka tana min addu’a.
Na bawa Aysher komai nawa zuciya ta jiki na da ruhi na ni kaina dukka nata ne. Wannan abun da na fada daga zuciya ta yake faisal ka kalli ido na ka tabbar da abinda nake fada maka. Jinin jiki na da jijiya sonta shike dawai niyya dasu. Shiyasa na fada maka in babu ita mutuwa zanyi Faisal.”
Ido ya lumshe yace
“Aysher kyakyawa ce ban taba ganin me kyan ta a duniya ba,  kamshin ta daban ne kullum matsayin ta dada girma yake a zuciya ta”
Murmushi ya saki yace
“Bata wannan kwalliyar ta hauka amman kyan ta mai daukar hankali ne idanun ta masu kyau da sani nutsuwa. Faisal son Aysher zautar dani zai in dai ban mutu ba Faisal ina son Aysher ya zanyi? na rasa Aysher.”
Abbah dake bakin kofa tin lokacin da Aliyu ya fara waya da Aysher yake wajen ya juya a hankali ya fita daga dakin. Faisal ganin Aliyu na neman fita a haiyacin sa yace
“Cool down Aliyu zaka samu Aysher!”
Kai ya hau girgizawa yana fadin
“Tayaya Faisal tayaya zan samu Aysher?”
Yaa Abubakar ne ya shigo ganin Abbah ya fita cikin damuwa. Aliyu na ganin sa ya fara kokarin tashi yana fadin
“Yauwah Yaya zo na sauke wani nauyi akai na Yaya wasiyya zan baka!”
“Wasiyya kuma Aliyu?”
Kai ya gyada ya kama hannun sa ya rumgume a kirji yace
“Yaya mutuwa zanyi akwai wani abu da na farashi nake so ka karasa min shi Yaya. Da farko Yaya in na mutu dukiya ta a raba gida hudu a bawa Aysher daya, daya a bawa gidan marayu daya a bawa Abbah da Mamah daya kuma a bawa magada na. Sai abu na biyu dan Allah yaya ka tsayawa Aysher a harkar karatun ta har sai tace ta gaji dan Allah Yaya ka daukar min wannan alkawarin!”
“Aliyu ba zaka mutu ba ka daina fadar haka!”
Kai ya girgiza yace
“Kace ka dauki alkawari Yaya!”
“Na dauka Aliyu amman wacece Aysher?”
Kai ya hau girgiza yana rike da zuciyar sa yana girgiza kai numfashin sa ne ya hau yankewa sai kuma tari take kuma ya fara aman jini nan Yaa Abubakar ya fita ya kira likitoci. Da sauri suka yo kan sa Mamah ta shigo tana ganin halin da yake ciki ta yanke jiki ta fadi. Nan aka fita da ita aka kai wani dakin.
*
*
*
Wayar na katsewa Aisha ta fada kan katifar ta tana sakin wani kuka mai taba zuciya kuka take iya karfin ta sosai. Kuka take tana juyi hadi da addu’a Allah ya tashi kafadun Yaa AK hakika ya sanyayar mata da jikin ta. Kuka take sosai ta rasa yadda zatayi. Tin tana kukan har ta kasa yi sai hawaye dake zuba a idon ta take kuma jikin ta ya rikice da zazzabi kan ta ya dau zafi ya farai mata ciwo kamar zai fadi.
*
Yaa Muhammad ne ya shigo gidan ya nufi dakin ta sallama yayi amman shiru wannan yasa ya bude labule ya shiga. Kwance ya ganta cikin bargo a hankali ya shiga ya yaye mata bargon dagota yayi yaji jikin ta zafi zau. Da sauri ya juyo da ita yana fadin
“Subhanallah!”
Yadda fuskar ta ta kumbura dan kuka ga zazzabin da ya rufe ta dan har rawa jikin ta yake yi. Daga ta yayi yace
“Aisha jikin ne?”
Ya ajiye ta ya fita yana kwadawa Ummah kira ta fito da sauri daga daki
“Ummah Aisha ne jikin ta zafi bari na samo napep!”
Ya fada ya fice daga gidan. Da sauri ta shiga dakin da Aisha take kwance nan ta taddata ko motsi bata iyawa hijab ta dauko ta saka mata sannan ta saka mata hijab Yaa Muhammad ne ya dawo ya dauke ta Ummah ta bi bayan su sai asibiti.Suna zuwa asibiti aka amshi Aisha aka shiga emergency da ita. Zaman jira sukai Yaa Muhammad kuwa ya kasa zama daga can sai yayi can. Basuyi awa daya ba suka saka mata ruwa sannan sukai mata allurai. Sannan aka basu gado. Wajen likita suka shiga nan yace
“Jinin ta ne ya hau shi ya haifar mata da ciwon kan. sai zazzabin na saka mata ruwa ga magungunan da za a siya zamu gani zuwa anjima yanayin jikin nata.”+
Jiki a sabule Muhammad ya fito daga office din magunguna yaje ya siyo sannan ya koma dakin da su Ummah suke. Maganin ya bawa Ummah yace
“Umma zanje na fadawa Baba duk abunda ke faruwa.”
“To shikenan!”
Daga nan ya fita kan sa a daure yake me yake damun Aisha da har zai haifar mata da hawan jini tabbas Aisha ta canja dan haka zai bincika ya gano.
Kasuwa ya isa ya sanar da Baba take Baba ya bar jira suka taho asibitin har lokacin Aisha bacci take yi. Zama sukai suna jimami Baba yace
“Me aka ce yana damun ta.”
Shiru Muhammad yayi da kamar ba zai magana ba sai kuma ya fasa yace
“Baba wai jinin ta ne ya hau shi ya sa take fama da ciwon kai sai zazzabin dake damun ta.”
“Hawan jini kuma Muhammad. Aishan nawa take?”
“Nima abin da ke damuna kenan!”
*
Sai yamma ta farka lokacin zazzabin ya sauka sai ciwon kai dake damun ta. Dan jiri take ji sosai sai Umma ce ta taimaka ta rakata bandaki tayo alwala tai sallah a zaune. Bayan ta idar ta koma ta kwanta lokacin su Yaa Muhammad da Yaa  suka shigo hannun su rike da leda sun kawo abinci.
Ya mai jiki sukai wa Ummah sannan Yaya yai mata ya jiki. Gefen Gadon Muhammad ya matsa ya zauna yace
“Ya jikin?”
Ido ta dan bude tace
“Da sauki!”
“Allah kara suaki.”
“Amin!”
Ta fada. Abinci Ummah ta zuba mata zata bata Yaa Muhammad ya amsa ya fara bata tana masa shagwaba da kuka haka ta gama aka bata magani tasha ta koma ta kwanta bacci ya kuma dauke ta.
Kwanan ta daya aka sallamo su, suka koma gida taci gaba da amsar maganin ta.
*
Kwance take ta rufa da hijab din ta ba bacci take ba idon ta kawai ta rufe. Dakin ya shigo da sallama ya tsaya kallon ta sam bata san ma yanayi ba. Zama yayi ya dan tabata da sauri ta bude ido kokarin mikewa zaune take yace
“Yi zaman ki Aisha!”
Mikewa zaune tayi tace
“Yaya bakina ba dadi!”
“Sannu me zan siyo miki ko Umma tai miki pepper soup ne?”
Kai ta gyada yace
“Fruit din sun kare ne?”
Kai ta girgiza.
Shiru sukai can yace
“Aisha dan Allah ki fadan gaskiya!”
“Gaskiyar me”
“Me yake damun ki?”
“Ni ba komai”
Murmushi yayi yace
“Meyasa kike boyen abu Aisha?”
“Nifa ba komai!”
“Da komai Aisha na dade da gane hakan na jima kuma da gane kina da damuwa wanda yanzu na kara tabbatar wa to dan me zaki na boye min?”
“Yaya wani boye abun yafi akan a fito a fade shi.”
“Ba gani ba Aisha damuwar ki tawa ce rashin damuwar ki shi zai hanani kwanciyar hankali ki sani na fison farin cikin ki akan nawa dan haka ki fadan me yake damun ki.”
Zamewa tayi ta kwanta kawai. Kallo ya bita dashi yace
“Ki fadamin Aisha ko da zai zama silar bacin rai na.”
STORY CONTINUES BELOW
Kai ta girgiza tace
“Ba zan iya ba Yaya kayi hakuri!”
Ta lumshe ido tana daura hannu a kan ta.
“Sannu kan ne?”
Kai kawai ta gyada masa yace
“Kinsha magani?”
Kai ta gyada masa. Yace
“Sannu bari naje nayiwa Umma maganar”
Ya mike ya fita. A tsakar gida ya samu Umma tana gyara zogale zama yayi yace
“Yau kuma zogale zaki ci Umma?”
“Kanwar ka zan kwadantqwa ko taji dadin bakin ta.”
“Kin kyauta peppersoup nake so ai mata bari yanzu zan siyo kajin.”
“Aisha yar gatan kowa!”
Yai murmushi ya fita bai jima ba ya dawo da kaji da kayan miya. Nan ya zauna suka gyara da Ummah sannan suka daura.
Suna zaune a tsakar gida Yaa Muhammad yace
“Umma wai me yake damun Aisha ne?”
“Bangane ba?”
“Damuwar ta Ummah nasan ke ba zaki kasa ganewa ba.”
Murmushi irin na manya tayi tace
“Kai sai yanzu kasan tana da Damuwa Muhammad?”
Shiru yayi can yace
“A’ah Ummah gaskiya anyi shekara da canjawar Aisha amman na kwanan nan yayi worse Ummah. Kuma kwanaki da na tambaye ta sai ta nuna auren mu take so shine dalilin da yasa na tada maganar auren mu duk da haka na gane tana da damuwa amman sai tace min wai ba komai. Umma ina tsoro wani abu ya samu aisha tinda gashi an fara jinin ta ya fara hawa saboda damuwa!”
“Haka ne Muhammad nima bata fito ta fadan damuwar ta ba dan in nai mata magana sai tace ba komai da na matsa matane tai min bayani a bayanan nata ne na gane inda ta dosa!”
Tagumi yayi yace
“To fa! Me yake faruwa?”
“Da farko zan baka shawara domin kuwa ina son ka janye maganar auren ka da Aisha ka bata dama ta fito da wanda take so!”
A zabure ya kalli Umma yace
“Bangane ba?”
“Eh shawara na baka amman in kaga zaka dauka kenan!”
“Umma ki sani komai kika fada min zan dauka ba shawara bace kamar umarni ne amman ina neman wata alfarma.”
“Ina jinka?”
“Umma dan Allah ki fada min dalilin ki na yin haka.”
Dagowa tayi ta kalle shi tace
“………………”
*
**
***
****
*****
******
*******
Hannu yasa ya rufe system din da sauri ta dago shima kallon ta yake yace
“Kece magani na doctor na fada miki kuma ina kara fada miki.”
“Shiyasa nace kaje a baka shawara dan ni babu ta yadda zan zama maganin ka!”
“Saboda me?”
“Saboda ni matar wani ce!”
Wata dariyar rainin hankali yayi yace
“Insha Alah matata ce ke Doctor kuma ki ajiye a ranki da izinin Allah ke tawa ce ba ta kowa ba.”
Ido ta zaro tana kallon sa yayi murmushi yace
“Dan haka ma gwara ki ban dama Doctor wallahi da gaske nake son ki da aure i love u with all my heart kinga gidan mu kije kiyi bincike akai na in kin samen da wani hali marar kyau sai ki ki amsar soyayya ta amman yanzu bansan dame kike wofantar da soyayya ta.”
“Ka kyale ka rabu dani bana son ka kuma ba zan so ka ba mutum daya zan so a rayuwa ta kuma shi zan so har karshen rayuwa ta ba wanda zai kara shiga zuciya ta shi kadai na baiwa zuciya ta dan haka ka kyale ni ka daina damu na da zancen soyayya bana so bana so ta shi kadai nake so da kauna.”
Ta fada tana kifa kai akan table din ta tana kuka kamar ranta zai fita.
Sosai yake jin kukan nata har cikin zuciyar sa sai yaji duk jikin sa yayi sanyi dan haka ya koma gaban table din yace
“Am unm.. Dan Allah kiyi hakuri ki daina kukan nan Doctor wallahi ina jin zafin sa a cikin zuciya ta. In har kinsan yadda so take ya kamata ki tausaya min daga alamu kin shiga wani hali a soyayya ko wanda kike so ya mutu ko wani abu ya faru please ki dauki kaddara kika sani ko Allah ya dauke shi dan ki zama tawa kika sani Allah ya dauke shi dan kaddara ta hada mu kinsan zaki hadu dani ne?”
Ya girgiza kai yace
“A’ah amman kuma tin daga lokacin da muka hadu kullum sai mun hadu me zaki kira wannan dashi Doctor sai gaki a gidan mu Doctor. Doctor kin siye min zuciya ta da komai naki komai kikai burge ni yake wallahi da gaske nake son ki Doctor in da zaki tsaga jinin jiki na son ki ne ke yawo zuciyata sunan ki da hoton ki take amfani dasu a ko da yaushe Ki tausaya min doctor ki tausaya min ina son ki da gaske Doctor. Kiyi hakuri in ni na saka ki kuka amman ki sani bazan taba daina son ki ba doctor. I love u Dr!”
Yana kai wa nan ya juya ya fita. Dagowa tayi jin rufe kofar sa. Kai ta jingina da kujera tana juya maganganun sa. Kai ta girgiza tace
“A’ah kaddarar da ta dauken Fu’ad ita zata dawo min dashi. Allah ka dawon da Fu’ad Allah kasa Fu’ad yana lafiya Allah ka kiyaye min Fu’ad dina.”
*
Yana fita ya tadda Jiddah na waya gun mota ya nufa kawai ya shiga. Har ya shiga ba ta gama ba sai horn yai mata wannan yasa ta karaso ta shiga tana fadin
“Mayi waya anjima nagode!”
Ta katse wayar kallon sa take yadda ya canja tace
“Lafiya honey?”
Shiru yayi tace
“Naga ka dade ba dai wata matsalar bace ba ko?”
“Nothing!”
“Ka tabbata?”
Kai ya gyada tace
“To wai kasan wannan doctor ne?”
“Me kika gani?”
Fuska ta dan bata tace
“Sai kallon ta kake in matar aure ce fa?”
“Bama ita bace Jiddah!”
“Ya akai ka sani!”
Shiru yayi tace
“ni dai bana son kana kallon mata.”
“Yaushe kika taba ganin ina kallon mata in ba yau ba. Kinsan bana yi in har na tsaya kallon abu to ya min ne da gaske!”
“What did you mean kenan!”
Murmushi kawai yayi. Tace
“Kasan dai ban son irin wannan wasan ko a duniya ba abinda na tsana kamar kishiya yadda ni ba zakai sharing dina ba kaima ba zan ba.”
“Haba?”
“Wacce irin tambaya ce wannan?”
Murmushi yayi yace
“ai kinsan namiji mijin nace hudu ne ko inda hali har kwarkawara ko? Kuma kinsan ban tabai miki alkawarin ba zan miki kishiya ba ko?”
Shiru tayi yace
“Dan haka ki zama cikin shiri ko da yaushe zan iya miki kinji ko?”
Murmushi ta saki ta kama dayan hannun tace
“Honey ni dai ban son irin wannan wasan!”
“Am not joking wife.”
Sakin sa tayi ta hade rai. Ya kalle ta ya shafa fuskar ta yace
“But i love u ko?”
“Na sani ita kuna wata fa!”
“To ina watan take a yanzu ai har yanzu banganta ba.”
Murmushi ta saki tace
“Da gaske?”
” zan miki karya ne!”
Kai ta girgiza tace
“a’ah ai kwara muyi zaman mu, mu biyu mu haifi ya’ya ko?”
Kai ya gyada mata kawai.
A haka suka karasa gida suna shiga ya nufi dakin sa dan yana son ya watsa ruwa itama daki ta shiga ta watsa ruwan.
*
Kasa komai tayi jikin ta yai sanyi har shida da rabi bata mike a inda take ba jin an fara kiran sallah yasa ta mike da sauri. Har ta dauko jaka sai ta ajiye ta wuce bandaki ta daura alwala ta zo ta tada sallah. Tana idar wa ta mike ta dauki jaka ta kira Momy. Momy ta dauka tace
“Ai na ta kira a baki dauka ba nasan wayar tana silent.”
“Wallah aiki ya rike ni amman yanzu zan fito.”
“Zaki iya driving ko na aiko driver;”
“Zan iya Momy!”
” shikenan ki kula Allah tsare.”
“Amin nagode.”
Ta fita ta nufi wajen motar ta. Shiga tayi tai addu’a sannan ta tada motar. A hankali ta dinga tukin tama rasa tunanin da zatayi gaba daya. A haka har ta karasa gida. Horn tayi mai gadi ya bude sannan ta shiga tai parking.
Jiki a sanyaye ta shiga gidan ta samu Momy zaune akan carpet tana karatun alkur’ani shiga tayi da sallama Momy ta bita da kallo bayan ta amsa. Zama tayi a kan hannun kujera tace
“Sannu da gida Momy!”
“Yauwah kin dawo lafiya?”
“Alhamdulillah!”
Ta mike tayi ciki da kallo Momy ta bita.
Tana shiga daki ta cire mayafin jikin ta ta nike sannan ta zare rigar jikin ta towel ta daura ta nufi toilet  tana shiga ta sakar wa kan ta ruwa ta jima a toilet ta fito ta zura riga kawai ta shafa turare ta tada sallah isha’i tana idar wa tayi shafa’i ta zauna tana jan carbi.
Tana shiga daki ta cire mayafin jikin ta ta nike sannan ta zare rigar jikin ta towel ta daura ta nufi toilet  tana shiga ta sakar wa kan ta ruwa ta jima a toilet ta fito ta zura riga kawai ta shafa turare ta tada sallah isha’i tana idar wa tayi shafa’i ta zauna tana jan carbi. Bayan ta gama tasbihin ta,  ta dauki alkur’ani ta fara karantawa. Karfe tara ta rufe ta ajiye akan sallayar da take. Kanta ta jingina da gado ta lulla duniyar tunanin rayuwar ta da makomar ta.+
Momy ganin har tara bata fito ba yasa ta mike ta dibar mata abinci tayo dakin ta. Duk sallamar da tayi bata amsa ba dan bata ma jin ta. Shiga tayi ta ajiye abincin akan mudubi sannan ta zagaya ta zauna a gaban ta dagowa tayi tace
“Momy!”
Kallon ta Momy ta tsaya can tace
“Me yake damunki?”
Kai ta girgiza tace
“Ba komai Momy!”
“Yanzu a duniya wa kike dashi da yafini Fateema in baki fadan damuwar ki ba wa zaki fadawa Fateema ko kin fiso ki dauwama cikin damuwa har tai miki illah. Shin in da mahaifin ku na da rai zai so ganin ki a haka kuma ya barki a haka. Sam ba zai yadda to dan me ni da nake uwa zan so ganin ki a haka. Fateema na rasa ya zanyi dake akan damuwar ki da Fu’ad shikenan ke ba zaki dauki kaddarar ki ba Fateema haba Fateema ki mika komai ga Allah Shi zai iya miki amman kina saka abu a ranki tayaya zaki na jin dadi ke kenan kullum damuwa da tunani da kuka a haka zaki kare rayuwar ki Fateema. In nace ki fitar da miji kice baki da wanda kike so Fateema shin zaman me zaki yi tayi min a gida yau da ace da sauran igiyar Fi’ad akan ki da sauki amman kina gani saki uku ne yanzu in fatan komawa wajen sa kike ai dole sai kinyi wani auren. Bama wannan ba yanzu ina kikaga Fu’ad wajen shekara daya da rabi rabonsa daku haba Fateema in har bakya son ganin damuwa ta kiyi hakuri dan Allah kema ki daina damuwar nan.”
Hawayen dake idon ta ne ya zubo tace
“Na daina insha Allahu Momy. Amman Momy wallahi ina son Fu’ad!”
“Nasani Fateema kita addu’a Allah zaba miki abinda yake mafi alheri. Sai shawara ta biyu da zan baki duk wanda ya fito miki ki bashi dama baki san wane alherin ke tafe dashi ba kinji?”
Kai ta gyada tana goge hawaye. Momy ta rumgume ta tace
“Ki daina kukan haka kinji kiyi ta addu’a muma kullum muna miki.”
“Nagode Momy!”
Abinci Momy ta dauko mata ta zuba mata tace
“Maza kici bari na kawo miki ruwa.”
“Momy ki barshi akwai a firij anan!”
“A’ah bari na dauko miki!”
Ta isa firij din ta dauko mata ta ajiye haka ta dinga ci tana mata hira har taci da yawa ta sha ruwa. Ranar tare suka kwana da Momy dan Momy bata son ta barta ita kadai tai ta tunani. Ai kuwa ilai kan tai baccin tunanin tai tayi da tunanin kalaman Aslam da ya tsaya mata a rai duk juyi sai ta tuna su. Tai ta tsaki kuwa.
Friday 2:00pm
Jannah ce ta shigo asibitin sanye da doguwar riga ta atamfa bata daura dan kwali ba mayafi kawai ta yafa sai jakar ta da takalmi a jikin ta. Mai gadi suka gaisa tace
“Please office din dr Fateema nake nema!”
“Kwatance yai mata ta isa. A bakin kofa ta tsaya ta fadi wajen wacce tazo. Shiga akai aka fadawa Fateema tace
“Abarta ta shigo.”
Ta shiga da sallama. Fateema ta mike da sauri ta rumgume ta tana fadin
“Ashe da gaske dai zaki zo!”
STORY CONTINUES BELOW
“Eh Dr ina yini?”
“Lafiya lou ya kike ya gida da Hajiya?”
“Lafiya lou!”
Ta fada suka zauna. Fateema ta mike ta bude firij ta dauko mata lemo da ruwa sannan tace
“Me zaki ci na sa a kawo miki?”
“Wallahi Anty a koshe nake daga gida nake.”
“Please mana ki zaba.”
“Allah na koshi.”
“Ai kuwa ko snacks ne sai kinci.”
Ta fada tana daukar waya tai magana sannan tace
“Ina Noor?”
“Tana gida tace bazata biyo ni ba zuwan ta daban nawa daban.”
“Allah sarki ina zuba ido.”
Knocking akai ta amsa aka shigo leda ce a hannun wacce ta shigo da sallama suka amsa ta durkusa ta ajiye ledar Fateema ta bude taja ta dauki kudi ta bata tace
“Nagode!”
Ledar ta dauka ta bude tace
“Bismillah please!”
“Nace na koshi fa wallahi amman bari naci springroll din nan.”
Ta dauki daya taci. Tana ci suna dan hira har Fateema ta mike zata round tace
“Zaki bini ne ko zaki zauna naje na dawo.”
“Muje na ga asibiti.”
Nan suka fita. Pateint dinta ta duba daga nan ta wuce tana nunawa Jannah tsarin asibitin. Sai hudu suka koma sallah sukai sannan suka fice daga asibitin zuwa radio station din.
Acan ma Jannah na zaune Fateema ta gudanar da program din ta na awa daya wanda 5:30pm ta gama tace
“Muje gida ko?”
“No Anty zuwa gida na musamman zanyi yanzu ai dare yayi ki bari zan zo ki ajiye ni a juction kawai na hau napep.”
“What napep a’ah muje na ajiye ki na gaida Hajiya nai mata barka da juma’a.”
“To shikenan nasan kuwa ta ji program din ki.”
Sukai murmushi suka wuce gidan su Hajiya. suna zuwa tai parking ta fito ta gyara yafen ta sannan suka shiga ciki.
A babban falo suka same su Noor da Hajiya. Hajiya na ganin ta tace
“Lale marhabun.”
Noor ta mike ta rumgume ta tace
“Sannu da zuwa Anty Doctor.”
Dariya sukai ta zauna suka gaisa da Hajiya sannan suka gaisa da Noor. Jannah kuwa tayi kitchen taje ta hado musu abinci ta kawo musu. Nan yace
“Doctor bismillah!”
“Kai a’ah na koshi.”
“Kai doctor me kika ci?”
Ta kalli Hajiya tace
“Dan Allah Hajiya kice taci abinci!”
Hajiya tace
“Fateema kici Mana ai Nan gidan kune!”
“To hajiya!”
Nan jannah tai serving nata ta fara ci.
Wayar ta ta dauka taiwa Momy text dn Kar taga ta dade. Tana gama cin abinci tana Shan lemo akai sallama a dakin.
Jin muryar sa Yasa ta kware da sauri suka hau Mata sannu. Shi kuwa zuba Mata Ido yai Yana kallon ta ya kasa ko da dauke kan sa. Sanye take cikin riga da siket na atamfa Dinkin yai Mata kyau ya kamata. Mayafin ta na ajiye akan cinyar ta.
Sai da ta dawo dai dai kowa yai Mata sannu. Ta amsa idon ta har yayi jajir.
“Sannu!”
Ya fada cikin taushin muryar sa.
“Yauwah Ina yini?”
“Lafiya Lou!”
Jannah tace
“Ina yini Uncle ?”
“Lafiya Lou Baby ya kike?”
“Alhamdulillah Uncle ka gane ta ita ce wannan doctor da nake baka labari wacce rannan suka zo ka gane ta?”
“No!”
Noor tace
“Antyn surutu!”
Ta kalli Aslam tace
“Ina yini Uncle?”
“Lafiya ya kike?”
“Lafiya Lou!”
“Hajiya ya juma’at?”
Aslam ya fada. Tace
“Alhamdulillah ya Jiddah?”
“Tana lafiya!”
Mayafi Fateema ta dauka ta yafa sannan ta tashi zata dauke kwanukan Jannah ta amsa ta Kai kitchen.
STORY CONTINUES BELOW
Fateema ta durkusa tace
“Hajiya ni Zan tafi.”
“Har Zaki tafi Fateema daga zuwan ki!”
“Wallahi Daman Jannah na dawo da ita nace na shigo nai Miki barka da jumma’at.”
“Amman wallahi nagode! Bari Ina zuwa.”
Ta mike tayi ciki. Jannah tabi bayan ta.
Zama Fateema tayi kanta a kasa Aslam kuwa in Banda kallon ta ba abinda yake. Daga baya ya koma ya zauna Akan kujera saitin ta ya fara daukar ta pictures ba Wanda ya Lura Dan ba flash Kuma wayar na a silent. Sai da yaji tahowar su Jannah sannan ya daina.
Hajiya ta mika Mata ledar hannun ta tace
“Gashi ba yawa agaida Hajiyar taki!”
“Zataji nagode!”
Ta mike Jannah ta amshi ledar. Suka fito Noor da Jannah Dan su rakata.
Mota ta shiga ta amshi ledar da Hajiya ta Bata tai godiya. Key tayiwa motar Amman Bata tashi ba. Kara yi tayi Taki ta tashi. Tayi tayi Amman Taki ta tashi. Fitowa tayi ta bude gaban motar ta danyi tabe tabe sannan ta dawo ta Kara tada motar Amman Taki tayi.
Kara komawa tayi Taki tayi. Bakaniken ta ta Kira ta fada Masa inda zai zo sannan ta tsaya.
Suna tsaye Aslam ya fito Jannah taje tace
“Uncle ko zaka Kai doctor gida kaga motar Taki ta tashi.”
Kallon ta ya danyi yace
“Ba matsala.”
Wajen Fateema ta dawo tace
“Aunty kizo Uncle yai dropping naki. In bakaniken yazo ya kawo miki motar gida ko?”
Noor tace
“Gaskiya kam. Muje!”
“Ku Bari da yazo zai taba nasan zata tashi.”
“Anty badai ki sani ba gwara ya kawo ki gidan kawai Kinga baku da nisa da gidan sa sosai “
Ba yadda ta iya haka tabi bayan su ba Dan taso ba. Suna zuwa har ya shiga. Jannah ta bude Mata gaban motar tana shiga wani sanyi da kamshin Mai Dadi ya daki hancin ta. Ido ta lunshe Jannah ta rufe kofar tana fadin
“Mun gode Sai munzo.”
Ido ta bude tace
“Nima nagode!”
Suka daga Mata hannu sannan suka juya sukai ciki.
Motar ya tayar mai gadi ya bude gate suka fita. Suna Hawa kan titi yace
“Doctor a gidan mu!”
Shiru tayi yace
“Ya aikin yau Daman bakiji yadda nai missing naki ba da har Zan shigo asibiti Kuma ban samu lokaci ba sai gashi Allah ya kawo ki har gida. Abin farin cikin ma gaki a motata Kai Alhamdulillah!”
Shiru ta Kuma Yi yace
“Kinyi shiru Doctor Dan Allah kiji tausayin Dan bawan Allah Nan mana.”
Kallon sa tayi ta dauke Kai. Tace
“Kasan inda zaka Kai ni ne?”
Murmushi yayi yace
“Gida na Zan Kai ki!”
“Akan me? Kaga in ba zaka kaini gida ba ajiye ni anan na sauka!”
Kallon ta yayi yace
“Sorry dear Mai da wukar gida Zan Kai ki Amman wata Rana ai a gidan nawa Zaki rayuwar.”
Kai ta dauke tana kallon Waje. Wayar ta ce tai Kara ta dauka tana fadin
“Assalamu Alaikum!”
“Wa’ailaikum salam Anty Fateema Ina yini ya gida ya aiki?”
“Alhamdulillah! Ya kike?”
“Lafiya Mimie ce nace Bari na Kira na gaishe ki nai Miki happy juma’at!”
“Ah Mimie ya kike yasu Izzy?”
Ta fada tana murmushi.
“Suna lafiya ga Izzyn!”
Ta amsa Nan suka gaisa suna ta Hira cikin sakin fuska sai murmushi take har sukai sallama.
“In kina murmushi Ashe kin fi kyau!”
Fuska ta tsuke yace
“To ai sai Naga kin Kara kyau ma har kinfi kina murmushi!”
“Bana so!”
“Menene bakya so Doctor fadar gaskiyar ko me?”
Shiru tayi yace
“Ni kam ban taba ganin likita marar tausayi ba irin ki kinsan a halin da nake ciki kuwa!”
Lokacin suka iso kofar gidan su zata bude mota ya saka lock juyowa tayi tace
“Buden Mana!”
“Ba sallama!”
Hararar sa tayi yai murmushi yace
“Kai Kinga yadda kikai kyau Dan Allah Kara Yi muga!”
Baki ta murguda yace
“Wow komai naki mai kyau ne Doctor I love u and I like all ur attitude!”
“Please ka buden kofa.”
Unlock yayi yace
“Sai when Kuma?”
Juyowa tayi ta harareshi sannan ta murguda baki ta juya ta bar wajen. Murmushi yayi ya bita da kallo har ta shige sannan ya tada motar ya bar layin Yana Jin nishadi a tare dashi.
*
Monday
Zaune take a office din ta sanye da maroon kalar less Wanda akai Masa ado da milk zare duk jikin sa stones ne Dinkin doguwar riga ne a jikin ta ya kamata daga Sama daga kasa a baje. Medium mayafi ta yafa a kafadar ta ta saka milk fashion da abin hannu da agogo. Tayi kyau sosai.
Juyi take akan kujerar ta tayi nisa a cikin tunanin ta taji an budo kofar dagowa tayi da sauri taga Aslam tsaye a bakin kofar sanye da maroon kalar suit tai Masa kyau sosai.
Kai ta dauke tace
Wai meyasa suka barin sa Yana shigo min ne?”
Ta saki tsaki.
“Good evening Doctor!”
“Evening!”
Ta fada fuska ba yabo ba fallasa.
Zama yayi yace
“Bani da lafiya Doctor!”
Paper ta yaga tai rubutu a jiki tace
“Kaje wajen Doctor Auwal ya duba ka!”
“Please Doctor ni ke nake so!”
“Lafiyar ka kalou kenan!”
“Wallahi am sick Doctor!”
Dagowa tayi taga yai kalar tausayi dan haka tace
“what’s wrong with you?”
“Bana iya Bacci ga ciwon Kai in ta tunani!”
“Me kasa a ranka haka?”
“Tunanin ki Doctor!”
Mikewa tayi ta dawo tsakiyar dakin tace
“Shiyasa nace maka lafiya ka kalou!”

DUNIYATA*+

*Ina ma’abota karatun littafan hausa? Ku matso kusa kakarku ta yanke saqa.*
*shin kun karanta littafin FARAR TAFIYA?labarin soyayyar Amina da Isma’il wanda ta qullu bayan qaddarar fyade ta gifta tsakaninsu.*
*ga kuma littafin RUMFAR KASUWA wanda ya lakuto bangarori da dama na abubuwan da suke faruwada yara masu talla a kasuwanni da shaguna,ya fito muku da illa tallace tallace da kuma barin yanmata suna yawo sakaka babu kimtsi*.
*sannan ya fito muku da hanyoyin da za ku bi ku ciro wa yaranku hakkinsu idan aka zaluncesu musamman akan fyade ko yaudara.sannan ya fadada muku matakan aurar da yaran da kaddara fyade ko yaudara ya afka musu tare da jan su a jiki da kuma nuna musu kulawa ba tare da an qyamacesu ba*.

*TO YAU MA GA WATA SABUWA NAN*

*Littafin DUNIYATA labari ne da ya zo muku a lokacin da kuke bukatar irinsa a duniyar rubutu,ya zo muku da sabon jigo mai ma’ana.tare da warware kullin da aka zarga cikin ruwan sanyi da karfin addu’a.labarin ya zo muku ne da salo na daban da saura.ya kuma taho muku da abin lura da cewa ba mata kadai suke fuskantar qalubale a rayuwa ba,maza ma suna fuskantarsa wanda na Muktar Jarumin littafin ya bambanta.za ku ji yadda badaqala ta karke tsakanin ďa da mahaifinsa ,ya kuma fito muku da illolin rashin yarda da qaddara.gwagwarmayar ďa namiji tsakaninsa da mahaifinsa wanda ta kai uba ya yi wa dansa qazafin yunqurin kisa.*

*Kina bukata? ko kuna bukata?*

*Ku garzayo domin biyan naira dari biyu kacal ta wannan account number 0140772170 MURJA SALISU UNION BANK sai ku turo shaidar biya a wannan number 07034624830*

*Ko kuma katin MTN na naira dari biyu ta wannan number 07034624830 ku tura shaida kuma still ta wannan number din*.
***
**
*
Monday
Zaune take a office din ta sanye da maroon kalar less Wanda akai Masa ado da milk zare duk jikin sa stones ne Dinkin doguwar riga ne a jikin ta ya kamata daga Sama daga kasa a baje. Medium mayafi ta yafa a kafadar ta ta saka milk fashion da abin hannu da agogo. Tayi kyau sosai.

Juyi take akan kujerar ta tayi nisa a cikin tunanin ta taji an budo kofar dagowa tayi da sauri taga Aslam tsaye a bakin kofar sanye da maroon kalar suit tai Masa kyau sosai.

Kai ta dauke tace
Wai meyasa suka barin sa Yana shigo min ne?”
Ta saki tsaki.

“Good evening Doctor!”
“Evening!”
Ta fada fuska ba yabo ba fallasa.

Zama yayi yace
“Bani da lafiya Doctor!”

Paper ta yaga tai rubutu a jiki tace
“Kaje wajen Doctor Auwal ya duba ka!”

“Please Doctor ni ke nake so!”
“Lafiyar ka kalou kenan!”

Wallahi am sick Doctor!”
Dagowa tayi taga yai kalar tausayi dan haka tace
“what’s wrong with you?”
“Bana iya Bacci ga ciwon Kai in ta tunani!”

STORY CONTINUES BELOW

“Me kasa a ranka haka?”
“Tunanin ki Doctor!”

Mikewa tayi ta dawo tsakiyar dakin tace
“Shiyasa nace maka lafiya ka kalou!”
Ta juya zata fita cikin zafin nama ya mike ya kamo hannun ta ya hada ta da bango. Yai.mata rumfa. Kamshin turaren su ya gauraya ya bada wani kamshi mai dadi. Shi take kalla kamar yadda shima ira yake kalla. Kai ta dauke tana yin kasa da idanun ta dan ya matse mata hannu. Kokarin gwacewa take yace
“Fateema da gaske nake bani da lafiya Kuma duk abinda na fada miki su ke damuna please ki taimaka min please!”

Shiru tayi ya kama kafadar ta yace
“Fateema look into my eyes!”

Kin dgowa tayi yace
“Please ki kalli cikin kwayar Ido na kiga yadda nake son ki. Ki tausayan ni bani na daurawa Kai na son ki ba Allah ne Amman Dan me Zaki na min haka Dan Allah ya dauran son ki so kike na mutu ko me?”

Hawaye ne ya fara biyo kuncin ta yace
“Wallahi da gaske nake son ki ba da yaudara ba. Ki taimakan Fateema ko ban Miki ba?”

Kai ta girgiza yace
“To menene matsalar?”

Kan ta ta kwace ta juya Masa baya tace
“Kayi hakuri ba son Kane bana Yi ba Amman na daina soyayya in ma soyayya zanyi akwai Wanda nake jira kayi hakuri Dan Allah!”

Zata wuce ya Kara Shan gaban ta yace
“Waye wannan Fateema Yana Ina Ina yake Ina ya tafi ya barki da bai tsaya ya amshi soyayyar ki ba.”

“Nima ban sani ba ya tafi ya barni a lokacin da nafi son sa da bukatar sa a lokacin da nake Jin ban da Wanda ya kaishi. Ya tafi ya barni ban San inda yake ba Ina ka tafi ka barni Dan Allah ka dawo waje na.”
Ta fada tana durkushewa a wajen. Durkusawa Aslam yai ya dago kanta yace
“Ya tafi ya barki akan me?”

Kai ta hau girgizawa yace
“Dan sadaukarwa ko Dan son kan sa!”

Tai shiru in Dan wadan nan abubuwan ne ya kamata kema ki samu farin ciki Fateema Kar ki bar wani ya ruguza Miki rayuwar kila Wanda kike domin sa Yana can yai aure har ya haihu am….”

“Karya kake Sam Fu’ad will never do this to me. Ni kadai ce zabin sa. Ni kadai yake gani a matsayin mace ni kadai yake so ba zai tabai min haka ba. Kada ka kawon wannan tunanin kada kasa wannan tunanin yana running a Raina Dan Allah Dan zai ruguza min farin ciki na Dan Allah ka Bari ka barni a Yana can zai dawo Kar kasa na fara tunanin Yana tare da watata ba Zan iya jura ba.”
Ta fada tana hade Kai da gwiwa.

Dago kan ta yayi yace
“Is alright Fateema Ki daina kuka Fateema kinji komai yai Farko Yana da karshe kinji yanzu ki daina kuka Allah na tare dake insha Allah komai zai dai dai ta. Yanzu ki tashi a kasan nan mu koma can muyi magana.”

Mikewa tayi a hankali ta koma kan two sitter ya zauna akan one sitter yana kallon ta tana hawaye.
“Nifa ba kuka nace ki min ba!”

Hawayen ta hau gogewa yace
“Ina son ki fadan wani abu akan rayuwar ki da dalilin ki amsar soyayya ta duk da naso na gane!”

Shiru tayi yace
“Say it out doctor nasan zaki samu relief kema.”
Ajiyar zuciya ta sauke. A hankali ta fara bashi labarin ta har haduwar su da Fu’ad da soyayyar su da zuwan Yaa Fauwaz. Dramar da aka sha har da rasuwar Dady da kuma yafiyar Yaa Fauwaz da auren su da Fu’ad rayuwar da suka sha da zuwan su gida wanda shine rabuwar ta da Fu’ad. Tana zuwa nan ta kifa kanta akan cinyar ta ta saki wani marayan kuka.

Ido ya runtse yace
“Dan Allah ki daina kukan nan Fateema!”
Dagowa tayi tace
“Anya zan daina kuka kuwa ina jin ni da na daina kukan masoyi na sai ranar da na koma ga mahallaci na.”

“Ina jin ki har yanzu ba labarin sa.”
Nan ta cigaba da bashi halin da ta shiga har fara aikin ta da komai. Sosai tausayin ta ya kamashi.

Yanzu ya gane akwai wanda yafi shi son Fateema,  amman shima yana jin sa a masoyin Fateema na hakika wanda shima zai iya bata farin cikin sa.

STORY CONTINUES BELOW

A labarin ta ya gane Fateema bata da masoyi sama da Fu’ad wanda ya sadaukar da farin cikin sa da rayuwar akan ta,  ya gane Fu’ad yai zaton tafi son Fauwaz shi yasa ya tafi ya barta dan ta auri Fauwaz. To shi dan me Fauwaz ya tafi ya bar ta kishi ko sadaukar wa. Kai ya girgixa dan a farkon fara bashi labarin shi kansa yasan Fateema ta fi son Fauwaz amman yanzu kan sa ya shiga duhu domin kuwa ya kasa gane *Wa take so?* duk da a yanzu maganar Fu’ad take amman yadda rabuwar su ta kasance a lokacin da ta fara cire rai da Fauwaz ya barta shi yasa Fu’ad ya tsaya a ranta.

Hakika Fu’ad masoyin asali ne yayi saudakarwa amman yayi garaje meyasa bai tsaya ya bincike akai ba.
“Sai hakuri Fateema abu daya zan tunasar dake shine ki sani a yanzu ko Fu’ad ya dawo ba aure a tsakanin ku ko kina zaton haka zaki kare rayuwar ki ba aure. Kiyi hakuri ki amshi kaddarar ki ni a yanzu a matsayin Yayan ki kuma abokin ki nake dan haka zan baki shawarar da zan bawa kanwata kuma kawata ce. Addu’a ita ce karshen komai kuma akace inso cuta ne hakuri magani ne. Kuyi hakuri nasan kinyi rashin masoyi kuma bazaki maye gurbin sa ba sai dai kiyi tai masa addu’a duk inda yake Allah ta kareshi da fatan alheri.”

Kai ta gyada yace
“To ki daina kuka yanzu me kike kin gama aiki ne ko me?”
Kai ta gyada yace
“To in nemi alfarma a gunki?”

“Ta me?”
“Wata unguwa zaki rakani!”
Kallon sa tayi yace
“Please!”

Agogo ta kalla tace
“Yamma ai tayi!”
“Is just five fa! Ba dadewa zamuyi ba.”

Shiru tayi yace
“Nifa bana siyar da kan mutune!”
Murmushi tayi tace
“To kaje gani nan!”

Mikewa yayi yace
“Nagode!”
Bandaki ta shiga ta dauraye fuskar ta sannan ta fito ta goge fuskar ta shafa hoda ta sa man lebe. Fitowa tayi ta rufe kofar ta sannan ta nufi parking space.

A tsaye ta same sa yana ganin ta ya karaso yana fadin
“Kinyi kyau kanwata!”
Murmushi tayi ya bude mata gidan gaba ta shiga ya rufe sannan ya zaga ya shiga ya tada mota mai gadi yai musu addu’a suka tafi.

Wani park suka isa yai parking ya fito itama ta fito suka shiga ciki tin daga enterence din wajen zaka san wajen ya hadu ba karya kana shiga wani sanyn da ni’ima a wajen daman ga yamma tayi ido ta lumshe suka isa wajen zama kan wasu hadadun kujeru.
Zama sukai wata mata tazo cikin uniform din wajen ta kawo musu lemo da ruwa da paper a hannun ta. Amsa Aslam yayi ya mikawa Fateema amsa tayi ta kalla ta mika masa tace
“Bana bukatar komai?”

“Saboda me?”
Kai girgixa. Ticking yayi ya mika mata ta amsa ta bar wajen batai minti goma ba ta dawo dauke da katon tray. Nan ta fara jere kayan dake hannun ta tin daga kan abinci snacks da kayan ciyeye ciye ne.
Bayan ta tafi yace
“Ki ci abinda kike so?”
“Bana jin yunwa!”

“Me kika ci a office?”
“Am fasting fa!”

“Oh yau fa monday ko?”
Kai ta gyada yace
“Bari ai miki parkaging nasa.”

Ya kira daya daga cikin masu aiki agun yace in zasu tafu zasu amsa ayi parkaging nasa. Amsa tayi suka zauna yana dan shan lemon sannan yace ta tashi su zagaya wajen duk wanda ya gansu sai sun burge shi sai a zata mata da miji ne

Sosai wajen ya burgeta dan har lillo ta hau rabar ta samu refreshment sosai ta saki Aslam sai ganin dariyar ta yake har 6:30 suna wajen sau da yaga time ya kure kuma tana azumi sannan yace ta taso su tafi. Abubuwan ya amsa sannan suka fita. A hanya aka sha ruwa dan haka ta sha ruwa. Mai fruit ya gani ya tsaya ya siya mata. Har kofar gida ya kai ta ya mika mata ledojin ta amsa tana fadin
“To Uncle nagode Allah saka da alher.”

Murmushi kawai yayi ta juya tai cikin gida yabi ta da kallo anan layin su yai magarib a wani masallaci sannan ya tafi gida.

*
**
***
****
*****
******
*******

STORY CONTINUES BELOW

Tagumi yayi yace
“To fa! Me yake faruwa?”

“Da farko zan baka shawara domin kuwa ina son ka janye maganar auren ka da Aisha ka bata dama ta fito da wanda take so!”
A zabure ya kalli Umma yace
“Bangane ba?”

“Eh shawara na baka amman in kaga zaka dauka kenan!”
“Umma ki sani komai kika fada min zan dauka ba shawara bace kamar umarni ne amman ina neman wata alfarma.”

“Ina jinka?”
“Umma dan Allah ki fada min dalilin ki na yin haka.”
Dagowa tayi ta kalle shi tace
“Kamar yadda ka fada ba tun yau ba na gane Aisha na da damuwa kuma ta sauya. amman sai take nuna min babu anfi shekara biyu tana wannan halin nata.”

Kai ya gyada. Umma tace
“Nayi nayi da ita ta fadan menene amman taki sauyin ta ya cigaba har kwanaki na same ta inda ta fara bani labari akan wani abu da ya shige mata duhu ba akan kowa bane sai akan wani wai Yaa AK wanda yake koya mata karatu.”

Gaban sa ne ya fadi jin an kira Yaa AK shi kadai wani lokacin sai yaji sunan yai masa amsa kuwa a zuciyar sa da kunnen sa wanda har abun ya fara bashi tsoro.

Umma.tace
“Tana fada min halin da take shiga na rashin sa da abubuwa wanda nagane son sa take tin a lokacin na farai mata addu’a Allah yasa kada tayi son maso wani domin kuwa na gane shi Yayan nata dan masu hali ne kaga ita zata sha wahala sai tausayin ka ya kamani.”

Dagowa tayi ta kalle shi tace
“Kwanakin baya ta shigo gida tana kuka da na matsa mata ne take fada min komai tsakanin ta da Yayan nata.”
Nan Umma ta fada masa duk yadda sukai da Aisha. Sannan ta daura da fadin
“Tin daga ranar da abin ya faru Aisha bata kara samun wata nutsuwa da kwanciyar hankali ba ina lura da ita sosai. Zuwan ka ne ma ya dan sa ta sake amman na tabbata da baka nan zata shiga wai hali dan damuwar ta zata fi haka.”

Shiru sukai gaba daya. Umma ta mike ta duba pepper soup din da take sannan ta dawo ta duba zogalen da take turarawa ta dauki tunatur da albasa da cocumber tana yankawa sannan tace
“A gaskiya Muhammad na gane Aisha na tsananin son Yaron nan domin tin lokacin ban kara ganin walwalar Aisha ba kuma nasan ba zai rasa nasaba da rashin zuwan sa ba wanda na zata korar sa tayi amman tacr min a’ah bata kore shi ba.
Muhammad kada kaji haushin Aisha ko kadan domin tana son ka kaima amman a gaskiya yadda na lura tafi son Yaron can duk da akan ka ta danne komai ta kori komai ta sadaukar da farin cikin ta dan samuwar naka hakika Aisha na son ka so bakadan ba amman a gaskiya naga alamar son da take maka bai kai wanda takewa Yaron can ba. Kuma in ka aure ta tamkar ka auri gangarar jikin ta ne zuciyar ta da ruhin tana wani wajen. Na bata shawara akan ta duba ta gano *wa tafi so?* amman tace min kai kai bayan kuma nasan ba haka bane tana yin haka ne dan alkunyar ido na tana yin haka ne dan son da take maka tana son ta sadaukar da farin cikin ta gareka wanda da matsala Muhamad domin duk yadda taso kyautata maka za asamu matsala tinda da son wani a zuciyar ta,  ni ba zan so dukkan ku ku shiga wani hali ba wannan yasa na baka shawara dan ance inso cuta ne hakuri magani ne. Kai na miji ne kai ya kamata ka hakura ita ta samu zabin ranta.
Ba dan na fison Aisha ba sai dan samar muku masalaha da nutsuwa ina fatan zaka dauki shawara ta. Kuma kana gani tin kan aje ko ina an fara samun matsala da karancin shekarun ta jinin ta ya hau gaba me kake tunanin zai faru ba dai fata nake ba.”

Shiru yayi zuciyar sa na bugawa da karfi da karfi shin yaya zaiyi me zaicewa Umma gaba daya kan sa ya dau caji yai masa nauyi. Itama Umma batai masa magana ba sai mikewa da tayi.

Kiran sallah magariba ya jiyo wannan yasa ya mike jiki a matukar sanyayeya isa yai alwala ya fita asallaci. A masallaci bayan an idar da sallah zama yayi kawai yai shiru gaba daya kwakwalwar sa ta kasa masa ko wannen tunani tunanin sa daya tayaya zai samar wa Aisha farin cikin ta.

Bai aune ba sai jin kiran sallah isha’i yayi haka ya mike akai sallah dashi sannan ya kara wani zaman. Har karfe tara sannan ya mike jiki a sanyeye ya fito har ya shiga gida sai ya juya ya koma gun mai fura ya sa aka saka mata nono da kwakwa da madara aka dama aka juye a roba ya biya ya taho gida.

A tsakar gida ya samu su Umma da Baba tin daga sallamar sa Baba ya gane ba lafiya ba. Durkusawa yayi ya gaishe su sannan ya mike ya nufi dakin Aisha. Umma ce tace
“Ga pepper soup din nata fa.”

Juyowa yayi dauki flask din ya nufi dakin nata ba tare da yai magana ba.
Tana cikin bargo ya shiga da sallama da kyar ta amsa masa saboda yadda kan ta yake ciwo. Zama yayi a gefen katifar ya yaye bargon yana kallon ta cikin so da tausayi. Hannun sa ya kai ya dafa kanta yaji zafi sosai har jikin ta.
“Kinci abinci?”

Kai ta girgiza sai hawaye ya fara bin fuskar ta. Dagota yayi ya zaunar yasa hannu ya fara goge mata hawayen yace
“Menene na kukan to Aisha? Ko jikin ne?”

Baki ta tabe masa zatayi kuka yace
“No don’t cry please kinji Aisha!”
Ya dauko Flask din ya fara bata pepper soup din. Nama daya taci ta kautar da kanta. furar ya bude ya dauki spoon ya fara bata tana sha tana masa shagwaba sai biye mata yake har tasha rabi sannan ya ballo magani ya bata da kyar ta sha sai da ya bari ya tsarga mata sannan ya maidata ya kwantar ya ja mata bargon ya mike ya fita. Yana fita bacci ya dauke ta da tunanin Yaa AK.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *