WANNAN RAYUWAR CHAPTER 11

 WANNAN RAYUWAR CHAPTER 11

Cikin gida suka dawo Hafsa ta shiga daki wayar ta tagani tana haske tana dubawa taga Ahmad ne dauka tayi tai sallama yace
“Ina kika shiga ne ina ta kira!”+

“Wallahi na fita naje gun Halima ne!”
“Ohk ya jikin nata?”

“Da sauki!”
“Allah kara sauki!”

“Amin”


“Daman zan fada miki gani nan karasowa! Zan zo naga my princess naga ita me takara sannan in amshi amsa ta.”

Murmushi tayi yace
“Toh Allah kawo ka lafiya.”
Yace
“Amin nagode! Kin shirya kenan”

“A’ah!”
“In nazo ma kya shirya ai.”

“Sai ka karaso.”
Ta fada yace
“Ok!”

Mai fruit ya sama ya siyawa Halima da yawan gaske sanna ya tada mota ya nufi gidan su Hafsa yana mai jin wani farinciki da dadi na ratsa dukkan jikinsa da zuciyar sa.

Yana kashe wayar ta mike ta canja kaya sannan ta zauna kirjin ta na dukan uku uku tunanin ta tayaya zata amshi soyayyar sa in taki kuma menene dalilin ta.
Tana zaune wayar tabta hau kara dauka tayi ta duba taga Ahmad ne dauka tayi yace
“Ina kofar gida!”

“Ok!”
Ta mike ta saka hijab sannan ta shafa turare ta fito. Umma ta sama tace
“Umma nayi bako bari naje mu gaisa.”

“To a kiyaye dai.”
“Insha Allah!”
Sannan ta fita. Yara ta gani suna shigo da bugun dankali da goya sai kayan marmari.

Kanin ta Lukman yace
“Yaya ke akace mu kawowa!”
“Ni kuma inji wa?”

“Yana waje!”
“Ok!”
Ta fada tana basu hanya sannan ta shimfida masa darduma ita kuma tayi waje. Tsaye ta ganshi jikin motar sa ya zubowa kofar gidan ido yana hango ta ya saki murmushi sannan ya fara takun sa mai kyau da nutsuwa yayo kofar gidan.

Sam bata san ya karaso ba, sai ganin sa tayi a gaban ta ba karamin kunya taji ba ta juya tayi ciki yabi bayan ta. Zama tayi a can karshen dardumar sannan shima ya cire takalmin sa ya zauna.

Kanta a kasa tace
“Ina yini?”
“Alhamdulillah ya kike?”

“Alhamdulillah!”
“Ya me jikin?”

“Da sauki!”
“Allah kara afuwa!”

“Amin!”
“Uhmm ina jin ki?”

Dagowa tayi ta dan kalle shi sai karaf suka hada ido. Kai ta dauke da sauri yai murmushi yace
“Ashe ke barauniya ce.”

Da sauri tana kallon sa. Yce
“You stole me heart!”
Waya ajiyar zuciya ta saki yace
“Haka ake kin dauke tawa amman kin ki bani taki biyu ta miki yawa ki taumaka ki ban taki zan kula miki da ita fiye da yadda zan kula da tawa.”

Bata san lokacin data sake wani murmushi ba tare da lumshe ido. Shima murnushin yake Yace
“Hafsa na fada miki ban taba soyayya ba kece the  first girl dana taba cewa ina so kuma kece macen da na taba  zama da fadawa ina so har nake bin ki kina gudu na. what I know is that your love makes love change me har nake abubuwa ba tare da na sani ba. Wanu lokacin cin naji sam in ban ganki ba kanar zan mutu ne. Hafsa i love you amson da ban san dashi ba da ban yadda da wani abu so kamar haka ba saib yanzu a yanzu ina jin I can do anything just to have you.”

STORY CONTINUES BELOW
Hafsa jin maganan Ahmad take har cikin ranta da duka gangan jikinta, takan rasa mai yasa take jin sonsa da kaunar sa a ko da yaushe tana ganin sa daban a cikin mutane domin tana ganin shi yafi sauran samarinta, ita dai tasan zuciyar ta ta riga ta kamu da sonshi ne, amma shine kadai yake magana da ita taji bata son ya Bari sannan takan sami nutsuwa Idan suna waya, takan rasa mai yasa ko wace kalma Indai ya fito daka bakinshi take jin dadinta ba, ta rasa dalilin hakan ga wani irin kwarjini da yake mata Sosai. Ba zata iya kin Ahmad ba domin yayi in ya tafi waye zai zo mata bata sani  amman kuma in suka aure ya same ta ba a yadda yai tsammani bafa?…….

Katse mata tunani yayi da fad’in
“My love ya ake ciki da maganar mu?”
Gabanta taji ya fadi ta yi kasa da kanta. Yace
“Bakya sona kenan!”

Kai ta girgiza yace
“Uhmm say it out mana.”
“Ni ban san me zance ba!”

“Iyee Lalla ashe dai Ahmad bai da sa’a da farin jini ace the first girll da ya taba gani yace yana so taki amsar sa. Allah sarki Ahmad ba tausaya maka yanzu shkn mutuwa zai yi.”
Tinda ya fara magabar ta dago tana satar kallon sa tana murmushi dan dariya ya bata sosai. Yace
“Oh dariya ma kike min ko?”

“To ai ni bance bana son ka ba.”
“Uhmm me kika ce to?”

Shiru tayi ya matso kusa da ita yana kallon ta kanta a kasa yace
“Hafsa aure fa zamuyi dole kunyar nan ki ajiye ta yanzu just kice kina sona shine baxa ki iya ba.”

Sai ya koma ya zauna ya shagwabe fuska ya daga hannu ya kai wajen fuskar sayace
“Ni Allah kice kina sona!”

Dagowa tayi ta bishi da kallo ya hau buga kafa yace
“Uhmm uhmm ni ki fada.”

Dariya ta fashe da ita sai ya saki kamar karya yana fadin
“Au dariya ma kike min.”

“No no please sorry nifa ba dariya bake ba.”
“Me kike in ba dariya ba ni ki fada min.”

Tace
“To is ok naji ina son ka.”
Da sauri ya dago yana kallon ta yace
“Da gaske?”

Kai ta gyada sai kuma ta rufe fuskar ta. Ya saki murmushin sa mai kyau yace
“Alhamdulillah yanzu zan iya turowa kenan!”

“Not nowa Deedat!”
“Why?”

“Dududu yaushe kayi aure!”
“Shine me? Ni dai gaskiya ina so kwanan nan.”

“Gaskiya ka dada lokaci ya kamata ko shekara ne kuyi!”.
” shekara Hafsa wallahi ba zan iya shekara babu ke ba ke ko five month ba zan iya ba. Zan baki nan da wata daya zan turo gida ayi maganar auren mu.”

“Deedat!”
“Menene matsalar ?”

“Gashi nan na dada maka!”
“Wannan ba matsalar ki bace ai.”

“Amman ai….”
“A bar maganar nidai ga yadda nace nan in kina sona ki accepting a haka.”

“To Allah yasa haka ya zama.mafi alheri.”
“Amin Baby na amarya ta.”

Shiru tayi yaxe
“Sai mu fara shiri ko?”
“Shirin me?”

“Bikin mu.”
“Kai Deedat da saura ka bari mana.”

“Na bari shikenan!”
Ta gyada masa kan ta.
Haka yai ta janta da hira har ta sake dashi. Da zai tafi aka kira Halima yai mata sanni ya bata 20k da kyar ta amsa sannan sukai sallama da Hafsa yace gobe zai dawo.

*
Yaba shiga gidan su bangaren mahaifin ya ya nufa. A falo ya same shi yana waya zama Yayi yana jira ya gama bayan ya kashe wayan  ya kalli Ahmad uace
“Yaushe ka shigo garin baka fada min ba.”

“Dazu Dady nazo ganin amarya tane!”
“Waxce fa?”

Fuaka ya bat kkamar zai kuka yace
“Wacce na fada maka mana Dady!”
“Oh na tuno ta. Wajen ta kazo kenan ka baro Hanna a can.”

“Dad na kasa zama.ne acan ita kawai bake son gani.”
“To yanzu ka ganta?”

“Yes Dad!”
“Sai ka koma gobe.”

“Sai monday Dad ya za ayi ina son a fara shirin bikin mu.”
“Amman Ahmad yaushe akai bikin ka ni nai maka alkawari zan maka auren wacce kake so amman ba yanzu ba sai ka kara zama da matar ka ka fuskance ta itama haka.”

“Har zuwa yaushe Dady!”
“Kuyi shekara.”

“Dady wallahi ba zan.iya shekara ba Hasa ba dan Allah ka taimaka min.”
“Shikenan nan da wata uku yayi!”

“Uhm wata uku Dady…”
“Eh! Bana son na dauko maganar Mum din ka ta ga lokacin yayi kusa.”

“Eh kuma fa haka ne.”
“Yauwah ka bari a yadda nace din amman ka cigaba da neman ta Allah tabbatar da alheri.”
Hugging Dadyn dinshi yayi tare da fad’in
“Godiya nake Allah kara gurma da nisan kwana. Allah jikan mahaifa.”

Dady ya amsa da
“Amin amin!”
Sannan ya mike zai fita Momy ta shigo.
“Damab yanzu ake ce min ka zo nace me.kazo ina ita Hannah”

“Tana Abuja.”
“Amman ka baro ta.”

“Haba Momy dan zan dan zo shine sai na tabo da ita. Yaushe dudud muka tafi.”
“Shiyasa nake mamakin zuwan naka ai.”

“Wani aiki nazo yi na kwana biyu.”
“Oh Allah bada sa’a “

“Amin Mony nah.”
Ya mike yace
“Bari naje na kwanta sai da safe.”

“Allah bamu alheru. Kaci abinci.”
“Na koshi.”
A ransa kusa fadi yake wane abinci zanci naga rabin raina

*
**
***
****
*****
******
*******
Yana tashi da safe ya hau hada jakar sa. Ya shiga yai wanka ya dauko jakar tasa ya fito falo ya ajiye. A dining ya samu Hajiyar da Dad din sa. Ya karasa ya gaishe da Dad ya amsa yana fadin
“Ya jikin Son!”

“Naji sauki dad!”
“Allah kara sauki.”

“Amin!”
Ya kalli Hajuyar yace
“Ina kwana Momy”

A share ta amsa ya zauna ya sha tea da bread kawai ya mike  Dad yace
“Ba dai har ka fito ba?”

“Yes Dad gwara naje da wuri.”
“Shikenan zan turo maka da kudi ka kiyaye Mu’azam Allah ya tsare hanya.”

“Amin Dad!”
Ya kalli Hajiyar sa ta dauke kai  yace
“Mom your prayer please!”

“Allah sauke ka lafiya.”
“Amin!”.
Ya fita driver yasa ya kaishi airport yana zuwa ya yanki ticket sannan ya zauna dan sai nan da awa byu jirgin zai. Duj ya matso dan ganin awa biyu  yake kamar sati Biyu.

A haka da kyar yaga lokaci yayi suka tashi shi kansa gani yaui kanar jirgin baya tafiya. A haka dai suka sauka lafiya. Taxi ya samu ta dauke shi su suka isa hotel. Ya kama daki ya shiga yai wanka.ya dan ci abinci sannan ya shirya ya fito.

Wayar da ta tubuta a address ya dauko ga unguwa nan da layi amman ba number gida. Haka ya fita ya fadawa ma napep inda zashi ba bata lokaci suka isa imdai dai inda ta fada. Tsayawa yayi a titin yana tunanin ta ina zai fara dan dogon layi nr.

Yana tsaye wani yazo wucewa yace
” Assalam alikun bawan Allah.”

“Wa’alaikum salam”
“Dan Allah tambya nakr!”..

” Allah yasa na sani “
“Gidan su wata Sakina.”

“Ayyah wallahi ba a unguwar nake ba.,”
“Ok nagode!”

Wani yazo ya kara tambaya amman bai santa ba wani gub mai shago yaje ya tambaya yace
“Sakina anan unguwar gaskiya ban san ta ba gudan wa tace maka?”

“Bata fada min ha gaskiya.”
“To gaskiya ba nan unguwar bane kla  wrong address ta baka.”

Ya tambayi fin mutum uku ba wanda ya sani tin yamma yake abu har magariba yai sallah ya koma hotel din da ya sauka jiki a sanyaye.

Sunyi wasa da Dady ya boye mada yace sun hadu tana gaishe shi amman sam.bai ganta ba dan kada ya tada masa da hankali ne.

*
A haka sai da yai kwana uku yana zuwa unguwar amman ba wanda yasan wata sakina domin yan gidn ba fita suka fiya ba bama Sakina da bata zama a garin. Gajiya yayi da hawa Napep kawia ya siyi nota.
*Dan Allah ku sani a addu’a akan Allah ya yayen abinda ke damuna ya biya min bukatu na na alheri.*

Abbah yace

“Ya zancen kafi Muhammad nace za aje a yi a gidan da na baka kace a dakata.”+

Kai yayi kasa dashi yace

“Haka ne Abba daman ina can nake aiko da kudi ana min gini anan to shine yanzu ma daga can nake an gama komai a jiya shiyasa nace a dakata. Kuma Abbah ina neman wata alfarma dan Allah.”

“To masha Allah hakan ma yana da kyau ai. Allah sanya alheri.”

“Amin!”

“To wacce alfarma kenan?”

“Abba daman so nake a bani dama na zuba kayan cikin gidan ba sai anje wani kafi ba ni zanyi.”

“A’ah A’ah Muhammad haka ma ya isa,  kaya an riga an siyo dan haka kayi hakuri kawai Allah yayi albarka.”

“Amin to Abba na gode yaushe zan kai ka, ka gano gidan?”

“Sai wani lokacin Muhammad!”

Hannu ya zura a aljihu ya ajiye keys din yace

“To ga makullin gidan nan sai a fadi lokacin da za aje kafin zan aiko motoci.”

“Haba Muhammad ai wahalar sai taimaka yawa.”

“Dan Allah Abba kada kace A’ah ka bari kawai azo a akai su.”

“To shikenan Allah ya kaimu gobe ne da safe tinda kaga a gobe zata tare kamar karfe tara sai su tafi ayo kafin.”

“To Allah kaimu.”

“Amin! Su Umma na ciki zan shiga na gaishe su.”

“Suna nan muje na rakaka.”

Suka mike Abba na gaba Muhammad na bin sa a baya har falon Umma dake zaune suna ta lissafi. Tana ganin sa ta mike tana fadin

“Ah Muhammad an dawo ashe.”

Ya durkusa yace

“Eh Umma ina yini mun sameku lafiya?”

“Alhamdulullah!”

“Masha Allah! Yasu Hajiyar taka?

” Tana lafiya. Tace agaishe ku”

“Masha Allah muna amsawa.”

Sannan yace

“To sai anjima.”

“To ka gaishe ta da yaran!”

“Zasuji nagode!”

Suka nufi dakin Mama dake zaune tana waya. suna shiga ta dinga binsu da kallo dan ita ta kasa gane Muhammad ma. Sai da ya gaishe ta sannan Abba yace

“Muhammad ne mijin Ummu fa.”

Fuska ta bata tace

“Oh ashe ya dawo!”

“Ya dawo dazu!”

“To madallah!”

Ya mike yace

“To sai anjima.”

“Mujima da yawa!”

Suka fito. Ya dan rissina yace

“To Abba ni zan koma.”

“To Muhammad ka gaishe da Babar taka.”

“Zata ji.”

Har ya juya Abbah yace

“Zo!”

Ya dawo yace

“Baka ga Ummu ba ko?”

Yai kasa da kansa ya kasa magana. Abbah yai murmushi yace

“Tana gidan Zainab nasan gobe zata dawo nima tinda ta dawo sau daya na ganta Zainab ta kwance min ‘ya.”

Muhammad yace

“Ba komai Abbah nagode.”

“To ka gaisa gida!”

“Insha Allah.”

Ya fice. Gidan Anty Zainab ya wuce kai tsaye bayan yai parking yaran suka taho suna ganin sa suka hau fadin

“Oyoyo Uncle!”

STORY CONTINUES BELOW

Ya dauki karami yana fadin

“Ya kuke?”

Baban yace

“ina yini Uncle!”

“Lafiya ya kake?”

Mai binsa ma ya gaishe shi. Karamin dake hannun sa shima yana gwaranci ya gaishe shi ya amsa yana murmushi. Sannan ya kalli Baban yace

“Kaje kacewa Umman ka Uncle yazo.”

Nan yai ciki da gudu. Bai jima ba ya dawo yace.

“Momy tace ka shigo.”

Shiga sukai tare ya basu sweet duk sukai godiya sannan suka koma can compound suna wasan su. Gaisawa sukai da Anty Zainab tana fadin

“Ya Hanya?”

“Alhamdulillah Anty ya gida?”

“Alhamdulillah.”

Sanna ta mike dan ta kawo masa ruwa da lemo. Tana mikewa ya dauki wayar sa ya fara neman layin Ummu!

*

Ummu kuwa tana can wajen gyaran kai da lalle dan tin safe wajen goma ta fita sai daya aka gama mata jan lalle sai da tayi sallah tasha maltina karfe biyu aka farai mata baki yadda ake zanawa kamar dashi aka hallice ta domin yai kyau ya hau kan kafa da hannun nata. Sai uku aka gama ta zauna dan ya bushe. Karfe hudu aka kankare sannan tayi sallah aka hau gyara mata kanta.

*

Tana cikin dryer taji wayar ta dake cinya tavfara vibrating dauka tayi taga Muhammad ne. Murmushi tayi ta dannan received sannan ta fito da kan ta dan answering call din.

“Amarya ta tana ina? Nazo gida ina ta zuba ido ban ganki ba.”

“Haba dai ka sauka kenan!”

“Na sauka Ummu tin dazu na kira ki baki dauka ba ai.”

“Ayyah wallahi ban gani ba wayar na jaka. Ka dawo lafiya ya hanya da gajiya.”

“Ban amsawa ta waya ki fito ina falon Anty Zainab kimin barka da zuwan.”

Tai murmushi tace

“Nifa bana gida!”

“Kina ina to?”

“Ina wajen gyaran kai fa.”

“A ina ne?”

Dai dai fitowar Anty Zainab. Tace

“Zoo road!”

“Ok gani nan.”

Ya mike. Anty Zainab tace

“Ina zaka kuma na kawo maka lemo da ruwa.”

“Anty Zanje wajen Ummu ne yanzu zamu dawo.”

“Ok! Sai kun dawo.”

Ya fice da sauri. Yana zuwa inda take yai mata waya yace

“An gama ne?”

Ta ce

“A’ah ana dai yi.”

“Ok!”

Ya fada ya fito daga mota. Babban waje ne dan haka ya shiga ya tambaya wajen manager can yaje ya fada masa yana son yaga matar sa ana gyara mata kai. Sunan ta ya fada nan ya sa aka duba room nawa take sannan yasa ai masa jagorancu.

Lokacin da suka shiga har an fito da ita daga dryer ana gyara mata kai. Ta runtsa ido saboda yadda taje jin zafin ana ja mata kai. Sam bata san ya shigo ba ta dai ji Mai gyara mata kan tace

“Welcome Sir!”

Bata ji mai ya yada ba dan hannu kadai ya daga ma matar. Sai da ta gama gyara mata sannan tace

“An gama Hajiya!”

Ido ta bude ta kalli kan ta da sai sheki yake ya sauka har gadon bayan ta. sannan ta kalli matar ta sakar mata murmusji tana fadin

“Thank you!”

Ta mike tana kade jikin ta za ta tafi zata dauki hijab din ta kenan ta ganshi zaune ya zuba mata ido. Da mamaki ta bude ido tana nuna shi. Mikewa yayi ya bude mata hannu a hankali ta karasa wajen sa tana zuwa ya rumgume ta yana fadin

“Uhmm Alhamdulillah finally am with my wife!”

Kokarin janye jikin ta take dan tasan basu kadai bane a dakin dame gyaran kai amman ya ki barin ta. Sai ajiyar zuciya da yake ta saukewa sai da ya nutsu sannan ya dawo yana kallon ta yace

“Sweetheart haka kika koma kinganki kuwa?”

Kunya ya bata tai saurin juya nasa baya. Ya juyo da ita yana shafa gashin kanta yace

“Kai amman gyaran nan yai kyau Sweetheart!”

Ya kamo hannu ta yana kallon zannen bakin lallan yace

“Tubarkallah masha Allah.”

STORY CONTINUES BELOW

Ya juyo tafin hannun nata da ya sha jan lalle bai san lokacin da ya sumbaci hannun ba dan Muhammad yana son lalle sosai. Duk wani iri take ji ya jata jikin sa yana fadin

“Da me lallen nan dame gyaran kan na sai na kara musu kudi kuma su zasu cigaba da miki domin yai min kyau sosai Ummu!”

“Kai Yaa Muhammad ai na biya su.”

“Wannan reward ne from ur husband saboda yadda yai kyau.”

“Uhmm ya kake ya hanya? Kai ko hutawa bakai ba kake yawo ko?”

“Zuwa ganin Gimbiyar tawa ne yawo.”

Murmushi tayi yace

“Kinsan da na ganki duk gajiya da abinda nake ji sun gudu!”

“Uhmm!”

“Kinyi kyau Ummu!”

Ya latsa jikin ta ya lumshe ido dan yadda yaji taushin jikin ta zama yayi ya daura ta akan cinyar sa ta fara mutsu mustun tashi yace

“A’ah Ummu mijin kine fa.”

Daina motsin tayi tai kasa da kanta kawai. Hannu yasa ya dago kanta yana kallon idon ta da sauri tai kasa da idon nata yai murmushi yace

“Haba Amarya ta ki barni naga kwayar idon naki mana.”

Mikewa tayi da sauri tace

“Dan Allah tashi mu tafi.”

Kallon ta ya tsaya yi tin daga sama har kasa. Doguwar riga ce a jikin ta mai A Shape ta kamata daga dama ta baje daga kugunta. Ganin kallon da yake mata yasa tai saurin janyo Hijab din ta tana kokarin sawa ya amshe.

“Dan ina kallon ki shine zaki rufe jikin ki Ummu mijin kine fa ni.”

Kai tayi kasa dashi,  ya matso yana rumgune ta ya saka kan sa a kaffadar ta yana shinshinar wuyan ta dake fitar da wani kamshi na daban dagowa yayi ya kissing forehead nata sannan yayi mata a kumatun ta, ido ta runtse yai wa idon ta sannan yai wa dogon hancin ta batai aune ba sai jin bakin sa tayi a cikin nata.

*

**

***

****

*****

******

*******

Zaman Fauziyya da Muhammad zaman lafiya suka tana faranta Masa Shima haka sai dai har yanzu ba wani Abu da ya shiga tsakanin su domin Fauziyya tana tsoro da kunyar in haka ta faru kada Muhammad ya juya Mata baya. Wannan yasa Shima ya share a haka suke Shan soyayyar su Yana kulawa da ita sosai baya son yaga bacin ranta ko Kadan.

Zaune suke a falo tana gaban flask shi kuma Yana zaune yace

“Baby jibi tafiyar mu ya kamata muje gida ki fadawa Hafsa Dan tare zamu tafi!”

Dagowa tayi da zuba Masa abinci tayi tana fadin

“Oh da gaske?”

Kai ya gyada Mata, tace

“Amman naji Dadi sosai. Kenan gobe zamu gida?”

“Haka ne Amman me za a kaiwa su Baba?”

“No Ummah dai Baba me zai bukatar?”

Ta fada duk Dan kada yai Mata fada.

Yace

“Duk da haka. Ga kudin da nake Tarawa Dan in zamu gida dubu dari ne Sai muje a siya musu kayan abinci da wasu abun ko?”

“A’ah Kaga Ina da kudi ayi amfani dasu kawai. Naka ka ajiye Kai da zamuyi tafiya Kuma zaka cikin Yan uwa Suma zasu so Kai musu dawainiyya ka ajiye na gunka na guna Sai ayi abinda za ayi dasu yayi?”

“Baby!”

Ya fada Yana kamo hannun ta. Dagowa tayi tana kallon sa. Yace

“Meyasa kike son kina hanani kyautata Miki!”

“Ba haka bane baka dashi ne tinda Ina dashi sai mu rufawa juna asiri naka ka ajiye can ai amfani dasu nawa ayi Anan in sun yi saura sai mu hada mu tafi dasu haka yayi?”

“Allah Miki albarka.”

“Amin!”

“Amman da nawa za ayi kiyi shiru kawai.”

“Angode Allah Kara budi ya saka da alheri.”

“Amin Baby na. Addu’ar budin kawai Zaki min Amman ban son godiya.”

Tai murmushi ta dauki spoon tace

“Ni zanyi feeding naka yau sai cikin ka ya fashe Zan barka.”

“In mutu kenan!”

Fuska ta Bata tace

“Please ka daina fada ka mutu in ka mutu Ina zani?”

Hannun ta ya kamo yace

“Shikenan kada kiyi kuka ba yanzu Zan mutu ba sai min haifawa Ummi Ya’ya guda ashirin!”

Ido ta zaro tana fadin

“What? Asihirin? Da Mata nawa?”

“Ke kadai!”

Kai ta hau girgizawa tace

“Ba zan iya ba so kake na zama tsoho kawai.”

“No ai Zan Taya ki ki haifi goma na haifi goma.”

Kai ta make tace

“Naki wayon wannan kawai salon wayo ne.”

Janyo ta yayi yace

“Da gaske kinga sai kina haifa man biyu biyu uku uku baifi sau biyar zuwa bakwai kin gama ba.”

Dariya tai tace

“Eh lallai sannu!”

“Da gaske?”

“Ni am not twins bare na haifa!”

“Kar ki damu Ummi na Twins ne kinga zamu iya samu Ina da kanne Mata twins too Kinga kila dai mu samu.”

“Kasan kuwa I like twins!”

“Sai kin gaji da haihuwar su.”

Hancin shi taja tace

“I will not indai jinin ka ne!”

Rumgume ta yayi tace

“Kaga muci abinci in ba haka ba zai sanyi na Sanka.”

Yai Dariya yace

“Kin samu dai.”

“Ni ba ruwa ba.”

Murmushi kawai yayi. Haka suka dinga cin abincin tana bashi a Baki Yana Bata a Baki har suka koshi Nan suka zube suna zuba soyayyar su.

Sai goma suka tashi suka cire Kaya wanka suka shiga sukai a can ma Sai da suka gama soyayyar tasu suka koma daki abinsu. Suka shafa Mai suka saka kayan Bacci suka shige bargo. Kanta ya haye ta fara kuka tana fadin

“Wannan kayi nauyi yanzu fa gaskiya dagani nice zan hau kan na.”

Sauka yayi ta haye kan da ta zagaye hannayen ta a jikin sa. Yai kissing goshin ta tace

“Bacci fa zamuyi not dis!”

“Ni wallahi am not satisfied!”

Ido ta zaro tace

“Kana so ka gama tsotse ni!”

“To ki bani the other things please.”

Take yanayin ta ya sauya nan ya hau lallashi.

Ai sai ta saka Masa kuka. Yace

“Haba Baby menene na kukan to?”

“Ina cutar da Kai Dan Allah kayi hakuri Kar kayi fushi Dani mala’iku su tsinre min!”

“Haba Baby ba haka bane kiyi hakuri Dan Allah ba zan sake ba I love you kinji.”

Da kyar tayi shiru ya lallabata tayi Bacci.

Mikewa yayi ya dauro Alwala ya dawo ya tada sallah. Har karfe biyu Yana kan sallaya.

*

Firgigit ta tashi tana kallon dakin da take tana kallon Muhammad ta sauko ta fada jikin.

“Lafiya?”

Ya fada Yana shafa bayan ta.

Kai ta hau girgizawa tana fadin

“Akwai abinda yake faruwa a gida!”

Ta mike ta dauki waya zata Kira number wayar Hafsat. Wayar ya amsa Yana fadin

“Da Daren nan Baby me ya faru?”

“Ni dai ka bani na Kira naji ya suke?”

“A’ah! Fada min!”

*Alhamdulillah. Nagodewa Allah nagode da addu’o’in ku. Alhamdulillah jiki yayi sauki ina mai godiya Allah ya saka ya bar zumunci. Hakika naga kauna sosai. Wanda suka kira da wanda sukai min text ta waya da whatsapp,  groups duk na gani kuma nagode. Allah saka da alheri naji sauki kuma ina dai mai kara barar addu’ar ku.*”Ni dai nayi mafarki da Yan gida Kuma abun ba Dadi!”

Tana fada ta fashe da kuka.

“Ya Isa haka?”

Ya rumgume ta Yana shafa bayan ta a hankali kukan ta ya dinga tsayawa har tayi shiru gaba daya. Ya dauke ta suka hau saman gado ya kwantar da ita.

Mikewa tayi da sauri tana Fadi

“Dan Allah Muhammad kada ka barni Ina son ka Dan Allah kada ka juyan baya.”

“Ki daina fadar haka Baby. Insha Allahu mutuwa ce kadai zata raba mu Ina son ki ba Zan taba barin ki ba.”

Kai ta gyada tace

“Mu kwanta to.”

Kwanciyya yayi ta shige jikin sa. Ya tofa Mata addu’a. Take Bacci ya dauke ta.

Karfe 5:10am suka farka Dan sun Saba a tare suke tashi. Wanka sukai ya tafi masallaci ita Kuma tayi a daki. Tana idar wa tayi addu’a sannan ta tashi ta hau gyara gidan.

Ta gyarra daki ta share ta saka turaren wuta sannan ta share tsakar gida ta wanke bandaki. Kitchen ta shiga tai shara sannan ta fara wanke wanke ta gama ta daura tea.

Sannan ta shiga ta fara wanka tana fitowa ta zuba tea a flask sannan ta soya kwai ta shige daki.

Daki ta shiga ta shafa Mai tai kwalliya ta saka wani bakin less Mai adon ja dinkin riga da siket yai Mata kyau ta daura dauri.

Sam Bata ji bude kofar sa ba sai ji tayi an daga ta ta baya a tsorace ta juyo tana ganin shine ta fada jikin sa tana sakin ajiyar zuciya.

Yace

“Wai tsoron menene haka?”

Kai ta girgiza tace

“Ina ka shiga.”

“Yawo.”

“Katafi ka barni.”

“To ba gashi na dawo ba.”

“Ba ruwa a dakai.”

Ta tashi a jikin sata fita. Ruwa ta hada Masa ta dawo tace

“Na Kai maka ruwan wanka.”

Janyo ta yayi yace

“Ke Yar Nan da ni kike fushi to tuba nake naje maganar shagon Nan ne.”

“Amman kace yawo.”

“Tsokanar ki naje. Kinga Naga kosai na siyo Mana.”

Amsa tayi tace

“Kaje Kai wanka sai mu karya.”

Daki ya shiga ya cike kayan sannan yai wanka ya shirya yazo suka karya. Shi ya wanke cups din da plate sannan ya dawo daki. Tace

“Yaushe xamu tafi ne?”

“Ai ma Bari Sha biyu tayi ko?”

“Kai ai Rana tayi Nan da goma dai!”

“Sha daya dai Baby goma yai safiyya.”

“Shikenan Allah kaimu “

Tin goma ta dauki mayafi da jaka da takalmi Yana zaune Yana Tai Mata Dariya Basu fita ba sai Sha daya d arabi.

Wani supermarket suka shiga ya siya buhun shinkafa da tafiya Mai Maggi sabulun wanki da wanka sai biskit da alawa na yara. Sannan aka saka musu a napep suka fito suka dau hanyar gida.

Sha biyu da arbain da biyar suka Shiga unguwar ana tsayawa a kofar gida ya fito ai da gudu ta fito ta fada gida ya bita da kallo Yana girgiza Kai.

STORY CONTINUES BELOW

Yara ya sama ya suka shiga da kayan.

Tana shiga ta fara kwadawa Hafsa Kira. Hafsa na daki ta juyo kamar an Kiran ta tana fitowa taga Fauziyya da gudu ta Karasa ta rumgume ta Yana fadin

“Anty na oyoyo!”

Da kyar suka saki juna sai sukai dakin Ummah. Nan ta fada kan Umma tana Fadi

“Umma Ina yini?”

Ummah na kallon ta yadda Tai kyau tai fresh da gaske tace

“Masha Allah.”

Nan suka gaisa. Sakina ta fito tace

“Wow Anty kinyi kyau!”

Ta rumgume ta duk yaran gidan suka bai baye ta ana ta murnar zuwan ta.

Yara da suka fara shigo da Kaya ne ta Tina da Muhammad a wajen.

Umma tace

“Ba dai tare kuke ba?”

Kai ta gyada tace

“Kinji Fauziyya! Hafsa je ki shigo dashi ai Alhaji ma Yana Nan bai fita ba.”

Nan ta mike Dan fadawa Alhaji zuwan su. A falo ta same shi ya fito zai fita yace

“Alhaji Fauziyya da Mai gidan ne suka zo!”

“To ba dai wani Abu suke so ba ko?”

“Gaishe ka suka zo Yi kawai.”

Komawa yayi ya zauna, yace

“Turo su.”

“Tana fitowa Muhammad na shigowa. Tace

“Kuje ku gaishe da Baban fita zai Yi.”

Gaba Fauziyya tayi Muhammad yabi bayan ta. A kasa ta zauna shima ya zauna a kasa. Tace

“Ina yini Baba?”

“Lafiya ya gida?”

“Alhamdulillah!”

Yaa Muhammad yace

“Ina yini Baba?”

Yace

“Lafiya ya gida Yaa aiki?”

“Alhamdulillah!”

“Ba dai wata matsala ko?”

“Babu.”

“Haka ake so!”

Fauziyya ta mike tayi Waje Muhammad ya saka hannu a aljihu ya Mika Masa bndir din 1k

Baba yace

“Ah har da wahala.”

“Baba ba yawa Daman gobe zamu tafi gida na kawo ta tayi sallama.”

“Toh madallah. Allah saka ana hakuri da ita.”

“Ba komai nagode!”

Ya mike ya shiga dakin Umma akan sallaya ya zuna suka gaisa da Umma Nan ma ya dauki bandir din 500 ya ajiye Mata yace

“Gashi ba yawa. Gobe zamu tafi gida na kawo ta kuyi sallama.”

“To Muhammad angode Allah kra budi.”

“Amin!”

Ya mike yace

“Zan tafi.”

Yana fitowa Baba ya fito ganin an jibge kayan abinci yace

“Wannan ba dai Kai ka kawo ba.”

Kan Muhammad a kasa yace

“Baba ba yawa ayi manage!”

“Ai Mai yawan kenan angode fa Allah saka. Madallah Kai Alhamdulillah!”

Muhammad yace

“Zan tafi so anjima Zan zo mu tafi da ita.”

“To to ba matsala.”

Muhammad ya fita shinkafar ya duba yace

“Ikon Allah Yar gwamnati a marar Nan. Azo aje a canjo a kawo Yar hausa.”

Sakina da ta fito tace

“Akan me Baba Kai da ba da kudin ka aka siya ba ko Kai akace ya kawo wa. To Umma ya kawo wa ai yasan yadda gidan yake shiyasa!”

Kallon ta kawai yayi ya fice Dan da yaran ko kallon sa basa Yi Amman yau har ana maida Masa magana.

Daki tashiga tana fadin

“Kinji Umma Wai Baba aje a canjo shinkafa zuwa Yar hauaa.”

Hafsa tashi muje mu shigo da kayan Nan.”

Suka shigo dashi. Fauziya ta mike tayi dakin su.

Hafsa tabi bayan ta tace

“Anty ya gidan kuwa?”

“Alhamdulillah ya gida Nan jiya nayi mafarki me yake faruwa?”

“Anty abubuwan da yawa bakiga Anty Sakina ta dawo ba.”

“Na gani.”

“Uhmm ita ma da alama dai ta tuba.”

“Masha Allah.”

“Anty farisa ta dawo yau da safe ta koma ma Amman ita sai a hankali.”

“Muyi ta mata addu’a Allah ya shirya.”

“Amin!”

“Mamah har yanzu shiru ko?”

“Wallahi kuwa?”

“Anty fa!”

“Uhmm sai abinda yayi gaba.”

Kai ta girgiza tace

“Yaran fa ba matsala ko?”

“Kai Anty an samu matsala last week bana fada miki Halima ba lafiya ba Anty Ashe ciki me da ita!”

“Ci me?”

“Ciki!”

“Ikon Allah waye Mata cikin!”

“Wani saurayin ta.”

“Yanzu ya ake ciki?”

“Ai sai da ya bare muka sani. Baba ya Bata wani magani ta Sha yasa ta fara bleeding cikin dare muka tafi asibiti wani abokin saurayin shi ya taimaka Mana kwana mu biyu zuwa uku aka sallamo mu Tasha wahala Amman yanzu taji sauki.”

Tagumi Fauziyya ta zuba tace

“Oh mu Kuma tamu kalar kaddarar kenan. Shin laifin mune ko n iyayen mu?”

“Anty ke lafin Mama ne mu kuwa laifin mu ne. Kece kadai Baki shiga abun Nan ta dadin Rai ba Amman mu fa gashi Allah ya Baki miji na gari kina zaune lafiya abun ki nasan da wuya mu samu rayuwa irin Taki domin ke daban ce a cikin mu.”

Ta fashe da kuka.

Fauziyya tace

“Menene na kukan to Ai akwai Allah. Allah Yana gani zai turo kema me share Miki hawaye ina Ahmad?”

“Yana Nan dogon labari ne.”

“Kada ki damu dake zamu tafi ai.”

“Da gaske?”

Kai ta gyada ta rumgume ta tace

“Naji Dadi.”

“Kada ki damu zamuyi magana a tsanake!”

“To!”

“Kince Farisa tazo?”

“Tazo tana ta fada Wai kinyi aure!”

“To uwa ta zan a zaune jiran ta kada nayi aure ko?”

“Nima Wai kada na biye Miki kaza da kaza dai.”

“Ikon Allah Allah ka shiryi Farisa!”

“Amin!”

“Yanzu ki tashi ki hada kayan naki bari naje wajen Ummah naji me take da bukata sai naga Halima daga nan!”

“Toh!”

Ta mike ta fita. A falon Ummah ta zauna tace

“Umma dama da Hafsa zamu tafi can dagin shi.”

‘To Allah ya tsare Fauziyya ya gidan badai matsala ko?”

“Babu Ummah.”

“Masha Allah.”

“Ku nan ba wata matsala.”

“Hmm kema kinsa halin Baban ku dai. Sai dai hakuri amman yanzu kinga kudin da ya ban na juya kuma ga kayan abinci ko?”

“Haka ne. Allah ya ganar da Baba.”

“Amin!”

“Ba labarin Mamah har yanzu ko?”

“Babu wallahi Fauziyya nima na shiga damuwa rashin abokiyar zamana ina addu’a Allah yasa tana lafiya ya dawo da ita lafiya.”

“Amin!”

Sakina ce ta shigo tabi Fauziyya da kallo tace

“Sis wai ya akai Baba ya yadda da auren ki.”

“Hmmm nima ban sani ba kawai fa ce min yayi an dauran aure miji na zai zo ya dauke ni.”

“Ikon Allah. Allah ya kyauta!”

“Amin!”

“Nima Allah ya kawon miji Baba ya yadda.”

“Amin Sakina. Ai auren shine rufin asirin mu.”

“Haka ne.”

Halima ce ta shigo Fauziyya ta bita da kallo,  kallo Halima tayi halima tai  kasa kai tace

“Ina yini Anty Fauziyya?”

“Lafiya lou ya kike?”

“Alhamdulillah!”

“Kije dakin Mamah gani nan ina son ganin ki.”

Gaban Halima ne ya fadi ta amsa da

“Toh!”

Ta mike ta fita. Ta kalli Ummah tace

“Ummah dan Allah kina sa ido akan yaran nan!”

“Me kika gani Fauziyya?”

“Ba komai Ummah amman kinsan hakkin tarbiyar mu na hannun ku a baya kunyi wasa da damar ku wadan ya jefa da yawa a cikin mu a halaka alhamdulillah Allah ya dubi zuciyoyin mu ya shirya mu ya kamata ace na kasa damu sun samu nutsuwa da tarbiya kar subi tafarkin da muka bi.”

“Haka ne Fauziyya insha Allah za a kiyaye Allah yayi albarka.”

“Amin!”

Ta mike tace

“Bari naje wajen Haliman!”

Ta fita.

Karfe bakwai ya tashi yai wanka ya shirya cikin milk wando da cofee kalar riga ya feshe jikin sa da turare cofe kalar takalmi ya saka ya futo ya kulle dakin sa.+

Resturant ya wuce kai tsaye abinci yasa akai masa order dankali ne da kwai sai juice. Kafin yaci ya tashi ya fita. Motar sa ya shiga ya tafi unguwar su Sakina. Layi layi ya dinga bi yana tambaya wanda ba karamim wahala yasha ba duk da a mota yake kan rana ya gaji a wani masallaci yai sallah azahar yai la’asar sannan ya daura daga inda yake. A unguwar yai magariba sai da yaga dare yayi ya hakura ya koma inda ya fitowa.

Washe gari ma tin safe yake bulayi a unguwar amma sam ya kasa samun gidan har yamma. Yunwa da yaji yana ji yasa ya nufi wani resturant acan akai masa order aka kawo masa amman sam ya kasa cin wani abun kirki. Tashi yayi ya shiga masallaci yai sallah ya zauna yana addu’a tare da fadin

“Ya Allah ina roka ka in Sakina alheri ce a rayuwa tavAllah ka bayyana min ita in kuma.l ba alheri bace Allah ka ciren ita azuciyata.”

Yana gama addu’ar ya rufe fuskar sa da hannu yana jin hawaye na zuba a idon sa. Hakika yau ya shiga tsaka mai wuya bai san damuwa ko rashi a rayuwar sa ba sai yau lallai yanzu ya gane rayuwa da abinda ke cikin ta.

In kaga Khaleel duk ya damu ga rashin lafiya da take damun sa na yadda ya saka damuwa a ransa. Wanda ya sa duk ya kara ramewa sam yaki fadawa Dad din sa komai.

Muhammad da ya idar da sallah ya mike zai fita ya hange shi yana kuka da sauri ya karasa yana fadin

“Bawan Allah lafiya?”

Kai ya hau girgizawa yana fadin

“Ka taimaka ka nemon ita wallahi ita ce rayuwa ta.”

“Ya isa daina kukan ka nutsu wa kake nema?”

Hawayen sa ya goge ya fara bashi labari briefly. Kai ya gyada yace

“Ya sunan ta Sakina!”

“Sakina wa?”

“Wallahi ban sani ba!”

“Baka da number ta.”

“Gata amman bata shiga.”

“Ikon Allah kuma number dai dai ce?”

Kai ya gyada amsa yayi yai trying amman a kashe. Yace

“Kuma nan unguwar tace maka?”

Kai ya gyada. Yace

“Yanzu ina da ina ka tambaya?”

“kasan unguwar babba ce na tambayi a layi yafi goma ba respond.”

“Ai gaskiya matsalar da kace sunan yarinyar kawai ka sani dama sunanvmahaifin tane da yafi sauki afi ganewa.”

“Haka ne.”

“Yanzu tashi na taya ka mu gani ko can kasan layi za a dace.”

Tare suka fita ya dinga rakashi suna zagawa.

*

Zaune ta same ta ita da Hafsa dake hada kayan ta,  zama tayi a gefen gado ta kalli Halima tace

“Hafsa ta fada min duk abinda ya faru ba dan komai ba sai dan nice babbar ku kuma tasan ina kawo mata mafita a matsalar ta dan kinsan ko Ummah da Sakina bata fadawa ba Halima me ya ja hankalin ki. Nasan dai Hafsa ta miki fada amman kiji tsoron Allah in ada kinyi a rashin sani to yanzu kikai ke da Allah ki wallahi wuta xaki shiga dan zina babbar masifa ce kuma kika yi sai Allah ya kamaki kuma ki jawa jinin ki tabo. Allah ya yafe mana baki daya.”

STORY CONTINUES BELOW

“Amin!”

Duk suka amsa tace

“Yanzu ya kukai da shi yaron?”

Kuka ta saki tace

“Sam ya daina kira na in na kira baya picking yanzu ma yayi blocking dina Anty Yaya zanyi ina son Isma’il!”

Murmushi Fauziyya tayi tace

“Kina zaton akwai sauran sonki a ran yaron.”

Ta girgiza kai tace

“Ai tinda kika bashi abinda yake so ba kuma wani abu da zaki bashi da zai burge shi kawai sorryn ki,  ai kinyi wasa da damar ki tin tini Halima Isama’il ba zai aure ki ba.”

“Wallahi yana so na Anty!”

“Ok shikenan yana sonki ya isa kice masa ya turo.”

“Zan fada masa insha Allahu!”

“To Allah tabbatar da alheri amman ki nutsu kada ki kara gigin aikata abinda kika aikata a baya na baki nan da sati biyu zuwa uku kan dai mu dawo ina son naji me aka tsaya ki fada masa ya turo in ya tashi turowa in Baba bai yadda ba wajen Mubammad zai zo Allah yasa mu dace.”

“Amin!”

“Ki fada min in kuna bukatar abu kada kuna tambayar maza daga abinda yake sawa suke fara lalata rayuwar yan mata kenan.”

“Hmmm Anty wallahi ban taba tambayar sa kwandala ba. Kisan duk rashin mubbamu da kwadayi.”

“Haka ne. Sai kiyi ta addu’a Allah ya yafe miki ya kuma shirya ki.”

“Insha Allahu.”

“Tashi kije!”

“Nagode Anty!”

Ta mike ta fita. Hafsat ta kalla tace

“Ke nifa abin nan ya ban mamaki ita ta kasa gane inda yaron ya dosa.”

“Anty kenan sai ma kin ga abokin sa da yake son ta yaro nutsatse mai hankali da haiba. Wallahi yafi saurayin nata.”

“To Allah zaba mafi alheri ammab ni nasan da wuya yaron na ya auri Halima.”

“Amin. Nima na jimabda gane hakan.”

Wayar Hafsa ce tayi kara ta kai hannu ta dauka tana ganin Ahmad ne ta ajiye. Fauziyya tace

“Ki daukavmana.’

“Anty kyale….”

“Ki dauka kar na bata miki rai.”

Dauka tayi tai sallam ya amsa yana fadin

“Amarya ta.”

“Na’am ina yini?”

“Lafiya lou alhamduliah ya gida?”

“Alhamdulillah!”

“Gani nan zan shigo anjima dan gobe da safe zan tafi.”

“Ayyah nima fita zanyi.”

Wani kallo Fauziyya ta aika mata tace

“Amman yaushe zaka shivo?”

“Nan zuwa magarib!”

Kai Anty Fauziyya ta daga mata tace

“To sai kazo nagode!”

“Aha i love you Baby!”

“Nima!”

“No no no say it out.”

Shiru tayi yace

“Ina jin ki”

“In kazo zan fada maka.”

“Shikenan me zan kawo miki?”

“Ba komai.”

“To sai nazo”

Ya kashe wayar. Fauziyya ta harare ta tace

“Ki zauna kiyi asara yaro yana son ki.”

“Uhmm Anty nifa tsoro nake ji.”

“Ki kwantar da hankalin ki.”

“Shikenan!”

Tace

“Kin gama hadawa.”

“Nagama.”

*

**

***

****

*****

******

*******

********

“Dan ina kallon ki shine zaki tufe jikin ki Ummu mijin kine fa ni.”

Kai tayi kasa dashi,  ya matso yana rumgume ta ya saka kan sa a kaffadar ta yana shinshinar wuyan ta dake fitar da wani kamshi na daban dagowa yayi ya kissing firehead nata sannan yayi mata a kumatun ta, ido ta runtse yai wa idon ta sannan yai wa dogon hancin ta batai aune ba sai jin bakin sa tayi a cikin nata.

Komai tsaya mata yayi dan nunfashin tamavdaukewa yayi na wucin gadi shina Muhammad wani abu yaji yana yawo a jikin sa ga kamshin jikin Ummu dake hargitsa masa tunanin sa ba soft lips dinta ga numfashin ta dake fitar wani kamshin mai dadi wanda yawan shan kanumfari ya saka hakq bakin ta kuwa kamshin strawberry saboda tana amfani da sweet nd cingum na flavour  strawberry.

STORY CONTINUES BELOW

Sai da yayi iya yin sa sannan ya sake ta da kyar ai kuwa jikin ta da ya gama yin sanyi tayi baya da sauri ya kamo ta ta fada jikin sa ya rumgume ta. Ido suka lunshe a tare. Sunfi minti biyu a haka sannan ya dago ta ya saka mata hijab yace

“Muje ko?”

Kan ta a kasa ta gyada masa kawai. Hannun ta ya kama ya dauki jakar ta da wayar ta suka fita. wajen manager suka koma yace a nemo wanda wanda sukaiwa Ummu aiki nan da nan aka kirawosu ya basu kyautar 15-15k sannan ya bawa Manager 20k suka tafi suna ta godiya.

Gidan gaba ya bude mata ta shiga ya rufe zannan ya bude baya ya ajiye handbag dinta mota ya shiga ya tayar ya kamo hannun ta yana fad8n

“Ya shirye shiryen Walima Ummu na?”

“Uhmm Alhamdulillah!”

Ta fada muryar ta na rawa. Ya kalle tabyace

“Are you ok?”

Kai ta gyada ya kai hannun ta dake rike a hannun sa dai dai bakin sa yai kissing ido ta runtse da sauri dan yadda taji ya shige ta har tafin kafar ta taji wani abu ya tsigar jikin ta ta tashi.

Tuki yake a haka har suka karasa gidan Anty Zainab ya parking ya fito kan ta fito ya bude mata ya bude baya ya dauki jakar ta sannan sukai cikin gidan tana gaba yana binta a baya.

A parlour suka samu da Anty Zainab,  Muhammadbya zauna yana fadin

“Mun dawo Anty!”

“Sannunvku an gama kenan!”

“An gama!”

“To maza kizo kici abinci ki kawo wa Muhammad ma.”

“Anty ni na koshi wallahi.”

Yaa Muhammad ya fada. Ummu da kanta ke kasa tace

“Nimana koshi.”

“Me kika ci?”

“Nasha lemo da ake acan fa.”

“Shine abinci tin safe kina can yanzun an kusa magariba. Ke fa haka kike bakya son cin abinci ko?”

“A’ah Anty ai na koshin ne shiyasa.”

“Kanki ai!”

Ta mike ta bar wajen. Ya kalli Ummu yace

“Zo nan!”

Karasowa tayi ta zauna yace

“Meyasa bakya son cin abinci?”

“Ina ci fa na koshi ne yanzu. Ita Anty ta fiso tai ta durawa mutum abinci.”

“So take kiyi kiba.”

“Ni bana so!”

Hancin ta yaja yace

“Fada min me kike so kici.”

“Nifa na koshi!”

“Ok!”

Ya mike yace

“Ana kiran sallah bari naje nai sallah zan dawo.”

Kai ta gyada tace

“To a dawo lafiya.”

ya mike ya fita ta koma ta zauna sai kuma ta mioe ta shiga daki.

Tana shiga ta fada kan gado tana mai lumshe ido tuna abin dazu yasa tsigar jikin ta gaba daya tashi davsauri ta mike ta cire kaya ta daura towel sannan ta shiga tai wanka ta fito daure da alwala doguwar riga ta saka ta tada sallah. Tana idarwa ta shafa mai da hoda sai ta kara kyau. Zama tayi tana kallon zanen lallen hannun ta yadda yayi kyau ya zanu lallai ta yadda da abinda Muhammad ya fada lallen yai nata kyau kuma ya amshi jikin ta. Shafawa tayi ta lumshe ido sai ta tuna lokacin da yayi wa hannun ta kiss da sauri ta bude ido take ta tuno yadda yai kissing nata wanda a time din ji tayi komai ya tsaya mata. Ido ta bude tana mai sakin murmushi fuskar sa take hanga kawai yadda ya kara kyau da haske. Murmushi tayi ta mike tayi sallah isha’i da taji ana yi tana idawa ta mike ta fito falo ta zauna tare da yaran Anty Zainab.

8:00pm wayar ta ta hau kara dubawa tayi taga Muhammad ne,  dauka tayi ta kai kunne ta tare da yin sallama. Amsawa yayi yace

“Sweetheart fito muyi sallama in tafi.”

“To!”

Ta mike ta shiga dakin Anty Zainab ganin ta tayi tana hada kaya ta tsaya dagowa tayi bayan ta amsa sallamar ta tace

“Menene?”

“Yana waje ne wai zai tafi.”

“Ya dawo ne?”

“A’ah yanzu ya kirani wai zai tafi.”

“To kije kice ya shigo yaci abinci.”

“Toh!”

Ta juya ta fita. Yana jikin motar sa a tsaye ta karasa ta tsaya tare da yin sallama. Amsawa yayi ta tsaya tana wasa da hannun ta,  kallon ta yake yana jin don ta kamar zai fasa zuciyar sa ya fito. Ji yayi ina ma ba za ayi walima ba da yanzu yana tare da matar sa. amman ba komai gobe by now ma suna tare insha Allahu.

“Zan tafi Ummu amman ji nake kamar kar na tafi na barki.”

“Anty ma tace ka shigo kaci abinci.”

“Anya Ummu na koshi fa.”

“Haba dai Yaa Muhammad dan Allah ka shigo kaci ko na kai maka can sittingroom?”

Tai maganar kamar zatai kuka. Duk sai ya rkkice yace

“A’ah muje to.”

Tare suka shiga tana gaba yana binta a baya. Suna shiga tayi dining ya zauna ta hau zuba masa abincin sai da ta gama ya kalle ta kalle shi tace

“Bismillah!”

“Ai tare zamuci.”

“Nifa na koshi.”

“Nima haka!”

“Haba dai please!”

“Kinga na koshi kema kin koshi to abinda za ayi kawai kici nima sai naci kowa sai yaci ko?”

Shiru tayi yace

“Tinda ba zakici ba nima haka tashi ki rakani in tafi.”

“A’ah zanci.”

“To fara ci”

Spoon ta dauka zata zuba ya ce

“Me wannan zakici ai.”

Ido ta zaro ya gyada kai yana danne dariyar da dan ba karamin dariya ta bashi ba. Kai ta langwabe………..

Ana magariba ya kira ta cewar yazo. Hijab ta saka ta mike Anty Fauziyya tace
“Zo nan ko yar hoda?”+
“Anty ai dare ne”
Jaka ta mika mata tace
“Maza shafa.”
Sannan ta dauko turare ta bata. Amsa tayi ta shafa tace
“To sai kin dawo.”
“Aha!”
Ta fita yana ganin ta ya shigo soron wayar sa ya dauko ya fara haske ta,  kai tayi kasa dashi tace
“Ina yini?”
“Lafiya lou ya kike ya gidan?”
“Alhamdulillah!”
“Masha Allah!”
Ledar hannun sa ya mika mata yace
“Gashi ba yawa!”.
“Nagode!”
“Good!”
“Gobe zan tafi Baby sai kuma na dawo zanyi kewar ki.”
“Hmm nima haka!”
“Da gaske?”
Kai ta gyada. Yace
“Naji dadi.”
Tai murmushi tace
“Nima yau zanbi Anty na zamu dagin mijin ta.”
“Masha Allah sai yaushe zaku dawo?”
“Nima ban sani ba.”
“Ba matsala mana communication in ta kama nazo nan din ma zaki ganni.”
“Gidan mutanen?”
“To ba wajen matata zan zo ba.”
Tai murmushi.
*
Muhammad da Khaleel yini sukai suna yawo a garin neman gidan su Sakina. Anan kasan layin su Sakina sukai sallah. Sannan suka fito ya fara kallon unguwar yace
“To ni ban sani ba ko wrong address ta bani.”
“Gaskiya dai ina tunani.”
“To nagode!”
“Ba matsala yanzu sai gobe kenan nima zan tafi gida.”
“Oh shigo to na sauke ka mana.”
“Ai ba nisa can layin zani fa zan dauko matata sai mu tafi gida.”
“Oh muje ba sai na sauke ka ba.”
“kar mu bata maka lokaci fa.”
“haba ba komai sai kace zani wani waje yanzu faaki zan koma kawai.”
“Shikrnan nagode.”
Suka shiga ya nuna masa suka isa layin su Sakina. Parking yayi inda yace yayi ya fita ya nufi kofar gidan su sakina.
*
Hafsat na ganin Muhammad ta karasa tana fadin
“Yaa Muhammad sannu da zuwa.”
“Yauwah Hafsat.”
Ya mikawa Ahmad hannu suka gaisa yace
“Kice tazo mu tafo kuma naga kina zance ai.”
“Oh shine mijin Antyn tamu ashe yayan mu ne.”
Suka kara gaisawa. Ahmad yace
“Ai nima tafiya zanyi je ki mata magana.”
Ta juya ta shiga waje suka fito tare. Khaleel dake mota yana tunani Muhammad yace
“Fito ku gaisa mana.”
Kamar kar ya fito ya fito suka gaisa. Hafsat ta dawo tace
“Yace kazo kuyi sallama da Ummah.”
“Toh!”
Ya kalle su yace
“Ina zuwa.”
Sannan ya shiga gidan. Sallama sukai da Ummah tai musu addu’a. Sannan Sakina da Hafsat suka fito har da Halima dan yiwa yayar tasu sallama.
STORY CONTINUES BELOW
Suna fitowa suka gaisa da Ahmad. Khaleel kuma yayi gefe yana answering cal. Fauziyya tace
“Ai basu gama ba muka fito.”
Ahmad yace
“A’ah Anty mun gama daman nima tafiya zanyi.”
“To shikenan.”
Suka gaisa da Sakina. Hafsa tace
“Ita ke bin Anty Fauziyya sunan ta Anty Sakina.”
Dai dai karasowa Khaleel ji sunan yasa gaban sa ya yanke ya fadin. Tace
“Sai Anty Farisa sai ni sai Halima sannan sauran kannen nawa.”
Kai ya jinjina yace
“Masha Allah. Mai jiki anji sauki.”
Halima tai kasa da kai.
Khaleel ya karaso Muhammad yace
“Ga Madam din ku gaisa!”
Dagowar da zai yi sai yaga Sakina a gefen ta ido ya hau mutsekewa. Sakina da hankalin ta ke kan Ahmad dake magana sam bata lura da shi ba.
Basuyi aune ba sai kawai ganin sa sukai a gaban ta itama a tsorace ta matsa tana duban waye
“Sakina!”
Ya fada yana nuna ta da yatsa itama Ta zaro ido tace
“Khaleel kaine?”
Kowa kan sa ne ya kulle Yaa Muhammad ya karaso yace
“Kada kacemin ita ce Sakinan da kake ta nema?”
“Ita cevMuhammad!”
“Ikon Allah to ai kanwar Madam ce.”
“Ikon Allah ashe na hadu da ita da na hadu da kai Allah ne yayi bamu sani ba sai yanzu.”
“Haka ne.”
Sai ya kalli Fauziyya yace
“Ina yini Madam!”
“Lafiya lou dan soyayya.”
Yai dariya yace
“Ai kanwar taki ce.”
Sukai dariya gaba dayan su. Ahmad yace
“To ni zan tafi sai da safe.”
Sukai sallama da kowa ya tafi Hafsat tabi bayan sa. Mota ya shiga sukai sallama ya tafi ta dawo.
Muhammad ya kalli Khaleel yace
‘Mu dai mun yafe rakiyar ka ga Sakina nan sai asha soyayya.”
“A’ah ai nayi niyya muje sai mu dawo da ita na ajiye ta.”
“Wallahi da kai zaman ka ai ba nisa.”
“Ni dai muje.”
Baya suka shiga gaba dayan su har Halima dan Sakina tace tazo suje. Muhammad ya shiga gaba.
Gidan suka isa yai parking suka fito sukai sallama suka shiga. Gaba yasa Sakina ta dawo sannan ya tada motar suka bar wajen kofar gidan su suka dawo Halima ta fita tai musu sallama tai cikin gida.
*
**
***
****
*****
******
*******
Farisa ce zaune da ita sanye da wani mini siket wanda iya kar sa duwuwun ta sai yar half vest kan ta ya sha gashin doki tana ta paintin face nata with makeup.
Momyn su ce ta shigo ta bita da kallo tare da hadiyar yawu ta dan shafi cinyar ta tace
“Tin da kika dawo bamu zauna ba gashi naga kina ta shiri ince fita zakiyi?”
“Wallahi Momy zamu party da Abby ne daga nan kuma zamu wuce Abuja zanyi sati daya.”
“Ah gaskiya ni kuwa ina bukatar information ba zan iya zama har kije kiyi sati daya ba.”
“To Momy me kike son kiji?”
“Abinda na aika ki gida ki jiyo min.”
“Momy akwai tashin hankali fa domin wallahi Anty Fauziyya duk ta canja tunani Sakina da Hafsa. Dan Hafsa ma aure ita ma take son yi?”
“What? Ita kuma sakinan fa?”
“Ita dai ta dawo gida ne kawai amman naji tana min wani wa’azi alamar tana son ta koma kan hanya.”
“Ai kuwa sunyi kadan suyi min haka ace duk su ukun ina laifin daya. Ke kinsan asarar da zanyi kuwa yan gidan ku su suka kara fito dani dan ban taba samun yan mata kamar ku ba yara ga kyau ga baiwa lallai kuwa dole su dawo hanya ita Fauziyyan fa?”
“Da gaske tayi aure sai dai ba wanda yasan gidan ta yanzu kisa a saka ido kawai a gano inda take duk abinda za ai shikenan.”
“Wa ta aura?”
“Kai ba wani mai kudi bane gaskiya.”
“Shit! Shi din ma zamu san yadda zamuyi dasu.”
STORY CONTINUES BELOW
“Yauwah ayi duk uydda za ayi amman kada a taba lafiyar su.”
Wani kallo ta aikawa da Farisa tace
“In aka taba fa?”
“Aah fa Momy yan  uwa nane wallahi ba zan taba tsayawa na gani za a cuce su ba dan sai inda karfi na ya kare.”
Tana kaiwa nan ta mike ta suri jaka ta fice. Momy ta bita da kallon mamaki da tsoro can ta mike ta fita dakin ta ta koma tana safa da marwa na tunanin abun yi.
Can ta dauki waya ta fara kira layin Hajiyar. Tana dauka tace
“Ya dai Hajajju manyan mata!”
“Uhmm ina sakina?”
“Ta tafi gida yau wajen sati daya.”
“Saboda me?”
“Kawai nace taje gida itama kuma tana so taje ta tafi.”
“aka me kikace taje gida?”
“Hmm ‘da na Khaleel ke son ta kinga kuwa tayaya zan tsaya haka ya faru shiyasa na kada ta gida.”
“Ikon Allah kenan ta yadda dashi shiyasa ta fara nutsuwa take son ajiye *wannan rayuwar* “
” kamar ya?”
“Yanzu yar uwar take fada min wai taji tana mata wa’azi da alama ta daina wannan harkar.”
“Haba dai ni bamuyi waya ba dan gaskiya ba zan iya tsayawa dana ya aure ta ba.”
“Daman kada ki so ma.”
“Shikenan nagode sai anjima zan bincika miki naji ya aza ayi.”
“Ok ina jiran ki.”
Ta kashe wayar tana kara neman wani layi. Ana dauka tace
“Uska!”
“Babbar Hajiya!”
“Zan turo maka hoton wata da address din gidan su amman tayi aure ina son a samon information akan ta nan da sati daya.”
“Angama Hajiya ina jiran ki.”
“Ok!”
Ta kashe ta tura masa picture da address din sannan ta mike ta dauki jaka da mayafi ta fice. Mota ta shiga ta figa ta nufi wani kauye can wajen bokan ta.
Tana zuwa ta tada layi amman da yake ita special ce aka kai ta ta zauna ya tashi ya tafi wajen ta. Yana zuwa tace
“Akwai matsala fa!”
“Matsalar me?”
“Komai ya fara lalace min!”
Wata dariya yayi mai rikitar wa yace
“Bana fada miki ba daman in har baki biya bukata ga yaran nan su hudu ba wallahi kin ta ganin matsala kenan kuma dole sai su dukka dan haka in kina son komai ya fara zama dai dai kije ki san yadda zakiyi ki samu biyan bukata ga yaran nan arzikin ki na a jiki su kada ki soma bari su kubuce miki.”
“Amman fa daya tayi aure suma biyun aure suke son yi!”
Wata dariya ya kuma yace
“Menene aure dan anyi aure shine me ai da auren ma  ana yin harkar!”
“Haka ne amman ita mai taurin kai ban mavsan inda take ba ko zaka duba min.”
Wani plate ya dauko mai kasa a ciki ya fara zane da jan kulunbo ta ihu ya daji yace
“A’ah ya haka?”
Ya kara barbaza kasar ya kara abun amman nan ma ya kasa ganin abinda yake son gani dagowa yayi yace
“Akwai matsala akan yarinyar nan amman ki bani nan dq kwana uku ki dawo zan fada miki kome ake ciki.”
“Shikenan sauran ukun fa kasan abunyi ka karkaton da hankalin su.”
“Baki da matsala kije kawai.”
“Nagode!”
“Bana bukata dan ba kyauta zan miki ba.”
Ta dire masa kudi mai yawa sannan ta mike ta fita tana murna aranta. Gida ra nufa wani super market ta gani ta tsaya tai patking ta shiga.
Tana shiga ta fara daukar abu ta juya kawai sai ta hango Rabi’a tana dibar abu ka kara kyau ta yi haske ga ciki a jikin ta har ya fito sosai. Mijin ta na tura basket din da take zuba kaya.
Da sauri ta karasa wajen su tana kiran sunan ta juyowa tayi ta tsaya kallon ta sai ta kalli Mustapha tace
“Jeka a lissafa bari mu gaisa.”
Kallon Momy yayi yace
“Sannu ina yini?”
“Lafiya lou ya kake?”
“Alhamdulullah!”
Ya fada yai gaba. Rabi’a ta kalle ta. Momy tace
“Kina gari daman?”
Kai ta girgiza tace
“A’ah nazo ne dan edd na yayi shiyasa muka dawo na haihu sai mu koma!”
“Yanzu da gaske kin bar harkar nan!”
Wani kallo tai mata tace
“Ban gane ba da a ciki aka haifen ni fa na tsaya dake ne albarkanci musulunci da kuma da na ki kula ki miji na yane mi jin wacece duk da na fada masa komai dakomai kuma ya yafe min dan haka ki bace min a gani kin ganni cikin rufin asiri kina wani yanzu na bar harkar nan aah me zanyi a ciki me ta tsinana min in banda kunci a cikin ta ke da kike ciki me ta tsinana miki. Ki maza ki tuba ki koma ga Allah tin kan lokaci ya kure miki amman in kinki zaki ga babban tashin hankali a rayuwar ki. Ni sai anjima.”
Ta juya tabi bayan sa. Tana zuwa taga an gama ya kama hannun ta suka fita.omy kuwa kallon su ta tsaya yi kawai. Tin fara barin Fauziyya a bariki komai ya kwace mata kuma alkadarin abun ya karye mutane ta da take jin dadi dasu take samun kudi duk suka bar tarwatse wasu sunyi aure wasu sun canja uwar daki. Siyayyar da batai ba kenan ta fita cikin bacin rai na in ta kama Fauziyya sai ta gama ilatatata ba zata bar ta ba sai ta zam tamkar matar ta sai tayi nadama data sanin barin ta da tayi.Dagowa yayi yana kallon ta yace
“Sakina na sha wahalar neman ki yau kwana na biyar a garin nan kullum sai na zagaye unguwar nan ina cewa gidan su Sakina amman ban dace ba.”+
“Ina ka hadu da Yaa Muhammad?”
“A masallaci ina kukan rashin ki.”
“Kuka kuma?”
“Wallahi kuka Sakina na rasa yaya zanyi to.”
“Haba sai kace ba namiji ba.”
“Namiji baya kuka kenan!”
“A’ah amman an san shi da juriyya ne.”
“Tawa ta kare akan ki ni kadai nasan me nake ji. Amman alhamdulillah.”
“Ya akai kazo nan to.”
“Wallahi gida zan kaishi da matar sa shine Ashe Allah yau zan ganki.”
“Ikon allah.”
“Sakina meyasa kika kashe wayar ki kin tadan hankali na rasa nutsuwa da farin ciki kin zama rayuwata ban sani ba.”
“Hmm sim din na karya shiyasa na manta ban dauki number ka ba.”
“Saboda baki damu dani ba ko?”
“Ba haka bane.”
“To yaya ne?”
“Kawia na manta ne.”
“To ya kike ya bayan rabuwa?”
“Sai godiya.”
“Masha Aah!”
Agogo ya kalla yaga tara tayi yace
“Dare Yayi My love zan koma masauki na gobe zan zo sai mu tattauna.”
“Allah ya kaimu nagode.”
“Amin i love you!”
Murmushi kawai tayi ya juya ya tafi. Ji yake kamar kar ya tafi amman dare yayi ga gajiyar da yayi.
*
**
***
****
*****
Yana komawa masaukin sa ya shiga yai wanka ya ci abinci sannan ya kwanta yana mai farin ciki baccin da ya jima baina shi yayi.
*
Karfe shida ya bar gida dan yana son ya zarce office. Ai kuwa karfe tara a office tai masa nan ya hau kan aiki da ya tarar masa ba laifi bai samu kan sa ba sai karfe daya da rabi yaje yai sallah ya dawo.
Waya ya dauka ya fara kiran Hannah wanda tin da ya tafi bata kira sa ba sai shi da duk safiya zai kira yaji ya take kuma da dare kan yai bacci zai kira yai mata sai da safe.
Dauka tayi yace
“Ya kike?”
“Lafiya and you?”
“Alhamdulillah!”
“Masha Allah.”
“Nace miki yau zan dawo ko?”
“Eh Allah kawo ka lafiya!”
“Amin. Me kika tanadar min?”
“Ba komai!”
“Haba dai ki shirya tarbar angon ki.”
“Uhmm sai ka dawo!”
Ta kashe wayar ta.
Yai murmushi ya fara neman layin Hafsat. Suna mota suna tafiya kiran ya shigo dauka tayi tace
“Ina yini?”
“Lafiya Alhamdulillah ya hanya?”
“Ai na jima da sauka.”
“Masha Allah kace hutawa kake!”
“Wane hutu aiki dai baki san ko gida ban je.”
“Ah haba dai sannu!”
“Yauwah. Ya hanya?”
STORY CONTINUES BELOW
“Alhamdulillah to Allah sauke ku lafiya!”
“Amin”
“Zan kira ki zuwa anjima.”
“Allah kaimu!”
Ya kashe ya koma kan aiki. Karfe hudu saura ya tashi yaje sukai sallah sannan ya siyo youghurt dan yunwa yake ji. Shi ya sha sai karfe shida ya baro office. Kan ya karasa gida har an kira magariba.
A masallaci ya tsaya yai sallah sannan ya fito ya karasa gida a gajiye. A falo ya same ta tana aikin nata wato kallo ga dukkan alamu ko sallah batai ba.
Mai aikin ta ce jin an bude kofa ta fito tana ganin sa ta durkusa tana fadin
“Sannu da zuwa!”
Zata amshi jakar sa ya daga mata hannu kawai yai ciki akan kujera ya zauna yana fadin
“Yaa Allah!”
Juyowa tayi taga yana mata wani kallo kasa kasa. Dan murmushi ta saki tace
“Sannu da zuwa!”
“Yauwah ya gidan?”
“Lafiya!”
“Please taimaka ki hada min ruwan wanka!”
“Toh!”
Ta mike ya bita da kallo yadda tayi kyau sanye take cikin dogon wando sai riga karama kayan sun mata kyau kan ta ya sha gyara. Mikewa yayi yabi hayan ta. Bata dakin tana bandaki ya tsaya kallon yadda aka gyara dakin yaji dadi duk da yasan da kyar in ita ta gyara din.
Kaya ya fara cirewa ta fito tace
“Na hada!”
Kofa ta nufa yace
“Ba za ko taya ni ba.”
“A’ah ban jima da yi ba.”
“To zo kiji!”
Ya fada yana kamo hannun ta. Yana janyo ta ta fada jikin sa. Rumgume ta yayi yana fadin
“Nayi missing matata fa.”
Itama da tayi missing nasa sai tai lafe a jikin sa. Dan haka ya samu damar aika mata da sakon sa. Sosai ta bashi gudunmawa har ya samu ya biya bukatar sa bai taba jin dadin da yaji a ranar ba dan duk wanda suke bata bashi hadin kai. Daukar ta yayi suka shiga sukai wanka suka fito ta nufi dakin ta dan saka kaya shima ya saka kayan bacci. Yai sallaj.
Yana zaune ta shigo tace
“Yaya abincin fa?”
“Kawon nan!”
Juyawa tayi sai gata nan dauke da basket ta dire shi. Ta dauki plate ya fara zuba masa fried rice din dai caslow da pepper chicken sannan ta mika masa. Saukowa yayi ya zauna ya fara ci ba laifi abinci yai dadi amman ba kamar yadda yake so ba.
Sai da ya gama ya shiga ya wanke bakin sa kan ya dawo bata dakin ta dauke basket din wayarsa ya janyo ya fara kiran layin Hafsat.
*
**
***
****
*****
******
Tin karfe goma suka bar gida ba su suka isa ba sai karfe biyar na yamma gaba daya sun gama gajiya sai sannu yakewa Fauziyya ji yake dama a jirgi suka zo ko dan ya rage mata wahalar tafiya. Direct gidan su aka wuce dasu.
Suna zuwa kofar gidan Daga Fauziyya Har Hafsa da kallo suka bi gidan dan kana ganin gidan kasan gidan sarauta ne. Mai gadi ne ya leko dan ganin waye yana ganin Muhammad ya ja baya yana fadin
“Barka da isowa ranka ya dade!”
Nan ya bude kofa suka shige kan su karasa parking space har labari yaje wajen Ummi cewa su Muhammad sun zo. Fauziyya da Hafsa a tsorace suke. Yadda suka ga manyan bafade sun zo sun zage mota. Hannun ta Muhammad ya kama yana fadin
“Menene?”
Kasa magana tayi. Ya sakar mata murmushi yace
“Kin gaji ko?”
Kai kawai ta gyada ya kalli Hafsa yace
“Sannu kanwata!”
“Yauwah Yaya!”
Taga ya kalla ya bada umarni nan da nan daya daga ciki ya bude masa kofa yana fita suka hau kirari suna fadin
“Takawar ka lafiya dan sarki jikan sarki,  ta kawar ka lafiya yarima mai jiran gado,  gaba salamin baya salamu lafiya dan babbar gida. Lafiya Yarima mai adalci. Barka da dawowa Yarima!”
Hannu kawai ya daga musu ya juya ya mika mata hannu ta dauro hannun ta akan nasa ta fito ita tsoro ma suka bata dan haka ta buya a jikin sa. Yace
“Menene?”
Kasa magana tayi sai kamkame sa da tayi. Kafa ya daga nan da nan suka basu hanya ya fara tafiya Fauziyya na makale dashi Hafsa na biye da su a baya tana bin su cike da mamaki.
A haka suka karasa harabar Inda Ummi ke tsaye ita da kuyangun ta. Yana ganin ta ya karasa da sauri ya fada jikin ta yana fadin
“Ummi na!”
“Barka da zuwa Mai babban suna!”
Kai yai kasa dashi yace
“Da fatan na same ku lafiya.”
“Alhamdulullah!”
Janye shi tayi ta karasa wajen Fauziyya da tayi kasa da kai tace
“Haba ka wani makale ni ga ‘ya taban mata sannu da zuwa ba.”
Ta rumgume ta. Zamewa Fauziyya zatayi ta kamo tace
“A’ah mu shiga daga ciki.”
Ta juya ta kamo hannun Hafsa tace
“Sannun ku da zuwa kun kwaso gajiya duk ya debo muku gajiya da ku taho a jirgi muje daga ciki!”
Taja su. Bayan su yabi yana fadin
“Ni kuma fa Ummi!”
“Kasan inda dare yai maka.”
“Shekara nawa rabon mu wato kin daina missing dina ko?”
“Ai ka ga mai min komai da ka kawon  sirika dan haka na yaye ka kan na samu jikoki in kara yaye ka.”
Yai dariya kawai yabi bayan ta. Daki guda kato wanda babu abinda babu a ciki ta kai su tace
“Ku huta kuyi wanka kuyi sallah kuci abinci sai mu gaisa.”
“Mungode”
Cewar Hafsa. Ta juya ta kalli Muhammad tace
“Shige muje ka barsu su huta suma”
“Ummi anan zan…”
Bai karasa ba taja hannun sa suka fice.
Ajiyar zuciya Fauziyya ta sauke ta daga kai tana bin dakin da kallo sai ta kalli Hafsa. Hafsa ma ita take kalla. Fauziyya tace
“Kai na ya kulle Hafsa!”
“Kema kenan bare ni. Na zata kinsa wani abu ma.”
Kai ta girgiza tace
“Ina fa.”
“To Allah ya kyau amman abun da mamaki.”
“Sosai ma.”
Ta mike tace
“Bari nayi wankan dan na gaji wlahi”
Ta shige bandaki dan yin wanka.
Wanka tayi ta dauro alwala. Tana fitowa taga an jere musu kayan abinci sai kace wanda za ayi walima a wajen dan yawan kulolin da aka jere. Hafsa ce ta shiga tayi wanka tana fito taga anyi sallah Har Fauziyya ta tayar da sallah.
Kaya ta saka itama ta tada Sallah tana idar wa tayi addu’a Fauziyya ta kassa da ta zuba tagumi tace
“Anty dan Allah kada kisa damuwa fa ki saki ranki!”
“To Hafsa.”
Tayi murmushi tace
“Taho muci abinci.”
“Zuba min!”
Zubo mata tayi ta miko mata. Amsa tayi ta dan ci kadan ta tashi ta koma ta kwanta. Hafsat kuwa ci tayi ta koshi kamar ba gobe.
*
Suna fita Ummi tace
“Dan Allah ka barsu su huta kai ma kaje kai wanka ka ci abinci ko?”
“Ina Abbi na.”
“Yana fada!”
“Ai kuwa sai na fara zuwa.”
Ya fita. Fada ya nufa wacce mai martaba ke zama da yamma. Yqna shiga aka fara kawo gaisuwa. Fuskar mai martaba kuwa cike take da farin ciki yake fadin
“Lalle marhabu Yarima barka da dawowa ina sirikar tawa.”
Kan Muhammad akasa ya karasa ya rumgume mahaifin nasa sannan ya zube ya kawo gaisuwa mai martaba yace
“ina sirika ta?”
“Abbi tana cikin gida!”
“Masha Allah kun iso lafiya?”
“Alhamdulillah!”
“Allah taimaka!”
“Amin!”
Mikewa yayi yace
“Abbi zanje na kintsa.”
“Afito lafiya.”
Ya juya ya fita. Sashen sa dake gefen na mahaifiyar sa ya shiga. Sashen na nan yadda yake sai kara kawata shi da akai da kayan more rayuwa yai kyau da tsari.
Ciki ya shiga yana mai sakin ajiyar zuciya finally ya dawo gida ya samo mahadin rayuwar sa yanzu rayuwar sa zatai dadi da inganci.
Wanka ya shiga yayi ya fito ya canja kaya su wani yadi mai kyau wanda akai wa dinki irin na sarauta sai ya fito a Yariman sa. Yayi kyau ya dada kwarjini. Da kyar ya iya shan fura ya fita saboda ana kira sallah magariba.
A masallaci sukai sallah basu baro masallacin ba sai da akai ishai bangaren mai martaba suka wuce tare suka ci abinci duk da duk hankalin sa na kan Fauziyya ko taci abinci ko ya take shine kawai tunanina.
Karfe tara taji an bude dakin da sauri ta daga kan ta tana ganin Muhammad ta mike da sauri ya karaso a hankali ya kama hannun ta yace
“Sannu ya gajiya?”+
“Alhamdulillah. Ina ka kawo mu nan Muhammad?”
“Gidan mu ne?”
“Gidan ku!”
Kai ya gyada yace
“Muje Abbi na son ya ga sirikar sa tin da na shiga fada yake fadin in kawo masa sirikar sa.”
Ya kalli Hafsat yace
“Taso kanwata!”
Mikewa tayi tabi bayan sa. Wani bangare na daban suka shiga wanda kyaun sa da haduwar ta suke daban. Suna shiga Ummi ta mike tana fadin
“Sannu da Zuwa!”
Ta kamo hannun ta. Fauziyya ta zame ta fara gaishe ta cikin girmamawa. Ta dago ta tana fadin
“Ya gajiyar hanua?”
“Alhamdulillah!”
Ta kamo ta ta zaunar a gaban Mai martaba kusa da muhammad. Gaishe dashi tayi ya amsa cikin farin ciki da tambayar ta ya hanya nan mata amsa masa. Hafsa ta gasihe ya amsa yana saka musu albarla.
Shiru yai yana kallon su can ya kalli Ummi yace
“Alhamdulilah yau ga Yarima da mata Fulani Yarima na ya girma ko a yau na mutu Yarima zai amshi mulki Alhamdulillah.”
“Lallai kam Allah shine abin godiya. Allah ya karawa Annabi daraja Allah kuma ya bashi ikon riko da dabiun ka ya bashi ikon yin adalci.”
“Amin Fulani. Baki na ya gaza yin godiya na rasa tayya zan nuna farin ciki na. Agobe akwai liyafa ta dawowar Yarima da mai dakin sa. Dan haka jibi akwai taro kamar yadda kika ce gata zakiyi yini bikin da ba ai ba.”
“Haka ne Ranka ya dade Allah ya saka da alheri.”
“Amin! Allah muku albarka gaba daya. Ina alfahari dake Fulani kin haifa min farin ciki abin alfahari na yaro daya tamkar da dubu Allah ya baku zaman lafiya da zuri’a mai albarka.”
“Amin Amin!”
Nan ya dinga musu addu’a da nasiha. Duk sai jikin su yai sanyi har Hafsa dake gefe ita ma.
Sai wajen goma da rabi suka baro bangaren Mai martaba dakin da aka kai su direct suka nufa. Bedroom suka shiga Fauziyya da Muhammad.
*
Hafsat kuwa ta zauna anan falo tana kallo can taji wayar ta na kara. Dauka tayi taga Ahamd ne murmushi tayi ta dauka ta kai kunnen ta tana fadin
“Asaalamu alaikum”
“Wa’alaikum salam!”
“Ya kake ya dare ya gajiya?”
“Duk Alhamdulillah. Gajiya taji muryar ki ta gudu.”
“Kai Deedat!”
“Da gaske!”
“Na zata kayi bacci ai!”
“Tayaya zanyi bacci banji muryar ki ba.”
Tai murmushi tace
” hmm kaji ai kaje kai bacci dan kasamu gajiyar ta tafi kaga gobe da aiki.”
“Korata kike?”
“Ni na isa?”
“Gashi nan kuwa.!”
“Aah tuba nake.”
Yai murmushi yace
“To shikenan zan tafi amman ya garin naku ya gajiya?”
“Alhamdulillah.”
STORY CONTINUES BELOW
“To kema kije ki kwanta ki huta kinji.”
” insha Allahu.”
“Gud nyt!”
“Nyt!”
Ta kashe wayar tana lumshe ido.
*
A bakin gado ya zaunar da ita ya durkusa a gaban ta yana fadin
“Ko mu tafi sashe na?”
Kai ta girgiza. Ya kama hannun ta yace
“Nasan kina cike da mamaki zulumi da tsoro amman ki min afuwa ki bafi har gata ranar da zaki tare zakiji komai da kike son ki.”
Kai ta gyada yace
“To ki saki ranki. Kinsan ina son ki bazan kawo ki inda za a cutar dake ba ko?”
Kai ta gyada yace
“Smile mana.”
Tai murmushi ya shafi fuskar ta sai kuma ya mike ya mikar da ita. Kissing nata yayi iya yin sa sannan ya sake ta ya nufi gado da ita yace
“Ki kwanta kinji Baby na. Sai da safe.”
“Allah bamu alheri.”
“Amin!”
Ya juya ya fita. A falo ya samu Hafsa yace
“Kanwata mun barki anan ko?”
“A’ah Yaya nima waya na gama.”
“To ga amanar amaryata nan!”
“Tai murmushi tace
” ai ta tashi daga amarya!”
“Aah wa ya fada miki ai kuwa ni amarya ce a waje na.”
Yai murmushi tace
“To shikenan.”
“Sai da safe!”
“Allah tashe mu lafiya.”
“Amin!”
Ya juya ya fita. Zata mike taji an bude kofa. Ummi ce ta shigo tace
“Ba abinda kuke bukata?”
“Babu Ummi.”
“To sai da safe!”
“Allahh tashe mu lafiya.”
Tana fita ta aiko wata kuyanga ta kawo musu kayan bacci. Katuwar leda aka kawo wanda kayan baccin sun kai kala goma. Amsa tayi tai godiya sannan tayi cikin daki dasu ta nunawa Fauziyya amman sai ta same ta  har tayi bacci. Itama kwamciyya kawai tayi take baccin gajiya ya dauke ta.
*
**
***
****
*****
******
*******
Tayi kiran tayi kiran amman bai shiga ba dan ya riga yai blocking nata. Number Kabir ta amsa wajen Hajata ta kirasa. Yana ganin number ta gaban sa ya fadi dauka yayi Sallama ta amsa sai tace
“Ina yini?”
“Lafiya lou Halima ya jikin?”
“Naji dauki Alhamsulillah!”
” masha Allah!”
Sai tayi shiru. Yai shiru shima can yace
“Ko jikin ne?*
” a’ah daman Isma’il ne in na kira bata shiga nace dan Allah ina son ganin ka.”
“Ok ba matsala zan shigo anjima.”
“Nagode!”
Sukai sallama. To shi tayaya zai sa ta fita harkar Isma’il ne. Tunani ya fara wayar sa ta dau kara yana dubawa yaga Sadiya ce.
Dauka yayi da sallama ta amsa suka gaisa tae
“Shine jiya baka zo ba!”
“Tuba nake ranki ya dade aiki ne yai min yawa.”
“Shikenan yau zaka zo!”
“Insha Allahu.”
“To gida zaka zo.”
“Gida kuma?”
“Eh yau bana son fita ne na fison kazo ka samen a gida ka ragen zaman kadaici.”
“Hmm Sadiya Rigima shikenan ki turon address zan shigo insha Allahu.”
“Allah ya yadda me kake so na girka maka?”
“Haba dai ni nagode ai yamma ce ba wani abu da nake bukata.”
“Allah ni ka fada ko nai kuka.”
Tai murmushi yace
“Kome kika ban ina so.”
” wayo ko?”
“A’ah ba wayo bane kawai dai!”
“Uhmm naji shikenan sai da kazo.”
” nagode!”
Ya kashe wayar yana dafe kan sa kan sa ya dauki caji dan Sadiya na rikita masa tunani. Ga Halima ko me zata ce masa.
Haka ya ture aikin ya koma ya zauna yana tunanin me zai faru in yaje wajen Halima.
STORY CONTINUES BELOW
Karfe uku ya mike ya tafi dan zuciyar sa ta kasa nutsuwa ya bari sai yamma yana zuwa ya kira ta ta fito. Mota ta shiga ya kalle ta tace
“Ina yini?”
“Lafiya ya kika?”
“Alhamdulillah!”
Sai tayi shiru. Yace
“Uhmm ina jin ki!”
“Akan Isma’il ne!”
“Me ya faru?”
Ya fada gaban sa na faduwa dan kar yaje ya fada masa halin da ake ciki. Tace
“Baya daukar wayata.”
“Nima bai fiya dauka ba.”
“Nifa yanzu in na kira bata shiga gashi Anty Fauziyya tazo jiya tace in har da gaske yake ya turo yaya zanyi to na same shi har nai masa wannan albishir din?”
Shiru yayi tace
“Ko ka bani wayar ka na kira ta nan na fada masa in ma laifi nayi nasan jin wannan labarin zai sanyaya masa zuciyar sa.”
“Halima kinsan menene ba wai baki ne ba zan ba amman!”
“Amman me? In har ba bani ne ba zakai ba kawai ka kira min ashi yanzu na fada masa nasan Isma’il zaiji dadi da wannan albishir din.”
Shikenan!”
Ya duaki wayar ya fara neman layin Isma’il yana dauka yace
“Please ka tsaya ka saurare ta.”
Bai tsaya yaji mai zai ce ba ya mika mata wayar kawai.
“Hello My love!”
Ta fada zuciyar Kabir ce ta buga da karfi. Ta can gefen yace
“Menene ki fadi abinda zaki fada saboda ina da abun yi malama.”
“Bansan me nai maka ba dan Allah kayi hakuri kuma kasan me? Albishin ka?”
“Ina ji!”
“Ance ka turo a gidan mu.”
Wani tsaki ya ja yace
“In turo inyi me?”
“Auren mu mana Love!”
“Amman ke wacce dabba ce ban sani ba Halima daman ke kina tunanin da aure a tsakanin mu ne. To Halima yanzu in na aure ki me zaki kai min gida na bayan abinda zaki kai min duk na gama kwasar sa. Haba Halima dan Allah ki cire wannan tunanin a ranki ni daman can ba so ki nake ba abinda ya kawo ni kenan kuma na samu mai zan tsaya kuma. Da Allahbina rokar ki da Allah ki daina damuna da kira kuma kada ki kara sakawa wani ya kirani.”
Ta shiga shock amman sai ta danne tace
“Hmm Baby wai tsokana ta kake yi ne. Naji ka ajiye tsokanar yanzu yaushe zaka zo dan na fada mata ta fada.”
“Ni sa’an ki ne dazan tsokane ki. Ki shiga hankalin ki. Nonsense!”
Ya kashe wayar. A kidimebta dago tana dafe kirjin ta. Sai kuma ta fashe da wani iri  kuka mai taba zuciya kuka take har numfashin ta na yin sama sama.
Kabir kuwa ji yake kamar tana zuba masa ruwan zafi. Ido ya runtse ganin abun na yawa ya dago yana lallashin ta amman kamar dada mata karfi yake da sauri ya fita a motar ya jingina a kofar gida yana hango ta ta cikin mota tausayin ta duk ya cika masa zuciya.
Ganin bata da alamar dainawa yasa ya koma motar dago ta yayi ya rumgume ta yana fadin
“Menene amfanin kukan naki Halima nasan me Isma’il ya fada miki dan me zaki damu da wanda baya son ki dan me zaki zubar da hawaye akan wanda bai damu ba abun da yake bukata kenan.”
Kai ta hau girgiza masa tana fadin
” ya zanyi ya zanyi? Sai da suka fada min ba son gaskiya yake min amman karya ta su sun ban dama amman ya watsan kasa a ido ka fada min Kabir ya xanyi Isma’il ya batan rayuwa ta waye zai auren shikenan na bata rayuwa ta yanzu za ana kirana da karuwa Allah ka kawo min mutuwa ko naji sanyi yanzu ni Isma’il yake fadawa baya so na.”
Ta kalli Kabir tana kuka tace
“Kai ma kasan baya so na ka boye min ka fada min kasani ko?”
Sai kuma ta ce
“Inna lillahi wainna illahir rajiun.”
Ta dafe kan ta kukan kuma ya dauke dif.
Hankalin Kabir ya tsashi ya dago ta yaga ta daina kukan amman da alamu bata cikin haiyacin ta hannun ta ya kama yace
“Halima!”
Kallon sa tayi yace
“Lafiya?”
Kai ta girgiza yace
“Kiyi hakuri ban san komai akan abunda ya faru tsakanin ku ba amman ki bari zan masa magana.”
“Hmm kai masa magana akan me? Mutum da baya so na ashe ba so na yake ba yazo ya lalata min rayuwa ta ne ya samu abinda yake so me kake tunanin zai min. Kila ta sandin wannan na mutu ko na shiga wani hali wa zan aura wa zai auren!”
Tana kaiwa nan ta bude kofa kawai tayi cikin gida.
Kai ya jinginar da kujewa sai kuma ya dauki waya ya kira Hajara. Tana dauka yace
“Ina Halima?”
“Tana daki!”
“Je ki duba kigame take?”
“Daki ta shiga ganta zaune kawai. Fada masa tayi yace
” shikenan kisa min ido akan ta.”
“Insha Allahu!”
Sannan ya bar wajen. Gidan Isma’il kawai ya nufa yana zuwa ya samu kofa a bude ciki ya shiga yana sallama ba kowa a falo wannan yasa ya zauna sai kuma ya mike ya shiga bedroom din sa. Kwance ya same shi da waya yarinya. Da sauri ya juyo bai tsaya ko ina ba sai cikin motarsa. Ysna shiga yayi gida yana mai tir fa halin Isma’il
Washe gari karfe bakwai a gida tai musu. Ummu dakin su ta shige tai kwanciyyar ta. Umma da Yaya Zainab sai hada hada suke na abubuwan da za ayi.+
Karfe Tara motocin daukar su ya zo Nan aka fada musu, Yaa Zainab ta shiga dakin Mamah inda su Sailuba da Rukayya suke sunci kwalliya kamar me.
Mama ta gaisar ta amsa sannan tace
“Daman kafi za’a tafi nace Bari nazo na fada muku.”
“To me za’a a kafa nasan dai ba wata tsiya bace.”
“Haka ne Mama Amman bama mu zamuyi kafin ba na dai fada Dane Dan company din su zasuyi komai!”
“To gamu Nan Zainab!”
Fita tayi tana Mai girgiza Kai.
“Ni ba inda zani!”
“Haba dai ku tashi muje mu kashe kwarkwatar idon mu!”
Mamah ta fada. Mayafai kawai suka saka suka fita. Umma dake tsakar gida tayi mamaki.
Zainab ma da ta fito daga dakin Abba tayi mamakin ganin su zasuje dukka. Waje suka fita suka samu mota suka shiga.
“Zainab nasan ba ruwan ki Amma ki kula!”
“Insha Allahu na turawa company din address Bari muje Kar suyi ta jira ga keys din.”
“To Allah tsare.”
“Amin Yaa Suleiman zai zo ya Kai ta wajen make up din ta zama cikin shiru Dan ayi da wuri Kar azo a makara.”
“Insha Allahu. Sai kin dawo.”
Ta fita. A mota ta samu su Mamah ta shiga wata daban aka dauki hanya Dan motoci hudu ne daya dagin Abba mutum biyu da dangin Umma mutum biyu itama sai wacce su Mama suka shiga da wacce Zainab ke ciki.
Tin da aka shiga unguwar jikin su Mama yai sanyi Dan so sukai suka unguwa marar kyau suna zuwa kofar gidan  gate man ya bude kofar a ciki suka samu motar kamfani na jiran su.
Parking akai. Su Mamah an shigowa gidan suka bi gidan da kallon mamaki. Key Zainab ta dauko ta bude bangaren su Ummu Nan suka shiga aka share akai mopping sannan suka fara kafi.
Mamah da Sailuba kuwa jiki. Su yai mugun sanyi dan ko motsi sun kasa. Dagin Abba da Umma ne suka ce
“Mu shiga muga gidan kan agama kafi.”
Ciki sukai su Mamah suka tsaya suna bin compound din da kallo. Sailuba tace
“Uhmm karyar banza kila ma hayar gidan akai Dan a nuna man burga kawai.”
“Ai kuwa nima abinda na fada bama yanzu da komai ake hayar sa dan naga wani shago a rimi Wai ana aran kayan kitchen da daki na wata daya wasu ma sati. Dan nasan gidan Nan dai Muhammad ba zai iya kama shi ba sai dai in haya irin na wata dayan Nan Dan a burge mu.”
“Ai kuwa dai.”
Rukayya dai kasa magana tayi Sailuba tace
“amman da akace Abba ya Basu gida.”
“Karyar tasa su amsa!”
“Ikon Allah muje mu kashe kwarkwatar idon mu Dan kila ba zamu dawo mu same su a gidan ha.”
Sukai ciki. Har an gama kafa gadaje da wardrobe da mudubi suna kan yin decoration din dakunan.
Wasu Kuma sun fara na falukan abin abun sha’awa kayan masu kyau da tsada suna ganin kayan sai da gaban Mamah ya buga hankalin ta ya tashi ta kallo Sailuba tace
“Ke mu koma gida tinda ba abinda zamuyi”.
STORY CONTINUES BELOW
“Ni dai Zan taho in an gama.”
“Shegiya marar zuciya.”
Cewar Sailuba suka fice ita da Mamah.
Kanin Yaa Muhammad suka gani wannan yasa yace
“Mai damu gida ba wani abun arzikin da zamuyi musu anan.”
Mota ya bude suka shiga sukai bar gidan. A mota ma Sai zagin su Umma da Ummu ake a haka ya suke su Yana tambayar kan da su waye wannan.
Restaurant din din da aka bawa order abinci ya zarce ya amshi abincin Yan kafi da lemo da ruwa ya nufi gidan.
Karfe Sha biyu har sun gama komai sai kayan ado da suke sakawa wasu Kuma suna ciki suna shara da mopping din dakin.
Karfe daya har sun gama suka zauna suna cin abinci da yaji kaji da kqyan hasi sai da suka gama sukai sallah sannan suka saka turaren wuta.
Corridor Nan duk an masa ado gidan ya Yi kyau ba karamin kashe kudi akai. Hatta sitting room din Mai gidan sai da suka saka masa Kaya Dan ma bedroom din da da falo an saka Masa.
Yaa Suleiman kuwa tin Sha biyu ya dauki Ummu suka tafi wajen makeup.
Su Anty Zianab na gama kafi aka fara sauka a gidan. Rukayya kuwa Bata uhmm bare uhmm sai vedio da ta dinga Yi dan ta nunawa su Mama.
Ai kuwa suna komawa ta hau nuna musu kalla suke duk bakin su ya mutu Dan ko Sailuba da ke auren Mai kudi gidan ta da kayan dakin ta Basu Kai na Ummu kyau da tsada da komai ba.
Sai suka rasa abun cewa. Suna zuane aka kawo musu abincin su daki shinkafa ce fried rice da sinasir tuwo waina bandashe dambu da lemuka Katan katan da ruwa kula kula aka kawo musu dq kaji kamar banza aka dire suka fita.
Rukayya ta zuba tagumi tace
“Wai duk a Ina suka samu wanna nasan dai Muhammad bai da wannan halin?”
“Kema kinsan Suleiman ne zai Yi Dan ya rufa musu asiri.”
“Ikon Allah!”
“To in bashi ba a Ina zasu samu!”
“Babu kam!”
Anty Zainab ce ta shigo tace
“Mama Ashe taho wa kukai?”
“To me zamu zauna muyi mu ba aiki ba!”
“Ayyah ai shiyasa na fada muku tin dazu!”
“To ai shikenan!”
“Yauwah Daman walima ce za ayi anjima Anan meena event center shine nace Bari na fada muku karfe hudu ne in Allah ya kaimu.”
“To Allah kaimu!”
Ta juya ta fita. Rukayya tace
Ammn fa ce min tayi ba abinda za ai gashi mun saka kayan da yafi ko wannen tsada Kuma!”
“Kada ki damu sai a saka wasu menene a ciki sai dai munje munga me za ayi.”
“Ai kuwa dai!”
*
**
***
****
*****
******
*******
Karfe hudu ya karaso kofar gidan ya aika a kira ta bata jima ba ta fito. A soro suka tsaya ta gaishe shi nan  ya amsa yana kallon ta. Kai tayi kasa dashi yace
“Gaskiya nayi missing naki Baby!”
Shiru tayi yace
“na shiga wani hali a rashin ki nazo na amshi soyayyar ki ko na samu sauki a zuciyata.”
“Dan Allah kada ka kawon zancen soyayya!”
“Saboda me?”
“Ni da kai na fada bamu dace ba bazan iya auren ka ba.”
“Akan me?”
” akan wani abu.”
“Dan Allah ki fada min wai me kuke boye min ne ke da Momy.”
“Kaje wajen Momy ita ta fada maka.”
“Taki shiyasa nazo ke ki fada min.”
Shiru tayi wata zuciyar tace ta fada wata na hanata. Can tace
“Na fada maka na jima ina bukatar aure amman mahaifi na yaki yai min wannan shine dalili na na fadawa ga halaka.”
“Wacce irin Halaka.”
Dagowa tayi ta kalle shi sannan tace
“Khaleel nida Momyn ka yan lesbian ne!”
Da sauri ya mike tace
“Abinda muke aikatawa kenan. Wannan yasa bata son ka auren kayi hakuri”
Tana kaiwa nan ta mike tayi cikin gida. Da kallo ya biya ya jima a wajen kan ya ja kafar sa ya fita dakin da ya koma ya rasa me yake masa dadi wato abinda mahaifiyar sa take aikatawa kenan. Anya kuwa ya yadda da Sakina ko dai ta fada ne dan ya hakura da ita.
A take yai booking flight ya bar kano a lokacin ba wanda ya kira taxi kawai ya sama dan ta kai shi gida. Yana shiga ya wuce sama dakin mahaifiyar sa ya wuce kai tsaye.
Kwance ya same ta da wata yarinya karama wacce ta samo gidan Hajiya Balaraba. Kan Yarinyar yayi ya dinga duka kamar Allah ya aiko sa da kyar ya kyale ta yayi dakin sa.
Key ya saka ya zube a wajen yana kuka wato da gaske abinda dai mahaifiyar sa ke aikatawa. Kuka yake sosai har numfashin sa na daukewa.
Tayaya za ai mahaifiyar sa ta zama yar lesbian tana lalata yara mata tana neman ya’yan cikin menene hakan innalillahi abinda ta fadi kenan.
Da kyar Hajiyar ta taikawa wa yarinyar ta shirya sannan ta dauke ta ta kai deriver ya maida ta can gidan Hajiya Balarana. Dakinta ta dawo ta fara safa da marwa ba abinda take ji sai tsoro yau Khaleel ya kama ta daman ya dawo ne ai bai fada mata zai dawo ba.
Da kyar tai wanka ta hau kan sallaya tayi sallah tana rokar Allah ya rufa mata a asiri ya shirya ta.
Ranar sam kasa fitowa tayi dan tana jin kunyar kallon dan ta da ya kama ta da wannan mummunar aikin. Khaleel ma kasa fita yayi ya rasa da wane idon zai kalli mahaifiyar ta.
Kan sa ya kulle ya rasa wane decision zai yanke haka ya zauna kan kace me ciwon kai da zazzabi sun rufe shi har rawar sanyi yake. Cikin bargo ya shiga ya lulluba. Da kyar Hajiyar ke fito dan sai ta leka taga baya waje wanda ita bata son rabon sa da waje ba yau kwana biyu tinda ya ka masu a wannan yanayin.
Sai da tayi kwana biyar bata ganin sa ta tambayi masu aiki suka ce ba inda ya fita tinda ya shigo bai kara fita. Nan tace  anya Khaleel yana lafiya. Kada dai ya kashe kan sa abinda ya daga mata hankali kenan ta nufi dakin nasa hankali a matukar tashe ta isa ta tura kofa ta bude shiga tayi.
Kwance ta hange sa cikin bargo da sauri ta karasa baya ta ja ganin yadda ya rame sosai idon sa a lumshe yana bacci abin tausayi. Hannu ta sa ta goge kwallar idon ta. Fita tayi ta kira Dr bai jima ba suka dawo tare.
Cikin bacci yaji ana taba shin wannan yasa ya bude idon sa yana ganin su ya fara kokarin mikewa. Dr yace
“Yi kwanciyyar ka.”
Gama duba shi yayi yan kalli Momy yace
“Ciwon sa ya tashi dan haka a kiyaye zai iya shiga ko wanne hali yanzu zan kawo masa magani dan Allah a kula dashi.”
“Insha Allahu!”
Dr ya fita ta juya ta kalli Khaleel da yai saurin rufe fuskar sa sam bai son ya kalle ta ma. Ta karaso da sauri tace
‘Khaleel dan Allah ka yafe min!”
“Me kikai min Mom? Baki min komai ba keda Allahn ki kiji tsoron Allah kada kinlbmutu kina aikata wannan bala’in domin in har kika yadda kina aikata wannan abun wuta zaki tafi kawai. Tayaya zan so haka Mom!”
Kuka ta fashe dashi tana girgiza kai.
“To dan Allah Mom ki tuba kibar wannan yar da shaidan ke ingiza ki kina binta sam Shai’dan ba son mu yake dan gani la’ananan Allah ne dan wuta wanda yasa sai ya kwashi rabon sa. Momy so kike ki fito a rundunar sa ranar gobe kiyama. Kinsan illar zina da madigo kuwa?”
Kuka take kawai.
“Allah ya yafe miki Mom Allah ya shirya ki.”
Ya koma ya kwanta. Tace
“Nagode!”
Ta mike ta fita dan samar masa abinci. Bata dawo dakin ba sai tare da maganin sa.
Da kyar ya dan taba ya sha magani sannan ya samu ya dan ji dama dama. Amman sai da ya kwanta ciwo na sati daya domin ya shiga tashin hankalin da bai taba shiga ba. Wacce yake so da aure tace masa ga abinda suke a gida yaga mummanar gani ya zaiyi.
Ya so ya cire Sakina a ransa amman kamar dada masa son ta ake  ya dauka wannan a matsayin kaddarq ne kuma hukunci ga mahaifiyar sa dake bin yaran mutune gashi nan Allah ya daura masa son wacce ta gama lalatawa.
Sosai ya dinga addu’a akan lamarin Allah zaba masa mafi alheri amman kamar kara masa son ta ake wannan yasa ya amshi kaddarar sa yasa a ransa kuma zai auri Sakina. Shiyasa ya fara shirin koma dan fada mata yana son ta a haka kuma zai aure ta kan yai wa Mahaifinsa da maganar neman masa auren sakinan
*Tofah ko Hajiyar zata yadda duk da haka*
Tinda ya tafi take cikin zulumi da fargaba. Bama da bai kara kiran ta ba itama tana son Khaleel amman bata jin zata iya auren sa saboda mahaifiyar sa da kuma shi kan da ba zai na ganin ta da daraja ba.+
Ta godewa Allah da ya ganar da ita bata mutu tana saba masa ba. Ta godewa Allah da ya ganar da ita tin wuri ba sai tayi nisan da bazataji kira ba. Lallai Allah na son ta da ya jarabce ta kuma ya shiryar da ita Allah ya kare ta ya tsare ta daga duk abun ki Amin.
Sallah ta gama tana jan carbi aka shigo ana fadin
“Anty Sakina wai kije inji wani a waje!”
“Wani kuma je kace waye?”
Ya juya ya fita. Bai jima ba ya dawo yace
“Khaleel ne!”
Da sauri ta mike tana fadin
“Khaleel da gaske Khaleel ya dawo to me yazo min?”
Amsar da ta gaza samu ta fita kawai tayi ta saka silifas sai kofar gida. Tana ganin sa taga ya rame. Kallon sa ta tsaya yi ya dago yana kallon ta sai ya sakar mata murmushi ya karaso soron gida. Jikin ta ne yai sanyi tai kasa da kai.
“Ina yini?”
“Alhandulillah na same ki lafiya?”
“Lafiya lou!”
Sai sukai shiru kowa ya kasa magana. Shine yai karfin halin fadin
“Sakina na dawo a karo na biyu na dawo da neman soyayyar ki. Na tafi naje gida da zulumi akan ki na so na cire son ki a rai na sai dai bani na sakawa kai na ba Allah ne ya saka min kinga kenan ba ta yadda za ai na cire da kai na. Amman na godewa Allah da yasa hakan dan wannan zai zama izina ko akan momy masu irin halin ta su gane. Dan haka zaki aure ni Baby?”
Tin da ya fara magana hawaye ya wanke mata fuska. Yana kaiwa nan ta juya masa baya tace
“Khaleel ba zan iya ba.”
Gaban ta ya dawo yana kallon ta yace
“Saboda mahaifiyata yar iska ce?”
Da sauri ta daura hannu akan bakin sa tana girgiza kai tace
“Ka daina fadar haka dan Allah!”.
“To ki ban dalilin ki!”
“Khaleel baka dace dani ba kaje ka samo mace kamila kamar ka ka aura.”
“Ni wa yace miki kamili ne?”
“Dabiun ka kadai sun nuna min haka Khaleel ba zan so in cuce ka ba ka, tq yadda ba zan zo a cuce ni ko wani nawa ba.”
“Amman aini nace ina son ki ko?”
“Khaleel amman….”
“Amman me?”
Kai tayi kasa dashi yai murnushi yace
“Ki cire batun Momy na ba ita zata zauna dake ba ni ina sonki a haka kuma ba yadda zatai da *Hukkuncin Allah* dan haka ki cire batun ta a ranki. Mahaifiyya tace ba zan taba iya canja ta ba ke kuma *Hadin Allah* ce ba yadda zanyi na yadda na aminta da ina son ki da aure kuma kada kisa wai zan na kallon ki a fasika in na kalle ki a haka tamkar na kalli mahaifiyya ta ne. Fatana kawai ki koma ga Allah aure na dake zai ceto ki daga wannan hanyar da izinin Allqh.”
Ya durkusa a gaban ta ya ce
“Dan Allah Love ki soni ki yadda dani wallahi ba zan iya rayuwa babu ke ba kwana biyun nan da nayi ni kadai nasan a halin da na shiga dan Allah Sakina!”
Ya karasa maganar yana kuka. Durkusawa tayi ta kama goge masa ido. Yace
“Ki daina gogen hawayen nan domin wanda zuciya ta keyi yafi wannan zafi da radadi ko shima zaki iya goge min. Ba abinda xaki ya gogu sai amsar soyayya ta. Wallah bake mutuwa zan yi. Ki taimakan na miki alkawarin rike ki da amana.”
STORY CONTINUES BELOW
Kai kawai ta gyada yace
“Kina sona zaki auren?”
Kai ta gyada da sauri ya mike ya rumgume ta yana fadin
“Nagode Love i love you so much!”
Ya sake ta yana mata wani kallo yace
“Amman bakya murna Baby!”
“Ina yi mana Khaleel a rayuwa ban taba zaton rayuwa ta zata sauya ba.
Na fada maka dalilin fadawa ta wanan halakar Baba na ne yaki aminta da nayi aure tin masu nema na da aure suna fito min amman sai yace nawa muke ni kuma Allah yayi ni macece mai matsananciyar sha’awa wannan yasa kawata ta fara nuna nayi wannan harkar in nayi ba wanda zai san ina yi tinda ba da namiji zan tara ba bare har na samu ciki kaji abinda yakai nini.
Shaidan yai min huduba nabi ta har na fara duk da nasan ba kyau amman ina neman mafita ne kawai.
Duk abinda nake yi ne ba a son rai na ba to yaya zanyi zan zo gida ne na zauna nai ta fama da sha’awa ba abin biyan bukata?
Tinda na fara kallon ka naji wani abu akan ka ashe ta sandin ka ne zan shiryu ta sanadin ka ne zan samu wata rahama Nagodewa Allah sa ya kawon kai cikin rayuwa ta ina rokan Allah da ya yafe min ya amshi tuba na.”
“Insha Allahu Sakina. Zan kasance tare dake zan zama kariya gare ki amman yanzu ya zamuyi da batun auren mu dan bana son a dauki lokaci.”
“Zanyiwa Yaya Fauziyya magana duk yadda muke ciki zan fada maka.”
“Nagode Sakina nagode da kika amshi soyayya ta.”
“Nice zanyi godiya da ka amshe ni bayan kasan koni wacece!”
” kada ki damu ina sonki. Kuma kada ki kara duba haka!”
“Nima haka!”
Ta fada tana rufe fuska. Matsowa yayi zai magana wayar sa ta dau kara zarowa yayi ya duba yaga Muhammad ne yace
“Ga mijin Yayar ki ma.”
Ya dauka ya kai kunne yace
“Assalamu alaikum!”
“Wa’alaikum salam romeo!”
Yai dariya yace
“Ya kake?”
“Alhamdulillah kwana biyu bana jin ka gaba daya lafiya dai ko?”
“Alhamdukillah naje gida yau na dawo garin ku!”
“Ah haba dai kasan muma mun tafi can garin mu gashi ina gayatar ka walima ma.”
“Ah haba dai a wane gari ne?”
Nan ya fada masa yace
“Insha Allahu zan zo har da Sakina ma.”
“Madallah ina jiran ku.”
“Sai munzo.”
Sukai sallama. Ya kalli Sakina yace
“Gobe zamu unguwa ki shirya.”
“Allah kaimu.”
“Amin. “
“Amman fa kwana biyu zamuyi”
“Kwana kuma?”
“Eh mana ko zan siyar dake ne?”
Kai ta girgiza yace
” to ki shirya.”
Kai ta gyada sukai sallama ta koma gida.
*
**
***
****
*****
******
*******
********
Tin washe garin zuwan su aka fara mata gyara kamar sabuwar amarya ban da hadin abubuwa da me gyaran ke ta bata wani ta sha wani taci haka dai. Ga kuyangu da aka zube mata su wajen guda biyar kowa da abinda yake mata.
Hatta kayan sawa kullum da wanda ake kawo. mata kala uku na safe rana da yamma. Sai gashi ta kara kyau tayi wani fresh da ita. Hafsat sai kwadata take tana fadin
“Anty kinga yadcda kika koma kuwa.”
Ummi kuwa ta hana Muhammad zuwa wajen ta sam. Ta kafa ta tsare tace ya barta ta huta dan gyara ake mata ba na wasa ba.
Shi da ita sai dai a waya yai tai mata shagwaba wai yayi missing nata har mamaki take dan kwana su biyar kadai amman duk itama ji take kamar sun shekara biyar basu hadu ba, ba abinda take bukata sai mijin nata ga hadin da ake mata yana saukar mata da wata sha’awar sa.
Tin zuwan su kuma kullum akwai masu zuwa gaishe ta kullum sai taga bakuwar fuska wai sun zo gaishe da matar Yarima. Wasu yara wasu manya wasu ma yan mata ne. Kuma yadda suke musu kamar sa maida su ciki.
Sosai Ummi ke kula da Su tamkar ya’yan ta komai ta samo tace su komai su. Dan ma Fauziyya na jin kunyar ta amman Hafsa hira suke sha abinsu su kamar sun saba da juna.
STORY CONTINUES BELOW
Satin su daya aka fara shirin walima da Mai martaba da Fulani suka shirya wanda za a fara da kilisa ta angwance washe gari ai zaman ago dayar washe garin ayi walima dayar ayi yini dayar ayi budar kai da kai amarya dakin ta.
Sosai Fauziyya tayi mamakin wannan abubuwa ganin ta jima da auren amman Ummi tace
“Yarima guda yai aure ba ayi wata walima ko abu ba ai dole ayi.”
Ana ya gobe fara Walima. aka shigo da wani katon akwati guda biyu da karami daya. Biyu na Fauziyya ne daya kuma na Hafsat. Kayan fitar bikin su ne komai da komai an tanadar musu tin daga kan kayan sawa sarka dan kunne mayafi takalmi da jaka da under wears komai da komai. Ummi tace
“Lefen ki yana gida Fauziyya kiyi hakuri abin yazo a kure kumamahaifin ki ya nuna duk baya son wadan nan abubuwan shiyasa amman yanzu maza ayi mu kamar yadda muke anan ina fatan ba matsala.”
Kan ta a kasa ta hau godiya. Ummi tace
“Kada ki damu ‘yata ai ba komai.”
Ta mike tace
“Mai lalle da gyaran kai zasu karaso anjima akwai abinda kike bukata?”
“Babu Ummi nagode Allah saka da Alheri.”
“Amim ‘Ya ta.”
Ta juya ta fita. Wayar tace tai kara ta dauka yace
“Yanzu dan Allah babu yadda za ai na ganki Baby!”
“Haba Yaya na sauran kwana nawa ka daure kawai baifi kwna biyar bata.”
“Ya salam. Kinsan yadda nake ji ne. Wallahi nayi missing naki alot.”
“Ka kara jurewa.”
“Gaskiya ki shirya ko zuwa yama in Ummi ta fita zan leko ko da dare.”
Zatai magana ya kashe wayar.
*
Zaune suke ana cire jan lalle mai baki ta fara zana mata ana gamawa ya bude aka kankare kai in kaga Fauziyya yadda tayi kyau ta dawo sabuwar amarya.
Hafsat ma an gamai mata nata tayi kyau sosai. Mai gyaran gashi ce tazo ta mata shamfo ta wanke aka shafa mai gashin ta ya kara saukowa yai bakin kirin. Tai kyau. Ummi ta shigo tare da kannen ta da suka zo biki.
Tana ganin ta tace
“Masha Allah ‘Ya ta ta fito fes tubarkallah.”
Kanwar Ummi tace
“Ah lallai Yarima ya iya zabe wannan ai dole ya rikice yanzu ya gama roko na wai dan Allah in san yadda za ai ya ganta ai kuwa dole anjima na kawo shi yaga amarya.”
Fauziyya dai kan ta a kasa ta gaishe da su sai yabon su suke suka fadin
“masha Allah yaran masu kyau dasu. Ga tarbiyya.”
Haka suka fita suna ta fada. Ummi kuma taji dadin yadda ake yabon su dan kowa abinda yake fada kenan.
Fauziyya na da kunya in suka shigo ta rufe fuska sai sun fita take budewa. Wannan na Dada burge Ummi na ganin yarinyar bata da matsala sam.
*
Momy kanwar Ummi ce ta kamo hannun sa suka shigo Ummi dake Falo tace
“Menene haka Sarah?”
“Ummi dan Allah ki barshi ya ganta yau fa sati daya yace rabon da ya saka ta a ido haba Ummin mu!”
Hararar su tayi tace
“Minti biyar na baka.”
Yace
“Nagode Ummi!”
Da sauri yai cikin dakin. Momy ta zauna tace
“Kema Ummi kya hora shi haka bayan kinsan ya riga ya tare da matar sa dole yaji kewar ta.”
Murmushi Ummi tayi tace
“Gata dai nai masa dan wani amarcin zai kara kwasa yadda nasa yar sudan da yar maiduguri suka gyara masa ita.”
“Ah lallai Ummi na son Autan nan nata mu baki sa an gyara mu ba.”
“Ai ku kun tsofa sai dai ya’yan mu ina su Juwairiyya ne da Kausar da Inteesar naji sun ce sun taho har yanzu basu karaso ba.”
“Suna hanya sun je an musu lalle ne.”
“Ok!”
*
Yana shiga dakin ya tadda Hasat a falo zama yayi yace
“Kanwata ya kike ya bakunta?”
“Lafiya lou Yaya ai mun zama yan gari. Ina yini?”
“Lafiya lou!”
“Masha Allah.”
“Ki ban number Ahmad sai shima a gayyace shi ko ya kika ce?”
” duk yadda kace Yaya!”
Yamika mata waya sa. Amsa tayi ya saka ya fara kiran sa yana dauka ya mika mata suka gaisa yace
“Oh kece ta nan sim din waye wannan?”
“Na Yaa Muhammad ne shi zai magana da kai.”
Ta mikanmasa. gaisawa sukai yace
‘To ina gayyatar ka bikin tarewar mu.”
“Au ku har sai anyi wani bikin tariyya to insha Allahu xan samu na shigo yaushe ne?”
“Zan turo maka da IV din tq whatsapp.”
“Ina jira.”
Sannan ya kashe ya mike yace
“Tana ciki ne?”
Kai ta gyada ya nufi dakin yana budewa wani kamshi ya doki hancin sa. Dakin ya shiga ya fara bin sa da kallo yaga ba kowa a ciki dan Fauziyya ta shiga tana wanka.
Zama.yayi bai jima ba ta fito daure da daurin kirji. Da sauri ya dago yana kallon ta. Tana ganin sa ta saki murmushi tace
“Sai da ka shigo kenan!”
“Ai na fada miki!”
Ya mike ya kamo ta ya zaunar yana fadin
“Wannan kece Baby? Kinga yadda kika koma kuwa!”
Murmushi tayi tace
“Kai maka canja ka kara kyau da haske.”
“Uhmm tsokana dai.”
Ya zaunar da ita a cinyar sa. Yana shinshina ta dan wani kamshi da take na musamman.
Fuskar sa ta shafa tace
“Ka bari na shafa mai!”
“In sha miki dai.”
Ya daga ta ya zaunar ya dauko mai ya fara shafa mata a kafa yana yi yana aika mata da salon sa. Ido kawai ta lumshe tana jin sa yana abubuwan sa. Take jikin ta ya fara amsar sakonnin da yake aika mata dasu.
Dan zare zanin jikin ta yayi ya cigaba da shafa mata mai yana tado da ita. Jikin ta take ya fara rqwa ya rumgumo ta yana shafa bayan ta a hankali ita kuma sai shigewa jikin sa tayi. Dole sai da ya bata hot romancing sannan ta samu ta dan nutsu. Shi da kan sa ya karai mata wanka ta fito ta shiya sannan suka zauna suna taba hirar soyayya.
Har aka kira magariba sannan ya tafi ba dan yaso ba kamar ya tafi da matar sa.
Karfe uku da Rabi an gamai Mata kwalliya amarya tayi kyau cikin peach kala material Wanda akai wa Dinkin doguwar riga sai mayafin kayan da aka dauro Mata a ka aka makele shi. Shigar Tai Mata kyau Kuma Bata nuna tsiraicin ta ba Dan dogon hannu ne Kuma ta bude. Su kansu masu makeup din Basu ta kwalliyar da ta burge su kamar ta Ummu ba. Tayi kyau har ba a magana.+
Sallah tayi tana zaune aka ce anzo daukar ta lokacin hudu da kwata. Mai makeup din da kanta ta rakata har bakin wajen. Wata sabuwar mota ta gani fara tas a wajen tsayawa sukai zata Kira number ya bude motar ya fito.
Sanye yake cikin milk din shadda wacce take kyalli ta Masa kyau ya sa bakin takalmi sau ciki ya daura hula Mai kyau da tsada a Kansa. Hannun sa daure da agogon azurfa sai zuba Kamshin yake.
Tin da ta daga Kai ta kalle shi Bata Kara dagowa ba Dan yai Mata kyau ba kadan ba. A hankali ya karaso ya kamo hannun ta. Suka wuce wajen mota.
Shiga tayi Shima ya shiga sai ya tsaya kallon ta.
“Baby Mie Kinga yadda kikai kyau kuwa!”
“Ka fini kyau Yaa Muhammad!”
“Wa ya fada miki ban taba ganin make up din da Tai kyau kamar Taki ba. Komai naki da ban ne Habibty nah.”
Murmushi tayi yazaro waya yai musu picture ya nuna Mata yace
“Kinga fa?”
Amsa tayi tana kallon yadda sukai kyau suka Dace da juna. Mika masa tayi yace
“Ibrahim Kai mu Ai Mana pictures kan mu karasa wajen!”
“To Yaya!”
Yace
“Ina yini Anty?”
“Lafiya Lou! Ya kake?”
“Alhamdulillah!”
“Masha Allah!”
Ya tada motar suka bar wajen. Gun hoto ya kai su mai kyau da tsari nan akai musu wajen kala goma aka turo masa sannan aka basu copy din suka fita.
*
Karfe biyar suna compound din wajen har an fara lectures. Anty Zainab ce ta karaso itama taci kwalliya cikin wani rantsatsen less tayi kyau sosai. Motar ta leka tana ganin Ummu ta saki mutmushi tana godiya ga Allhah.
Fitowa sukai akai musu jagora zuwa wajen da aka tanadarwa amarya da ango zama sukai aka daura faga inda aka tsaya a lecture din. Lecture ake mai ratsa zuciyar mai sauraro akan aure da biyayya ga miji. Kowa yai shiru yana sauraron lecture din.
Gefe na kalla naga tawagar su Mamah ce da su Rukayya da Sailuba sun ci kwalliya sun cakare ba laifi sai buda hanci suke gaban su plate ne na abinci sai bowl na pepper soup dayan kuma snack ne da lemo da ruwa an ajiye musu kowa abinda ke gaban sa kenan.
Can kuma su Umma ne da wasu daga kawayen ta suma sun ci kwalliya mai kyau kowa da mayafin sa akai. Sai gefe kuma dagin Abba da Umma ne sai wasu daga kawayen Ummu tin na isilammiyya har da wanda sukai university ma. Daya bangaren kuma dangin Hajiyar Muhammad ne da abokan sa daga can gefe. Kuma kowa an ajiye masa abincin sa a gaba.
Sannu a hankali kuma aka fara rabon kayan da Anty zainab ta bayar ayi. Shima dai lemo da ruwa ne a jakar sai cake da springroll da donot sai memo da aka rubuta suna  su da kur’ani da jaka. Kowa haka aka dinga bashi.
STORY CONTINUES BELOW
Daga wannan malamar ko malamin ya gama wani zai amsa yayi kuma sosai aka karu dan sun kawo hadisai da ayoyi na hujja ga abinda suke fada. Karfe shida da arbain aka tashi saboda ana kiran magariba. Karasawa sukai Ummu ta gaida Hajiyar Muhammad sannan suka je aka gaisar da Ummah.
Wajen Mamah suka karasa Rukayya na ganin sunyo wajen ta mike ta bar wajen zuciyar ya na bugawa dan tinda taga Muhammad taga ya canja ya kara kyau da girma sai zuciyar ta ta karye. Gaisawa sukai suka bar wajen ya nufi masallaci itama masallacin mata taje tayi sallah. Sai da suka idar sannan ya kira ta dan zai mai da ta gida kan azo kai amarya.
Karfe takwas suka karasa gida ta bude mota zata fita yace
“Baby!”
Juyowa tayi yai mata murmushi itama murmushin tai masa ta fita ta shige gida. Tana shiga ta tadda Anty Zainab a dakin su. Tana hada mata ruwan wanka. Tana fitowa tace
“Yauwah shiga kiyi wanka dare nayi Ummu!”
Kayan ta ta cire ta shiga tai wanka ta fito ta shafa mai. Hoda kawai Anty Zainab ta shafa mata sai magic lipstick wanda in an saka yake canja kala sai kwalli. Tai mata turaren wuta na musamman sannan ta bata kayan ta wata atampa ce Red wacce akaiwa adon red da blue. Ta saka ta dauko mata laffaya blue kala itama ta saka. Ta dauki flat shoe blue ta saka tai mata wanka da turaruka kala kala sannan ta hade mata kaya ta tas. Sallah isha’i tayi sannan ta kama hannun ta suka nufi dakin Mamah.
Mamah na zaune da su Rukayya suka shigo. Zainab tace
“mama tazo miki sallama”
“To Allah kiyayye!”
“Amin!”
Ta kamo hannun ta suka fita. A dakin Abban suka samu Umma. Zama sukai Abbah yana kallon Ummu fuskar sa dauke da farin ciki yana fadin
“Alhamdulillah!”
Gaishe shi sukai ya amsa sannan yace
“Yanzu nake magana naga har takwas da rabi ba akai ta ba.”
“Wallahi Abbah yanzu muka dawo ne amman ai an gama sai tafiya motoci ma suna waje.”
“Masha Allah!”
“Ummu duk abinda zan gaya miki na riga na fada miki su a bayabsai dai kawai in kara fada miki kalmar da zaki rike ta a rayuwar ki wato Hakuri mai hakuri shike da riba a komai. Ki zama mai hakuri da biyayya ga mijin ki ina alfahari dake kuma zan ta alfahari dake. Allah ya baku zaman lafiya yayi miku albarka Allah kema ya baki masu miki biyayya”
“Amin !”
Suka amsa sannan Umma tace
“Allah ya kai ki lafiya ya bada zaman lafiya Ummu!”
Rumgumr Umma tayi tana fadin
“Umma ki yafe min!”
“Baki min komai ba Ummu Allah miki albarka.”
Gaban Abbah ta karasa zata durkusa ya dago ta ya rumgume tana fadin
“baki min komai ba Ummu Allah miki albarka.”
“Amin!”
Ya kamo ta a haka suka fita ya saka ta a motar da za’a dauki amarya. A motar Daga kanwar Umma sai ta Abbah. Anty Zainab kuma a gaba haka suka tafi Ummu sai kuka take suna ta lallashin. Ta.
Duk wanda yaje yaga gidan sai dai kaji yana sa albarka da addu’ar Allah bada zaman lafiya. Haka aka kai ta dakin ta akavzaunar sukai mata nasiha sannan suka taho.
Kasancewar ba wasu kawaye ne da ita ba ya rage Anty Zianab ce kadai. Gyara gidan ta kara ta sakabturaren wuta sannan ta kira Muhammad yace gashi nan yana hanua. Mikewa tayi tace
“To Ummu ni zan tafi.”
Da sauri Ummu ta mike ta rumgume Anty tana kuka tana fadin
“Anty kinyafe min ina bata miki.”
“Baki min komai ba Ummu ina alfahari dake Allah yai miki albarka ya baki zaman lafiya.”
“Amin.”
Ta jata ta zaunar akan gado ta fadin
“Kiyi biyayya sannan kiyi duk abinda na saka kaki kinji. Allah bada zaman lafiya.”
Ta mike zata tafi tace
“Anty ki tsaya ya shigo.”
“A’ah Ummu ai yana hanya yanzu zao karaso kinji.”
STORY CONTINUES BELOW
Kai ta gyada ta mike tace
“Na tafi.”
Ta fita kuka Ummu take tna addu’a a cikin ranta kawai.
*
**
***
****
*****
******
*******
Ranar walima.
Karfe biyu su Khaleel da Sakina suka zo. Da aka shiga da ita wajen su Hafsa ta ganta sai kanta ya kulle. Basu jima da zuwa ba Ahmad ya dire duk suna tare da Muhammad a sashen sa.
Kan lokacin walima yayi. akai mata makeup mai kyau. Amarya ta saka ash kalar less mai ado da maroon kalar zare ta saka alkebba tai kyau. Wajen da aka tanada dan ita aka kai ta aka zaunar.
Muhammad ma yasha shadda Ash kala sai kyalli yake gefen maza ya zauna. A haka aka yi taro mayan malamai sukai wa’azi sosai jikin kowa yai sanyi na wajen.
Sai gab da magatiba aka tashi anci an sha an raba gift da duk wanda yazo. Kowa ya tafi dan yin sallah. Fauziyya na idarwa kanwar Ummi ta shigo ta sa tayi wanka. Wasu sabbin kaya aka kawo mata ta saka farar atamfa ce mai adon golding. Haka alkebbar ta ma fara ce da adon golding tai kyau. Aka dauke ta aka tafi da ita wajen Ummi da Abbi. Nasiha sukai mata sannan aka shige da ita sashen su.
Ginin kadai abin kalla ne dan ya tsaru kuma an zuba komai mai kyau da tsada. Dakin ta aka kai ta aka zaunar sannan suka tafi suka barta. Sai Sakina da Hafsa a wajen ta.
Karfe tara ango da abokan sa da Khaleel da Ahmad suka shigo.  Nan aka danyi barkwanci akai addu’a sannan sukaiwa Amarya da ango fatan alheri suka tafi tare da Sakina da Hafsa.
A kofar part din Ummi suka tsaya suka sha hirar su. Sai goma sukai sallama kowa ya tafi dan kwanciyya.
*
Muhammad na rufe kofa ya juyo ya dawo. Dago Fauziyya yayi ya yaye mata mayafin yace
“Su Ummi duk sun mai da min mata sabuwar amarya ni dai kada kiji kunya ta kada ki manta munyi watanni da tarewa.”
Ya fada yana rumgume ta.
Kai ta make tace
“Ai kuwa dole duk abinda ake a ranar amarcin mutum a sake min.”
“Ke kici tudu biyu kenan.”
Kai ta gyada. Daukar ta yayi yace
“Baki da matsala muje muyi sallah mu sake godiya gareshi sai kuma na ciyar dake daga nan sai kuma!”
Ya kanne mata ido daya. Ta shafa kansa suka shiga alwala tayi suka fito sukai sallah suna idarwa ya dauko naman da suka shigo dashi a baki ya bata hayan sun gama ya shiga suka wanke bakin su. Sannan ta fito ta canja kayan baccin ta.
Shima bayan ya saka ya hau gadon. Ta juyo tana kallon sa yace
“Kashe mana fitilar.”
Kashewa tayi ta nufi gadon ta haye kan sa. Rumgume ta yayi yana kissing goshin ta. Yace
“I love you Baby!”
“I love you more.”
“I need you.”
Shiru tayi sai tace
“Nima.”
“Da gaske?”
Kai ta gyada yace
“Baby wallahi ina bukatar ki.”
Kansa ta kama tace
“Ai ni taka ce!”
“Da gaske?”
Kai ta gyada. Nan ya hade bakin su. Daga haka ya fara romancing nata tana maida masa da martani. A haka har ya raba ta da komai na jikin ta shima haka. Tin daga yaddavtaji yana aika mata sakonnin da bata taba jin irin su ba jikin ta ya fara sanyi. Dan ta yadda yana matukar bukatar ta bama yadda taga yana ta rawar jiki ido kawai ta lumshe wani ta taya shi wani kuma ta share. Lokacin da taji yana laluben inda zai shiga sai da abun ya bata mamaki domin ta yadda da gaske Muhammad bai san taya ake abun ba amman cikin hikima da ilimi ya nemi hanyar sai da ya gane sannan ya fara addu’ar saduwa da iyali.
Ido kawai ta runtse dan tana tuna ranar da Kamal ya fara raba ta da mutumcin ta lokacin bata san ma yanayi ba saboda maganin da ya saka mata. Wasu hawaye ne suka zubo mata. Jin yana kokarin shiga wajen bai bashi dama ba yana ta kara dannawa sai ya bata tausayi. A haka da kyar ya samu ya danna wanda daga ita har shi sai da suka saki wani ihu ita na azaba shi kuma da dadi.
Yana shigar ta ya saki wata ajiyar zuciya nan ya fara having sex da ita. Yi yake yana jin sa a wata duniya ta daban da bai taba shigar ta ba. Dan ya kasa jin ya hakura da ita. Sai da ya dauke wajen awa uku yana abu daya da kyar ya samu ya zare jikin sa ya rumgume Fauziyya wacce take kuka. Shima kukan ya sakar mata domin abun da yaji ya matukar kashe masa jiki domin bai taba zaton samun abunda ya samu ba. Sai kuma ya hau tambayar kansa anya da gaske Fauziyya ta taba bin maza kuwa domin shi a yau ji yayi kamar a leda ya bare ta bama da yadda ya shige ta.
Fauziyya ganin yana kuka sai ya kara karya mata zuciya kila yana kukan bata kawo masa budurci bane dan haka sai ta kara sakin wani kuka. Cikin tashin hankali ya matso yana fadin
“Innalillahi wainna illahir rajiun Baby menene kike kuka ko ban miki bane? Ko ban kai yadda kike so bane?”
Kai ta hau girgizawa ya dago ta ya rumgume yana fadin
“Fada min kukan me kike?”
“Muhammad ina kuka akan dalilai da yawa na farko kai kukan me kake?”
“Kukan farin ciki na samu abunda ban taba zaro ba dan Allah Baby ke ba virgin bace? Ni dai wallahi ji nake a budurwa na sameki.”
Sai ta kara fashewa da kuka. Hankalin sa ne ya tashi yace
“Menene Baby me kuma nayi ya saki kuka?”
Kai ta girgiza tace
“Ina kuka na yau zakayi danasin aure nane.”
Hannu ya daura a bakin ta yana fadin
“Ba zan taba danasani ba. Fatana ki zama uwar ya’ya na har abada mu hadu a aljanna cikin gida daya.”
“Ina son ka My Honey love.”
“Nima ina son ko Baby.”
“Yau naji abunda ban taba ji ba. Having sex with you once yasa na samu nustuwar da ban taba samu ba yasa naji dadin da ban taba ba. Dan Allah kada ka barni dan Allah kada ka guje ni.”
“Ba zan taba ba Baby ki kwantar da hankalin ki kuma ni ji na nake na sameki a budurwa dan Allah ki daina tuno da abin baya.”
Sai kawai ya fara kissing nata ta ko ina itama nan ta fara mada masa da martani. Nan suka kara komawa ruwa. Kiran sallah shi yasa suka tsagaita ba dan sun gaji ko sun koshi ba.
Daukar ta yayi sukai bandakin su wanka sukai sannan ya fito sukai sallah dan har an idar da sallar. Suna idarwa suka koma gado.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *