WA NAKE SO CHAPTER 25
Www.bankinhausanovels.com.ng
Hannu ta daura akan cikin ta, ta dago tana fadin
“Yaya da gaske ciki ne dani?”+
Kai ya gyada mata. Hawaye ne ya zubo a idon ta na daya na farin ciki itama zata zama uwa, na biyu zata haifawa Fauwaz Baby, na uku na tinawa da Fu’ad. Yau inda Fu’ad ne ya zai ji. Dan Bata San shi da Fauwaz Wanda yafi son Ya’ya ba. Kuma kila wannan rabon shi ya raba ta da Fu’ad.
Dago ta Fauwaz yayi yace
“Ki daina kukan Nan.”
Shesheka ta fara. Yace
“Baby menene ko akwai wani abun?”
“Yaya Nima Zan cika maka buri na Haifa maka Baby.”
“Allah ya rabaku lafiya Allah yai miki albarka.”
“Amin Amin! Yaya nah.”
Yai kissing lips din ta. Daga Nan suka wuce gida.
Daren ranar kwana sukai suna Shan soyayyar. Wanda Fateema har tsoro Fauwaz ya dinga bata. Yadda yake Mata kamar bai taba sanin ta ba. Sunbatu da kuka gashi kamar zai maida ta cikin. Har goshin asuba suna Abu daya sai da yaga ta galabaita ya sarara mata ai kuwa ko Alwala batai ba bare wanka Bacci ya dauke ta.
Fauwaz kuwa da yai wanka dawowa yai ya Kura Mata Ido. Addu’a yai Mata ya koma kan sallaya. Kwana yayi akan sallaya. Dan da aka kira assalatu ma shi ya tashe ta ya taimaka Mata Tai wanka ya tafi. Tana idar ta dawo ta kwanta.
Shima Sai da ya dawo ya koma yai bacci. Karfe takwas ta tashi da sauri ta shiga kitchen ta fara hada Hadar daura abincin safe.
Karfe goma ta Gama Tai wanka ta shirya cikin atamfa Mai kyau. Tai dauri ta Kara Yin kyau.
Tana gaban mirrow ya karaso ta juya tana kallon sa cikin Shirin sa na manyan Kaya. Yai Mata kyan da bai taba Mata irin shi ba.
Murmushi tayi ta karasa tana fadin
“Yaya na ka ganka kuwa kamar sabon ango yau kayi wani kyau na daban.”
“Angon kine Baby. Yadda kike ko da yaushe sabuwa ce a waje na haka yasa nake zaton kamar kullum a leda nake bare ki.”
Ya kamo hannun ta Yana fadin
“Dan Allah menene sirrin? Kullum a sabuwa nake Jin ki tamkar a lokacin nake Kara sanin ki with a special test Baby.”
Hannu ta daura akan bakin sa tana fadin
“Yaya kana ban kunya.”
Ta fada tana juyawa baya. Ya daura kan sa a kafadar ta yana fadin
“Wai kunya yau ni ake Jin kunya Baby.”
“Kai Yaya ai kullum Ina Jin kunyar ka.”
Ya juyo da ita yace
“Da gaske?”
Dagowa tayi ta Harare shi tace
“Ni kake tambaya.”
Kan gado ya zauna yace
“Haka ne fa. Na Tina Baby na akwai kunya wanda ita ke Kara Miki kyau. Ina kaunar ki Baby da sonki zan mutu.”
Ya daura hannun sa a kan cikin ta yace
“Ina kaunar ka Baby na. Ina ma Zan kasance dakai da na nuna maka so da kauna.”
“Me zai hanaka kasancewa dashi.”
Janyo ta jikin sa yayi ya hade bakin su. Wani kalar kiss ya fara bata wanda bai tabai mata shi ba. Nan da nan ya kashe mata jikin ta.
STORY CONTINUES BELOW
Ta shiga maida Masa da martani. Nan suka jiyar da Junan su wani dadi. Sai da ta farai Masa kukan yunwa ya kyale ta. Wanka sukai Bata saka komai ba da towel ta fita falo ta hado tea. Shi tasha sannan ta mike Sai ga Yaa Fauwaz Nan ya shigo sanye da kayan sa daban ba Wanda ya cire ba.
“Ina Zaki?”
“Kaya Zan saka!”
Ya kamo ta ya yo dining ya zauna ya daura ta akan cinya abinci ya fara Bata tana ci Shima Yana ci. Yana gamawa ya dauke ta sukai daki.
Akan gado ya ajiye ta ya dauko Mai ya fara shafa mata. Baya ta juya ya lakata Amman sai ya mike da aika Mata da wani Abu ta Bayan ta.
Nan ta fara Mika Dan yadda sakon ke shigar ta. Nan ta shige jikin sa. Haka suka Kara samun nutsuwa sai da suka nutsu suka Shiga Dan suyi wanka.
Suna fitowa ta tsaya a gaban Mirrow zata shafa Mai. Ya fito Yana aika Mata da wani kallo. Kallon sa tayi tace
“Yaya Wai wannan fitinar dake idon ka ta Taki ta kyale ka.”
“Na kasa samun gamsuwa dake ne. Mararin ki nake. Bana son na takura Miki ko Dan unborn Baby na.”
Tai murmushi tace
“Yaya kenan am all yours ko kana son na daga tafiyar ne?”
“No no no ba za ai haka ba zamu tafi zuwa anjima.”
“Hmm in da takura Yaya na hakura zuwa wani lokacin.”
“A’ah Baby na. Ki karasa Shirin ki zuwa Sha biyu zamu daga.”
“Toh!”
“Ko na shafa Miki man ne?”
Ya fada yana kanne mata ido daya.
Tace
“Hmm in kana so.”
“A’ah Kar Baby na yace Dady ya fiya takura.”
Tai murmushi ya shafa Mai ya shirya ya fita. Yana fita yaga Gloria ta taho daga parking space tana Kad’e hannayen ta.
Kallon ta ya tsaya har tazo wucewa ta sashen Fateema ta dago sai sukai Ido hudu da Fauwaz da sauri ta nufi sashen ta tana zuwa ta shige kitchen ta wanke hannun ta.
Bayan ta ya biyo yana shiga ya tsaya kallon dakin. Annur ne ya fito yana ganin Dady ya zo ya gaishe shi yace
“Dady Ina Mum?”
“Tana daki!”
“Dady naje na gaishe ta?”
“Jeka.”
Ya fita a guje. Yana fita Gloria ta fito tana goge hannun ta da karamin handkachief.
Kallon ta ya tsaya ta fito ta zauna akan kujera. Ya Kara kallon ta sai ya matsa Yana kallon ta. Yace
“Me Kika fita kikai a parking space!”
“Ban gane ba shikenan ni bazan fita ba?”
“A’ah ai Naga bakya fita ne.”
“Yau to na fita shine me?”
Murmushi ya saki Dan ya manta yaushe rabon ta ya bashi amsa kamar haka. Wannan yasa ya ji dadi yace
“Is ok yanzu kin tashi lafiya?”
“Ina ruwan ka?”
“Haba Gloria mijin kine fa Wanda kike so Fauwaz ko na canja Miki ne?”
Kallon sa ta tsaya yi, yace
“Kiyi hakuri in Ina Miki ba dai dai ba Amman ki sani kamar yadda nake son Fateema kema Ina son ki kace fa uwar ‘da na Wanda nafi so haba Gloria kina tausayi na Mana. Kinsan Ina son ki da kinfi mutunci. Please ki dawo kamar da macece Mai hakuri da mutunci da tausayi Amman yanzu kin daina tausayi na fa meyasa?”
Kai tayi kasa dashi yace
“In na Miki ba dai dai ba ki yafe min. Auren Fateema da nayi addinin mu ya yadda Kuma kada ki manta Ina son ta. Na dawo na same ta cikin matsanacin Hali auren ta da nayi ya ceto ta bakya ganin zan samu lada Kuma iyayen ta da nawa sunji Dadi. Fateema na da hankali da hakuri Bata da hayani ko bana Raye ita Mai kula dake da Anjur ce in Kika Bata dama Zaki gane hakan.”
Nan ma shiru tayi yace
“Ki zo mu zauna zaman lafiya nawa rayuwar duniyar take. In mune gobe ba mu bane. Dan Allah kiyi hakuri kizo mu zauna lafiya Gloria my love.”
STORY CONTINUES BELOW
Kai tayi kasa dashi. Yai murmushi yayi yace
“Any way yau zamu tafi Zan maida Fateema kan na tafi Ina neman yafiyar ki, ki yafen Kinji.”
Batai magana ba ya dago ya kalle ta ya mike ya zaro kudi a aljihu sa ya dire Mata yace
“Sai na dawo.”
Ya juya ya fita. Bangaren Fateema ya Shiga ya dauko akwati Nan ta ya saka a mota sannan ya koma suka fito ya kamo ta suka Shiga Bayan mota. Driver da Annur suna gaba. Driver ya tada motar suka fice. Fauwaz ya fita Yana kallon gidan.
Annur dake gidan gaba yace
“Dady ba da Mom zamu ba?”
“Eh Kai ka koma Kano ma kenan.”
“But Dad banyi sallama da Mom ba.”
“Kwayi waya!”
Fateema ce ta kalle shi tace
“Yaya Bata san tare zamu tafi ba kenan.”
“Kinsan halin ta. Yanzu zata ce Bata yadda ba. Amman yanzu in na dawo na fada mata.”
“Amman Yaya da ka fada Mata ko?’
“Don’t worry komai zai Yi normal na fara ganin canji a tare da ita.”
“Allah yasa.”
Ta kwantar da kanta a jikin kujera ta lumshe Ido. Janyo ta jikin sa yayi ya gyara Mata kwanciyya ta lumshe Ido suna tafe suna Hira har Bacci ya dauke ta.
Har ta farka taji hannun sa a kan cikin ta. Ta Waiwayo tana kallon sa. Tace
“Yaya!”
Kiss yai Mata a goshi Yana fadin
“Ina Jin lafiyar Baby nane!”
Murmushi tayi tace
“Annur Bacci yayi ne?”
“Eh!”
Ta daura hannun ta akan hannun sa tana fadin
“Ni dai Yaya in na Haifa maka Baby nasan shi zaka fi so.”
“Ita dai zan fi so. Amman ba xanfi son ta akan ki ba.”
“Kar kasa na fara kishi da ita fa.”
“Babyn tamu?”
Baki ta turo ya duka yai kissing lips din ta yace
“Ina kaunar ki Baby na.”
“Me too!”
“Allah Miki albarka!”
Tace
“Amin!”
Ya dauko mata maltina ya mika mata yana fadin
“Baki fara jin yunwa bane?”
“Wallahi na fara naga ban dauko komai bane.”
Bari mu shiga Kaduna sai a samar miki wani abu ko?”
“Malt din ma is ok Yaya.”
“No Baby na fa?”
Tai murmushi.
Sha tayi ta koma jikin sa ta lafe kamar me bacci shi kuma yana shafa bayan ta a hankali
*
Sun gauta kaduna driver na sharara gudu yazo wani waje ya hangi wani Rami. Burki yazo ya Danna Amman ya dannan yaki dannuwa suna Shiga Ramin wani karfe ya caki tayar ta fashe take motar tayi ciki daji ta bugi wata bishiya take gaban ta ya kama da wuta duk yan ciki suka sume sakamakon.buguwar da sukai.
Wata mota da tazo wucewa ta hangi motar su Fauwaz na cin wuta. Da sauri suka tsaya suka nufi motar duk a sume suka fito dasu.
Nan aka Kira motar emergency take suka wuce dasu asibitin Kano Dan sun kusa shigowa sosai.
*
**
***
****
*****
******
*******
********
*********
**********
************
Bayan ta kawo Masa ta koma gefen Mamah Yana ci suna Hira. Har ya gama ya kalli Aisha yace
“Mu tafi ko?”
“Ni anan Zan kwana!”
Mamah ya kalla yace
“Mamah Dan Allah haka ake Yi?”
Aisha ta kalla tace
“A’ah Aisha tashi kibi mijin ki sai da safe!”
A hankali ta mike tace
“Sai da safe.”
“Allah bamu alheri.”
Ta fita ya mike yai wa Mamah sallama ya fita. A hanya ya same ta ya karasa yace
“Da ki tsayani.”
“Allah Sweetheart ka daina bani kunya!”
“Me nayi?”
“Gashi Nan.”
Janyo ta jikin sa yayi ya daura kan sa akan kafadar ta yace
“Ko?”
STORY CONTINUES BELOW
Ya zura hannu ya dago ta ya dauke ta. Kafa ta fara wuntsilawa tana fadin
“Ni dai ka sauke ni.”
Bai kula ta ba suka shige bangaren su. Bai ajiye ta a ko Ina ba sai akan gado.
Nan ya fara romancing nata tin tana nokewa har ta bada Kai bori ya hau.
Washe gari da safe suka d’aga. Haka suka koma suka cigaba da soyayyar su tana kula dashi Yana kula da ita.
Satin da suka dawo ta fara wani zazzabi da ciwon Kai sosai abin ya fara damun ta tin tana boyewa Aliyu har ya gane haka ya tada hankali
Yana dawowa ya ganta ta sanye da riga Mai dogon hannu da dogon wando. Saboda yanayin zazzabin da take ji. Yana rumgume ta yaji jikin ta da dumi yace
“Baby love jikin ki zafi fa!”
“Weather ne kawai Sweetheart!”
“A’ah fa yau kwana biyu kina fada min haka fa.”
Tai murmushi ta Kama hannun sa tace
“Kaga muje ka watsa ruwa kada a Kira magariba a Ina ka tsaya yau ma?”
Tayi gaba. Hannun ta ya janyo ya jingina da bango Yana bin ta da kallon sai Kuma ya zura hannun sa a cikin rigar ta yaji zafi.
Daukar ta yayi ya ajiye Akan kujera tare da daukar wayar sa ya fara neman layin Doctor su.
“Please kazo gida yanzu!”
“Ok Sir.”
Ya kalle ta yace
“Me yake damun ki?”
“Ni fa ba komai!”
Ido ya tsare ta dashi tace
“Yaya zazzabi ne fa kawai.”
“Meyasa Kika boyan!”
“Bana son ka damu me.”
“Kinsan rashin sanin ai zai fisa na damu ko?”
“Kayi hakuri love Amman ya ma fa daina na Sha paracetamol. Kasan me?”
“A’ah.”
“Gobe Mujahida zata zo fa.”
“Ah haba lallai kina da bakuwa gobe.”
“Muna da ita dai Kuma ma ai Mujahida ba bakuwa bace Yar gida ce.”
Hancin ta yaja yace
“Ya kike ji yanzu?”
“Yaya ni fa normal.”
“Ba wani normal kalli fa yadda Kika fada Amman shine Baki fadan ba nake takura Miki ko?”
“Kai Baby ai Zan iya mn.”
“Ni dai kada ki Kara.”
Kunne ta kama tace
“Insha Allah. Muje kai wankan ko?”
“No sai yazo ya duban ke. Kila ma yawan aikin da kike Yi ne.”
“Ba ruwan aiki Yaya.”
“Bari yazo Allah in yawan aiki ne kin daina.”
Kiran sallah magariba Yasa ya mike yai Alwala itama tayi sannan ya tafi masallaci.
Tare suka dawo da Dr. Ya Shiga ya Kira ta, ta fito Sanya da hijab har kasa. A kan two sitter suka zauna ya farai Mata tambayoyi ta bashi amsa. Jinin ta ya dauka yace zai je ya dawo.
Bayan isha’i Aliyu na dining Yana cin abinci Aisha na Shan hadin da tayi na Zuma da Aya da Madara tana Sha Dr ya dawo. Hijab ta saka ya shigo. Falo suka koma ya zauna Yana murmushi yace
“Congratulations Sir your wife is pregnant!”
Ido ya zaro yace
“What?”
Kai ya gyada yace
“Yes!”
Juyawa yayi Ya rumgume ta Yana fadin
“Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah Allah nagode maka Allah ka bani yara na gari masu albarka.”
Ya mike yai sama ya dawo da check na kudi masu yawa ya Mika Masa yace
“Nagode Doctor yanzu ka Bata magani zazzabin nan na damun ta sannan me kake ganin zata daina aikin nan bai daga cikin ciwon nan kuwa.”
“Kai Sweetheart Dan Allah.”
Ta kalli Doctor tace
“Wai Dan aikin gida ne Shima fa dakin mu kadai nake sharewa sai girki Amman ba abinda nake komai yi ake ya hana ni “
Yai murmushi yace
“Ba matsala wannan akai stage din da in taje za ana cewa tana motsa jikin ta ma. Zan Bata magani da zai Kara Mata jini da lafiya. Allah ya inganta.”
“Amin!”
Ya Kama hannun ta Yana sakar Mata murmushi. Magani ya Bata ya mike Aliyu yai Masa sallama.
Washe gari kuwa shi yayi komai. Break ma hanata hadawa tayi sai lallabata yake kamar kwai. Da Rana Sai ga Mujahida nan Aisha tai ta murna ta cika Mata gaba da kayan motsa Baki bayan ta gama ta Kai ta dakin da zata zauna.
Suna zaune kan yamma zazzabi Mai zafi ya rufe Aisha. A haka Aliyu ya dawo ya same ta hankalin sa ya tashi Nan ya Kira Dr ya fada Masa. Dr yace ba wata matsala a sannu zata daina tana Shan maganin da ya Bata.
*
Hajara ta Shiga tashin hankali Dan da ta je gida wajen su Momy ma a falo suka shanya ta Basu fito ba daga baya suka aiko ace Mata ba zata samu damar ganin su ba.
Washe gari da ta zo shine ta samu Sha’awa zata tafi gidan Aisha kamar yadda suka shirya ita da Momy dan su fara aikin su na bata maganin hana daukar ciki.
Wani kallon suka bita dashi. Hajara ta zauna tana fadin
“Ina Kuma Zaki?”
“Gidan Yaa Aliyu!”
“Wanne Yaya Aliyun?”
“Wannen kika sani tsohon mijin ki.”
“Me zakije kiyi? Na zata zaki tayani kishi.”
“Ni da gidan wana!”
“Haba Sha’awa gidan Aliyu wajen Aisha fa kenan ke da kike tayani kishi.”
Wata Dariya tayi tace
“Wa ya fada miki tayaki kishi nake. Ina kishin dai dake da Aishan!”
“Kamar ya?”
Ta Kuma sakin wata dariyar tace
“Ke bari na fito Miki a mutum ni bana son ki wallahi Sam. Ina tare dake ne kawai dan na rabaki da Aliyu Kuma Alhamdulillah cikin sauki kin rabu dan haka yanzu zanje na raba Aisha dashi kamar yadda na rabaki dashi. Dan haka ina son na fada miki kada ki Kara shigo nana nan dan ba gidan ku bane.”
Ta juya ta kalli Momy tace
“Na tafi.”
Ta fita ta bar Hajara tsaye ta kasa tunanin komai ma.
*
Suna zaune a falo da kyar ta sa Aliyu ya tafi aiki. Wanda take kwance Mujahida na kitchen tana soya Mata wainar fulawa. Wayar Mujahida ce tai Kara tana dubawa taga Shu’aibu dauka tayi yace
“Ina waje fa.”
“Gani nan to.”
Ta fito da plate ta ajiye Mata tace
“Bari na canja Kaya Shu’aibu yazo Yana Waje.”
“Oh ba zai shigo ba.”
Ta fada tana cin wainar.
“Zai shigo man bari naje Kar na shanya shi a Waje.”
Tayi dakin ta. Bata jima ba ta fito. Twce
“Bari naje.”
“Kice Dan Allah ya shigo.”
“To.”
Ta fita. A bakin kofa suka hadu da Sha’awa zata shigo da kallo ta bita. Wani kallon banza Sha’awa ta sakar mata. Ta bangaje Mujahida
Ido ta zaro tace
“Ikon Allah.”
Ciki ta shige. Ta bita da kallon Mamaki to me ya kawo Mujahida gidan.
Gate ta ji an bude ta kalla taga Yaya Aliyu ne. Shu’aibu ne ya Karasa ya fito yace
“Ah yau Kaine a gidan?”
“Wallahi nazo wajen Mujahida.”
“Au bama gun Baby love ba ko?”
“A’ah Yaya har ita.”
Yai murmushi yace
“Shikenan!”
Ya karaso wajen Mujahida yace
“Menene tsakanin ku ne?”
“Kai Yaya zumunci kawai!”
“Kema fada.”
Yai ciki. Aisha na cikin cin waina taji sallamar Sha’awa. A tsorace ta dago tana amsa sallamar.
Murmushi Sha’awa ta saki tace
“A’ah Antyn mu ya naga kamar bakya murna da zuwa na.”
“A’ah sannu da zuwa Bismillah!”
Ta zauna tana fadin
“Ya hanya?”
“Alhamdulillah!”
Ta mike tana fadin bari na kawo miki lemo da ruwa.
Tayi firij ta dauko mata ta ajiye Akan tray da cup tazo a ajiye Mata.
Zata koma ta zauna taji sallamar Aliyu da sauri ta dago tana amasawa.
Aliyu tsaye ya bude Mata hannu. Da sauri ta karasa ta fada jikin sa. Ya rufe hannun Yana kissing wuyan ta.
Sha’awa dake kallon su taji kamar zuciyar ta zata buga. Daukar ta yayi ya karasa dakin ya dire Akan kujera yana fadin
“Sha’awa dake kallon su taji kamar zuciyar ta zata buga. Daukar ta yayi ya karasa dakin ya dire Akan kujera Yana fadin
“Me kike ci?”
Ya dauko plate din. Tace
“Wai Sweetheart har ma yaushe ka fita.”
“Tunanin ki ya hanani na sake dole na dawo naji dumin jikin ki naji ya ajiya ta take?”
Hancin sa ta ja tana fadin
“Kai Love!”
Ya ajiye plate din ya fara kissing nata. Gyaran murya Sha’awa tayi da sauri suka dago suna kallon Sha’awa.
Fuskar Aliyu ya Bata. Ta saki murmushi tace
“Ina yini Yaya?”
“Lafiya kece yau a gidan?”
“Wallahi nace Bari nazo na gaida Antyn mu.”
“Kin kyauta!”
Ya mike Yana kamo hannun Aisha. Plate din ta dauka sukai sama. A bedroom suka zauna ta fara cin wainar.
Ya zauna Yana kallon ta yace
“Menene wannan?”
“Waina zaka ci ne?”
“A’ah a’ah ai sai ku.”
“To shikenan ka bar Dadi.”
“Wai me ya kawo Sha’awa ne?”
“Nima ban sani ba Bakaji me tace ba?”
“Ni dai bana son ki yadda ta shige Miki.”
“Haba Yaya Yar uwar kace fa.”
“Duk da haka.”
“Naji to.”
Sai ta ajiye plate din tana bata fuska tare da daura hannu akan kirjin ta yace
“Ah lafiya?”
Da sauri ta mike tayi bandaki kan ta karasa ta fara shara amai. Nan ya bi Bayan ta ya kamata Yana Mata sannu. Bandaki ya kai ta ya gyara jikin ta ya cire Mata kayan jikin ta. Kan gado ya kawo ta ta kwanta ta lulluba da bargo saboda zazzabin da take ji.
Shi ya gyara wajen ya dauko Mata Kaya ya saka Mata. Nan wani Aman ya Kara zuwar Mata. Kan ta Kara tashi ta Kara sakin wani Aman. Sai da tayi Aman fin sau uku duk hankalin Aliyu ya tashi.
Ya Kira Doctor yace gashi Nan. Bai jima ba ya zo har dakin ya kawo shi. Yace
“Me taci?”
“Gashi Nan yana da matsala ko?”
Wainar ya kalla yace
“A’ah kawai tambaya nayi.”
“Ok yanzu ya za ayi sai amai take.”
“Bari ai Mata allura ko?”
“To!”
Ya fada ya karasa wajen Aisha tace
“Baby love ayi allurar?”
Kai ta gyada tana rawar sanyi. Ya dago ta ya daga rigar ta ya zame zanin jikin ta ya soka Mata allurar ta shige jikin sa tana sakin Yar Kara. Ya fara mulmulawa Yana Mata sannu.
“Zazzabin fa Doctor!”
“Tasha Paracetamol ya Isa ma.”
“Ba wani Abu da za a Kara?”
“Kar ka damu zai sauka. Na sauyin da ta samu ne.”
“Ok shikenan!”
“Allah Kara sauki.”
Ya fita. Sannu ya dingai Mata. Sunyi minti ashirin sannan zazzabin ya sake ta. Sai gashi ta mike tana fadin
“Yaya muje kaci abinci.”
“No Love kwanta ni bana Jin yunwa.”
“Haba dai me kaci.”
“Kawai.”
Ya Mai da ta ya kwantar. Aisha ta ce
“Ni Yaya muje please!”
STORY CONTINUES BELOW
*
Mujahida da Shu’aibu ne suka shigo. Ya kalli falon tace
“Bismillah.”
Ya koma ya zauna. Ta harari Sha’awa tayi sama. Dakin da suke tayi knocking. Aliyu yace
“shigo.”
Shigowa tayi ta kalli Aisha tace
“Ah lafiya?”
“Wallahi sai amai take yanzu Dr yai Mata allura ma kuma zazzabi ne a jikin ta.”
“Ayyah sannu Antyn mu. Daman Shu’aibu ya shigo ku gaisa.”
Da sauri ta dire kafa a kasa tana fadin
“Haba Bari naje.”
Kamo hannun ta yayi Mujahida ta fita yace
“Kiyi a hankali.”
Kai ta langabar ya mike ya Kama hannun ta. Suka sauka.
A kasa suka same su har Sha’awa. Aisha tace
“Lah mun barki nan ko. Please Mujahida nuna Mata dayan dakin da ke kusa da naki sai ta zauna.”
“Ok Antyn mu!”
Ta kalli Sha’awa tace
“Muje!”
Ta mike suka tafi Aisha tace
“Ki watsa ruwa sai kizo ki ci abinci.”
“Ok!”
Tayi ciki. Suna shiga Aisha ta kalli Shu’aibu tace
“Yaya nayi fushi.”
“Am sorry Kanwata yaushe na dawo dududu.”
“Ni ba wani Nan zuwan Mujahida ya kawo ka.”
Mujahida na kai ta dakin tace
“Ni ban San me ya kawo ki gidan Yaya ba Allah dai ya tsare Mana Antynmu.”
Tana fada ta fita
*
A falo suka zauna suna Hira. Sai yamma sannan Shu’aibu ya tafi yacewa Mujahida zai dawo da dare.
Lokacin da zasuyi sallah magariba tana Alwala ta tado da zazzabin ta. Dan da kyar Tai sallah ta haye kan gado ta rufa da bargo. Har akai isha’i tana kwance
Sai da ya dawo yaga Bata falo sai Sha’awa. Tana ganin sa ta mike tana gyara riga tare da turo kirji shi ko Lura da itama bai ba. Ya nufi stair tace
“Yaya?”
Juyowa yayi tace
“Sannu da zuwa.”
“Yauwah!”
Kawai ya fada yai sama. Ta koma ta zauna tana tsaki. Mujahida da ta fito daga dakin ta saki Dariya tana fadin
“Iska na wahal da me kayan Kara. Wallahi Yaa Aliyu yafi karfin ki nidai nasan ba zuwan Allah kikai ba.”
Wani kallon ta wurga Mata Tai sama.
Aliyu na Shiga ya same ta kwance Akan gado Nan ya Isa da sauri. Yana bude ta.
Jan bargon tayi tana kuka yace
“Zazzabin ne?”
Kai ta gyada ya dafa kanta yace
“Sannu Baby love.”
Kai ta gyada. Yace
“Me Zaki ci kan Kisha magani?”
“Ni Fura nake so!”
Knocking akai Aliyu yace
“Waye shigo!”
Mujahida ce ta shigo ta ce
“Ah lafiya Kuma?”
“Wallahi zazzabin ne ya dawo!”
Ya fada kamar zai kuka!
“Ayyah sannu Antyn mu!”
Kai ta gyada yace
“Please Mujahida samo mata fura ta Sha.”
Ta amsa masa ta fita. Kitchen ta shiga ta debo mata a wacce aka dama Masa. Tayi sama amsa yayi ya Bata tana gamawa ya balli magani ya Bata
*
Tana Sha ta dafe kirji. Yace
“Lafiya!”
“Amai nakeji.”
Janyo ta yayi jikin sa Yana shafa bayan ta a hankali.
Aman ne ya yunkuro ta janye jikin ta da sauri tayi bandaki a guje.
*
Nan ta hau kelayashi. Yabi bayan ta yana shafa Bayan ta gama ya dauraye Mata Baki sannan ya dauko ta ya ajiye ta akan gado. Bandakin ya shiga ya gyara sannan ya dawo ya kamo hannun ta yace
“Me Zaki ci to?”
Kai ta girgiza yace
“Haba dai ba abinda kikaci fa tin Rana.”
“Ni bana Jin yunwa.”
“Sannu to. Ba abinda kike Sha’awa.”
STORY CONTINUES BELOW
Kai ta gyada. Take Bacci Kuma ya dauke ta. Yana zaune a wajen Yana ta kallon ta. Mamah ce ta Kira suka gaisa ta tambayi Aisha. Kallon ta yayi yace
“Mamah Aisha Bata da lafiya yau sai amai take Yi komai taci.”
“Subhanallah Jikin ne?”
“Eh!”
“To gobe Zan zo na duba ta. Allah Bata lafiya.”
“Amin.”
“Tana Ina?”
“Bacci take!”
“Ok ai Mata sannu!”
“Zataji.”
Ya kashe wayar. Mikewa yayi ya Shiga Tai wanka ya fito ya saka kayan baccin sa. Zaune ya same ta ya karaso yace
“Kin tashi Baby love?”
Kai ta gyada ta ce
“Yaya me kaci?”
“Ba komai!”
Kafar ta, ta saukar tace
“Bari na kawo maka abinci!”
Kamo hannun ta yayi yace
“A’ah Yi zaman ki Bari Zan dauko fura.”
“A’ah Yaya baka ci komai bafa tin dazu Kadan kaci abincin!”
“Barshi Zan dauko.”
“Dan Allah ka Bari na kawo maka.”
Sakin ta yayi yace
“Ki kula!”
Ta gyada kai. Tana sauka taga Sha’awa ta zubowa stair kallo. Kai ta dauke tace
“Kina zaune na barki ke kadai ko?”
“Wallahi fa.”
“Wallahi zazzabi ya kwantar Dani Ina Mujahidar ai da kunyi Hira.”
“Ta fita ne!”
“Ok kinci abinci to.”
“Eh naci!”
“Ba abinda kike bukata?”
Kai ta gyada. Ta wuce kitchen ta daukar wa Aliyu abinci sa ta fito tai Sama. Akan carpet ta ajiye ta zuba Masa. Sai da yaci sannan ta mike tayi Alwala tai sallah.
Lafiya suka kwana Amman da safe ko kitchen bata samu ta leka taga me ake girkawa ba saboda zazzabi. Aliyu na kanta a tsaye duk ya rasa Yaya zai Yi. Ya Kira likita yazo ya saka Mata ruwa ya tafi.
Karfe Sha biyu ya zare Mata ta tashi a Bacci ruwa ya hada mata Ttai wanka sannan ta zauna ya kawo Mata tea da dankalin da aka soya. Dan kalin kawai taci ta Sha magani. Nan taji zuciyar ta, ta fara tashi ta Bata fuska yace
“Menene?”
Kai ta girgiza sai ta daura hannun ta akan bakin ta, ta mike a guje tayi Bayi. Kai ya girgiza ya mike yabi bayanta. Amai take ta shararawa. Bayan ta gama ya wanke bakin ta ya dawo da ita ya gyara wajen.
Dr ya Kira yana dauka yace
“Am sorry Dr wallahi Aman nan yaki ya tsaya da taci Abu fa Sai ta dawo dashi.”
“Ikon Allah.”
“Wallahi.”
“Aman ne sai a sannu zai lafa Amman zan zo ko allura ce ai Mata ko?”
“Dan Allah kazo.”
“To gani Nan.”
Kofa sukaji ana Knocking ya mike zai bude tace
“Yaya Bari na bude.”
“Haba Baby love Yi zaman ki.”
Ya mike ya bude kofa Yana budewa yaga Mamah da sauri ya matsa Yana fadin
“Sannu da zuwa Mamah!”
Ciki kawai ta shige tana fadin
“Yauwah Ina Aisha?”
Aisha na Jin sallamar ta mike ta dire kafa. Mamah tace
“Yi zaman ki Aisha.”
Ta sauka ta durkusa. Mamah ta karasa ta dago ta. Maryama da Mujahida suka shigo tace
“Ya jikin?”
“Da sauki Mamah. Ina yini? Ya hanya?”
“Alhamdulillah!”
Maryama ta karaso tana fadin
“Allah sarki sister har kin fada kuwa. Sannu ya jikin?”
“Da sauki ya kike ya hanya?”
“Alhamdulillah!”
Ta mike tace
“Bari na kawo muku ruwa ko?”
“A’ah dawo Aisha zamu dauka da kan mu ke da Baki da lafiya.”
“Mamah ai naji sauki.”
STORY CONTINUES BELOW
“Wallahi Mamah haka take yau tin safe fa zazzabi ya rufe ta yanzu ne ma ya suaka tai wanka Shima tana karyawa ta amayar Amman sai tace za tai aiki.”
“A’ah Aisha kina bi a sannu fa.”
“Toh Mamah. Dan Allah ki Bari na kawo muku.”
“Haba Aisha ki zaman ki Dan Allah.”
Mujahida ta sauka ta kawo musu lemo da ruwa da abinci anan suka faraci. Sai da suka Shiga suka watsa ruwa sannan suka fito suka zauna a falon sama har da Aisha dake kwance Akan kujera bayan likita yai Mata addu’a.
Sai yatsina fuska take. Mamah na Lura da ita. Tace
“Yadai Aisha?”
Mikewa tayi Tai daki a guje Aliyu ya bi bayan ta. Amai ta shiga tana yi Yana wanke Mata Baki ta fito ta fada saman gado tana Mai da numfashi.
Aliyu ya fito fuskar sa kamar zai kuka yace
“Sannu Aysherr!”
“Yauwah Yaya!”
Ta fada tana lumshe idon ta. Fita yayi yaje gun Mamah. Mamah tace
“Ya dai?”
“Mamah ni Aman nan na damu na ba wani abinci fa take ci ba.”
Aisha ce ya fito ta koma ta zauna Kai ba kace ita bace taje tai amai.
“Aliyu sai a sannu fa.”
“Yanzu ba wani Abu da za ayi!”
“Hmm Baba na kenan.”
Sha’awa ce ta shigo dakin. Mamah ta bita da kallo. Dan bata San tana gidan ba.
Takaraso tana fadin
“Mamah Ashe kunzo ya hanya?”
“Alhamdulillah!”
“Wallahi Bacci nake sai yanzu na tashi Naga su Maryama a kitchen.”
Ta kalli Aisha tace
“Ya jikin Antyn mu?”
“Da sauki.”
“Allah Kara sauki.”
“Amin!”
Ta kalli Aliyu tana kashe Ido tace
“Yaya Ina kwana?”
“Lafiya!”
Ya fada Ya nufi gun Aisha Yana taba jikin ta. Yace
“Sannu Heartbeat!”
“Yauwah!”
“Baby love me Zaki ci?”
Kai ta girgiza ya kalli Mamah yace
“Mamah me za a Samar Mata taci?”
“Bari naje kitchen din Naga.”
Ta mike ta sauka. Ya dago Aisha ya saka ta a jikin sa. Sha’awa dake zaune ta mike ta bar falon a fusace.
Daki ta Shiga ta dauki waya ta Kira Momy. Tana dauka yace
“Momy kamar fa ciki ne da Aisha yanzu ya zanyi?”
“Ciki Bayan Wanda Hajara ta zubar?”
“Eh wallahi.”
“Ai kawai Kisan yadda zaki zubar dashi!”
“To Momy tayaya?”
“Kije ki samo magani ko a chemist ne.”
“To sai anjima!”
Ta kashe wayar tana zaga dakin. Mamah na Shiga tayi Mata faten wake Wanda ta saka hanta da alayyahu da dankali.
Ta gama ta bawa Maryama ta Kai Mata. Aliyu da kan sa ya amsa zai Bata. Aisha ta girgiza Kai tace
“Yaya amai!”
“Ba zakiyi ba Aisha Kadan Zaki ci.”
Da kyar ya lallaba ya Bata ta fara ci. Ta danyi spoon uku ta dauke kai. Yace
“Dada Mana.”
Spoon daya ta Kara ta dauke Kai. Sai da sukai haka Sai uku sannan ya barta ta kwanta a kirjin sa Yana shafa Bayan ta. A haka har ya lafa Kuma batai aman ba.
Da dare ma kunu Mamah tai Mata tasha. Kwanan Mamah biyu ta koma Bayan taje ta gaida Umma.
Anan ta bar Maryama ta cigaba da kula da Aisha.
Tin da sha’awar taji Aisha na da ciki ta shiga tashin hankali sosai. Sai ta fara tunanin tayaya zatai ta zubar da cikin jikin ta, ta Kuma raba Aliyu da Aisha.
Aisha Kuma sosai Maryama da Mujahida suke kula da ita. Duk da da taci Abu take Aman sa.
Kwance take da safe Akan gadon ta. Bacci take sosai. Sha’awa ce ta shigo dakin ganin tana bacci yasa ta juya tana kallon kofa sai ta matso kusa da gadon tana Kara kallon kofa alamar dai rashin gaskiya.
STORY CONTINUES BELOW
Bakin gadon ta karasa aka budo dakin a tsorace ta juyo tana kallon kofar. Mujahida ce ta shigo hannun ta rike da plate ta soyo wa Aisha plantain. Kallon ta, ta tsaya yi.
Aisha ta bude idon ta tana kallon su. Sha’awa ta wayance tana fadin
“Uhmm Daman na shigo nai Miki sannu ne Naga kina Bacci. Ya jikin?’
“Da sauki!”
Ta juya ta fice ta gefen Mujahida.
Shigowa Mujahida tayi tana bin ta da kallo. Mikewa Aisha tayi tana fadin
“Yaa AK bai Gama training din ba?”
“Bai fito ba.”
“Me kuke dafa Masa.”
“Maryama ce keyi tana kitchen plantain din na kawo miki!”
Amsa tace
“Nagode.”
Ta mike ta shiga bandaki. Wanka tayi sannan ta fito ta shirya.
Aliyu na dakin training din sa aka budo dakin. Shi ya zata ma Aisha ce ya juyo Yana fadin
“Wai har kin tashi?”
Sha’awa ya gani tana sakar Masa murmushi. Fuska ya Bata tace
“Ina kwana Yaya?”
“Lafiya Lou!”
Ya juya ya cigaba da abinda yake. Shiru tayi can tace
“Yaya Daman gani nayi tinda ka saki Hajara me zai Hana ka Kara wani auren!”
Da sauri ya juyo Yana fadin
“What? Ni nace Miki Ina bukatar wata matar ne?”
“No Yaya Amman zama da Mata biyu Yana da fa’ida bama yanzu da Antyn mu ke laulayi dole ka nemi wani Abu ka rasa a wajen ta kaga in kana da wata matar zata taimaka maka.”
Wani kallo ya wurga Mata. Wanda yasa Tasha jinin jikin ta.
Yace
“Na fara Wasa dake ne? Malama get out of my side!”
Jiki na rawa ta fita a dakin.
Plate din plantain din ta dauka ta fita. Dakin training dinsa ta nufa a bakin kofa ta ga Sha’awa ta tsaya kallon ta, to me ta hau sama take musu Bayan dakin su na a kasa.
Tana ganin ta tace
“Lah kin fito kenan!”
“Eh!”
Ta bude dakin ta shiga da sallama. Juyowa yayi ya sakar mata murmushi tare da amsa sallamar tata ya mike ya karaso Yana fadin
“Kin tashi kenan!”
“Eh Yaya!”
Plate din hannun ta ya amsa Yana fadin
“Yau Kuma shi Zaki ci.”
Kai ta gyada ya zaunar da ita yace
“Tea fa?”
“A’ah!”
“To lemo fa?”
“Yauwah gwara shi a kawon na mixed fruit Yaya!”
“Ai akwai a firij din dakin Nan Bari na kawo miki.”
Ya mike ya dauko Mata lemo da ruwa ya ajiye Mata. Ta ce
“Zo muci.”
Ya dauki plate din yana fadin
“A’ah zo in Baki.”
Ya dauki fork ya fara Bata tana amsa.
Sosai taci sai kuma ta Bata fuska yace
“Menene?”
Hannu ta daura a kirjin ta ya dauko Mata sweet ya Bata ta amsa ta fara Sha sai taji ya lafa Mata tana shanyewa ta karaji Aman na taso Mata. Ba yadda ta iya da gudu ta karasa toilet ta fara Aman.
Yabi bayan ta Yana shafa Bayan ta har ta gama ya dauraye Mata bakin ta. Ya gyara wajen daukar ta yayi sukai dakin su.
Akan gado ya kwantar da ita ya kalle ta cike da damuwa Yana fadin
“Baby love Aman Nan na damu na.”
“Haba Yaya ai ba wani Abu bane.”
“Ni wani Abu ne a guna.”
“Muje na hada maka ruwan wanka ko?”
Komar da ita yayi yace
“A’ah Yi zaman ki.”
Ta bata fuska yace
“Yaya kana hanani abubuwa da yawa na samun Lada.”
“Baby Love ko kallon ki da nake Ina Jin Dadi ma Zaki samu lada. Allah Miki albarka kinji!”
“Amin Yayan mu.”
Yai kissing goshin ta ya mike ya shiga yin wanka. Tana kwance ya fito ta mike ta sauka ta dauki towel ta goge masa jikin sa ta dauko Mai yace
“Baby love bakya gajiya ko?”
“Ina aikin yake?”
“Hmmmm ai ke haka Zaki ce.”
Ta karasa ta saka Masa Kaya tana fadin
“Yaya Dan Allah ka koma aiki yau sati daya fa baka je ba.”
“Ina jinyar matata nane!”
“Ni lafiya ta kalou.”
“Ban yadda ba.”
“Allah please ka koma kaji Yaya.”
“Sai Monday!”
Ido ta zaro yace
“Yaya yau fa Tuesday!”
Ya hade kan su dogon hancin sa Akan nata yace
“Eh Mana!”
“Yaya ka tafi yau.”
“Korata kike Yi ko?”
“A’ah Yaya!”
Ya kamo hannun ta suka fita. A falo suka samu Maryama da Mujahida.
Dining suka nufa. Aisha tace
“Sannun ku da aiki ni dai kun hanani komai ko?”
“Ba ruwan mu Momy ce ai.”
“To ni naji sauki kuma Zan fada Mata.”
“Allah Kara sauki.”
Maryama ta fada tazo zatai serving din Aliyu. Aisha tace
“Ni ki barni nayi kada na sangarce ku tafi ku barni da aiki komai kuyi min ai abin yai yawa.”
Sukai murmushi. Tace
“Kedai kice Zaki serving mijin ki kawai.”
“Naji.”
Ta zuba Masa ta koma ta zauna yace
“Kefa?”
“Na koshi.”
“Dan plantain din da Kika ci?”
“Yaya duk wannan da naci.”
Ta kalli Maryama tace
“Ku zauna ku karya Ina Sha’awan ku kira ta.”
Kan Maryama ta tafi ta fito. Ta karaso dining din ta zauna a gefen Aliyu tana wani kwarkwasa. Ta kalli Aisha tace
“Antyn mu ke me Zaki ci? In dafa Miki.”
“No ni na koshi!”
“A’ah Anty ki Fadi ko menene Zan dafa Miki.”
“Yanzu na koshi anjima ko wanai lokacin naji yunwa Zan fada Miki. Yanzu kuci abinci.”
Aliyu ne ya gama ya mike Aisha ta mike tana fadin
“Yaya zaka je aikin ne?”
Ya kamo hannun ta yace
“Heartbeat!”
Ta fada jikinsa ya janye ta sukai sama. Maryama ta tabo Mujahida sukai Dariya. Mujahida tace
“Yaya da Antyn mu Yan soyayya.”
“Allah barsu tare.”
Tsaki Sha’awa ta saki ta mike tayi ciki. Mujahida ta saki Dariya tana fadin
“Banza.”
Gumi Mamah ta fara ta dauki waya tana neman layin Maryama amman ina bata dauka ba dan ta bar wayar a daki ita kuma tana wajen su Aisha.
Layin Mujahida ta fara nema a gigice amman shima ba a dauka ba. Layin Aliyu ta fara nema cikin tashin hankali.
*
Zaune suke suna hirar su sosai. Aliyu ya kalli Aisha yace
“Wai bakya jin yunwa ne?”
Fuska ta dan bata. Ya kalli Maryama yace
“Wayayi wannan kunun?”
“Nice nayi kuma ita tace tana so.”
Cup ya dauka ya zuba mata ya miko mata. Fuska ta bata yace
“Haba Baby love kisha ko yaya ne kinji Heartbeat ko akwai abinda kike so?”
Kai ta girgiza tace
“A’ah!”
Ya kai mata kofin baki kenan wayar sa ta hau kara. Maryama ce ta miko masa tana fadin
“Lah Mamah ce.”
Cup din ya sakar mata ya amshi wayar ya kai kunnen sa. Tare da sallama. Mamah ta amsa a firgice tana fadin
“Aliyu kana ji na?”
“Eh Mamah lafiya?”
Aisha da ta kurbi kunun ta hadiye da kyar tana dagowa jin a yadda ya tambaya dan daga muryar Mamah zaka san ba lafiya ba.
“Ina Aisha ya take?”
“Gata nan tana lafiya.”
“Ba dai abinda yake damun ta ko?”
“Eh Babu menene Mamah?”
“A’ah shikenan.”
“Dan Allah ki fada min Mamah.”
“Babu komai fa. ka kula da Aisha kawai ban yadda daga yanzu ta kara cin komai na cikin gidan nan ba.”
“Bangane ba Mamah!”
“Eh kada ta kara cin komai na gidan nan daga yanzu kanaji na.”
“Eh Mamah amman saboda me?”
“Ni dai na fada maka.”
“To shikenan”
Ya kashe wayar da sauri ita da Maryama suka ce
“Lafiya Yaya?”
Kallon su yayi yace
“Lafiya lou!”
Maryama tace
“Amman Yaya….”
Karar wayar sa ta katse mata maganar da zatayi ya duba Mamah ce ya dauka ya kai kunne sa. Mamah tace
“Ina Maryama?”
“Gata nan!”
“Bata wayar!”
Mika mata yayi ta amsa tace
“Mamah lafiya?”
“Lafiya lou ina wayar ki?”
“Tana daki.”
“Shikenan kina jina ko Maryama ki kula da yar uwar ki sosai. Ban yadda ta kara cin komai na gidan na ba har ruwa da lemo in tana so a fita a siyo kina jina ko?”
“Eh Mamah amman saboda me?”
“Ba komai kawai.”
Ta kashe wayar. Kallon Aliyu ta tsaya shi kuma ya dafe kai. Sai aka bar Aisha a cikin zulimi. Ta kalli Aliyu ta kalli Maryama da kyar ta bude baki tace
“Yaya lafiya wai?”
Hannun ta ya kama yace
“Ba komai fa.”
“Amman naga damuwa a fuskar ku.”
“Ba lomai fa.”
“To Allah yasa.”
Ta daga cup din ta kara kurbar kunun. Tana hadiyewa ta kara dagawa zata sha Maryama ta zaro ido ta mike da sauri ta amshi cup din hannun ta. Fuska Aisha ta bata tace
“Menene haka in sha zakiyi ba ga wani nan ba ki diba mana.”
STORY CONTINUES BELOW
Flask din ta dauke tayi kasa dashi. Aisha ta kalli Aliyu tace
“Yaya kai mata magana.”
“Kyale ta yanzu me kika so kici?”
“Ni kunun kawai nake so kuma na hannun ta.”
“A’ah banda wannan!”
Ta saka masa rigima nan ya hau lallashi da kyar tace
“To a yi min wani tinda ka hanani shan wancan.”
“Bari na fadawa Umma ai miki ko?”
Ya dauki waya ya fara neman layin Yaa Mustapha yana dauka yace
“Please kacewa Umma kunu Aysher ke so kuma garin ya kare tai mata yanzu zan zo na amsa.”
“Ok!”
Ya kashe wayar ta mike tana fadin
“Yaya tare zamu mu amso bari na watsa ruwa.”
“To ko nazo na tayaki.”
Kafada ta make tana fadin
“Naki wayon”
Tayi ciki. Wanka ta shiga tayi ta fito tana zaune a gaban mirrow ta fara shada mai taji cikin na murdawa. Baki ta cije tana taba cikin nata. Ji tayi kamar an soka mata allurori da sauri ta mike tana dafe cikin. Sai kuma taji ya lafa. Wardrobe ta karasa ta dauki kayan ta, ta saka ta dawo gaban mudubi zata shafa turare kenan taji cikin ta ya kuma sokawa sai kuma taji kamar ana jijjiga mata kayan cikin bata san lokacin da ta zube a kasa tana juyi ba.
Sosai cikin ke murda mata wanda yasa ta kwanta tana juyi rike da cikin ta bakin ta a cije ta kasa tashi bare ta kira Aliyu.
Yana zaune mitin goma bayan gama waya da Mustpha ya kira wayar yace
“An gama na kawo muku ne?”
“A’ah Madam tace tare zamu zo bari mu zo mu amsa.”
“Alright.”
Aliyu ya mike da niyyar shiga daki dan kiran ta. Maryama ce ta shigo tace
“Yaya ina Aishan?”
Tana daki menene?”
“A’ah ba komai.”
Ya juya yai ciki ita kuma ta zauna anan falon kofa ya bude yana fadin
“Ko kin fasa zu….”
Maganar sa ce ta tsaya ganin Aisha kwance a kasa tana juyi. Da gudu ya karasa yana kiran sunan ta abinda yaja hankalin Maryama kenan ta mike tabi bayan sa. Durkushe ta ganshi gaban Aisha yana fadim
“menene Baby love!”
Hannun sa ta kamkame tana fadin
“Yaya ciki na wayo zan mutu. La’ilaha illaha muhammad rasulillah.”
Sai jumfashin ta ya dauke take ya gigice yace
“Maryama fito mana da mota.”
Ya dauke ta a guje Shi ma ya rufa mata baya dauke da Aisha a hannu. Mujahida da Shu’aibu dake compound suka karaso suna tambaya lafiya. Ba wanda ya kula su Aliyu ya shiga baya shi da Aisha Maryam ta tada motar Mujahida ta shiga baya shuaibu ya shiga gaba.
Horn ta dannan mai gadi ya bude gate kan ya matsa ta fararo saura kadan tabi ta kansa. A guje ta fice a gidan ta hau titi sai government house.
Akan idon Sha’awa komai ya faru dan haka sai jikin ta yai sanyi. waya ta daga ta kira Momy tace
“Momy na shiga uku kada ta mutu.”
“To ai da zata mutu mu da yafi ma. Kinga ba ta rage mana wani abun ko?”
“Momy baki ga a yadda aka fita da ita bane kaar gawa.”
“To sai ki je ki tonawa kanki asiri ko?”
“A’ah.”
“To kiyi shiru kiyi pretending yanzu kije ki samu ki zubar da ragowar kunun in bata shanye ba.”
“Toh!”
Sama ta nufa ta duba falo ba flask din ta duba bedroom nan ma babu. Kitchen ta shiga ta duba nan ma babu kwata kwata. Sai ta tsaya tana tunanin to ina aka kai flask din. Daki ta koma ta kira Momy ta fada mata. Momy tace
“Ko an wanke ne?”
“To kila.”
“Shikenan yanzu ki dauki ragowar maganin ki kai dakin ta ki ajiye in komai ya lafa sun dawo gida sai ki tona mata asiri kice daman kinga tana sha kinji!”
“To Momy.”
Ta kashe wayar.
*
*
*
Mamah na gama waya da su Aliyu ta mike ta kalli Hajata tace
“Taho muje wajen Abbah!”
Ta mike tabi bayan ta.
STORY CONTINUES BELOW
Ba kowa a dakin sa sai shi kadai dan haka suka shiga suka zauna yace
“Ah Fulani an dawo.”
“Na dawo ranka ya dade.”
“Ya dai na ganki a haka.”
Hajara ta nuna masa ya kalle ta yace
“Ai Hajara ce.”
Kai ta gyafa ta kalli Hajara tace
“Yi masa bayani.”
Nan tai masa bayanin komai. sosai Abbah hankalin sa ya tashi tayaya za a ce da matar sa ake hada duk wannan abubuwan
“Innalillahi wainna illahir ajiun.”
shine kawai abinda Abbah ke fadi yace
“Yanzu ya za ai Hajiya?”
“Ai dole gobe muje can dukka azo nan a tara su.”
“Haka za ayi. Yanzu kin kira su Aliyun?”
“Na kira nace kada su bari taci komai na gidan.”
“Hakan ma yayi Allah ya kare ya tsare”
“Amin!”
“Bari muje sai da safe.”
Ta mike Hajara tabi bayan ta a hanya suka hadu da Momy zataje wajen Abbah dan ita ke da girki. Tana ganin Hajara tare da Mamah tace
“Ah Hajara ce a gidan namu.”
“Ita ce!”
“Kina lafiya dai ko?”
“Lafiya lou.”
Suka wuce daki ta bisu da kallo tana tabe baki
Suna shiga daki Mamah tace
“To Hajara dare yayi ko zaki kwana anan.”
“A’ah Mamah bance zan kwana ba a gida”
“Ban number na kira in sun.m matsa sai akai ki.”
Ta fara kiran layin nan Baban ta ya dauka. Mamah tai masa bayani cikin rawar jiki yace
“Ba ko.ai Allah kaimu.”
*
**
***
****
*****
******
*******
********
*********
Ranar Partyn anan suka kaddamar da komai da tarihin company inda suka ce su sun hada ne dan daga Fu’ad ba Dan kansu ba Amman shi Kuma yace Sam ba za ai haka ba domin kuwa yadda aka fara dole su Kare tare. Fu”ad ya samu ban girma sosai ba ga gwamnatin ba haka nan ba ga yan uwa abokan kasuwancin sa ba, sai da yai hawaye dan sai ya tino da yau Yana tare da iyayen sa da Fateema wane Dadi da farin ciki zasu Shiga.
Haka akai party lafiya aka tashi suka rankayya gida dasu Anwar da Maman sa da kanwar Anwar. Ranar a gidan ma walima sukai da dare.
Kwana biyun da su Maman Anwar sukai sun Saba sosai da Fu’ad haka Nusaiba da Fu’ad ya dauke ta tamkar kanwar sa uwa daya uba daya.
Ranar da zasu tafi suka kaisu har airport duk suka tafi suna Jin ba Dadi.
Daga Nan suka cigaba da gudanar da aikin su, cikin aminci tsakanin Anwar da Fu’ad.
*
Nusaiba tin da ta koma gida ta fara fuskantar matsala domin kuwa sai ta fada tunanin Fu’ad duk ta rasa nutsuwa Wanda har Mama ta gane ta na cikin damuwa Dan haka ta Kira ta. Zama tayi kanta a kasa.
Mama tace
“Me yake damun ki Nusy?”
Kanta ta Kara kasa dashi Mama tace
“Ki fada min Mana Auta ta!”
“Mama ban San ta Ina zan fara.”
“Zaki iya ta ko Ina Nusy Zan fahimce ki.”
Kai tayi kasa dashi tace
“Mama na kasa cire Yaa Fu’ad a zuciya ta da tunani na.”
“Fu’ad Kuma wanne Fu’ad?”
“Mama Fu’ad din Yaa Anwar!”
Mama tai murmushi tace
“Gaskiya ne Auta ta tana da hankali sosai.”
“Kamar ya Mama?”
“Saboda kin Yi zabe mai kyau. Fu’ad ya cika na miji Wanda ya cancanci a so shi Kuma Zan goya Miki baya Amman ba za ki fito fili kice kina son sa ba. A’ah sai dai ta siyasa Zaki tusa Masa kan ki ba ta fili ba Shima da kin gane Yana da wacce yake so ko baya ra’ayin ki sai ki hakura ki Mika lamuran ki da addu’a ki cigaba da addu’a Allah zaba mafi alheri bana son kije inda ba za a soki ba kamar yadda kike nagartaciyya haka ma Fu’ad Dan ba yana da halin sa. Dan Haka zan so mu hada zuri’a ta da Fu’ad Allah bada sa’a”
STORY CONTINUES BELOW
“Amin!”
Mama ta dafe Baki tace
“Ba kunya!”
Fuska Nusy ta rufe da hannu Mama tai Dariya tace
“Shikenan?”
“Mama tayaya Zan tusa Kai na.”
“Ki samu number sa kina yawan kiran sa Kuna gaisawa sannan Kina bashi kulawa ta musamman daga Nan Zaki fara shige masa. Sauran ai ke macece ko?”
Da gudu Nusy ta mike tayi dakin su. Mama ta saki murmushi tana fadin
“Allah tabbatar da alheri!”
Nusy na Shiga daki ta dauki wayar ta. Number Fu’ad ta tsaya kalla Sai ta dannan Dailing sai ta katse. Can dai da kyar ta runtsa Ido ta fara Kira. Yadda wayar ke din din haka zuciyar ta keyi.
Yana dauka taji muryar sa Mai dadi da sanyi tai Mata sallama. ajiyar zuciya ta sauke. Amman sai ta kasa amsawa.
“Hello hello!”
Fu’ad ya fada. Shiru sai ya dauke wayar ya katse. Sai da sukai haka sau uku ana hudun ta daure tayi sallama. Ya amsa Yana Mai son ya gane wacece.
Ganin ya kasa gane wacece yace
“Wacece Dan Allah?”
“Haba Yayan mu ai ma gaisa tukkuna ko?”
“Ok ya kike?”
“Alhamdulillah!”
“Good wace?”
“Wai Yayan mu baka gane wacece ba?”
“Wallahi ban gane wace ba.”
“Nusaiba ce fa.”
“Oh Nusy ya kike ya Mama ai dazu ma munyi waya ya karatun?”
“Komai lafiya. Au shiyasa nace ni Bari na Kira na gaishe ka tinda Kai kaki.”
“Affuwan to bani da number kine ai.”
“Saboda baka dauken a kanwa ba ko?”
“No ba haka bane Kanwata.”
“To Yaya ne?”
“Aiki ne yai yawa kinsan bana samun zama daga wannan sai wannan.”
“Haba dai yakamata kuna Dan hutawa sannan ku dauren kuyi aure Dan ma Naga Yaya shi ya fara shiri.”
“Aure ai sai ku Kanwata.
“Kai fa?”
Yai murmushi yace
“Yanzu Ina aiki Zan kiraki later ki gaida min Mama please.”
“Ok Ina jiran kiran naka. Mama zata ji.”
“Nagode!”
Ya kashe wayar. Kai ya dafe sai Kuma ya koma kan system din sa da aiki.
Tin tana jiran call na shi har ta cire Rai Dan kwana biyu kenan tazarar da Kiran Sa da tayi.
Yana aiki wayar sa tayi Kara. Ya duba ya dauka ba tare da ya gane number ba yai sallama. Sai da ta lumshe Ido sannan ta amsa.
Shiru yayi Yana son tuna muryar Amman Ina sai kawai yace
“Wacece?”
“Wacece Kuma Yayan mu!”
Ta fada tana Yi kamar zatai kuka.
“Am sorry Kanwata ai ban dau muryar ba.”
Shagwabe murya tayi tace
“Ni dai Yayan mu bai kanwar Dani ko?”
“A’ah Kanwata kiyi hakuri kinsan yanayin abun namu.”
“Shikenan ya aikin?”
“Alhamdulillah ya gida da su Mama.”
“Duk suna lafiya.”
“Ya ckul fa?”
“Alhamdulillah!”
“Yauwah ana dagewa kinji Kanwata.”
“Naji Yaya nagode!”
“To sai anjima ko!”
“Kira nayi fa muyi Hira.”
Kai ya dafe yace
“An sorry Kanwata Zan Kira in na Gama aiki.”
“Haka fa kace ranan Kuma baka Kira ba.”
“Zan Kira wannan Karan insha Allahu. In ban Kira ba ki Tina min kinji.”
“To nagode!”
“Bye!”
Ya kashe wayar.
Ilai kuwa Sam ya manta Dan Sai da yai Shirin baccin wayar sa ta fara Kara dauka yayi Dan Bacci yake ji. Kunne ya Kai Yana sallama ta amsa tana fadin
“Na Tina maka.”
STORY CONTINUES BELOW
“Thanks let me call you “
Ya kashe ya fara neman layin nata. Bayan ya Kira ta dauka ta Kai kunne tana fadin
“Yayan mu ya aiki?”
“Alhamdulillah!”
“Masha Allah!”
“Kefa?”
“Nima haka.”
“Good!”
“Yaya Kai Dan wane kasa ne?”
“Kasar ki Mana.”
“Hmm kasan kana kama da larabawa.”
“Bana son tsokana kanwata.”
“Da gaske nake Yaya.”
“To ni Dan Nigeria ne mahaifi na Dan Hadeja ne Mahaifiyya ta ma haka. But mu fulani ne.”
“Good Kaine first born?”
“No am last born Autah kamar yadda kike Autah!”
“Baka kaini ba.”
“Hhh in nace nafiki kada ki Musa min.”
“Saboda me?”
“In Kika ganni Akan ciyar Hajiya ta Zaki zata Baby ne.”
Ta dauka hannu Akan Baki tana fadin
“Shine kake son ka kwacen Mama ko to daga Hajiyar ka har Mama nice Autar su.”
“Ki tsaya Wasa duk Zan kwace su ne.”
“Hhh haba dai.”
“Eh Mana.”
“Zamu gani.”
Yai hamma yace
“Kwanwata bakya Jin Bacci ne?”
“Ina tare da Yayan mu tayaya zan yi Bacci.”
“To ni dai bacci nake ji.”
“To Yaya sai da safe.”
“Allah bamu alheri.”
“Amin nagode!”
Sukai sallama. Daga haka kullum sai Nusy ta Kira shi tin tana takura Masa har ya fara sabawa sosai suka shaku da Junan su sosai.
Nusy Bata da magana a ko Ina sai Yayan mu kowa Yayan mu haka take sai dai baka zauna da ita ba.
A haka bikin Anwar yazo Amman Sam Fu’ad yace ba zai je Nigeria ha har fada sukai da Anwar ya tafi ya barshi Amman yaki ya bishi. Duk da komai na tsarin bikin dashi akai wasu event din ma shi yasa ayi shi.
Nusaiba ma tana can tana jiran zuwan Fu’ad Dan duk wayar da suke bai taba ce mata bazai zo ba. Dan haka ta tanadi lokacin Dan ta bashi kulawa ta musamman. Amman me a wajen dinner tai ta zuba Ido bashi. Wajen Yaya taye tace
“Wai Ina Yayan mu ban Ganshi ba.”
“Bai zo ba.”
Tai Dariya tace
“Wasa kuke min dai ko?”
Murmushi yayi Mai ciwo yace
“Zan miki wasa ne.”
Idon tane ya kawo ruwa. Ta bar wajen ta fita.
Sabir abokin Anwar dake son ta Wanda ita ta dauka Wasa ne na abokin Yayan ta. Yana tsaye yaga Nusy ta fita, Dan haka yabi bayan ta. A waje ya same ta tana kuka ya Karasa Yana fadin
“Subhanallah me ya faru sweetheart?”
Dogowa tayi hawaye na bin kumatun ta. Hannu tasa ta fara goge hawaye yace
“Wa yasaki kuka Beauty.”
Kai ta girgiza yace
“Kina son zuciyar sweetheart din naki ta fashe.”
“No Sweetheart ba komai fa.”
“Meyasa kike kuka to my beauty Kinga fa duk kin bata kwalliyar.”
Juyawa tayi. Ya koma gaban ta Yana leka fuskar. Tai murmushi ya amshi jakar ta ya bude yace
“Ga powder ungo shafa kinji ki koma yadda kike haka kawai za a bata wa sweetheart rai.”
Amsa tayi ta shafa yace
“Masha Allah Kinga My beauty.”
Tai kasa dakai. Yace
“Muje to.”
Suka koma ciki. Haka aka karasa dinner ba Dadi jikin ta a sanyaye
Da ta koma gida ta shige daki. Fara neman layin sa tayi sai dai duk Kiran da tayi bai dauka ba.
Haka ta hakura ta cire ta Kaya ta Shiga Tai wanka.
Lokacin da ta Kira yana asibiti dan sai da ya koma gida ya dauki waya ya shiga. Zama yayi a kan gado ya dauko system Dan zaiyi aiki wayar sa ya dauko ya Dan duba Abu anan yaga missed ba adadi.
Dubawa yayi yaga Anwar ne da Nusaiba. Hakika shi kan sa ya san bai kyauta ba. Fara neman layin Anwar yayi sai dai a kashe. Layin Nusy ya fara nema. Fitowar ta daga wanka kenan taji karar dauka tayi zata kashe wayar sai taga Fu’ad ne da sauri ta dauka ta Kai kunne. Sai kawai ta sakar Masa kuka.
“Ya salam me yake faruwa?”
“Yaya mu meyasa baka zo ba?”
“Am sorry Kanwata wallahi aiki ne ya rike ni.”
“Amman Yayan mu kwana biyu zuwa uku kawai.”
“Kiyi hakuri Mana Nusy nima naso nazo abinda Nan za a kawo Mana amarya Zan tsaya a wajen event din Nan da zamuyi da abokan aikin mu kinga au zai fi ko?”
“Ni Yaya mu da kayi shawara Dani bai yi ba.”
“To ayi Hakuri Kanwata.”
“Uhmm ni ba ruwa na da kai.”
“Haba Kanwata Yayan kine fa!”
“To ba Kai bane.”
“Ai na baki hakuri ko?”
“To na hakura yaushe zaka zo.”
“Sai wata Rana.”
“Kasa lokaci “
“Ba sai na saka ba Zan zo.”
“Ok shikenan.”
“Kije ki kwanta kinji.”
“Ok nagode.”
Haka aka gama biki Ango Anwar da amaryar sa Husnah suka tare satin su biyu suka daga.
Gida guda ya samu ya siya aka saka duk abun bukata. Yaso su tare da Fu’ad Amman kememe Fu’ad yaki aminta.
Da suka sauka a airport Fu’ad yaiwa text Nan Fu’ad yaje dauko su. Suna zuwa suka rumgume juna. Fu’ad yace
“Allah Sanya alheri friend kayi hakuri.”
Janye shi yayi yana hararar sa. Ya kalli Husnah yace
“Amarya barka da zuwa.”
“Yauwah aminin Ango muna fushi.”
“Haba dai Amarya ke da Zaki bashi Baki.”
“Ba Zan amsa ba.”
Anwar ya fada. Husnah tace
“Da Wasa nake ba ruwa na ai kun fi kusa.”
Anwar yai gaba. Husnah da Fu’ad suka bi Bayan sa suna Hira. Mota suka Shiga suka tafi. Gida suka Shiga shi Kuma ya tafi bayan ya Kai musu kayan abinci.
Kwanan su biyu da dawowa akai party na abokan aikin Anwar Nan aka watse.
*
Yana office yana aiki Anwar ya Shiga. Tsayawa yayi a jikin kofa yana fadin
“Ka tashi muje muci abinci ko?”
“Abinci kuma haba dai. Kaje kawai ni bana Jin yunwa.”
Waje Anwar ya samu ya zauna yana fadin
“Kamun abubuwa da yawa Ina dauke Kai daga wannan in Kai min ba ruwana da Kai wallahi da gaske nake!”
“Me nayi Kuma?”
“Many things Kuma Kai ma ka sani ka tashi mu tafi .”
Mikewa yayi yace
“Muje kada ka cinye ni.”
Suka fita. Fu’ad yai driving har gidan. Suna Shiga suka samu Husnah taci kwalliya ta mike tana fadin
“Ah ah ah yau waye a gidan?”
“Husnah bana son haka fa kada ki Kara hada mu please.”
Anwar yai ciki yace
“Ai ba sai ta hada ba mun Gama haduwa ma ko Sweetheart?”
Kai ta gyada. Fu’ad yai kwafa yace
“Zan dauko Nusy tana shigar min.”
“Ayyah Nusy ba abinda zata shigar maka dama dai Fateema ce.”
Nan take mood din Fu’ad ya canja.
Anwar yace
“Kaga tashi muje muci abinci nasan zaka shiga school ko?”
Kai ya gyada. Suka karasa. Husnah tayi serving nasa sannan ta barsu.
Haka komai ya dinga tafiya Nusaiba da Fu’ad sun shaku sosai a dayan bangaren Kuma Sabir na ta budirin sa Amman Sam Nusaiba Bata San Yana Yi ba ita ta Fu’ad take kamar yadda Shima bai San tana yi ba.
Haka suka dinga rayuwa na tsawon shekaru. A shekarun nasarori masu yawa sun same shi. Ya hada karatun sa inda ya zama likita ga business da yake Yi.
Abin da yasa yaji Yana son tafiya gida shine da zarar ya kwanta bai da aikin yi sai mafarkin Fateema. Gaba daya bai da sukuni