WA NAKE SO CHAPTER 16

 WA NAKE SO CHAPTER 16

Www.bankinhausanovels.com.ng 

Yana shiga daki ya zauna a bakin katifar sa yana mai rike kan sa. Tausayin Aisha na kara ratsa zuciya da dukkan jikin sa. Hakika bai taba kawo wannan ranar a ran sa ba wacce zai iya cire son Aisha a ransa amman dole ya daure yayi haka ko  dan yin biyayya ga Umma sannan ko dan samuwar farin cikin Aisha.+

Yana son Aisha har bai son adadi ba lallai zai mata abinda take so ko ta samu sauki a ranta. Yana zaune Umma ta shigo rike da kwanon abincin sa. dagowa yayi ya kalle ta. ta ajiye tace

“Ban fada maka wannan maganar dan kaima ka sa damuwa a ranka ba,  na fada maka wannan maganar dana warware wannan matsalar ina fatan ka gane.”

Kai ya gyada yace

“Insha Allahu komai zai warware Ummah na.”

“Allah maka albarka ka ci abincin sai da safe!”

Ta juya ta fita. abincin ya dauka zai ci sai yaji ina ba zai iya ba taya zai iya cin abinci zai rabu da masoyiyar sa. Dukka tsarin sa da komai akan Aisha yayi su yanzun komai zai tarwatse masa kenan.

Alwala yayo ya kwanta amman sam ya kasa runtsawa tunanin Aisha ya gama cika masa zuciya da ruhin sa can wajen sha biyu ya mike ya dauro alwala yazo ya tada sallah ya jima yana sallah sannan ya fara karatun alkur’ani wanda ya sa ya fara jin sauki da nutsuwa a cikin ransa.

Har asuba idon sa biyu sai da yayi sallah asuba sannan ya dawo take bacci ya dauke shi mai nauyi kuwa.

*

*

*

Sosa jikin Aliyu ya tashi dan likitoci kansu sai da ya dau caji da kyar suka samu numfashin sa ya dawo sukai masa allura sannan yankoma bacci yana mai fadi

“Aysher!”

Sosai jikin yan uwan sa yai sanyi da ganin halin da yake. Abbah yana dakin da Mamah take sai lallashin ta yake. Sai da taji ance Aliyu na bacci sannan ta samu nutsuwa.

Tare suka je ta gansa sannan tai tayi masa addu’a tana tofa masa.ita kanta Hajara sai da Aliyu yai matukar bata tausayi yadda ta ganshi kwance sanye da oxygen dan har da hawayen ta. Haka suka kare zaman asibitin ranar sai wajen sha biyub dare suja tafi gida.

*

Washe gari da safe.

Zaune suke a falon dakin. Aliyu na ciki har lokacin yana bacci dan da ya farka suke karai masa allurai sai ruwa dake ta shiga jikin sa Maryama da Hajara na cikin dakin a wajen sa.

A falon kuma Abba ne da Mamah sai Yaa Abubakar,  Yaa Usman,  Umar,  Farouk,  Faisal sai Doctor dake duba sa. Bayan Doctor ya gamai musu bayanin duk abinda yake akwai ne ya mike yace

“You have to do your best to find out what he want or don’t want. I wish you all the best and Quick recovery to him “

Yana kaiwa nan ya fita. Shiru dakin yayi kowa akwai abunda yake sakawa can Yaa Abubakar yace

“Na tsorata jiya domin Aliyu har wasiyya ya fara barmin yadda naga jikin sa ya tashi yasa na fara zaton da gaske mutuwar zaiyi shiyasa ya bar min wasiyya amman abinda yafi dauren kai a wasiyar tasa yadda yake nananta min akan na tsayawa wata yarinya a harkar karatun ta. Shin wacece wannan yarinyar shine abinda nake so na sani.”

Shiru sukai. Faisal ne ya sauke ajiyar zuciya sannan yace

“Ban san me zai damuwa Aliyu ba har da zai kawo masa wannan ciwon amman ina zaton akan Aisha ne!”

STORY CONTINUES BELOW

Yaa Abubakar yace

“Yauwah sunan yarinyar da ya fada min jiya. Did you know something?”

Kai ya gyada yace

“Da jimawa mun hadu dashi a saudiyya tin bayan da muka gama secobdary school sai ta waya ko chat muke haduwa amman face to face bama haduwa tin a school ni nake iya rayuwa da AK. To zuwan sa saudiyya mun hadu wanda anan ne yake bani labarin Aisha shima bai fito ya fada min ba da farko ya nunan yana son ya koma gida nace yana missing family ne yace a’ah sister sa. The way yake fadan yadda yake missing nata na gane ba sister sa bace uwa daya uba daya wanda yadda yake fadar abu akan ta da kaji zaka san akwai soyayya da kyar Aliyu ya fada min ko wacece ita.

Ya hadu da ita a garin da yake yanzu wanda haduwar su Allah ne ya hada su kuma yarinya ce karama amman tana da kaifin basira da ilimi sosai ta canjawa Aliyu tunani da tsarin sa. Zan iya cewa ita ce babbar mai bawa gwamna shawara duk da bata san shine gwamna ba.”

“Kamar ya?”

“Yaje mata as a sibling to governor.”

Nan ya basu labarin akan haduwar tasu kamar yadda Aliyu ya tsokata mishi kadan daga labarin nasu.

“AK ya kasa bayyana mata wanda da kyar nayi convicing nasa ya fada mata amman fa bai fada mata ba. A haka ya cigaba da dawainiyya da soyayyar ta,  ganin ba zai fada mata ba yasa na bashi shawara akan ya fara nuna mata so da kulawar sa wanda har ya bayyana mata yana son ta amman sai ta fada masa tana da wanda zata aura wanda wannan ya zama kamar yaya a gunta dan cousin nata ne kuma ita ba zata iya cewa ba zata aure shi ba. But a yadda na fuskanta lallai Aisha na son Aliyu kawai dai ba zata iya kin auren dan uwan nata bane.”

“Wacece Aisha?”

Abbah ya fada. Mamah tace

“Tabbas ita ce.”

“Ita wa?”

“Ita ce wacce tazo a ranar da muka baro garin.”

Mikewa yayi ya kalli Yaa Abubakar yace

“Ka samar min jirgi mai tashi a yau.”

Sannan ya fita a dakin. Fita Yaa Abubakar yayi dan samar masa jirgin. Mikewa Mamah tayi tabi bayan Abbah.

Tana fita taga zai shiga mota da sauri ta karasa ta shiga suka koma gida. A falo ya zauna ta zauna a gefen  sa tace

“Ya dai Alhaji?”

“Kinsan tin ranar na lura da ganin ta da Aliyu yayi ba karamin kwanciyar hankali da jin dadi ya saukar masa ba. Kuma kiga yadda yake damun mu akan yaushe zata zo yana son ya ganta. Kuma kina jin yadda yarinyar ta canja rayuwar Aliyu lokaci guda da kuma irin mahimmancin da take da shi a rayuwarsa. Sannan ni kaina jiya naji duk wayar da sukai da abubuwan da ya fadawa Faisal. A da Aliyu bai san so ba kuma bai san yaga mace yaji wani abu game da ita ba dan ni nasan waye shi na tambaye shi zabin sa kan nai masa aure ya bani zafi dan bai da zabi akan mace yau Allah ya nuna min zabin Aliyu Alhamdulillah.”

Ya kalle Mamah ya ce,

“Wannan yana nufin Aisha ita ce samuwar lafiyar sa da farin cikin sa. Dan haka ba abinda zamuyi masa sai mu aura masa yarinyar nan, saboda ya na da matukar mahimmanci Aliyu ya cigaba da rayuwa domin karasa abinda ya fara ina son ganin iyayen yarinyar nan”

Umma ta girgiza kai ta ce,

“Alhaji yarinyar da an mata miji a yadda mukaji labari an kusa musu aure kuma itama ta fadawa Aliyun haka”

   

Abbah Ya kalle Mama yace,

“Wani miji ne da ya fi Aliyu,  duk wanda ya samu Aliyu a matsayin miji ya dace yaro ne mai ilimi da amfani dashi ga tarbiyya. Babu wanda zai ki Aliyi babu wanda zai ki gwamna,  babu wanda zai fi gwamna dan sarki ? Kuma ba zata taba samun miji mai son ta kamar Aliyu ba mutum da ya fi son farin cikin ta akan nasa,  mutumin da ya yadda ya mutu ita ta rayu,  mutumin da ya sadaukar da rayuwar sa akan ta,  mutumin da ya bata lokacin sa,  kulawar sa,  soyayyar sa wanda bai duba matsayin sa da mulkin sa ba. Hakika Aliyu ya fi cancanta da Aisha.”

   

Numfashi Abbah yaja sannan ya kalle ta ya ce,

“Abinda Aliyu yake so zai samu ko aure aka daura mata za a warware shi bare kuma ba a daura mata aure ba”

Dogowa Mamah tayi ta kalle sa cikin fuskar damuwa ta ce,

“Ranka ya dade ban san ka da haka ba, na san ka da adalci da tausayi kar son danka ya makantar da kai, mu bi abin nan a hankali. Sannan shi kansa Aliyu bai son abinda zai taba ran yarinyar nan”

STORY CONTINUES BELOW

Ya kalle ta yace,

“Haka ne Fulani ni sarki ne mai adalci kuma zanyi bakin kokari na wajen ganin anyi adalci kuma adalcin  kenan da zan mata ta auri miji irin Aliyu burin ko wace mace a duniya ta samu mijin da zai mallaka mata komai, kima, daraja, dukiya, daukaka, so da kulawa,  tausayawa komai za ta same sa a karkashin inuwar Aliyu me ya fi wannan ? Bayan kinji ance itama tana son sa. Ba Aliyu kadai zan wa adalci ba zan yiwa ita kanta yarinyar adalci dan ta samu cikar burin ta da nutsuwar ta zanyiwa Shi wanda zata aura adalci dan na takaita masa wahalar da zai sha bayan ya auri wacce take son wanin sa,  sannan zan takaitawa iyayen ta wahala akan fuskantar damuwa da zasu fuskanta a tsakanin ya’yan nasa a karshe zan yiwa d’a ba adalci dan ya samu mace mai ilini da tarbiyya wacce zata zama mai masa jagora ga aljanna Sannan ina son jika na dan Aliyu ya fito daga tsatson yarinyar nan. meyafi wannan adalaci Fulani?”

Kai Mamah ta gyada kawai dan ta kasa magana ma. Mai gidan nata yana da gaskiya kuma tasan ba zai abinda ba dai dai ba shi sarki ne adali. Ta yadda take godiya ga Allah kenan dukiyar su ko mukamin su bai sa sun canja daga yadda suke wajen riko da addini,  tausayi da adalci ba.

Abbah yace,

“Tinda yake bawa Faisal labari nasan yarinyar ba banza ba domin duk Yarinyar da Aliyu ya gani ya yaba har ma ta birge shi, har ma ta iya canja masa rayuwa da tunani lokaci guda,  har ta iya jefa shi a wannan hali saboda rashin ta ba karamar mai baiwai ba ce. Dole akwai wani abu, wata baiwa da Ubangiji ya mata wanda zan so hada zuriya da ita, jininta da na Aliyu zai haifar da wani abu mai daraja. Ya kike gani Fulani.”

Ita dai Mamah jin sa take kawai tana tunanin kar aje iyayen yarinyar suki yadda fa. Tasan Mai martaba zai iya komai dan samuwar yarinyar nan ga dan sa amman kar aje ayi ta wata hanya da bata dace ba. Kamar yadda take son Aliyu haka take ji wata soyayyar Aisha aranta sosai. Dan haka a zuciya take addu’a tana fadin

“Ya Allah ka gyara wannan al’amari ka tsira da wannan yarinya daga fadawa halaka ka zaba mata abun da yafi alheri, Allah ka tabbatar da alkhairi a rayuwarta.”

   

Wayar Abba ce ta dau kara ya zaro yaga Abubakar ne dauka yayi. Yaa Abubakar yace

“Abbah kana ina?”

“Ina gida!”

“Ok an samu nan da thirty minute zai tashi amman a Abuja zai sauka.”

“Ok gani nan bari na karaso.”

“To!”

Ya kashe wayar ya kalli Mamah yace

“Lafiya Fulani ta?”

“Ranka ya dade ina tsoro ne!”

“Tsoron me Rashida? Dan Allah kada ki karyar min da gwiwa mana ki bani kwarin gwiwa yadda zanje na gudanar da abun zai kai ni ki min addu’a.”

“Allah bada sa’a.”

“Aliyu Fulani na. Zan tafi airport zaki rakani ko zaki koma asibitin.”

“Muje na raka ka sai na koma asibitin.”

Suka fita suna zuwa airport din basuyi minti goma ba su Abbah su Abbah suka fara harama. Da zai tafi ya dafata yace

“Ina bukatar addu”ar ki Fulani.”

“Allah tsare ya bada sa’a!”

“Amin nagode sai kinji ni.”

“Ayi adalci ya sarkin mai adalci da tausayi da son talakawa.”

Juyowa yayi yace

“Insha Allah!”

Juyawa sukai suka tafi asibitin. Aliyu yana kwance tamkar gawa ba abinda yake motsi a jikin sa sai ta jikin computer da suke ganin yadda numfashin sa ke tafiya.

*

Tin kan su tashi ya fadawa President cewar gashi nan sauka a garin sa. Wannan yasa kan ya sauka an turo tawagar masu tarbar sa da bashi tsaro. Bagare guda aka sauki Mai martaba.

Wanka kawai yayi bai bi takan abinci ba ya dauki wayar sa ya kira mr president yana dauka yace

“Kazo yanzu please.”

Ya kashe waya.

Mamah ya kira yace

“Fulani na sauka lafiya.”

“Alhamdulillab kaci abinci?”

“Ba zan iya ciba har sai na cikawa Aliyu burin sa. “

“Haba Alhaji Ranka ya dade. Dan Allah ka daure kaci.”

“Wallahi ba zan ita ba.  Ya jikin nashi ya tashi?”

“A’ah har yanzu dai nima dazu nai musu magana suka ce ba matsala baccin ake so yayi da yawa.”

“To Allah bashi lafiya ki cigaba da min addu’ar sa’a.”

“Allah bada sa’a.”

“Amin!”

Ya kashe wayar.

Ba ai minti biyar da gama wayar sa da Mr president ba ya shigo dakin da sallama amsawa Mai martaba yayi. Mr president yace

“Ai na barka ka ne ka huta ka dan samu nutsuwa sai in shigo.”

“Kasan ba zuwan dadi nayi ba.”

“Haka ne ya jikin Aliyun?”

“Da sauki Zuwan kenan daman.”

Kallon dining Mr president yayi yace

“Baka ci komai ba ai Alhaji Kabir!”

“Sam bana jin yunwa Alhaji Ahmad abinda ya kawoni nake so naje na aikata kawai.”

“Me ya kawo ka?”

“Akan danka ne Aliyu game da rasbin lafiyar sa.”

Nan ya fadawa Mr president komai a takaice sannan yace

“Yanzu haka zanje nemar masa auren yarinyar ne ina fatan za a dace”

“Haba Alhaji Kabir menene zaka tashi hankalin ka yar wacece ita yarinyar?”

“Ba yar kowa bace mahaifin ta mai rufin asiri ne.”

“Shine ka tashi hankalin ka. Ka kwantar da hankalin ka ko a yanzu kake son a daura auren zan iya sawa a dauko ubanta a daura musu auren.”

Murnushi Mai martaba yayi yace

“Nima ina da wannan ikon Alhaji Kabir amman ka sani mu muke nema dole mubi komai a sannu kuna aure zamu hada ba wani abu ba muna neman saka albarka da yin abu a mutunce.”

Shiru Mr president yayi. Mai martaba ya mike shima ya mike yace

“A gaskiya ban taba haduwa da mutane irin ku ba Alhaji Kabir Allah ya baku dukiya mulki da iko amman sam basa gaban ku komai kuna ui saffa saffa. Zamana da Aliyu ba karu da abubuwa da yawa kamar tsoron Alah gaskiya da rashin cin amana kuma na gane wannan gado yayi daga wajen ka. Ka sani dani za’aje nemarwa Aliyu aure ko a ina ne kuma zan tsaya masa da dukiya ta da komai nawa.”

Rumgume shi Mai martaba yayi yace

godiya nake.”

“Amman ai ya kamata kaci wani abu ko?”

“Bazan iya ba.”

“Haba a samo maka ko soft abu mana.”

“Muje kawai Alhaji Ahmad.”

Ba yadda Mr President yayi haka suka fita yasa aka dauko private jet nan suka hau sai garin su Aisha. Security na buye dasu wasu a kita suka mara musu baya wasu kuma na tare dasu.

A gidan gwamnati suka suka basu tsaya sanya ba suka bawa PA bayanan abinda suke nema nan da nan ya fita ya nemo musu address din gidan su Aisha. Ba bata lokaci Mr President,  Mai martaba da PA suka dauki hanyar gidan su Aishan.
*
*
*
Tana kwance a dakin ta,  ta kira wayar sa tafi sau nawa bai dauka ba. Mikewa tayi ta cire kayan ta,  ta daura towel sanna ta saka hijab babba ta fita ta shiga bandaki dan Ummah ta hada nata ruwan wanka.. Tana shiga Yaa Muhammad ya fito daga dakin sa sanye da manyan kaga a jikin sa milk shadda kansa ba hula. Dan ranar friday ce. Dakin ta ya nufa yai sallama yaji shiru kawai ya shiga.
Bata dakin dan haka ya tsaya yana bin dakin da kallo zama yayi a gefen katifar ta wayar ta dake kan katifar ya gani ya dauka yana juyawa ya bude ta yana danne danne call log ya shiga sai yaga *Yaa AK* ne last call din da aka kira but ta saka not connected. Ta kira yafi sau ashirin ajiye wayar yayi zuciyar sa na bugawa da karfi da karfi. Can kuma sai ya dauki wayar ya shiga inbox.
Sunan Yaa AK ne a duk list of message din da aka turo shiga yayi yana bi yana karantawa yadda yaje karantawa daga jikin sa gar zuciyar sa rawa suke dan tsabar kidimewa. Kuma ya kasa ajiyewa. Sakonni ne tun wandan ya fara turo mata da wanda yake nuna kulawar sa da soyayyar sa da wanda akai na kwanaki akan tana da wanda take so.
Wayar ya ajiye ba tare da ya fita daga inbox din ba sai kuma ya dauja ya shiga sent message auma duk Yaa AK aka kmturawa. Karanatawa yahi yankoma yana compairig nasu da wanda ya turi ya je kan wani na Yaa AK kawai ya ajiye wayar ba tare da yakarasa karantawa.
Da sallama ta shigo dakin kan ya amsa ta shiga a tsorace ta dafe zuciya dan ba tai zaton ganin kowa a dakin ba. Duk da yana cikin wani hali sai da ya saki murmsuhi ya mikeya na fadin
“Matsoraciyya.”
Baki ta turo ta karaso cikin dakin ta zauna tace
“Kai Yaya na ba dole ba ka bani tsoro ban fa san ka shigo ba.”
“To sorry na shigo naga bakya nan shine na zauna jiran ki.”
“Wanka nayi?”
“Ya jikin?”
Baki ta turo tace
“Sai yanzu kazo dubani bana so. Kana can kana baccin ka baka san ya nake ba ko?”
“Haba Kanwata kema kinsan kina raina jiya banyi bacci bane sai dazu shiyasa.”
“Me ya hanaka yin bacci?”
“Tunanin kanwata.”
“Haba dai menene na tunani na bayan ni takace ai da kazo kai ta kallo na har baccin yazo kaga ba wani tunani gani gaka ko?”
“Hmmm Aisha kenan.”
Ya fada yana murmushi. Baki ta kara turowa tace
“Me nayi?”
“Shirme mana!”
Fuska ta kwabe kamar zatai kuka tace
“Shirme Yayana na fadamaka abinda zaka ji dadi fa.”
“Haka ne naji dadin to.”
Murmushi ta saki tace
“Naji dadi Yaya na yayi farin ciki.”
Sai ta dan bata fuska ta dago ta kalle shi idon ta na kawo kwala. Ya kalle ta yace
“Menene jikin ne?”
Kai ta gyada tace
“Kai nane kuma.kasan me?”
Kai ya girgiza gace
“Yayana gabana sai faduwa yake kuma sai naji ina jin rsoro.”
STORY CONTINUES BELOW
“Kiyi ta addu’a insha Allahu Alherri ke tunkaro ki.”
“Allah yasa to”
“Amin! Mekika ci?”
“Na kasa shan tea din nace koko nake so shima Umma tayo min kaganshi can ka dauka kasha.”
“Ke kuma me zakici?”
“Ni ban sani ba.”
Kokon ya dauka ya sha ya mika mata yace
“Kema kisja!”
Ka fada ta make yace
“To bari na samo miki wani abu.”
“Nagode!”
Ya mike ya fita. Umma ya gaisar ya fita a gidan gaba daya.
Dankali ya siyo mata da plaintain da kwai ya taho zai shiga gida ya samu motoci guda biyar a kofar gidan nasu. Karasawa yayi PA ya karaso ya mika masa hannu suka gaisa yace
“Muna neman Malam Abubakar!”
“Lafiya dai?”
“Lafiya lou baki yayi ne.”
“Yana kasuwa!”
“To dan Alah zaka iyai min iso!”
“Ba matsala bari na shiga na fito sai na rakaka!”
Ya nufi cikin gidan. A daki ya same ta har ta saka kaya tana kwance. Yana shiga ta mike ya mika mata ledar yace
“Dan Allah kici bari naje na dawo.”
Ya ajiye ya juya ya kai bakin kofa tace
“Yaya ina son maltina!”
“Ok zan taho miki da ita.”
Ya fita ya koma PA ya dauke sa a mota sai kasuwa. Suna zuwa Baba ya gane PA dan haka ya taso yana fadin
“Barka da zuwa.”
PA ya gaishe shi cikin girmamawa sannan yace
“Daman baki akayo suna gida sun zo wajen ka.”
“Ina fatan dai lafiya?”
“Alhamdulillah lafiya lou.”
“To shikenan bari na taho.”
Yaa Muhamad ne ya dawo dauke da katon din maltina wannan yasa suka nufi gida.  Suna zuwa Baba yasa aka shmfidda tabarma a soro sannan yayi musu iso kan su karaso.
Sosai Baba yayi mamakin ganin manyan mutane duk da bai san mai marhaba amman da ka gansa kaga babban mutum sai shugaban kasa da suke gani a television da poster amman yau shine a gaban sa sai yaji wani faduwar gaba to me yake fauwa me akayi wadan nan manyan mutanen ke neman sa.
Suna zama PA ya mike haka ma Yaa Muhammad da ya fito daga cikin gida ya kaiwa Aisha maltina ya gaishe su zai fita Mai martaba yace
“Ku zauna ayi a gaban ku.”
Kallon Mr president Yaa Muhammad yake da mamaki da alajabi dan shi gani yake anya shine ma. Zama yayi a gefen Baba.
Mr President ne yayi gyaran murya yace
“Kamar yadda kuka sani sunana Alhaji Ahmad Yahya shugaban kasar nan wannan aboki nane Sarkin Kano Alhaki Kabir Ahmad! Ban fada muku mu su waye ba dan son a sani sai dan yana da kyau mu fada kafin mu fara maganar da ta kawo mu muna fatan babu matsala.”
Baba jiki a sanyaye yace
“Babu insha Allahu!”
Mr president yace
“……………..”
*
**
***
****
*****
******
Tana shiga ta ajiye kayan hannun ta anan parlour. Daki ta shiga tai brush tai alwala tayi sallah tana idarwa ta dawo parlour anan ta samu Momy ta zauna a kasa tana fadin
“Momy ya gida?”
“Alhamduliah! Yaushe kika shigo banji motar ki ba.”
“Wallahi tana asibiti fita mukai ni da Uncle ne…”
Sai kuma tayi shiru kawai.
“Waye Uncle?”
“Uhmm uhm daman wannan dan uwan su..”
Ta rasa yadda ma zata fada. Murmushi Momy tayi tace
“Dan uwan su wa?”
“Ina gidan da mukaje da Hajiyar Fu’ad?”
“Eh!”
“To dan gidan ne!”
“A ina kuka hadu?”
“Momy wata rana zan je asibiti na buge masa mota tin daga lokacin muka hadu yana zuwa kuma asibiti in bai da lafiya haka ya kawo matar sa ranan ma.”
STORY CONTINUES BELOW
“Ina kuka je yau!”
“Wani waje na rakasa.”
“Saboda me to?”
“Ni dai yace dan Allah na rakashi ne!”
“Ko dai saurayin kine?”
Ido ta zaro tace
“Kai Momy a’ah ni.”
“To kije kici abincin!”
Jan ledar tayi tace
“Ga takeaway ya min!”
“Wanda nai miki fa?”
“Shima zanci.”
“Kamar gaske!”
Tayi murmushi. Tare suka ci da Momy dan wanda Momy tai mata sai afirij ta saka su.
Sai goma ta shiga daki ta fara cire kaya tai wanka sannan ta dauro alwala tana saka kayan bacci wayar ta ta hau kara karasawa tayi ta dauka tana ganin bakuwar number. Receive ta danna sannan ta kara akunne
“Barka da dare Doctor da Fatan kinsha ruwa lafiya?”
Ajiyar zuciya ta saki jin muryar sa. Tace
“Alhamdulillah ya ka koma gida nagode sosai Allah saka da alheri agaishe da Madam!”
“Zata ji. Amman baki kwanta ba.”
“Yanzu zan kwanta.”
“Masha Allah sai da safe swt dreams!”
“Thank you same!”
Ta kashe wayar tana daukar irin turaren Fu’ad ta shashana sannan ta dan shafa a jikin ta ido ta lumshe ta ajiye sannan ta hau gado tana bismillah kwanciyya tayi taja pillow daya ta rumgume a jikin ta. Hannu ta saka ta kashe fitilar dakin ta fara addu’a. Ido ta rufe take bacci mai dadi ya dauke ta.
*
Washe gari da safe ita tayi komai na gidan sannan ta koma dakin ta tai wanka ta fito ta shirya ciki riga da siket na atamfa tai kyau. Purple kalar hijab ta daura yai mata kyau sosai. A falo ta samu Momy har kasa ta durkusa ta gaishe ta. Tea ta hada tasha da dan bread da kwai sannan ta yiwa Momy sallama ta tafi. Driver ne ya kai ta dan motar a asibiti ta kwana.
Tana cikin bude kofar office din ta wayar ta tai ‘kara dauka tayi duk da batasan number
“Assalamu Alaikum!”
Ya fada.
“Wa’ailkum salam Uncle ashe kai ne ka tashi lafiya?”
“Au baki saving number ta ba.”
Murmushi tayi yace
“Kace bakya Yayan dani ko?”
“A’ah!”
“To kiyi saving.”
“Insha Allah!”
“Kin tashi lafiya?”
“Alhamdulillah ya madam?”
“Tana lafiya!”
“Masha Allah.”
Ta shiga ta ajiye jaka yace
“Kin karasa asibiti ne?”
“I just arrive!”
“Ko nazo mu gaisa ne?”
“Haba dai ka tafi aikin ka kada ka makara!”
“Kuma fa haka ne in na taso zan iya zuwa!”
“Wannan ba matsala!”
“Godiya nake!”
“Sai anjima!”
Ta kashe wayar. Zama tayi tana duba files din gaban ta.
4:50pm ya shigo asibitin parking motar sa yayi ya fito gaisawa yayi da wasu staff din dan har sun fara ganeshi ya nufi office din nata ba shamaki yai kbocking ta amsa sannan ya shigo da sallama a bakin sa. Kanta na kan system tana aiki ta amsa. Kallon ta ya tsaya yi tayi masa kyau da hijab sosai abinda Jiddah bata sawa kenan in ba sallah zatai ba.
Jin bata karajin motsin sa ba yasa ta dago tsaye ta ganshi bakin kofa tace
“Ka karaso mana.”
Murmushi ya saki yace
“To Yasayada!”
Gira ta daga dan neman karin bayani ya nuna ta da yatsa. Murmushi ta saki tana fadin
“Hmmm!”
“Kinyi kyau dashi sosai! Ina son Hijab. Mata ne basu gane ba amman Hijab yana musu kyau sosai!”
Da sauri ta dago dan statement din Yaa Fauwaz kenan in ta saka hijab ya ta koda ta.
Kai ya daga mata alamar menene ta sauke kan ta kawai tana cigaba da dannan system. Sai kuma ta bude baki kamar ba zatai magana ba tace
“Ina yini?”
“Lafiya ya kike ya aiki?”
“Alhamdulillah! Ya naka?”
“Same!”
“Masha Allah.”
“Aikin me kike ne?”
“Wani sako aka turon nake maida reply ne!”
“Ok!”
Gamawa tayi ta kalle shi yace
“Ko zamu dan fita?”
Agogo ta kalla ta girgixa kai tace
“Yamma tayi!”
“Just thirty minute Dr yana da kyau kina samun time din ki kina dan hutawa da shakatawa.”
Tabbas ita macece mai son haka amman rashin Fu’ad duk komai ya fita a ranta. Shiru tayi yace
“Minti talatin kawai zan dawo dake!”
“Shikenan!”
Ya mike ta mike ta dauki jakar ta sannan ta bi bayan sa. Mota ya bude mata ta shiga wani resturant mai kyau ya kai ta. Shiga sukai suka zauna. Ice cream yasa aka kawo masu da gasasshiyar kaza.
Suna zaune aka kawo ya dauki nasa ya fara sha. Kallon sa tayi sai tayi kasa da kai
“Menene?”
“Ina son sanin wani abu akan ka?”
Murmushi yayi yace
“To bismillah!”
Kai ta girgiza ya bqta fuska yace
“Ba kyau mai da hannun kyauta baya please!”
Ja tayi tai spoon daya ta ajiye yace
“Sunana Ahmad Yahya Ahmad amman da Aslam ake kira na saboda naci sunan kakana mahaifin baba na kenan. Nine auta a gidan mu kuma ni kadai ne namiji. Mahaifi na dan boko ne kuma dan kasuwa dan siyasa kuma dai. Ya rike mukamai masu yawa daga a siyasar har a aikin sa Yana da kudi da rufin asiri wanda yanzu ni nake kula da duk companies din sa. Matata daya Jidda bani da ya’ya kin sani sai yayye na mata guda shida Noor da Jannah ya’yan yata ne ta hudu!”
Ya fada yana tafa hannu yace
“Shikenan ko akwai wani abu da kike so kiji?”
Kai ta girgiza ta kalli agogo taga shida saura tace
“Zan tafi.”
“Ai bakici komai ba.”
Kai ta girgiiza ya kira aka musu parkaging kayan ya biya sannan suka fita. Asibiti suka koma ta dauki motar ta ya saka mata ledar sannan ya rufe ya juya ya shiga tashi. Yana gaba tana bin sa a baya har suka hau titi sai da zasu rabu yai horn ya daga mata hannu itama ta mai da masa.
*
10:00pm tana kwance akan gadon ta bayan tai addu’a har ya fara bacci taji wayar ta na kara hannu ta saka ta dauka ta kai kunnen ta
“Kanwata ya kike ya dare?”+
“Alhamdulillah!”
“Gud just call to say gud nyt!”
“Thank you!”
“You are welcome gud nyt!”
“Have a sweet dreams!”
Ta kashe wayar.
*
*
*
Washe gari
9:00 am zata fita tayi round kenan ya kira ta. Dauka tayi tace
“Morning Uncle ya aiki?”
“Alhamdulillah and yours?”
“Same!”
“Gud Allah taimaka!”
“Amin thanks!”
“Never mind daman na kira naji ya kika tashi ne?”
“Alhadulillah nagode sosai.”
“Aha bye!”
*
5:00pm sauri take tana hada jakar ta dan zata shiga tayi siyayya ta tafi gida tana isa bakin kofa aka budo kofar kallon ta ya tsaya yi tana sanye da hijab har kasa Ash kala.
“Wow beauty!”
Ya fada yana shigowa. Kallon sa tayi ta dan saki murmushi tace
“Ina yini?”
“Lafiya lou Dr kinyi kyau wallahi kallan ya amshe ki!”
“Ko nagode!”
“Ina zakije ne?”
“Wallahi ina son na shiga sahad ne nayi siyayya!”
“Amman ba neman rakiya.”
Murmushi tayi yace
“Muje to!”
Fita tai ya biyo bayan ta. Motar ta ta nufa ta shiga shima ya shiga tashi tana fita ya bi bayanta har suka karasa sahad tana parking shima yayi ya fito tare suka shiga ciki amman kowa yayi gun da zai siyayyar sa.
Gun perfurms ta fara zuwa ta jidi wanda take so sannan ta karasa wajen man da take shafawa ta dauka ta dauki na kitson ta. Gun sanitary pad ta karasa ta dauki ledar kenan taji yace
“Har yanzu baki gama ba?”
Da sauri ta maida ta juyo tace
“Eh!”
Ta bar wajen murmushi yayi ya dauki sanitary pad ya saka a basket din sa ya nufi counter din. Total akai masa ya biya ya tsaya jiran ta.
Daga nan gun wajen sweet and bisket ta tsaya ta zaba ta saka a basket ta karaso tana zuwa ya matso kusa da ita yana fadin
“Ya dazu kika bace min.”
Murmushi kawai tayi kudin aka dada kan Fateema ta bayar ya mika ATM card din sa zatai magana yace
“Please sorry!”
Shiru tayi aka diba suka fito gun motar ya ta shiga ta saka kayan ya karasa ya saka na hannun sa sannan yace
“Ina zuwa!”
Gun sai da ice cream ya isa ya siyo leda biyu sannan ya dawo. Leda daya ya dauka a wacce ya ajiye ya bar mata daya sannan ya ajiye mata ledar ice cream daya a cikin motar yace
“To anan zamuyi sallama ko”
Kai ta gyada yace
“Ok bye ki gaida Momy!”
“Nagode!”
Ta fada juyawa yayi ya shiga motar sa tana tsaye ya fito yace
“Lafiya?”
Kai kawai ta girgiza ta shiga tata motar ta tayar suka fice a tare.
A falo ta zube kayan bayan ta shigo sun gaisa da Momy ledar da ya saka mata ta dauko ta bude pad din da ta ajiye ce a ciki kai ta girgiza ta bude ledar taga wasu Hijab ne a ciki masu masifar kyau guda uku. Budewa tayi Momy ta fito tana fadin
“Kai amman Hijab din nan yai kyau nawa kuma?”
STORY CONTINUES BELOW
“Ni bani na siya ba.”
Kallon ta Momy ta tsaya yi tace
“Kamar ya nawaye to?”
Shiru tayi can tace
“Uncle ne ya siya min fa.”
“Amman sunyi kyau angode.”
“Ki dauki daya!”
“A’ah a’ah ke ya siyawa ban dauka.”
“Dan Allah Momy.”
“Allah ban dauka ki siyon dai irin sa.”
“To shikenan!”
Ta kwashe kayan na Momy ta kai mata daki nata kuma ta ajiye anan falon.
As usual 10:00pm tana zaune yau tana karasa kallon wani film da ta fara gani a bollywood kira ya shigo wayar ta tana dubawa taga Uncle dauka tayi da sallama yace
“Ya kika koma gida?”
“Alhamdulillah Uncle and u?”
“Same yau ya naji ki da karfin ki.”
“Ban kwanta bane!”
“Me kika tsaya yi?”
“Kallo!”
“Which channel?”
“Bollywood!”
“Ok let me join you!”
Ya canja channel ya fara kalla yace
“Yana da kyau ne?”
“Eh ba laifi!”
“Ok bari na kalla sai anjima zan kira ki in an gama.”
“Alright!”
Ta kashe wayar tana kallo. Bayan thirty minute ne tana cikin kallo taga yayi hugging din ta yana kissing din ta ido ta rufe da sauri take ta tuna tare suke kalla da Aslam wata kunya taji ta kamata wanda duk taji wani iri kuma ta tsargu haka suka dinga abubuwa daga baya mikewa ma tayi ta kashe kayan kallon tayi dakin ta.
Ruwa ta watsa ta saka kayan bacci sannan ta kwanta bata jima da kwanciyya ba taji yana kiran wayar ta kin dauka tayi dan ita duk kunya ya ishe ta akan abinda akai a film din haka ya kira sau biyu bata dauka ba ya barta kawai.
Washe gari tana mota zata asibiti taji wayar ta na kara a handfree ta saka tayi sallama ya amsa yana fadin
“Kin tashi lafiya?”
“Alhamdulillah ya gida da Madam?”
“Tana lafiya shine jiya ina kira baki dauka ba.”
“Ayyah ai bacci nayi muna gama waya na kashe na tafi na kwanta!”
“Da gaske?”
“Eh!”
“Amman film din yayi kyau gaskiya ki nema ki karasa kallon sa love story din nasu me dadi.”
“Ko?”
“Eh!”
“Ya aiki?”
Ta bagarar da maganar.
“Yanzu zan karasa.”
“Ok Allah kiyaye hanya.”
“Amin nagode!”
Ta kashe wayar.
Da yamma ma asibitin yazo duk da ba fita sukai ba amman tare suka kare zaman asibitin ita tana aiki a system shi kuma yana danna wayar sa ko yai answering call har time din tashin ta yayi tare suka fito a parking space suka tsaya. Ta kalle shi tace
“To nagode fa sai gobe?”
“Eh gobe zaki shigo ne?”
Kai ta girgiza tace
“Gaskiya a’ah zan huta kuma dis weekend!”
“Kace zanyi missing naki in naji na kasa jurewa zan zo mu gaisa.”
Tai murmushi kawai ta shiga mota har ya shiga ya fito ya leka ta window din ta. Kallon sa tayi tace
“Menene?”
“Nothing! Bye!”
Ya daga mata hannu kallo ta bisa dashi har ya shiga motar ya tayar ya fita. Murmushi kawai tayi ta girgiza kai ta dauki hanya itama. Tana cikin tafiya tazo kwanar da take dauka ta tafi gidan Fu’ad. Kai ta girgiza kawai dan ta jima ma bata leka ba.
*
*
*
Ranar asabar bayan tayi sallar asuba tayi azkhar mikewa tayi ta fara gyaran dakin ta, su wardrobe komai sai da tai masa gyara na tsanake dan ranar karamin sanitation tayi ta gyara kayan ta da dakin ta ta fita falo ta gyara ta canja tsarin kujerun sannan ta shiga kitchen duk sai ta gyarasu. Sannan ta daura musu kunun gyada da yamball ta gama ta jere a dining sannan ta haye sama dan ganin me Momy takeyi dan bata sauko ba. Wardrobe din ta tadda ta tana gyara amsar kayan hannun ta tayi tana fadin
“Inakwana Momy?”
STORY CONTINUES BELOW
“Lafiya lou. Kin tashi lafiya?”
“Alhamdilillah!”
Gyara wardrobe din ta amsa ta karasa sannan ta fita danyin wanka Momy ma ta shiga yin wanka.
Tana fitowa taji wayar ta na kara,  wajen wayar ta isa ta dauka ta kai kunnen ta
“Assalamu alaikum!”
Ta fada ya amsa da
“Wa’alaikum salam ba dai baki tashi ba ina ta kira baki dauka ba.”
“Na tashi ina wanka…”
Sai tayi shiru tana toshe baki dan kunya taji da tace tana wanka.
“Ok kin tashi lafiya?”
“Uhmm!”
“Ya gida Ya Momy?”
“Tana lafiya!”
Ganin shi bai dauki komai ba yasa itama ta dan sake suka gaisa sannan sukai sallama. Mai ta shafa ta saka wani black pencil siket ta saka orange kalar bodyhuge sannan ta kama gashin ta ta saka black hula sannan ta feshe jikin ta da turaren dake gaban mirrow dinta.
Sannan ta fito Falo a dining ta samu Momy na hada kunu karasawa tayi ta zauna ta dauki cup ta zuba kunun ta saka sugar da madara sannan ta dauki spoon ta diba ta sha yamball din ta fara ci taci kadan sannan ta saka pepper soup ta sha ta sha kunun.
A falo ta zauna tana kallo tana aiki a system din ya. Momy tace
“Anjima zaki mika ni gidan bikin fa.”
“To Momy daga nan na shiga na gaida Hajiya.”
“Da kin kyauta kuwa!”
5:00pm suka fito ita da Momy. Fateema sanye da wata ash kalar atamfa wacce akaiwa zane da red colour dinkin riga da siket ne yai mata kyau ta saka red veil da red hill shoe sai tai kyau tana taku dai dai duk da batai kwalliya ba man lebe ne kawai sai hoda a fuskar ta.
Momy na sanye da less itama tayi kyau tayi lullubinta. Mota ta bude mata ta shiga sannan ta ta rufe ta zaga ta bude ta shiga suka dau hanya. Tana driving aka kira ta dubawa tayi taga Aslam ne. Dauka tayi ta kai kunnen ta tace
“Barka da Yamma!”
“Yauwah Barka kadai! Ya kike ya gida?”
“Alhamdulilah!”
“Kina gida ne?”
“No kaga zan kai Momy gun biki!”
“Ok da zan zo amman shikenan bari na tafi gidan Hajiya kawai ki gaishe da Momyn.”
“Zata ji.”
Ta kashe ta kalli Momy tace
“Momy yana gaishe ki.”
“Ina amsawa.”
Suna zuwa wajen bikin Fateema tace
“Sai na dawo!”
“Ba zaki dan leko ba?”
“In na dawo na shigo Momy!”
“Shikenan ki gaida Hajiyar!”
“Zataji.”
Tayi reverse ta bar wajen gidan Hajiya ta nufa mai gadi na bude mata kofa a compound ta samu Hajiya sanye da mayafi har da jaka a hannu. Parking tayi ta fito ta durkusa tace
“Ina yini Mama?”
“Lafiya Alhamdulillah ya kike gida?”
“Alhamdulillah!”
“Muje daga ciki daman gidan Hajiya Fateema zanje.”
“A’ah Hajiya kije kawai daman biyowa nai na gaishe ki kuma na gaishe ki.”
“Dan Allah mu shiga ko ruwa ne kisha.”
Haka tabi bayan ta aka kawo mata ruwa da lemo,  ruwan ta dan sha sannan tace
“To Hajiya bari na tafi.”
“Ki zauna Fateema sai nai mata waya kawai nace sai gobe.”
“A’ah Mama kije daman nima wucewa zanyi na biyo.”
“To shikenan!”
Suka fito tare. Momy tace
“Ina Audu driver!”
Mai gadi yace
“Hajiyar cikin gida ce ta aike shi.”
“Ikon Allah bari na koma in ya dawo ya kirani.”
“Mama muje na ajiye ki mana.”
“A’ah kar na wahalar dake.”
“Ba komai Mama!”
Ta bude mata gidan baya Hajiyar Fu’ad tace
“A’ah gaban ma ai yayi ke da ba driver ba.”
“Ba komai Mama ai girman kine?”
“A’ah gaban ma yayi.”
Ta shiga ta rufe ta zaga ta tada motar
“wacce unguwa ce?”
“Inda mukaje ranan fa.”
“Oh!”
Ta tada motar ta dauki hanya suna zuwa tai horn mai gadi na lekowa ya shaida motar dan haka ya bude musu parking tayi ta fito ta budewa Hajiya. Motar Aslam ta gani ta dauke kai.
Hajiya tai gaba tabi bayan ta. Har falon suka samu Hajiya da Jannah. Jannah na ganin Fateema ta mike ta rumgume ta tana fadin
“Oyoyo oyoyo!”
Hajiya da Hajiya Fateema suka saki dariya. Sakin ta tayi tace
“Ina yini Hajiya!”
Hajiya tace
“Lafiya ya kike ina yar uwar taki?”
“Tana ciki.”
Durkusawa Fateema tayi tace
“Ina yini Hajiya?”
“Lafiya lou Fateema ya gidan?”
“Alhamdulillah!”
“Ya aiki?”
“Alhamdulillah.”
“Allah taimaka.”
Jannah tace
“Taho mu shiga ciki!”
Taja hannun ta. Wani falo suka shiga da ban suna shiga kamshin turaren sa yai mata sallama. Wannan yasa ta dago da sauri ai kuwa suka hada ido yana zaune akan kujera ya zuba mata ido.
Taja hannun ta. Wani falo suka shiga da ban suna shiga kamshin turaren sa yai mata sallama. Wannan yasa ta dago da sauri ai kuwa suka hada ido yana zaune akam kujera ya zuba mata ido.
+
“Au Uncle kana nan dama bari mu koma dayan dakin.”
“No kuyi zaman ku fita ma zanyi yanzu.”
“Bismillah!”
Jannah ta fada zama tayi ta dan saci kallon sa tace
“Ina yini?”
“Lafiya lou ya kike?”
“Alhamdulillah!”
Jannah tace
“Uncle ka gane ta?”
Kallon Fateema ya tsaya yi. Jannah tai murmushi tace
“Uncle Doctor nan ce fa.”
“Oh na tino ta ya aiki Doctor?”
dagowa tayi ta kalle shi ya kanne mata ido daya tai saurin dauke kai yace
“Alhamdulillah.”
Fita Jnnah tayi dan kawo mata ruwa ya kalle ya yace
“Yau dai sai na ganki ashe?”
Hararar sa tayi tace
“Ban sanka ba.”
Murnushi yayi yace
“Sorry kanwata kinsan Halin Jannah da surutu fa ni ai bance ban ganeki ba.”
“Gashi nan wai ka tunani kace.”
“To ayi min hakuri.”
Shiru tayi yace
“Please!”
“Shikenan!”
Yace
“Ina bikin?”
“Momy na ajiye naje gaida Hajiya shine na sameta zata zo nan na kawo ta.”
“Au tare kuke da Hajiya?”
Kai ta gyada yace
“Naje ranar friday ai mun gaisa.”
“Ka kyauta!”
Ta fada. Yai murmushi ya kalle ta yace
“Amman fa kinyi kayu!”
Murmushi tayi ta saci kallon sa yau dai manyan kaya ne a jikin sa. Ash kalar shadda tai masa kyau.
“Ni fa?”
Ya tambaya. Tace
“Same!”
“Nagode.”
Jannah ce ta shigo hannun ta dauke da plate da juice da cup ajiyewa tayi sannan tace
“Bismillah!”
“Ni a koshe nake!”
“Kamar ya gaskiya sai kinci.”
Ta bude juice din ta tsiyaya mata.
“Allah Jannah na koshi.”
“Uncle kai mata magana!”
Jannah ta fada.
Yace
“Ai daman haka take?”
“Wa din?”
Dagowa yayi suka hada ido da Fateema sai ya kalli Jannah yace
“Me wai?”
“Nace Kace taci. Shine kace wai daman haka take shin nace wa?”
“Oh ai ni ba dake nake ba.”
“Dawa kake?”
“Chat nake maganar zuci ta fito.”
“Oh! To kace taci please!”
Kallon Fateema yayi yace
“Kici please!”
Lemon ta dauka tayi sipping sannan ta ajiye tace
“To cake ko meat pie!”
Cake ta gutsura taci sannan ta ajiye ta sha lemon. Mikewa Aslam yayi yace
“Kila dan ina dakin ne ko Doctor!”
Ya fita. Da kallo ta bisa sannan ta dauke kai.
STORY CONTINUES BELOW
6:00pm Hajiya ta aiko Fateema ta futo su tafi tare suka fito da Jannah da Noor suka rakata har gun mota ta shiga suka tafi anan suka juya sai dube dube take ta ida zataga Aslam dan ga motar sa nan.
A bakin gate suka hadu ya leko ta window gefen Fateema ya kalli Hajiya yace
“Hajiya har kun fito?”
“Eh Aslam zamu tafi dare yayi.”
“To ku gaida gida.”
Ya kalli Fateema yace
“Allah tsare!”
“Amin!”
Ya matsa ta tada motar suka tafi. Tana sauke Hajiya tace juyawa zatai dan zata dauko Momy ta ajiye Hajiya ta juya ta nufi daukar Momy.  A kofar gidan tai parking ta fito ta kusa cikin gidan da yake cike da yan biki ido ta fara wullawa ko zataga Momy amman babu ita cikin gidan ta shiga ta same ta zaune a falo ita da Maman amarya da wasu kawayen su.
Tana shiga Maman Amarya ta mike tana fadin
“Ah Fateema sannu da zuwa!”
Ta rumgume ta. Fateema ta zame ta durkusa ta gaishe ta sannan ta gaishe da sauran kawayen Momyn tata.”
Maman Amarya tace
“Shine baki shigo ba kika tafi gidan Maman ki ko?”
Kai Fateema tai kasa dashi. Maman Amarya tace
“Ga gate pass nan na dinner gobe in an kai ta za ayi dan Allah kizo ‘ya ta.”
“Insha Allahu!”
Momy ta mike yace
“Sai goben in nazo.”
“Allah kaimu!”
Suka fito da Momy da Maman Amarya sai Fateema dake bin bayan su. Abakin kofa suka hadu da Amarya da kawayen ta zasu shigo. Amarya na ganin Mony tace
“Momy ba dai tafiya ba. Ni ban ga Fateema bama.”
“Tafiya zanyi wallahi ga Fateema nan sai yanzu ta shigo.”
Ta nuna ta. Kamo hannun ta amarya tayi tace
“Ya kike sister?”
“Lafiya Alhamdulillah!”
“Amman gobe dai zaki zo da wuri ko?”
“Zan shigo dinner dai insha Allahu.”
“To dan Allah kizo sister”
“Insha Allah!”
Ta sake ta tai musu bye sannan suka shige. A bakin gate sukai sallama da Maman amarya suka gita.
A hanya tace
“Momy da naje gidan Hajiya fa unguwa zataje yau ma munje gidan su Uncle wallahi yan gidan suna da mutunci sosai acan ma muka same shi shima.”
Momy tai murmushi tace
“Suna lafiya?”
“Alhamdulilah!”
“Masha Allah.”
Horn tayi mai gadi ya bude suka sauka tace
“Momy kila sai naje na taho dasu Baba ko?”
“Suna nan dawowa dis ending month ai!”
“Haba ai gwara sunje sun zauna.”
Kowa dakin sa yayi dan an kira sallah sukai alwala sukai sallah.
*
**
***
****
*****
******
*******
Mr President ne yayi gyaran murya yace
“Kamar yadda kuka sani sunana Alhaji Ahmad Yahya shugaban kasar nigera wannan aboki nane Sarkin Kano Alhaji Kabir Ahmad! Ban fada muku mu su waye ba dan son a sani sai dan yana da kyau mu fada kafin mu fara maganar da ta kawo mu muna fatan babu matsala.”
Baba jiki a sanyaye yace
“Babu insha Allahu!”
Mr president yace
“Dan Alhaji Kabir wato Aliyu shi yake mulkin garin nan naku a matsayin gwamna na karkashin sojoji wanda ni na saka shi saboda kwazon sa da hazakar sa, wanda a yanzu kowa ya gani ya kuma shaida da aikin nasa dan ba a iya gida Nigeria ba hatta a waje an san da wannan gari naku da kuma gwamnan ku saboda aikin da yake yi tsakani da Allah dan talakawa ba dan ya samu wani abu ba. Anjima ba’a samu wanda yai mulki irin haka ba wanda yake aiki da kudin sa da aljihun sa ku shaidane kun gani kuma kuna jin dadi a garin ku.”
Kai Baba ya gyada yace
“Wannan haka ne domin koni shagon da nake a kasuwa shi ya ban shi da jari, ya’yana uku ya saka su a makaranta daya aka bashi horo akan sana’a wanda yanzu yake kasuwanci,   banda wutar lantarki da muka samu da ruwan famfo da titina da gyara asibito ci da makaranta har auta ta ma yanzu ta zana jarabawar gama karatun ta duk da taimakon wannan gwamnati dan haka ba abinda zance sai dai nace sambarka da saka masa albarka kamar yadda ko wanne mutum a garin nan ke saka masa albarka.”
STORY CONTINUES BELOW
Kai su mai martaba suka gyada suna jin dadin yabon da yaiwa Aliyu duk da sun saba ji amman wannan daban da wadan can. Mr president yace
“To Alhamdulillah ko a iya haka kasan waye Aliyu dan yana da hali da dabi’u masu kyau ga ilimi da amfani dashi wannan shiyasa na damka masa wannan kasar a hannun sa.”
Kai suka gyada. Mr president yace
“Ba komai yasa na kawo duk wannan ba sai dan abun da muka zo dashi zai shafi wannan maganar ta son sanin waye Aliyu da asalin sa. Kan mu shiga da nisa dai zan fada muku halin da Aliyu yake kan na fada muku dalilin shigar sa da komai.”
Shiru sukai. Mr president ya kalli Mai martaba sannan ya kalli Baba yace
“Yau kusan sati uku Aliyu bai da lafiya wanda a sati biyun duk bai mu’amala da kowa hatta iyayen sa da mu kan mu ga PA sa nan ko gidan gwamnati baya zuwa mai gadi yace tin yana fita masallaci har ya kasa fita,  to wannan yasa mahaifin nasa Alhaji Kabir dame dakin sa sukayo takkayiya anan suka same shi cikin wani mawuyacin hali,  wanda yake fama da jinya bayan an kira likito ci suka tabbatar da yana cikin damuwa dan jinin sa ya hau kuma zuciya sa ta kamu da ciwo ga ulcer da ta kamashi saboda rashin cin abinci. Wannan yasa mahaifin nasa ya dauki suka fita can kasar egypt acan ma bayan gwaje gwaje duk result din su ya nuna abinda likitocin mu suka fada,  a kwanaki biyu da zuwan su Egypt sai da suka zata ya mutu Allah yayi da sauran kwanan sa a gaba wanda da taimakon Allah da likitocin ya dawo a yanzu condition din da yake ya zarce tunani domin yana kan matakin karshe a rayuwar sa dan har aman jini yake,  shekaran jiya ciwon sa ya tashi bayan gama magana da wani abokin sa akan wata yarinya da yake so. Takai ta kawo Aliyu yana bada wasiyya akan yarinyar da yake so akan cewar  in ya mutu lallai a tsaya mata akan karatin ta da kuma bata dukiya mai yawa da yayi.”
Ya nuna Alhaji Kabir yace
“kan wannan yaji wayar da sukai da yarinyar da maganganin da ya fadawa abokin sai akan soyayyar yarinyar wanda daga lokacin jikin sa ya tashi dan yau kwana biyu kenan bai kara farkawa ba domin likitoci sai allurai suke masa da saka masa ruwa hakika rayuwar Aliyu na cikin hatsari.”
Gyaran murya yayi yace
“Nasan zakuce mai ya kawo wannan maganganun ko? To ba komai bane face Aliyu yana fama da son yarinyar ka Aisha wacce ya fito ya fada mata ita kuma ta nuna bata son sa akwai wanda sukai alkawarin aure dan haka ne ma ya janye dan son samuwar farin cikin yarinyar da barin ta amman hakan bai nuna shi wai ya hakura ba ya bar wa zuciyar sa son Aisha wanda ya janye sonta ya barta ta auri wandan take so domin sadaukar da soyayyar sa gareta,  a yanzu dai shawarar da likitoci suka bayar shine a daure a samar masa da abinda yake so ko a magance masa abinda yake so. Wannan yasa muka zo dan neman alfarma dan Allah ba dan mu ba badan matsayin ba ko dan ceton ran wannan bawan Allah dake wahaltawa alumma ku bashi auren wannan yarinyar shi waccan a bashi hakuri inda halin yin hakan muna fatan zaku amshi koken mu.”
Shiru Baba yayi. Yaa Muhamad kuwa jikin sa ya mutu tunani yake daman akwai wanda yake son Aisha har haka. Akwai wanda zai iya sadaukar da son da yake mata dan samuwar nata akwai wanda zai sadaukar da rayuwar sa dan burin ta ya cika akwai me son ta har haka bayan shi. Lallai Aliyu ya bashi tausayi dan bai zata ya’yan masu hali suna da irin wannan halaiyar ba don yana ganin suna samar duk abinda suke so ta karfi da yaji ne in wani ne zaiyi iyayin sa ya samu Aisha a ciki kuma har da kisa saboda yana da damar yin komai yana da iko da mulki da komai. Amman yana jin a ransa tayaya shi zai iya rayuwa ba Aisha yana jin a ransa tayaya zai soma tayaya.
Mai martaba ne ya gyara murya yace
“Duk abinda Alhaji Ahmad ya fada haka ne,  kuma ni jiyau ne akan son da Aliyu yakewa Aisha ba algus a cikin sa hakika zamu kula muku da yar ku kamar yadda zamu kula da ya’yan mu kuma ba zamuyi muku dole ba inda matsala sai ku fada mana.”
Mai martaba ya fada yana zaro waya nan yai musu connecting vedio call a wayar Mamah tana dauka tace
“Ranka ya dade kun karasa ne ya kuka yi?”
“Gamu a wajen Fulani ina son ki nuna musu a halin da Aliyu yake ciki.”
Mikewa tayi ta saita wayar ta ta nuna musu Aliyu dake kwance kamar gawa duk jikin sa naura ke aiki ga ruwa dake shiga jikin sa. Take duk zuciyar su ta karye daukar wayar tayi tana kallon screem din ta hade hannu tana fadin
“Dan darajar Allah Alhaji in da hali a taimaka a bamu auren Aisha domin samuwar rayuwar dan mu. Ba muyi haka dan d”an mu kawai ba sai dan abubuwa da yawa Malam na daya ita kanta yarinyar tana son Aliyu tana kunyar amsar sane dan wanda akace zata aura kuma dan riko da alkawari na biyu shi kansa wanda zata aura zai samu nutsuwa akan ya auri wacce ke son wani dole hankalin ta zai rabu guda biyu kuma zata shiga damuwa wanda zai zama silar damuwar sa shima kuma iyayen ta zaku samu nutsuwa yar ku ta auri wanda take so zata samu nutsuwa su zauna lafiya sai nan karshe shima Aliyun zai samu nasa farin cikin da cikar burin sa dan Allah a taimaka mana inda halin yin hakan. Nagode!”
Mai martaba yace
“Shikenan Fulani zakiji yadda mukai sai anjima.”
Baba ne yai gyaran murya yace
“Aliyu yazo min da maganar yana son ‘ya ta wanda na fada masa tana da wanda take so amman yazo ya nemi soyayyar ta to gaskiya ban sani ba ko yazo ko bai zo ba dan na sanar da mahaifiyar ta. Kuma baton wanda take so gashi nan ‘da nane shine dana na fari Aisha yar Yayana ce wanda Allah yaiwa rasuwa Maman ta kuma ta koma garin su ni naki bata yarinyar dan in ta tafi mu wa zamu kala mu tina da mahaifin ta. Aisha aguna ta taso amman wannan ba zai sa nai mata dole ba. A sati uku da ya gabata aka bawa Muhammad auren Aisha wanda nan da wata daya za ayi komai. Ni ba zan wa kowa dole a cikin su ba amman zanyi kokarin fahimtar da dukkan su dan haka yanzu zan kira Aisha anan aji ta bakin ta har da mahaifiyar tata ma dashi kan sa Muhammad duk yadda akai ni kuma dan zartar da hukunci kamar yadda suka zaba.”
Mr president yace
“hakan ma yayi kuma wannan shine adalci fatan mu Allah yasa a dace ya zaba abinda yake mafi alheri.”
Kai Mai martaba ya gyada yace
“Amin!”
Baba ya mike yai cikin gida. Umma ya sama ta gama girki tana zubawa baki a kula yace
“Ina Aisha?”
“Tana daki!”
“Ki gama ki samen a soro.”
“To lafiya dai ko?”
“Lafiya lou!”
Ya nufi dakin Aisha. Tana zaune tana neman layin Aliyu har lokacin surutai take tana fadin
“Yaa AK ina ka shiga ka  kunna wayar kar zuciya ta ta buga……”
Ya nufi dakin Aisha. Tana zaune tana neman layin Aliyu har lokacin surutai take tana fadin
“Yaa AK ina ka shiga ka kuna wayar kar zuciya ta ta buga……ka kunna naji ya kake ko zan samu nutsuwa dan Allah ka kunna.”+
Tafada tana fashewa da kuka Baba ne yai gyaran murya sanna yai sallama da sauri ta shiga goge hawayen idon ta,  ta dago tana amsa sallamar sa.
Kallon ta ya tsaya yace
“Lafiya ko jikin ne?”
Kai ta girgiza sannan yace
“To kizo ki samen a soro.”
“Toh!”
Ya fita ta mike ta dauki katon hijab har kasa ta saka. Tana fitowa ta samu Umma ta shiga daki soro kawai tayi ganin baki yasa gaban ta ya fadi ta durkusa ta gaishe su cikin girmamawa a ciki ba wanda ta sani kan ta a kasa tace
“Baba gani.”
“Zauna nan bari Umman taki ta fito.”
Zama tayi a bakin tabarmar da ta cika soron. Batai minti biyar ba Umma tayo soron sanye da hijab har kasa, itama tana ganin manyan mutane ta tsaya daga bakin soron ta durkusa sula gaisa sosai sannan Baba yace
“Bismillah man.”
Takalma ta cire ta shigo ta zauna kusa da Aisha. Shiru wajen yayi can Baba yace
“Wannan iyayen Aliyu ne,  sunzo ne neman auren Aisha.”
Gaban Aisha ne ya fadi ta dago da sauri ta kalli Baba sai kuma ta kalli Yaa Muhammad shima ita yake kalla kai ta hau girgiza masa idon ta na kawo kwalla. Kai ya girgiza mata ya dan saki murmushi na bata kwarin gwiwa wannan yasa tai kasa da kanta.
Baba yace
“Sun fadan komai akan yaron da rashin lafiyar da yake da komai amman nace su bari aji ta bakin yarinyar da yaron tukkuna kan mu muga me ya dace!”
Kai Umma ta gyada. Baba ya kalli Aisha yace
“Aisha kina son Aliyu!”
Kan ta yana kasa ta kasa dagowa. Baba yace
“Aisha magana fa nake yi!”
“Baba dan Allah kayi hakuri ni ban san ya zanyi ba amman….”
Sai kuma ta toshe bakin ta da hijab ta fashe da kuka a guje ta mike ta bar soron duk suka bita da kallo.
Kai Umma ta hau girgizawa,  Baba yace
“Ke kinsan wani abu akan yaron ne Masa’uda?”
“Nasani Malam amman ni ban san ya zanyi da Aisha ba domin nima na gane tana tsananin son yaron nan dan tin lokacin da ya bar zuwa gidan nan tun lokacin Aisha bata da nutsuwa da walwala jiya muka gama magana da Muhammad akan matsalar dan har ina bashi shawara akan ya bawa Aisha dama ta kawo wanda take so dan kai shaida ne kaga halin da ta shiga na rashin lafiya kwana ki biyu da suka wuce wanda kace jinin ta ya hau to gaskiya ba zai rasa na saba da damuwar da ta shiga akan yaron nan ba. Abinda na riga na gane Aisha na son yaron sai dai ba zata iya cewa bata son Yayan ta ba.”
Kai Baba ya jinjina yace
“Amman meyasa bansan da duk wannan matsalar ba.”
“Malam kayi hakuri ammam nima ina yin iya tawa ne dan ganin Aisha ta gane wa take so kan muzo maka da magaar to kasan Aisha da zurfin ciki kuma ina ganin tana jin kunya ko dan mu muka haifi Muhammad.”
“Ashha bayan ni banda wannan a rai na fi daukar Aisha a matsayin ‘ya ta abinda take so shi zan mata ko shi Aliyun da ya samen na fada masa ba zan wa Aisha auren dole ba yaje ya nemi soyayyar ta. Lallai Aisha yarinya ce mai tarbiyya da gudun bacin ran mu wannan shi zai kawo duk wannan abun.”
Yaa Muhammad ya kalla yace
“To Muhammad ya zamuyi yanzu!”
STORY CONTINUES BELOW
Gaban Muhammad ne ya fadi,  kasa yayi da kansa yace
“Baba Aisha abar sona ce kuma ta cancanci in mata komai a rayuwa tinda har Aisha ta iya sadaukar da farin cikin ta dan bani nawa akan me ni ba zan sadaukar da nawa ba. Ni kaina na sha fada mata nafi son farin cikin ta akan nawa,  tinda mukai magana da Umma nima na yanje a raina ba zan auri Aisha ba zan bata zabi ta auri wanda take so,  dan haka Baba nima na amince Aisha ta auri Aliyun Allah yasa haka ne mafi alheri Allah ya basu zaman lafiya ni kuma Allah ban hakuri da juriyyar rashin Aisha. Ina musu fatan alheri.”
“Allahu Akbar!”
Mai martaba,  Mr president,  da PA suka hada baki suka fada. Maiartaba bai san lokacin da hawaye ya taru a idon sa ba ya mike yazo ya rumgume Muhammad da shima idon sa ya cika da hawaye yace
“Allah maka albarka Allah ya baka hakuri da juriyya Allah ya kawo kaima mai son ka kamar yadda kake son ta,  Allah ya zama gatan ka nagode Muhammad nagode Allah ya saka maka da alheri.”
“Ba komai Ranka ya dade!”
“A’ah ka kira ni da Abbah kamar yadda ya’ya na ke kira na kaima ‘da nane kaji ko?”
Kai ya gyada sai kuma ya mike yai cikin gida dan bai san a halin da Aisba take ba.
Tana shiga daki ta zube tana kuka fargabar ta daya yaya Yaa Muhammad zai dau wannan alamarin sai yaga kamar ta yaudare shine ita ya zatayi ita bata ce masa ya turo ba kuka take bilhakki da gaskiya. Sam bata ji sallamar Yaa Muhammad ba sai ji tayi an dago ta tana dagowa taji kamshin turaren sa kan taga fuskar sa ta fada jikin sa ana fadin
“Ni kai nake so Yaya na ba wanda nake so a gaban ka kai nake so Yaya na.”
“Stop crying Aisha! Menene na kuka to?”
Kai ta kwantar a kirjin sa tace
“Kada kace na yaudare ja Yaya na na fada masa kai zan aura bansan ya akai ya aiko su ba sam.”
“Ba shine ya aiko su ba Aisha! Aliyu bashi da lafiya bai san sunzo ba.”
“Tayaya suka sani to?”
“Aisha duk abinda za a shuka sai ya fito ko ke da kanki kikai magana kika burne wata rana sai ta fito,  bare Allyu a son ki dole ya fadawa wani wannan yasa suka zo amman sam bai san sunzo ba.”
Dagowa tayi tana kallon sa tace
“Amman baka ji haushi ba ko? Yaa AK bai san zasu zo ba da ba zai bari ba. Domin ya hakura dani Yaya na.”
“Na sani Aisha nasan waye Aliyu sai dai ban san shine Yaa AK ki ba mutum ne mai imani da ilimi da adalci.”
Shiru tayi yace
“Ki daina kuka kinji?”
Kai ta gyada tace
“Kaje kacewa Baba ni kai nake so shi mun gama magana da shi.”
“Baki da matsalar wannan kowa ma yasan kina so na Aisha.”
Murmushi ta saki ta janye jikin ta tan koma ta zauna. Kai ta dafe yace.
“ya dai?”
“Ciwo yake min!”
“Kinsha magani?”
Kai ta girgiza yace
“Kinci dankalin?”
Shima kai ta girgiza yace
“Saboda me?”
A zuciya tace
“Saboda ban san halin da Yaa AK yake ciki ba.”
A fili tace
“Na kasa ne Yaya na ga shi gabana sai faduwa yake.”
“Sannu ki daure kici sai kisha magani kinji.”
Kai ta gyada ya fara bata a baki taci kadan tace ta koshi magani ya bata ta sha sannan ya bata maltina da ya kawo ko kallon ta batai ba ita ta sha sannan ta kwanta ya mike ya fito a dakin yana runtse idon sa.
Umma ce ta shigo tace
“Zo ka kai musu abibci Muhammad a siyo musu lemo da ruwa.”
Dauka kulolin yayi da plate ya fita da su anan soro ya same su anan ta hira. Fita yayi ya kawo lemo da ruwa duk suka zauna suka ci ba tare da nuna komai ba aka ci aka koshi sannan Mr president yace
“Muna kara neman wata alfarma dai in ba matsala.”
“Babu matsala insha Allahu!”
“Muna son a daura auren Aisha da Aliyu inda hali mu tafi da ita taje wajen sa in sun dawo ta tare!”
Shiru Baba yayi sai can yace
“Daman in an daura aure ai ta zama mallaki sa ko? Dan haka ba matsala zan fadawa Maman ta dashi yayan nata yanzu sai a daura ko?”
STORY CONTINUES BELOW
“Muna gidiya Allah kara gurma!”
“Ba komai.”
Mikewa Baba yayi ya shiga a tsakar gida ya samu Umma da Yaa Muhammad tana bashi baki. Baba yace
“lafiya dai ko?”
“Ba komai!”
“To daman sun nemi alfarmar a daura auren ne shine nace to ya kuka gani?”
“Yadda kace Malam!”
Yaa Muhammad ya kalla yace
“Kai fa?”
“Duk yadda kace Baba yayi.”
“To yanzu za a tafi masallacin jumma’a in an idar sai a daura amman suna son subtafi da ita can wajen mijin nata fa.”
“To Malam Allah ya tabbatar da Allah ya sanya alheri ya bada zaman kafiya.”
“Amin!”
Kiran Sallah aka farayi Baba yace
“Muhammad je ka kai musu ruwan alwala.”
Nan ya fita ya kai musu dukai alwala aka tafi masallaci Juma’a dan ranar friday ce kan a tada sallah Baba yace in an idar a tsaya za a daura aure sannan ya kira waya ya kira Yaa Mustapha da Umar akan su kawo Alewa da Goro kamar yadda Mr Preaident ya sa PA yaje ya kawo ba tare da su Baba sun sani ba.
Ana idar da Sallah Yaa Mustapha da Yaa Umar da Yaa ibrahim,  Shu’aibu duk sunzo daboda kiran da Baba yai musu sai kuma PA shima da ya karaso. Liman ne yace ina masu daurin auren? Nan Baba da Mai martaba da Mr president suka karasa wajen liman kowa yaga Mr president yayi mamaki dan wasu gani suke anya kuwa shine wasu suce shine wasu suce ba shine ba.
A haka aka ce ina waliyin ango Mai martaba yace Baba ne,  sannan akace ina waliyin amarya aka nuna Mr president nan aka hau hada hadar daurin aure. Mai martaba ya fito da kudi masu yawa ya bawa Baba. Baba ya amsa zai magana Mai martaba ya girgiza kai. Nan Baba ya bawa Mr president sadakin Alyu. Mr president ya amsa a matsayin waliyin Aisha nan aka daura aure akai addu’a aka shafa fatiha.
Nan ladan ya hau fadin an daura auren *Aisha Isah* da *Aliyu Kabir*  Allah ya sanya alheri ya bada zaman lafiya. Sosai Su Yaa Umar,  Shu’aibu,  Ibrahim da Mustapha suka hau mamaki. Muhammad kuwa sai ya hau raba alawa da goro shi da PA kowa aka dinga bashi jakar alawa da damin goro daurin auren da ba a shirya masa ba amman ya samu halatar manyan mutan dan sarakuna biyu ga na kano ga na garin ga mr president da wasu manyan mutane wanda dubun nan mutane suka shaida dan babban masallacin juma’a ne a garin da kowa yawancin ke zuw. mutane suka karasa suna yiwa su Baba da Mr president murna da Allah sanya alheri.1
Daya a ciki bayan sun gaisa yace
“Dan Allah kaine..?”
Sai yai shiru murmushi Mr president yayi kawai suka fita tare da su Baba aka dauke su a mota tare da masu basu tsaro sukai tafi can gidan Baba. A kofar gidan Baba suka tsaya. Mr presdient yace
“Ga sadakin ‘yata a bata abinta yanzu zamu tafi.”
Nan PA ya kawo alawa da goro masu yawa ya jibge a soro wai a rabawa yan uwa da abokan arziki na daurin Auren Aisha da Aliyu.
Su Yaa Muhammad ne da yan uwan su suka karaso nan Baba yace
“To yau zaku tafi kenan?
“Eh!”
“To ku shigo ku zauna kafinta fito ko?”
“Eh hakan za ayi.”
Suka karasa suka zauna. Mai martaba bakin sa yaki rufuwa saboda murna da yake ciki.
Ciki Baba ya shiga yace
“Ina Aishan ne?”
“Tana daki!”
Dakin ya shiga ya sameta a kwance ya kalle ta yace
“Aisha jikin ne dai?”
Kai ta gyada yace
“Me yake miki ciwo”
Kai ta nuna masa ta fara kokarin tashi yace
“To daman jikin Aliyu ne ya tashi shine Mahaifin sa ya roki alfarma a basu ke kuje dan ya damu yana son ganon ki. Ina fatan zaki je.”
Wani dadi taji a cikin ranta domin itama bata da buri sai na taga Ya jikin Yaa AK din yake dan haka tace
“Zani Baba.”
“To Allah miki albarka Aisha.”
“Masa’uda!”
Ya kwalawa Umma kira ta shigo da sauri tana fadin
“Na’am Malam gani.”
STORY CONTINUES BELOW
“Dan Allah ki dan hada mata kayan da zatai amfani dasu naga bata jin dadi har yanzu!”
“To malam!
Ta dauki wata karamar jaka ta zuba mata kaya kala biyar da underwears da hijab da brush da soso da komai Baba ya amsa ya kalle ta yace
“Tashi muje.”
Ta mike a hankali ta saka hijab din da Umma ta bata sannan ta fito a bakin kofar daki taga Yaa Muhammad gun sa tayi sai kuma tai kasa da kai tace
“Yaya kaji Baba wai zanje na dubo Yaa AK ya fada maka ko?”
“Ya fada min Aisha ki masa sannu da jiki kinji.”
Kai ta gyada tana goge kwalar da ta zubo mata. Ta juya ya buyo bayan ta. Tace
“Umma na tafi.”
“To Aisha Allah kiyaye Allah ya tsare.”
“Amin!”
Sannan tabi bayan Baba. A waje ta same shi tsaye dasu Mai martaba. Mota guda aka bawa Aisha ta shiga Baba ya saka mata jakar kayan ta a ciki. Sanyin da kamshi yasa ta lumshe ido sai kuma taji faduwar gaba bata taba tafiya tabar garin ta ba bare kasar ta. Anya hakan ya dace kuwa. Sannan suka kara gaisawa dasu Mai martaba sukai sallama suka shiga wata mota har sun tayar Mai martaba ya kalli Mr president yace
“Anya ba zamu dauji wani nasu ba ko dan hankalin su ya kwanta su samu nustuwa itama yarinyar haka.”
“Haka ne Kuma Alhaji Kabir kana da kaifin basira.”
Driver suka tsayar sannan suka fito Baba yace
“Lafiya?”
“Eh mun canja shawara ne nace mai zai hana Yayan nata yazo su tafi ko dan hankalin ku yafi kwanciyya itama haka.”
Baba yai murmushi yace
“Ba matsala ai mun yadda daku.”
“Duk da Malam Abubakar!”
“To shikenan amman za a kara bata lokaci dan zai hada wani abun ko?”
“Ba sai ya dau komai ba yazo mu tafi kawai.”
Juyawa Baba yayi ya kira Muhamad ya karaso yace
“To Mai martaba yace dakai za aje.”
“Haba dai Baba ai ba matsala suje kawai.”
“A’ah ‘dana kazo muje kaji.”
“To shikenan.”
Mai martaba ya kama hannun sa suka shiga mota sannan suka karai wa Baba godiya sukai gaba dayan su sai gidan Gwamnati.
Anan suka sauke PA sannan sukq dauki sauran securityn su suka koma Abuja a jirgi.
Suna sauka aka fara nemar musu jirgin da zai tashi. A lokacin aka bawa kowa inda zai sauka Aisha dai a kwance take da kyar ta sha tea dan matar Mr president first lady Hafsat ce kula da ita da kanta, tasa tayi wanka tasha magani ta kara samun saukin jikin ta. Ta koma ra kwanta.
Su Mai martaba kuwa tare da Muhammad suke. Muhammad yayi mamaki halin mai martaba yadda yake nuna son sa da kula dashi. Lokacin da ya kira yana bawa Mamah labarin abun da ya faru yayi mamaki domin yadda ta dinga murna da kabbara hadi da hamdala.
Haka yan uwansa Yaa Abubukar da Yaa Usman sunfi kowa Murna sai Maryama haka ma Faisal suka kagu suga zuwan su Aisha dan suga Aishan nan da Aliyu ya kusan ya mutu akan ta.
A daren suka tashi gaba dayan su. Da zasu tafi Aisha taga Yaa Muhammad sosai taji dadi da wata nutsuwa. Yadda Mai martaba yake wa Muhammad har mamaki take yi yana sonsa daga lokacin ta gane hakan.
*
Suna sauko duk yayen da kannen Aliyu suka zo airport dan tafiya dasu. Aisha dai kanta na kasa taki yadda kalli kowa a haka ta gaishe dasu sukai musu barka da zuwa. Gida aka wuce dasu aka bawa Aisha daki guda Yaa Muhammad dakin su Yaa Farouk aka kaishi anan sukai wanka sannan aka kawo musu abinci.
Aisha na shiga ta zauna tana dafe kan ta dake sara mata dan ciwo ga gajiyar hanya,  wanka ta shiga tayi ta fito ta zauna a bakin gado kan ta tashi ta shafa mai ta saka wata doguwar riga ta atamfa. Hijab ta saka kalar atamfar sannan ta tada sallah dake kan ta.
Tana zaune akayo knocking ta mike ta karasa ta bude mai aikin gidan ce ta kawo mata abinci amsa tayi tai mata godiya sannan ta koma. Ajiyewa tayi ta zauna,  sai kuma ta mike ta bude abincin yunwa take ji amman sam sai taji ba zata iya cin komai ba,  ba abinda take so ta gani inba Yaa AKn ta ba.
STORY CONTINUES BELOW
Bayan awa daya aka kara knocking ta mike jiki a sanyaye ta bude kofa. Umar ta gani yai mata murmushi yace
“Abbah yace in kingama ki taho ku tafi asibitin!”
‘To!”
Ta fada kawai tana bin bayan sa dan a shirye take suna fita ta samu dukkan su a falo daga nesa ta tsaya Abbah ya mike yace
“Muje to!”
Ta fita suka tsaya kallon ta Yaa Abubakar ne yace
“muje to!”
Bayan Abbah tabi tana tafiya kamar zata fadi dan yadda take jin jiri ga yunwa a haka ta karasa ta jingina da motar dake wajen. Fitowa sukai har da yaa Muhammad.
Umar ne ya bude mata wata mota ta shiga sannan ya shiga mazaunin driver ya kalli Yaa Mubammad yace
“Bismilliah!”
Ya shiga mazaunin kusa dashi sannan ya tada motar kowa ya shiga mota. Abbah da Yaa Abubakar da Yaa Usaman. Har sun tada motar Farouk ya fito da sauri motar da su Aisha suke ciki ya shiga ya bude baya ya shiga yana ganin ta yace
“Ah ashe Antyn mu ce anan !”
Ita dai shiru tayi suka dau hanya suna isa suka parking suka fito a baya ta dinga binsu har suka shiga reception din. Aisbitin ya hadu iyakar haduwa suna shiga suiai left suka kara shan kwana anan right hand suka shiga sannan suka shiga dakin farko. A falon suka samu Mamah zaune Hajara da Maryama suna ciki wajen Aliyu dake ta bacci.
Mamah na dagowa taga Aisha ta mike tace
“Taho ‘ya ta!”
A hankali ta taka ta karasa zata durkusa dan gaishe ta Mamah ta rumgumo ta tana fadin
“Sannun ku da zuwa ya hanya?”
“Alhamdulillah ina yini Mamah!”
“Lafiya lou ya kike?”
“Alhamdulillah ya mai jiki?”
“Da sauki!”
“Allah kara sauki.”
Abbah ne da ya shigo yace
“An samu ‘ya an manta damu ko?”
Ya kama hannun Muhammad yace
“Zo mu shiga.”
Sukai dakin da Aliyu yake ciki. Muhammad na ganin sa sai da ya tausaya masa ya ji kuma lallai yayi babban ceto da ya bashi Aisha Allah ya sa haka ne mafi alheri ya bashi dangana.
Abbah ya karasa ya zuba masa ido sannan ya juya ya fita. Karasawa wajen gadon yai yana kallon sa. Maryama da ta fito daga toilet ta tsaya kallon sa kawai dan bata san waye ba.
Faisal ne ya shigo yana ganin Muhammad ya mika masa hannu yaxe
“Kaine yayan Aishan kenan!”
Kai ya gyada yace
“Ya mai jikin?”
“Da sauki ina Aishan?”
“Tana wajen Fulani!”
“Ikon Allah ai ban ganta ba.”
Maryama na jin ance Aisha na wajen Fulani ta fita da sauri tana zuwa ta ganta ta saki ihu ta rumgume ta tana fadin
“Sannu da zuwa Antyn mu!”
Aisha tai kasa da kai tace
“Ya me jikin?”
Hannun ta ta kamo tace
“Yau dai naji dadi zan cikawa Yaya burin sa ga Antyn mu a wajen sa.”
Zasu shiga dakin Faisal da Yaa Muhammad suka fito suna magana. Kallo daya Yaa Muhammad yai mata ya dauke kai, ita kuwa kanta a kasa suka shiga dakin. Hajara da aka kira ta mike zata fita tana ganin Aisha ta tsaya kallon ta kawai. A ranta take cewa
“wai wacece wannan yarinyar ne?”
Sabosa kiran da ake mata yasa ta saka kai ta fita. Suna zuwa gaban gado Maryama tace
“Kalli Yaya!”
Dagowa tayi tana ganin sa ta zaro ido yadda ya rame yana kwance kai ba zaka ce yana da rai ba da sauri ta karasa bakin gadon sa ta toshe bakin ta hawaye ya fara zarya a idanun fa.
Dafata Maryama tayi tace
“Ai da sauki Ki daina kuka.”
Kai ta hau girgizawa tana fadin
“Innalillahi wainna illahir rajiun Yaa AK Allah ya baka lafiya!”
A gefen gadon ta kifa kan ta tana kuka Maryama ta dago ta tace
“Dan Allah ki daina kukan nan.”
Dagowa tayi ta kara kallon sa,  zuciyar tace ta kara karye wa dan sai ta tuno da kalaman da ya dingai mata wanda suke nuni da na ban kwana ne. Dan haka tace
“Dan Allah Yaa AK kada ka tafi ka barni ka tashi dan Allah!”
Sai kuma ta daura hannun ta a goshin sa,  tana daurawa ya bude idon sa a hankali tin yana ganin duhu duhu har ya soma ganin hasken dakin.
Tana ganin ya bude ido tace
“Yaa AK!”
Zuciyar sa ce ta buda ya juyo da sauri ido hudu sukai duk suka kasa daina kallon junan su. Shi gani yake tamkar a mafarkin da ya saba Aisba a gaban sa.
Hannun sa ya dago a hankali ya daura akan nata yaji hannun ta saki yayi ya kara rike hannn sosai magana yake son yi amman ya kasa sai ido da yake binta da shi. Ita kuwa in banda hawaye ba abunda ke zarya akan idon ta ta zuba masa ido.
Daya hannun ya daga ya kai fuskar ta yana goge mata hawayen idon ta tare da girgirza kai Maryama na ganin haka ta fita dan kiran Doctor duk suka bita da kallo yan falon Mama ce ta mike ita Mai martaba suka shigo dakin ganin Aliyu ya farka sosai suka ji dadi kan suyi wani mahgana Doctors sun shigo dakin da saurin su.
“Please get out!”
Duk suka Fita Aisha ta juya zata fita ya kamo hannun ta ya rike tsam. Kallon sa Doctor yayi yace
“ka kyale ta tafita mana Aliyi!”
Kai ya girgiza ya kara janyo hannun ya saka a kirjin sa ya rumgume. Kallon su suka tsaya yi Babban likitan dake kula dashi yace
“Ku kyale ta!”
Tana rike dashi suna tai masa gwaje gwaje idon sa yana kanta ya kasa daina kallon ta sam. Hawayen idon ta har lokacin bai daina zuba ba dan haka ya goge mata wani ke kara zubowa kuma bai gajiya da goge matan. Kujera wani doctor ya mika mata yace
“Have a sit!”
zama tayi dan jiri take gani sosai,  ajiyar zuviya ya sauke ganin ta zauna ya kara rike hannun ta. Sunfi awa biyu akan sa sannan suka gama gwaje gwajen nasa suka fita suka barsu a dakin.
Su Yaa Abubakar ne suka bi bayan doctor din Abba da Mamah suka shigo dakin. Aisha ganin su yasa ta fara kokarin janye hannun ta amman ya kara rikewa gam. Kai tayi kasa dashi jawai.
“Sannu Aliyu!”
Kai ya gyada Mama tai masa sannu shima haka. Sun jima tsaye Abbah yace
“Bari naje nai sallah.”
Sannan ya fita Mamah ma ta fita dan tayi sallah.
Su Yaa Abubakar na zuwa likita yace
“Alhamdulillah ya farka lafiya kuma jinin sa ya fara sauka yanzu zai cigaba da amsar magani ne Allah ya kara masa lafiya.”
“Amin doctor mun gode.”
Suka fito suma masallaci suka tafi. Suna zaune Nurses masu kula dashi suka shigo dan zasu tainaka yai wanka kuma su bashi abinci amman kememe yaki ya saki Aisha.
Abbah ne ya shigo yaji suna masa magana yace
“Me yake faruwa?”
“wanka zaiyi amman yaki ya sake ta!”
“Kuje da ita.”
“Ok sir!”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *