WANI AURE CHAPTER 20

WANI AURE

CHAPTER 20


kyakkyawar yarinyar ce dai ta sake zuwan masa. deeni kuwa dake kwance warwars akan makeken royal bed dinshi ya zuba mata Idanunshi kawai , tundaga kan kwantaccen sumar gashinta kanta yake binta da wani irin mayataccen kallo mai cike da tsantsar sha,awa yayinda zuciyarsa ke wani irin harbawa da sauri da sauri ..ganin yarinyar ta miko masa zara zaran yatsun hannuta masu matukar kyau da daukar hankali ne yasa shi azamar fizgota jikinsa batare da wani bata lokaci ba ya rungumeta tsam tsam ajikinsa tare da cusa kanshi cikin sumar kanta yana shakar dadeden kamshin jikinta “take yarinyar itama ta narke masa ajiki tana taba wasu part na jikinsa cikin wani irin salo a haukace tamkar wani zaki DEENI yasoma romancing din every part of her “cikin zafi zafi ya hade bakinsu waje daya  yasoma tsotsa tare da lumshe rikitattun idanu..  …….. sosai yake juya yarinyar  yadda ya so batare da  wani abu yamasa shamaki  ba.

daidai komai yagama faruwa atsakaninsu ne ya farka  afrigice zaune   kmr jiya yana sauke numfashi sama sama..
    tare  da karanto addu’ar da duk tazo bakinsa na neman tsari daga sharin shedan ,ganinsa mafarkinsa nasaba da sharin shedan dan gabadaya yarasa dalilin dayasa yatsinci kanshi cikin irin wannan yanayin mai cike daban  tsoro da alajabi .. hakika shi  bazai ce Ga abinda  ke damunsa acikin yan kwanakin nan dayasa yake tsintar kanshi cikin irin wannan birkitaccen yanayin ba . +

Tsawon lokaci ya dauka yana zaune Yayi shr kawai  yana tunani.

  ” yayi yayi  ya gane abinda ke damun rayuwarsa  Amman Sam yakasa domin   duk ta inda ya duba bai gano  takamaiman abinda yasa yake irin wannan mafarkin ba ….. ‘ahankali yasa hannushi  yajanwo  hanky  agefen bed dinsa ya goge gumin daya rufeshi . dan duk da  AC dake aiki acikin dakin bai hana Gumi  tsatsafo masa ta koina ajikinsa ba ..  .. sannu ahankali yakai idanunshi kan agogon bangon dake manne a dakin.
karfe biyu yagani daidai ajiyar zuciya ya sauke tare da koma  yayi   kwanta lamo…. yana juyi kawai batare yasan abin yi ba dan kwata kwata idanunshi ya kyan kyashe bbu alamun  bacci acikinsu   tunani kawai yake yana juyi. …

Washegari

da safe byn ta idar  sallar asuba  bata  koma bacci  ba saboda tasan yanayinta domin tana  komawa bacci me nauyi ne zai dauke ta.

  ” kowa Kuma yasan yadda baccin safe yake    dan haka    kishigida kawai Tayi  kan pray mate .

karfe bakwai daidai ta fito daga dakin da’aka sauke ciki. shr koina babu  motsen kowa ballanantana mutun ya saka ran ko akwai wani  bil,adama acikin gidan kasancewar week end ce.

tafiya take ‘ahankali  cikin tsanyi  jiki , har ta iso part din ummi takutsa kai  ta shiga da sallmarta … 1

nan ma shr  ba motsin  kowa ciki “can taji   ” alamun  motsen ruwa a bathroom  dan Haka tabbatar da ummi tana.

” bata wani  tsaya batawa kanta  lokaci ba ta soma yin abinda yakaita,  daidai  nablah tagama gyara koina  ummi tafito daga bathroom..

tana ganin nablah ta saki fuskarta sosai tare da yin  murmushi  . nablah   ta gaishe da ummi  cike da girmamawa .

Ummi ta amsa tana mai Bin nablah din  da wani irin kallo mai hade da mutuntaka .

Jikinta  nablah a sanyaye takarasa toilet din ummi  tawanke koina tasss  … sai da tabbatar data gyara duk inda aka nunamata tasss ..

Amman banda part din mai gida Dan  so take sai ta gama da koina acikin  gidan sannan tashiga  part dinsa   saboda tsaro ..

Tsaye take a bakin kofar  da zata shigar daita cikin part din mai gida.. hannuta rike da  handle din kofar  .

  “takasa murdawa tashiga a dalilin  zuciyarta da tasoma  wani irin harbawa da sauri .
ta dinga jin wani  irin ajikinta wani  irin yanayi ne na daban ta tsinci kanta ciki  .
,yayinda   wani part na zuciyarta ke bata umarni tashiga kawai batare da wani tsoro ko fargaban ba , a tunaninta   may be ma yafita  ,duk  dai tasan  week end ce bai zama lallai yazanmato yana ciki ba.
Amman kwata kwata fargaba datake ciki  ta hanata yunkurin kusawa cikin dakin ..
,sai da ta runtse idanunta tare da tattaro  jaruntar ta sanyawa gangar jikinta ,  sannan ta iya murda handle din a natse  tashiga dakin ,da idanun take bin  dakin da kallo Sha,awa.
    koina tsab tsab  tamkar an gyara   bbu wata alamun da zai nuna mutun na rayuwa a cikin dakin , ahankali ta kamo  gefen  lip’s din  bakinta ta Dan ciza   kadan kana   ta soma abinda ya kaita  .

STORY CONTINUES BELOW

   Daki daya ya rage a cikin part din  da bata gyara ba Dan haka  ta kutsa  ciki ta soma da wanke  toilet ta zo kan royar bed dinshi, ahankali tasa hannuta kan  blanket  din dake rufe da gado  da niyyar cirewa ta  nike  Dan kwata kwata batayi tunanin zata samu bil ,adama  kwance cikinsa ba”  a tsorace Tayi  sauri sakin blanket din 

  ‘ tana zare idanu waje tare da furta  wayyo Allah nah a kasan ranta , take  jikinta ya dauki kirma ta gigice tama rasa hanyar fita dan neman tsira    daga cikin  dakin.

  tsabar  rikecewa batasan sanda ta kama  handle din  kofar bathroom ba ta afka ciki … Ai ko  tana ganin ba kofar fita bace ta sake  juyo da   sauri ,bbu inda baya rawa ajikinta  tare da tattara kayan moupystick dinta   tabar dakin  da saurin bala’i tana haki sama sama tare  da fidda  numfashi .

A can bakin corridor din dake  tsakanin part din deeni da ummi taja ta tsaya ta sake  fidda numfashi  tare da   addu’ar Allah yasota.. ..

shi kuwa deeni dake kwance ya sake lumshe rikitattun idanunshi  kawai dan  tun  shigowarta dakin idanunshi ke bude ganin itace yasa shi  sake lafewa jikin pillow , dan shi ko yaya akayi motse zai farka.

yadda yaga ta gigice ne  ya fi tsaya masa arai .
Dan Haka a tsanake ya tmbyi kansa  to me hakan yake nufi da wannan gigicewar dayaga tayi ?

tabe bakinsa yayi tare da jan tsaki sannan  yacigaba da  baccinsa .

Sai  kusan azahar sannan yatashi  ,yashiga bathroom yayi wanka hade da alwala yana fitowa ya goge jikinsa ya shafa lotion  ya zira jallabiya   long  sleeve tare da fashe  ilahirin jikinsa da turaruka masu mugun kamshi da daukar hankali….

   ahankali yake saukowa daga step hannushi rike da gefen jallabiyarsa   har ya iso babban falon gidan inda ya tarar da duk ahalin  gidan zaune  .

ya gaida ummi  yayinda zeenat ta gaidashi .

nablah da tun 
saukowarsa taji tana kiciniya da numfashinta  dake namen barin gangar jikinta ta gaisheshi  muryarta aciki.

Yana jinta Yayi banza daita tamkar   bai jita ba  Sai ma hankalinsa daya dauka kacokan yamayar kan ummi dake  kallo, muryarsa a dake yace  first lov ni zani masallaci ta juyo tana dubansa  tare da ce wa  To sai kadawo yarona , sa kai ya fice .

  takasan   idannu  take kallon  every step of him  dab ..dab… kmr wani jinin sarauta yayinda  duk takunsa daya ke  daidai  da bugun zuciyarta har ya bace wa ganinta idanunta nakansa km Sai lokacin  tasamu  natsuwar zuciyarta,  dan gabadaya ilahirin jikinta bbu inda bayi sake  ba .

Muryata Ummi ce  tasa ta sake dawowa cikin natsuwarta . nablah ki dawo   kan kujera man  ki zauna kin wani je can kin rakube akasa… maza taso  kidawo nan  kusa dani kinji “ki saki jikinki damu  nan ma tamkar gida ne , a sanyaye nablah ta Mike tayi kmr yadda  ummi ta umarceta  .

Ummi tacigaba da magana . kishirya zuwa anjima akwai doctor  da zata zo ta miki test kinji  nablah  cikin sanyin muryarta tace to…..

Ummi   tasa hannu ta dauki remut tana canza channel zuwa zeeword  .

,  zeenat ta dan juyo a wulakance tana kallon inda nablah ke zaune tare da  watsa mata wata uwar  harara ..   bakinta ta tabe kawai cigaba da aikawa nablah da harara iri batare da tabari ummi taganta ba   ita dai  haka kawai take jin tsanar yarinyar har cikin ranta .

  hirar ball ummi da Zeenat keyi jifa jifa har suka gangaro kan hirar duniya   ummi ce  ke kokarin  saka nablah ciki hirartasu ” yayinda   ita km nablah Ido ne  kawai  nata ko  murmushi Dan kwata kwata ita batasan ma  me zata dasu  ba’ dan Haka tacigaba da sauraronsu  har zuwa  sanda mai gidan ya  dawo daga masjid  tare da wata mata suka shigo ..

byn sunyi shafta da wasa da dariya tare da mdm zeenat wanda  hakan ya nuna  alamun sun saba da junansu  sosai ba tun yau ba ..
” ummi ta  umarce doctor din data shiga da nablah ,hakan ce takasance domin   bata tsaya wani  tmbyr ummi  ba Dan tasan abinda zatayi .
abinda yabawa nablah  mamaki bai wuce ganin  komai  na aikin likitoci dake cikin dakin ba.
  bbu abinda bbu  har gadon kwanciyar marasa lafiya akwai shi a dakin. +

, Doctor din ta umarce nablah  data zauna” ta zaro sirinji acikin hand bag dinta .

ta zuki jininta wanda hakan bai sa hankalin nablah  tashi ko daya ba saboda daman hakan  yana daga  cikin budget dinta.

byn doctor din   ta dibi  jininta  tashiga wani daki still dai acikin dakin da suke ciki  tare da bawa nablah umarnin    Wuce wa.

Ta Mike jikinta  bbu kwari Sai dai bbu  wata alamun damuwa ko fargaba atattare daita .

direct hanyar step  tabi ” ta nufi dakinta” koda tashiga dakin ma rasa abinyi tayi domin   kewar yan gidasu ne tattare da zuciyarta” tana ji  kmr taje tasamu  ummi  ta roketa takirawo mata number  auntyta  su gaisa .

tunawa datayi Killa ma yanzu haka ummi na can tare da mutun da ko kafafunsa ta kalla zuciyata tamkar zata tarwatse  takeji”  yasa ta share kawai  taki koma gurin ummi ..

Sannu ahankali Yau kusan  kwanakin  nablah  goma  kennan a gidan Amman bbu Wanda yayi mata bayanin komai   dangane da jininta da a gwada.

duk da hakan  bawai ya dameta bane  illa rashin jin muryar   daya daga cikin ah’linta  ,tunanin hakan ne yasata .

Mikewa  tsaye cikin hanzari  da niyar zuwa tasamu ummi ta taimaka ta kiramata  auntyta .

bude kofarta ke da wuya taga mutun tsaye  abakin kofarsa  yana kokarin yiwa kofar dakinsa da key .

Da sauri ta  risinawa tana  gaishe shi  shiru yaki  amsawa   km bai da alamun zai  amsa din     sai ma dauke kansa dayayi yacigaba da abinda yake .

Jikinta yayi maseefar yin  sanyi da abinda deeni yayi mata.

Dan haka  ‘ahankali ta dinga daga kafafunta  yayinda   Rainta yake a dagule tana jin wani irin ciwo mai radadi   , duk da kasancewarta  mai  matukar  hakuri da rashin sauri fushi akan abu. Amman abinda mai gidan yayi ya taba   ranta  .
domin  a rayuwarta idan akwai abinda ta tsana da Gani bai wuce tsagwaron   raini hankali  da cin fuska tare da  isgilanci ba dan zata iya dauka komai Banda su  .
ahankali   ta dinga    daga kafafunta dasuka gama sagewa ta nufi hanyar da zata sadata da ummi . dan  gurinta kadai take samun sausauci acikin gidan. +

A tsanake yabita da Idanunshi     tare da rike kungunsa  da hannu daya yana bin bayata da wani irin matsiyacin  kallo.

  yayinda zuciyarsa ke  harbawa ko kifta idanunsa  bai da alamun yi ” so yake ya tabbatarwa idanunsa abinda yake Gani a cikin  mafarkinsa ,  hajabi dake sanye ajikinta    bai hanashi yimata kallon kurulla ba ”  gabadaya idanunshi sun rufe ya shagaltu da kallon Surar jikinta a bayyane …  domin  ganinta yake murarta ba tare da wani hijabi ba   .

  Jin yadda idanunshi ke yawo a tsantsar jikinta ne ” yasa  Kirjinta ke wani irin  harbawa da sauri tamkar wacce ake bugawa guduma a kahon zuwa .

Yanayin sanyita da tafiyarta yasake shagaltar dashi ba dan deeni  yagaji da kallonta ba ,ya dauke idanunsa akan ba Sai Dan gudun juyowarta cikin sautsayi.

What lokaci tana kan step Dan ko rabi batayi ba dan kallon da kafe dashi ne ya sayayar mata jiki tare da rage mata kuzarin jikinta .. ahankali  km tasoma jin  kmr takun mutun   abaya daidai ta kai rabin step din cak…. taja ta tsaya tare da rabe jikinta gefe daya .

alamun tana son bawa duk wani mai son wuce dama ,duk da oready jikinta yabata alamun mutumin data baro tsaye ke saukowa  sakamakon kamshin turarensa mai tada hankali da ta keji  …

shr kusan two minutes sannan  yazo ya wuce ta gefenta zuciyarsa na tacigaba da harbawa .duk da Bai    bari jikinsu ya tabu da juna .

Tana nan  tsaye har yazo ya wuceta tare da    bude wata kofa ya  shiga   dan kusan  har yanzu bata gama sanin kan dakun nan gidan ba.

,inda tasan zata samu  ummi kai tsaye  ta nufa zaune suke ita da Zeenat kmr  koda yaushe suna kallo TV suna hira abunsu hankali kwance. Yayinda  kayan fruit ke gabansu da sallmarta takarasa inda suke  sannan tasamu guri kan Tia’s ta zauna tana wasa da  Zara zaran yatsun hannuwanta.  ummi ta juyo ahankali  tana  duban nablah  byn ta amsa sallamarta  kallonta kawai take Tare  da nazarinta   .

yayinda zeenat tunda ta juyo ta mata  kallo daya ta dauke kanta tare da  mai hankalinta kan film da,akeyi .

Sai da ummi tagama nazarinta tsab sannan ta takira sunan nablah ..

Nablah  ya’akayi ne ?

Nablah tayi kasa da kanta tana cigaba da yamutsa yatsun hannuta  a atsorace  muryarta cike da sanyi  da in…inna.. tace dan… Allah daman  ina..Ina. son nayi magana ne  da auntyna ta fadi hakan idanunta suna masu  cikowa  da hawaye. domin daukarta ko baza su kiramata auntyta bane shiyasa duk takoma wani iri   .Ummi  tayi murmushi kawai Tare da sake zubawa nablah ido   ganin yadda duk  ta dawo kalar tausayi ..
ummi ta girgiza kanta sannan tace  yanzu akan   zakiyi magana da auntynki  ne duk kika dawo haka tamkar zakiyi  da kuka?
   .. gsky  nablah akwai shagwaba atare dake tasa ummi takarasa fadar haka Tare da Mika  hannu ta janyo  wayarta dake gefe tasoma   dealing number Salmah ta Miko mata  wayar tare da nunawa nablah wani daki da hannuta . Kishi Ga nan kiyi wayarki kinji diyarta .. haushi da takaici ne gabadaya suka gama turnuke zuciyar Zeenat dake zaune gurin  tamkar ta tashi ta shake wuyar nablah ta dinga a zuciyarta , tarasa yadda zatayi ne kawai yasa ta dinga  ja tsaki tana aiyana yadda zatayi da yarinyar..
+

wayar manne da kunnenta  har tashiga dakin  da ummi ta nuna mata ,daidai nan  murya aunty Salmah  ta doki dodon kunneta tun kafin nablah tayi magana aunty Salmah tace assalamu alaikum hjy anyi lafiya .

murya  nablah cike da doki da  shagwaba aunty  ba hjy ba ce nablah ce .

Aunty Salmah tayi murmushi A’a nablah.. yana ji muryarki haka kmr kina cikin damuwa ?

Sai da nablah ta sauke ajiyar zuciya sannan tace bazaki jini cikin damuwa ba  , byn kewarku ta dameni duk sai aunty Salmah gigice.
tace ko dai akwai da  matsala ne a gidan?
” nablah tace  uhmmmm fa ba matsalar komai.. in ma akwai matsalar nan bai wuce   kewarku ba .

Nablah tacigaba aunty  baki bawa mama number wayar hjyr bane kmr   yadda  kika ce gsky    zuwa yanzu na matsu da son jin muryarta,  km  kmr naganni agabanta haka nake ji ,aunty Salmah tace Eh ban bata number ba  nafison zuwa nan da sati biyu tukun nasan zuwa wannan lokacin kingama  da sanin halin mutane gidan , ni dai abinda nake so dake ki zauna lfy da kowa Amman da kinga akwai  matsi    da  takura  just give me a cul” furrrrr zaki ga aunty ki kmr flay.

nablah   ta saki  sanyayyayiyar murmurshin dayasa  dimple dinta  lotsawa sosai wanda hakan ke   sake fito da ainihin bawar kyawun da Allah yayi mata . +

Ahankali ”  tace Allah aunty bbu matsalar komai  fa aunty Salmah tace to.to. shikenan ,ki kama kanki da kyau km  ki dinga saka hijab dinki  duk inda zaki shiga a gidan .

Nablah tace har baccima dashi nake aunty Salmah Tayi  yauwa Yar gari nablah na  murmushi tasake bude baki da niyar tambayar auntyta  dip …maganar ta tsaya …… Tana zaro Idanu waje sakamakon hasken dataga ya  gwaraye  dakin gabadaya  duk daman can akwai  wuta a dakin  dan koda tashigo fan na aiki ..

kwance yake akan kujera  idanunshi a lumshe yana kallonta kmr ranar farko daya soma ganinta  a rayuwasa .

murya aunty Salmah  taji tana cigaba da cewa lfy  na jiki   shr  kin dauke wuta kmr NEPA.

A daburce tasoma in in na , A’a…….uhmmmm ba komai to yanaga duk  kin rikece kigayamin in wani abu  nablah tace Allah  bbu komai aunty to   kigaida hjy zan Kuma bawa mama number hjy  zuwa jibi inshallahu ki kwantar da hankaliki zata kiraki, itama ta matsu taji muryar autata ,da kyar nablah dake kokuwa da numfashinta ta iya bude baki  tace to aunty  sannan ta kashe  wayar Tare da  sauke wayar daga  kunnena.

har lokacin bai dauke idanunshi akanta ba wanda shi kansa basan ma Yana kallon nata ba .

  Itama shanyayun idanunta ta zuba masa kawai  tana kallon  kwakkywar  fuskarsa dam …taji kirjinta da zuciyarta sun amsa a lokaci  daya take ta soma jin  tsoron yanayin  irin kallon dayake mata.

,jikinta kuwa  Banda kirma bbu abinda yake ,takoina  gumi ya dinga   tsatsafo mata  ajikinta   Jira kawai take taji yace arrrrrrr ta arce da gudun maseefa Amman Sai kawai taga sabanin haka, domin  ko motsa bakinsa bai da alamun yi  ballanantana akai gasamun fitowar  kalma daya daga bakinsa Sai ma taga   tabe bakinsa  tare da dauke idanunshi akanta .

aransa kuwa cewa yayi munafuka kawai Tayi wani shr   kmr ba yanzu tagama   wage baki tana waya  ba..😍😍😍

Ni dai  nace uhmmmm  deeni Banda  kin fad ar gaskiya…nooooo
komawa yayi sosai yayi  kwanciyarsa normal ganin datayi ya  kina ya kwanta ne  yasa tayi saurin juyawa da jikinta na rawa ta bar dakin har hijab dinta na neman hardeta  kafafuwanta . +

” afrigece   ta dawo parlour  inda ta bar su ummi .

Ummi kadai tagani zaune  Banda  mdm muzeenat ko Ina tashiga oho ita dai tunda tasamu    ta mikawa ummi  wayarta ta bawa karfa iska  .

tayi shr sannan komai ta tuna ta dagamin kai …

Koda tashiga dakin ma  bayi tashiga dan jin yadda   cikinta ke murdawa  ,tun sanda take tsaye gaban horo  dan sunnan data bashi kennan take jin yadda cikinta ya cure guri daya  .

toilet tayi sosai byn tagama tashiga cikin bathtub ta kunnawa kainta” shawa  ta dade kwance  tana jin dadin yadda ruwan ke rasa kowani part na  jikinta .

sai data  soma jin kiran sallar ne a masallaci dake cikin gidan sannan  tayi alwala ta fito jikinta daure da towel zigidir tayi gaban mirrow tana goge sauran wuraren dake da ruwa ajikinta yayansa take bin koina ajikinta da kallon, yadda yanayinta  ya  canza gabadaya  ‘ahankali tayi murmushi tana sake kallon kanta  doguwar rigar mai dagon hannu ta zirawa jikinta tare da zira hijab dinta  ta tada ikama…

Byn ta idar da sallah ne ta Mike ‘ahankali  jikinta a tsanyaye    takarasa  jikin window dakinta .
” ta makale hade da dan  zuge labule window kadan ,ta yadda zata ji dadin  hango  abinda ke wakana a compound  din estate din. +

Tana nan tsaye tana  kallon yadda  motocin ke shige da fice a cikin estate din ,  ta zurawa waje Ido sosai kmr mai shirin hango wani abu na daban aciki estate din, yayinda take shakar wata  iska ta musamman  mai dadi da ratsa jiki.

wanda rabonta da jin irin  haka ta dade ,  tun kafin   shigowarta  cikin gidan.

,har wani lumshe shanyayun  idanunta take  sakamakon farinciki data tsinci kainta ciki.

,Ta dauki tsawon  lokacin  makalle  agurin tana shan iska  “karar bude kofar dakin data ji anyi ne. 

Yasa ta  dan juyo da sauri   hade da sakin labulen window.

ahankali  nablah ta sauke idanunta fess. akan Zeenat dake tsaye kikam.. tana    mazurai . take gaban nablah Yashiga faduwa da sauri  a yatsine Zeenat ke watsawa nablah  wani irin mugun kallon wanda ke hautsina kayan cikinta  , ganin irin kallon rashin arzikin  da  Zeenat ke  binta dashi ne . yasa nablah shan  jinin jikinta.

tabe baki Zeenat tayi sannan tace Yar iskar baiwa…  kawai abinda yakawo kennan , kin wani zo kin nemi waje a daki kin zauna kina tamkar boka dan tsabar  munafurci ,  to kike so yayi  miki sauran  aiki da yayi saura uhm ?

Nablah tayi saurin girgiza  kanta  tare da cewa  dan Allah aunty kiyi hakuri wlh na dauka ko  mungama aikin ne.

Zeenat , ta  sake watsamata wata uwar  hararar hade da kallon banza.. wanda hakan ya suka  sake  frigita zuciyar nabla dake tsaye  Amman ta dake batare da tabari Zeenat din ta gane yanayin data ciki ba  .

Mtsssssss Zeenat taja tsaki tare da cewa dan Allah  malam ni   fito ki kije ki karasawa mutane aiki sannan km ki daura min  abinci ,Yar isakar   baiwa…   nablah tayi shr tare da dago shanyayun idanunta   tana kallon Zeenat dasu ,yayinda take jin zuciyarta tamkar zata kama da wuta tsabar takaicin sunan da Zeenat din kirata dashi .

Zeenat tace 
Kin wani tsareni da idanunwa narai narai kina  kallona ko baza kiyi bane ?
    a tsanake batare da  wata  alamun tsoro ko fargaba ba  nablah  tace zanyi  .. 
Ok minti biyu  kacal nabaki “naganki a kitchen “idan kika kuskura kika bata min lokaci zakiga yadda zan ci ubanki a gidan nan ” tana gama fadar haka 
ta juya fuuuuuu tasoma tafiya  tana  kunfar baki. +

“Nablah tayi zuru kawai  tare da  bin bayan Zeenat  da wani irin kallon mamaki da alajabi abinda tayi mata.

dan ko kusa batayi tsammani zata  fuskanci irin wannan babbar wulakancin ba mai cike da al,mara .

Yau itace   aka aiki tajawo aka zagin mahaifinta..abanza uban ta fa aka zaga  ,ta furta akan akasan ranta, wato  silar ainkinta ne  jawo a dinga wulakanta mata uba Haka   km  ma har da kiranta da sunan  baiwa…baiwa fa takirani dashi ta sake maimaita sunan  a filli gabadaya abin yazo mata    wani iri km abazata”  tamkar ba gaske ba.

  Anya kuwa rayuwar  zata yuwu a Haka tun ba,aje koina ba an fara da zagar mata mahaifnta.
” Anya kuwa zan iya  daukar wannan kalar kaskancin da  iskanci kuwa ,abinda ta tmbyi kanta da kanta  Keenan?

,’ahankali ta furzar da iska ta bakinta  tana furta wlh da sake Dan   zan iya  daukar  komai na kunci rayuwa  Amman Banda  zagar min iyaye .

,

,  Mtssss  taja tsaki itama tana harara kofar da Zeenat tabi .cikin sanyi jiki ta nufi  kitchen   .

Ko minti biyu batayi da daura ruwan abincin dare ba   Zeenat takaraso ta tsaya a bakin  kitchen din tana kiran..  ke….ke.. nablah dake tsaye tana jin Tayi banza daita duk da tasan daita take sannan km   taki juyowa …

Sai ma cigaba  da aikinta Tayi.
  Sai da Zeenat ta sake maimaita kiranta sannan nablah da ke ..Kusan Sau uku sannan nablah ta juyo a danketa tana kallon cikin idanunta Zeenat .

Zeenat tace  ,Yar iska yarinya kawai  kina jin mutane suna kiranki Amman dan dakikanci irin naki kika yi shr..ko

nablah ta hadiye bacin ran dataji yana taso mata tun daga tsintsiyar kafafunta ,sannan  tace kiyi hakuri  basan dani kike ba”   sbd  ita kalmar   ke.. din da kika ce bata daga cikinta   sunan nablah….

. eyyyye  Zeenat ta fadi Haka tare da  ta ware ido tana kallon nablah da mamaki ni zaki kawa rainin hankali , nablah tace kiyi hakuri aunty barainin sense bane a zafafe Zeenat  tace yi min shr stupid girl kawai ni zaki kalla kicewa ba sunanki ke ba…. Dan  bakida mutunci ,  to kisani  ni daga yau  da sunan ke … zan dinga kiraki ,Dan Allah idan nakiraki dan ubanki  karki amsa kiga yadda zanyi dake a cikin gidan nan .. .

nablah ta datse  lip’s din bakinta na kasa da karfi gaske  jin zafin abinda Zeenat tace mata  , kusan minti biyu tsakani nablah  ta sake duban inda Zeenat ke tsaye har lokaci gabadaya gabobin jikinta sun sage muryarta cike da rauni km Haka kawai ta tsinci kanta da cewa kiyi hakuri aunty .da hannu Zeenat ta katseta .. yimin shr Dan Allah dan bana son sake jin ko muryarki ne .. km ki sauke  pot dinan  ki daura min indomi yanzu yanzu taja tsaki tare barin kitchen din. +

cike da mamaki  yarinyar  Zeenat takarasa ta zauna ranta a abace  wahake take fidda numfashi  dan   kwata kwata bata taba jin tsanar mai aikinta irin yadda take jin haushin nablah .

Gashin yarinyar kmr bata da  wani alamun tsoro atare atare daita  .

Cikin  mintinan da basu  wuce biyar ba  ta sauke  indomi ta yuye   a plate sannan  ta sake maida pot din abinci dare kan gas .

zaune  ta sameta   ta hankice a parlour  sai faman  cika take tana batsewa tare da hura hanci ‘tana kada kafa daya ..

ahankali  nablah ta ajiye mata plate din indomi agabanta akan center table  tare da kwalbar  vitermilk kana   ta juya ,tabar parlour .

,banda tunanin da mamaki Zeenat  bbu abinda nablah keyi  .

ko meyasa ita takasance irin haka ba kmr ummi ba ,mai matsananin son mutane da kyautata musu” km tana lura da irin yadda ummi  din  ke matukar bawa duk wasu mutane  dake shigowa cikin  gidan, kulawa ta musamman ” sabanin ita wannan bazanr matar mai kama  da mutane China .

, ‘Ahankali nablah tacigaba da aikinta na zagin Zeenat din aranta sai data gyara koina tsab .

sannan taje  tambaye Zeenat din ko akwai wani  sauran  aikin  da zatayi Dan gujewa cin mutuncinta .

,a yatsine Zeenat din ta dago fuskarta tamkar hadari sannan  tayi mata  nuni da hannuta alamun zata iya wucewa kawai .

jikinta a mace tabar gurin ,  da kyar ta dinga   daga kafafuwanta tsabar gajiya datayi , yayinda idanunta suka ciciko da Hawayen batayi kokarin hana hawayen idanunta zubowa ba,sbd tashin hankali take ciki da wutar dake ruruwa a zuciyarta  tana tafe   tana   kukan zuci yayinda hawayen idanunta ke sake  cigaba da bin fuskarta…

ahankali  ta  hau  step  daidai conar da zata kaita dakinta.

anan suka  kusan cin karo da deeni da ba dan Allah yakiyaye da sai daita tajita a faffadan kirjinsa . sakamakon hannunta duka biyu datasa tana goge Hawayen idanunta   ..
daddaden kamshin turarensa ne  ya doki hancinta a frigice tayi  sauri  janye jikina..
  Ta makale jikin bango batare da tasan Tayi hakan ba , jikinta ya dauki rawa kirrrrrrma    hawaye km sharrrrrrr suna  sake bin  fuskarta ido cikin ido suke kallon juna ,itace ta soma janye idanunta ta  ta runtse  gam tana jinra kawai taji saukar mari ..
,  tsayawa yayi  cak  Shima  yana karemata  kallo up and down . +

STORY CONTINUES BELOW

A tsorace   tasa tafin hannunta duka ta rufe fuskarta dashi.. kijinta na sake daukar kirrrrrrma .

‘Ahankali  ya ja  wani irin mugun  tsaki mtsssssss wanda hakan ya sake jefe zuciyar nabla shiga   cikin rudani .

,   yana  tsananin jin haushi yadda yarinyar ke behaviors kmr wata  dakiykiya   .. 

harara ya zabga mata   kana ya sake jan tsaki sannan ya yasoma taka step  . tana jin takunsa har sai da yakurewa step din Sosai sannan ta bude idanunta  da sauri  ta fada dakinta tare  dannawa kofar key ..

.ta fada kan gado takarasa  fashewa da wani sabon  kuka…. Mai cin rai  blaming kanta kawai take ta yadda tayi sanadin jefa kanta cikin meyakawoni matsala.

, meyakawoni cikin wannan gidan ?

meyasa na kawo kaina cikin  halaka irin haka ?

anya kuwa nayiwa kaina adalci Dana zabarwa kaina irin wannan rayuwar ,mai cike da kaskancin da wahala ..
Anya kuwa  zan iya cigaba da yin wannan aikin kuwa ? Haka ta dinga jerowa kanta  tambayar iri iri batare da tasan abinda yakamata Tayi ba ..
yanzu irin rayuwar da zanyi kennan?
  ..Ta sake jeho kanta  tmby.
agigice tatashi  zaune  ta jingina bayanta da jikin gadon dakin  tare da  zubawa celling dakin Ido  tana tunanin abinda yakamata tayi “shr yabiyo baya  na wani dan lokaci .

tuno  auntynta datayi ne yasa tayi saurin  sauke ajiyar zuciya, Dan tasan ita kadai ce zata iya  fidda ita a wannan halin wulakancin datake ciki , batare wata matsala ba.  ai aikin bai zama  dole ba  ,  da sauri ta hau goge  Hawayen fuskarta  tace zan kwantar da hankalina na zuwa wani lokaci “kafin nasamu yin waya da  auntyna . ahankali ta Mike tashiga bayi ta dauro alwala sallar magrib koda ta idar ma  bata tashi ba sai datayi isha’i a gurin .

,  bata bi takan komai ba dan ko abinci bataji zata iya  zuwa ta sakawa cikinta ba .
ballallantana  ta hadu da hawan jini ,da  ciwon ulcer  wato deeni da Zeenat .

,Ta   kwanta anan ta dunkule jikinta  cikin hijab  tare da lumshe idanunta kawai” duk da ba  wani bacci takeji ba, ahankali  tarinka jin yadda  zuciyata tasoma beating  dip….dip….  kafin daga baya tashigayi da sauri da sauri sakamakon tunowa da Mr horo datayi  …

  “Tarasa dalilin dayasa  duk sanda tayi arba dashi  ko  ta tuno shi   take shiga cikin  tashin hankali, ba.
,  addu’a tasoma aciki.  zuciyarta ya Allah…ya Allah kamin tsari dashi da duk wani wani  shirin dake tattare dashi  . Allah idan zama acikin gidan nan  alkhari ne a rayuwarta  Allah kasamun natsuwa da hakuri  zama da matar gidan .
  ,idan km bbu alkhari  Allah  ka fidda cikin kowace irin maseefa cikin sauki . haka tayi tayi yan  addu’oita , har taji zuciyarta ta dan samu natsuwa daga tashin hankali data shiga na wuncin gadi ,daga karshe   bacci mai nauyi yayi gabadaita.

Acan kasa kuwa DEENI ne kwance akan thrre sites hannunsa rike da remut yayinda  zeenat ke zaune a gefenshi suna hira ,rashin ganin nablah yasa duk ummi  ta damu har   . takai ga tambayar zeenat  ita  ,  ummi tace ni kuwa ina yarinyar nablah take ne  har yanzu banga saukowarta ba ko lafiya?deeni dake zaune yaji gabansa ya fadi zuciyarsa tashiga harbawa .

zeenat  ta Dan yatsina fuska  kana tace wa ummi  .  ai tun  dazu kafin ki dawo  ta  sauko  taci abincinta ta koma dakinta dayake      fita ummi   tayi ,yau . Ummi ok na jita shr ne .sannan tacigaba yabon nablah yarinya mai  hankali wlh .
  Zeenat taji magannun ummi na neman saka mata ciwon kai ,ta barta da karyar data   ,sharara mata ta ba gaira ba dalili   . +

Zeenat ta Mike tsaye  tsam  tare da yiwa ummi sai da safe Dan itama yau bacci take son yi da wuri sbd tana da lecture karfe goma  daidai na safe .. .

ita data shiga dakinta da niyar   samun natsuwa Amman zuciyar tashigo mata da tunani iri iri ciki kuwa  har da maganar haihuwar da bata km samu ba har yanzu  wanda shine jigon rayuwarta  a gidan mijinta  ..

‘Byn tafiyar Zeenat ummi dago Ahankali tana duban deeni tare da  kiran sunanshi..

DEENI dake kwance  ya amsa hade da dan mikewa zaune ya mai da hankalikasa kacokan  a kan umminsa .

Ummi ta numfasa sannan tacigaba   deeni  naji  kamin shr game da zance yarinyar nan mai aiki… , gabansa ya yanke ya fadi  rasssssss …jin abinda   ummi tace  “ya zubawa ummi ido kawai  yayi shr yarasa me zai ce mata  ”  saima shiga wani yanayi da yayi .’ahankali

ya runtse idanunshi  yana Jin tamkar  ummi  ta watsa masa ruwan zafi yake ji da wannan maganar yarinyar  datayi masa.
dan zuwa yanzu ya dauka ummi tabar zance ne kwata kwata  ganin bata sake mishi maganarta ba .
“ummi tace kamin shr DEENI idan kasan baka shirya yin komai ba akai  mezai hanna ni kabarni na aiwatar da komai domin  nasan   abinda zanyi ..
“ahankali deeni  ya bude rikitattun idanunshi ya zubawa ummi su kawai yana  kallonta ,kada masa kanta  tayi alamun abinda ta fada din  haka take nufi  .
yace  first lov kiyi hakuri Dan Allah zansan abin yi  Amman dan Allah kidan karamin lokaci kadan kinji first lov .
Ummi tayi shr can Kuma tace shikenan Ni daita  burina bai wuce nasamu abinda  nake  fatan samu daga yarinya ba .. tan Ga fadar Haka ta mike tana mishi sai da safe .

  ,Karfe shadaya daidai deeni Yashiga dakin Zeenat byn ya gama shirin bacci  cikin wasu  ratsasun kayan  bacci.m masu matukar kyau.

    batasan shigowarsa  ba tana can duniyar  tunani “ahankali DEENI yakaraso har inda take tare da   ya kamo tafin  hannuta cikin nasa Yana murzawa  sannan ta juyo ‘ahankali tana sauke naunauyen ajiyar zuciya.

ya tsareta da idanunshi kawai sannan   yace meke damunki  Zeenat ?

Ke ke nan  kullun bakya gajiya ,ki raba kanki da wannan  tunani ,kisani tunani shine abu mafi sauki dake saurin nakasa rayuwar  Dan Adama  Amman ke kin maidashi abincin cinki kullun ..,kinsa Allah ba tunaninki ke damuna ba ,halin da first lov zata shiga sanadin wani abu ya sameki nake .idan  akwai abinda kika san yana  dumunki please tell me…
tayi shr kawai tana kallonsa sun dade a haka suna kallon junansu   sannan ,  ko me ta tuna Kuma  ta sakar masa murmushi karfin hali ta matse hannushi cikin nata gam tare da  lumshe masa  idanunta ta girgiza masa kai alamun bbu komai . +

Deeni yace I you sure bbu komai” ta dage masa girarta daya kmr yadda yake mata shima, har taso tabashi dariya yayi murmushi tare kwantowa jikinta  ya rungumeta  ajikinsa tsam tsam  Yana aika mata da sakwanninsa masu matukar birkita mata kwalkwaluwa ..   hannuwansa duka yasa ya zagaye kugunta  dashi  ,Haka kawai Yashiga aiyanata  yarinyar, ‘ahankali ya sake narke mata ajiki yana duk inda hannushi yaci karo dashi itama cikin kwarewa tasoma  romancing dinshi .

ranar dai kwana sukayi suna jiyar da kansu dadi  deeni yayi  Tayi batare gajiya ba  .
Iya  murzuwa Zeenat Tayi shi a hannun DEENI  har kai  saka  masa  kuka sannan  yabarta ya Mike  Yana mata korafin tacika  ragunwaci.
ita batace masa komai ba .  washegari gari  ma da kyar tasoma tashi yayinda  da kyar ta dinga  kafafunta,  bayi tashiga  ta gasa jikinta da ruwan zafi  .

baita tabar gidan ba Sai wuraren 9 AM .. ..

Tun byn fitar Zeenat nablah ke faman  aikin gyaran gidan batare da samu damar zama ta huta ba.
  ,duk da matar gidan bata nan   hakan bai hanata yin kokarin taga ta kammala da aikin ba .
+

Tana tsaye a kitchen din yayinda hannuta ke kai kawon   gogen kayan kitchen din  Wanda  ya zame mata  dole kullun garin Allah Ya waye sai tayi.

  laraba ce tashigo kitchen din tana yimata sannu tare da sanya hannu tasoma kokarin taimakawa nabla da  wasu  ayyukan .

Nablah Tayi murmushi dama kinbarshi aunty yanzu zan gama ai”

Karki damu sis nima zaune nake bana aikin komai shiyasa kikaga naxo .

gashi km Naga kmr  aikin Yayi miki yawa dan nasan yadda yanayin aikin gidan nan yake da  cin rai  km bai karewa.
  ” Dan ma  Allah taimaka  madam  batanan da yanzu tasa jininki ya hau kilometers duhu.

,Dan har gara hjy da mai gidan akanta ” Dan shi maigidan kwata kwata  baya shiga harkar mutune yayinda ita   hjy   wani lokacin   takan tausayawa mutun.

nablah tace Haka ne  .laraba tacigaba

amman ita madam Komai zata saka mutun Sai ta nuna maka iko da isa ” Ga zagin rashin mutunci , tamkar ta haifi mutane , km duk irin  aikin da zakiyi mata idan bai gamsar daita  a banza yake a gurinta  .

nablah Tayi shr kawai tana sauraronta  batare da tace mata ba , komai Sai ma maida hankalinta  datayi kan aikinta.

laraba ta sake  cigaba kinsa Allah ko abinci kika dafa wannan matar , muddin baiyi mata ba wlh dole ki sake yin wani  .

Nablah dake tsaye ‘tana  aikinta , tace nifa Ina ganin kmr mdm din nan taki , kwarkwar ce…….

  “Haba aiko  laraba ta kwashe da wata muguwar  dariya , kai   gsky nablah baki da kirki wlh  madam din ce kwarkwar tana mai  sake kwashewa da dariya .

nablah ta bar abinda take ta juyo Sosai  tana duban inda  laraba take .

Kinsa Allah  wlh Ni kallon kwarkwar nakewa  matar nan  sbd wasu abubuwa dana Ga tana yi  Na marasa hankali.

nan dai sukai ta hirarsu tare da  zagin Zeenat din ,.
nablah har da cewa Allah Yasa ogon madam yakarowa mdm amarya labara Tayi saurin kai hannuta ta toshe wa nablah baki ,tare da leka parlour sakamakon jin kmr  motsin mutun .
  “ganin     bbu alamun  kowa ne yasa ta dawo ta tsaya  kusa da nablah . +

“ai inaganin  abinda mdm din tafi   tsana kennan a rayuwarta .

  “kishiya…. uhm zata iya yin komai akan mijinta. ba kya ganin ko inda mijinta yake bata son  ana zuwa ,ke ko kananan kaya kika saka wlh  Sai takawa mutun  miki birki da guzirin  Harare da zagin .

,kinji ba , ai abinda yasa  kikaji nace miki ,  Ina mata kallon kwarkwar  ,Dan some time sai inga kmr  tana  hararata byn ban mata komai ba inji cewar nablah.

Laraba ta numfasa sannan tace shiyasa  lamarin  zaman gidan Sai kin kara da  hakuri. nabla ta sauke naunauyen ajiye zuciya sannan tace indai   hakan kike fama da matar nan  Na jinjina miki dan gsky kinyi kokari wlh.

, ai a Haka ma   bakiga   komai ba indai mdm ce  inji cewar laraba , Dan naga kmr ke  kina da wani      matsayi a  gidan” tunda har an barki kina ganin mai gidan ,gashi km har  special room  aka baki a sama.

” Mtssss nablah taja wata muguwar tsaki  matsayi ko walaha byn  bakada wata  darajar a idanun masu gidan. “nabla ta sake yin kasa kasa  da muryarta  Dan kar wani yajiyo abinda zata ce sannan tacigaba abinda zan fada din nan  Dan Allah bana son ki fadawa kowa” Amman  Allah nayi mugun tsanar mdm  Zeenat  din nan byn Haka km Ina fatan  Allah Yasa mijinta ya kara aure.

, Dan kawai nayi  kallon irin  kalar haukar da zatayi koda yake ma ,may be by the  time din   da zai kara  auren ma ,na dade da   barin gidan Dan bana jin zan  dau wani   lokaci a gidan nan .
, laraba tayi saurin marairaice fuska   haba nabla Dan Allah kada kiyi Haka ,Karki tafi ki barni na rigada na saba dake banzan so ki tafi kibarni ba .hakuri kawai zakiyi da halinta ,kiyi abinda yakawo ki.
laraba  da nabla suka cigaba da aikinsu  suna hira sama sama laraba Na sake  cigaba dabawa nablah labarin gidan dama estate din gabadaya ,Da yake  ita  tana fita sosai .
nabla sai murmushi take km tana kwadayin fita taga yanayin estate din  Dan tun zuwanta gidan ko get bata sake lekawa ba .
+

Washegari  gabadaya da gyre gyre  aka tashi  dashi a gidan.

koina ka kalla a  hargitse  yake saboda wani gyara da  za’a a sama da km zuwan  bakuwar daza suyi daga kasar  India, kmr yadda  nabla taji  zeenat nafawa wata friend dinta datazo .

   kai kawo nablah ta dinga yi tsakanin upstairs da downstairs , kallo daya zakamata  ka gane tsansar yadda ta fita haiyacinta tsabar gajiyar dake tattare daita dole ma  kaji ta baka tausayi .

tsaye take kusa da  zeenat ta takure jikinta waje daya , byn ta gama waken kayan da Zeenat din  tayi amfani dasu ,banda harara da kallon banza bbu abinda take jiho mata .

,A zafafe Zeenat din ta kallo inda nablah ke tsaye   kinzo kin wani  tsayamin a kai kmr zaki tsotsemin jinin  jiki   ki dauki plastic ki kawai my hrt.. takarasa fadar Haka tana watsawa nablah wanimugun harara .

Nablah tasa  ‘hannu  kennan zata dauka  sai ga laraba tashigo kitchen  wasu kayan wando jeans da Riga   Tayi gurin  frij  .

zeenat ta kallite  ta kalli kayan jikin laraba sannan ta watsa mata wata uwar  harara ,har  nablah ta ji hantar cikinta sun cure gurin daya  .

Fuskarta a yatsine Tace meyye haka kuma  laraba …kinsa   bana son wannan iskanci a gidana .

bama na hanaki saka  irin wayan nan  kayan ba?

  Nablah ta dago ta dubi aunty laraba  jens ne a jikinta sai riga iya gwiwa .

   ok  karuwanci  kika zo yimin a gida ko me?

  , da sauri laraba  tasoma bata hakuri .
dan Allah madam kiyi hakuri wlh  bazan sake sanya su  ba wannan mistake ne .
,da hannuta mdm Zeenat  ta dakarta da ita ya isa bana son jin komai  daga yanzu ma na kashe sa irin iriin wayandanan kaya muddin kina son zamanki ya daure  dani. sannan ta kallo inda nablah   tsaye  har lokacin bataje inda ta aiketa ba ,tsawa ta buga mata  ke kuma  tsayuwar uban  me kikewa mutane da bazaki wuce ba   kin wani tsareni  da shegun idanuki masu kama dana mayu..  bazaki wuce inda na aike ki ba.Duk da  nablah taji maseefar  tsoron  yadda taga  Zeenat Tayi Amman hakan bai sa ta nuna ta fito da tsoronta filli ba a dake sannan km fuskarta a hade   ta  bar kitchen  din  hade da tausayawa kai banta. +

Domin bata  ganin laifi Zeenat   sai nata domin ita takawo kanta da kanta cikin wannan maseefa.

  Ta Dan tsaya kafin takarasa parlour mai gidan Tasa ‘hijab dinta  tana goge hawayen daya yasoma bin kuncinta dan  iri irin abinda   zeenat takeyi musu  yana  taba mata zuciya  sosai .

‘cikin sanyin jiki  tasoma tafiya har ta iso parlour da mai gidan yake tare da  bakinsa  da sallamarta tashigo. muryata fal cike da tsoro da fargaba.

   kallo daya DEENI yayi mata ya dauke idanunsa sai abokansa  guda biyu ne  suka amsa mata  sallamar.

, ahankali cikin tafiyarta  mai daukar hankalin ga duk wanda ya kalleta  , ta karaso ciki sosai ,  ta tsugunna ta ajiye plastic din da cup’s .

Banda   kallon kasa ido  bbu abinda DEENI yake mata ,’ahankali tare da natsuwa ta soma tsiyaya  musu coffee . 

cikin wata kwasatsiyar murya taji ance ke zaman me kikeyiwa mutane anan  …. oya live this place now…

   Gabanta ya dukan uku uku ,cikin tsananin tsoro hade da tashin hankali ta Mike tsaye , jikinta  ,har rawa rawa yake tasoma kokarin daga kafafunta yayinda  idanunta suka ciciko da hawaye tafff, ta bar parlour,  daidai bakin kofar main parlour  ta kusan ci karo da  zeenat da sauri taja da baya ta tsaya, tana mai sa  bayan hannuta tana goge hawayen dake bin  fuskarta.

Zeenat ta tsaya kawai tana kallonta tare da nazarinta da kyau sannan tace  kukan munafurcin uban  me kikeyiwa mutane ,kmr ba aikin kudi kikazo yi ba tasoma maseefa tana  zaginta . +

, duk yadda nablah taso hadiya damuwar dake zuciyarta  hakan yakasa samuwa , domin kuwa sabon Hawayen dake makale a idanunta ne suka samu nasarar zubowa .

  , uhmmmm daman Sai Dana gaya ummi tabari a sallemiki Dan nasan  bazaki iya tabukawa mutane komai Amman tace Sam…

Yanzu kukan iskanci me kikeyiwa mutane nablah ta girgirza kai tare da cewa bbu .

Zeenat ta tasoma kada kai cewa   zama ayi komai din sannan   ta Miko nablah wani karamin jug mai dauke suga  tace ungo Ni  ki kaiwa    mijinta baiwar banza kawai.

,jikinta a sanyaye  km  badan ranta yaso ba  ta sake koma parlour   …

byn ta fito ne  ma abokinsa manir yace DEENI  ina kasamo wannan fine bby din mai tsabar kyau gaskiya tamin kyau sosai  …..

Take  DEENI ya hade rai tamkar Wanda yaji wani mugun abu .. meye matsalarka daita ?

Manir yace yarinyar ce tamun kyau kawai  , a  fusace deeni yace bakowa bace facce    house girl dina.

dayan abokin nasa ne  yace  gaskiya yarinyar tana da kyau sosai ba karya gashi Tayi maseefar ta haduwa dayawa .

irin  wayan nan Ai  nashiga mota ne  da kewaye kasashen duniya .

A zafafe DEENI yace  bafa nason iskanci nan naku idan abinda yakawoku kennan natashi nakama gabana .

Manir yayi dariya tare da cewa kai fa matsalar kennan to laifi ne dan mutun yaga abu ya yaba sai  km yazama abin damuwa.

Fahad  dake zaune yana nazarin deeni ya amshe da cewa   kai meyasa DEENI kike yin irin haka ne ? Kacika daukar komai da zafe.

DEENI  ya hassala  dan takaici Dan  Allah ni kun dameni da zance wata  banza yarinyar ni wlh duk na Raina da ajinku wlh .

  ” da har kuka tsaya karewa wannan banzar yarinyar kallo ”  fahad yace idan kai makahone baka gani  mu wlh muna  Gani ,kuma  dole mu yaba baiwar da Allah yayi .

  , ‘Ahankali ya ture document din dake zube gabansa ,Coffeen  da nablah tasoma  siyaya a cup, din yasa ‘hannu  ya dauka yasoma  kurba ahankali ahankali  tare da lumshe ritattun  idanunshi .

Manir da fahad  suka bishi  da wani irin kallo ganin abinda yayi . yayinda manir ya cika da mamakin deeni .

Fahad   yace  mekake nufi yanzu  da haka sai da hadeye wanda ke bakinshi sannan yace ga abinda nake nufi nan kuwa ,  kowa ya yakama gabansa.

Manir yayi murmushi sannan yace to munji amman zai siyayyamu coffee to  , juyar da fuskasa yayi wani gefen sannan yace  ai duk kuna da ‘hannu ,idan baku tashi Sha ba ,kubarshi .

murmushin fahad  ya sake yi yace  da alamun rashin mutunci  kawai kake son yimana . +

DEENI  ya daga kafadunsa,  duka a alamun  I don’t care .

nan dai suka mai da abun wasa atsakaninsu  suka cigaba dayin  abinda ya kawo su byn sungama ne DEENI ya Mike yace yana zuwa .

Zuwa yayi   ya canza kayan jikinsa zuwa kanan kaya  sai kamshi  mat Hamilton 27  yake zubawa   part din ummi  yashiga yana kiran sunanta  .. first lov..  were are you .

jin shiru bata amsa bane yasashi  kutsa kansa cikin bedroom dinta kai tsaye batare da yayi tunanin wani abu .

Ita  kuwa dake   zaune  tana jerawa  ummi  kayanta  da mai wakin yakawo dazu  a Waldrop ta  zabura ta Mike  tsaye da   sauri,  duk ilaihi  jikinta bbu inda Bai dauki  rawa ba  saboda tsabar tsoron muryar data  jiyo.

Sosai kamshin turarensa ke kusanto dakin alamun yana gab da shigowa .   gashi   bbu  komai ajikinta  daga ita sai  daguwar riga   mai ‘hannu harmless  cikin sauri sauri ta  soma neman hijab dinta .

data cire amman tarasa inda ta ,ajiye   .

har yashigo dakin , cak ta tsaya ta kasa kwakwarar motse ,jin tsayuwarsa jingine da kofa yasa take kirjinta ya buga yayinda  zuciyata tashiga  ..

  aikin da tasaba a duk  sanda , ta kasance tare da DEENI.

shima tsaye cak  yana Kare mata   kallo  tsab wanda in ba lura mutun yayi   da kyau ba.

,ba za’ice  ita yake bi da wannan mayataccen  kallo ba .

shida kansa yasan in yace yarinyar batayi ba , tabbas karya yake km  son ranshi ya fada .

    ahankali   yakaraso dakin  sosai yana sake kiran sunna ummi . kainta  a sunkuye a kasa yayinda  zuciyata ke  wani irin bugawa da sauri  cikin siririyar muryata mai cike da in inna … tace ta.. tana.. bathroom …

Bai ma tsaya wani sararonta ba ballanantana  ya nuna alamun yaji abinda tace ba ,  tunda shima yaji alamun haka.

juya kawai yayi yabar dakin cikin takunsa ,na tsanyaye namiji .

  Numfashi ta sauke tana may sa dukka  ‘hannuna ta dafe kirjinta dashi  tare da  sauke ajiye zuciya.

wayyo Allah  wannan mutumin  ba dai  frigita mutane  ba .

numfashi ta dinga  fitarwa  ‘ahankali ‘ahankali har  ta dawo normal .km Sai a lokacin taga  hijab din ta washe   a gefen ‘tsabar rudewa ce tasa  takasa Gani.

  fitar shi  bai fi da minti uku ba ummi  tafito tanawa nablah  sannu da aiki sannan tasamu  waje ta zauna,  tana dan Jan nabla  da hira , itama  dai ba laifi  takan dan saki jikinta ummi dan tafi zeenat sau dubu har aka kira sallah suna  tare da ummi  dan dakin tadawo yanxun saboda aikin da za’a yi Wanda ya hada  har da dakin nablah.

Mikewa tayi nablah Tayi tare  cewa ummi Ina son  naje  nayi sallah .

murmushin ummi Tayi  haba nablah yanzu sallah ma sai kin tambaya ,ummi girgiza kawai tare da cewa  ,jeki kawai kiyi sallahrki kinji  ..

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *