YANCIN MATA CHAPTER A

 YANCIN MATA CHAPTER A

* Tafiya take tana cikin sauri tana duba agogon dake d’aure a tsintsiyar hannun ta , yarinya ce y’ar kimanin shekara goma sha biyar tana sanye da dogon hijjabi da alama daga islamiyya ta dawo , titin tas babu kowa gashi magariba ta gabato hakan yasa take ta sauri dan tasan halin unguwar tasu yanzu sai a sace mutum .

+

Wata mota ce bak’a k’ira Benz tazo ta gifta yarinyar a guje , cike da tsoro yarinyar ta cigaba da sauri kamar zata tashi sama , cak motar ta tsaya tare dayin reverse har ta dawo inda yarinyar take

Wasu maza ne suka fito daga motar basu tsaya wani tunani ba suka fesawa yarinyar wata hoda a fuska , nan dake tayi baya zata fad’i suka taro ta suka saka ta a mota suka cigaba da gudu.

Sabon sirinji suka d’auko suku dibi jinin yarinyar sannan suka rife sirinjin , basu tsaya a ko ina ba sai a bakin wani asibiti d’aya daga cikin mazan ya d’auki wannan jinin ya shiga cikin asibitin .

Direct lab ya nufa yana zuwa ya mik’a musu kamar yadda suka saba , gwajin cutar k’anjamau akayi akaga babu ,  sannan akayi na ciwon hanta shima akaga babu , result din ya karb’a ya juyo a guje ya koma cikin motar suka cigaba da tafiya.

Basu tsaya a ko ina ba sai a bakin wani k’aton gida mai bala’in kyau ,horn suka danna mai gadi ya bud’e suka shiga cikin gidan , parking suka yi cikin sauri suka d’auko yarinyar suka shiga da ita parlourn gidan.

Bedroom suka shiga da yarinyar suka kwantar da ita suka fito suka tsaya suna jiran ogan nasu yazo .

Basu wani dade ba ya fito daga d’aya d’akin ya tafiya dak’yar kamar Wanda baya San taka k’asa , zama yayi a kan d’aya daga cikin yace “Aikin Ku yayi kyau zaku iya tafiya”

Cikin rawar jiki suka amsa da “An gama ranka ya dad’e a ji dad’i lafiya” suna gama fad’ar hakan suka juya suka fita daga parlourn.

Mik’ewa yayi ya shiga d’akin da yarinyar take , murmushi yayi yace “Babu laifi tayi” k’arasawa kan bed d’in yayi tare da kwanciya kusa da yarinyar, a hankali ya zame mata hijjabin daga jikin ta ya Zuba mata ido yana kallon ta , tab’e baki yayi kamar yaga kashi haka ya zuge zip d’in rigar ta ya fara sha’anin sa .

Bai bar yarinyar nan ba sai ya tabbatar yayi mata kaca-kaca sannan ya kyale ta , wani bakin Abu ya d’auko ya kama hannun yarinyar ya rubuta _BAD MAN_ da manyan bak’i tare da yin singing a gaba , kayan ta ya d’auko ya saka mata sannan ya fito daga d’akin.

Kallon agogo yayi a yaga har sha d’ayan dare tayi tsaki yayi ya dau waya ya kira yaran sa yace ” Dalla malamai kuzo Ku d’auke min wannan bazawarar a gida na”

Jin ya ambaci bazawara yasa suka gane ya yiwa yarinyar fyade ,cikin rawar jiki suka dawo gidan suka d’auke ta suka shiga mota suka jefar da ita a inda suka d’auke ta.

Bad man kuwa shiryawa yayi cikin k’ananan kaya ya shiga mota ya nufi club.

Washe gari

*****

“Umme na shirya zan tafi wajan aiki” wata kyakykyawar budurwa ta fad’a tana rataya jaka

Wacce aka kira da Ummen tace “To Hazifa Allah ya kikaye hanya Allah ya bada sa’a”

Hafiza tace “Ameen Ummee na , ina Hanifa?”

Ummee tace “kema kinsan tunda suka samu hutun makaranta bata da aiki sai bacci”

Hafiza tayi dariya tace “To in ta tashi ki gashe ta na tafi ” ta fad’a tana fita daga gidan.

Sauri take ta Dan ta isa titi sabida ta kusa makara a wajan aiki, mutane ta gani a kan titi an cika a waje d’aya da alama akwai abinda ya faru a wajan , da sauri ta k’arasa wajan tana fad’in “lafiya jama’a meya faru?”

Wani mutumi yace “wani Mara imanin aka samu yayiwa k’aramar yarinya fyad’e kalli kiga halin da take ciki” ya fad’a yana nuna inda yarinyar take

Cikin tashin hankali Hafiza ta k’arasa wajan ta durk’usa a gaban yarinyar , ganin halin da take ciki yasa Hafiza ta fara hawaye tana fad’in ” wannan ai Iman ce y’ar mak’otan mu , Dan Allah Ku samo mota mu kaita asibiti “

Adaidaita sahu aka tsayar aka saka yarinyar da take sume bata numfashi ,

Suna zuwa aka shiga da yarinyar d’akin taimakon gaggawa likitoci suka rufu akan ta Dan ganin Dan ceto rayuwar ta ,

Zama Hafiza tayi tana tunanin halin da yarinyar take ciki , wajan minti talatin wani likita ya fito ya kalli Hafiza yace “muje office”

Bin bayan sa tayi suka shiga ta zauna yace “Fyad’e aka yiwa yarinyar nan na rashin imani dan Yanzu haka sai da aka yi mata dinki kuma itama akwai wannan tambarin a hannun ta”

Dukan table Hafiza tayi tace “Bad man again”

Dr Amin yace “Eh tabbas abinda yake jikin hannun ta kenan”

Cikin b’acin rai Hafiza tace “Wai waye wannan Bad man din ?”

Dr Amin yace “Allah ne ya sani Dan har yanzu ko full name dinsa ba’a sani ba balle kuma a san fuskar sa , kuma duk wacce yayiwa fyad’e sai yayi mata wannan tambarin a hannu, lauyoyi , y’an sanda har yanzu basu gano waye wannan mutumin ba”

Hafiza ta mik’e tace “Ni BARRIER HAFIZA nayi alk’awarin ganin bayan wannan mutumin , nayi alk’awari sai na gurfanar dashi a gaban kotu”.

📖* mik’ewa Dr Amin yayi yace “Ina bayan ki Barrister nima zanyi k’ok’ari wajan ganin an kamo wannan Bad man din”

+

Juyowa Hafiza tayi tace “Nagode sosai , dani da kai zamu had’a k’arfi da k’arfe wajan ganin bayan wannan mutumin, yanzu mu koma wajan Iman d’in”

Fita suka yi daga office d’in suka koma d’akin da aka kwantar da Iman , basu dad’e da shiga ba ta farka tana bud’e ido a hankali , nan take abinda ya faru ya shiga yi mata yawo a kwakwalwar ta ,

Juyowa tayi ta kalli Hafiza da ta Zuba mata ido tana kallon ta, cikin kuka Iman tace “Aunty Hafiza meye ya faru dani bayan wannan mutanen sun zuba min Abu a fuska?”

Cikin Tausayi Hafiza tace “ki kwantar da hankalin ki Iman ki daina kuka kinji”

Bud’e k’ofa akayi aka shigo ko ba’a fad’a ba ansan dangin Iman ne suka k’araso , Maman ta ta k’arasa wajan tana goge hawaye ta zauna kusa da Iman d’in tace “kiyi Hak’uri Allah yana bayan mai gaskiya, Allah ya tona asirin nan mutumin” ta fad’a cikin dashewar murya

Mik’ewa Hafiza tayi ta isa kusa da Iman ta dafa ta tace ” Iman a cikin Wanda suka Zuba miki Abu a fuska babu Wanda zaka iya ganewa?”

Iman tace “bazan iya gane su ba tunda ta baya na suka biyo daga nan kuma ban kuma sanin inda kaina yake ba sai yanzu”

Numfashi Hafiza ta sauke tace “Mama zan tafi wajan aiki amma insha Allah zan iya bakin k’ok’ari na wajan ganin na binciko wannan mutumin”

Mama tace “Allah ya baki sa’a Hafiza , Nagode sosai Allah yasa kiyi nasara akan sa”

Murmushi Hafiza tayi tace “Ameen Mama daman addu’ar Ku make nema , ni na tafi Allah ya k’ara lafiya” ta fad’a tana fita daga d’akin.

Sallama tayiwa Dr Amin ta fita daga asibitin.

Da kallo Dr ya bita yana wani irin murmushi dashi kad’ai yasan ma’anar sa .

Hafiza kuwa bata wuce ko ina ba sai cikin babbar kotun dake garin Kaduna , bayan an gama shari’ar y’an uwanta lauyoyi ta kira maza da mata ta had’a meeting bayan su zauna Hafiza ta kalle su tace ,

“Na had’a wannan meeting ne badan komai ba sai dan mu had’a kai mu kama wannan Bad man d’in da yake cutar y’ay’a mata a banza , yanzu maganar da nake muku y’ar mak’otan mu Iman tana can a asibiti a kwance , meye amfanin mu in  banu binkico wannan azzamulin ba , sabida na taimakawa mata nayi karatun lauya kuma har yanzu ina kan baka ta , ya kuke ganin za’a b’ollowa abin?”

Mik’ewa barrister Hidaya tayi tace “Sam bada ni za’ayi wannan aikin ba haka kawai ina zaune lafiya , ai nasan kin San Barrister Hadiza itama irin halin kine da ita ta nace sai ta gano wannan mutumin in takaice miki labari karshe sawa yayi aka d’auko ta yayi mata fyad’e na rashin mutunci kuma d’auki hotunan ta tsirara ya watsa su a social media, tsabar bakin ciki sai da ta kusa mutuwa wallahi, Dan haka Hafizatu Allah ya baki sa’a nayi nan” ta fad’a tana fita daga wajan.

Jin haka yasa sauran matan suka tsorata suka dinga barin wajan sai da ya zama daga Hafiza sai maza guda biyu a zaune , Hafiza tace ” to ko kuma zaku gudun ne?”

D’aya daga ciki ya mik’e yace “wacce Hidaya ta baki labari tare suka had’a kai da Barrister Buhari shima bai kyale shi ba sai da yayiwa matar sa da k’anwar sa fyad’e kuma ya turo masa hotunnan yace masa in   bar aiki a kansa ba wallahi sai ya yad’a su a media, nima bazan iya ba Allah ya baki sa’a”

D’ayan yace “A’a nima tsaya ni mu tafi bazan iya ba wallahi inason matata da y’an uwana ” ya fad’a suna fita tare daga wajan.

Dukan table tayi tace “wai waye wannan Bad man d’in? Su kuma matsorata kowa ya gudu sun barni ni kad’ai , to ni da Allah na dogara babu abinda ya isa yayi min indai Allah bai tsara hakan ba, ” mik’ewa tayi ta rataya jaka tace “ina nan akan baka ta na ganin bayan mutumin nan” ta fad’a tana fita daga wajan.

******

Sauke wayar yayi daga kunne yayi murmushi mai baiyanar da sirrin kyaun sa yace “Barrister Hafiza sabuwar customer ta kenan , ina yi miki barka da shigowa rayuwar Bad man , da kinsan waye ni da bakiyi gangancin k’ok’arin shiga rayuwa ta ba amma babu komai nasan ta yarda zan b’ullo miki sai kinyi Dana sananin sanin sunana a rayuwar ki”

Waya ya d’auka ya kira yaran sa suna d’auka yace “another baby” kawai ya kashewar wayar ya cigaba da murmushi.

*Tofa ya akayi yasan shirin Hafiza a kansa*🤔

__________📖* Basu d’auki wani lokaci ba suka kawo masa yarinyar da ya bukata , kamar yadda suka saba sai da suka biya asibiti akayi gwaje-gwaje sannan suka kawo ta .
Bai d’auki wani lokaci mai yawa ba ya fito yana tab’e baki yana tsaki kamar Wanda akayiwa dole , zama yayi a kan kujera sannan ya d’auki waya ya kira su yace suzo su Fitar masa da yarinyar daga gida , da rawar jiki suka iso suka d’auko ta kamar jaririya suka fito
Har zasu fita ya dakatar dasu da fad’in “duk Wanda zakuyi Ku tabbatar wannan yarinyar asibitin cikin gari aka kaita, bance Ku kaita ba amma kusan inda zaku ajjiye ta ” ya fad’a yana danna waya kamar bashi yake magana ba
Ciki da bin umarni suka amsa da “an gama oga” suka juya suka fita.
*****
Hafiza kuwa koda ta fito daga wajan meeting d’in gida ta wuce , koda ta k’arasa gida a zaune ta tarar da Ummee da Hanifa a zaune suna cin Abinci , sallama tayi ta zauna ba tare da tace komai baba
Cike da mamaki suke kallon ta , Hanifa tace “Aunty Hafiza lafiya kuwa?”
Tsaki Hafiza tayi ta bawa su Ummee labarin duk abinda ya faru har had’a meeting d’in da tayi sai da ta basu labari , Salati Ummee tayi tace “kai amma wannan yaro baya kyautawa , to ai ni banga ta zama ba tashi zanyi naje asibitin na dubo Iman d’in Ku zauna a gidan bara naje na dawo” har zata mik’e sai kuma ta koma ta zauna tace “yauwa Hafiza d’azu Abbie dinku yace na fad’a miki kinyi karatu kin gama kin fara aiki to dole ki fito da miji ayi miki aure , yace ya Zuba miki ido ne yaga iya gudun ruwan ki to yaga baki da alamar yin aure yanzu to baki isa ba cikin wanda suke zuwa Neman auren ki ki Fitar da d’aya , na Isar da sak’o” tana gama fad’a mata haka ta Mike ta shiga d’aki ta tayiwa Abbie waya ta tambaye shi zuwa asibiti ya barta sannan ta fito ta tafi.
Tunda Ummee tayiwa Hafiza wannan maganar tayi shiru bata yi magana ba , Hanifa tace “wai tunanin ne kike yi ne?”
Hafiza tace “ba tunani nake ba kawai dai ina tunanin Wanda zan aura zai bar ni na cigaba da aikina kuwa?”
Hanifa tace “wannan ai ba matsala bace tun kafin ayi auren zakuyi da wajewa in ya aure ki zai barki ki cigaba da aikin ki , indai yasan mahimmancin alk’awari zai barki kiyi wallahi”
Hafiza tace “hakan kuwa za’a yi Nagode y’ar uwata”
*WACECE HAFIZA?*
Alhaji Kabir Fulani shine sunan mahaifin ta haifaffen garin Kaduna amma asalin su fulanin Gombe ne, shi kadai iyayen sa suka Haifa tun yana yaro mahaifin sa wato Isma’il Fulani da mahaifiyar sa wato Ladi  tun yana yaro Allah yayi masu rasuwa ya taso a hannun kanin mahaifinsa wati Jamilu wanda ake kira da Kawu Jamilu , Ummee wato Batulu itama y’ar garin ce ita kad’ai ce matar Alhaji Kabir Fulani , Alhaji Kabir Mai arzuki ne dai-dai gwargwado ci da sha da sutura , kudin makaranta babu abinda ya gagare shi Dan har Makkah ya biya yaje shida Kawu da kuma Ummee ,
STORY CONTINUES BELOW
Y’ay’an su biyu duka mata babbar itace Hafiza , ta biyu kuma Hanifa su kad’ai Allah ya basu hakan yasa suke mutukar kaunar yaran , duk da son da suke musu basu bari tarbiyyar su ta lalace ba sunyi k’ok’ari wajan ganin su bawa yaran tarbiyya ,
Hafiza y’ar shekara ashirin a duniya kyakykyawa ce sosai sai dai ba fara bace sosai Dan Hanifa ta fita haske , tun Hafiza na yarinya in taji labari an yiwa yarinya fyad’e kuka take yi sosai wani lokacin ma ta saka cin Abinci sabida kuka , hakan yasa ta lashi takobin yin karatun lauya kodan ta tsayawa yara mata ta karb’ar musu *Y’ANCIN SU* idan irin hakan ta taso,
Mahaifan ta sun bata kwarin guiwa sosai wajan ganin ta cimma burin ta a rayuwa ,  a haka har ta kammala digree dinta tayi dautar kasa ta fara aiki ,duk wani case na fyad’e indai yazo hannun ta sai ta San yadda tayi taga karshen sa, B’angaren islamiyya kuma tayi sauka tun tuni harda haddar alkur’ani izu sittin akan ta itada Hanifa.
Wannan kenan
Suna zaune Hafiza tana cin Abinci yaro yayi sallama yace ana sallama da Hafiza a waje , kafin tayi magana Hanifa tayi saurin cewa “jeka kace tana zuwa “
Hafiza ta kalle tace “meye haka?” Hanifa tace “eh ina sane nayi hakan nasan in ba haka nayi miki ba ba zuwa zakiyi ba”
Tsaki tayi ta Wanke hannu ta ta saka hijjabi ta fita .
A tsaye ta mutumin yake ya juya baya , sallama tayi masa tare da sunkuyar da kanta sabida yadda kirjin ta yake bugawa da k’arfi , cike da fara’a saurayin ya amsa yana murmushi yace “malama Hafiza an wuni lafiya?”
Hafiza tace “Lafiya lau ” Saurayin yace “To nidai sunana Hafiz haifaffan garin Kano amma ina zuwa nan nake da zama sabida anan nake aiki , wato Hafiza tunda na dora idona akanki naji duk duniya babu wacce nake so kamar ki , wallahi kuma da gaske nake ba karya nake ba kuma ni da shirin aure naza ba yaudara ba , shin zaki iya karb’a ta a matsayin masoyin ki?”
Tunda ya fara magana ta sunkuyar da kai tana sauraran abinda yake fad’a  a hankali tace “hakika ina godiya sosai da har kazo ka furta ni Kalmar kana sona , duk Wanda yace yana sonka a duniya ya gama yi maka komai amma ka bani lokaci zanyi tunani”
Murmushi yayi yana k’ara jin sonta har cikin zuciyar yace “haka ne malama Hafiza zan baki lokaci kiyi tunani kiji in na kwanta miki a rai to Masha Allah haka ake in kuma akasin haka ne kaii bama a fatan hakan”
Yadda yayi ne ya bata dariya hakan yasa tayi murmushi
Yace “ko zan iya samu number wayar ki domin mu dinga gaisawa ?”
Hafiza tace “babu komai kowa na saka maka ” yace “kai amma Nagode”
Ya ciro wayar sa ta saka masa number sannan sukayi sallama ya tafi.
Da murmushi akan fuskar ta ta shiga gida , Hanifa na ganin yanayin fuskar ta kwashe da dariya tana fad’in “da alama angon yazo yau kenan , tb gaskiya Aunty Hafiza kin fad’a da yawa wannan Zuba murmushi haka”
Itadai Hafiza d’aki ta koma bata kula ba , har zata zauna wayar ta tayi k’ara tana dubawa taga Dr Amin cikin sauri ta d’auka yace “Hafiza kiyi kizo asibiti yanzu an kuma kawo case d’in Bad man”
Hafiza tace “ya salam wai wannan wane irin mutum ne haka , shikenan nan dai gani nan zuwa insha Allah” ta fad’a tana kashe wayar tana fatan Allah yasa wannan taga wata shaida da zata iya gane shi ko yaran sa ko gidan sa
Fitowa tayi ta fad’awa Hanifa sannan ta bar gidan cikin sauri.
*****
Zaune yake akan kujera yana danna laptop , wata yarinya ce ta sakko da sauri ta bud’e k’ofa zata fita ya Daka mata tsawa da fad’in “ke!! Dawo?”
Cike da shagwaba ta dawo ta zauna tana fad’in “haba Yaya Dan Allah wai kama ta sai ka dinga hana ni fita na fad’a maka babu abinda zai same ni”
Tsaki yayi yace “ke wai kunnen k’ashi ne dake? sau nawa zance miki ki daina fita kedai sai dai driver amma bakya ji ko?”
Tace “Haba Yaya Dan Allah nifa na rasa meyasa baka sin ina fita ni kad’ai bayan babu abinda zai same ni”
Cikin tsawa yace “Tashi ki bani waje!”
Cikin rawar jiki ta mik’e ta koma d’aki tana kuka.
Bad man kuwa ko a jikin sa Dan ko zata yi kukan jini baza ta fita ita kad’ai ba sabida yasan akwai mutane da yawa irin sa , haka kawai tsautsayi ya fad’a kan kanwar sa shiyasa yake killace ta sabida baya son duk abinda zai b’ata mata rayuwa.
*Tofa lallai ma wannan Bad man din*🙄
__________📖* Cikin sauri Hafiza ta fita daga gidan bata wuce ko ina ba sai asibiti, tana zuwa ta ga Dr Amin yana jiran ta tana isowa suka shiga d’akin tare ,
+
A kwance yarinyar take tana faman kuka mai sauti , k’arasa wajan ta Hafiza tayi ta zauna kusa da ita tace ” Ya sunan ki?”
D’ago kai Yarinyar tayi cikin kuka tace “Haleema” Hafiza tace “A wacce unguwa kike ?”
Haleema tace “A unguwar Sarki” Hafiza tace “ko zaki iya gane Wanda suka d’auke ki ?”
Girgiza kai tayi alamun A’a , Hafiza tace “ko kinga wata alama ko murya da zata iya sawa a gano Wanda yake aikata wannan laifin?”
Haleema tace “tun lokacin da suka d’auke ni ban kuma sanin inda kaina yake ba sai yanzu”
Hafiza tace “to kiyi Hak’uri ki daina kuka insha Allah saina karb’ar muku Y’ANCIN Ku”
Kallan Dr tayi tace “muje office” tare suka fita suka shiga office din , Hafiza ta kalli Dr cikin damuwa tace “Dr har yanzu fa bamu da hujja a hannu da zamu tunkari wannan mutumin”
Dr yace “nima abinda nake tunani kenan wallahi “
Hafiza tace “Amma babu komai hakan bazai saka muja da baya akan abinda muka yi niya ba , ni bara na tafi zan San yadda zanyi wajan ganin na samu abinda nake so” sallama tayiwa Dr sannan ta tafi gida.
Bayan kwana biyu
Soyayya mai k’arfi ta shiga tsakanin Hafiz da Hafiza dan yanzu har Abie yasan da maganar Hafiz,
Zaune suke akan tabar a surun gidan su , Hafiz ya kalli Hafiza yace “ya dai wai lafiyar kalau kuwa?”
Hafiza tace “Ai bazan tab’a samun lafiya ba inhar banyi nasara akan wannan mutumin ba”
Hafiz yace “wa kenan?” Hafiza ta kwashe labarin Bad man gabad’aya ta gayawa Hafiz da kuma kudurin ta a kansa.
Hafiz yace “Ko ni ina bayan ki akan abinda kike sonyi kuma zan taimaka miki har ki cimma burin ki, Amma Hafiza bakya ganin kin saka kanki cikin matsala duba da irin abinda yake yiwa duk Wanda yayi yink’uri irin naki?”
Hafiza tace “ni da Allah na dogara kuma shi zai kare ni a duk inda nake Dan haka wannan abun bai dame ni ba Sam”
Hafiz yace “haka ne , Allah ya baki ikon aiwatar da komai cikin salama”
Murmushi tayi tace “Amin masoyina”
Daga nan suka yi sallama ya tafi .
Tunda Hafiza ta koma gida take tunanin yadda zata b’ullowa wannan Bad man d’in , k’arar wayar ta ta katse mata tunani , d’aukar wayar tayi ta duba sak’o ne aka turo mata sai da babu number bare suna , bud’ewa tayi taga ance _Barr Hafiza ina yi miki barka da shigowa rayuwa ta, ki tabbatar next target dina a cikin unguwar Ku zanyi shi koma a kanki zamu gani ko zaki kare y’an matan unguwar ko zaki kare kanki, (Bad man_.)
Gaban ta ya fad’i ganin abinda aka rubuta , nan da nan jikin ta d’auki rawa a ranta tace “to ya akayi yasan dani? Ya akayi yasan nufina akan sa? Na shiga uku ni Hafiza yanzu ya zanyi ya akayi sirrin mu yake fita?”
Babu mai bata wannan amsar dole ta mik’e ta fita tsakar gida .
Abie da Umme da Hanifa suna zaune suka ga ta fito cikin sanyin jiki ta zauna tayi tagumi , Cikin kulawa Abbie yace “Hafiza lafiya na gani haka ?”
Hafiza tace “Abbie wannan mutumin dana ke son kamawa shine yayi min message yanzu duk ya San abinda nake yi”
Hanifa tace “ya akayi yasan dake balle abinda kike shiryawa?”
Hafiza tace “nima ban sani ba wallahi, kuma yace wai wacce zai d’auke nan gaba a cikin unguwar nan take zata iya yuwa wai nice”
Zaro ido Hanifa tayi tace “Mun shiga uku to yanzu ya zaka kiyi Aunty Hafiza?”
Abbie yace “babu bantun wani shiga uku babu abinda ya isa yayi miki Wanda Allah bai tsara hakan ba , Dan haka Ku kwantar da hankalin ku kar kusa damuwa a ranku kunji”
Sai a lokacin hankalin Hafiza ya kwanta tayi ajiyar zuciya , bata k’ara cewa komai ba har kowa ha bar wajan .
Washe gari
“Ummee sauri nake fa zan tafi makaranta na kusa makara” Hanifa take fad’a tana fita daga gidan a sauri
Jin Fitar ta yasa Hafiza sauri fitowa tana kwalla mata kira amma ina Hanifa tayi nisa , Ummee tace “me zata yi miki kike kiran ta?”
Hafiza tace “Ummee yau bana so wata budurwa a unguwar nan ta fita in ba haka ba suna cikin hatsari”
Cikin damuwa Ummee tace “Kar ki damu zata dawo lafiya”
Hafiza tace “Allah yasa” ta fad’a tana komawa d’aki cikin sanyin jiki.
Gab da azahar Hanifa ta taso daga makaranta , rana ta bud’e sosai babu kowa a hanya hakan yasa take sauri kamar zata tashi sama , bata yi aune ba taji an toshe mata hanci da wani abu nan da nan ta daina gani sosai , daukar ta aka yi cak suka saka ta a mota dasu d’au hanya a guje.
__________📖* Ko da suka k’arasa gidan d’aukar ta suka yi cak suka shiga da ita parlourn gidan , har zuwa lokacin Hanifa tana gani kad’an-kad’an , cikin bedroom suka shigar da ita suka fito .
+
Tashi yayi ya shiga d’akin bayan ya rife fuskar sa da wani kyalle , zama yayi kusa da ita tare da mirgino ta tayi ruf da ciki , abinda ya gani ne ya sashi mik’ewa cikin b’acin rai ya fita daga d’akin tare da kiran yaran sa cikin tsawa , da gudu suka k’araso ya kalle su yace ,
“Waye ya Baku damar d’auko min yarinyar da kuka San taba period ehhh? An fad’a kuma kowa kazami ne irin Ku , tu kafin raina ya b’aci kuje Ku d’auke ta Ku mayar da ita inda kuka d’auko ta ” yana gama fad’ar hakan ya juya ya bar parlourn .
D’akin ya koma ya d’auko wannan bakin abun kamar yadda ya saba yayi mata Zane a hannu amma ita nata zanen ba irin na sauran bane , yana gamawa ya bar d’akin, su kuma suka d’auke ta suka bar gidan .
******
“Ummee wai lafiya har yanzu Hanifa bata dawo ba?”.
Ummee tace “ni kaina abin ya bani mamaki Dan bata tab’a kaiwa yanzu bata dawo ba “.
Nan da nan idon Hafiza ya ciki da kwallah tace “Allah yasa ba d’auke ta akayi ba” ta fad’a hawaye na Zuba daga idon ta.
Gaban Ummee ya fad’i amma sai ta daure tace “Bama haka bane insha Allah tana cikin koshin lafiya”.
Hafiza ta bud’e baki zata yi magana suka jiyo muryar Abbie yana fad’in”kuna ina kuzo Ku shinfid’a tabarma a kwantar da ita”.
Cikin saurin Ummee ta d’au tabarma ta fita dab Hafiza har tayi gaba , ganin Hanifa an shigo ta ita a hannu yasa Hafiza fashewa da kuka tana fad’in” shikenan ya cuci rayuwar y’ar uwa ta, Allah ya isa bamu yafe ba”.
Shinfid’a tabarma Ummee tayi cikin sanyin jiki , Abbie ya kwantar da ita ya zame mata hijjabi yana shafa kanta .
Hafiza ta tace “Abbie asibiti ya kamata mu tafi tunda kaga ko numfashi bata yi sosai”.
Ummee tace ” Haka ne gwara mu tafi asibitin ” ta fad’a tana saka hijjabin dake kan igiya.
Abbie mik’ewa yayi yace “bara na samo mai adaidaita sahu” ya fad’a yana fita daga gidan cikin sauri.
Babu jimawa ya dawo aka d’auki Hanifa aka nufi asibiti.
Bayan an duba ta akayi mata allurar bacci , Dr Amin ya kalli Hafiza yace “Alhamdulilah baiyi mata komai ba kuma da alama jinin ta mai k’arfi ne dan allurar bata saka ta bacci sosai ba , Allah ya bata lafiya” ya fad’a tana fita daga d’akin.
Ajiyar zuciya Hafiza tayi ta kalli hannun Hanifa , da sauri ta mik’e ta k’arasa ta rik’e hannun tana dubawa , cikin tsoro tace “Allah bazai ba ikon k’ara d’aukar ta ba azzalumi”.
Kira ne ya shigo wayar Hafiza koda ta duba sai taga sunan Hafiz d’in akan screen , d’auka tayi ta fita bakin k’ofar d’akin , tace ” Assalamu alaikum my love”.
Murmushi yayi cike da soyayya yace “Wa’alaiki salam habbity gani nazo gidan nagan a rufe kina ina?”.
Hafiza tace ” bana gida muna asibiti Hanifa ce bata da lafiya “.
” Subahanallahi wanne asibitin ne?”
Tace “Na cikin gari” yace “OK ganin zuwa insha Allah”. Ya fad’a yana kashe wayar.
Babu jimawa ya iso ya kira ta tazo suka shiga d’akin tare , cike da kunya yake gaida Ummee da Abbie , cikin fara’a suka amsa Dan har ga Allah Hafiz ya kwanta musu a rai .
Fita yayi daga d’akin Hafiza ta bi bayan sa basu wuce ko ina ba sai office d’in Dr Amin , da sallama suka shiga bayan sun gaisa Hafiza tace ” Dr wannan shine Hafiz shine Wanda zan aure Dan haka duk abinda nake yi akan Bad man shima ya sani”.
Murmushi Dr yayi suka k’ara gaisawa da Hafiz , Hafiza tace “duk duniya babu Wanda yasan abinda nake shiryawa sai ku , Dan haka ya kuke ganin zamu b’ullowa lamarin?”.
Kafin wani yayi magana Abbie ya leko yace ” Dr kazo ta farka “.
Tare suka mik’e suka koma d’akin , Hafiza ta zauna kusa da ita tace ” sannu Hanifa babu abinda yake damun ki?”
D’aga kai tayi alamun babu , Hafiza tace “ki kwantar da hankalin ki babu abinda ya same ki , Hanifa babu wata alama da kika gani da zata sa mu gano wannan mutumin?”.
Hanifa tayi ajiyar zuciya tace ” Na gani”.
Ciki da zumud’i Hafiza tace “mai kika gani?”
Hanifa tace “irin rubutun da yake hannu na shima akwai a hannun sa , naso na gano fuskar sa amma da yake bana gani sosai banga komai ba”.
Hafiza tace ” good ko yanzu mun fara samun shaida , bayan shifa ?”
Hanifa tace “ban kuma ganin komai ba sai dai fari ne sosai”.
Hafiza tace ” Masha Allah mun fara samun shaida akan wannan mutumin”.
Ganin ta samu lafiya yasa Dr ya bata sallama suka tafu , Hafiz ne ya d’auke su a motar sa ya kaisu har gida , basu wani jima da komawa gida ba sak’on text ya shigo wayar ta.
Cikin sauri ta d’auki wayar ta fara karanta sak’on kamar haka _Barr Hafiza an fad’a miki kowa irin kine Mara wayo , sarai nasan Hanifa k’anwar kice domin babu abinda ban sani ba akan ki malama hafiza, Allah ya taimaki k’anwar ki period take lokacin da aka kawo ta Dan yanzu labari yasha bam-bam amma fa hakan ba yana nufi na kyale ta ba Sam ban Hak’ura ba, ko da yake naga har shaida ta baki a kaina, ni fari ne kuma inada rubutu a hannu baki San ina sane nasa aka Zuba mata powder da taba da k’arfi ba sabida na sauk’ak’a miki nemana yasa nayi hakan , kuma abinda nake so na samu tunda ta fad’i wani abu daga cikin abinda nake dashi a jiki na , nasan zakiyi mamakin yadda sirrin ki yake fita ko ? To ba abin mamaki bane a ko ina yara na suna nan Dan haka kar ki wani damu , bye ( Bad man)_.
Wata irin zufa ce ta karyowa Hafiza duk da sanyi da ake a gari , itafa wannan Bad man d’in ya fara bata tsoro mutum kamar aljani , a fili tace “to waye yake Fitar min da sirri na ? Yau fa a gaban mutum shida na fad’i wannan maganar , ni ta farko Abbie da Ummee sai Hafiz da Dr da kuma Hanifa, ko a mafarki nasan Abbie bai San wani Bad man ba balle kuma Ummee , to waye Hafiz ko Dr????”.
Nan take zuciyar ta ta bata amsa da Hafizzzzz.
__________📖* Cikin sauri ta d’auki waya ta kira Hafiz yana d’auka tace “Dan Allah kazo gidan mu yanzu akwai maganar da zamuyi dakai”.
+
Jin haka yasa Hafiz tunanin ko ance ya turo iyayen ayi maganar aure aikam ya bata amsa da gashi nan zuwa .
Babu jimawa ya k’araso ya kira ta waya yace gashi ta fito , babu jimawa ta fita ta shinfid’a musu sallaya suka zauna .
Cike da zumud’i Hafiz yace ” gani Allah yasa Abbie ne yace na turo “.
Hafiza tace ” ba Abbie ne yake Neman ka ba nice nake Neman ka, Hafiz ina so ka fad’a min tsakanin ka da Allah Bad man ne ya turo ka lek’en asiri ko kuwa?”.
Cikin rashin fahimta yace “bangane abinda kike nufi ba ko zakiyi min bayani sosai?”.
Hafiza tace ” abinda nake nufi shine , Hafiz da gaske aure na kazo yi ko kuwa turo ka akayi Dan ka dinga kaiwa Bad man sirri na?”.
Zuba mata ido yayi har ta gama magana sannan yace “Hak’ik’a kinyi mutuk’ar bani mamaki Hafiza ban tab’a tunanin ko wani ne yazo yace miki abinda nazo yi kenan zaki amince ba sai gashi da bakin ki kike fad’a , Hafiza meye ribata in nazo a matsayin d’an lek’en asiri? Wacce riba zan samu a cikin abinda kike zargina dashi , a ina nasan wani Bad man ma balle nazo a matsayin yaron sa , ko a mafarki banyi tunanin zaki zarge ni akan wannan abun ba , kinsan yarda nake sonki kuwa? Babu second d’in duniya da zata wuce ba tare Dana tuna kiba , kinsan yadda kika shiga cikin zuciya ta kika samu fada wacce babu wata mace da ta tab’a shiga cikin ta? Hafiza duk duniya in kika cire iyayena babu wacce nake so sama dake amma da yake ke ba sona kike ba shine kike k’ok’arin d’aura min laifin da bansan hawa ba balle sauka, nagode da abinda kika yi min , kuma kin bani mamaki wallahi” .
Tunda ya fara magana Hafiza ta sunkuyar da kai tana sauraran sa cike da nadamar abinda ta aikata , sai yanzu take tunanin to ai tun kafin tasan Hafiz sirrin ta yake fita , d’ago ido tayi shima kuma dai-dai lokacin ya kalle ta ai kuwa suka had’a , cikin sauri ta d’auke kanta dan baza ta iya had’a ido dashi ba , gashi idon nasa ya koma ja kamar ba fari ba.
Cikin sanyin murya tace “Dan Allah Dan Annabi kayi Hak’uri my love, na yanke hukunci ne ba tare Dana yi tunani ba , dan darajar iyayen ka ka yafe min wallahi nayi nadama kaji”.
Hafiz ya kalle ta yace “Hak’uri akan me zan Hak’ura bayan har yanzu abinda kike zargi na dashi bai goge a cikin zuciyar ki ba, wai ni kike zargi Hafiza hmm”.
Nan da nan hawaye suka fara zarya a idon Hafiza , cikin muryar kuka tace ” Dan Allah kayi Hak’uri ka yafe min , na rasa yadda zanyi ne wannan lamari na Bad man ya fara bani tsoro sabida duk abinda muka tattauna d’azu sai da yayo min text ya fad’a min , gashi da private number yake turowa balle nayi amfani da number nabi diddigin layin , kuma yace a ko ina yaran sa suna nan ni na fara tsorata dashi”.
Ajiyar zuciya Hafiz yayi yace “wai ma kina da tabbacin shine yake miki text d’in? , zata iya kasancewa ma wani ne yake son tsora taki “.
Hafiza tace ” shine domin ranar da yace zai sace wata a unguwar mu kuma hakan ta faru , sannan message din yau ma ya kuma tabbatar min dashi ne”.
STORY CONTINUES BELOW
Hafiz yace “haka ne kuma , addu’a zaki dinga yi Allah ya baki ikon gano shi kisa su Ummee ma su taya ki da Addu’a insha Allah komai zai zo da sauki”.
Tace ” Haka ne , amma fa ina zargin Dr yanzu “.
Hafiz yace ” oh my god , wai meye yake damun ki ne haka? , kin matan ta zato zunibi koda ya kasance gaskiya ba”.
Tace “duk da haka ya kamata naje na samu Dr d’in”.
Hafiz yace ” kar kije ki bari sai zuwa wani lokaci sabida kar kije kiji kunya”.
Ajiyar zuciya tayi tace “yadda kace haka za’a yi , yauwa d’azu jiya Abbie yace na sanar da kai ka turo magabatan ka sun gama binkicen da zasuyi “.
Wani sanyi Hafiz yaji tun daga d’an yatsa sa har kwakwalwar sa , cikin fara’a yace ” Alhamdulilah Allah ya kusa cika min burina na mallakar ki a matsayin mata , yau d’in nan zan sanar da uncle gobe suzo “.
Hafiza tayi murmushi tace ” Allah ya kaimu d’an gidan uncle, naga alama kana ji da uncle d’in nan.”
Murmushi yayi yace “ke kuwa dole naji dashi bani da kowa fa da zan kalla nace iyayena ne sai shi , kinga kuwa dole naji dashi.”
Cikin Tausayi Hafiza tace “Abban ka ya rasu ne?”.
Hafiz yace ” Eh Abba na ya rasu yau kusan shekara goma kenan , Mama kuwa tun a haihuwar k’anwata Janan Allah yayi Mata rasuwa , yanzu a hannun uncle muke gabad’aya daman mu uku Mama ta haifa Yaya ta Aunty Salima sai ni sai Janan, sai Wanda muke uba d’aya su kuma su biyu ne namiji d’aya mace d’aya amma duk na girme su”.
Hafiza tace “Allah ya jik’an su Mama yasa aljanna ce makomar su”.
Murmushi jin dad’i yayi yace ” Ameen nagode sosai”.
Hafiza tace “yaushe zaka kawo min Janan d’in?”
Hafiz yace “sai bikin mu ya kusa tunda kinga tana kano ba’a nan take ba”.
Hafiza tace ” to Allah ya kaimu lokacin “.
Yace ” Ammen Matata”.
Da haka suka yi sallama ya tafi.
Washe gari da safe iyayen Hafiz suka baiyana a gidan su Hafiza , daman ta sanar da Ummee tun Dare aka yi musu Abinci mai rai da lafiya.
Cikin fara’a Abbie ya barbe su suka zauna , D’aya daga cikin bak’in ya kalli Abbie fuskar sa d’auke da fara’a yace “Ni sunana Hamisu Ni k’anine ga magarayi mahaifin Alhaji Ali” ya nuna na gafen sa yace wannan kuma k’anin mahaifiyar sa ne Alhaji Muktar , d’ayan kuma abokina nane Wato Malam Badamasi”.
Cike da da farin ciki Abbie yace “sannun Ku da zuwa”.
Alhaji Hamisu wato uncle yace ” Hak’ika Alhaji Kabir naji dad’i had’a zuri’a da kai Dan munyi binkice sosai akan yarinyar ka an tabbatar mana da tarbiyyar da ilimin addini irin nata, tunda Hafiz ya same ni da maganar aure nayi farin ciki sosai dan da babu yadda ba’a yi yayi aure ba sai yace lokaci baiyi ba , wannan dalili ne yasa muka tawo da kud’in aure ina babu damuwa kuma muna so a tsayar da bikin wata hud’u masu zuwa”.
Abbie yayi gyaran murya yace “to Alhamdulilah hak’ik’a nima nayi farin cikin had’uwa da Ku , muma kuma binciken mu ya tabbatar mana da Hafiz a gidan tarbiyya ya fito hakan yasa na tuntub’i yarinya tace tana sonsa nace tace masa ya turo , maganar biki nan da wata hud’u kuma ni ina Neman alfarma a barshi nan da wata biyar in Allah ya kaimu”.
Alhaji Hamisu yayi murmushi yace ” ai babu damuwa wallahi duk abinda ka yanke shine dai-dai , da hud’un da biyar d’in duk d’aya ne ” .
Mik’awa Abbie kud’i uncle yayi yace “wannan shine kud’in aure , wannan kuma shine na saka rana” ya fad’a yana mik’awa Abbie wani kud’in.
Murmushi Abbie yace “Masha Allah ya nuna mana lokacin , Bismillah ga abinci ” Abbie ya fad’a yana matso da abincin kusa dasu.
Tashi Abbie yayi ya bar musu parlourn ya koma cikin gida.
D’akin Ummee ya shiga ya tarar da ita a zaune tana gyara kaya ita da Hanifa , nan Abbie ya kwashe komai ya sanar da ita , kud’in ya mik’a mata yace “budu d’ari uku suka kawo da kud’in aure Dana sa rana kuma kamar yadda muka yi dake bikin nan da wata biyar ne”.
Ihu Hanifa suka jiyo a tana fad’in ” wayyo dad’i za’a yi biki a gidan nan , Aunty Hafiza ta kusa zama amarya”.
Abbie ya kalle ta yace “kema Allah ya kawo miki naki na aurar dake”.
Ummee tace ” Ameen , in yaso ta k’arasa karatun a gidan mijin taba”.
Mik’ewa Hanifa tayi ta bar d’akin a gudu Dan ita kunya ma suka bata.
Hafiza na d’aki tana waya da Hafiz Hanifa ta shigo a guje tana wak’a , Hafiza tayi tsaki tace “lafiyar ki kuwa?”.
Hanifa tace ” Aunty Hafiza amaryar Yaya Hafiz, bara kiji na baki labari an tsayar da auran Ku nan da wata biyar masu zuwa”.
Muryar Hafiz ta jiyo a wayar yana hamdala yace “Hanifa da gaske kike?”.
Mik’a mata wayar Hafiza tayi tace ” sai ki bashi labari”.
Karb’a tayi tace “wallahi Yaya Hafiz da gaske yanzu naji Abbie yana sanar da Ummee”.
Cikin farin ciki Hafiz yace “kai naji dad’in wannan labarin dole ne na baki kyauta in nazo, bawa Hafiza wayar.”
Mik’a mata wayar tayi ta fita daga d’akin.
Bayan bak’in sun gama cin Abinci suka yiwa Abbie sallama suka wuce Kano cike da farin ciki.
Bayan kwana biyu
Hafiza na zaune a d’aki tana tunanin tunda suka yi maganar nan da Hafiz bata kuma jin labarin Bad man ba , kenan dai Dr ne d’an lek’en asiri tunda gashi baiyi mata text ya sanar da ita abinda suka tattauna da Hafiz ba , Dr d’in ne kenan , tana cikin tunani wayar ta ta hara ringing tana dubawa taga sunan Dr , d’auka tayi tare da yin sallama , bayan sun gaisa yake sanar da ita sabon case d’in Bad man ga yarinyar ma a kwance .
Kashe wayar tayi ta d’auki hijjabi ta fito tsakar gida , kallon sama tayi ganin yadda garin yayi bak’i da alama ruwa yana gab da sauka , a ranta tace “dole naje wajan yarinyar kodan naji ta samo wata shaida , so nake na gurfanar da Bad man d’in nan kafin bikina”.
Ummee ta lek’o tace ” Hafiza ina zakije a wannan hadarin?”
Hafiza tace “Ummee an samu case na wannan mutumin ne shine nake so na samu yarinyar naji ta samu wata shaida, bara na d’auki lema ” ta fad’a tana shiga d’aki.
Bayan ta fito Ummee tace “Amma Hafiza dole ne zuwa yanzu? Ki bari sai anjima mana.”
Hafiza tace “to Ummee bara na koma ciki”.
Komawa tayi ta zauna a d’aki babu jimawa aka fara ruwa mai k’arfi.
Ba a wani jima ana yi ba ya tsagaita , aikam Hafiza ta mik’e tayi Ummee sallama ta fita daga gidan.
Koda ta isa Asibitin kamar kullum babu abinda yarinyar ta gani sai dai itama da wannan rubutun a hannun ta , cike da takaici Hafiza ta tawo gida , jin garin yayi sanyi iska na kad’awa yasa Hafiza tafiya a k’asa tana tafiya tana tunani .
Tafiya yake a mota a hankali yake binta a baya yana tuk’i yana murmushi har suka isa wajan da ba mutane ko kad’an , fitowa yayi daga motar Dan yau da kansa yake so d’aukar ta , a hankali yake Binta a bayan har ya iso daf da ita.
Cak ta tsaya jin kamar ana binta, juyowar da zata yi taji an fesa mata abu a fuska tayi baya zata fad’i ya rik’o ta ta had’o jikin sa , d’aukar ta yayi ya shiga mota da ita ya fisgi motar da gudun tsiya.
__________📖* Bai tsaya a ko ina ba sai a parking space d’in gidan sa , bai tab’a lokaci ba ya bud’e motar ya fito ya d’auki Hafiza kamar jaririya ya shiga da ita cikin gidan.+
Shigar sa parlourn yasa yaran saurin mik’ewa suna kallan k’asa , kwantar da Hafiza yayi yana murmushi ya kalle su yace ,
“Kun San wace wannan?” Girgiza kai sukayi alamun A’a.
Bad man yayi y’ar dariya yace “Wannan itace sabuwar Barr d’in nan da take son kai Bad man k’ara kotu , tana son kama ni amma kuma ni na kama ta kalle a nan sai yarda nayi da ita” ya fad’a yana murmushi mugunta.
D’aya daga cikin yaran sa yace “Ita d’inwa Oga yanzu fa kalle a kwance a gaban ka kuma wai itace take son kama ka” tare suka saki dariya da sauran yaran.
Alama yayi musu da subar parlourn cikin sauri kuwa suka fita tare da kullo musu k’ofa.
Zama yayi a kan kujerar da ya kwantar da Hafiza yana kallon fuskar ta , hannu yasa ya cire hijjabin dake jikin ta yana cigaba da kallan , d’ago kanta yayi yace “kalle kifa a hannu na a haka kike so ki kama ni ? Hmmm baki San waye ni Dan baki gangancin shiga rayuwa ta ba , amma yau zan tabbatar miki da koni waye ” ya fad’a yana saka bakin sa cikin nata.
Kissing d’inta yake sosai kamar zai cire mata baki , a hankali ya zare bakin sa ya d’auko wayar sa ya shiga camera sannan ya kara bai da bakin sa cikin Mata , d’aga wayar yayi ya d’auke su hoto , sosai hoton yayi kyau ya fito tar duk Wanda yaga pic d’in sai ya gane wace shi kuma daman da glass bak’i a fuskar sa ya d’aura bak’in kyalle bakin sa ne kawai a bud’e, kallan pic d’in yayi ya saki dariya .
Hannun sa yasa a baya ya zuje zip d’in rigar ta a hankali ya zare ta ta dawo daga ita sai breziya , kallan cikin ta yayi tare da yi mata kiss akan cikin ta , hannu yasa zai balle mab’alin bayan ta wayar sa ta fara k’ara, fito da hannun sa yayi tare da Jan tsaki ya d’au wayar yana dubawa .
Ganin mai kiran yasa ya d’auka da sauri , babu jimawa a ajjiye wayar ya shiga bedroom d’in sa ya d’auko bak’ib ruwan nan yayi mata rubutua ciki sannan ya mayar mata da hijjabi ya d’auke ta suka fito , a mota ya sata shima ya shiga yaja motar da sauri.
Inda ya d’auke ta nan ya mayar da ita ya ajjiye ta , dai-dai lokacin da ya shiga mota dai-dai lokacin Hafiza ta bud’e ido , kafin idon ta ya gama washewa tuni motar tayi nisa .
A hankali abinda ya faru ya fara dawo mata , cikin sauri ta mik’e sai tana duba jikin ta  , hawaye suka fara Zuba a daga idon ta tana , dakyar take tafiya har ta k’arasa gida.
A k’ofar gida ta hango Hafiz da Abbie suna faman safa da marwa a wajan ko wanne fuskar sa d’auke da muguwar damuwa , Abbie ne ya fara hango Hafiza tana tawo wa , cikin sauri suka k’arasa inda take Abbie ya rik’e ta ganin yadda jiri yake b’ibar ta , a hankali suka shiga gida aka kwantar da ita .
STORY CONTINUES BELOW
Hafiz ya Zuba mata ido yana kallon ta cike da tausayawa , Abbie ne yace “Hafiz ka kwantar da hankalin ka ai gata an ganta “.
Ajiyar zuciya yayi ya sunkuyar da kai yace ” Abbie bara na koma gida anjima zan dawo kafin lokacin ta dawo dai-dai “.
Suka yi sallama ya juya ya fita.
A hankali ta idon Hafiza ya cigaba da washewa har ta daina jin komai ta dawo normal , mik’ewa tayi da sauri tana kalle-kalle , Ummee ta rik’e ta tace ” sannu kinji”.
Hafiza tace “Ummee Ku fad’a min dan Allah yayi nasara a kaina ko?”.
Ummee ta girgiza Mata kai alamun A’a , Hafiza tace ” tayaya kuka San bai yi min komai ba? Anje asibiti ne?”.
Ummee tace “Hafiza ni mahaifiyar kice ko ba’a je asibiti ba zan iya gane komai da ido na, Dan haka ki kwantar da hankalin kema addu’a ta kare ki kamar yadda ta kare y’ar uwar ki”.
Ajiyar zuciya tayi tace ” Ummee ina Abbie? “.
Tace ” yanzu ya fita yaje masallaci “.
Mik’ewa da zata yi Hanifa ta hango rubutu a cikin ta , Cikin sauri Hanifa tace ” Aunty Hafiza kinga rubutu a cikin ki”.
Kallan Cikin ta tayi idon ta taf da hawaye tace “me aka rubutu bana gani sosai?”.
Hanifa ta matso kusa da ita ta kalli cikin ta ta fara karantawa ” Baki kama ni ba sai gashi ni na kama ki , Allah ya taimake ki an yi min kiran gaggawa da yanzu kin zama cikakkiyar bazawara , amma ni kere na yawo zabo na wayo wata rana za’a kuma had’uwa , na samu number d’in Wanda zaki aura a wayar ki ki kuka da kanki kafin kiga abinda zan turo masa , BAD MAN.”
Hanifa tace “Mun shiga uku me zai turowa Yaya Hafiz ?”.
Cike da k’unar rai Hafiza tace ” nima ban sani ba, koma meye nasan insha Allah Hafiz zai saurare ni , bara naje nayi wanka?” Ta fad’a tana mik’ewa ta shiga d’aki tana share hawaye.
Ummee tayi tagumi tace “Allah ka shiga tsakanin na gari da mugu.”
Bayan sallar i’sha Hafiz ya dawo , bayan ta fito sun zauna Hafiz yace “ya jikin naki ?”.
Hafiza tace ” da sauk’i babu abinda yake damuna daman d’azun ma bacci ne bai gama saki na ba”.
Hafiz cikin damuwa yace “kina so kice bai yi miki komai ba?”.
Sunkuyar da kai tayi tace ” nima ban sani ba gaskiya , amma Ummee tace babu abinda yayi min”.
Ajiyar zuciya yayi yace “Allah ya tsare gaba “.
Tace ” Ameen.”
Hafiz yace “yanzu dai ya shirin bikin mu?”
Ta bud’e baki zata yi magana wayar sa tayi k’ara , d’auko wa yayi ya dub’e message d’in , cike da tsanin b’acin rai yake kallon screen wayar nan da nan idon sa ya juya ya koma ja kamar garwashi .
Ganin yanayin ya sa Hafiza tace “lafiya meye yake faruwa?”.
Mik’a mata wayar yayi ba tare da yace komai ba.
Kallan wayar tayi ta ganta a kwance a d’ago kanta ana kissing d’in bakin ta , fuskar mutumin ta kalla sai dai ko kalar bakin idon sa bata gani ba Dan babu abinda ake gani a fuskar sa .
Nan take wani irin amai ya taso mata aikam ta shiga kwara shi a wajan , saurin mik’ewa yayi ya k’arasa gabanta yana yi mata sannu , ruwan da ta kawo mai ya bata ta kuskure bakin ta , shi kuma ya kira Hanifa a waya tazo ta gyara wajan sannan ta koma ciki.
Kallan shi tayi hawaye na anbaliya a idon ta tace “wallahi kaji na rantse babu abinda na sani ban San yayi hakan ba wallahi ,ka yarda dani Dan Allah”. Ta fad’a fashewa da kuka.
Rasa yadda zaiyi mata yayi kawai sai ya rungume ta yana bubbuga bayan ta alamun rarrashi , a hankali ta dinga sauke ajiyar zuciya , yace ” ki kwantar da hankalin ki in ma yayi hakan ne Dan ya b’ata tsakanin mu to bai isa ba dan ni wallahi ji nayi kin k’ara shiga rai na, kiyi shiru ki bar kuka komai ya wuce , bana so ki fad’awa kowa abinda aka turo min nima kuma babu Wanda zan fad’awa kinji”.
A hankali take d’aga kai tana goge hawaye.
Kallan k’ofa tayi taga ana hasko su sa fitila duk da haske dake wajan , zame jikin ta tayi tace masa “kaga kamar wani yana kallon mu”.
Mik’ewa yayi ya fita daga d’an harabar gidan ya nufi k’ofa , biyo bayan sa tayi itama .
Ai mutumin na ganin sun taso ya bar baki k’ofar da gudu , kafin su k’arasa har ya shiga mota ya bar wajan a guje.
*Tofa waye kuma Wannan*🤔
* Cike da tsoro Hafiza tace “Waye Wannan yake mana lab’e?”.
+
Ajiyar zuciya Hafiz yayi yace ” Allah ne yasan waye , inma wani abun ne Allah ya mayar masa dashi kansa.”
Hafiza tace “Ameen ya Allah.”
Komawa suka ciki babu jimawa yayi mata sallama ya tafi gida.
*****
Zaune yake a mota yana kallon Hafiz ya fito daga gidan su Hafiz , kwafa yayi yace “bazan tab’a yarda Wannan banzan ya auri Barr ba sai na San yarda zanyi na lalata aure , nine na dace da ita ba wani ba ” Cikin fushi yaja motar ya bar unguwar da gudu.
*****
Bayan wasu watanni
Kwanci tashi babu wuya a wajan Allah yau gashi bikin Hafiza saura sati biyu , shirye-shirye biki ake sosai , an kawo laife akwati Bakwai cif ko wacce cike take da kaya .
Har zuwa lokacin Hafiza ta kasa samun wata hujja da zata nuna mata waye ma Bad man balle ta saran kama shi , amma duk da haka tana kan bakar ta nason kama shi.
B’angaren ango yace baya buk’atar wasu dinner ko wani abu , haka itama Hafiza tace ana d’aura aure ayi walima ya wadatar ba sai anyi wani Abu ba.
Rana bata k’arya
Ranar juma’a misalin k’arfe biyu na rana aka d’aura auren Hafiz da Hafiza cikin sadaki naira budu sittin , tunda Hafiza taji an d’aura aure jikin ta yayi sanyi ta rasa abinda yake damun ta .
Tana zaune a d’aki taci kwalliyya tayi kyau kana ganin ta kaga amarya , text ne ya shigo wayar ta ta d’auka ta duba , _Amarya sai gashi har kinyi aure ba tare da kin cika burin ki ba , duk da dai nasan har yanzu baki Hak’ura ba nima ba Hak’ura nayi ba zan cigaba da yin abinda zai sa ki cigaba da nema na , Byeee_.
Ajiyar zuciya tayi tace “zan cigaba da Neman ka Bad man saina wulak’anta ka .”
Hanifa ce ta shigo tana fad’in “Aunty Hafiza ki fito an shirya wajan waliman”.
Babu jimawa aka fara walima aka taro malamai aka yi wa’azi mai ratsa jiki , amarya ta dinga kuka kamar ranta zai fita , a haka aka gama walima aka d’auki amarya bayan tasha nasihoyi aka nufi gidan ta .
Aunty Salima da Janan suna gidan amarya suna jiran isowar su , Ai Janan naji k’arar motar ta fita da gudu tana murnar ganin Antyn ta.
Masha Allah gidan Hafiza ko mak’iyin ta ya gani sai ya burge shi balle masoyin ta .
Duk inda tayi Janan na mak’ale da Hafiza har akace su fito zasu tafi Kano , babu yarda suka iya dole suka fito suka d’au hanyar Madinan Nigeria 😝.
Bayan kowa ya watse gida ya rage Hafiza ita kad’ai , babu jimawa Ango Hafiz ya shigo yana baza k’amshi , zama yayi a kusa da Hafiza yana kallon ta yana murmushi yace “Amarya ta lafiya kike kuka?”.
Shiru tayi masa kamar taji shi ba , murmushi yayi yace ” yau kuma shariya ake ji, to shikenan tashi kiyi alwala muyi sallah mu godewa ubangijin”.
Ba musu ta mik’e ta shiga band’akin dake cikin d’akin tayi alwala ta fito , ko da ta fito bata ganshi a d’akin ba da alama d’aya d’akin ya shiga.
Babu jimawa ya dawo hannun sa d’auke da sallaya ya shinfid’a musu suka tayar, bayan sun idar ya kama goshin ta yayi mata addu’a sannan yayi mata y’an tambayoyi tana bashi amsa .
Gabatar mata yayi da Abinci, duk da yuwar da take ji cokali biyu tayi tace ta k’oshi.
Hararar ta yayi yace “ban gane kin k’oshi ba me kika ci?”.
Ta yamitse fuska tace ” babu komai kawai dai na k’oshin ne.”
Ciko cokali yayi ya kai baki ta yace “oya bud’e kici Abinci”.
Bud’ewa tayi ya zuba mata , haka ya dinga ciyar da ita sai ya tabbatar ta k’oshi sannan ya kyale ta.
Tashi yayi ya fita daga d’akin ganin ya fita yasa Hafiza tayi ajiyar zuciya ta mik’e ta rage kayan jikin ta ta kwanta.
Ko da Hafiza ya fita d’aki ya koma ya chanja kaya zuwa na bacci sannan ya dawo d’akin , ganin har ta kwanta yasa yayi murmushi ya nufi kan gadon tare da kashe wutar d’akin.
Runtse ido Hafiza tayi har ya kwanta a bayan ta tayi kamar tayi bacci , kallan taga tayi taga mutum a tsaye da alama Neman hanyar da zai shiga yake.
Cikin tsoro Hafiza ta mik’e tace ” kaga wani a bakin taga”.
Mik’ewa yayi shima yana kallon wajan cike da mamaki , a hankali ya bud’e k’ofar,  ganin yana niyar fita tayi saurin dirowa tace “kar ki fita dan Allah nasan bazai wuce Aiken Bad man ba ka dawo kar suyi maka wani Abu .” ta fad’a tana k’amk’ame shi sosai.
D’ago kanta yayi yace “shikenan bara na lek’a ta tagar naga waye”.
Kulle k’ofar yayi ya dawo jikin tagar ya d’an lek’a a hankali , karaf idon Hafiza akan Hannun Mutumin , kallan Azufar hannun sa take tana tunanin a ina tasan Wannan azurfar ? Cigaba tayi da kallon hannun sa tana tunanin inda tasan irin azurfar.
Zaro ido tayi sakamakon tuno azurfar da tayi , a hankali tace ” Dr Amin”.!!!
__________📖* Tace “A’a amma dai ya…” Kafin ta k’arasa ya katse da fad’in “Amma me? Haba Hafiza yanzu akace ki fita ke sai fita? Yaufa kwanan ki d’aya tak a gidan miji , ni bance zan hana ki aikin ki ba za ki cigaba amma ba cikin kwanakin nan ba , kuma dole ki goge number Wannan Dr kuma ki gaya masa kar ya k’ara kiran ki inso in an sami information d’in ya fad’awa wata nurse d’in tayi miki waya ta gaya miki koni na fad’a miki.”
+
Itadai tayi shiru bata ce komai ba sai da ya gama sannan ta d’ago tace “kayi Hak’uri daman ai nima bance zan fita ba kuma zan goge number d’in nasa kamar yadda kace .”
Murmushi yayi yace “Ko kefa , zuwa lokaci in Allah ya kaimu sai ki cigaba da zuwa wajan aikin ki , ki cigaba da Neman Wanda yafi Bad man ma”.
Itama dariya tayi tace ” tab aka samu Wanda yafi wancan mutumin ai da ko wacce mace ta daina fita.”
Bayan sallar azahar Hanifa ta zo suka sha hira bayan la’asar ta koma gida.
Bayan kwana biyu
Hafiza tana kwance a parlour ta kwantar da kanta a kan cinyar Hafiz tana danna waya.
Hafiz yace “Hafizty”. Tace ” Na’am sweet H”.
Yace “Zuwa next week insha zamu je Kano kiga y’an Uwana da dangina.”
Cikin farin ciki Hafiza tace “Kai amma naji dad’i daman inason zuwa Kano.”
Murmushi yayi yace “bake kad’ai ba duk d’an Nigeria burin sa yaje Kano , ke kinsan Kano kuwa ? “.
Tab’e baki tayi tace ” nasan dai bata kai Kaduna komai ba”.
Dariya yayi yace “Lallai ma ai idan kika shiga Kano gani zaki yi Kd k’auye ce sosai yarinya , ta Dabo tumbin giwa koda me kazo an fika, kema fa yanzu cewa kikayi kina son zuwa.”
Haushi Hafiza taji tace “Eh koda mai kazo an fikan amma kazo garin mu aiki, mai yasa baka bud’e company acan ba sai nan?”.
Dariya yayi sosai yace ” Haba yarinya ke har kya fad’awa Kano kasuwan ci karfa ki manta sune Center of commerce sune cibiyar kasuwan cin gabad’aya , kawai dai taimakawa garin Ku nayi na bud’e company “.
Hafiza tace ” Oho dai kome zaka ce kaci albarkacin garin , kuma ka daina cemin yarinya ” ta fad’a a shagwab’e.
Zaro ido yayi yace “to tsohuwa kike so nace miki kome?”.
Tace ” nidai bana so ka dinga ce min yarinya bayan kama da kad’an ka girme ni.”
Yace ” to shikenan aunty tsohuwa yi Hak’uri mantawa nayi nace miki yarinya. ” ya fad’a yana k’unshe dariya.
STORY CONTINUES BELOW
Mik’ewa tayi ta zauna tana dire-diren k’afa tana cewa “Allah ni ba tsohuwa bace Kaine tsoho mai shekaru talatin da wani abun ni kuwa fa”.
Rik’e baki yayi yace ” ikon Allah kin cika rigima , to shikenan an koma yarinyar. “
Zata yi magana wayar ta ta fara k’ara d’auka tayi ganin sunan nurse d’in da suke magana Yanzu .
Sallama tayi bayan sun gaisa take sanar da ita new case d’in Bad man , godiya tayi mata ta kashe wayar tana kallon Hafiz da ya zuba Mata manyan idon sa yana kallon ta.
Kallan sa tayi tace “An k’ara samun sabon case d’in nan wallahi”.
Tab’e baki yayi yace ” To sai me?”.
Rik’e hannun sa tayi tace “Dan Allah ka barni naje kawai tambaya zan yiwa yarinyar na dawo kaji.”
Shiru yayi yana nazari akai , can kuma sai yace “to naji bara a idar da sallah isha sai muje na kaiki”.
Murmushi tayi tace ” tam Allah ya kaimu lokacin. “
Yace “kin tayar da hankalin ki gabad’aya akan Wannan mutumin , Allah ya kaimu ranar da zaki kama shi oh ranar ai har rawa nasan sai kinyi.”
Dariya tayi tace “Abinda yafi rawa ma wallahi zanyi , har azumi sai nayi na godiya ga Allah”.
Kallan ta yayi ya d’age gira yace ” ko?”.
Tace “wallahi , Allah dai ya nuna mana ranar.”
Mik’ewa yana cewa “Ameen , bara na shiga masallaci kafin na dawo ki shirya”.
Tace ” To a dawo Lafiya.”
Bayan an idar da sallah ya shigo a parlour ya zauna yana jiran fitowar ta , babu jimawa ta fito sanye da dogon hijjabi hannun ta rik’e da waya  tace , “Yauwa na shirya”.
Hannu ya mik’a mata alamun tazo , ba musu ta mik’a masa nata ya jawo ta ta fad’a jikin sa ya zuba mata ido yace ” Wa ya baki damar saka Jan baki in zaki fita.?”
Girgiza kai tayi alamun babu kowa .
D’ora bakin sa yayi kan nata a hankali yake lashe Jan bakin , sai da yakai minti biyar yana Abu d’aya sannan ya sake ta ya jingina da bango yana ajiyar zuciya ido a lumshe.
Kallon sa tayi tana K’ara ganin kyaun da Allah ya bashi , cikin sa’a kuwa suka had’a ido , cikin sauri ta d’auke kai Dan baza ta iya jure ganin idon sa ba gani take yana wani ruwa kamar hawaye.
Mik’ewa yayi yace “tunda kin gama kallon nawa tashi mu tafi , yarinya anga d’an kyakykyawa” ya fad’a yana fita yana dariya.
Koda suka isa asibitin Hafiza bata nemi Dr ba nurse d’in ta kira ta gaya mata inda aka kwantar da yarinyar ta shiga.
Kamar kullum babu wata shaida da yarinyar ta gani sai Wannan singing d’in , sallama tayi musu ta fito cikin sanyin jiki da bak’in cikin rashin samun komai.
Har ta gota office d’in Dr Amin sai kuma ta dawo ganin k’ofa a bud’e amma an saki labule , tsayawa tayi jin abinda yake cewa da alama waya yake.
Dr Amin yace “Wallahi oga yanzu na ganta ta shigo asibitin nan , ok haka za’a yi , na gane kar ka damu za’a yi yadda kace , ai bata da yawo sosai komai zai tafi dai-dai.”
Ganin yana k’ok’arib fitowa yasa tayi saurin barin wajan , mota ta koma ta shiga suka d’au hanya.
Tunda ta shiga tayi shiru tana tunanin to dawa Dr Amin yake waya? Wacece wacce yake magana a kanta?.
Hafiz yace “Lafiya Hafizty na ganki wani iri?.”
Dai-dai lokacin suka k’arya kwana layin babu kowa Dan ko cikakken haske babu , zata yi magana kenan suka ga mota tasha gaban su wasu mutane sun fito suna rik’e da bindiga a hannun su.
Cike da tsoro Hafiza take kallan mutanen jikin ta na rawa ta k’ank’ame Hafiz tana salati .
Ganin mutanen basu motsa ba yasa Hafiz d’ago ta daga jikin sa yace ” Kar ki damu babu abinda zai faru damu , Allah na tare damu , ki zauna a mota bara na fita naje wajan su” ya fad’a yana k’ok’arin bud’e mota.
Rik’e shi tayi tana hawaye tana girgiza masa kai , tsabar tsoro da fargaba maganar ma taki fita .
Hafiz yace “ki sake ni gwara naje in ba haka ba suka k’araso zasu kashe mu gabad’aya gwara naje ke ki zauna” bai tsaya jin abinda zata ce ba ya bud’e motar ya fita.
Kamar jira suke kuwa yana fitowa suka saki harbi ji kake tasssssss.
Dai-dai lokacin Hafiza ta kwalla k’ara .
 Saurin sunkuya Hafiz yayi zuciyar sa na bugawa da sauri , ganin basu same shi ba sai suka fara tukaro su cikin tafiyar tak’ama .
+
Hafiza kuwa jikin ta banda rawa babu abinda yake yi , hawaye kuwa ya Wanke mata fuska , k’arar wayar Hafiz ce ta katse mata tunani .
Cikin sauri ta d’auka bata duba waye ba ta k’ara a kunne , daga can aka ce ” Hafiz kana gani nagi a k’ofar gidan ka?”.
Cikin kuka Hafiza ta fara magana muryar ta na rawa tace “Kuzo Ku taimake mu zasu kashe mu.”
Cikin tashin hankali ASP Yahya yace “Su waye ? Kuna ina ? Nutsu kiyi
min bayani.”
Ganin sun zo daf da motar yasa Hafiza tace “Suna nan bayan gidan idan ta tawo ta d’aya kwa…..” Bata k’arasa ba aka bud’e motar aka wanka mata Marin da yasa ta gigicewa bakin ta ya fashe.
Karb’ar wayar suka yi suka doka ta da k’asa , d’aya yasa hannu ya jawo ta ya fito da ita daga cikin motar.
Fito da Hafiz suka yi suna wata irin dariya kamar mahaukata .
Fizge hannun sa yayi da k’arfin sa yaje ya cincike hannun Hafixa , ya kalle su yace “duk abinda zaku yi ya tsaya iya kaina kar Ku kuskura Ku k’ara gangancin tab’a min mata in ba haka ba wallahi sai nayi shari’a da mutum.”
Dariya suka yi d’aya daga cikin su yace “mu daman ba wajan ka muka zo ba wajan matar muka zo , an bamu umarnin mu tafi da ita kuma babu abinda zamu fasa ” ya kalli na gefen sa yace “wai me kuke jira ne?”.
Da sauri suka nufi inda Hafiza take , hango Y’an sanda d’aya gada cikin su yayi ai bai tsaya yi musu magana ba ya jefar da bindigar ya arce a guje.
Ganin ya gudu yasa na kusa dashi ma guduwa ko waige bai yi ba , ogan nasu ya yunk’ura zai gudu yaji bindiga a kansa .
Cak ya tsaya ya d’aga hannun sama , Asp Yahya ya da yara sa ” Ku tafi da su tunda saura sun gudu”.
STORY CONTINUES BELOW
Tasa keyar Ogan akayi da yaro guda d’aya saka tafi dasu police station.
Durk’ushewa Hafiza tayi a wajan tana kuka , tsugunawa Hafiz yayi gaban ta yace “to meye na kukan muka ? Godiya za muyiwa Allah da ya kub’utar damu , tashi ki shiga” ya fad’a yana mikar da ita tsaye.
Asp ya kalli Hafiz yace ” Sannu Hafiz Allah ya kiyaye gaba , amma su waye wad’anan mutanen?”.
Hafiz yace “Allah ne masani ni kaina bansan daga ina suke ba , ya akayi kasan muna nan?.”
Nan ya kwashe yadda suka yi da Hafiza ya fad’a masa , yace ” Kar Ku damu tunda yanzu suna hannun mu zamu san yadda yasa su Wannan aiki , yanzu zan huce can zuwa da safe kuma kuzo station d’in dan ayi komai a gaban Ku”.
Godiya Hafiz yayi masa sosai suka shiga mota suka tafi.
Tunda suka tafi Hafiza take kuka har suka k’arasa gida bata ui shiru ba.
A parlour ta zauna tana kuka sosai , zama yayi kusa da ita ya kwantar da kanta a jikin sa ya zare hijjabin dake jikin ta yana bubbuga bayan ta a hankali.
Yace “to kukan ai ya isa haka ki godewa Allah tunda babu abinda ya faru damu , gashi har anyi nasarar kama su Wannan ai abin farin ciki ne , kiyi Hak’uri ki daina Wannan kukan mana” ya fad’a yana goge Mata hawaye.
Ajiyar zuciya take yi cikin rawar murya tace “waye Wannan yake neman rayuwa ta ne ? Daban an kira kaba da yanzu sun kashe mu , Hafiz na tsorata sosai ban tab’a tashin hankali irin Wannan ba , me suke nema damu ? Gashi kaima laifi na yana Neman shafar ka .”
Hafiz yace “Kada ki damu komai yazo k’arshe da izinin Allah , ki cigaba da addu’a, sannan bana so ki fad’a kowa abinda ya faru yau sabida kar hankalin su Umme ya tashi tunda komai ya wuce “.
Hafiza tace ” To bazan fad’a insha Allah, amma fa ni akwai Wanda nake zargi.”
Hafiz yace “wa kike zargi?”.
Tace ” Dr Amin , ranar da aka shigo gidan nan daman nace maka naga zobe irin nasa, bayan nan kuma hand chief d’in da ka d’auko again shima irin sa yake amfani dashi, sannan d’azu a asibiti naji yana waya ya ace ayi abinda yace yau ya ga yarinyar ta shigo asibiti yanzu komai zai tafi dai-dai , shiyasa kaga jiki na yayi sanyi a mota tunanin maganar Dana ji yana yi nake , tabbas shi nake zargi ko nace shine ma.”
Hafiz yace “Haka ne tabbas kowa yaji haka zaiyi tunanin shi d’in ne, amma kar muyi saurin yanke hukunci zuwa gobe ai zamu ji koma waye tunda yaran suna hannun mu , yanzu dai tashi muje mu kwanta dare yayi.”
Bata yi musu ba ta tashi suka shiga d’aki.
Washe gari
*POLICE STATION*
“Wallahi tallahi kunji na rantse in Baku fad’a min Wanda yasa Ku Wannan aikin ba sai na b’alla muku k’afa” wani d’an sanda ya fad’a hannun sa rik’e da sanda.
Ogan yace “Sai dai fa kuyi duk abinda zaku yi amma wallahi baza mu fad’a ba”.
D’an sandan yace ” OK tunda Kaine mara kunyar mai bakin magana kai zan abtar , bara kaga” ya fad’a ya d’auko fulaya ya kama d’an yatsan sa ya matse da fulayar .
Ganin azabar da ake yiwa babban sai d’anyan ya tsorata jikin sa ya fara rawa .
Su Hafiz kuwa koda suka iso office din Asp Yahya suka shiga , bayan sun gaisa yayi musu jajen abinda ya faru , sannan suka nufi inda yaran suke.
Suna shiga aka fara k’amewa ana sarawa Yahya , ya kalle su yace “Wai har yanzu basu yi bayani ba?”.
D’an sanda yace ” eh sir har yanzu sunki su fad’a mana Wanda yasa su Wannan aiki tun jiya ake Abu d’aya. “
STORY CONTINUES BELOW
Yahya yace “Ku cigaba da dukan su har sai sun fad’a , Hafiz ga waje can mu zauna” ya fad’a suna zama akan wani banci.
Jin ance a cigaba da yi musu azaba yasa ya d’auko wani k’aton dutse ya saka hannun daya yaron a k’asan dutsen ya zauna akai .
Sai ku hannun ya bada sauti k’assss , wata k’ara ya saki yana ihu yana fad’in “Dan Allah kuyi Hak’uri zan fad’a, zan fad’a wallahi.”
Jin haka yasa au Hafiz suka taso suka dawo wajan , d’aga hannun nasa yayi yace “uhum ina jinka.”
Kallan babban yayi yaga yana sakar masa harara , amma babu yadda ya isa dole ya fad’a Dan gaske bai shirya mutuwa yanzu ba.
Cikin muryar wahala yace “bamu muka saka kanmu Wannan aikin ba samu akayi”
D’an sandan yace “waye ya saku?”.
K’ara kallon babban yayi ganin ya d’auke kai yasa yace ” Wani ne wai shi DR Amin, yazo ya same mu akan muje mu d’auko masa Matar sannan kuma Ku kashe mijin , a cewar sa wai shi kad’ai ya dace ya aure ta ba wani ba, na fad’a muku to Dan Allah Ku barni na tafi gida.”
Hafiza ta kalli Hafiz tace “kaji magana ta ko ? Daman nasan za’a Rina”.
Asp Yahya yace ” kuna ina ?”.
Cikin sauri sauran y’an sandan suka fito suna k’amewa , yace “yanzu ba sai anjima ba duk inda Dr Amin yake aje a tawo dashi.”
Sara masa suka yi suka amsa da “an gama sir ” suka fita.
Zama Hafiza tayi hawaye suka fara zarya a idon ta ta rik’e hannun Hafiz tace “tabbas to yana da masaniya akan Wannan mutumin Dana ke nema .”
Hafiz yace “a Dan yarda da maganar ki ba amma a Yanzu na yarda zai iya yin komai ma.”
Wajan minti ashirin sai ga Dra an shigo dashi , kwace komai nasa akayi aka saka shi a cell.
Kallan yaran sa yayi a cikin cell d’in yace “meyasa Baku fad’a min an samu matsala ba ? Meyasa kuka ce musu nine na saku ? Zamu had’u zaku San ni kuka yiwa haka.”
Ogan yaran sa yace “kodai mu muce zamu had’u ba , an fad’a maka azabar da muka sha a hannun nan kwalawan zamu kyale Kane ? Akan ka zamu wuce wallahi zaka gani.”
Shigowar Yahya yasa suka yi shiru basu k’arasa ba , kallan sa yayi yace “Malam Amin ko zaka iya fad’a mana meye dalilin ka na son cutar da bayin Allah?.”
Ba tare da wani shakka ko tsoro ba Dr Amin yace “tunda nake a duniya ban tab’a jin son wata mace ba sai Barrister , ban furta mata ba har tayi aure to gaskiya bazan iya jure ganin ta da wani bani ba , hakan yasa na shiga gidan nan a ranar da ka kaita sai dai kash rashin hanyar da zan shiga d’akin ya hanani aiwatar da abinda nayi niya , shine kawai yau Dana ga ta fito tazo asibiti sai nayi amfani da damar nace suje su kashe mijin ta sannan su d’auko min ita.”
Yahya yace “kana ganin da ka kashe mata miji kai bazaa kashe ka ba? Meye ribar ka idan kayi hakan , ko da yake bai dame ni ba zamu mik’a k’arar nan kotu domin alk’ali ya yanke muku hukunci dai-dai daku.”
Hafiza tace “nifa ina zargin Dr da yasan Bad man Dana ke nema , ko kuma shi Bad man d’in.”
Murmushi Dr yayi yace “Duk iskanci na ban kai nan ba , ni bansan wani Bad man ba , ban tab’a ganin sa ba balle har na zama yaron sa , iya abinda na aikata gashi nan na fad’a amma ni Sam bani da wata masaniya akan Bad man.”
Tsaki Hafiza tayi tace “k’arya ne sai anyi bincike za’a gane gaskiyar.”
Dr yace “ai daman ba burina ki yarda ba , tunda nidai nasan bansan wani Bad man ba kije can ki samo shi.”
Janye ta Hafiz yayi yace “kiyi shiru ki rabu dashi.”
STORY CONTINUES BELOW
Hafiz yace “Yahya nagode da taimakon ka gare mu , duk abinda kaga ya dace ayi domin mu zuwa gobe insha Allah zamu wuce Kano .”
Musabaha suka yi sannan suka fito.
Gidan Umme suka wuce suka yi musu sallama Dan Kano zasu tafi.
Tunda suka koma gida Hafiza tayi tagumi tana tunanin to in ba Dr bane Bad man to waye ? Ita fa kanta ya k’ulle ta rasa mafita .
Har Hafiz ya zauna kusa da ita bata sani ba , yace “Hafizty wai me yake damun kine?”.
Tace ” bani da buri a rayuwa ta da wa wuce na kama wannan mutumi , sai gashi Wanda nake zargin ma bashi da masa niya akan komai , duk ranar Dana kama Bad man zanyi farin ciki sosai , Allah ya nuna min wannan rana.”
Hafiz yace “ta Yaya kika gane bashi da masaniya?”.
Tace ” ni lawyer ce inda karatun fahimtar yanayin d’an Adam , tabbas bashi da masaniya akan komai Sweet H.”
Hafiz yace “To Allah ya baiyana miki yadda kike nema.”
Tace “Ameen ya Allah , buri na kenan a rayuwa.”
Shirya kayan su suka fara yi kafin dare sun gama had’a komai.
Hafiza na kitchen tana Girki tana raira y’ar wak’ar _Hafiz gani nazo bani in baka zab’i kai na zab’a muyo rayuwa_.💃🏻
Shigowar Hafiz kenan daga masallaci ya dawo ya sautin muryar ta kitchen tana wake shi .
Bakin k’ofar kitchen d’in ya tsaya ya hard’e hannu sa a kirji yana kallon ta cike da so .
Bata zata ba taji an rungume ta ta baya ya kwantar da kansa a kafad’ar ta yace “Wannan wak’a haka Hafizty kaii yau an wak’e ni.”
Sunkuyar da kanta tayi Dan ita kunyar sa ma take ji , rik’e baki yayi yace “toh sabon salo susa da shebir wai har yanzu kunyar nan na nan daman ? Ai na zata na cire wallahi , amma no case yau zan yi mata kaca-kaca kar ki damu.”
Hafiza ta turo baki gaba tace “To ka cikani na shigaba da aiki na.”
Yace “kina so na kyale ki kiyi aiki?”.
Tace ” eh mana.”
Yace “To sai kinyi min kiss.”
Zaro ido tayi tace “rufa min asiri ai indai ka ganni a lahira kaini akayi.”
Shima zaro manyan idon sa yayi yace “Ai daman kowa ma kaishi aka yi, indai baza kiyi ba to kuwa baza kiyi aikin ba” ya fad’a yana k’ara matse ta.
Ganin yak’i ya kyale ta sai tace “to naji amma sai ka rife idon ka.”
Ba musu ya rife idon sa ya juyo yana kallon ta.
Kallon sa tayi tana jin kaunar sa na ratsa ta , a ranta tace “gaskiya Hafiz kyakykyawa ne komai Allah ya hore masa , ji gashin ido kamar ya saka eyelashes.”
Katse mata tunani yayi da fad’in “am waiting for u fa.”
Kujera ta d’auko taka sannan ta rife ido itama tana d’aura bakin ta kan nasa tayi sauri d’auke wa tare da fad’in “shikenan nan dai nayi “.
Bud’e ido yayi yace ” wai me kikayi haka ? Tab ni banji komai ba Dan haka ki k’ara yi in ba haka ba in anjima yarinya hmmm. Ya fad’a ya girgiza kai alamun zamu had’u.
Da sauri tace “to naji bara na kuma d’in.”
Rufe idon sa yayi , ta k’ara yin irin na d’azu tana niyar d’auke wa taji ya kamo lips dinta da sauri , rik’e ta yayi sosai a jikin sa sai yayi mai Isar sa sannan ya kyale ta .
Ya kalle ta da idon sa da suka koma red yace “bashi kika d’auka anjima zaki biya , cigaba da aikin ki bara naje na dawo muyi aikin tare ” ya fad’a yana fita daga kitchen.
Ajiyar zuciya tayi tace “Kaii Hafiz k’arshe ne a love wallahi” ta fad’a tana lumshe ido.
Washe gari da huri suka shirya suka d’au hanyar Kano.
Suna tafiya a mota taji k’arar shigowar text a wayar ta , tana budawa tana private number d’in da ake mata message.
Bud’ewa tayi taga an rubuta _Na kusa baiyana kaina gare ki zaki ganni very soon amma baki isa ki kama ni , zan shiga rayuwar ki cikin kwanakin nan saina hana ki kwanciyar hankali, ki dawo daga Kano ina nan ina jiran ki. (BAD MAN)_
Gaban ta ya fad’i hankalin yayi bala’in tashi tsoro da fargaba suka shige ta .
Ya akayi yasan ta tafi Kano? Bayan babu Wanda yasan maganar daga y’an gidan su sai Asp Yahya sai Dr da kuma yaran sa tunda a gabansa Hafiz ya fad’a , to waye ya fad’a masa.????
Pretty kwantar da hankalin ki bad man dai ya kusa zuwa gidan Ku Ku gaisa🤣🤣🤣🤣😂😂😂

Hafiz ya katse mata tunani da fad’in “Lafiyar kuwa ?”.

+

Bata yi magana ta mik’a masa wayar , bai karb’a yace ” rik’e kinsan bana so ina tuk’i ina danna waya kawai ki fad’a min abinda faru.”

Tace “Message akayi min aka ce min wai sai an takura rayuwa ta , kuma yana gab da baiyana kansa a gare ni amma wai ko ya baiyana ban isa na kama shi ba .”

Tsaki yayi yace “wai Wannan mutumin kike nufi? Shi har ya isa da zaice baza ki iya kama shi ba , ya baiyana kan nasa daman haka muke so ai , nidai buri na ki cire damuwa a ranki .”

Shiru tayi bata kuma magana ba .

Gab da azahar suka shiga garin Kano mai tarin albarka , tunda suka shigo Hafiza take faman baza ido tana santin garin kana ganin ta kaga y’ar k’auyen garin  Kd.😜

Basu wuce ko ina ba sai Sakkoto road , a bakin wani tank’amemen gida suka tsaya Hafiz ya fara danna horn .

Da yake an ba’a San da zuwan su ba sai mai gadi ya lek’o ai yana arba da Hafiz ya bud’e k’ofar yana washe baki , ko da suka yi parking Hafiz suka gaisa da mai gadin sannan ya Bud’ewa Hafiza ta fito ya rik’e hannu suka shiga cikin gidan.

Tun a parlour ya fara k’wallawa Janan kira , jin muryar Yayan ta yasa ta fito da sauri tana murnar zuwan sa.

Turus ganin Hafiza tsaye tana sakar mata murmushi ai sa ta fasa zuwa wajan Hafiz ta rungume Hafiza tana kwallawa Mama kira .

Mama ta fito tana fad’in “Haba Janan Wannan kira haka , lafiya?”.

Tace ” Mama Yaya Hafiz ne yazo tare da Aunty Hafiza. “

Sai kuwa Mama ta washe baki tace “Kai sannun ku da zuwa , kunsha hanya Ku zauna mana .”

Zama Hafiza tayi tana sunkuyar da kai , Mama ta harari Hafiz tace “meyasa baka fad’a min zaku zo ba ai Dana shiryawa y’ata Abinci .”

Dariya yayi yace “mamaki muke son Baku shiyasa.”

Janan tace “Ai kuwa kun bamu mamakin , kash gashi Aunty Salima bata nan jiya suka yi tafiya da mijin ta , amma nasan zata ji haushi wallahi. “

Rik’e baki Hafiz yayi yace “kice na shiga uku da mita , Mama ina Uncle d’in?”.

Mama tace ” Yana masallaci amma yanzu zaka ganshi.”

Hafiz yace “muma bara muyi sallah sai muzo asha hira ” ya fad’a yana rik’e hannun Hafiza alamun ta Mik’e.

Bige hannun sa Mama tayi tace “kai kam Hafiz baka da ta ido wallahi, to babu inda zata kaje ka dawo , D’iya ta tashi muje ciki” ta fad’a tana Jan hannun Hafiza suka shiga d’aki.

Bayan an idar da sallah Hafiz da Uncle tare suka shigo suna hira , a parlour suka yada zango uncle yace “Wai ina Hafizan ne?”.

Mama da ta fito yanzu tace ” Yanzu zata fito ” ta fad’a tana shiga kitchen.

STORY CONTINUES BELOW

Hafiza ta fito tana sunkuyar da kai ta zauna a k’asa tace “Barka da Rana”.

Murmushi Uncle yayi yace ” Haba tashi ki koma kan kujera , sai kace wata bak’uwa maza tashi.”

Mik’ewa tayi ta zauna a kan kujera tana wasa da zoben hannun ta , Uncle yace “Ya aikin naki?”.

Tace ” Alhamdulilah “.

Uncle yace ” Masha Allah , ina fatan dai lafiya kuke zaune ko?”.

D’agowa tayi ta kalli Hafiz aikuwa suka had’a ido ya kashe mata ido d’aya yana d’aga mata gira , sunkuyar kai tayi tace “Babu komai “.

Uncle yace ” Masha Allah haka ake so.”

Hafiz ya kalli uncle yace “Uncle wai kuwa su Mu’azzam suna zuwa kuwa?”.

Uncle yace ” A’a basa zuwa , ai idan kaga Mu’azzam a gidan nan to wata babbar matsalar ce ta kawo shi , to gwara ma Humaira ta kan zo wajan Janan amma shi da Mahaifiyar sa ko lek’e , kuma ko da wasa uwar taji labarin Humaira tazo gidan nan ta shiga uku inta dinga zagin ta wani lokacin ma har da duka , da bakin ta Humairan ta fad’a min dan ita tana son y’an uwan ta.”

Ajiyar zuciya Hafiz yayi yace “Na rasa abinda nayiwa Aunty gabad’aya bata k’auna ta , kuma ni a matsayin uwa na d’auke ta ba kishiyar uwa ba , da ace Umma tana raye yadda zan yi mata biyayya haka zan yiwa Aunty , ta hana y’an Uwana zuwa inda nake kofa zuwa gaishe ta nayi banda harara da tsaki babu abinda take min , ni inason y’an uwa na kuma zamu je gidan dan Hafiza ta sansu su Santa.”

Uncle yace “Hakan yayi kyau Allah ya baka ladan zumunci.”

Hafiz yace “Ameen”.

Haka aka dinga hira ana wasa ana dariya .

Bayan sallar i’sha an gama cin Abinci kowa ya mik’e ya tafi d’akin sa aka bar Hafiza da Hafiz a zaune .

Mik’ewa Hafiza tayi cikin Tsokana tace “to nima dai zan kwanta sai da safe ” ta fad’a tana niyar barin wajan.

Rik’e hannun ta yayi yace “ok bara muje mu kwanta a d’akin da zaki kwana d’in” ya fad’a yana mik’ewa.

Zaro ido tayi tace  “ka Yanzu in akace kazo mu kwana a d’akin Janan sai ka kwana?”.

D’aga kafad’a yayi yace ” to sai me ba wajan Matata nazo ba.”

Hafiza tace “to kuwa baza ayi Wannan abin kunyar dani ba.”

Matsowa yayi kusa da ita sosai har tana jin saukar numfashin sa , ya zuba mata ido yana yi mata wani irin kallo cikin wata irin murya yace “Meye Dan na kwana kusa Matata ? Ni bana jin kunyar kowa a ko ina zan nuna ke Matata ce .”

Yanayin da yayi maganar da kuma yadda yake kallon ta yasa jikin Hafiza yayi sanyi tana jin wani Abu nayi mata yawo a jikin ta , kasa magana tayi ta kau da kai Dan bata so su had’a ido .

Murmushi yayi ganin yanayin da ta shiga sai rik’e hannun ta yana matsawa a hankali yace “Baki ce komai ba kinyi shiru”.

Nan ma tayi shiru bata amsa ba , bakin sa yakai satin kunnen ta yace ” Kina wani basarwa bayan kema kinyi kewar mijin ki .” bai tsaya ta bashi amsa ba ya ja hannun ta suka  d’akin sa.

Washe gari a gajiye Hafiza ta tashi dan ba k’aramar wahala tasha ba a hannun Hafiz , ganin yana wanka yasa ta gyara parlourn sannan tayi wanka ta fito ta nufi d’akin Mama.

Suna zaune an gama karyawa ana hira ana dariya Hafiza ta shigo.

Har k’asa ta durk’usa ta gaida Mama da Uncle sannan ta zauna tana sunkuyar da kai.

Janan ta kalli Hafiza tayi murmushi tace “Aunty na an tashi lafiya?.”

Hafiza tayi murmushi Dan har cikin zuciyar ta tana k’aunar Janan tace “lafiya lau “.

STORY CONTINUES BELOW

Kafin Janan tayi magana Hafiz ya shigo parlourn , kallo d’aya Hafiza tayi masa ta d’auke kai Dan yadda taji gaban ta na fad’uwa tsabar kyaun da taga yayi.

Janan ta saki baki tana kallon sa tace ” Yaya nah Wannan kyau haka kamar zaka je gasar kyauwawa na duniya gabad’aya. “

Murmushi yayi yace “kin cika surutu Janan , ya na ganki a gida ina makarantar?.”

Janan tace “ai mun sami Hutu Dan da Baku zo ba mana da cikin satin nan zan sauka a Kaduna.”

Hafiza yace “yayi kyau.”

Janan ta shagwab’e fuska tace “Dan Allah Yaya ka dawo nan da zama ina so na dinga ganin ka kusa dani Dan Allah ka dawo nan.”

Kallan ta yayi yaji tausayin ta har cikin rainsa amma sabida ya nunawa Uncle da Mama kara sai yace “haba Janan to anan d’in me zai ciki? Ga Abban ki ga Maman ki to meye abin damuwa kuma? Kedai kawai yau shagwab’ar ce ta tashi.”

Uncle yace “duk da haka dai da zaka dawo nan d’in sai yafi , ko ba’a gidan nan ka zauna ba sai ka sami gida daga cikin gidajen ka ka zauna muma muna so mu ganka kusa da mu ba iya Janan ba kawai.”

Murmushi Hafiz yayi yace “To Uncle za’a duba a gani.”

Mama tace “ai gwara a duba d’in”.

Hafiz yace ” Mama wai ni ina su Fadil ne badai har Yanzu bai samu Hutu ba ?”.

Mama tace “Hmm kaima dai ka fad’a Hafiz har yanzu yace basu samu Hutu ba kasan karatun likitanci akwai wahala shiyasa ba kasafai suke yin Hutu ba.”

Janan tace “Allah sarki Yaya Fadil yana can England ana karatu , nayi kewar sa sosai wallahi ji nake kamar na tashi na bishi.”

Uncle yace “ko zaki yi tsuntsuwa ki bishi?.”

Gabad’aya parlourn aka sa dariya.

Mama tace “Hafiza baki ci komai bafa kike zaune , haba Hafiza bak’unta zaki yi mana a gidan nan tashi ki had’a abinda zaki ci.”

Hafiz ya shagwab’e fuska yace ” Nifa Mama?. “

Tab’e baki tayi tace “ai na daina yi da kai tunda na samu d’iya .”

Akayi dariya gabad’aya .

Bayan sun gama cin Abinci Hafiz ya kalli Hafiza yace “idan kin gama ki same ni a mota.”

Ya kalli Mama yace “Mama gidan Aunty Zamu je .”

Mama tace “ai hakan yana da kyau gwara kuje d’in.”

Uncle ya Mike yace “to nima dai na wuce wajan Sana’a ta” ya fad’a yana fita daga parlourn.

Janan tace “Yaya Dan Allah nazo na raka Ku ? Kaga gidan babu kowa saura mu kad’ai .”

Kafin yayi magana Hafiza tace “d’auko mayafin ki muje.”

Ai kam da sauri ta mik’e tayi d’aki tana murna.

Shi kuwa Hafiz mota ya shiga yana jiran fitowar su .

Tare suka fito Hafiza ta bud’e gaba ta shiga Janan kuma ta shiga baya.

Baice komai ba suka fara tafiya sai sautin karatun alkur’ani da yake tashi a motar , ta mudubi ya kalli Janan da take ta washe baki Dan yasan farin ciki take sun fita tare dashi .

Murmushi shima yayi yana jin k’aunar kanwar tasa har zuciyar sa .

Janan ta katse masa tunani da fad’in “Aunty Hafiza wai kwana nawa zaku yi?”.

Hafiza tace ” Kwana biyar munci d’aya yanzu saura hud’u. “

B’ata rai Janan tayi tace “Haba Aunty ina laifin wata d’aya.”

STORY CONTINUES BELOW

Hafiza tayi dariya tace “lallai ma Janan wata fa kika ce.”

Janan tace “eh mana , Yaya nah Dan Allah ku bari sai kunyi wata d’aya sai Ku tafi.”

Banza yayi mata bai kula ta ba , nan take ta tsuke bakin ta dan tasan hali .

Bata k’ara magana ba har suka k’arasa gidan da zasu je.

Sai a sannan Hafiz yayi magana yace “Janan duk abinda zasu ce miki kar ki tanka musu kiyi musu shiru.”

Janan tace “to “.

Bud’e motar suka yi suka shiga cikin gidan.

Da sallama suka shiga parlourn.

Wata hamshak’iyar mata ce a zaune a parlourn dak’yar ta amsa sallamar tasu.

Tunda taga Janan da Hafiz ta b’ata rai kamar taga mutuwar ta , Hafiza tace ” Barka da rana “.

Wani banzan kallo tayiwa Hafiza sannan tace ” barkan ki.”

Hafiz ya kalle ta yace “Aunty mun same Ku lafiya?”.

Cikin masifa tace ” da baka same mu lafiya ba zaka ganni a zaune anan ? Nifa bana son shishshigi a cikin lamura na.”

Janan kuwa daman ita Tsoro Auntyn take bata sai tayi shiru bata ce komai ba.

Humaira ta fito da gudu tana fad’in “oyoyo Yaya Hafiz da Janan “.

Wata banzar harara Aunty tayiwa Janan amma tayi mata banza kamar bata ganta ba Dan ita tana son y’an uwanta.

Kusa da Janan ta zauna tace ” Sis kwana biyu.”

Janan tayi murmushi tace “kedai bari sis exams ta sani a gaba amma yanzu na gama har munyi Hutu.”

Humaira ta tace “nifa daman na daina kula Yaya Hafiz , baya nema na gabad’aya ya manta dani.”

Murmushi Hafiz yayi yace “haba kin tab’a ganin inda Yaya ya manta da k’anwar sa ? Ban manta dake ba kawai dai aiki ne yayi min yawa.”

Murmushi Humaira tayi tace “kuma fa haka ne big bro shiyasa nake ji da kai.”

Ta kalli Janna tana nuna Hafiza tace “Aunty Hafiza ko?.”

Janan tayi dariya tace “Ashe dai zaki gane ta.”

Wani tsale tayi taje ta rungume Hafiza tana fad’in “kai masha Allah gaskiya Yaya Hafiz ka iya aure Wannan zankad’ed’iyar mata haka , Aunty Hafiza sannu da zuwa .”

Y’ar dariya Hafiza tayi tace “yauwa Humaira mun same Ku lafiya?”.

Tace ” Lafiya lau wallahi bara na kawo muku ruwa.”

Ai tana juyowa taji saukar mari a fuskar ta , cike da mamaki Humaira ta kalli Aunty tace “Aunty lafiya kika mare ni?.”

Aunty tace “ban sani ba, da yake y’ar iska ce bara mutunci wacce bata San ciwon kanta ba shine zaki dinga kula wad’annan gadon tsiyar , bara kiji daga yau na kuma ganin kin kula d’aya daga cikin su sai na yi miki tsinanne duka , ko uwar su Aminatu ce zata dawo daga lahira Yanzu bata isa na kula taba balle kuma yaran ta , banza shashasha Mu’azzam ne kawai yake Goya min baya amma ke badan nasan ke y’ata bace cewa zanyi ke jinin tsiya ce wallahi , Ku kuma bara kuji daga yau kar na k’ara ganin k’afar Ku a cikin gidan nan tunda ba da kud’in Aminatu dana Ali na gina shi ba , daga yau sai yau kar wacce ta kuma tako k’afar ta nan gidan”.

Cikin fushi Hafiz ya mik’e yace “Dan ina yi miki biyayya a matsayin ki na kishiyar uwata ba hakan yana nufin tsoron ki nake ji ba , ke badan ina ganin idon Humaira ba da ke har kin isa kizo kina zagin iyaye na , akan iyaye na babu abinda bazan iya yi ba zan cire kallan mahaifiyar da nake miki naci miki mutunci in yaso daga baya na dawo dashi , ki kula ki kuma shiga hankalin wallahi, kuzo mu tafi” ya fad’a ya fita daga parlourn.

Bayan sa suka bi duk jikin sa a sanyaye , suna shiga motar yaja ta da gudun tsiya ya bar unguwar.

Tunda suka shiga babu Wanda yake yiwa wani magana har suka k’arasa gida.

Ko kula su baiyi ba ya bud’e motar yayi cikin gida , parlourn Mama suka shiga ita da Janan .

Mama ta kalli su tace ” daga ganin fuskar ku Maimuna tayi abinda ta saba , kai wannan mata wane irin tsana take yiwa mahaifiyar Ku haka ? Matar da take cikin kabari amma da ita take gaba ni na rasa wannan Abu wallahi. “

Janan tace “ke dai Bari Mama zagin yau yafi na ko yaushe Dan yau har sunan Umma da Abba ta ambata a cikin maganganun ta , ran Yaya Hafiz ya b’aci sosai Dan tunda muka tawo bai kula kowa daga cikin mu ba.”

Mama ta kalli Hafiza tace “Kinga fa irin kishiyar uwar da Allah ya bawa su Hafiz , Yanzu dai ki tashi kije ki bashi Hak’uri ki kwantar masa sa hankali.”

Hafiza tace “to” ta mik’e ta nufi d’akin sa.

A zaune ta ganshi ya jinginar da kansa jikin kujera ya rufe ido , a hankali ta k’arasa ta zauna a kusa dashi ta rik’e hannayen sa duka biyu tace “Dan Allah kar kasa damuwa a cikin ranka ka kwantar da hankalin ka tunda Allah yaga niyar ka kuma zai baka lada , Dan Allah ka cire damuwa a ranka.”

Bud’e ido yayi da suka koma ja yace “Zan iya jure komai a rayuwa ta amma banda zagin iyaye na , duk mutuncin ka da nake gani indai zaka bud’e baki ka zagi iyaye na to wallahi bazan kyale ka ba .”

Hafiza tace “Shiyasa nace kayi Hak’uri ka cire komai a ranka in ba haka ba zaka jawowa kanka wani ciwon , Dan Allah kar ka rik’e wannan a cikin zuciyar ka.”

Shiru yayi bai kuma cewa komai ba har akayi kiran sallah ya mik’e ya nufi masallaci.

Da daddare suka zaga dangin mahaifiyar sa , sosai yaga kauna ana nan nan dashi , Hafiza kuwa kamar a cinye ta sabida murnar ganin ta , hakan sai ya Wanke wancan b’acin ran da yake tare dashi.

Bayan kwana uku

Hafiza taji dad’in zama a gidan Uncle Dan sosai ake nuna mata kauna .

Yau suka tashi da shirin komawa garin Kaduna Dan ana tayiwa Hafiz waya akan yana da aiki sosai a company.

Bayna sun gama suka fito Janan ta ruk’unk’ume Hafiz tana kuka , ba k’aramin Tausayi ta bashi ba , ganin irin kukan da take sai uncle yace “kiyi shiru kinji Janan zuwa wani satin nayi miki alk’awarin zuwa Kaduna mu zauna har hutun ki ya k’are , sai mu zauna a gidan mu na can ki kwantar da hankalin.”

Sosai tayi farin ciki dajin wannan labari ta dinga murna , Sallama suka yi Hafiza ji take kamar kar ta rabu da Janan haka suka yi sallama suka d’au hanyar Kd.

Gab da Magariba suka shiga garin Kaduna , koda suka k’arasa  mai gadi suka yi horn ya bud’e musu suka shiga cikin gidan .

Washe gari.

K’arar wayar tace ta tashe ta daga bacci , mik’a hannu tayi ta d’au wayar ganin message ne gaban ta ya fad’i Dan tasan ba alkairi bane .

_idan kina son gani na kizo unguwar rimi layi na ashirin da biyar gida mai lamba goma , ammafa kika sake kika fad’awa wani wallahi sai na kashe k’anwar ki Yanzu nake so kizo ba wai sai anjima ba , na baki nan da minti ashirin.(Bad Man)_

Cikin sauri ta mik’e ta saka hijjabi ta fita daga gidan.

Adaidaita sahu ta d’auka ta nufi inda yayi mata kwantance gaban ta na fad’uwa.

Koda suka k’arasa k’ofar gidan mai gadin ya kalle ta yace “Oga yace a fad’a miki kinyi sake lokacin da ya baki ya wuce Dan haka zaki ita komawa” yana gama fad’a mata haka ya juya ya koma wajan zaman sa.

Cikin sanyin jiki ta hau mota ta koma gida.

Tana bud’e k’ofar parlourn taga Hafiz a tsaye a parlour da alama ita yake nema .

Kafin tayi magana ya katse ta cikin tsawa yace “ina kika je da sassafen nan? Wa kika tambaya da zaki fita ? Me kika fita yi?”.

* Jikin ta banda rawa babu abinda yake , sai yanzu take dana sanin rashin fad’a masa.+

Durk’ushewa tayi a wajan zata yi magana yayi saurin katse ta da fad’in “Bana son wata magana kawai ki fad’a min ina kika je.?”

Fashewa tayi da kuka tace “D’azu ina bacci akayi min text akace nazo unguwar rimi zanga Bad man , kuma na sake na fad’awa wani sai an kashe Hanifa , na rasa yadda zan yine shiyasa naje kawai Dan Allah kayi Hak’uri ni daga yau ma na fita daga Wannan case d’in na gaji” ta fad’a tana k’ara fashewa da kuka .

Jikin sa yayi sanyi a hankali ya tako inda take ya mik’ar da ita tsaye yace ” Shikenan daina kuka , amma da kin sani kin sanar dani da wani Abu ya faru dake fa? Daga yau in irin haka ta faru kafin ki yanke hukunci ki sanar dani , Yanzu to kin ganshi d’in?”.

Girgiza kai tayi tace “Ban ganshi ba lokacin Dana k’arasa sai akace wai time d’in da ya bani ya wuce .”

Yace “Shikenan ya wuce , amma baza ki bar case d’in nan ba ki cigaba Allah yana tare dake.”

Tace “to , bara na had’a break fast” ta fad’a tana shiga kitchen.

Cike da Tausayi Hafiz ya bita da kallo yana raya wani Abu a ransa.

Bayan Sati Uku.

Hafiza ta shigo gidan da sallama , yana zaune a kan kujera yace “har kin dawo daga gidan Ummeen?”.

Tace ” Eh na dawo , Ashe jiya kaje shine baka fad’a min ba , Abbie ya fad’a min irin Alkairin da kake musu Nagode sosai Allah ya bar mu tare.”

D’agowa yayi yace “Dan na yiwa iyaye na Abu sai kinyi min godiya Dan shishshigi , to daga yau bana so kar ki k’ara.”

Murmushi tayi tace “To insha Allah bazan k’ara ba.”

Yace “Kwana biyu case d’in mutumin ki shiru.”

Tace “kaima dai ka fad’a , idan anaso aga farin ciki na a duniya bai wuce ace yau gashi na kama shi ba , zanyi murna sosai.”

Hafiz yace “Allah ya kaimu time d’in, bara naje office ana jira na.”

Tace “To sweet H a dawo lafiya, ka kular min da kanka.”

Murmushi yayi yayi mata kiss a goshi ya juya ya fita daga gidan.

Hafiza na zaune tana danna waya tana karanta sabon novel d’in da Gaskiya writers suka fara , cike da nishad’i take karantawa dan ba k’ara min dad’i littafin yake yi ba.

K’arar Abu taji kamar an bugi gate , da sauri ta mik’e ta saka hijjabi ta fita .

Cak ta tsaya ganin wasu mutane fuskar su a rufe sun ritsa mai gadi da bindiga , jikin ta ya fara rawa da sauri ta juya zata koma taji ance,

“Kin d’aga k’afar ki zan fasa miki Kai.”

Cak ta tsaya jikin ta na rawa hawaye na zuba daga idon ta .

STORY CONTINUES BELOW

K’arasawa wajan ta mutumin yayi yace “bake mai taurin kai ba kin nace sai kin San waye Bad man , to shikenan ki cigaba yace a fad’a miki Yanzu aka fara wasan ” bindiga ya d’auko ya d’aura Mata a goshi yana dariyar mugunta.

Had’e rai yayi kuma ya kalle ta yace “Kinsan Wannan hoton da yayi miki lokacin da ya sace ki ? To yace a fad’a miki zai watsa shi a media sai ya b’ata miki suna” yana gama fad’ar haka yayiwa yaran alama da su bar gidan .

Cikin sauri kowa suka bar gidan.

Kasa motsawa Hafiza tayi a wajan kawai sai durk’ushe a wajan ta saki kuka mai ban Tausayi.

Wannan yace irin rayuwa ce ? Shikenan mai laifi bazai bari a kama shi ba? Tunda haka suka nima na Hak’ura na fita daga harkar su , na Hak’ura. Hafiza ce take magana ita kad’ai tana girgiza kai .

Tana zaune a wajan motar Hafiz ta shigo gidan , cike da mamaki yake kallo ta ganin ta zaune a tsakiyar gida.

Fitowa yayi ya nufi inda take , ganin yanayin ta yasa ya gane babu lafiya , kama ta yayi yace “me kike yi anan ? Tashi maza ki koma ciki” ya fad’a yana mik’ar da ita.

Girgiza masa ka ta fara tana fad’in “na Hak’ura na rabu dashi , shima kuma ya fita daga rayuwa ta , Allah yana gani ai nayi iya bakin k’ok’ari na .”

Cikin rashin fahimta Hafiz yace “waye wai ? Meye ya faru?.”

Parlour tayi a guje tana hawaye bata tsaya bashi amsa ba.

Binta yayi a parlour ya ganta tayi tagumi tana girgiza kai kamar mahaukaciya.

Cikin tashin hankali Hafiz yace “ki nutsu ki fad’a min abinda ya faru.”

Cikin rawar murya tayi masa bayanin komai ta d’aura da cewa “Ni  na Hak’ura da kama shin amma da zan samu ko ganin sane nayi nasan waye “.

Rungume ta yayi yana bubbuga bayan ta danshi Tausayi ma take bashi.

Ajiyar zuciya take saukewa a haka har bacci ya d’auke ta.

Kwantar da ita yayi yana kallon fuskar ta cike da Tausayi , a ransa yace ” Nayi miki alk’awari insha Allah komai zai zo k’arshe , zan taya ki Neman Wanda kike nema .”

Haka Hafiza ta kwana ranar kamar Mara lafiya.

Bayan kwana biyu.

Cikin kwanakin Hafiza bata da magana da ya huce ta gano waye Bad man , ta zage sosai tana bincike .

Yau ma kamar kullum tana zaune tana tuno irin singing d’in da yake yiwa yara wayar ta tayi k’ara.

Dubawa tayi taga private number , cike da fargaba ta bud’e message d’in.

_Daga Yanzu har zuwa dare zaki iya zuwa kiga waye Bad man tunda naga duk basirar ki kin kasa ganowa shiyasa na yanke hukuncin baiyana miki kaina , kizo Governor road layi na sha biyar gida mai number 2, idan kika zo yara na zasu shigo dake kar ki damu zaki ganni yau amma baki isa ki kamani ba , kuma zan cigaba da abinda nake yi bawai zan fasa ba._

Tana gama karantawa Hafiz ya sauko da sauri yana duba agogo , cikin sauri Hafiza tace “yauwa kaga” ta fad’a tana mik’a masa wayar.

Karb’a yayi ya karanta yace “Alhamdulilah haka muke so daman , yanzu kinga sauri nake zanje office ki bari sai anjima sai muje tare.”

Girgiza kai Hafiza tayi tace “Dan girman Allah ka barni naje insha Allah babu abinda zai faru , Dan darajar Kabarin iyayen ka ka barni.”

Babu yadda zaiyi dole yace “ok maza tashi ki d’auko hijjabi na sauke , amma Allah ya sani bana son zuwan ki ke kad’ai amma kin nace.”

Bata tsaya sauraran sa ba tayi ciki da sauri , hijjabi ta d’auka ta fito tace “na gama .”

Cikin rashin fara’a yace “muje” Dan baya son Fitar .

A k’ofar gidan da yayi mata kwatance ya sauke ta yace “Nama fasa zuwa office d’in ta muje tare” ya fad’a ya bud’e k’ofar motar.

Tsayar dashi tayi tace “basai ka shiga ba kila in ya ganka ya fasa baiyana kansa , a waya a hannu na duk abinda ya faru zan yi maka flashing ” bata tsaya sauraran sa ba tayi cikin gidan.

Hafiz kuwa zuciyar sa tana fad’a masa kawai yabi bayan ta , hakan yasa ya bud’e motar ya shiga cikin gidan .

Har cikin parlourn aka shigar da Hafiza Wanda suka shiga da ita duka fuskar su a rufe take.

K’arar takalmi taji hakan yasa ta juya Dan gannin waye .

Mik’ewa tayi tayiwa mutumin kallan up and down tace “daman Kaine Bad man d’in ? Mtwsss Ashe ma ba wani abun arzuki ne da kai ba , to……”

Katse ta yayi ta hanyar d’aura hannun sa akan lips dinsa yace “shihhhhhhh .”

Fuskar a rufe hakan yasa maganar sa bafa fito sosai ba yace “bani ne Bad man ba kinga Bad man can” ya fad’a yana nuna mata wata k’ofa.

Zubawa k’ofar ido tayi Dan ganni waye zai b’ullo.

K’afar sa sako kafin ya bud’e labulen fuskar sa ta fito .

Da sauri Hafiza ta mik’e tace “A…………….”

Ku canka😜

__________📖* Da sauri Hafiza ta mik’e tace “A’a Meya kawo ka nan ?.”

+

Murmushi yayi mai sauti yace “Bani kika zo nema ba hala?”.

Cikin rashin fahimta Hafiza tace ” Ni da muka rabu da kai akan ka tafi office ya akayi ka shigo nan?.”

Matowa yayi yazo kusa da ita yace ” Hafizty ba Bad man kika zo nema ba?”.

Tace “Kwarai kuwa kama ka sani ai.”

Y’ar dariya yayi yace “Bud’e idon ki da kyau kiga Bad man tsaye a kusa dake , Hafiza duk wayon Neman Bad man da kike ba wani bani ila ni!!”.

D’an tsaki tayi tace ” Dan Allah ka daina had’a kanka da wancan mutumin , in zuwa kayi ka taimaka min kawai ka fad’a min.”

Murmushi yayi yana nannad’e hannun rigar sa , nan take Wannan bak’in zanen ya baiyana .

Gaban ta ya fad’i amma bata nuna ba Dan ita gani take wasa yake.

Bai kula ta ba ya d’auko wani spray ya fesa a wajan nan take rubutun ya goge kamar babu shi a wajan.

D’ago kai yayi ya kalle ta yace “har yanzu baki yarda ba ko?”.

Itadai tana tsaye ta kasa motsawa , cikin rawar murya tace ” idan kasan wasa kake Dan Allah ka daina”.

Hafiz yace “Hafiza wallahi! Wallahi!! Nine Wanda kike nema , nine dai Bad man kuma nine Hafiz d’inki , kinsan dai bazan yi rantsuwa akan k’arya ba.”

Zuba masa ido tayi Dan duk yadda zata yi Dan taga hawaye ya zubo ta kasa , dafe kai tayi dan ji take kamar zai b’alle .

Cikin rawar murya tace “Hafizz ! ka cuce ni ka gama dani , kayi wasa da hankali na , na zauna da Wanda nake nema ido rife na zauna da mai lefi mazinaci , fasiki mai lalata y’ay’an mutane , ka cuci Hafiz” sai a sannan hawaye masu zafi suka fara zarya a idon ta.

Murmushi yayi ya tsuguna a kusa da ita ya d’age gira d’aya yace “Sauk’ak’a miki nema na fa nayi , Yanzu baga shi kinsan waye Bad man , Haba Hafizty ki daina zubar da hawayen mana” ya fad’a yana k’ok’arin share mata hawaye.

A fusace ta mik’e tace “kar ka kuskura k’azamin hannun ka ya tab’a ni , Kuma bara kaji sai na maka ka a kotu an yanke maka hukunci mai tsauri , Na tsane ka ! Kuma dole ka sake ni ko kana so ko baka so.”

Mik’ewa yayi ya zauna akan kujera ya d’aura k’afa kan d’aya yace ” Tab’a ki Yanzu na fara Hafiza domin ke Matata ce , zancen kotu kuma eh ki kaini amma baki isa kisa a kulle ni ba , baki da hujjar da zaki bawa kotu a kaina, saki kuma wallahi bazan sake ki ba domin kuwa ina mutuk’ar sonki kuma babu Wanda ya isa yace na sake ki”.

STORY CONTINUES BELOW

Fashewa tayi da kuka ta fara tafiya tana girgiza kai , wani jiri ne ya d’auke ta aikam ta fad’i sumammiya.

Cikin tashin hankali Hafiz ya mik’e ya d’auko ruwan sanyi ya shafa mata a fuska , ajiyar zuciya tayi tana bud’e ido a hankali.

Ganin ta jikin Hafiz sai ta fashe da kuka tace “Dan Allah kace min mafarki nayi ba gaskiya bane Dan Allah .”

Tausayi ta bashi sosai amma babu yadda zaiyi dole ya sanar da ita .

Rungume ta yayi yace “Ki daina damun kanki akan abinda na fad’a miki , Hafiza ba mafarki kikayi ba nine dai Hafiz dinki kuma nine Bad man , kuma…..” .

Sakar Marin da yaji a fuskar sa ya hana shi k’arasawa , mik’ewa tayi tana kuka sosai tace ” Allah ya isa tsakani na da kai Hafiz , ka cuci rayuwa ta ka raba ni da farin ciki na , Ashe duk Wannan abubuwan da suke faruwa duk kai ka shirya ? Kaine kake yo min message Kaine ka turo mutane gidan ka suka ritsani da bundiga , Kaine ka sace ni , Kane ka sace k’anwata , duk abinda yake faruwa Ashe duk cikin shirin Kane ,  Me nayi maka ka zab’i ka hukunta ni ta Wannan hanyar ? Na tsane ka Hafiz na tsane ka bazan k’ara zama da kai ba dolen dole ka sake ni kuma wallahi tallahi alk’awarin Dana d’auka sai na cika shi karka ga wai kana matsayin mijina sai na wulak’anta ka kamar yadda kake wulak’anta y’ay’an mutane , mazinaci , fasik’i , mayaudari , kayi wasa da hankali na nima kuma zanyi wasa sa naka , ka jira sammaci” ta fad’a tana juyawa zata bar parlourn.

Duk da yaji zafin maganganun ta amma haka ya d’aure yace “dakata mana Matata , duka Wannan abinda kika lissafa babu Wanda za’a cika shi , ki kaini kotu ban hana ki ba amma baki isa kisa alk’ali ya kama ni ba , saki kuma da kike fad’a bazan sake ki ba domin kina d’auke da cikina a jikin ki , mazinaci , fasiki , mayaudari duk naji kuma na karb’a amma ki fad’a min Yaya sunan matar mazinaci , fasiki , fad’a min Yaya sunan ta ? Tabbas nayi wasa da hankalin ki Wanda koda wanine yazo yace miki nine Wanda kike nema baza ki tab’a yarda ba , duk abinda kika fad’a nine na tsara shi kuma ya tafi dai-dai yadda nake so , nasan Yanzu babu inda zaki wuce sai gidan Ummee ko ? To kije maza ki k’arasa” bai tsaya jin abinda zata ce ba ya juya ya shiga d’akin daya fito.

Da gudu ta fita daga gidan tana kuka sosai k’afar ta ko takalmi babu , koda ta fito bata damu da mutane ba haka take kuka harda shashshek’a .

Mota ta Tara ta hau ta fad’a masa inda zai kaita , tunda ta shiga take kuka tana tuno irin rayuwar da suka yi da Hafiz , Ashe duk yaudara ce ba sonta yake ba , har suka k’arasa bata sani ba sai da mai adaidaita sahun yace ” baiwar Allah mun iso fa.”

Jikin ta na rawa ta fita , hannun ta ta duba babu komai , ganin haka sai mai adaidaitan yace “barshi kawai Allah ya baki lafiya” ya fad’a yana barin wajan Dan shi kallon mahaukaciya yake Mata.

Da gudu ta shiga gida tana kuka , Ummee tana zaune tana ninkin kaya taji shigowar Hafiza , fad’awa kan Ummee tayi tana kuka sosai.

Abbie da yake zaune shida Hanifa cikin tashin hankali yace “Lafiya Hafiza meya faru? Ina Hafiz d’in?.”

Cikin kuka tace “Abbie Hafiz ya cuce ni ya yaudare ni , Ashe daman ba sona yake ba , ni kawai kusa ya sake ni bana sonsa na tsane shi.”

Cikin fargaba Ummee tace “wai meye ya faru ne Hafiza? Me Hafiz d’in yayi miki ?”.

Tace ” Ummee shine Wanda nake nema , shine Wanda ya sace ni ya sace Hanifa yake lalata y’ay’an mutane , Ummee Ashe shine Bad man d’in da nake nema yayi wasa da hankali na ya aure ni na zauna dashi har tsahon wata guda ba tare Dana sani ba , Dole ya sake ni Ummee ” ta fad’a tana k’ara sakin kuka mai cin rai.

Kafin Abbie yayi magana Suka ji sallamar Hafiz tare da shigowa gidan.

Mik’ewa Hafiza tayi da sauri tace “ka Fitar mana daga gida nan ba gidan y’an iska bane , na fad’a maka bazan zauna da kai ba na tsane ka”.

Kallan Ummee Hafiz yayi yace ” kin gani ko Ummee gabad’aya na rasa abinda yake damun ta ,sai wasu maganganu take tun d’azu , nifa gani nake anya Wannan binciken da take bai tab’a mata kwakwalwa ba?”.

Ummee ta rik’e Hazifa tace “Na ga alamun hakan kuwa , gashi duk abinda ka fad’a a waya tazo tana yi , Allah yasa dai ba asiri yayi mata ba.”

Abbie ya dafa kafad’ar Hafiz yace “kar ka damu Hafiz zata dawo dai-dai insha Allah.”

Cikin damuwa sosai Hafiz yace “Allah yasa”.

Wata k’ara Hafiza tayi tace ” Ummee yana wasa da hankalin Ku kamar yadda yayi wasa da nawa , Abbie duk abinda yake fad’a muku k’arya yake ba gaskiya bane.”

Kallan Hanifa da take kuka Abbie yayi yace “jeki maza ki kirawo min Dr Faruk yazo yayi mata allurar bacci.”

Da sauri ya fita Dan itama gani take yayar tata ta fara zarewa.

Fusge- fusge take tana kuka tana fad’a musu Hafiz k’arya yake amma ina su Abbie gani suke Hafiza asiri aka yi mata ko kuma shafar aljanu.

Zuwan Dr yayi mata allura nan da nan bacci ya d’auke ta .

A k’asa Hafiz ya zauna yayi tagumi idon da yayi ja kamar garwashi.

Kallan sa Abbie yayi cikin Tausayi yace “kayi Hak’uri kaji yanzu gashi can ana kiran sallah tashi kaje tayi sallah.”

Mik’ewa yayi jiki a sanyaye ya fita daga gidan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *